Yarima Ashaman Complete Hausa Novel




 

[1/22, 6:31 PM] It'z B Y ebrerheem: YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa



Ina matuk'ar godiya ga dukkan masoyana aduk inda kuke, wasu sun kirani sunmin murnar kammala littafin NIDA D'ALIBATA, duk wadanda bana cikin grps dinsu ,inajin jinjinarku da fatan alkhairi agareni nagode sosae.naso sai new month wannan novel yafito to amma sbd wasunku sun kagara nayisa ,hakan yasa nayi sbd farincikin Ku...😍😍


GARGAD'I

banyarda wani ko wata yajuyamun novel ta kowace sigaba,sabida haka in kunne yaji.....


BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM


🅿1&2


Wasu 'yan matane  kyawawa guda 2zaune awani had'ad'd'an garden.

      "Kowaccen su da lemo na rober agabanta", yesmin da kanta ke duke tana jin haushin k'awarta kubra data tursasata zuwa garden d'in .


dan ita bata saba xuwa irin wad'an nan guraranba nashak'atawa,kasancewarta talaka kuma marainiya  .


" tarakotane sabida batason yawan jayayya."


d'ago kanta tayi ,masha ALLAH "

ALLAH yayi halitta gun wannan yarinya, dan kyakkyawa ce ajin farko ,itaba faraba, itaba bak'ba ,chacoolat colour ce ,ga dan k'amin bakinta dke d'auke da pink lips,ga golden eyes dinta ga cikakkiyar gira dke son had'e wa afuskarta sbd yawa.


Yesmin fa tahad'u ta ko ina dan duk cikakken nmjin da yaganta dole ya k'yasa...


"d'agowa tayi zatayiwa kubra magana ,kawai taji jiniya da busa, annufo gun."


Cikin dan firgita kubra tace friend ta shi dan ALLAH mubar gun nan kada yaxo yasamemu agun nan dan ba mutumcine dashiba inkatab'osa,kinga mutane na fita tun kafin ya ida isowa,ta fad'a had'e da nunawa yesmin mutanan dke fita dg cikin garden d'in.


Kicin kicin da fuska yesmin tayi tace nifa bangane mikeke nufiba ,wanene zamu tafi sbd shi??


Zaro ido kubra tayi tace dan ALLAH friend muje kada kijamana matsala ,gashi har body guards d'in sa sun fara fitowa shima yanxun zai fito ,dan inyaxo yasamemu nan zai saka a wulak'antamu dan inyaxo nan garden d'in kowa fita yake abarsa sbd bayason hayaniya komai garden d'in nanya san hakan.


"" doguwar tsuka yesmin taja ,tace wlh babu inda zani, inyazo yasameni yakasheni koyayyi gunduwa gunduwa dani .ko kansa farau sarauta ne ,ai kud'i Muka biya Muka shigo ba kyauta ,inwani abu yake tinkaho dashi ai saiya Gina ta shi yaje ya huta, bawai aci zarafin mutane afita dasuba sbd shi."";;


Ajiyar zuciya kubra tayi dan dama tasan halin yesmin bata raina kowa kuma bata yarda arainata ba.


Waigawa tayi taga har an bud'e wa ,yarima Ashman k'ofar mota dan yafito,Aida sauri taja hannun yesmin tace pls friend muje gashinan ,fisge hannunta yesmin tayi tace bbu inda zani saina gama hutawa,ta zauna ta aza k'afa d'aya kan d'aya.


"Koda kubra taga haka tasan yesmin da kafuwa,gashi ta hango yarima yana doso gurin ai da sauri tabar gun,axuciyarta tana  tausayawa yesmin akan abinda yarima zai mata..


Waigowa nayi dan ganin waye yafito a motar,wow wow lallai irin su yarima ashman ake kira one in thousands dan guy din yahad'u ta ko ina ba karya,farine dogo kyakkyawa, karfaffa ga faffad'an kirji ga wani saje bak'i sidik  daya k'ara fito masa da kyansa, hancinsa  har baka ga red lips dinshi da sexy eyes  d'in sa masu tafiya da imanin y'an mata.

Cikin nutsuwa hade da k'asaita irinta 'yayan sarakuna ,yarima Ashman yake tafiyaya nufi gun da yesmin ke zaune had'e da yiwa body guards d'in sa alamar kar su biyosa.


" sama da k'asa yakalleta ,ya yatsina fuska kamar yaga kashi."


Tsartar da yawu yyi ,cikin husky voice insa yace  WHO ARE U?


"Ashek'e yesmin ta kallesa ta d'aure fuska had'e da cewa, I don't no speak English."


da sauri ya kalleta ,azuciyarsa yace lallai zan koyawa wannan villager girl din nan hankali,nida mata ke bi suna mun biyayya sai wannan wawiyar zata rainamun hankali.


Matsawa yyi gundatake ya aza k'afarsa mai takalmi sawu ciki kan k'afarta,runtse idanunta ta yi sbd azabar dataji,kuma jin kamshin turaren sa yasa tagane shine yatakata dan sadda yanufo gun irin kamshin taji gashi taji yyi yawa akusada ita.


Cikin b'acin rai tace mlm meye haka ?kad'agamun kafa dan naga bbu alamar kasan darajar d'an Adam,tafad'a batare da ta kallesa ba.


Tsaki yaja,yace keda dabba duk d'aya kuke aguna, dan naga bakida kunya had'e da tarbiya....


Cikin bacin rai hade da tsanarsa yesmin ta katsesa ,da cewa ya isa haka ,ai duk marar kunya da tarbiya yabiyo bayan ka,ta fada had'e da janye  k'afarta da karfin tsiya.


Wani wawan mari yarima Ashman yayiwa yesmin yana huci,Wanda Saida jinta yadauke na wucin gadi.


Cikin bacin rai yanunata da yatsa yace ki iya bakinki ko ke wacece,nafi karfin mace tagayamun magana wlh wawiya dke sokuwa.


Dafe kuncinta yesmin tayi  cikin jin xafin Marin tace ALLAH ya isa mugu....wani Marin yasake yima ta ,aibata yi watawata ba ta dauki lemon dke gaban ta watsa masa ajikin fararan suit dinsa.


Cikin damuwa tsananin mamakinta da al,ajabinta yake kallon kansa,atake ransa yyi mummunan b'aci dan bbu Wanda yataba yi masa irin wannan wulakancin sai ita.


Cikin haushin ta had'e da tsanarta yyi gunta rai bace."


"Ita kuwa yesmin ganin yanayinsa yasa ta tsorata matuk'a musammun dataga ya nufota ."


"Aida sauri tayi baya ta Neman guduwa."


Taku biyu yyi yasa hannunsa ya fincikota ,had'e da janta yanufi gun motar guda dg cikin motocin dayaxo.


"Itakuwa sai k'ok'arin kwatar kanta take takasa,domin ta tsorata tanagudun kada yyi mata wani abu, dan tatsani ayi mata fyad'e arabata da martabarta.


Hakan da ta tuna yasata ,sake tsorata.


Shikuma yarima azuciye yabud'e gdn baya yawurgata yarufe,be damu da yadda guards d'in sa da ma'aikatan gun ke kallonsuba .


Bude gidan gaba yyi yashiga had'e da yimusu,alamar kada Wanda yabiyosa ,atsiyace yaja motar yabar gun........😍😍


Hmmmmmmm tofa fans ina jinku me zakuce??


Share pls

[1/22, 6:31 PM] It'z B Y ebrerheem: YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Wannan page din nakine miss Zarah marubuciyar ASEEYA kiyi yadda kkso dashi, ngd sosae da kulawarki gareni.


🅿3&4


"Yasmeen takai k'ololuwar tashin hankali da firgita inbacin kakkarwa bbu abinda jikinta keyi,sai kok'arin b'alle marfin motar take amma takasa."

        Cikin tsoro had'e da tsiwa take cewa wlh mlm ka'ajiyeni ko ance maka ni y'ar iskace ne?dazakazo dani wannan mugun da jin ne.

"Aibaka isa cikakken nmj ba,indakakai da inda namaka laifin zaka dauki mataki amma wai baka satoniba."

       Banxa yyi da ita kamar tana magana da bango saima yakur'e volume din wak'ar music yana sauraro ko gundatake bai kallaba yacigaba da tukinsa.

Itakuwa data gaji da rashin kunyarta sai tayi shiru tana adduar kubuta dg hannunsa.

Bata auneba taga yyi parking agaban wani had'add'en get house nashi na shak'atawa Wanda ko mai martaba baisan yanada gidanba.

",fitowa yyi fuska a tamke ,yabud'e gidan baya da nufin ta fito amma sai ta k'i fitowa ma dg motar,kwafa yyi yasa Zara zaran hannayensa ya fincikota ,tana tirjewa had'e da zaginsa ,amma bai tsayaba yyi cikin gidan da ita.

     " wani dakine yawurgata ciki ta fad'i k'asa kanta yabigi tayis d'in dakin",sannan yarufeta ciki yafita .

Ido kawai yasmeen ke zarewa ,inbacin rawa bbu abinda jikinta keyi dan tasadak'at Repin dinta zaiyi".

Be jimaba yadawo da ga shi sai farar jallabiyya ajikinsa  yanufi indatake zaune ,Aida sauri ta rik'a ja da baya had'e da runtse idonta tana salati da Neman tsari dashi axuciyarta.

       "Koda taji k'amshinsa sosai tasan yazo gab da ita cikin rawar murya had'e da yin kalar tausayi tace pls kayi hakuri natuba ,bazan sakeba kaji tsoron ALLAH kada ka rabani da martabata.......wata doguwar tsuka yaja had'e da tafa hannayensa yace me Kika d'auka da zanmiki?"

girgiza kansa yyi yace you are a big loser Ashe rashin kunyar taki ta cikin cokalice ,ainazata girman kanki da ixxa baxasu barki kibada hkuri ba. Oh kindauka ni yarima zan iyayin wani abu dke ,to never nafi k'arfin hakan ,keko dogarawana  ra guards dina sunfi karfin yin hakan dke Balle ni sbd ke baki daga cikin tsarin irin matan dasuka amsa sunan su mata irinkune suka rako mata duniya.yasmeen batace komaiba saidai zuciyarta kamar ta fashe sbd tak'aicinsa da irin bak'ak'en magana ganundayake gaya mata. "

Kallenta yyi ayatsine yace dalilin d'aukoki shine ki wankemun kayan da Kika bata sannan ki koma gida inkink'i kuma to zaki iyayin shekara anan har sai kin wankesu sannan kifita anan gidan!"ke bakikai darajar dazan saki wankiba nadai sakakine sbd ke Kika b'atasu dan.....cikin tsawa tace ya isah haka kayadaiko to bazan wankeba nafi karfin inyima wani k'aton gardi wanki ALLAH yakiyaye wlh.


"dariyar rainin hankali yyi yace ok ba damuwa zaki iya kwana anan har sai sadda kikayi obey tukum kin koma gida." Yana fad'a yafita yarufe k'ofar da k'arfi.


"Zama tayi tacigaba da kuka da tunanin gida."


can taga kuka bana ta bane gashi har 6:00pm tayi ga 7:00pm ake magrib inhar ta wuce magrib batadawo gd ba ,batasan irin tashin hankalin da umman ta da yah Omar zasu shigaba.


"Kawai saita mik'e ta isa gun k'ofar ta nata jijjigata tana bubbugawa."


can taji karar anasa makulli za'a bude.


Baya tad'anyi dg gun k'ofar ,yana budewa yakalleta yana murmushin mugunta yace kincanja shawara ne?


"Tsaki taja hade da hararansa tace kabani inwanke abudemun intafi gida."


Sama da k'asa yakalleta yace kinceci kanki daga yauma kisake gwada yiwa wani nmj rashin kunya.....


Cikin tsiwa tace aikai ba nmj bane dan naka cika ba ,matsoracin nmj ne kai kuma raggo ai inda namaka laifin zaka dauki mataki amma ba kasatoni nanba.


Baki b'ude yake kallonta yana mai maita raggo,azuciyarsa lallai yarinyar nan  da wlh ni manemin matane Dana nuna mata kuranta nacemun raggo.


Amma a fili sai yyi tsaki yace nike cikawa baki kinamun rashin kunya,bacin kina hannuna sai yadda nayi dke ko?


"Murguda baki tayi tace abani na wanke "


Fita yyi bbu jimawa yadawo da kayansa data bata yajefeta dasu,had'e da nuna mata bayi yace komai na ciki ki wanke dakyau dan inbasu fitaba zaki canja.


Cikin wani bak'in ciki daya tokare mata zuciya had'e da mamaki ,wai ita yasmeen zatayiwa wani gardi wanki,ta dauki kayan ta wuce toilet din dake d'akin.


"Batafi 15 minit ba tafito da bucket din da kayan ke ciki ta bude k'ofar ta fita."


A parlour tasameshi zaune ,fuska adaure ta aje bucket din tace gashi abudemun na fita.


Ko kallonta beyiba ,yakai5minit tukum yaduba kayan yaga sun fita d'auka yyi yabar parlourn bbu jimawa yadawo had'e da watsa mata yan sauran ruwan dke cikin bucket din.

dan zabura tayi tana  maijin mugun tsanarsa kuma tad'auki alkawari suka sake had'uwar saita nasa abinda baya tunani.


K'ofar yaje yabude ,beyi maganaba yadai tsareta da firgitattun sexy eyes dinsa.


"Aida sauri ta zo ta bi gefensa ta fita ,tana fita ta juyo taganshi zai rufe k'ofar ta ce ALLAH ya isa mugu azzalimi dan is....Aida sauri ta arce ganin yabiyota ta bude get din ta

fita.


" murmushi yyi dan tabasa dariya ganin akwaita da rashin kunya amma sai tsoro, tsaki yaja yakoma had'e da cewa gobema kiyiwa wani rashin kunya."


Yasmeen na fita, ta tsorata da yadda taga hanyar ba kowa ga dajine,axuciyarta taita tsinewa yarima.


"Gudu takamayi can ta fito bakin titi shima sai motoci jefi jefi ke wucewa".


Nan tacigaba da tafiya,kamar dg sama taji ance yasmeen.


da sauri ta juyo dan ganin me kiranta.


" wani Habib ne d'an anguwarsu ,zai wuce da mashin ,ai da sauri ta tsaya suka gaisa ta tambayesa gida zashi yace eh.


Nan ta hau bayan mashin din tace da sun shigo anguwarsu yasauketa ta ida da kafa ,yace to nan suka tafi.....


Ahanya yake tambayarta ina taje ,?nan hanyar dabata da kyau".


K'arya ta masa tace wata course mate dinta ce key in bath day ,shine taje kuma bata ganeba ganin marece yyi tadawo.


Habib yace gara dakika dawo sbd hanyar batada kyau.


Bayan sun iso ,yasauketa inda tace,ta yi masa godiya sannan ta ida isa gida.


Tana shiga ana kiran magrib,umma ce tsakar gida ke alwalla.


Nan tace yasmeen ina Kika tsaya sai yanxun har magrib tayi?


'Cikin inda inda tace umma bansami abin hawa da wuriba ,ga bamugama lakca da wuriba.


Umma tace to ai Alhmdllh tura kindawo lfy jejiyi alwallah.


To tace taje tayi ta wuce daki....


WANENE YARIMA ASHMAN??......


Share pls

[1/22, 6:31 PM] It'z B Y ebrerheem: YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


hakik'a banida bakin godiya ga masoyan wannan novel,inajin dadin yadda kuke sonsa tun kafin ayi nisa sannan insha Allah zaku ruk'a samun 2page kullum indai banida wani uxuri,amma banyi alkawariba,nagode sosai love u all💋💋🌹


🅿5&6


WANENE YARIMA ASHMAN?


Yarima Ashman saurayine matashi d'an kimanin shekara32 aduniya .

     Yana tak'ama da ilimi,kud'i,saurauta had'e da k'asaiita",bayason raini ko kad'an kuma bayason shishshigi,akwaisa dason girma."gashi miskiline na karshe dan yanada girman kai haka jama'a ke cewa dan in yayi maka magana sau daya ko biyu bazaisake ba,kuma bayashiga abinda be shafesaba.

       Barrister Ashman kenan ,lauyer ne mezaman kansa yakammala karatunsa na law a k'asar jodan. Ayanxun haka yazama cikakken barrister ,baya shigarma masu kud'i akan kara ."talakawa yake taimako kuma kyauta baya karbar ko sisinsu ",dan shi aganinsa bbu mai kudin daya isa yadaukesa lauyensa har yabiyasho,hakan yasa  talakawa ke mugun sonsa  suna kaunarsa", ko guri zaibi ya wuce zakaga anatafi  ana d'aga masa hannu hade da yima sa kirari.

" hakan yasa yyi suna sosai ko ina agarinsu ,kuma masu kud'i marasa tsoron ALLAH basa sonsa."

        Yarima mutumin kirkine don baya shaye shaye da Neman mata irin na samarin yanxun ga kuma uwa uba ilimin addini dayake dashi.

"Maimartaba isma'il khaleed sarkin bauchi  shine mahaifinsa ."

        Yanada mata2 hjy falmata da hjy rahama ,hjy falmatace uwar gida tanada yara5 lubna ,Ashman,Hanna,sadeeq,sa Auta salim.

Hjy rahama tanada yara3sameera ,sageer sai Maryam."family ne  dke zaune lfy cikin ganin mutuncin juna da girmama nagaba da mutum."

Yarima iyayensa nasonsa da danginsa dan inkagansa gaban amminsa tana lallab'asa saikace shine Auta.yanada son yara sosai fan kanwarsa dke bimasa tanada yara twins munib da muniba ,yarima nason yaran sosai sun shak'u da yaran har shopping yake musu yaje gidansu yakai musu ", kowa yana mamakin sa dan inbada daliliba baya zuwa gidajen yan gidansu mata masu aure ba."

       Tun bayan yarima yafara aiki mai martaba  yaso yyi aure amma sai yace ai yarinyar dazai aura  bata ida karatuntaba .

Hakan yasa sarki yasharesa kafin yyi lokacinsa .

"Yarinyar da yarima keson ya aura wato salma ",yanason ya auretane sbd tana mugun sonsa dan ita ta tura kanta gunsa,ta dauki tsawon shekara tana binsa tana rokar soyayyarsa  dg karshe yaga zata kashe wata yarinya sbd shi,daganan yaga zai iya aurenta tunda zata iya komai sbd shi,amma bawani sonta yakeba,tabbas ya yarda akwai so amma shi aganinsa yafi karfin zubda ajinsa yace yanason mace saidai ita tace tana sonsa.

" da kyar ya amince ma salma zai aureta amma yana mata wulakancin da yaga dama dan inba ita takirashiba baya kiranta ,kuma kota kira saiyagadama yad'aga kiran."

Yahad'u da salma a akasar Jordan itama tazo karatu har ya kammala karatunsa yabarta yanxun saura shekara1tayi degree dinta tadawo Nigeria kuma itama yar bauchi ce.

"Tana mugun sonsa musammun a cikin kawayenta tana alfahari dashi,shikuwa yana juyata kamar bante,ko wani guri zata saita kirasa ta tambayesa ,inyace bazatajeba to ko iyayanta sunce taje bazata jeba.

       " alokacin dasuke tare akasar Jordan yayimata alkawarin zai aureta hakan yasa ta nuna masa ko romancing juna surikayi,yanuna ma ah ah had'e da yin fushi sosai da ita dan nuna mata yyi zai iya rabuwama da ita akan hakan Dan yatsani mace marar tarbiya.kuma bawai dan bayada bukatar hakanba ah ah,saidai yana tsoran aikatawa da zunubin da zai daukarwa kansa.


Salma yarinyace yar kimanin25years tataso cikin gata dan iyayenta sun batata da kudi tana yadda take so.


Salma Nada wani boyayyen Hali danbakowa yasantadashiba ko yarima bai saniba.


"Y'ar lesbian ce ta bugawa ajarida ,inataga yarinya ta mata tofa duk yadda zatayi sai tayi tabiya bukatarta da ita,Wanda a Jordan ne ta lalace tazama yar lesbian gakuma  shaye shaye tanayi.


" saidai bata taba bari yarima yaganeba."


dan ita tana sonsane amatsayinsa na kyakkyawa kuma dan sarki amma bawai dan yabiya mata wata bukata ba in ya aureta.


WACECE YASMEEN?


Yasmeen yarinyace yar kimanin shekara 18,mahaifinta mlm ahmadu yarasu shekara2da suka wuce Wanda shiga akayi har gida aka kashesa amma ba'son kosuwa sukayi kisanba kasancewarsu talakawa.


Mariya wato umman su yasmeen asalinsu yan yolane fulanin can fatauci yakawo mijinta da yayansa Kawu bala agarin bauchi har suka zauna da iyalansu.


"Yasmeen su biyune agun iyayansu daga yah Omar sai ita ."


Sunsha wahalar rayuwa bayan mutuwar ubansu.


",Kawu bala mugune na karshe mai matuk'ar son abun duniya da had'ama ga ganin gari dan zai iyayin komai sbd kud'i".


Yanada mata 1da yara 4bashir,Rukayya, saude sai Musa.


Bashir da'ake kira da bash tantirin marar mutuncine bayada aiki sai Neman mata dayiwa yara fyade ,askul d'aya suke da yasmeen tana 100level yana 400lavel.


Kawu bala bayan rasuwar mlm ahmadu wato mahaifin yasmeen duk Dan abinda yabarmusu Saida ya k'wace da karfi da yaji harda filing daya fara ginawa sukoma da iyalansada kasancewar gidan haya sukewasu tumaki5da shanu2dayake kiwo duk yakwace.


Umma mace mai hakuri da kawaici batace komaiba tabarsa ga ALLAH.


" hakan yasa  suka tagaiyara ko abinda zasu ci gagararsu yake ,mai gidan dasu zaune yace su zauna kyauta yayafe musu kudin hayan.


Umma nayin wankau da surfe da haka suke cin abinci ga karatun yah Omar.


"Awahalce yah Omar yakamma NCE dinsa ,itakuwa yasmeen tana gama secondary skul tadakata da zuwa skul.


Cikin ikon ALLAH yah Omar yafara faskare yana siyarwa ALLAH yasa ma abun albarka jar yayi dan shago na langa langa yana siyarda kayan tireda,umma nayin cincin Nome ,aya ,anasiyarma ta ak'ofar gida gun da yah Omar keyin tired a.


" da haka har yamaida yasmeen a skul yanxun tana label 1 sannan yasayi fili yyi daki1da bayi suka tashi suka koma gaba daya yah Omar shine gatansu.dan shi bayata karatunshi burinshi shine yaga yasmeen takammala nata karatun dan mugun jida ita yake sosai.


AKawai wani Alh jamilu ,dan siyasane kuma ,mutane suna zargin dan mafiyane dan ba'asan meye sana arsaba.


Yakasance yana auri saki yanada matarsa uwar gidansa ,gidanta daban yake.


sannan yanada wani had'adden gida can yake auran yan mata yakai duk wadda ya aura batafin5or8month yake bata Jan kati ya auri wata dan barin kudi yake ma mata har su yadda su aureshi duk wadda ta yi  shekara 1to ta Dade .


Anacikin haka yaga yasmeen xata skul abakin titi yaganta,duk yarufe ta tafi da imaninsa.


Cikin kwana2 yyi bincike akanta yagano komai har da mutuwar ubanta da cutarsu da Kawu bala yyi ,yajikuma Kawu bala Nada son kud'i,ai sai yaji dadi sosai.


Nan yaje har gida yafadamasa bukatarsa nan Kawu bala ido ga kud'i ya yarda  ,had'e da cewa duk runtsi sai ya auri yasmeen ne bar gidanba Saida yana Kawu bala dubu Dari biyar yace wannan somun tabine."


Shikuwa Kawu bala yagama shawara soyake kawai ya fidda rana yaje yasanar da umman yasmeen dan yagama yanke hukunci,Ammafa injisa.


Kuma sun yi da alh jamilu bayan kwana2yadawo yaji abinda ake ciki.


Cigaban labarin...


Share pls

[1/22, 6:34 PM] It'z B Y ebrerheem: YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Wannan page din nakine FATIMA ZOIS marubuciyar ZARAH TAWACE  kiyi yadda kkso dashi ina mugun jidake irin sosai dinnan😍😍


I'M SICK PLS I NEED YOUR PRAYERS👏🏻😰😰


🅿7&8


Cigaban labarin..


""" bayan yasmeen ta idar da sallahne,suna zaune da Umma suna fira yah Omar yashigo d'akin,da sauri yasmeen ta tashi tana masa sannu da zuwa ta karbi ledar hannunsa."

     Budewa tayi ,murmushi tayi tace Yayana nid'aya nagode,zama yyi yana yar dariya yace baby (dayake haka yake kiranta)duk mijin da kka aura yabani da zaryan siyan fura any time.

"Keko gundurarki batayi?" Murmushi tayi tace ni bata wani gundurata wlh ,ko umma nah?

       Girgiza kai umma tayi tace eh hakane tunkina karama kike sonta.

"Tashi tayi tace barama nadama abata,nan tafita tsakar gd", umma takalli yah Omar tace ga abincinka nan!to yace had'e da jawo kular yyi bissimilla yafara ci,saiga yasmeen ta shigo da kwano da ludayi.zama tayi suna fira abin kwanin sha'awa,yah Omar be fitaba sai da aka kira isha'i.


**** **** *****


Washe gari byn yasmeen ta gama ayyukan gd ta shirya dan xuwa skul,tana fitowa dg gida yah Omar zai shiga nan tafara masa shagwaba adole saiyakaita skul.

" yar dariya yyi dan yah Omar akwai saukin kai yace to baby muje."daa,kayan sana'ata zanfito dasu amma muje nakaiki,turo baki tayi,shikuwa gd yakoma yafito da mashin ta hau suka wuce skul.

"Yana ajeta ,kubra data hangosu da sauri ta nufosu dan jiya tunda yarima yatafi da yasmeen bata runtsaba."

       Kallan yah Omar tayi tagaidashi cikin sakin fuska ya amsa had'e da yiwa yasmeen bye bye yatafi abinsa.

"Kubra taja hannun ta tace my friend wai ina yarima yakaiki jiyane?"dan wlh banyi baccin kirkiba nayita addua ALLAH yasa kada yyi Repin dinki. wata doguwar tsuka yasmeen ta ja had'e da cewa ni wlh har ma na manta da wannan sarkin girman kan,nanta labartamata yadda sukayi dashi.

" ajiyar zuciya kubra tayi tace to Alhmdllh tunda baimiki komai ba, nima nayi tunanin bazai mikiba k'ila  sbd gsky mutumin kirkine haka naji abakin jama 'a.

      "Yatsina fuska yasmeen ta yi tace can ta matsemasa", amma nayi alk'awarin duk sadda Muka sake haduwa dashi saina masa rashin mutunci"wlh."

Kubra tayi y'ar dariya tace hmmm kibidai ahankali wlh nidama yace yana sonki don zakuyi matukar dacewa da juna wlh,zaro ido yasmeen ta yi had'e da bankawa kubra harara tace ALLAH yakiyaye dan natsanesa wlhy kadama kisake wannan tunanin. ta fad'a rai bace, had'e da cewa ni ba sa'ar soyayyarsa bace!sbd ni talakace ba yar kowaba,kuma ko ba hakaba bazan soshiba,inkika sake mun irin wannan maganar to zamu rabu wlhy.

"dafa kafad'arta kubra tayi tace ALLAH yabaki hkuri ,ban fadaba dan inbata miki raiba ALLAH yahuci zuciyarki,nan taja hannun ta had'e da kara bata hkuri suka wuce dan daukar lectures.


___________________


da misalin karfe 12:30pm  su yasmeen neda kubra zaune a cikin k'awayensu,bayan sunfito dg lecture. Sai fira suke kafin ashiga wata .


" kamar dg sama yasmeen ta ga bash gabanta ,yana wani cika yana batsewa."


Sai wani cin magani yake shiga Wanda ake tsoro a skul din.


"3quarter ne da t shart ajikinsa yyi wani dan iskan aski,irin na tantiran yan duniya,cikin isa yakalli yasmeen sama da k'asa yace ke zo ina son magana da ke.


" banxa tayi dashi ta nunama batasan dashiba."


Sukuwa k'awayen su jininsu akan akaifa yake kada bash yahad'a dasu dan sunsan bashshida mutumci ko kad'an.


"Koda yaga taki kulasa, cikin fushi yace ke dabbar inace?" ina miki magana zakimun banxa.afusace yasmeen ta tashi tsaye had'e da nuna sa da yatsa tace kai wawa Wanda baisan ciwon kansaba,me ruwanka danine?da har kake shiga rayuwata haka ajeni kayine da zaka kirani duk sadda katashi to ni yasmeen nafi karfin hakan ga kowane jaki kuma inason kas.....wani wawan mari bash yyiwa yasmeen har Saida tafad'i k'asa ta kife bakinta ya fashe ya na jini.


"Azuciye bash yyi kanta yana cewa yau zaki son koni wanene ,zaki gane gwamma kid'a da karatu dan ko wannan sakaran Omar din be isa ya kwaceki a hannunaba ni zakiyiwa rashin kunya ,yafad'a yana tunkararta,ji yyi an rik'e masa hannu wa ta baya...."


Yasmeen kuwa sbd galabaita kasa tashi tayi,jitayi ankama hannun ta and'agowa tana d'agowa wazata gani...?


Hmmm tosu wanene suka rik'ema bash hannuwa?


Shin wa yasmeen ta gani?


Domin jin amsar wannan tambaya muhadu a page nagaba...


Yawan comments yawan typing....😇😇


Share pls

[1/22, 6:34 PM] It'z B Y ebrerheem: YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Sakallahu bi khairan ga masoyana aduk inda kuke .hakik'a adduo inku sunkarbu nasami sauki .wadanda suka kirani da masu text message ngd ana tare🤝🤝.


🅿9&10


Afusace yasmeen ta k'wace hannun ta da k'arfi ganin yarima ne tacigaba da galla masa harara.

"Wani mugun kallo yyi mata dan Saida tad'ago yagane itace  dan dayasan itace wlh dabazai taimaka mataba sbd sadda yahango abinda ke faruwa yana nesadasu,sadda ya iso har yamareta ta fad'i."

      Itakuwa yasmeen kallon dogarawa da guards din yarima take ganin sun rurruk'e bash dogara natamasa bulalai masu rai da lfy .

"Cikin kasaita had'e da Jan aji yarima yyimusu alamar su daina su biyoshi", nan yanufi gun motarsa da sauri akafito da kujera yazauna aka matsa da bash gabansa,nan yyi kneeling yana ahi da tuba yana bada hkuri.

    Kwata kwata yarima beso bimata hakkintaba dandai kawai ga idon jama'a inyafasa yyi karanta kuma dan ALLAH yyi.

" kallon bash yyi yawani yatsina fuska kamar yaga kashi yace shot up your mouth "!

Tsit bash yyi yana tsoran kada asake tozartasa agaban mutane  ,dan dayasan haka zata faru dayabarta yasameta har gd yyimata rashin mutunci.

    " cikin kakkausar murya yarima yace kaji kunya kato dakai kana sa insa da mace harka daketa wato kune bata gari to zansaka akoreka dg skul din nan."dukawa bash yyi yana k'ara bada hkuri",nandai yarima yyi masa last warning inyasake kamasa saiya yabawa aya zakinta. Nan bash yatashi yana godiya yatafi."


Yasmeen kuwa tabbas taji dad'in taimakonta da yarima yyi amma  sai fa tacika alk'awarinta datayi nayi masa rashin mutunci.


"Koda tahango yasallami bash kawai saita dauki viju milk din dke gabanta ta nufi gunda yarima yke."


Wani murmushin mugunta tasaki data iso gunsa,shikuwa yatsina fuska yyi yana mata kallon tsama yace ke stupid girl lfy  zakixo kina mana wani iyayi naki.


"Ahankali tace nazo nayimaka godiyane."


"Cikin jin haushinta yace banyi dankeba dan ALLAH nayi."


Kafin yasake magana tayi wuf tawatsa masa viju milk ajiki har fuskarsa Saida tasamu.


Wani mugun bakin ciki,haushi ,kunya nadamar saninta da taimakonta da yyi duk yaji azuciyarsa.


Da sauri yasmeen ta fara k'okarin guduwa sbd tsoron hukuncin dazai mata.


"Yarima kuwa ko afuska be nuna yaji haushin abinda tamasa Co's aitayine dan tab'ata masa rai ,dayake namijin duniyane saibai nuna yadamuba.


dogarawansa yaga sun nufeta da sauri yyi musu alama su kyaleta.


Cikin mamakinsa yasmeen ta bar gun jiki asan yaye.


"Shikuwa yarima cikin bak'in ciki yabar gun yashige mota 'dan dama gun wani lacture ne abokinsa yazo besamesaba yahango bash nayiwa yasmeen haka shine yaje dan yataimaka mata yaga itace.ga idanun jama'a akansa ana mamakin rashin mutunci irin na yasmeen ace mutum yyimaka wannan taimakon amma tasaka masa da haka."


Itakuwa yasmeen tayi tsantsar nadama da Dana sani akan abunda tamasa .


"Cikin bacin rai kubra ta bud'e mata wuta tana mata fada da nuna mata rashin kyautawarta ga yarima ."


Fad'awa jikin kubra tayi tana kuka had'e da cewa wlh nasan ban kyautaba da nasan inda zan gansa da wlh naje nabasa hkuri wlh.


Tsaki kubra tayi tace bakin alk'alami ya bushe ,ki saurari hukuncin dazai miki agaba in kunhad'u.


Tuni yasmeen ta k'ara tsorata da nadama ,dan gsky bata kyautaba da yanxun bash yyi mata abinda yaga dama dabai cecetaba.


Nan kuma taba kubra tausayi,ganin tadamu sosai nan ta kwantar mata da hankali har akatashi dg skul suka tafi gida,yesmeen gaba d'aya da damuwa ta yini.


         ********

6angaren yarima kuwa kamar yahad'iyi zuciya dan bak'in cikin tozarcin da yasmeen tayasa.


Wani mugun tsanarta yasakeji hade da haushinsa ,amma yadauki mummunan kudiri aduk lokacin dasuka sake had'uwa da ita.


"Koda suka isa gd part din sa ya wuce yaje yasake d'aukar wani babban wanka cikin kananun kaya yyi masifar kyau duk macen data gansa dole ta k'yasa,saidai fuskarsa bbu walwala."


Koda ya ida shirwa part din amminsa yawuce.


A parlourn ta yasameta ta  d'an kishingid'a kuyanginta namata fita da tausa ga kayan marmari agabanta."


Sallama Yy ya zauna ,nan kuyangin suka fita bayan sun mik'a gaisuwarsu ga yarima.


Amminsa ta kallesa atake tagane yana cikin damuwa.


Cikin kula tace my son lfy naga kamar kana cikin damuwa?


"girgiza kansa yyi yace ah ah kainane kemun ciwo."


Badan tayardaba tasharesa,can tafara jansa da fira nan tace my son akawo maka fura mutuniyarka?


Aibaisan sadda yyi murmushi ba sbd yanason fura arayuwarsa baya gajiya da Shanta,da sauri yace eh ammi nah zan sha.


Nan ta Danna wata karaurawa saiga wata guyanga,tazo ta xube gabanta t ana cewa ALLAH shi taimakeki ,nan ammi tace ta kawo fura batafi minti3tadawo da kwaryar fura ta aje ta fita.

"Nan yarima yabude yyi bissimilla yafara cika ludayi bebar furarba Saida yaji cikinsa kamar zai fashe tukum sannan ya aje,sai dariya amminsa ke masa."

Fira suka fara jefi jefi shida ammi har Auta salim yadawo dg skul yazauna ana firardashi.

      Duk sai yarima yaji azuciyarsa wasai yadaina jin wannan b'acin ran da yasmeen ta haddasa masa.

___________________

Bayan kwana2 Kawu balane zaune yana tunani,can yace bari naje ayita takare da zafi zafi ake dukan k'arfe.


"da sauri yafita yaja mashin bai tsaya ko inaba sai k'ofar gidan su yasmeen."


Kafe mashin din yyi zai shiga ciki,saiga yah Omar da yahangosa yazo yaduk'a yagaidashi,ayatsine ya amsa yana wani harare harare.


Shikuwa yah Omar yagaidashine sbd umarnin umma amma badan halinsa ta horesu da su cigaba da bashi girma  da daukarsa uba duk abinda yyimusu shida ALLAH.


Amma yah Omar yaji fad'uwar gaba sbd duk sadda Kawu bala zaizo to bazun alkhairi yakeba da sharri yake xuwa.


"Haka yah Omar yazauna jiki asan yaye."


Shikuwa Kawu bala ko sallama bbu ya kutsa kai cikin gidan da wata roba yaci karo beyi wata  wataba yatakata had'e da yin kwallo da ita.


Umma dke zaune tsakar gd koda taji haka tasan balance dan duk sadda zaixo to haka yake yi inxaishigo.


Saurin rufe jikinta tayi ,yana shigowa tace Yayana ina wuni ?


Tsaki yaja yace kirike gaisuwarki tamiki amfani,dalilin xuwan nan shine dan insanar dake matsayina nah uba ga yasmeen nazaba mata mijin daya dace da ita.


Wato alh jamilu bushasha kenan.


Cikin bacin rai umma tace bala! bala!! baala!!!cikin kakkausar murya dan yakaita bango tace wlh ! Wlh!! Wlh!!! Abinda bazai taba faruwa kenan ba matukar ina Raye bbu Wanda ya isa yasiyarmun da y'ar mutumin da ake zarginsa dan mafiyane dan zalinci zaka aurawa yasmeen.


Baki sake Kawu bala ke kallon umma dan Saida yau tayarda mai hkuri bai iya fushiba.


"Cikin boron kunya yace kisaka ido kiyi kalllozan nunamiki na isa da yayan d'an uwana,yana dadin haka yafita afusace.


Yasmeen dke daki Ta's tagama jin komai da gudu tafada jikin umma tana kuka Dede nan yah Omar yashigo yana tambayar lfy dan yaga Kawu bala yafita afusace.


Nan umma ta labarta mai komai hade da cewa yamaido kayan siyarwarsa gd yanxuN zasu tafi yola shida yasmeen sai komai yadaidaita sudawo.


Ba musu ya fita nan umma ta had'a musu kayan su acikin akwatai ,yana dawowa tace kaje zan kira baba mlm away a kafin Ku isa ALLAH yakiyaye nan yah Omar yaja hannun yasmeen suka fita.


Ita kuawa umma suna fira ta fita tanufi gidan aminiyarta atika.


Bayan sun gaisa ta zaiyana mata abinda ke faruwa had'e da cewa meye shawara?


Arika tace abu mai sauki kije gun yaron nan yarima indai Kika masa bayanin komai to insha Allah zaibi miki hakkinki.


Zaro idanu umma tayi tace aibamuda abinda zamu biyasa ,atika tace abu mai sauki ai kyauta zai miki shifa taimakon talakawa yake  kuma dan ALLAH.


Kibari ga Yahaya nan zai fito da adaidatarsa saiya mikaki offishinsa ai yasani indai akabarki Kika gansa tofa insha ALLAH damuwarki ta kare.


Nan Yahaya yafito mahaifiyarta tace yamika umma babu musu yace to nan umma bisa waje sukayi sallama da atika.


Yahya yabudema umma ta shiga yaja adedetar had'e da Baron anguwa r....


Share pls

[1/22, 6:34 PM] It'z B Y ebrerheem: YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿13&14


Jiki ba kwari suka nufi cikin kotun .

Yarima yakalli umma yace mama kije ganinan xuwa,to tace ta shiga cikin kotun.

      Shikuwa yarima gun mota ya wuce yadauko rigarsu ta lauyoyi yasaka aisanaga ,haibarsa da kamalarsa had'e da kwarjinsa sunsake bayyanah.

"A cikin kotun kuwa kowa ya hallara alkali da barrister's kawai ake jira."

Kawu bala kuwa inbacin harara bbu abinda yake aikawa da Umma dan tunani yakefa kada allura ta tona galma.

Alk'aline yashigo kowa ya mik'e tsaye bayan ya zauna kowa yazauna.

     Megabatarda da kara yagabatar had'e da tambayar lauyoyin masu kariya su fito.

"Cikin takun kasaita yarima yashigo sai kallonsa ake " wani mugun kallon tsana da k'iyayya Kawu bala da alh jamilu suka aikama sa,sarai yagansu amma sai yanuna be gansuba dan tunda yashigo idanshi ke Kansu musammun alh jamilu dan besan balaba amma ganinsu tare yasa yagane balane.

Nan shima barrister saminu yazo yabaiyana agun.

      Alkali da abukaci ganin umma gabanta,bbu musu ta fito alk'ali yyi mata tambayoyi akan abinda take kara nan ta sanar da shi kamar yadda yarima yafad'a mata.

Sannan aka bukaci Kawu bala yafito ,cikin fad'uwar gaba da muxurai bala yafito nan alkali yyi masa tambayoyi yana amsawa cikin inda inda.shikanshi alk'alin yalura bbu gsky atare da bala.

   "Yarima kuwa sai murmushi ykeyi yana cewa good".

Bayan alkali yagama yiwa bala tambaya ,yabukaci ganin alhj jamilu.

Bayan ya fito alk'ali yakallesa yace Kaine Wanda bala yabawa auren diyar k'aninsa ? Alh jamilu yace eh!

Alk'aliyace kuntab'a magana da yarinyar kunsan juna?yace ah ah ,alk'ali yace yaje ya xauna.

    Bayan yyi yan rubuce rubuce yace lauyoyin masu kariya ko kunada tambayoyin dazakuyi?

" da sauri yarima  yad'an rusuna yace akwai yahmai girma mai shari'a ,alk'ali yace kotu tabaka dama barrister.

Nan yarima yace inason ganin bala agaban kotu.

Nan Kawu bala yafito kamar zaiyi xawo sbd yadda yatsorata ainun lol..

Yarima yakallesa yace inason kagabartawa da kotu sunanka da matsayinka agun yarinyarda zaka aurawa alh jamilu bacin kasan yarinyar bata sons....upjection my lord barrister saminu yakatse yarima had'e da cewa, yah mai girma mai sharia yakamata lauyan mai kariya yasan abinda zai rik'a tambaya sbd koba komai ai yarinyar diyar k'aninsa sace kuma yana da iko akanta tunda mahaifinta baya Raye...alk'ali yace k'orafi be karb'uba barrister ,dole ya amsa wannan tambayar.

    Wani murmushin mugunta yarima yyiwa barrister saminu.

"Kawu bala cikin in,ina yasanar da kotu sunansa da matsayinsa gun yasmeen."

       Yarima yace bayan rasuwar k'aninka wane taimako ko kulawa kabawa wannan bewar ALLAH da y'ayanta?eh...nah ..ban ..banida haline shiya sa.

Yarima yace sadda alhj jamilu yazo Neman auranta gunka kayi shawara da mahaifiyar yarinyar kafin ka amince?ah ah banyiba.

Yarima yace good ,to amatsayinka na Wanda besan cinsu,shansu,iliminsu ,tufafinsu,farat d'aya sai kace dole sai yarinyar tamaka biyayya ta auri Wanda bata so....da sauri barrister saminu yace up jection my lord yakamata lauyan me kariya yadena jifar Wanda ake tambaya da laifi  kokuma ko kuma d'ora masa laifin dabai aikata ,koba komai ai sai inyanada halin taimaka musu zai tammaka musu..

Al'kali yace barrister akiyaye."kwafa yarima yyi yabukaci ganin alh jamilu nan yafito, yarima yabuk'aci yyiwa kotu bayani wanene shi? Nan yagabatar da kansa ,yarima yakallesa yace Kaine Wanda bala yabawa auren diyar k'aninsa? Yace eh yace to yanxun kun hadu da yarinyar kunyi mgn yace ah ah.yarima yakalli alk'ali yace yamai girma mai shari'a da waddannan hujjoji nike so wannan kotu me adalci tabiwa Mariya da yarta hakkinsu gun hana Wannan auren da bala kawunta yabawa Wanda bataso ,yin auren zai iyasa Rayuwar yarinyar tagaiyara,yanxun haka Tana karatune dan taimakon kanta kasancewarta marainiya ,inason kotu tahana bala koda yawan xuwan dayakeyi gidan Mariya sbd yana daga mata hankali ita da yaranta na gode yamai girma mai shari'a..


Alkali yakali barrister saminu yace ki kanada abin cewa,yace eh yanason yayiwa umma tambaya ,alkali yace Mariya ta fito kotu nasan ganinta gabanta.nan ta fito.


Barrister saminu yakalleta yace ke mecece gun yarinyar?


"Tace mahaifiyarta".


Yace miyasa bakya son aurenta da alhj...up jection my lord yarima yakatse barrister saminu,had'e da cewa lauyan Wanda ake k'ara yasan irin tambayoyun da zaiyi, ai ba dole sai yaji dalinlintaba wannan sirrin xuciyartane  .  alk'ali yace barrister akiyaye.


" wani mugun kallo barrister saminu yyiwa yarima,shikuwa ko ajikinsa."


Nan brr saminu yace Umma taje ta zauna .


Alk'ali yyi gyaran murya yace ko akwai wasu tambayaoyi da lauyoyi zasu sakeyi ga mai kara da waddanda ake tuhuma?


Sukace ah ah.


duk'awa alk'ali yyi yacigaba da yan rube rubucensa ,sannan yad'ago yafara magana kamar haka ,bayan korafe korafe daga bakin lauyoyi musammun barrister Ashman isma'il khaleed wannan kotu ta zartar da ........😇😇menene kotu ta zartar??🤔🤔


Share pls

[1/22, 6:34 PM] It'z B Y ebrerheem: YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿11&12


Wannan page din nakune mmn shukra novels comments dinku na jiya yafi nakowa nagode sosae da nuna kaunarku gareni ana mugun tare😍😍


Basu tsaya ko inaba sai office din yarima,byn Yahaya yyi parking umma ta fito yanuna mata gun da zataje tanemi iso sannan yatafi.

      "Nan tanufi gun cike yake da securities", nan umma taje ta rakub'e tana yan kalle kalle tama rasa mezata ce ne?

Can wani yakalleta yace hjy lfy?

" ahankali tace dan ALLAH inason ganin y'allab'ai ne",nan yace ok xokibi layi nan to tace ta tsaya bayan mutum 6itace ta7.

      Haka umma taitabin layi tafi awa2 har akayi sallar la'asar tukum layi yazo kanta.

"Nan tashiga tana addu ar samun nasara", har cikin office din aka shiga da ita sannan security din yafita yabarsu."

Shikuwa yarima hakimce yke kan kujera yana cikin suit bak'ake sunyi bala'in karbarsa kansa aduk'e yana yan rubuce rubuce . umma kuwa k'asa ta duka cikin muryar tausayi tace ranka yadad'e nazo gareka kataimakamun danALLAH kamar yadda ALLAH yataimakeka! da sauri yarima yadago yakalleta duk saiyaji tabasa tausayi yji bbu dadi kamar wannan dattijuwar ta duk'a gabansa aita haifi kamarsa,da sauri yace mamah tashi Ki xauna yanuna mata kujerar gefensa.

bbu musu ta tashi ta zauna"ahankali yace ina sauraronki fad'amun damuwarki nan umma ta fad'a mishi komai da komai harda zalincin da bala yyimusu da kashe megidanta da akayi ba'asan kowanene yyi kisanba.

Ajiyar zuciya yarima yyi yace sadda akakasheshi kunkaisa asibiti anduba meya kasheshi ,?tace ah ah  Aida wuk'a ne akayi kisan.

Ok kawai yace yana tunanin alh jamilu bushasha dan gsky dole yasa ido akansa sbd mutane da yawa na zarginsa .

      "Batare daya kalleta yacigaba da cewa to yanxun bakison ya aureta ?" da sauri tace eh yace to yanxun zan mik'a case d'in kotu ,nikumane lauyen dazai kareki kin fahimta ?umma tace eh yace sannan banison kiji tsoro ko shakkunsu ki fito kifad'i gsky hakan zaibamu samun nassara akansu  insha ALLAHU .

Umma tace to insha ALLAH zanbada had'in kai."umma batabar gunba Saida yarima yatura case d'in kotu ,sannan yakarb'i Nokia dinta yasaka number ta awarsa yace duk abinda kenan zaikirata.

"godiya da saka masa albarka umma taitayi,hakan yak'arasa yarima jin kaunar matar dason taimaka mata sbd yanason talaka mai mutunci gaahikuma sai saka masa albarka take."

     Haka umma ta fito tahau adedeta ta wuce gida murna fal aranta.


Tana xuwa gida ta dauki wayarta takira baba mlm wato yayan mahaifinta Wanda yaruk'eta ya auradda ita kasancewarta ta tashi iyayenta sun rasu shiya mayemata gurbinsu.


Bayan ta shiga yad'aga suka gaisa nan tazaiyana masa abinda ke faruwa had'e da cewa tamayi k'rarsu kuma yasmeen da Omar suna hanyar xuwa gunshi.


"" nan yace to gara da ta yi kararsa dan shima bala yakaisa bango nan sukayi sallama ta kashe kiran"


Yah Omar ta kira yace ai befi awa1 su ida isaba,wayar yasmeen ta karba had'e da tambayar umma ko Kawu balan yadawo?


"Umma tace ah ah."


Nan sukayi ta yar fira tukum sukayi sallama had'e da cewa insun isa zasu kirata.


___________________

6angaren yarima kuwa bebar office ba Saida aka tabbatar masa da cewa ankaima alh jamilu bushasha da Kawu bala takardai sammaci gobe  da misalin karfe 12:pm za'a fara shariar.


"Sannan yadawo gida ,bayan yyi wanka yahuta bayan sallar isha'i yakira umma ta d'aga had'e da yin sallama nan yarima yagabatar da kansa had'e da yima ta bayanin lokacin da za'ayi shariar dakuma kwatanta mata kotun saidai yace taje kamar misalin karfe 11:am kawai dan xaimata wasu tambayoyi.


" nan tace to had'e da yimasa godiya sukayi sallama. "


YOLA


Ban garensu yasmeen kuwa sai ana kiran magrib suka isa yola.

     Kaitsaye gidan baba mlm suka wuce ,asoro suka samesa zaune shida wasu jama'a dan gidansa baka rabashi da mutane.

        "Murmushi yyi irin nasu na tsofi yace yakalli yasmeen yace ga amaryata !ga amaryata!!yar dariya tayi tace ,amaryarka tsohuwadai Tana kuma cikin gidanka ba.duka sukayi dariya nan itada yah Omar suma gaisa ta shiga ciki ,shikuma yah Omar yatsaya sukayi mgrib tukum yashiga ciki yasamu har yasmeen tayi wanka abinta.

Nan shima yaje yyi sukayi isha I akaci abinci ,sannan baba mlm yashigo sukayi ta fira dasu yasmeen  sai da dare yafara tukum yasmeen tacewa inna wato matar baba mlm ita bacci takeji ,yah Omar ma yace shima bacci n zaiyi.inna tayi murmushi tace raggaye dku kawai time k'asa zan barki ki kwana kaikuma zaure zaka kwana dariya akayi gaba d'aya.

Nan yasmeen tayiwa yah Omar sallama ta wuce dakin inna tahaye kan babban gadonta mai rumfa irin na daa."

Shima yah Omar yaje ya kwanta.


        ********

Alh jamilune keta safa da marwa a parlourn sa yana mamakin wai kamarshi wata banxar talaka marar y'anci  zatayi kara.murmushin mugunta yyi afili yace zan dauki barrister saminu inkinsan wata aibaki San wataba tunda naga yarki na kwadaitu da ita dan haka kota yaya sai hak'a na yacimma ruwa ya bushe da dariya irinta bosawa.


Wayarsa yadauka ykira bala."


Yana d'agawa bala yace wai kaji wannan matsiyaciyar k'ararmu tayi Ashe?


"Wata dariya alh jamilu yakece da ita yace hmmm karabu da ita aimune akanta ai nadauki barrister ita inama sukaga kud'in daukar barrister tunda kace ai talakawane sosai.


Kawu bala yace eh gsky can ta matse mata ai gobene haka aka rubuta jikin takardar  sammacin.


Ok kawai yace had'e da cewa to sai goben kazo sai mu wuce tare ko.


" bala yace to, nan sukayi sallama."


Da misalin karfe 11pm yarmane zaune akan katafaren bed dinsa ga lap top agabansa yana using da ita.


Kiran salma ne yashigo wayarsa ,tsaki yyi dayaga itace yashare dan bayason takura arayuwarsa musammun inyana abinda yashafi aikinsa bayason amatsamasa.


Sake kiran taitayi ,Saida ta masa5miss call akira6 yyi peaking call din,cikin shagwaba da kissa tace haba baby kanajin kirana shine kayi ignoring dina kamun adalci kenan?


Lumshe idanunsa yyi yace pls salma una wani aiki zankiraki latter,da sauri tace aikin yafini mahimmanci matsayina na wacce zaka aura?


"Atak'aice yace eh."


Cikin jin haushin kalamansa tace to nagode dan talura kwata kwata bata gabansa,katseta yyi da cewa wato fushi kikayi ko ?


"Eh nayi saina rarrasheni kabani hkuri."


Yar dariya yyi yace hakan baya cikin tsarina ni Prince ashman nafi karfin bawa mace hkuri ko rarrashinta saidai nitabani takuma rarrasheni,kuma bama kiranki kadai ba zanyi kinsan nanda 5weeks zanxo nan k'asar yin wani course na 3month kinga muna tare har kigaji da ganina.


Cikin xak'uwa tace to baby ina sauraronka, nan sukayi sallama  yakashe wayar dan yakosa sugama ya ida aikinsa.


Washe gari tun 10:30 am yarima yanufi kotun daza ayi Shari ar.


Cikin motarsa mai bak'in glass yazauna ina sauraron xuwan umma.


"Befi minti10 yahango mai adedeta ya ajiyeta ta nufo gun."


Nan yafito,umma na k'okarin gaidashi ,amamakinta taga duka yagaida ita ,cikin jin kunya ta amsa fuska sake, yarima ya zauna kan wata kujera umma ta biyosa nan yafara magana da ita dagaya mata koda sun dauki lauyer inya mata  tambaya ga irin amsar dazata bashi,sannan yafadamata yaddac xatacewa alkali inya tambayi akan me take k'ara?


Synkai kusan 30 minit yarima nakarawa umma karfin guiwa yana nuna mata yadda zasuyi ,cikin ikon ALLAH su sami nassara .


Kamar daga sama umma ta hango Kawu bala yafito dg mota shida alh jamilu.


Wani fad'uwar gaba alhj jamilu yaji shida Kawu bala dasuka ga umma na magana da barrister Ashman isma'il khaleed ,sun tabbatar shine lauyen dazai kareta....


Share pls


YARIMA ASHMAN🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Wannan page din nakune, YARIMA ASHMAN FANS grp1,2&3 kuyi yadda kkso dashi inamugun ji daku😍😍



Mmn musaddeeq &mmn Bilkisu nasadaukar da wannan page gareku nagode sosae da kaunarku gareni da masoyana baki daya🙏🏻🙏🏻🙏🏻.


🅿15&16


Wannan kotu ta zartar da hukunci kamar haka,

       Bala dole yahakura dayiwa y'ar k'aninsa auren dole ,abarta tazabi Wanda takeso".Sannan kotu tabawa Mariya damar duk sadda bala yasake xuwa gidan ta batare da ixinintaba koda tashin hankali to ta sanar kotu."

Sannan alh jamilu dole yahakura da wannan auren ,inma yyima bala hidima ko kaimasa kudin  auren to yakarb'i kayan sa.

      Wannan hukunci dole kubisa sbd wannan kotu bata lamunci acanza wata  sharia ba inhar tayi hukunci  akanta".

Alk'ali yana kaiwa nan yabuga guduma kowa yatashi .

"Yarima yakalli umma yyi murmushin samun nassara yamike  dan fita had'e da yiwa umma nuni ta biyosa.

gab da yarima zai fita yaga alhj jamilu ,Kawu bala brr saminu fuskarsu murtuk kamar an aiko musu da sakon mutuwa ,wani mugun kallo barrister saminu yyiwa yarima, murmushi yarima yyi Wanda yasan yak'ara batawa barrister saminu rai.

Ida fita yyi had'e da tsayawa gefen wasu  kujeru yana jiran umma.

" hango su alh jamilu da Kawu bala yyi suna mgn sannan suka shiga mota sukabar gun .

Umma nafitowa ta isa gun yarima tanata fara'a ,tsayawa tayi had'e da cewa 'y'allab'ai ngd sosae da da wannan taimako da karamci dakamun bazan taba mantawaba ALLAH yyimaka albarka yasa kagama da duniya lfy, cikin jin dadin addu ar ta yace ameen mama ,kada kidamu .

"Ahankali yarima yace amma mama ina ganin maganar kisan mai gidanki dukda kince anjima amma gsky zansake binkice akanta harsai Nagano ko wanene yyi kisan insha ALLAH  dan inad'an wani zargi daban.to amma zan yi tafiya wata k'asa zanyi wata3dana dawo insha ALLAH zankiraki inxo har gd sai musake binkice.

Cikin jin dadin maganganunsa  umma ta ce to amma ngdsosai ALLAH yasaka da alkhairi, murmushi yyi yace ameen ,nan sukayi sallama ya wuce gd itakuma tahau adaidaita ta nufi gd cikin farin ciki.


        *********

Bangaren Kawu bala da alh jamilu kuwa ,tafe suke cikin mota rai bbu dadi, alh jamilu cikin b'acin rai yace wlh saina nunama yaron nan kalata wlh yabi a hankali kada yaga d'an  sarkin garin nan yanemi yatakani ,naga bayan wad'anda suka fisa taurin kai bare shi karamin kwaro wlh sai inyi ajalinsa.

" bala yyi tsaki yace bar mutsiyaci wlh kamar nashak'esa ",inyasan wata ai baisan wata kaga yanxun kawai mubari ayi sati2da yin shari'ar nan sai intura yan fashi suje har gdansu yasmeen d'in su satomun ita inrufe fuska ta nabiya buk'a da ita inaga hkan xai fi,alh jamilu yafad'a yana kallon bala.

      Bala yyi dariyar bosawa yace hakan yyi nima dg nan sai a satomun uwar nahuta da ita dan tun bayan mijin yarasu naso aurenta tak'i"alh jamilu yace tabbas haka xamuyi nan suka cigaba da mugayen maganganunsu.

Shikuwa bala dadi fal aransa dan dama yana tunanin kada alh jamilu yace yabiyasa kudinsa dan yanagani d'aukewar numfashi kawai zai sa ya iya bada kudin nan.


___________________


Bangaren  umma kuwa cikin jin dadi ta isa gd takira bb mlm ta sanar da shi komai  yyi murna da hakan sannan yace to cikin satin nan zasu dawo dan duka yau kwanansu d'ayafa .


" umma tace to nan sukayi sallama. "


WASHE GARI


     YOLA

da misalin karfe 10 nasafe ,bayan yasmeen ta karya tayi wanka ta fito soron gidan dan gaisawa da mlm da yah Omar.


"Tana shiga tasami mlm shida wani dattijo kamarsa saidai shi daga ganinsa yanada wadata sosai."


Cikin tsokana ta ce ina kwanan Ku tsaffi?


Murmushi sukayi suka gaisa,ana wasa da dariya ,nan yasmeen ke tambayar mlm ina yah Omar ,kafin yace wani abu yah Omar yashigo tare da wani yaran mlm .


Murmushi yah Omar yyi yace oh baby banisa nayiba taso muje ciki mu gaisa kinga tsaffin nan na kallanmu.


Yar dariya tayi tace eh gsky muje.


Mlm da amininsa sukace kulbabbi kawai."


Aminin mlm yace mlm wa,annan yaran wai suwane?

ne wlh yau nafara ganinsu sai naji duk sun kontamun arai.


Mlm yasanar da amininsa matsayinsu agunsa had'e da cewa ai yayan mariyane dan yasan shiya riketa,kuma yalabartamai dalilin zuwansu ,kuma yasanar dashi komai akan yadda Shari ar takasance.


Ajiyar zuciya tsohon yyi yace to inba damuwa ni ina nemawa jikana aurenta.


Mlm yace to! to!! to !!ngane amma kana ganinba matsala ?


"Hmm bbu wata matsala nayi iko da iyayansa balleshi ma."


Baba mlm yace to zankira mahaifiyarta indai ta amince to xanmaka mgn ammafa yarinyar nan karatu take.


Tsoho yace ba damuwa in anyi auren zata cigaba.


Mlm yace to shikenan nan yyi sallama da amininn nasa .


Wayarsa mlm yafito had'e da kiran Mariya ,bayan sun gaisa yazaiyana mata komai da komai akan yadda sukayi da alh tsoho amininsa.


Umma tayi shiru tana tunani ,can tace baba bakomai kabasa aurenta ,nasan bazaka yadda ta auri mutumin banxaba,amma kada kafad'a mata intazo zansanar da ita dan kartaji yanxun asami matsala .


",intaxo mun rarrasheta da Omar harta yarda ALLAH yasa hakanne yafi alkhairi."


Mlm yace amin hade da sakamata albarka ,nan tace to gobe sudawo gd sbd makarantar yasmeen d'in, nan mlm yace yauwa aiko anyi auren to xata cigaba da karatunta.


"cikin jin dadi umma tace to nan sukayi sallama ."


Adaren ranar mlm yaje har gidan alh tsoho yasanar dashi sun amince ."


Atake yace jibi za'a zo da uban yaron yagaidakai yanema masa auren  dan yanxun zan sanar dashi awaya.


Nan baba mlm yadawo yasanar dasu yah Omar gobe zasu tafi gida su shirya ,ji yasmeen tayi gabnta yafad'i tace miyasa zasu koma?


Mlm yace ai komai yadaidaita anfasa aurenta da alh jamilu.


Murna sukayi ta yi itada yah Omar.


Washe gari tun bayan sallar asuba yah Omar da yasmeen sukayi ban kwana da baba mlm da inna ,suka wuce tasha abinsu....


6angaren umma kuwa ,sai fargaba take dukda tasan yaranta akwai tarbiyya gashi suna mata biyayya tasanma dole yasmeen ta amince tunda sun gama mgn da Mlm bazata so mlm yyi k'arantaba ko mutuncin sa yazube.da wannan tunanin ta yini ,kuma kad'an kad'an takira su taji sun kusa isowa gd....


Bayan azahar suka dawo,umma tarbesu da abinsha Dana ci Saida suka huta sosai sannan umma tace yasmeen taje tayi wanka.


"Bbu musu ta ce to had'e da fita dg dakin."


Tana fita umma ta kalli yah Omar dke cewa nima bari naje gidan kwana nayi wankannan...


Umma ta katsesa dacewa zauna muyi mgn ,nan yazauna yamaida hnkalinsa gunta.


Nan tazaiyane masa  komai akan baba mlm yabada auren yasmeen ga jikan amininsa.


Zaro ido yyi yanuna be yardaba,umma tanunasa illar hakan had'e da cewa inason Omar kucireni kunya katayani shawo kanta dan yanxun inta shirya zan mata maganar.


Hade da cewa harda kai nakeso katayini rarrashinta kaji ,dan inkanuna kayarda nasan xata amince kuma zata cigaba da karatynta bayan auren,nafiso ayi da yardarta banson tayi zaman kunci,kuma inason nunama bala cewa iko daku yana hannuna  yaga ko bbu shi tsab yasmeen xata auru..


Yah Omar yace eh gsky Dan akazo Neman aure ta gun Kawu bala ai saiya kunyatamu karshema tak'i yin daraja gun mijin sbd Kawu akwai son abin duniya.


Umma tace yauwa Ashe kagane?gashi can ta fito yi shiru ,nan yah Omar yyi shiru had'e da latsar wayarsa ,adedenan yasmeen ta shigo dakin tana cewa yaya kaje kayi wanka ,kallonta yyi yace jeki shirya tukum zanyi mgn  dke ,batakawo komaiba ta shiga k'uryar d'akin dan shiryawa itadai umma batace komaiba tana jira yasmeen ta shirya ayi mgn....


Share pls


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿17&18


Bata wani jimaba ta fito cikin doguwar Riga ta atamfa.

         Xama tayi kusada yah Omar had'e da aza kanta gefen kafad'arsa tana cewa yah baya wanka yazama kazami,"yar dariya yyi yace keko ?"baby kin maidani kakanki  ko? Murmushi tayi ,had'e da kallan umma tana cewa wai ummu wanne d'an arzikin yakareki akotu ?dan nidai mlm da yabamu  lbr yace karar su kikayi ,kukayi shari'a

"Ahankali umma ta zaiyane musu irin taimakon da yarima yamata da jajircewarsa,har da inyadawo zai sake binkice akan mutuwar mahaifinsu.

Aidaga yah Omar har yasmeen sunyi mamaki dukda shi yah Omar yasan yarima yanada taimakon talakawa,kuma shi yadauki alkawarin duk runtsi sai yyi binkice yagane Wanda yakashe musu uba to gashi ALLAH yakawo masu yarima yataimakesu.

Cikin jin dadi had'e da k'aunar yarima yah Omar yace gsky mutumin nan yyi mana mutunci ALLAH yabiyashi yakareshi dg Sharrin abin halitta.

" umma tace ameen yah ALLAH."

          Yasmeen kuwa mamakine fal aranta amma sai asan tabbas yarima besan matsayinta agun ummaba dakuma cewa itace za'ayiwa auren ,inda yasani bazai taimakesuba,wani iri taji azuciyarta intatuna rashin mutunci datayi masa  amma indai tasake had'uwa dashi zata bashi hkuri ammafa bazata d'auki rainiba gsky Dan.. Ummace ta katseta da cewa Auta ina Neman wata alfarma agunki?

       da sauri yasmeen tace alfarma umma?"aikinfi karfin hakan aguna saidai kibani umarni kawai.

Cikin jin dadin magnarta umma tace duk abinda nasakaki zakumun kinmun alk'awari?

Yasmeen tace eh,

Umma tace to baba mlm yabada aurenki ga jikan amininsa yyi hakane dan daga ni har Ku ya isa damu ,kuma yyi hakane sbd baki kula kowa bakya soyayya duk da bansan ko a skul kinayiba.

Azabure yasmeen ta d'ago kanta dg kafadar yah Omar idanunta cike da kwallah tace aure !umma karatunfa?umma tace xaki cigaba ai ,tace to wanene za 'a auramun ?umma tace nima bansanshiba amma ai kinsan bazai had'a ki da mutumin banxa ba ko?"

        Yah Omar ne yadafa kafad'arta yace baby nah kiyi hkuri kinji kiyi biyayya ga umma da Mlm dkuma ni dan nima inason auren nan ALLAH yana tare dke kuma zai taimakeki.

Fuska cike da hawaye tace to yaya na amince tunda kaima ka amince!

Cikin tausayinta yace yauwa babyn yah Omar amma kidena kuka kinji?to tace ta share hawayen ta.

      Umma taita sakamusu albarka,nan yah Omar yafita dan yaje yyi wanka.


           *********

Mai martabane zaune shida ammi kan 2seeter yarima yana zaune gabansu kan  carpet yana sauraren yaji kiran me ,memar taba yake masa.


"Ahankali mai martaba yace ASHMAN!  "


da sauri yakalli abban sa dan yasan  wannan kiran da yyi masa babu wasa afuskarsa da maganarsa.


"Sarki yace inaso inbaka umarni matsayina na mahaifinka dan nasan kaf a y'ayana bbu maimun biyayya kamarka "


To alh tsoho yazab'a maka matar dazaka aura sauran sati 1yau sannan yau zanje yola nagaida kakan yarinyar kuma gobe zaa sata a lalle.


Arazane yarima ke kallon sarki da amminsa yace Abba pls...da sauri sarki yace oh musu zakamun toko ni danake sarki inajin maganar alh tsoho Balle kai.


Cikin tausayi had'e da rarrashi ammi tace yi hkuri kaji my son kayi biyayya ni inajin ajikina akwai alkhairi awannan auren kaji?


"Wani irin yanayi na haushi ,takaici bakin ciki yarima duk yashigesu danshifa bayason raini gsky ,dalilinsa na yarda kenan  ya auri salma dan yasan zata masa biyayya irin yadda ykeso shiya sa kuma baida ra'ayin mace2".


Sarkine yace kayi shiru ,indan yarinyar dakakesone aiba damuwa inta ida karatun saika aureta.


Jiki a sanyaye yarima yace ALLAH yasa hakan shi yafi alkhairi. Yana fad'a yabar dakin.


" sarki da ammi sun tausaya masa to bbu yadda zasu iya tunda alh tsoho yagama yanke hukunci."


Yana fita part din sa ya wuce had'e da yiwa guards dinsa dke gadin part din cewa duk Wanda yazo nemansa ace bayanan.


Kan bed ya kwanta kife kansa namasa zafi yanajin haushin wadda akace zai aura duk da bai taba ganintaba.


"Amma yadauki alwashin saita kwanmace da ma bata auresa"


Tunani yake yanxun in salma taji irin rigimar dazatayi masa dan yadda take nuna kishinsa zata iya yin   kinsan kaima,lumshe idanunsa yyi ga tafiyarsa Jordan nanda4weeks saima bayan auren kenan zaitafi .


Juyi kawai yake kan bed yana tufka da warwara.


BAYAN KWANA2


Mlm yakira ammi yace dg yau yasmeen tadena zuwa skul da ko inama kuma gobe za'azo asata a lalle dan dan sarki ne zata aura yyi shirune yaga cikin jikokin alh tsohon wanne yazaba mata dan yanada jikoki da yawa,yakuma fad'a mata jiya sarki yazo da kansa yagaidashi yakawo masa abin arziki.


Cikin mamaki da al'ajabi umma tace ta baba sukayi sallah.


Tunani take cikin yayan sarkin garinnan wa yasmeen zata aura?


Kwata kwata batayi tunanin yarima bane dan ta d'auka yanada aure.


Hakadai taita tunane tunane dg nan ta kira aminiyarta atika tazo har gd suka fara shirye shiryen tarbar bak'i.


Ummma yah Omar tabawa kudi yyi musu soyayya daidai karfinsu dan gobe suyi girkin tar bar baki.


Washe gari.....


Share pls


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿17&18


Bata wani jimaba ta fito cikin doguwar Riga ta atamfa.

         Xama tayi kusada yah Omar had'e da aza kanta gefen kafad'arsa tana cewa yah baya wanka yazama kazami,"yar dariya yyi yace keko ?"baby kin maidani kakanki  ko? Murmushi tayi ,had'e da kallan umma tana cewa wai ummu wanne d'an arzikin yakareki akotu ?dan nidai mlm da yabamu  lbr yace karar su kikayi ,kukayi shari'a

"Ahankali umma ta zaiyane musu irin taimakon da yarima yamata da jajircewarsa,har da inyadawo zai sake binkice akan mutuwar mahaifinsu.

Aidaga yah Omar har yasmeen sunyi mamaki dukda shi yah Omar yasan yarima yanada taimakon talakawa,kuma shi yadauki alkawarin duk runtsi sai yyi binkice yagane Wanda yakashe musu uba to gashi ALLAH yakawo masu yarima yataimakesu.

Cikin jin dadi had'e da k'aunar yarima yah Omar yace gsky mutumin nan yyi mana mutunci ALLAH yabiyashi yakareshi dg Sharrin abin halitta.

" umma tace ameen yah ALLAH."

          Yasmeen kuwa mamakine fal aranta amma sai asan tabbas yarima besan matsayinta agun ummaba dakuma cewa itace za'ayiwa auren ,inda yasani bazai taimakesuba,wani iri taji azuciyarta intatuna rashin mutunci datayi masa  amma indai tasake had'uwa dashi zata bashi hkuri ammafa bazata d'auki rainiba gsky Dan.. Ummace ta katseta da cewa Auta ina Neman wata alfarma agunki?

       da sauri yasmeen tace alfarma umma?"aikinfi karfin hakan aguna saidai kibani umarni kawai.

Cikin jin dadin magnarta umma tace duk abinda nasakaki zakumun kinmun alk'awari?

Yasmeen tace eh,

Umma tace to baba mlm yabada aurenki ga jikan amininsa yyi hakane dan daga ni har Ku ya isa damu ,kuma yyi hakane sbd baki kula kowa bakya soyayya duk da bansan ko a skul kinayiba.

Azabure yasmeen ta d'ago kanta dg kafadar yah Omar idanunta cike da kwallah tace aure !umma karatunfa?umma tace xaki cigaba ai ,tace to wanene za 'a auramun ?umma tace nima bansanshiba amma ai kinsan bazai had'a ki da mutumin banxa ba ko?"

        Yah Omar ne yadafa kafad'arta yace baby nah kiyi hkuri kinji kiyi biyayya ga umma da Mlm dkuma ni dan nima inason auren nan ALLAH yana tare dke kuma zai taimakeki.

Fuska cike da hawaye tace to yaya na amince tunda kaima ka amince!

Cikin tausayinta yace yauwa babyn yah Omar amma kidena kuka kinji?to tace ta share hawayen ta.

      Umma taita sakamusu albarka,nan yah Omar yafita dan yaje yyi wanka.


           *********

Mai martabane zaune shida ammi kan 2seeter yarima yana zaune gabansu kan  carpet yana sauraren yaji kiran me ,memar taba yake masa.


"Ahankali mai martaba yace ASHMAN!  "


da sauri yakalli abban sa dan yasan  wannan kiran da yyi masa babu wasa afuskarsa da maganarsa.


"Sarki yace inaso inbaka umarni matsayina na mahaifinka dan nasan kaf a y'ayana bbu maimun biyayya kamarka "


To alh tsoho yazab'a maka matar dazaka aura sauran sati 1yau sannan yau zanje yola nagaida kakan yarinyar kuma gobe zaa sata a lalle.


Arazane yarima ke kallon sarki da amminsa yace Abba pls...da sauri sarki yace oh musu zakamun toko ni danake sarki inajin maganar alh tsoho Balle kai.


Cikin tausayi had'e da rarrashi ammi tace yi hkuri kaji my son kayi biyayya ni inajin ajikina akwai alkhairi awannan auren kaji?


"Wani irin yanayi na haushi ,takaici bakin ciki yarima duk yashigesu danshifa bayason raini gsky ,dalilinsa na yarda kenan  ya auri salma dan yasan zata masa biyayya irin yadda ykeso shiya sa kuma baida ra'ayin mace2".


Sarkine yace kayi shiru ,indan yarinyar dakakesone aiba damuwa inta ida karatun saika aureta.


Jiki a sanyaye yarima yace ALLAH yasa hakan shi yafi alkhairi. Yana fad'a yabar dakin.


" sarki da ammi sun tausaya masa to bbu yadda zasu iya tunda alh tsoho yagama yanke hukunci."


Yana fita part din sa ya wuce had'e da yiwa guards dinsa dke gadin part din cewa duk Wanda yazo nemansa ace bayanan.


Kan bed ya kwanta kife kansa namasa zafi yanajin haushin wadda akace zai aura duk da bai taba ganintaba.


"Amma yadauki alwashin saita kwanmace da ma bata auresa"


Tunani yake yanxun in salma taji irin rigimar dazatayi masa dan yadda take nuna kishinsa zata iya yin   kinsan kaima,lumshe idanunsa yyi ga tafiyarsa Jordan nanda4weeks saima bayan auren kenan zaitafi .


Juyi kawai yake kan bed yana tufka da warwara.


BAYAN KWANA2


Mlm yakira ammi yace dg yau yasmeen tadena zuwa skul da ko inama kuma gobe za'azo asata a lalle dan dan sarki ne zata aura yyi shirune yaga cikin jikokin alh tsohon wanne yazaba mata dan yanada jikoki da yawa,yakuma fad'a mata jiya sarki yazo da kansa yagaidashi yakawo masa abin arziki.


Cikin mamaki da al'ajabi umma tace ta baba sukayi sallah.


Tunani take cikin yayan sarkin garinnan wa yasmeen zata aura?


Kwata kwata batayi tunanin yarima bane dan ta d'auka yanada aure.


Hakadai taita tunane tunane dg nan ta kira aminiyarta atika tazo har gd suka fara shirye shiryen tarbar bak'i.


Ummma yah Omar tabawa kudi yyi musu soyayya daidai karfinsu dan gobe suyi girkin tar bar baki.


Washe gari.....


Share pls


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


dedicate to my sister asma'u sayyadi ina mugun jidake😍😍


🅿19&20


Washe gari

     "" tun da wuri umma da yasmeen suka gyare gidan suka dafa abinci mai rai da lfy daidai karfin su.yayinda atika takawo kunun aya cike da kula yasha kayan k'amshi da kwakwa ansakashi a robobi an d'ora k'ankara sama.

      "Umma tji dad'in hakan ,nan aka shimfid'a tabarmi atsakar gidan Manya sannan atika tasaka yasmeen tayi wanka ", da kanta atika ta taya yasmeen shiryawa dan bataso koda suke talakawa araina y'ar aminiyar ta.nan umma ta fito mata da sabuwar gown fara y'ar kanti sabuwa tace tasaka.

Cikin mamaki yasmeen tasaka kayan dan tunani take wai dan gidan wanene zata aura aketa wannan shirin haka lallai .dan umma bata gayamata ba ko ta tambaya sai tace bata saniba.

" masha ALLAH tayi wani mugun kyau kamar yaune aka d'aura auren ta fito a chacoolat colour d'inta.nan atika taita yaba kyawunta had'e da fesheta da turaruka masu dadin k'amshi.

Ko zama yasmeen batayiba saiga kubra tashigo da sallama ,tagaishe dasu umma tana mamakin kwalliyar da yasmeen tayi dan batasan ankusa aurentaba .

Tazone taji lfy jiya da yau bataje skul ba."nan suka zauna  kan kujera itada yasmeen suna gaisawa nan take tambayar yasmeen dalilin kin zuwanta skul?"

Nanvtasanar da ita yau saura 6days auren ta Amma taroketa kada ta sanar da kowa a  friends dinsu dan bbu wani event daza 'ayi kuma zata koma skul.

Kubra tayi mamaki sosai sannan tace to bazata sanar da kowa ba had'e da cewa wazaki aura?

Bbu boye boye ta sanar da ita kakanta ne yabadata dan tayarda da kubra sosai amma taboye maganar auren ta da alhj jamilu.""";;


Ana gama sallar azahar motocin  gidan sarki sukayi parking agaban gdn su yasmeen sai kida'a ake da busa ,nan aka fara shiga da kayan lefe da saka lalle..


Cikin farin ciki su inna atika suka shiga tarbar b'aki hade da gaisawa cikin mutunci.


Yasmeen kuwa itada kubra sunsha mamaki jin busa fa gud'a irin na saurauta ,azuciyarsa yasmeen tunani take tokodai dan sarki ne zata aura,tunawa tayi da yarima wani mummunan fad'uwar gaba taji....inna atikace takatse mata tunani dacewa d'ago nasakamiki alkyabba,nan tasake shiga rud'u bayan tasaka mata ta fita waje...


"" kubra ta kalli yasmeen tace friend kodai yarima zaki aura ? dan gsky dg gani dan sarki ne tunda ga kid'a da busa kuma ansaka miki alkyabba ,kuma nahango ana shigowa da kayen lefenki masu yawa....tsakin da yasmeen tayi yasaka kubra yin shiru cikin haushin fatan kubra ta ce ALLAH ykiyaye akace miki shikad'aine d'an sarki shidama yanada aure."""


Yar dariya kubra ta yi tace hakane ,munxuba ido muga wanne ne angon naki?


Atsakar gida kuwa ,bak'i sunci sunsha bbu wulak'anci ko nuna k'yama ga gidan ,hakan yyiwa umma dad'i sosai tasan yasmeen tadace da dangin miji fatanta ALLAH yasa mijinma hka yake.


Nan suka bada lefe da manyan wayoyi guda2abawa yasmeen ta rik'a amfani dasu,had'e da cewa ga kuyangi 2nan dazasu zauna da yasmeen har lokacin daza akaita gdn mijinta suruk'a koya mata dressing irin na gidan sarauta da sanar da ita yadda tsarin gidan yake da yadda zata zauna da kowa.


Godiya sosai su inna atika sukayi sannan suka mik'e dan tafiya,had'e da cewa sarki yyi iznin securities suyi gadin gidan har zuwa ranar daurin auren .


Umma taji dad'i sosai nan ,cikin kudin da baba mlm ya aiko matadasu na gaisuwar yasmeen suka bada dubu100tukwici aiko sukace ah ah sarki yace karsu karbi komai .


Cikin farin ciki su umma da inna atika da dangin umma sukayi ta masu godiya suka tafi gida.


Nan inna atika ta shiga gun yasmeen tasanar da ita ga kuyanginta dazasu rika kula da ita da nuna mata komai na sarauta.


dan zaro ido tayi axuciyarta tace to ta tabbata d'an gidansu zan aura to wlh bazan dauki yarainamun hankaliba dan yana yayan mijina...inna atika ta katseta da cewa to kidai kama kanki banda yawan surutu kuma kidinga basu umarni sbd kuyanginkine tana fadin hakan tafita..


Kubra tace oh friend kinxama ginbiya dg yau gsky kinji dadinki ,kafin yasmeen tace wani abu har kuyan gin sun shigo.


da sauri suka zube suna kwasar gaisuwa dan ammin yarima ta gargadesu dasuyi mata biyayya kada subata mata rai ,intasami sunyi laifi hukuncinsu yana gun yarima.


Masha ALLAH kawai suke cewa axuciyarsu ganin kyawun yasmeen, sun tabbar itace ta dace da yarima sarkin  k'asaita dan yanda yake da kyau dole sai mai kyau irinshi.


"" cikin  yanga yasmeen ta d'aga musu hannu alamar amsawa  .


Basuyi mamakin hakanba sbd shima yarima da wuya yyiwa bayi  ko kuyangi mgn saidai yad'aga musu hannu.


Nan suka saka mata sarka da yan hannu da takalmi irin na sarauta.


Ita dai kubra sai kallonsu take tason yin dariya ganin yadda yasmeen tayi bala'in kama kanta dan bbu raini dukda hakan  ba bak'ontane ba gun yasmeen.


Nan dai suka zauna sunama yasmeen fita dabata  labarin ban dariya,nan kubra ta tambayi sunansu.


daya tace binta ,daya tace  sabila .


Ana gama sallar la'asar kubra ta tafi da xumar ranar juma'a xata dawo..


          *********

Alh jamilu ne zaune a get house d'insa yana hutawa saiga Kawu bala yashigo kamar zai fad'i yazo yazauna.


Baki na bari yakalli alh jamilu yace wai Ashe yarinyar nan aure za'a mata yau saura kwana6 kuma dan sarkin garin nan zata aura .


"What's alhj jamilu yyi exclaiming ."


Kawu bala yace wlh yau matsiyaciyar ta turo  danta shegen yakamun i,b na daurin auren,wlh dan bashir baya nan Dana saka yasumar mun dashi...


Alh jmilu yace ni yanxun bukatata bazata biyaba kenan?


Bala yace eh  danfa ina tunanin Wannan d'an iskan yarimai k'aninsa ne zata aura shiyasa ya hakikance a kotu.


Alh jmilu yace saimu saka assato tota yau kawai.


Bala yace ai gidan su ance tsare yake da security gsky.


Hmmm alh jmilu yace zansake wata shawarar amma sai fa na d'and'ani yarinyar nan naji tasting d'inta.


Dariya suka sheke da ita gaba dayansu.


____________________


Bayan kwana 5

Yarage gobe daurin aure duk Wanda yaga yasmeen inba farin sani yyi mata ba bazai ganeta sbd yadda tayi kyau tayi fresh jikinta yyi simil sai gyara take sha bata aikin komai sai kwanciya bacci ko latsar waya dan ta yi mugun jin dad'in wayar ,saidai wani gefen nazuciyarta na fargaban auren da kuma inyarima yagane itace kaninsa ya aura kozai mata rashin mutunci...


Sannan duk abinda yakamata kuyanginta su sanar da ita ko koya mata sunyi kuma tafahimci komai dan yasmeen akwai brai.


Anyi mata dulka halawa da k'unshi had'e da turaren jiki Wanda yabi jikinta ko guri ta zauna saikaji kamshi.


Ga masuyimata kwalliya kullum sai sunxo.


Ayaune kubra ta bude mata WhatsApp dantadunga chat da friends dinsu.


Sai kurantata kubra keyi ganin kyawun datayi cikin 5days.


Ammafa kubra ranta yabata cewa yarimane yasmeen zata aura kawaidai bata sani ba ko kuma boye mata akayi ,amma barata xuba ido dan batasan yiwa yasmeen maganar yanxun ran yasmeen zai baci dan talura tatsani yarima...


Kubra batabar gidanba sai dare.


Washe gari.....


Share pls


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿21&22


Washe gari.....


Tunda wuri masu kwalliya sukazo suka shirya yasmeen cikin Swiss vowel lace pink colou aka azamata alkyabba fadin kyawun datayi bata lokaci ne.

Kubra dashigowarta kenan byn sun gaisa ta kalli yasmeen tace wow ran gimbiya yadade ALLAH shi taimakeki.

"Yar dariya yasmeen tayi tace oh hada xo la ma ko"?

Kubra tace kinyi ba karya wlh irin haka saiki zauta angon naki inyaganki had'e rai tayi dan gabantama fad'uwa yke.

       " tace hmmm wlh kirabu dni pls da maganarsa.

Shiru kubra ta yi ganin kuyangin sun shigo d'akin suka tsaya gefen yasmeen suna mata fita ,had'e da fira.


   ***** *****  *****

Bangaren yarima kuwa tun sauran 5days bikin ammi kefama dashi akan yaje gidansu yasmeen,amma sai yamata karya yace ai yaje ko invitation na bikin abokinsane salis yaraba wa mutane amma shi ko ganin invitation din bayasanyima.

Ayauma  Saida ammi tayimasa Ta's sannan yaje yashirya cikin wani lallausan farin vowel mai tsada yar ciki da babbar Riga yasha aikin hannu da bakin zare ya aza hula,takalmi ,agogo duka baki ,ga kansa yasha gyara sai wani fitinannan kamshi yake tashi ajikinsa saidai fuskar nan tasa bbu annuri .


Salis amininsa yace wow friend kayi kyau ..kafin yarima yyi mgn wayarsa tayi ringin yana dubawa yaga ammice.


Ya na d'agawa tace kasameni a part dina. "


Kashewa yyi yakalli salis yace jirani ina zuwa,nan yafice dg part din sa yanufi na ammi.


Ya na xuwa yasameta  tsaye kusada wani corridor kasancewar fa jamaa yan biki acikin part din ta.


Kallonsa tyi tace dubeka yadda kawani had'e rai wato kanunawa duniya bakasan auren ko?to itama matar taka tursasata akayi danma kasani.


Wani xafi yarima yji azuciyarsa  dayaji ammi tace wai matarsa...


"Ahankali yace pl ammi kiyi hkuri."


Cikin tausayinsa tace zan hakura,amma kasaki ranka agun daurin auren nasan jamaa zasuyita tayaka murna anamaka ALLAH yasa alkhairi.


To ammi"


Tace to maza jeka befi saura30 minit ayi d'aurin aurenba,bece komaiba yajuya yatafi ,ammi takoma gun bak'inta.


Yarima kuwa badan yasoba yadan dai saki ransa ,nan guards dinsa suka bisa a motar da zaishiga shida salis suka wuce  gun da ayi daurin auren.


da misalin karfe 11:00am dubban jama'a suka shaida d'aurin auren yarima Ashman da yasmeen Ahmed.


Agun daurin auren sai mutane keyi masa fatan alkhairi. dan abokansa da'idaikune sukaje dan yahana salis yasanar dasu.


Anatashi dg gun d'aurin auren yarima yasulale yanufi part din sa yarufe kansa yana tunanin kamarsa prince ace ammasa auren dole Aida kunya friends dinsa sujima .


Tsaki yyi afili yace haba yarinya wlh zaki gane shayi ruwane tunda kika yadda aka auramikini...


__________________

Yasmeen kuwa ana cewa ai andaura auren aisaita barke da kuka dan taga da gaske xata rabu da ummanta da yah Omar dinta.


Bbu irin rarrashinda kubra da inna atika basuyi mataba amma taki shiru har aka shiryata za'a fito akaita gdan mijinta.


Saida yah Omar yaje ya rarrasheta ,Wanda shima daurewa kawai yake dan yashak'u da babynshi da yawa.


daza a fito da ita kuwa da k'yar aka banbareta dg jikin umma sai kuka take haka akasata mota sai gidan Sarki dan Sarki yace can gidan zasu fara xama tukum .


Bayan sun isa ko ina sai kid'a da busa akeyi had'e da bud'a nan aka fito da yasmeen akawuce da ita part dinsu ammi dan badata amana..


dangin umma da aminnanta sun yaba da karamcin da iyayen yarima suka musu haka suka baro yasmeen tana kuka, akabarta dg ita sai kubra sannan suka nufo gd .


Ana gama isha I bayan yasmeen ta shirya cikin super ,kubra tayi mata nasiha had'e da cewa sai sun had'u a skul,yasmeen naji nagani kubra ta tafi tabarta.


Zama tayi kan bed kanta duke gaban ta said dukan Tara Tara yake azuciyarta  tace ko ya,yake mijin nawa?oho ,wayarta tajawo tana dan daddannawa.


Yarima kuwa ana yin isha'i yawuce part din sa yyi wanka ,zuciyarsa cinkushe ya kwanta kan bed had'e da jin haushin amaryar tasa.


Wayarsa yad'auka dan yakashe kiran ammi yashigo ciki... gabansa yafadi afili yace ALLAH yasa ba wannan muguwar al'adar ta gidan nan zaamunba dan wlh da an cuceni.


dagawa yyi ganin takusa tsinkewa,yyi sallama ammi tace kazo yanxun inason ganinka,d'it ta datse kiran,,,,,,,


Jallabiyya fara yasaka ransa bbu dadi yanufi part din ammi."


"Yana zuwa ko mgn beyiba ammi tayi maza ta miko masa farin k'yalle tace gashi dan ALLAH kabi musu y'a ahankali kaji my son  dan nayi mgn da jakkadiya ta je ta rakata d'akinka tafad'a cikin jin nauyinsa.


Wani fad'uwar gaba yaji yak'i karba ,yana tunani haba wai suna nufin dole yakusanci yarinyar nan gsky da sake bazai iy...tsawar da ammi ta masa ne yasa yadawo hayyacinsa rai bace tace oh bazaka karba ko to kayi duk yadda kke so ta fada had'e juyawa da nufin tafiya da sauri yarima yaduk'a yace pls ammina wlh zan yi yadda kikeso yyi saurin karbar kyallen .


" ahankali tace to jeka Saida safe ALLAH yasa muga alkhairi".


"da sauri yafita yabar dakin"


Bangaren yasmeen kuwa ta na zaune jakkadiya ta shigo ta gaida ita had'e da cewa zata shiryata ba musu ta tsaya akashiryata dan umma ta gargadeta kada tayi musu da kowa.


Saidai ganin ansaka mata alkyabba saman kayan baccinta yasa gabanta  fad'uwa had'e da rawar jiki.


Rufe mata fuska jakaddiya tayida wani gyale  had'e da kama hannunta suka nufi part din yarima........


Share pls


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Wannan page din nakine maman kids kiyi yadda kkso dashi ina mugun yinki totally😍😍


🅿23&24


"" suna shiga jakkadiya tayi sallama had'e da rissinawa tana gaishe da yarima"

Cikin kasaita ya amsa sallamar fuska had'e, wani mummunan fad'uwar gaba yasmeen taji dan bazata tab'a mantawa da muryar yarimaba.

     " lallai tashiga tarama ba ukku ,take jikinta yahau rawa da kirma sbd razana kamar tasaki fitsari a wando ,bata auneba taji jakkadiya tasaki hannunta tana cewa yarima ALLAH yatashemu lfy tafita.

Ai yasmeen jitayi kamar ta xura aguje dan yanda ta tsorata....muryar yarima ta daki dodon kunnenta inda yake cewa  ke wawiyar inace ?ba'a koyamiki gaida na gaba dkeba zakiyiwa mutane tsaye aka yafad'a had'e da Jan doguwar tsuka..

"Yasmeen batace komaiba tana kallonsa tacikin mayafin da aka rufeta  kasancewar dum night ce kunne a d'akin bbu haske sosai,hantar cikin sai juyawa take dan tasan intayi mgn yanxun zaiganeta.

       Cikin isa had'e da gadara yace inaso ki saurareni da kyau kiji dokokin dazan kafamiki dan karya d'aya acikin su hmmmm sai kinyabawa aya zakinta".

Nah 1 I really hate you ko ganinki banason yi  banasonki ko kad'an na aureki sbd biyayyar iyayena amma ni Prince nafi karfin nasoki never wlh.

     Nah 2kada kisake indai ina gidan nan kifito da Wannan k'azamar fuskar taki Dan banason ganinta kirik'a saka nik'ab kada kibari muhad'u bbu nikaf a fuskarki.

" azuciyar yasmeen tace good bazanso kaganni yanxunba saina shirya irin rashin m din dazanmaka had'e da bakak'en maganganun daka gayamun nima narama....jitayi yace nah3babban kuskuren dazakiyi shine kai k'arata gun iyayena ,innagane hkan sorry for your self wlh.

Nah 4wanki nah da guga ta had'e da gyaramun dakinah yadawo gunki danba Hutu kikaxoba ,kafin my salma ta shigo cikin gidan kihada danata kiyi dan baiwa aka kawo mana .yana kaiwa nan yyi tsaki had'e da cewa ke xonan .......cikin jin haushin kalamansa taje gab da shi ,tsaki yyi yasa hannunsa ya fisgota tafad'a kan bed din dayake zaune kai kuma bisa farin kyallen da Umma tabashi...

"Yasmeen inbacin kiran sunan ALLAH akan yakamata dauki bbu abinda take dan ta yi bala'in tsorata da yarima ,bata auneba taga cikin mugunta ya ware mata k'afafu da karfin tsiya had'e da yima ta rumfa da fad'ed'an kirjinsa,kuka yasmeen ta fashe dashi.

Yarima bbu wani romancing ko rarrashi dan ko hannunta betaba ba hanyarsa kawai yabi.

Ckin rashin tausayi da mugunta had'e da nuna mata k'arfinsa na d'a nmj ya afkamata bayaji baya gani.....

Yasmeen kuwa ihu take tana kiran ummanta da yah Omar suxo su ceceta ,amma yarima bemasan tanayiba ....firgitacciyar kara tasaki,atake numfashinta yad'auke."

         Shikuwa yarima Saida yamaidata cikakkiyar mace yasamu nutsuwa sosai da ita tukum yasaurara mata yana maida numfashi. "

Cikin wulakancin sa yace ke dallah can kitashimin dg kan bed basabonba....shiru yyi ganin batayi mgn ba  hannunsa yasa kan shafaffen cikinta yaji bata  numfashi,yatsina fuska yyi alamar ko ajikinsa.

"Umma yakira wadda dama batayi bacciba ,tana d'agawa tace lfy yayadai?cikin in ina yace dama dama... Axo afita da ita ....yana fada yakashe wayar.

" tashi yyi yawuce toilet dan tsabtace jikinsa",yabarta nan yashe kan bed.

Befi 10 minit da shiga toilet ba jakkadiya tashigo da  doctor Aisha wadda ke zaune acikin asibitin masarautar ita da mijinta suna kula da duk Wanda yake acikin gidan inbashida lfy .

Jakkadiya ta taimakawa doctor Aisha suka dauki yasmeen had'e da farin k'yallen sukabar d'akin.,,,,,


Kai tsaye a hospital din dke cikin masarautar akawuce da yasmeen ,jakkadiya tabar doctor nabata treatment d'in dayadace, ta nufi part din ammi...


"Tana shiga tasami ammi da alkyabba ajikinta sai safa da marwa take a parlour ta tanajiran dawowar jakkadiya.,,,,


Tana ganinta da sauri ta karbe farin kyallen tana cewa yajikinta?


" cikin damuwa had'e da tausayin yasmeen jakkadiya tace to gashi dai can doctor na dubata dan gsky ina tunanin tasami rauni ,k'ila gaddama tamasa dan asume Muka d'aukota.'''''''


Salati ammi tayi tace subhanallahi oh yaron nan ,kije ki kwana da ita kirarrasheta da safe sannan tadanji sauki amaidota part dinta zan shigo insha ALLAH.


"To tace ta fita".


Ammi ta bude farin k'yallen tagansa duk jini ,murmushi tayi tace alhmdllh  lallai kincika ya'a ta gari ALLAH yahad'amun kanku yabaku zuri'a d'aiyiba. nan ta nufi part din hjy rahama wato abiyar zamanta dan nuna mata shaidar  matar yarima ta kawo budurcinta lfy....


Bangaren yasmeen kuwa duk kulawar da tadace anbata Saida akayi mata d'inki tukum numfashinta yadawo akayi mata allurar bacci dan data farko ihu da kiran ummanta da yah Omar takeyi..jakkadiya ita ta zauna da kuyangin yasmeen gunta.


        *********


Yarima kuwa yana gawa kimtsawa yacanxa bed sheet ya kwanta ,saiyaji sa wasai kamar ansauke masa wata damuwa nan take bacci maidad'i yadaukesa Wanda rabon dayayi irinsa har yamanta...


Washe gari... Tun 7:am yasmeen ta tashi ba  laifi taji karfin jikinta ,a toilet din asibitin jakkadiya tahada mata ruwan dumi had'e da rakata toilet din ta fito ta koma part din ta ta dakko mata ksyan sawa.


Tana fitowa tasaka tayi sallah ,saidai kallo d'aya zaka mata kasan tana cikin damuwa ga idanunta har sun kunbura.


Jakkadiya ce ta kamata suka wuce ciki dan ta yi break tasha maganinta.


Koda sukaje part din yasmeen, suka sami ammi ta aiko da break fast mai rai da lfy, duk da akwai kukun dazai rik'a yiwa yasmeen girki..


"" tea mai kauri jakkadiya tahada mata, bayan tasha tabata farfesun kaji da sinasir shima ba laifi taci nan akabata mgni tasha..""


Bata dad'e da shan mganinba ammi ta shigo da kuyanginta abayanta suna take mata birki da sauri jakkadiya da kuyangin yasmeen suka zube suna kwasar gaisuwa,had'e da barin parlour, cikin girmamawa yasmeen kekokarin tashi ta gaishe da ammi ,ammi naganin haka ta yi saurin cewa ah ah y'ata yi zamanki  kinji keda bakida lfy ta fad'a had'e da dafa kafadar yasmeen din.


Cikin jin kunya yasmeen tace ina kwana mama?


Murmushi ammi tayi had'e da cewa lfy yajikinki ?


"Sunkuyarda kai tayi tace da sauri".


Ammi tace ALLAH yyimiki albarka kinji kiyi ta hakuri wataran zaku saba da yarima kuma dan ALLAH kidaukeni amatsayin uwa ,amminki dan haka yaran gidan nan ke kirana.


Cikin jin kaunarta yasmeen tace to ammi ngd ,murmushi ammi tayi tace kada kidamu bara naje xandawo anjima abbanku mai martaba yace agaidake.


Ahankali yasmeen tace ina amsawa,nan ammi ta fice ,sannan kuyangin yasmeen suka dawo suna aikinsu wato kula da duk wani motsinta.


Ammi na fita ,tawuce  part din ta ,acan tasami yarima ,yana ganinta yahau Sosa kai had'e da gaidata...


Bayan ta amsa ta hararesa tace wato shine duk gargad'in da namaka kabimusu y'a a hankali shine Saida kamata rauni ko? dan doctor tacemun saida tamata d'inki.


Cikin jin kunya yace gaddama fa tamun ammi hararansa tayi tace aisai ka rarrasheta ni yanxun bansan jin wata mgn kaje ka duba jikinta, ba musu yace to had'e da barin part din..


Yana fita azuciyarsa yace ta ma mutu manah me ruwana yyificewar dg gidanma baki daya.


Yasmeen kuwa da marece Saida takira yah Omar da Umma suka sha fira sosai kuma bata nuna musu komai sbd batason sakasu adamuwa.


"Ammi ma Saida tasake xuwa dubata,ta tambayeta dazun yarima yazo yaduba ? Yasmeen tace eh ammi tace to next week insha ALLAH zata koma skul.


__________________


Hakafa rayuwa taita tafita inda yanxun har yasmeen ta kwanta 3agidan kuma ta warke sarai sannan bata sake xuwa d'akin yarimaba dan yanxun wani mugun tsoronsa take tunda hakan tafaru.ko ganinsa ma bata sakeyina dan batamasan ganinsa.


Yarima kuwa yasharene ganin batayi gyaran dakinba da wankin da yace amma yakyaleta ganin ance bata lfy ,amma ganin har3days ta wuce batayiba yadauki alk'awarin dg yau inbata yiba zatasha mamakinsa dan baya daukar raini,be fitaba Saida ya hargitsa part din sa dan intaxo tasha wahala gun gyarawa...


Yasmeen kuwa zaune take tana chat da friends dinta ta tuna da dokokin yarima da sauri ta ta shi jikinta na rawa ta aje wayar kan bed,had'e da daukar keys dan dama tun randa taxo gidan jakkadiya tabata  su tace na part din yarimane.


Duk ta rude dan ita tama manta da wasu dokokinsa ,alkyabba taaxa saman kayanta tukum ta dauki nik'ab dinta ta fito ,a parlour tahad'u da kuyan ginta tace kada Wanda yabiyota sukace to nan ta nufi part dinsa ta na xuwa ta bud'e tasha mamakin ganin d'akin ahargitse nan ta hau gyarwa.


Bayan ta gyara  parlour ta koma bed room ,kudi tagani yan1000 Rafa 2ak'asa ,Rafa 2atsakkiyar gado daya a k'arkashin fill,ko tabasu batayiwa tagyare d'akin fest tayi moping had'e da wanke toilet sannan ta turare dakin daairfreeshners masu dad'in kamshi.


Kan mirror ta kwalla tags pics ba mace guda 2 tasha bealiching bbu tsari agefen pic din asaka my salma ,yatsina fuska ta yi had'e da yin tsaki afili tace hmmm meyake nufi to ? Yana tunanin xanji haushi ko kuma ni bar'auniyace dazai aje kudi yaga koxan d'auka ?ALLAH yakiyaye nida zai sawakemun aurensa dayafi me b'ak'ar zuciya kawai...


Wata kofa tagani gab da toilet ta bud'e amamakinta sai tags filine hade da swimming pool da resting chairs agun ga igiyar shanya adaure gefe ga tulun kayan wankin yarima kulle cikin wani farin yadi ga soaf Asama da klin.


Wani haushi da tausayin kanta taji dan  yanxun hakactagaji  da yawa ,amma yazati k'addararta ce ,haka taje ta dakko bucket a toilet din sa ta dawo tana kuka tana wankin har ta gama ta shanya jikinta sai ciwo yake mata dan  ta kai awa2 tana durxar wankin kayanyarima  bayan tagama ta rufe part din ta koma part din ta...


Yarima kuwa be dawo gidanba sai 2:30 pm dan dama haka yake dawowa gd ,bayan yabud'e part din wani kamshi yadaki hancinsa komai gyare fas  kal kal har cikin xuciyar yaji dad'in ganin dakin hakan ,gun sha k'atawar yabude yaga ta wanke kayan ta shanya har sun bud'e daure fuska yyi yawe wato bata gogeba ko tabarmun kaya cikin rana ko?


Fitowa yyi yasa ka aka kira masa jakkadiya ,bayan tazo yace ta turo masa yasmeen dan ko sunanta bai saniba kawai yace dai wannan yarinyar aturomasa ita,to jakkadiya tace ta nufi part din yasmeen....


Share  pls


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Banida bakin da zangodemuku masoya wannan novel saidai incigaba da nishadantarku da farantamuku, kuyi hkuri masu yimun mgn ta PC bana musu replay  ina gani kuyimun uxuri inada uxururruka ngd sosae ina gani Ina jin dadi  ina mugun yinku irin sosai dinna😇😇


🅿25&26


     Jakkadiya nashiga tasami yasmeen kwance kuyanginta na mata tausa dan ta gaji over", nan ta sanar da ita sak'on yarima " wani b'acin rai taji amma sai ta daure tace to ganinan."

          Nan ta sallami su binta suka fita tashi tayi ta aza alkyabba ajikinta ta dauki nik'ab d'inta ta nufi part dinsa ranta b'ace taji dalilin kiranta .

"daidai bakin k'ofar shiga tatsaya ta d'aura nik'ab d'inta sannan ta shiga, kan bed tasamesa hakimce yawani hade rai"

Canxa murya tayi yadda bazaigane ba tayi sallama, ayatsine ya amsa yana wani basarwa amma yakafeta da ido yana tunanin kamar yasan wata da irin wad'an nan idanun ,koda ta lura da kallon dayake ma idanunta saita dukar da kai tsaki yyi had'e da cewa ke baki iya gaisuwa ba ko?"

      Tace ina wuni? Kirik'e banaso",meyasa kikabarmun kaya arana baki gogeba dan kinrainani har inbaki umarni kik'ibi ko??

"Azuciyar ta kuwa jitake kamar ta masa rashin kunya kome zai faru yafaru dan yakaita bango....atsawace yace ko bakya jine?

" ahankali tace bbu nefa yanxun kuma bayanxun za'a tada ingeen ba"shiyasa .

Tsaki yyi yace matsalarkice wannan nabaki nanda awa d'aya da Rabi kigogesu kisaka kuyanginki suyiwa sarkin gd magana yahad'a garwashi asa acakwal kimun gugata ya fad'a atsawace.

      Bewar ALLAH da sauri ta taje ta kwaso kayan duka ta daure a wani yadi fari tazo zata fita yace keeeeee!

"Innayi binkice naga bakekikayi gugarnanba hmmm nidakene agdan nan,batace komaiba ta fita.

Tsaki yyi yaduba gun da ya'aje kudin nan yaga abinsa sannan ga pics in salma ko tab'asu ba'ayiba"

Girgiza kai yyi ya wuce toilet yyi wanka yafito ,shiryawa yake amma yanajin wani yanayi atare dashi dan tun ranar da yakusanci yasmeen yagane cewa yanadaga cikin maza masu buk'ata ,yanason hakkinsa dan yasan ta warke amma girman kai bazai bari yanuna yanasoba ko yace akawota d'akinsa.

        Hakadai yagama shiryawa yaje yaci abinci ,yawuce gun ammi dan yasha fura mutuniyarsa.


Bangaren yasmeen kuwa tana fita dg part dinsa tacire nik'ab d'inta, tawuce ciki,nan tasaka akayowa sarkin gd magana yahad'a mata garwashin,bbu jimawa aka kawo sai turi ri yakeyi .


Karba tayi ta sallami kuyanginta ,bed room in ta ta nufa ta fara gugan dan dama ta iya goge kayan maza sbd a gd tana taya yah Omar gugan kayansa.


Haka tayitayi tana kuka duk ta d'askane hannu ga hayak'in garwashin saita fita ,ahakadai taita wahala duktayi xufa harta gama.""


"Wanke fuskarta tayi ta aza nik'ab d'inta sannan tadauki kayan taje bed room d'insa ta aje ta fito."


Wanka tayi ta had'e da yin sallah ta kwanta agajiye bacci yyi gaba da ita.


      **********


da dare da misalin karfe 8:30pm yarimane kwance saman bed din sa sai juyi yake dan wata irin sha'awa yakeji,can wata dubara ta f'adomishi ,tashi yyi yanufi part din amminsa.


Bayan sun gaisa tabashi fura yace ah ah ,tayi mamaki dan ba'amasa tayin fura yak'i Shanta .


"" kallonsa tayi ta ce kaje ka kwanta kabarta ita d'aya haka akeyi"?


dukar da kai yyi yace nifa bada ita nake kwanaba ,bata xuwa dakina.


Tsaki umma ta yi tace laifinkane k'ila ma tsoronka take kaida zaka rarrasheta haba my son kaje za'a rakota amma gsky kadunga kula da ita harta saba dakai basaima anrakotaba ,takaikanta gunka kaji ta fad'a cikin sigar rarrashi.


"To ammi"


Ya fad'a amma bawai dan zaiyiba danbega yarinyar dazai iya b'ata time dinsa ya rarrasheta tab da sake wlh..


"Sallama sukayi da ammi yanufi part din sa,,,,,


Yasmeen kuwa harta kwanta abinta tafara bacci jakkadiya tashigo tace taxo suje mijinta nakira.


Nan yasmeen tace ah ah taje ,ita taje,jakkadiya tace ah ah umarnin sarauniya ne kiyi hkuri muje.


'''''''Kamar tayi kuka ta dauki nik'ab d'inta ta bita.


Dede bakin k'ofar jakkadiya tatsaya had'e da murd'a k'ofar tacewa yasmeen gimbiya shiga, ji yasmeen ta yi kamar ta kai mata bugu dan haushi hadai tashiga,ita kuma tayi tafiyarta.


Yarima na kwance kan bed kamar me bacci yyi xuru yanajiran shigowarta saigata ta shigo.


Ko sallama batayiba ta zauna kan carpet tace gani,,,


"" cikin rainin hankali yace lfy ,kirankinayi ne?xaki shigoma mutane daki bbu sallama"".


Tashi tayi ta ce ok bara naje tunba kirana akeba......


Share pls


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿27&28


""da sauri yace ke inkika fita wlh ranki zai b'aci ,nasan ammice tace kixo shine dan raini zaki koma ko ?"

Shiru tayi had'e da zama batace komaiba.

"Keeeeee! Xonan " murya na rawa yasmeen tace mexan maka kayi hkuri pls ban warkeba ALLH kuwa ,tafad'a gaban ta fad'uwa sbd tuna wahalar datasha last4days.

Tsaki yyi yace matsalarkice wannan ainima basonikeba kawai dai xanbi umarnin ammi,kuma aikema kinaso taimakonki zanyi...katsesa tayi da cewa ah ah ni wlh banaso,kuma ai saika kwanta bbu Wanda zaigane ko kayi ko bakayiba....

"Mamakin wayon yarinyar yake ,cikin tsawa yace wai bazakixoba ko mene?"

      Cikin tsiwa tace yah isa haba saikace wata yar ka ,eh d'in baza azoba.

Ahassale yace nikike gayawa mgn lallai zaki fuskanci hukunci,sannan ayanxun zanyi abinda nike so dke ta k'arfi inga Wanda ya isah yahana .

Yasmeen ta tsorata sosai hanyar guduwa kawai take nema ,bata auneba taji ya fincikota had'e da makata saman gado da sauri ta tashi zata gudu ,da k'arfi yamaidata had'e da rike mata hannuwa gam ,sai ihu take tana kok'arin kwacewa amma ta kasa ,shikuwa ko ajikinsa ,yadda yyi a firs night d'insu haka yyi saidai bai jimata rauniba.

Amma taji jiki kuka kawai take yi tawani k'ame gu d'aya ko motsin kirki batayi har yagama kuma taji tsafi amma baikai na farkoba.

      "Tashi tayi da k'yar ganin yashige toilet ta fice xuwa part din ta".

Shikuwa yana fitowa yyi tsaki yace garama da Kika fita dan danasameki korarki zanyi ,kuma zanmiki maganin rashin kunya.

Nan yashirya yyi kwanciyarsa bacci mai dadi yyi gaba dashi.

" yasmeen kuwa Saida tashiga ruwan dumi tad'ad'e aciki tukum tyi wanka ta fito ta kwanta xuciyarta cike da tsanar yarima kuma tasha alwashin kota halink'a k'a saita rama abinda yyi mata dole tafara shirin ramuwar gayya wadda ta fi gayya zafi.


       *********

Washe gari byn yasmeen tayi break tashirya cikin lace milk ,tayi kyau,Saida ta daidaici lokacin da yarima baya gidan tukum ta fito ta nufi part din ammi dan gaisheta.,,,,,,


"" bayan sun gama gaiwa ,ammi tace munyi mgn da my son gobe zaki fara zuwa skul,yacemun aikunyi mgn nik'ab zaki rik'a sakawa ko?,,,,,


Cikin mamakin karyar yarima yasmeen tace eh.


Ammi tace ok to dan ALLAH ki kula kinji dukda nasan kinada kamun kai amma ki k'ara gobe driven ki xai fara kaiki nan tace to ammi ngd.kafin ammi tayi mgn ,Maryam (y'ardakin hjy rahama)da salim autan ammi sun shigo tare da sallama,amsawa yasmeen tayi bayan sun gama gaiwa,nan su kace antynmu ina  yayah?


""" rasame yasmeen zatace tayi kawai tace ya fita.,,,


Ihu sukayi dan zasu sakata su wala tunda bayanan bare dakayi abu k'an yyimaka hukunci.


Itadai ammi sai dan murmushi take tana kallonsa.


Maryam yar kimanin 16 years, salim kuma 15 years dan shekara d'aya ke tsakanunsu da gudu suka fad'a jikin ammi kowa na cewa shine Auta.


Yasmeen takallesu tana dariya tace oh Ku ,to nidai kada Ku karyamun ammina.


Murmushi ammi tayi tace hmmm wlh yasmeen haka nike fama da su indai week end ne, abinsu baya tashi sai in yarima baya gidan.


Maryam da kanta ke bisa cinyar ammi tace Anty nice fa k'ara ba salimba,da sauri salim yace ah ah nine karami pls Anty Maryam d'agamun cinyata,itadai yasmeen murmushi kawai take ana cikin hakan saiga su ,munib da muneeba twins din hanan (k'anwar yarima) suka shigo  nan ammi tace to sarakan b'annah waye yakawoku?


"" cikin yarinta sukace driver ne,had'e da cewa ina uncle dinmu yake?"


Ammi tayi y'ar dariya tace bayanan amma ga antinku nan matarsa.


"" da sauri suka fad'a jikin yasmeen suna cewa lah kece amaryar uncle kinada kyau wlh... dariya yasmeen tayi dan akwaita dason yara dan gidansu bbu yara ,tashi tayi tace kuxo muje kunji yaranah.


Bbu musu suka bita,su Maryam kuwa da salim suka cigaba da tab'atarsu ajikin ammi dan hartasaba da hakan.


Yasmeen kuwa itadasu munib da muniba bed room in ta tashige dasu sukayi ta mata surutu had'e da fira nan tabasu su sweet da drinks da biscuit da chacoolat ,aiko cikin murna sukayi ta ci daman abinda suke so kenan har suka gama sukayita dudumarsu ,acikin yini guda yasmeen ta shak'u da yaran basubar part din ta ba sai dasukaji ance yarima yadawo tukum.


Ita kuwa yasmeen tunawa tayi bata gyra masa d'akin sa dan haka ,anayin la'asar bayan tayi sallah  taje ta gyara masa.


Yarima kuwa dayadawo d'azun ganin bata gyaraba  da zaisaka akirata sai yafasa yabari yadawo inbata gyaraba tagane kiranta.,,,,,,


"Koda yadawo saiyaga ta gyara sai kawai yashareta."


Yasmeen kuwa dare nayi saita rufe k'ofar ta tacewa kuyanginta injakkadiyya taxo suce tana part din yarima to sukace ,azuciyarta tace dg yau zan faramaka rashin m ba gobe skul zaniba aisaika ganni bare kamun muguntar.


Bangaren yarima kuwa ,tun 8:30 yake jiran yaga ankamasa yasmeen yabiya bukatarsa amma yaji shiru ,kuma girman kai bazai  bari yyi mgn ba.


Koda yaga 10:00 pm tayi yacire rai da zuwanta ,haka yayita juyi kan bed dg bisani bacci yyi gaba dashi.


Jakkadiya kuwa koda ammi tace taje ta raka yasmeen gun yarima,taje akace tana can ai,saita koma ta sanar da ammi...


Ita kuwa ammi dad'i taji afili tace to hakan yyi kyau ai ,gara da Sarki yace sufara xama gabanmu dan muga kalar zamansu ,da can dg shi sai itane dasunyi yadda suka gadama ga yarima da zuciya,nan ta wuce ciki sukayi sallama da jakkadiya......


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿29&30


Washe gari tun 8:00am yasmeen tagama shirinta kasancewar takira kubra ta tambayeta wane time zasu fara lectures ?

         Tace 10 pm ,tana gamawa tawuce part din ammi tagaidata taxo tayi break ko 10,dinbata idaba driver yakaita skul sai d'adi takeji duka yau 8dsys rabonta da fita amma yau sai wani dadi takeji."su kubra sai tsokanarta take wai tagama boye yarimane mijinta aiyanxun tagane".

Tsaki kawai yasmeen keyi batace komaiba sbd tatsani ayi mata maganarsa.

"Yaya Omar takira tace yazo tana skul su gaisai ," nan yace mata baya gida yanxun haka exam zai rubuta,cikin mamaki tayi masa fatan samun nassara.

         Yarima kuwa sarai yasan yasmeen yau xata koma skul ak'agare yashirya dan yaje yaci mata mutunci dan yaji haushin abinda ta masa jiya, amma sai dai yanazuwa fada gaisheda mai martaba ,aiko yatsaidasa yin wani lissafi,"lokacin dayadawo harta tafi.


       ********

Alh jamilune zaune akatafaren parlourn sa yana hutawa had'e da tunanin yasmeen.

         "  can yyi tsaki had'e da d'aukar wayarsa yakira bala yace yazo yanason ganinsa",yana fad'amasa yadatse kiran.

Befi minti15 ba ,saiga bala yazo ko gaisawa basuyiba alh jamilu yace ashedai wannan mutsiyacin yaron nan yarima yasmeen ta aura?"

Kawu bala yace eh wlh nima jiya nasani dan ko me d'akina hanata nayi xuwa gun dan iskan bikin saidanayi binkice nasani nima.

        "Amme yanxun meye shawara?alh jamilu yace hmmm ai nagama shawara saura aiwatarwa ", kuma ina binkice akan sa ,sbd yasamun ido yanxun haka ancemun yana binkice akaina wlh ,kuma saura2weeks yatafi wata k'asa kaga kafin yadawo saimu shirya.

" Kawu bala yace hakane ,kecewa sukayi da dariya.,,,,


Yasmeen kuwa da dare bayan ta rufe k'ofar ta ,ta kira yah Omar nan yake mata bayani ai scholarship yasamu insha ALLAH da exam d'in dayayi tafito zai tafi kasar Cairo yyi digree d'insa acan .


"Yasmeen taji Dadi sosai nan ta tayasa murna,had'e da tambayarsa shekara nawa zaiyi?"


"Yace biyu"


Amma duk karshen shekara zaizo gd Hutu nan sukayi sallama.


___________________

Hakafa yasmeen tayi ta wa yarima kullum da dare saita rufe k'ofar ta tace ace tana gunsa tun jakkadiya nazuwa harma tadaina xuwa dan duk azatonsu yasmeen ma agunsa take kwana.

     "Shikuwa yarima yana cikin bukatuwa amma yaki nuna hakan ga kuma wasan yan buyan dasuke dan bata yarda ta fito waje saibaya gidan", inkuma skul ne tayi tafiyarta ."gyran d'akinsa intadawo takeyinsa.,,

Shikuwa damuwarsa shine buk'atarsa shiyasa yakeso yaje suyi mgn da salma dan gsky yagaji da jiranta.

Anacikin hakan har sati 2ta wuce Yakama gobene yarima xai tafi Jordan".

Kuma sun gama mgn da Sarki akan banda yasmeen zai tafi sbd karatunta.

   'Ayanxun haka kwance yake kuma yasha alwashin yau kota halin k'ak'a saiya biya buk'atarsa kafin gobe yatafi sbd 3month zaiyi aigara yarage zafi.""""


Yananan kwance yaji horn da sauri yabud'e window kawai yaganta ta fito dg mota alamar dg skul tadawo ga nik'ab daure a fuskarta.


Aida sauri yanufi part din ta sbd yana keys din yabud'e yashiga yarufe ,yatsaya bayan kyaure.


"" yasmeen kuwa agajiye tadawo ,tana bude bed room d'inta ta shige had'e da rufewa ,kokarin cire nik'ab d'inta ta ke,kawai hancinta yajiyo mata k'amshin turaren yarima."";


Arazane tajuyo taga yarima tsaye ,yana jifarta da shu,umin kallo,cikin yatsina fuska had'e da isa yace kin gama kuje kujen ?nace kingama yafad'a atsawace .


Gaba d'aya jikinta rawa yake sbd tsoro fatanta kawai ALLAH yasa kada yakusanceta,murya na rawa tace yi hkuri,pls ayayinda take ja da baya.


"Tsaki yyi yace keki sanshi hkuri ko,yanxun inga wa ya,isa ya kwaceki a hannuna."


Kuma dama inajin haushinki kinmun rashin kunya rannan ban hukuntakiba,ko?


To bari kiji dan nasan kinsan gobe zantafi,kuma ba dauwama zanyi acanba,ko bayan bani nan Kika karayamun dokoki nidakene nadawo,kuma gyara part d'ana farillah agareki,sannan Dana dawo my salma zata shigo gidan nan wato wadda nukeso kixama yar kallo sannan abinda kikak'i badawa dama ni baso nikeba ,ammice ke turoni sbd mace akwai rauni musammun ke dan naga kinada jaraba. Karki fad'a wani yanayi nadaban gara ataimakamiki amma badan wai kinkai ajindazanyi hakan dakeba.


Harara ta galla masa tace mlm ya isheka hakan ,kasani nima bana sonka ko kad'an na yi biyayya ne ga iyayena na aureka amma bawai dan ka isaba dan inada Wanda niko so inkuma batun jarabane aiko bunsuru yasha famaka lfy ta Wannan fannin danban.... Wani wawan mari yarima yyi mata atake tasaki k'ara had'e da dafe gun tana kuka.,,,,


"Cikin kakkausar murya yace ,ke wawiyar inace,da aurena akanki kike zancen wani,hmmmm wlh duk ranar da hakan tasake faruwa saikin gane shayi ruwane,nikike cewa bunsuru ko ?"


,,,,to xannuna  nuna miki aikin bunsuranci,yana fadin hakan yashiga zare belt in dke d'aure ak'ugunsa.,,,,


"tana ganin haka ta tashi dan guduwa Aida sauri yafincikota yahaye samanta ,bbu romancing ya afka mata ,sai ihu da kuka take tana kiran ummanta da yah Omar ."


Yarima be sarara mataba Saida yyi yadda yaso da ita tukum dg bisani yasauka ,itakuawa idonta arufe hawaye nabin gefen nik'ab d'inta ,bayan yamaida kayansa ,yakai hannunsa dan cire nik'ab d'inta sbd kawai yatsintsi kansa da son ganin fuskarta.....wayarsa ce ta yi ringing da sauri yajanye hannunsa,ita kuma ta bude idanunta,taga yana waya yana kokarin bud'e k'ofar d'akinyafita,cikin muryar ta ta zahiri tace ALLAH ya isa mugu azzalimi tana fadin hakan tawuce toilet da gudu tarufe.


Kwafa yyi dan kiran uxuri ake masa a office akan tafiyarsa Jordan, amma sak muryar saitamasa kama da muryar wannan marar kunyar,yasoma ganin fuskarta amma kawai yafita.,,,


Itakuwa yasmeen Saida tasha kukanta,tukum ta yi wankan had'e da alwallar magrib.


Bayan yasmeen tayi isha I,taga ankirata da bakuwar number kuma ta k'asar waje ,cikin mamaki ta d'aga by surprise taji muryar yah Omar .


Cikin shagwaba ta ce oh yah Omar shine kayi tafiyarka bakazomin ban kwanaba?


Murmushi yyi yace sorry my baby tafiyarce tazo ,cikin sauri shiyasa amma aiga waya nan ko saimudunga gaisawa ko?"


"Tace eh"


Nan ta sanar da ita ai kud'i n jarinsa yagyara gidansu yasiya ma umma firigin tana Sana'a kuma rannan Sarki yayiwa umma aike da kayan abinci.


Cikin jin dadi tace kai dan ALLAH yace wlh ,shiyasa nike so kiyi biyayya ga yarima baby dan ALLAH kindace da miji da surukai nagari.


"To Yayana zanyi."


Amma jiya munyi waya da Umma bata fad'a munba.


Yace k'ila ta shafa a be ,yasmeen tace gsky naji dad'in gyara gidan nan da akayi wlh.,,,,


Yace eh nayi hakanne yasmeen dan ko yaya kada dangin mijinki su rainaki duk da cewa mu talakawa ne amma munrik'e talaucinmu.


Yasmeen tace hakane aizanje gidan tunda umma taki zuwarmun taganni saidai muyi waya...


Yar dariya yyi nandai sukayi ta gira har suka gama,sukayi sallama.


Yasmeen kuwa dadi kawai takeji ga kuma wannan d'an zafin kan gobe zai tafi ,kai gobe sai tayi party dan murna.afili tace bbu wani part din sa dazan dunga gyarawa kullum kuma ko nik'ab din saizani skul zan saka ....


Haka tayi ta tunaninta har bacci yyi gaba da ita...


Washe gari tun 8:00am yarima yagama shirinsa yyi sallama da kowa har ammi saidatace yyi sallama da yasmeen ,yace eh sunyi bacci matake yanxun,amma yana mamakin sunanta dan saiyau yaji sunan.


Nan yawuce mota akakaisa airport, bbu nata lokaci jirgindu yatashiiiii......


    JORDAN.....


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮

(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


DUK ZUCIYA TANA SON ME KYAUTATA MATA,TANA K'IN ME K'UNTATA MATA......inagodiya ga masoyana aduk inda kuke..🙏🏻🙏🏻


🅿31&32

  

JORDAN

Yarima nasauka dg jirgi yahau tasi, kai tsaye masaukin salma ya wuce ahanya yakirata har sau biyu bata d'agaba tsaki yyi yana tunanin ina tabar wayar."

      sake kira yyi akaro na3 amma bata dagaba"

Itakuwa salma tana can tana masha arta itada wasu turawa su ukku agado d'aya jin anmatsamata da kira yasa tayi tsaki had'e da mik'e wa don taje ta kashe wayar,tana dubawa taga yarima ne.kuma da layin k'asar tasan yana cikin kasar kenan.

"Zaro ido tayi da sauri ta maida kiran Saida takusa tsinkewa yad'aga ,cikin iyayinta tace baby hii kakira ina bacci ne!yarima yawani yatsina fuska yace eh gani akasar gashima yanxun ak'ofar gidan da kike za'a ajiyeni."

Cikin inda inda tace eh.. to aguna zakazo tsaki yyi yace bansaniba to dawa kike tunani zanje gunshi mitts yakashe wayar had'e da biyan me taxi kudinsa yafito yanufi get din gidan.

       Salma kuwa tanajin yakashe atsorace tayiwa abukan watsewar bayani ga Wanda zai aureta nan zaixo yanxun sutafi ",to sukace nan suka maida kayansu sukafita.

da sauri salma ta fito parlourn gdn shegiyar fuskannan tata a kod'e taci bleaching ga attachment na gashi anmata Kitso dashi danko wankan safe batayiba bad'alarsu kawai suke aikata.

       " suna fita sukayi clashing da yarima ",wani mugun kallo yyi musu dan har cikin zuciyar sa be yarda dasuba."

K'ofar parlour ya murd'a yashiga da gudu salma ta zo ta fad'a jikinsa tana murnar ganinsa.

"Ahankali yajanyeta dg jikin sa suka gaisa takamasa drinks sai kallonta yake dan saiyaga yau duk ta masa muni ,wata zuciyar tace k'ila dan bbu make up afuskarta"

     Fuska ba walwala yace su waye wadancan suka fita dg nan?

"cikin rashin gsky tace ai course mate dintane", tsaki yyi yace me sukazo yi a masaukinki? ai sai in a skul ne har zakiyi wata hudda dasu amma aibbu dacewa suxo matsayinki na musulma me kishin addininta."

Yatsina fuska ta yi tace oh bandanjin dadine sukazo dubani,badan ya yardaba yace ok.

Nan suka fara fira sai wani shige masa takeyi tana iyayi.

"Can yace bara ya wuce masaukinsa zasuyi waya anjima,shagwaba tafara yimasa wai anan xai sauka,had'e rai yyi yace kinada hankali kuwa?" Kodan zan aureki ai ke ba maharra mata bace da zan zauna gu d'aya fke harxuwa wani lokaci".

Ahankali tace eh fa baby dadina dakai kana kishin addininka.

Yar dariya yyi yace nixan wuce saimunyi waya.

har bakin get ta rakosa taso yimasa kiss a kumatu to tanagudun yanxun yaji haushi koyafa wa'azinsa.

"Koda ya fito wata taxi yahau ,ya isa masaukinsa ." su ammi yakira yace ya sauka, tayi murna sosai had'e da cewa yakira yasmeen eh kawai yace dan besan aja maganar danshi ko number ta bashida ita.,,,,


      NIGERIA

Kawu balane tafe kan mashin nasa ,betsaya ko inaba sai gidan su yasmeen dan yasami labarin yah Omar baya k'asar yana waje karatu ,shi azatonsa duk Sarki da yarima ne suka kaisa kuma suna sakarma umma kud'i sosai shine yazo ayi wacce za'ayi ya amshi hakkinshi ,amma a haukansa.

"Tun asoron gidan yaga ansaka tayis ga fenti anyi ancanza k'yaure ,ai afili yace ai dole ma abani kasona wlh dan bazan bar banzaba kokuwa indauki mummunan mataki".

      Kutsawa yyi cikin gidan bbu kowa a tsakar gd ai sai kawai yahankad'e labulen yana harare harare.

" umma kuwa itada inna atika da wata mako'ociyarsu suna fira ,kamar dg sama sukaga Kawu bala ."

     cikin tsanarsa umma tace mlm lfy zaka shigo gidan matan aure?

kallonta yyi sama da k'asa yace ba musayar kalamai nazo muyi dkeba hakkina nazo kibani a matsayina na ubah ga yasmeen  danbake kadai zaki ci dukiyarba nima abani kasona kokuma wlh in...ihun da inna atika ta kurmane yasasa yin shiru jin tana cewa jama'a kukawo agaji kwarto da rana kiriri wayyo ALLAH .... Aisai Kawu yafara zare ido ganin zasu ja masa sharri Aida sauri yana baza babbar Riga yabar gidan yanajin umma nacewa gobe ka amsa kiran alk'ali.

gabansa yaji yafad'i dan ya manta da alkali yahanesa da xuwa gidan nan yaja mashin insa yabar anguwar."""


Inna atika kuwa cikin jin haushin Kawu bala tace to indai anyi bincike  to munzama masu shaidar yazo har gidanki yaci mutuncinki agabanmu.(kasancewar umma ta sanar da ita yarima zaizo yasake binkice akan mutuwar mijinta)


"Nan umma tace eh ngd sosae dan ni nama rasa yazance masa ,aigara da Kika masa hakan,nandai sukayi ta tattaunawa akan maganar.",,,,,


Ban garen yasmeen kuwa tasaki jikinta hankalinta kwance tayi kyau da haske batada wata damuwa ,aikin kawai taci ta kwanta sai suwa skul dan ta aje babin yarima acikin dustbin.

Tsakaninta da kowa lfy dan yanxun ta k'ara shakuwa sosai da ammi inkaganta suna fira ko kaganta kan cinyar ammi baka cewa itace .sunshaku sosai wani lokacin agabanta yarima ke kiran ammi su gaisa da ammi tace kota bata saitace aibasu Dade da yin wayaba.


Maryam ,salim munib da muneeba kuwa sun shak'u sosai da yasmeen dan su Maryam da salim ksi tsaye yanxun suke xuwa part dinta su sha fira wani lokacin siyita bata labarin kirkin yarima da kuma yadda yake hukuntasu insunyi laifi agidan. ..

Bata cewa komai saidai tayi murmushi kawai amma azuciyarta tanajin haushinshi sosai.

" wani sa inkuma apart d'in ammi ake firar tare da ammin."



Twins kuwa duk week end hanan ko driver ke kawosu gun yasmeen har ammi na mamakin shakuwarsu da yasmeen......


       **********


Yarima ne zaune awani park yana hutawa gabansa wasu turawa ne dg gani masoyane ,mace da nmiji,sai hira suke be auneba yaga wata tazo watsawa saurayin maltinah ajikinsa tanamasa bala I....


"" atake yarima yatuna da marar kunyarnan data watsa masa  viju milk ,wato yasmeen danbesan sunantaba marar kunya shine sunan da zuciyar sa take kiranta da shi.,,,,


Tuno dan karamin bakinta yyi Wanda take murgud'awa tana rashin kunya dashi ,afili yace haba ai xankoma gd duk sadda Muka sake had'uwa dke saina fasa bakin tsiwar...


Tashi yyi tsaye dan tafiya,tunawa yyi da rabonsa da  ganin sallama yaukusan 10 days jiyayi yanason ganinta..


"Taxsi yahau yawuce can".


Bayan yasallami dan taxsin  ya wuce cikin gidan.


Aparlo yaga bbu kowa zama yyi yana tunanin kotana toilet amma shiru yakira wayarta bata shiga..


" tsaki yyi yace to tana ina?"


Mik'e wa yyi don fita wata xuciyar tace kashiga ciki kaduba kasan ko ba lfy in wani abu fa yasameta ,bakowa agdan gashi kai ALLAH yakawoka..


da sauri ta wuce hanyar bed room dinta.


"Yana xuwa ya murd'a k'ofar d'akin...


Salma da ke zir itada abokan masha ar tata akan bed suna aikata bad'alarsu jin anmurdo k'ofar yasata d'agowa da sauri by surprise sukayi ido hudu da yarima...


Share pl


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿33&34


"" salati kawai da inna lillahi wa inna ilaihir raju un kawai yake maimatawa."

saurin juyawa yyi yabasu baya dan besan ganin tsiraici wani.

      "cikin rawar jiki had'e da fad'uwa gaba salma tayi saurin zura doguwar Riga ta kori abokanan watsewartata ," da gudu ta fito dan taga yarima yafita a hassale.

dede get tagansa zai bude yafita sai kwala kira take be sauraretaba yabude get zai fita tayi saurin rik'emasa Riga.

Ahassale yajuyo had'e da d'auketa da kyawawan maruka masu rai da lfy yabuge hannunta data rik'esa yanunata da yatsa cikin mugun tsanarta yace  inaso ki dauka baki tab'a sanin wani yarimaba arayuwarki ko a hanya Kika nuna kinsanni wlh sainamiki abinda zakiyi nadama na tsaneki bana k'sunarki ko kad'an na kuma godewa ALLAH da yatoni asirinki kafin na aureki ran da bayan na aureki Nagano hakan hmmm sorry for your self wlh.

Cikin kuka tace haba baby kayi hkuri meyayai zafi haka kuskurene kada kamun haka bazan ...tsakin da yyine yasakata yin shiru ,miyau ya tsitta yace wawiya kazama ,shaid'aniya to kimasani Dana aureki wlh gara na tabbata bbu aure arayuwa ta zan miki adduar shiriya inda rabon zaki shiryu,dama ni bawani sonki nikeba Balle kiyiwa xuciyata lahani kekika tura kanki gareni  dan haka yarima ba naki bane .

"Ayanxun haka inada mata agd inbaki saniba kisani ."

      Sannan dg yau bazaki sake ganinaba agidanki keko wani gunma Kika ganni Kika nuna kinsanni hmmmm kinsan sauran,ayanxun haka sai naje nayiwa jikina wankan tsarki sbd nashigo gidandake da najasa da k'azanta hatta kayan dke jikin innacire su yanxun nida sakasu har abada wlh ,yana kaiwa nan yyi tsaki had'e da ficewa dg gidan.

Itakuwa guiwa sake ta koma ciki saidai tasha alwashin ta koma Nigeria saita binkice akan wacce yake cewa ya aura ....


Yarima kuwa rai bace ya isa masaukinsa,toilet yashige yyita wanka kamar zai canxa fatar jikinsa.,,,


"" bayan yashirya yaxo yakwanta rai bbu dadi,tunanin irin wulakancin da yyiwa yasmeen kawai yake yi,tunawa yyi a first night d'insu  yayimata mugunta kuma yasameta budurwar,yatuna irin wulakancin da kuntatawar dayaruk'a yima duk sai yaji jikinsa yyi sanyi."duk sai yaji tausayinta."

     Afili yace anya ba hakkin yarinyar nan bane ke bina? ji yadda salma halinta yakasance Ashe ita bata garice ,ALLAH na gode maka daka baiyanamun abinda ke boye,lallai gara da nayi biyayya ga iyayena da yanxun banyarda da wannan aurenba da nayi asara biyu oh lallai insha ALLAH bazan sake cutar musu da yarinyaba ,amma fa bazan dauki rainiba .,,,,,


Haka yarima yyita tufka da warwara shi daya da ga bisani bacci yyi gaba dashi.


*****  *****  ******


Yarima ne zaune yanata shirye shiryen komawa Nigeria sbd yagama   abinda yakawosa amma bai sanar da kowa ba yanaso yyi surprise dinsu kawai...


"Yana gamawa kai tsaye air port yawuce bedadeba jirgin su yatashi."


       NIGERIA


Yasmeen ce da Maryam a part din ta suna fira ,kawai taji ta tuna da yarima,gabantane yafad'i data tuna tunda yatafi bata gyara masa part dinsa ba gashi yau yafi 3month datafiya ,Aida sauri ta kalli Maryam tace mery bara naje part din yayanku nadawo."'"


Maryam tace to Anty nan ta fice dg dakin.


,,,,itama yasmeen fita tayi taje ta bude' part din ,gun ksyan wankinsa ta duba yagansu da sauri ta wankesu Ta's ta shanya sannan ta fara gyaran ko ina napart dinsa.,,,,


6angaren yarima kuwa tun a jirgi yakira sarkin gd yace kada yasanar da kowa yaturo masa motoci azo adsukesa yanxun a ai port....


Yana sauka kuwa yasami driver da guards dinsa sunxo faukarsa ,nan sukayita kawo gaisuwa ,had'e da bud'e mota yashiga akajata..


"Yasmeen kuwa bsuan ta gyara ko ina toilet yarage da sauri ta kwaso kayan yarima ta aika aka kira sarkin gd tace tabasa nan da awa1 yagoge yabada akai part dinta .


Haka kuwa akayi  sadda ta gama komai ta turare dakin ta fita tasamu har an kawo kayan da kanta ta d'auko tazo ta bude sif din kayansa dan jerawa tsaye tayi baki sake ganin lodin kayan yarima ,hartafara jerawa taji fitsari da sauri ta cire gown din dke jikinta yazamana dg ita sai wando iya gwuiwa Wanda yyi bala'in fito mata surar mazaunanta sai have vest wadda ko cibiyarta bata rufeba ta shige toilet ...


Bayan ta fito nata tsaya mayarda rigarba tacigaba da jera masa kayansa...


driver nayin parking aka budema yarima ya fito kai tsaye part din ammi ya wuce ,yasameta kishinged'e ana mata fita aida saurita tashi tana cewa ah ah wanake gani ?my son xuwan bazata ,murmushi yarima yyi ya rungumeta nan barori da kuyangi akayita xubewa ana kwasar gaisuwa gun yarima dayimasa barka da dawowa .,,,,,


"" ammi ce ta kallesa tace amma yasmeen bata saniba ko ?"


Yatsina fuska yyi yace eh bata saniba.


Ammi tace oh Ashe itama baka gayamata ba,to kaje ka watso ruwa kazo kayi lunch ko?


"Ahankali yace to ammi nah had'e da ficewa yanufi part dinsa."


Yana xuwa ya murd'a k'ofar by surprise yaji ta bude wani k'amshi yadaki hancinsa, da mamaki yakutsa kai ciki ....


Share...


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿35&36


Straight bed room yanufa "ahankali yabude k'ofar by surprise yaganta tsaye gun sif d'in kayansa ", tana shiryamasa su.

     Wani irin tausayinta yaji ,domin yalura tanada biyayya dukda akwaita da tsiwa.

" kurema jibgegen k'ugunta yyi da ido yana kallo",azuciyar sa yace dama haka yarinyar nan take.

Atake yaji tsohuwar sha'awarsa ta motsa."

Amma saiyayi shiru yanaso yaga tajuyo kozaiga fuskarta.

Yasmeen kuwa batamasan dashiba tana gama jerawa ta rufe ,kawai sai hancinta yajiyo mata k'amshin turaren sa da sauri ta juyo idanunta tsab cikin na yarima."

Cikin tsantsar mamaki yarima ke kallonta azuciyarsa yana cewa me marar kunyarnan taxo yimun ad'aki?" Wata zuciyar tace kasan ko itace matar taka ko kanwartace ......

Yasmeen cikin firgita ta dauki gown dinta dan sakawa dan batayi tsammanun xaidawo yauba tunani take  yau tafaru ta k'are yaganta bbu nik'ab oh lallai amma to sai me inma yagane ashirye take da rama abinda yyi mata. "Shikuwa yarima dayake dan duniyane saiya boye mamakinsa naganinta  dan be tabbata itace amma bara yyi mata wata tambayar ko tanan zaigane in itace .

Fuska a had'e yawani kalleta yace keeeeeeeee!

" meya kawoki  d'akina ?"cikin tsiwa tace to bakaine kace na ringa gyarawaba kobakanan!

Atake yagane cewa itace  kenan ,shine ta boye kanta tunda tasan batada gsky ,haba shiyasa dayakalli idanunta saiyaga kamar yasan me irinsu Ashe itace aiko yanxunma yafara hukuntata.

Yatsina fuska yyi ganinta saka gown dinta, yace ke kin gama boye wannan kazamar fuskar taki  kin dauka ban sankebace akabani sadaka ,ai k'yaleki nayi naga iya gudun ruwanki ,,,,.


"" murgud'a baki tayi tace eh din saika dauki mataki.""


A hassale yyi gunta aiko ta kauce tana son gudu ,nan suka fara zagaye d'akin ",yarima yaga inbaiyi da gskeba bazai kamata .aisaima tarainasa cikin xafin nama ya cafkota had'e da wurgata saman bed yyi suka zai fad'a kanta ,cikin zafin nama ta mirgina gefe yafad'a kan katifar had'e da bige kansa.'''''

" aiko yasmeen ta kwashe da dariyar mugunta had'e da cewa alhakinane kuma kaida ALLAH wlh."

Tsaki yyi had'e da fisgota ya mirgina yadawo samanta, da sauri ta rufe idonta tana turesa had'e da son kwatar kanta amma ta kasa cikin husky voice insa yace kingama yimun rashin kunyar da dariyar??"

      Kinsan dama inajin haushinki ,kimmun ALLAH ya isa ko ?


Shiru tayi taki bude idanunta ga hawaye harsun fara zuba dan tasan saiyayi sex da ita.


"" amamakinta taga yana korin cire mata kayan jikinta duka abinda baitab'a yimataba kenan.""""


Cikin kuka tace dan ALLAH ka bari wlh nadena maka rashin kunyar kayi hkuri pls.


,,,ko sauraronta beyiba da karfi yacire mata komai had'e da Jan bargo yarufesu ,yahau romancing dinta abinda baitabayiba.,,,,


Ita kuwa ta rufe idonta sai kuka take ta tsaya kamar gunki ki mitsin kirki takiyi sai hawaye kawai dake ta xuba afuskarta.


Yafi awa d'aya akanta Saida yasami gamsuwa tukum yasahirta mata ,amma yana jin zafin yadda duk sadda yake kusantarta take wannan kukan da k'amewa gu d'aya ,koda yatashi dg kan bed din tsaki yyi hadeda shigewa toilet .,,,,,


Tanajin karar rufe k'ofar toilet din ta bud'e idanunta da k'yar ta tashi sbd yadda takejin zafi ak'asanta.


"Ahankali tamayarda kayan jikinta ta xo xata fita  Dede toilet ta tsaya   da iya k'arfinta tace ALLAH ya isa mugu azzalimi ,kuma an k'ara cewa d'in... Tana fadin haka tayi sauri ta fita abinta.


Shikuwa yarima sarai yajita ,kwafa kawai yyi yace haba yarinyar nan zanyi maganinki wlh dani kike mgn.,,,,,


Yana gama shirinsa cikin kananun kaya sai wani kamshi yake yi nadaban ,sajen nan nasa yak'ara fito da kyawun fuskarsa.

          Gun dining area ya wuce yafara lunch.,,,,,


Yasmeen kuwa baiwar ALLAH Saida ta shiga ruwan dumi  ta gasa jikinta sannan ta yi wanka ta  ta kwanta tayi bacci ,bayanta tashine tayi sallar la'asar ta wuce part din ammi...,,,


Yarima kuwa yana gama lunch yakoma part dinsa yadauki laptop yafara aiki ,Kiran la'asa yasashi ajiyewa ya wuce masjid din dake cikin masarautar yyi sallah .,,


" koda yafito dg masjid part din ammi ya wuce dan yanason yasha fura mutuniyar tasa."


Yanashiga ,yaga kan yasmeen bisa cinyaryar ammi kuma kanta bbu d'ankwali ,ammi nashafa kanta datayi parking dinsa yyi liya liya baki  k'irin dashi.  d'ayan gefen ammin Maryam ce kanta kan kafad'ar ammin suna dariya ga salim tsaye gefen Maryam yana tab'ara wai sai Maryam ta tashi yazauna.


Cikin mamakin yadda yasmeen tashaku da ammi yakarasa parlon da sallama.


Aida sauri salim ya zauna dan yana mugun tsoron yarima,hararansa yarima yyi yace me kakeyi  cikin mata?"


Ammi ta karba da cewa gun amminsa yaxo ai,kwafa had'e gallawa salim harara yarima yyi yace ammi ki shagwaba yaran nan da yawa wlh  duk saina gyara muku xama,kallon Maryam yyi yace daga mata kafad'a da sauri ta janye kanta data aza bisa kafad'ar ammi.


Satar kallon yasmeen yyi wadda atsorace take dan tasan ta masa laifi,kuma ammi na lura da yadda ta tsorata dan taga yarima...


Yarima yyi mamakin gashin yasmeen kamar ba yar hausawaba wannan gashi haka can kuma sai yyi tsaki har yafito fili ,har ammi tayi masa kallon tuhuma,da sauri yace ke waiba Nahanaki yawo bbu d'an kwaliba?


"" cikin mamakin karyar sa dabayajin kunyar yinta yasmeen ta jawo d'an kwalinta ta d'aura,,,,.


"girgiza kai kawai ammi tayi batace komaiba."


Maryam da salim ma sunyi shiru dan sun San abu kadan inkayi to laifine agun yarima.


,,,,,yarima kuwa tunawa yyi da ALLAH ya isa da yasmeen tayi masa ,wani murmushin mugunta yyi had'e da mik'e wa tsaye ya kalli yasmeen da kanta kebisa cinyar ammi yace taso muje inbaki tsaranarki...


Ammi kuwa har cikin ranta taji dad'in hakan, kallon yasmeen tayi ta ga duk ta wani rude, tace yasmeen bakiji abinda mijin naki yace bane?


,,,cikin dan tsoro tace kaje ganinan,wani hausji yaji tana masa musu agaban yara,atsawace yace xakixo muje ko kuwa... hararar da ammi ta masa ce tasashi yyi shiru ,sum sum yasmeen ta shi tabi bayansa.........


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿37&38


Yasmeen na fitowa taji an funcikar mata hannu Ashe yarima ne ,yalab'e yanajiranta."

     K'ok'arin kwacewa take amma yak'i saketa harara ta galla masa had'e da cewa mlm lafiyarka kuwa?" Ina zamana zaka wani kirani !

Murd'e mata hannun yyi yace bansani ba,muje ki karbi hukuncinki ba ALLAH ya isa kikamunba ko?"

Hmmmm wlh ki shiga hankalinki dani ,cikin jin zafin murde mata hannu da yyi tace pls sakeni sai muje ",as hek'e yakalleta cikin bada order yace muje ,ganin bbu wasa a fuskarsa yasa tayi shiru fuskarta daure gashi yaki' sake ta a haka suka nufo part dinsa inma yaga mutane ko ajikinsa bayajin komai dan anganshi rik'e da hannunta.

" kan kujera ya zauna had'e da sake mata hannu fuska d'aure yace oya zokimun tsallan kwad'o "!

      Zaro ido tayi had'e da cewa what? Yace yes kobazakiyi bane?"

Cikin tsiwa tace eh baza ayiba nafi karfin hakan wlh kaida ALLAH ka zauna kayita cin zalin dina ta fad'a had'e da Jan doguwar tsuka.

Cikin mamakin ta had'e da jin haushin ta yace nikikewa tsaki?"

Tace eh anyi saika dauki mataki dayadace.

Ahassale yamike kafin ta arce yarik'e ta har yad'aga hannu da nufin marinta komai yatuna sai yafasa ,yaja tsaki had'e da cewa ni abokin wasankine yaushe nafara wasa dke ne ?? Belt din dke k'ugunsa yafara k'ok'arin cirewa da sauri yasmeen tace me xakayi inkacire  batare da yakalleta yace abinda nayi d'azun ko zaki hana?"

Cikin muryar shagwaba ta ce ayya wlh nabari kaji bazan sake maka rashin kunyar ba  dan ALLAH kada kayimun komai wlh banaso ....hararanta yyi yace stupid girl kawai oya tashi kimun tsallen kwad'o ko kuma nasake maimaitawa yanxun nan".

Haka kuwa akayi tana hawaye tana tsallen kwad'o tun tana na marmari hartafara galabaita ,shikuwa yarima latsa wayarsa kawai yake bema damu da itaba.

Zuwa can tasaki k'ara had'e da fad'uwa k'asa .

      "da sauri ya kalleta yawani yatsina fuska yace saiki tashi kije ciki duk ranar da kikasamun ALLAH ya isa sainamiki abinda yafi hakan."

Batace komaiba ba ,tafita da k'yar take tafiya sbd jitake cinyoyinta na mata ciwo.

Tana fita kuma duk sai yaji bbu dadi ganin tana kuka kuma batace komaiba.

Tashi yyi yawuce toilet yyi arwallar magrib .

Yasmeen kuwa cikin mugun tsanarsa ta nufi part dinta tasa ruwan zafi ta gasa cinyoyinta tayi sallar magrib ,tananan akayi isha'i bayan tayi ko abinci bata Ciba ta kwanta da alk'awarin d'aukar fansa gobe."

"Ammi kuwa ganin yasmeen shiru yasaka ta tura salim ya duba a part din yarima yaga tana can in tana can yakyaleta inbata can yakirata,aiko yaje a window salim yaga yadda yarima yasaka  yasmeen tsallan kwad'o aiko yaje yasanar da Umma ranta yab'aci sosai ana gama isha i ta nufi part din yasmeen ,har bed room dinta taje tasameta kwance dukda yasmeen din ta boye damuwarta amma kallo d'aya ammi tayi mata tagane ,bayan sun gaisa ta tambayeta da gske yarima yasaka ta tsallen kwad'o ,kawai sai yasmeen ta tuna yadda yakaresu a kotu ai itama yakamata ta karesa nan tace ah ah  wasa ne suke shine ta duk'a amma besakataba.

" cikin mamaki ammi tace to shikenan nan sukayi sallama."

Yarima kuwa har cikin ransa beji dad'in abinda yyi wa yasmeen ba ,part din ammi ya wuce,k'ila ma tana can wata zuciyar tace masa ,yana xuwa ko gaisawa basuyiba ammi ta zaiyane masa yadda salim yafad'a mata da yadda yasmeen tace mata,had'e da cewa meye gskyar maganar?"

shikuwa yarima yyi mamakin yasmeen bewar ALLAH wato taji maganar dayaga yamata akan kada ta kai kararsa gun iyayensa da watace saita fad'a inyayi mgn tace ai tambayarta akayi ."ahankali yace eh umma wasane muke k'ila autanki be luraba zaizo yahad'a nidke.

Murmushi tayi tace ai gsky yafad'a dan banaso kaci zalinta dan wlhy kadace mata ga ta da biyayya ,yarinyar nan bata tab'a yimun musuba ko gaddama duk umarnin Dana bata bitakeyi.

Shiru yyi yanajin wani irin tausayinta duk sai yaga be kyautaba kuma ai shikeja tana masa rashin kunyar.

Sallama yyiwa ammi yatafi part dinsa ya kwanta..


Washe gari yasmeen ce ta fito dg toilet dg ita sai towel Wanda ko Rabin cinyoyinta be rufeba ta tsaya gaban dressing mirror tana taje gashinta ji tayi an murd'a k'ofar tana juyowa taga yarima dg shi sai farar jallabiya ajikinsa  ,batace komai ba taja hijab ta rufe jikinta ganin yadda yatsareta da idanunnsa.


"" tsaki yyi yace ke meye nawani rufe jiki meye abin kallo ajikinki.""


Ayatsine tajefesa da wani mugun kallo had'e da cewa abin ganin ka gani shiyasa da baka ganiba dabazakace meye na rufewaba kuma dan ALLAH inkanada zuciya dg yau kada kasake kusanta ta tunda bbu abun gani ajikina,,,,.


Mamakin ta kawai yake yama rasa me zaice ,amma saiya basar had'e da cewa oh ai ammi zaki gayamawa ai ita ke turoni ,amma nibaxanyi musu da itaba.


Abinda yakawoni  kije kihadamun ruwan wanka zanje na gaida su ammi da mai martaba,innadawo baki had'amunba kinsan sauran kema,yana fad'in hakan fuuuuu!!yafice tsaki tayi tace bazan had'anba ka kasheni in ka tashi...  can kuma tayi shiruuuu da sauri tace yesssss!hakanko zanyi in rama abinda yyi munko..


da sauri ta saka doguwar Riga ta fito ta nufi kitchen da sauri ta duba gunda cefane yake Wanda aka yanka bbu bata lokaci ta wanke ta tace ruwan da rariya tasamu dan karamin bucket ta juye sai murmushin mugunta take ta wuce part din yarima...


,,,,,tana xuwa ta wuce toilet ta had'e masa ruwan wanka had'e da juye ruwan datawanke cefane dasu ciki da sauri ta fito ta wuce part din ta Dan tashirya tayi tafiyarta skul inma yaga ne itace to bazai sameta agidanba.,,,,,


Yarima kuwa yanadawowa dg gaishe da iyayensa ya wuce toilet  yashige cikin bahon wanka yafara watsawa jikinsa ruwa xuwa fuskarsa  arazane yabari sakamakon yajin dayaji a fuskarsa da idanunsa aisaiyaji gaba d'aya jikinsa yadauka da zafi da rad'ad'i cikin firgita yafita dg cikin bahon wankan ko ina jikinsa yaji yakeji da radad'i kamar yyi ihu ga yakasa bude idanunsa be aune ba yabigi bango besan sadda yasaki k'ara ba azuciyar sa kuwa yana tambayar kansa meke shirin faruwa danine? dafe kansa yyi yanajin yana Sara masa dan yabugu sosai lalibe yarikayi har ya iso gun tape yakunna  da sauri yafara wanke fuskarsa  amma nata dainaba cikin dauriya ya bud'e idanunsa dasukayi jajir yadauko sabili ya sabe jikinsa ko ina da fuskarsa  amma be denajin zafin da radadinba yadai rage ,tunawa yyi da yasmeen ce yace ta had'a masacruwan wanka,wato itace tayi masa hakan lallai yarinyar nan ta tsanesa da yawa ta iya ramuwar gaiyya amma zasu hadu ne da ita ...


Haka yayita  tunane tunane da jin haushin yasmee har ya fito dg wankan amma jikinsa bedawo normal  ba a fili yace amma yarinyar nan batada tausayi  ko kad'an amma zankamata yau ...


         *********


6angaren yasmeen kuwa tana skul amma data tuna yarima saitayi ta dariya son ranta tana hango yadda zai ruka zangai inyaji yaji...


"" bata dawo gidaba sai gab da magrib dayake tasan batada gsky sai ta rufe part din Saida akayi isha I sannan ta nufi part din ammi ."""


Bayan sun gaisa ta zauna suna fira,kamar dg sama saiga yarima yashigo da sallama abakinsa  yazauna suna gaisawa da ammi yasmeen kuwa kamar ta xura aguje dan tana gudun kada yace ta tashi suje ... bata gama tunaninba taji yace baby Ashe kina nan Kika barni ni d'aya ko to xo muje ni bacci nikeji ...


Zaro idanu kawai yasmeen keyi, cikin in,ina tace um um nidai kaje zamuyi fira da ammi na...


Ammi daketa faman murmushin jin dad'in yadda yarima yafara son matarsa har sun fara sabawa tace oh nibbu ruwana da shiga tsakanin mji da mata kibi mijinki kike Saida safe..


Cikin shagwabar da yasmeen batasan tayiba tace  pls yayah kaje gani nan xuwa..shikuwa yarima mamakin jin takirasa da yaya yake yasan pretending ne tayi kamar yadda shima yyi amma har azuciyarsa yaji dad'in yayan datace inama ta ruk'a kiransa haka ga shagwaba r data fara kamar katta dena ..


"Fita yyi hade da cewa wato firan sirri xa ayi ba'a naji ko ?" To natafi ya fice.


Girgiza kai ammi tayi tace oh yasmeen ni nalura da kamar ma gudun mijin naki kike ko?


"Ahankali tace ah ah ammi."


Ammi tace to tashi kije gunsa kinji y'ata ,jiki na kwari ta mik'e dan tsoronta guda kada yyi irin na jiya ya lab'e..


Tana fita tabi wani corridor Wanda said sadata da part d'insu taji an fisgota hade da rufe mata baki tana juyowa taga yarima ne....


Share pls...


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writers)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Wannan page din nakine baby Musa kiyi yadda kkso dashi ,ina mugun jidake irin totally din nan.😍😍


🅿39&40


Ciki tsorata tace meye haka wai?bece komai ba yaja hannunta da  k'arfin tsiya ,tana turjewa amma yak'i saketa

      "part d'insa yanufa da ita ". atake jikinta yafara rawa dan tasan me kwatarta sai ALLAH.

" ahankali tace pls kayi hkuri wlh nabari!tsaki yyi had'e da makata saman bed yace aidama haka kike cewa kinbari amma gobe ki k'ara garama kinyi shiru dan yau hukuncinki sai na kwana inayin sex dake.

"Kafin tace wani abu ya afka mata yafara romancing d'inta azafafe."

       Itakuwa tashiga aikin nata wato turesa da kuka amma bemasan tanayiba.

"Aikinsa kawai yakeyi, haka yyita abinda yaga dama da ita har yasamu nutsuwa ,asannan yalura da yadda take kuka kamar ranta zai fita."

wani zafi yaji axuciyarsa dan yanxun mugun jin haushi yake inxai kusanceta ta rik'a masa irin wannan kukan nata sai kace wadda suka aikata aikin ashsha ne da ita."wata zuciyar tace masa k'ila dan ta tsaneka shiyasa.

       "doguwar tsuka yaja had'e da shigewa toilet ," yana shiga ta tashi ta wuce part din ta dan ta jigatu a hannun yarima.

shikuwa rai bace yashirya ya kwanta abinsa har bacci yyi gaba dashi.

"Yasmeen kuwa ta d'auki niyar ramawa amma ta bari sai gobe byan tadawo dg skul dan gobe da safe zata tambayesa taje gidansu tun sadda taxo gidan bata tab'a xuwaba saidai syi waya da ummanta.....


Washe gari bayan tagama shiryawa tasaka nik'ab d'inta ta nufi part dinsa ,gaban mirror tasamesa yana fesa turarukansa ,adak'ile ya amsa sallamar ta ta sbd har yanxun haushinta yake ji.

     " ahankali tace damaaa...dama in in ...innadawo dg skul zanje gidanku tunda nazo bantab'a zuwaba."

ayatsine yace  kebaki iya gaisuwa ko?kinwani kama cewa dama dama .. Mitt's bakimasan sunanaba ko to inbazaki kira sunana ba kifasa xuwa.cikin marairaicewa tace pls kaji kabarni,tsaki yyi yace bazakijeba.

Ahankali tace innace maka yaya ba laifi?"

"Aitake kansa yawani fasu cikin k'asaita yace inzaki iya ba damuwa yafada had'e da tab'e baki."

Ashek'e yasmeen ta kallesa sama da k'asa tace never wlh nakiraka da hakan har kafara jin dadi ko ta bakasamu, tafad'a had'e da galla masa harara.

       Afusace yace to bazakijeba stupid girl kawai aikece da tura kai kin wani shigomun daki oya get out of my room.

"batace komai ba ta fita ,amma tasha alwashin saitaje kota halin k'ak'a ,part din ammi taje ta fada jikinta tana kukan shagwaba had'e da cewa ai gd takeso xuwa yarima yahanata..

Nan ammi takirasa yana dagawa tace oh waimeke damunka ?,kasakata adamuwa bakaganin bata tab'a zuwa gidansuba tunda taxo.

" ahankali yace ayya ammi wasafa nake mata taje shikenan murmushi tayi tace yauwa ALLAH yyimaka albarka,takashe wayar had'e da kallon yasmeen tace to y'ar ammi kije wasafa yakemiki  ainasan bazai hanakiba.

To tace sukayi sallama ta fita.

Yarima kuwa sai sauri yake yaxo part din ammi gaisheta koxaiga yasmeen amma yana zuwa yaga wayam.

"bayan sun gaisa ammi ta kallesa fuska bbu walwala tace wato kai bakasan abinda yadaceba ko?"

"Ahankali yace menayi ammi?

       Tace rashin xuwa ka gaido mahaifiyar yasmeen mana.

Shiru yyi bece komaiba,ammi tace to gobe tunda lahadi zan saka sarkin gd yakaika gidan kagaisheda surukartaka dan baban yasmeen din ai yarasu saura mamanta tarage.

" wani tausayin yasmeen yaji ashema ita marai niyace".ahankali yace to ALLAH yakaimu sukayi sallama yafita.,,,,,,


       ***********


Yasmeen kuwa sai gurin 2:30pm suka gama lectures nan driver yadauketa sai gidansu ,bayan ta fito dg motar tace masa yadawo4:00 pm yad'auketa."""


,,,,tun a soron gidansu taga canji da irin gyaran da yah Omar yafad'amata yyi,cikin murna tayi sallama ,umma dake d'aki tafito jin muryar autarta da gudu yasmeen taje tayi hugging dinta suna murnar ganin juna suka shige daki....


Nan fa yasmeen tayi ta ma umma fira da shagwarta ,sannan taci abinci ,umma tayita mata nasihar xaman aure da yayi biyayya ga mijinta suna nan akayi kiran sallar la'asar.


Nan yasmeen tayi sallar, umma tabata wani magani kala 3,wai na zafine ta rik'a sha da madara da kuma wani na ruwa a jarka nan yasmeen tace ta gode dan tayarda maganin zafinne.


Nan driver ya aiko taje,sallama sukayi da Umma tabata daddawa,kub,ewa busassa,kuka ,man sharu takaiwa ammi...


"" koda suka isa gida yasmeen part din ta ta wuce taje ta shirya cikin Riga da sket na pink lace tayi masifar yin kyau ga maroon lip stick tashafa sai k'amshi take ta nufi part din ammi..""


Bayan sun gaisa ,ammi sai masha ALLAH take cewa azuciyarta dan bbu karya yasmeen tayi kyau,sakon ummanta taba ammi nan ta karba cikin jindadin kayan tana godiya.


Bbu jima yarima yashigo dan yasha fura ,kawai yasami yasmeen acan,bayan yagaisheda ammi ,yakalli yasmeen cikin pretending yace oh baby shine baza'amun mgn ba ko?wato d'azun nayi laifi ko?to aiyanxun kinje kin gaidota ai,turo baki tayi tace um um niban hakuraba munbata.


Murmushi ammi tayi cikin jin dad'in yadda suka fara son junansu tace nidai bbu ruwana ni y'ar kalloce...shiru tayi sakamakon yaya sageer dayashigo dakin.(dan dakin hjy rahama Wanda ke amerika karatu) hugging din ammi yyi suka gaisa ,yadawo yyi hugging din yarima bayan sun gaisa ya zauna yana tambayar umma su twins din hanan,idanunsa suka hasko masa yasmeen ,wow kawai yace axuciyarsa yakureta da idanu dan shima ba laifi guy d'in yahadu.


"Ahankali yasmeen tace ina wuni yah hanya??" dan ta tsargu da kallonta dayakeyi.


Shikuwa yarima kafesu yyi da ido yanajin wani haushin da besan kiname bane .


Murmushi sageer yyi yace wow she is very beautiful..had'e da kallan ammi yace  ina kikasamu wannan babyn?


"Murmushi ammi tayi tayi saurin cewa ai antynkuce yasmeen mstar yarima kasan kanacan akayi auren dan umma ta lura da yadda yanayin yarima yacanxa shiyasa tayi saurin sanar da sageer kowacece yasmeen.


Tashi yarima yyi had'e da dakewa yasaki murmushi had'e da mik'awa yasmeen hannu yace baby xomuje nayi wanka kinji..


,,,,mak'e kafad'a tayi tace um um nidai,girgiza kansa yyi yace inbakixoba bazan sake goyakiba,d'an ware ido tayi kamar gaske tace um um sorry muje amma zaka goyanin kaji ta fad'a cikin muryar shagwabar da batasan tayiba...


Sageer kuwa cike da tsantsar sha'awar su da yadda suka birgeshi yake kallonsu ,yana cewa aransa ALLAH yasa minal dinsa taruka masa haka suna soyewarsu dan bikinsa befi sati3 ba,dan gsky broth dinsa yaga sa'a dayasamu wannan xuk'ekiyar yarinyar.


Ammi kuwa cikin kunya takalli yarima ganin zai kama hannun yasmeen tace oh son yanxun kazama marae kunya ko?


Sosa kai yyi yace to ammi kice ta tashi muje ko.


Tashi yasmeen tayi ta ce muje tana murmushi,shikuwa sageer kallon ammi yyi yace bara nashi ga ciki,nan suka fito dasu yarima suna fira kowa yyi gun daya nufa.


" suna shan kwana yasmeen ta kwace hannunta ,bece mata komaiba yajata suka shige part dinsa.


Kayansa yafara kokarin ragewa,tuni yasmeen ta fara zare ido ,cikin tsawa yace dallah mlm kije kihadamun ruwan wanka kin dauka wani abu zanmiki?"


Sum sum ta wuce toilet, bayan tahad'a ta fito fuska asake dan har tatuna muguntar dazata masa.


"" daga shi sai boxer ajikinsa ,kalli d'aya yasmeen tayi masa ta dauke kanta dan bata taba ganin nmj babba ahakaba ko yah Omar agidan kwana yake wanka kuma shima yarima bata tab'a ganin sa bbu kayaba dan duk lokacin da zai kusanceta idonta arufe yake.


Duk saita ji tsoro ,nufota yyi yace shine kikaje Kika had'ani da ammi ko?yafada had'e da matsawa gab da ita kamar zai rungumeta.


Cikin tsoro ta kafe kirjinsa da gashi ke kwance bak'i k'irin tana mamakin ganin jikinsa a murde kuma duk gashi.


"Cikin shagwaba ta ce to bakaibane kak'i barina.hannu yasa ya dan murde mata baki ,yana kallonta dan yau ta masa kyau,fuska adaure yace dg yau nasake ganin kinje part din ammi bbu alkhabba ajikinki nidakene ,yafasa had'e da murde mata kunne,yar k'ara tayi tace to pls sakemun kunne kaji?


"" saketa yyi cikin wani yanayi yafad'a toilet din. "


Yana shiga ta koma part din ta, kitchen ta wuce gun da ake aje kayan miyan gargajiya ta bude had'e da d'akko yaud'o ta fito tana dariyar mugunta cikin wani cup ta xuba hade da xuba ruwa taje dadai toilet din da yarima ke wanka taxuba bakin k'ofar.,,,,


da sauri ta fita had'e da tsayawa abakin k'ofar ta labe ta hangen toilet din ajikin kyauren d'akin.


"Bayan yan mintina yarima yafito d'aure da towel ak'ugunsa  ga wani a wuyansa dan goge jiki ,kawai ya aza k'afarsa akan ruwan yaud'on da yasmeen ta xuwa...


Ai wani suuuuuuuuuuuuuuuuuuuuu!!!yayi suka jikake timmmmmmm!k'uru,rummmmm!yarima kansa yabugi gaban gado,wata yar k'arar wahala yasaki  had'e da kallon gaban toilet din yaga me ya takane?


"" zaro ido yyi gani yaud'one,atake yagone yasmeen ce tayi hakan.,,,


Yah salam kawai yace had'e da cewa anya yarinyar nan ba kasheni zata yiba..ganin ko ta shi yakasa dan jikinsa yabugu....k'arar bude k'ofar ce yasha yajuyo yasmeen yagani,tana k'yalkyala dariyar mugunta har wushiryarta ta fito ,shagala yyi da kallonta,ji yyi tace oh su yarima amfad'i to ina k'asaitar taka?hmm wlh naso ace a gaban kuyangine da barori su ganka,aidanasani nayi maka video, tafad'a had'e yimasa gwalo..


Yiyayi kamar zai tashi ai da sauri ta arce,dariya yyi dan tabasa dariya dan yalura akwaita tsoro da Jan fad'a.


Afili yace lallai yarinyar nidakene gobe .


Da k'yar yatashi yashirya yawuce masjid bedawoba sai bayan isha,I .


Part din ammi yawuce kodan yaga yasmeen amma bbu alamarta dg bisani sukayi sallama ya wuce  part dinsa yaje ya kwanta dan akwai inda yake son xuwa gobe kuma yaje yagaido mahaifiyar yasmeen.


Yasmeen kuwa dayake tasan batada gsky ana yin magrib ta sallami kuayanginta ta gark'e part dinta,tayi kwanciyarta,tana tunanin yadda zasu kwashe gobe da yarima.,,,,


Washe gari...


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(Palace of excitation and pleasant writers)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Wannan page din nakune mmn fareesa fans club  Kuyi yadda kukeso dashi ina mugun yinku😇😇.


🅿41&42


Washe gari da wuri yasmeen ta shirya ,bayan sun gaisa da ammi ta wuce skul.

       Yarima kuwa har part din ta yaje kuyanginta sukace bata nan tana skul kwafa yyi had'e da tafiyarsa dan yagaido ammi.

"da misalin karfe 12:yarima yakira sarkin gd suka samesa a office shida driver ," nan suka nufi anguwarsu yasmeen.

"Suna cikin  tafiya wayar yarima tayi k'ara ,har yaki d'agawa can kuma yad'aga dan bakuwar number ce,bayan yyi sallama ,me kiran yace  ya'llabai pls Kuyi binkice akan alh jamilu bushasha wlh yanxun ina xaune yaransa suka wuce da mota harda yara 2da gudu.

Ahankali yarima yace ok zanbincika yanxun inada wani uxuri ....be rufe bakiba ta glass yahango wata mota ta wuce atsiyace da sauri yacewa driver yabi motar."

Aiko nan suka cigaba da bin motar sukaga tabi wani hanya dabbu mutane sosai da ga nesa yarima sukayi parking.

Kawai yaga alh jamilu yafito dg cikin ciyawu ,yakarbi yara 2 sai kuka da ihu suke kawai yaga haske ya wulla yana d'agowa sukayi 4eyes da yarima.

       Cikin rashin gsky had'e da fad'uwar gaba yafara inda inda da cewa wai su mayarda yaran tunda ba'an iyayansuba.

Yarima kuwa kaf yana ganinsu kuma yyi musu pics kala kala da camerarsa.

Alh jamilu yasaki yaran hankali tashe yashige motarsa dan Neman mafita tunda yarima yaganshi.

"Yaran su yarima suka dauka had'e da tambauarsu anguwarsu suka fad'a harcan yarima yakaisu yakarbi number ta iyayansu akan xainemesu suyi mgn yanxun yana saurine.

Acikin motar yakira mutumin d'azun yace yace aiyaga yaran yamaidasu gun iyayensu."

      Nan yarima yace yazo gobe anason zaiyi mgn da shi a office insa.

"Nan suka d'auki hanyar gidnsu yasmeen, tun a hanya yarima keyin mamakin ganin anguwa r dan shi azatonsa yasmeen sai a quarters ba irin wannan anguwarba dan yadda yaga tahade da yawa."

bayan sunyi parking, sarkin gd yanuna masa gidan ,yayinda shida driver suka tsaya waje,nan yarima yatura wani yaro yace ga ASHMAN nan mijin yasmeen zaishigo.

"nan yaron yadawo yace yashiga", tun asoro yarima yafara tausayin su axuciyarsa yace oh ashedai talakawa ne amma kuma yasmeen batada son abin duniya.

Nikuwa nace hmm da sadda ba'a gyara gidan bane kaganshifa.

Sallama yyi bbu kowa atsakar gidan, fes tayisd'in wanke kal,axuciyarsa yace aidama yasmeen nada tsabbata Ashe agun ummanta tagado...jin muryar umma yyi tana amsawa had'e da cewa yashigo...

Cikin mamaki yashiga axuciyarsa yanacewa kaddai ace wannan ce mahaifiyar yasmeen kuma yasmeen ce yakare a kotu....benuna mamakinba afuska,cikin fara'a yashiga had'e da duk'awa jar k'asa yagaishe da Umma .

Ta amsa cikin kula da k'arayi masa godiya,nan yace ammi da yasmeen nagaida ita  tace tana amsawa ai jiya yasmeen dintaxo.

" yace eh Aida tare zasuxo wani aiki yarukesa yafad'a yyinda yake kallon pic d'in yah Omar dake makale da bango,ahankali yace umma wanene wannan?

Murmushi tayi tace Omar ne yayan yasmeen bayanan yana karatu.

Yace masha ALLAH fan yatuna inyasmeen na masa raki shitake kira.

Bayan shiru ya ratsa nan yarima yace umma inason sanin labarin mutuwar baba tundg ana gobe zai rasu xuwa yanxun??"

Umma tace to,yace bayan shariar bala yaxo ?nan ta sanar dashi yadda sukayi da ihun da inna atika tayi masa.

Yarima yace good gara da yaxo sunanan hakanma yazama shaida,amma inason ganin photon baba,to umma tace tashige k'urya bbu jimawa ta fito da photon taba yarima.kure pic din yyi da ido dan tabbas yasan abbansu yasmeen saidai yamanta inda yasanshi kuma yasansa da dadewa.

Nan umma tayi ajiyar zuciya tace ana gobe zai rasu,ina zaune ina tankad'e garin tuwo damarece yashigo  cikin wani yanayi kallo d',aya namasa yanagano yana cikin damuwa.

     daki na bisa ina tambayarsa meke faruwa ,yace bbu komai....kafin nayi mgn bala yashigo bbu sallama a fusace ,kamar zai tureni nayi saurin bashi hanya yana cewa ina amadun yake? nixaka gayawa mgn sbd nanemi taimakonka ka toxartani cikin mutane.

baba bece komai ba kansa duke,kwafa bala yyi had'e da cewa zakaga abinda zai biyo baya....yana fadin hakan yyi saurin fita dg gidan.

      ",umma tacigaba da cewa nan natambayesa meyahadasu dan shi mutum ne mai hakuri da juriya bala na kuntata masa amma sai yahkura.

Nan yacemun wai shanuna guda 2danike kiwu xanbashi guda yasiyar yyi aure Wanda koyyi auren yan kwanaki zai saki matar ,shine nanuna masa illar hkan,Aiko yyita masifa aini mijin tace ne shiyasa shanyayye kawai,saina rabu da shi nadawo gd shinefa yabiyoni.

Tace nikuma nace ALLAH yakyauta..

" acikin dare gurin karfe ukku da wani abu naji motsi da kara ,saina fito jin motsin dg d'akinsa sai na nufi can Dede k'ofar natsaya naji abban yasmeen nacewa dakai za'ahada baki amun haka kaci amanar zumunci.....dede iya nan naji ina shiga dakin Muka hade da wasuasa2 fuskarsu aboye subi gefena da gudu suka fits ,nayi saurin karasawa ciki ,kwance nasamesa jikin jini yanason gayamun kosu wanene amma rai nakokarin fita Kalmar shahada nayita maimaitamasa yana amsawa yafad'i rai yyi halinsa...umma tafad'a yyinda hawaye ke xuba a fuskarta dan jitayi mutuwa tadawo mata sabuwa.,,,,,


Yarima ma kuwa yatausayamusu daurewa kawai yyi amma har idanunsa sunyi ja..


Tsaye ya mik'e yana xarya a parlour n.


"" umma tace da safe nida umar mukasanar da makota ,wasu da yawa sunso ayi binkice amma sai bala yaxo yana wani hawaye wai mubari ga ALLAH tunda dai yariga da ya mutu shikenan.badan munsoba nida yarana mukabarwa ALLAH. ""


,,,,,,nan ta sanar da shi gadonsu daya kwace.,,


Ajiyar zuciya yarima yyi yace amma umma ke atunaninki na zuciyarki wakika zarga akan kisan Abba? dukda bakida tabbas amma kinsan xuciya da sak'e sak'e.


"Umma tace wlh bala nazarga."


Yarima yace good nima shina zarga sbd alamomi sun nuna hakan.


Yanxun in son xuwa gidan nala din yanxun akwai wasu tambayoyi da zanmasa Wanda tanan ma zamu kara kafa hujjoji masu k'arfi.


Umma tace to.


Nan takira inna atika tace aturomata Yahaya yanxun in yana gida.


Bayan sun gama wayar takalli yarima tace ga yaro dazai kaika  nan xuwa,yace to.


"nan yafito da wata na'ura kamar redio yamik'awa umma ta karba yace duk sadda Kawu bala yaxo gidan nan ki tabbatar kin fito da ita kinsaka a hijan sannan Kuyi mgn yafad'a had'e da nuna mata wani gefe yace nan zata latsa in sun gama ta sake latsawa.


Umma tace to had'e da godiya da saka ma yarima albarka..adedenan Yahaya yashigo.


" nan umma ta sanar dashi gidan Kawu bala zai kai yarima yace to had'e da kai gaosuwarsa gun yarima suka fita sai godiya da saka albarka umma keyi.


Sai bayan sun tafi umma ta lura da radar yan dubu guda2 da yarima ya aje girgiza kai tayi tace basu gajiya da hidima dg shi har iyayansa ,amma da nagani wlh bazan karbaba abun yyi yawa.


Ak'ofar gida kuwa ,yarima yasami sarkin gd da driver sunajiransa nan shida Yahaya suka shige ,Yahaya yadi anguwa r dazsu nufa han suka nufi can.


Sunayin parking agaban gdn Kawu bala ,yarima yace wa Yahaya yaje yyi masa sallama da Kawu bala..


Nan sarkin gd yafito da wata kujera yarima yazauna mutanan anguwar sai kallonsu ake adaidai nan Yahaya da Kawu bala suka fito dg gidan bala.....


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writers)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


story & written by mmn fareesa


🅿43&44


Wani mummunan fad'uwar gaba Kawu bala yaji sakamakon ganin yarima hakimce akan kujera agaban gdn sa."

      Tambayar kansa yake me yaronnann yazo nema agunsa? wata zuciyar tace kasan ko gaidakai yazoyi matsayinka na sirikinsa."

girgiza kansa yyi yace akwai wata a k'asa ,gun yarima ya isa bbu ko sallama kai tsaye yace yaro lfy me kazo nema aguna?"

Yarima yyi murmushnsa na k'asaita yace ,Niko nazo Neman babban abu kuma muhimmi agunka,ak'agare Kwu bala yace inajinka.

"Yarima yakafesa da ido yana nazartarsa dan haryagano wani abu atare dashi" ahankali yace shekara2 dasuka wuce k'aninka yarasu ko?

atake wata zufa ta yankowa Kawu bala yace eh mene natambaya Wanda yamutu ai yarigada yamutu.

Yarima yad'aga kafad'a yace aganinka kenan dan ni yanxun ma aguna mutuwar sabuwace!

Kawu bala yace to mekake nufine da hakan ai d'an uwanane nike da iko akan komai ,kuma tunda iyalinsa sunce sun bari ga ALLAH bashikenanba.

"Murmushi yarima yyi yace hakanma yyi amma amatsayinsa na d'an k'asa yanada hakkin daza ayi masa bincike agane sanadiyar mutuwarsa.

Afusace bala yace to ni me nawa aciki dazakazo har k'ofar gidana kana gayamun mgn oho kaida mariyar kuka had'a baki kuyimun sharri kuce Nina kasheshi ko me?shiru yarima yyi dan yagama fahimtar abinda yazo fahimta ,tashi yyi yace to tunda baza kabari  muyi mgn ba inkaje gaban hukuma kayi bayani.

" wani ihu Kawu bala yyi yace ohni nashi ga ukku dan anganni talaka za'amun sharri ,"ALLAH ya isa tsakanina da Mariya...adedenan bash yazo zai shiga gd yanata shan sigari ,kawai kunnuwansa da idanunsa suka ankarar dashi,gunsu yanufa dan yalura da yarima batare da guards dinsa yakeba.

"Cikin ixxa bash yaja babansa gefe hade da cewa wa Nene yasaka kuka haka ?gaban bainar jama 'a dan har mutane sun fara taruwa suna kallon su.

      Kawu bala yanuna yarima yace ga Wanda keshirin cimun mutunci da girmana da komai a...yarima yakatsesa da cewa  kayi sabo babba dakace wai da girmanka ,ina girman yake anan..afusace bash yawatsa yarima wani mugun kallo yace kai dakata ,nan a anguwarmu kazo ,kuma wadanda kadogara  dasu suke taremaka fad'a ai basu biyokaba kaga kamun ba daidaiba saina suburbudaka anan...sarkkin gd da driver ne suka katse bash da cewa kai wawa hattara kasan inda kake mgn yarima mai jiran gado yafi karfin hakan..azuciye yarima yadakatar dasu hade da matsawa gab da bash ,ya kallesa sama da k'asa yatsartar da yawu, yaro yarone,yaro besan wutaba saiyataka zannuna maka kalata,dan ko agaba kabada labarin hakan dukda ni yarima nafi karfin hada jiki da k'azami irinka amma zankoyamaka hankali tukum nasakaka amota  naje narufe narufe banxa...

aituni bash jikinsa yafara kirma dan yagane cewa yad'ebo ruwan dafa kansa...be auneba yaji yarima yasaka k'afarsa me takalmi sawu ciki ya tad'osa yafad'i k'asa warwas, yasaka kafarsa yatakasa iya k'arfinsa ,atake bash yasaki k'ara ...

Nanfa mutanan anguwa sukafara taruwa suna kallo sunajin dadi dan dama bash  ya ishesu da halin akuyancinsa ..shikuwa Kawu bala kamar yyi kuka dan bakin ciki dan har yafara jin dadi bash zai suburbudi yarima yakunyatasa ,saigashi Ashe rabon shi yariman ya kunyatasu.

Bbu bata lokaci yarima yacigaba da suburbudar bash duk yakumbura masa fuska dg bisani  yayima sargin gd nuni asaka bash a boot din mota,nan yazo yaci ka aikin yarima,Kawu bala kuwa kamar yafashe dan bakin ciki,nan yarima sukabar anguwa r afusace...


A police station suka wuce ,yarima yace su ladabtar masa da bash,sannan suka wuce gd...


     *********

Yasmeen kuwa duk atsorace take dan batasan wane hukunci yarima zai yanke mataba,koda tadawo dg skul part din ta ta nufa Saida akayi isha'i  takira ummanta,nan ta sanar da ita yarima yazo kuma  zai fara binkice akan mutuwar abbansu harda kudin da ya ajemata duk tafadawa yasmeen. "wani irin yanayi ta tsintsi kanta duk saitaji dama batayi masa wannan muguntarba. Jiki a sanyaye sukayi sallama .sannan taje part din ammi dan su gaisa ,shima atsaitsaeye suka gaisa ta fito tanata sauri dan kada su hade da yarima .....jitayi an rungumota tabaya, kobata dubaba tasan yarimane sbd k'amshin turaren sa dataji...


" ahankali tace pls yaya kayi hkuri nabari wlh bazan sakeba kajiiiii!"


Shima a hankali yace nibabu abinda zanmiki,muje d'akina kimun tausa,zanyi bacci badan tasoba tace to dan atunaninta wayo yyi mata..


Saketa yyi yace muje,binsa tayi suna tafiya,suna zuwa Dede k'ofar part dinsa ta zura aguje hade da cewa ALLAH yaya mugunta zakamun bazanxoba.


Lumshe ido yyi jiki ba kwari yanufi ciki dan duk wata iron sha'wartace ta motsa masa amma bayason takurata har taruk'a masa kuka,dakyar yasamu yyi bacci.


da misalin karfe 9:30pm Kawu bala ne da alh jamilu ,zaune suna mgn a get House dinsa,bala yace to kaji irin cin mutuncin dayayima na acikin bainar jama'a..


Alh jamilu yyi ajiyar zuciya hade da labartawa Kawu bala ganinsa da yarima yyi d'azun da rana,dg karshe yace meye shawara?


Kawu bala yace duk'o kaji,wata mgn yarad'a masa a kunne wadda nima banjiba...


"" wata dariya suka kece da ita,alh jamilu yace kai gsky ka kawo shawara ,brain dinka naja mutumina,dahar nayi shirin guduwa dg garinnan wlh yau da dare..."


,,,Kawu bala yace ah ah aibbu batun Barin gari muna nan daram,hahahahaha ,sai dariyar bosawa suke..,,,


Washe gari byn yarima yashirya yyi break yakira umma yasanar da ita yadda sukayi da bala ,hade da cewa yanxun xaije yamik'a case d'in kotu,cikin jin dadi umma tace to sukayi sallama.


Part din ammi yaje yagaishe da ita,yafito da kamar yaje gun yasmeen sai yafasa yaje parking space zai dauki mota nan guards dinsa da driver suka nufosa yyi musu alamar ah ah shi d'aya zai fita..


"Motar yashege yaja hade da barin gidan".


Tafiya yakeyi har ya wuce garden din da nanne farkon had'uwarsu da yasmeen ,aisaiyadawo yyi parking yashiga, gun wasu kujeru yazauna yana hangen gun da yahango yasmeen zaune farkon had'uwarsu,lumshe idanuwansa yyi yayi shiru,yafi 30 minit can kuma yatashi yafita...


Dede gun da yayi parking yanufa yana bude murfin k'ofar dg bayansa yayi ance y'allab'ai.. Yana juyowa mutane biyu yagani kafin yyi magana sun maza sun goga masa wani k'yalle bak'i,atake cikin yan d'ak'iku yafita hayyacinsa besan inda kansa yake ba yafad'i,suka jasa suka sakashi moto sukabar gun kasancewar duk gun motocine bbu Wanda  yagansu....


Share pl


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story&written by mmn fareesa


🅿45&46


Wani gidane can karshen gari suka kaisa ,acikin wani d'aki akayasar dashi aka rufe k'ofar dan dama gidan na yan kiddinapping ne duk masu tsaron  gidan fuskarsu arufe take ,idanunsu kawai kake gani....

        "Acikin gidan Sarki kuwa ", yasmeen ce zaune a waiting parlour na part dinsu,itada Maryam da salim suna fira bbu skul kasan cewar week end ne."

fira suke jefi jefi yasmeen nakallon agogo dan tasan 2:30 pm yarima kedawowa amma har 3:00shiru,koda dg ankira la'asar saita wuce ciki dan yin salla ,shima salim da Maryam suka mik'e hade da cewa yasmeen sun had'e a part din ammi."

    Bayan ta idar da sallar ,direct part din ammi ta nufa ,bayan sun gaisa ammi tace oh lfy yasmeen har 4 tagota amma mijinki baidawoba ?ko kinkirasa ne?"

   rasa mezatace tayi dan ita batada number yarima,amma saita dake tace eh takira amma bata shiga."

Ammi tace to bara nakirasa ALLAH yasa lfy dai,yasmeen tace ameen, dan itama saitaji wani iri dabaidawoba.

     Kiransa ammi tayi amma wayar akashe ,nan dai sukayi shiru dukda dai basu yarda lfy ba dan bai kaiwa har haka baidawo gidaba."

Koda ammi taga 6:00pm tayi ,ai asukwane ta nufi part din me martaba ta sanar da shi hankali tashe."

nan akakira guards dinsa ana tambayarsu ko sunsan gun dayaje yau ?"sukace ah ah ai gsky yace kada Wanda yabiyosa,Sarki yasaka akirasa amma duka layikan akashe,nanfa gaba d'aya gidan Sarki kowa hankalinsa tashe yake ,musammun ammi ,yasmeen kuwa kuka tasakawa ammi ita afitomata da mijinta.

"ita kanta ammin hawayen take dan duk a y'ayanta bbu Wanda yashiga ranta kamar yarima.

      " anagama isha'i Sarki yyi report a police station da kafofin sadarwa."

Aiko nan gaba d'aya anguwar Sarki da wasu anguwarni zuwa garin bauci aka dauka wai annemi ,barrister yarima Ashman  ba'agansa.

Umma natsakar gida taji aredio,hankali tashe takira yasmeen ,yasmeen na kuka tace eh umma ba'asan inda yakeba tun safe dayafita be dawoba,umma tace harfa waya munyi dashi da safe,anya ba makiyansa bne yasmeen? "

Tace k'ila umma ALLAH ne mafi sani,nan umma tace insha ALLAH ,ALLAH zai karesa kiyita addua da sallar dare kikai kukanki ga ubangiji,nima zantayi insha ALLAH ko wane hannu yake zaisami kariyar ubangiji..

Yasmeen tace to umma zanyi nagode sukayi sallama."


Babu bata lokaci duk wasu masallatai addua akema yarima dan kowa yasan shi mutumin kirkine mai son talakawa,addua kawai da saukar alkur ani ake masa ,wasu har kuka suke ,dan rasa irin yarima acikin wannan zamani hasarace babba ga al,umma,kowa yabansa yake yana addu ar ALLAH yatsaresa aduk inda yake..,,,


      *******

Yarima kuwa bai farkaba sai gab da magrib,kafin ya bude idonsa yaji mgn hade da dariya,atake komai yadawo masa ,salati yaketa maimaitawa ,yaki bude idonsa."


,,,muryar Kawu bala da alhj jamilu yaji suna cewa,amma ai antabbatar mana cewa bazaikai mgrib ba zai farka.,,,


Alh jamilu yace eh hakane, inma yamutu me ruwanmu,kawai inyafarko ,mukarbi number Sarki aturamasa text cewa yana gun gummu,sai ankawo milion150. Tukum mubadasa..


Kaga in sun bamu saimu kashesa mugudu......dariya suka sheke da ita..


Yarima kuwa shiru yyi,duk yanajinsu,kaf Saida yagama jin tukum yafara motsa kafarsa dake d'aure da iggiyoyi.


da sauri su Kawu bala da alh jamilu suka saka safar fuska,suna kallonsa.


"Bude idonsa yyi ,kallo d'aya yyi musu yaganesu,amma dayake yafisu brain aisaiyyi pretending da cewa ,subahannallahi ,Ku suwanene Ku?mekukeso aguna ,cikin wata murya alhj jamilu yamik'a masa waya yace kasakamana number mahaifinka.


Yace Kuyi me da ita?


Yace kasaka mana ,ko in yankemaka harshe, nan yakarba yasaka,bala yakallesa da jajayen idanunsa yace bamuson komai dg gareka,kudine kawai za'a bayar mu maidaka gd ,yana fadin hakan suka fita shida alhj jmilu...


Yarima innalillahi wa inna ilaihir raju un kawai yake maimaitawa,dan yasan indai suka kashesa to kwanansa ne yakare kuma bazaiji haushiba sbd adalilin gaskiyarsace hakan tafaru,inkuma yanada rabon shan ruwa ko ta halin k'ak'a saiyafita,kuma yana fita acigaba da case din dan indai akan gsky ne to yanxunma yafara yin gsky a aikin sa...


"" suna fita, alh jamilu yarubuta taxt kamar haka."


       Yarima!

Yana gunmu,saikunbada naira million 150 tukum mu badasa

Zamu kiraku anjima inkukayi yunk'urin saka  yan sanda zamu kasheshi, kuma zamu fad'i gun da zaku aje kudin.......


Yana gamawa yatura, suka kece da dariya...


Maimartaba da familyn sa harda yasmeen ,duka a fada anata jajanta lamarin gakuma can jami an tsaro suna nasu aikin,kawai taxt yashigo wayar Sarki,da sauri maga takarda yaxube hade da cewa ALLAH shitaimakeka mai martaba sarkin talakawa adali ga sako,inkayi umarni ,aikatawa ne nawa akaranta?


"Sarki yad'aga kai alamar eh".


Maga takarda yyima waya kuri,kowa yamaida attention dinsa agunsa dan jin me xaice....?


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


🅿47&48


Ahankali maga takarda yyimusu bayanin komai da aka rubuta..

"salati kawai kowa keyi hade da tsantsar tausayin yarima".

Sarki kuwa yau bbu batun sarauta tashi yyi yana inna lillahi wa inna ilaihir raju un kawai yake maimaitawa yana zagaye fada."

Yasmeen kuwa kuka ta fashe dashi dan sai yanxun tagane cewa tabbas tashak'u da yarima gashi ayini guda dabata ganshiga ko abinci takasaci ,hawaye kawai take amma azuciyarta tana wani zargi.

       Ammice itama tana hawaye takama yasmeen tana rarrashinta suka nufi part din ta sbd xata dawo suyi mgn itada Sarki."

Sageer kuwa k'uri yyi wa yasmeen da ido yana kallonta harsuka fice,wani irin tausayinta yaji,dan ganin dayayi musu itada yarima azatonsa suna matuk'ar son junansu.

"nan kowa ya watse dan xuwa yin nafilfili da addu a akan ALLAH yatsare yarima", Sarki kawai da mama aka bari wato hjy rahama dan itakeda girki."

     Ammi kuwa rarrashin yasmeen taitayi da ban baki had'e da lallabata taci wani abu dan ammi na lura da ita tun break bata sake cin komaiba ,kasancewar sai 4take lunch kuma a time d'in aka fara jajan yarima."

Yasmeen kuwa catayi bazataciba,ita ba abincine gabantaba,tayidai shiru",jiki a sanyaye ammi a batta a part din ta nufi na Sarki dan suyi mgn.

"tana zuwa tasami Sarki zai tada sallah,nan tace abban yarima yanxun meye mafita?"

       Sarki yace insha ALLAH zai fito lfy,inaji ajikina duk inda Ashman yake to tadalilin gskiyarsace hakan yafaru,kuma koya fito zai cigaba da tsaya akanta.

Kije kigayawa ubangiji ,dan duk masallatai ance anata masa addua da saukar alk'ur ani nima yau bazanyi bacciba insha ALLAH zankai kukana gun ubangiji.

       "nakira number dasuka turo text message da ita amma akashe,muna nan munata jira ko million 200sukace sai abasu dan ceton ransa...

Ajiyar zuciya ammi tayi ,jiki asan yaye tace to bara natafi, ALLAH yasa kada su cutar mana dashi.

Sarki yace ameen tafita yakabbara sallarsa.";;;;;


"" tana zuwa tasami yasmeen kan prayer mat tana sallah ,ga alk'ur'ani gefenta da casbi.,,,


Wani irin tausayinta had'e da k'aunarta taji,azuciyar ta tace lallai yarima yadace da mace ta gari,yah ALLAH katsaresa aduk inda yake.lallai koda yarima yamutu bazata bari yasmeen tasubuce musuba dole ta auri wani dg cikin y'ayan gidan,wata zuciyar tace bazaima mutuba sai yaga y'ayansa hardama jikoki,da Wannan tunanin ammi ta wuce toilet tayi arwallah taxo ta tada sallarta.,,,


Haka kuwa ammi da yasmeen suka kwana kai kukansu gun ubangiji,Saida sukayi sallar asuba tukum bacci barawo yyi gaba dasu....


     ************

6angaren yarima kuwa ,har akayi isha 'I yana a d'aure ,sai gurin 8:30pm akazo kamasa wani galbaranren abinci da pure water 2 ,ko kallon abincin beyiba ya juya Kai had'e da cewa kukwanceni nayi sallah..

     Wanda yakawo abincin bece komai ba yafita Jim kad'an yadawo da shida wasu katti6 suka kwance yarima had'e da nuna masa toilet din dake cikin d'akin nan yashiga yakama ruwa had'e da alwarla yazo yakalli Gabas yafara rama sallolin dke kansa har xuwa isha'i.

Yyi nafilfili da shafa'i da wutiri sannan yyi adduar samun kubuta dg hannun wad'annan azzaliman..

sannan yatashi,kuma duk kattin nan suna kallon sa ,cikin wata murya sukace ga abinci yaci,ruwa 1kad'ai yafasa yasha shima sbd k'ishirwa amma badan yanasoba,ya ce bazaici abincinba,kamasa sukayi suka d'add'aresa kamar d'azun."

suna fita yyi shiru yana tuna tashin hankalin da family nsa zasu shiga insuka sami lbrin halin dayake ciki,yasandai ammi zatashiga damuwa sosai kuma yasan xata masa adduar dama danginsa baki 'd'aya."

        Tunawa yyi da yasmeen ,afili yace koyazataji intasami labari?,koxata damune?wata zuciyar tace bazata damuba sbd ta tsaneka.... Lumshe ido yyi yacigaba da hailala da tahamidi..


,,,washe gari tun da safe sukazo kamar jiya suka kwancesa yyi sallah suka sake dauresa dan yak'icin abin Karin kumallon dasuka kawo masa...,,,


Agidan Sarki kuwa sai gurin 9:00am su ammi da yasmeen suka nufi fada,idanun yasmeen duk sun kumbura sbd kuka da rashin bacci..


"Suna shiga suka sami Anty lubna yayar yarima,da hanan sai sameera sunxo sai kuka suke Sarki na kwantar musu da hankali akan za a maidosa."


Wayar Sarki tayi k'ara ,maga takarda yaduba da sauri yace ALLAH yabaka yawan rai number da aka turo sako ve,da hanxari Sarki yakarbe wayar had'e da d'agawa..


"" alhj jamilu dke zaune gaban yarima shida Kawu bala cikin canxa murya yace kunshirya zaku bayar da abinda Muka buk'ata?"


"da sauri Sarki yace eh."


Yayinda kowa yyi tsit a fada anajin maganar alh jamilu kasancewar Sarki a hands free akasaka wayar.


Alhj jamilu yacigaba da cewa inkuka wuce yau Baku kawoba xamu kasheshi ,da sauri Sarki yace ah ah dan ALLAH kada Ku cutar mana dashi ko yanxun kukeso zamu kawo kuma bazamu saka police ba a case d'in...


"" wata dariya alh jamilu yakece da ita azuciyarsa yace hmm yau nike mgn da Sarki haka bbu ladabi da fadane danasha bulalai.


Wayar yakarawa yarima akunne Wanda yyimusu k'uri da ido yana sauraronsu,amsa yyi yace da sauri yace abbana!


Sarki yace ashimanuna,dan duk sadda Sarki yaso nishad'i da hakan yake kiransa,yace basuyimaka komaiba ko? Yace ah ah Abba ina amminah?


da sauri ammi ta matso ta karb'i wayar had'e da d'agowa tana kallon yasmeen dke hawaye,cikin tausayinsa tana hawaye tace my son gani kaji kana ran ammin ka da sauran yan uwanka baki daya insha ALLAH zakafito lfy ,hawaye yarima yaji na tausayin amminsa ,da wasu banxaye suka d'aga mata hankali hartake xubbada hawayenta,lallai wlh duk sadda yafito su bala da alhj jamilu kashinsu yabushe...


"Ahankali yace amm I ina yasmeen?


Kallon yasmeen dke kuka ammi tayi tace gatanan bataci batasha sai kuka kwana tayi tanamaka addua batayi bacciba wlh da sauri yace ammi bata wayar......


" alhj jamilu dake saurarensu yyi saurin kwace wayar yakashe."yana dariyar mugunta,yarima jiyayi da ace ba ad'aure yakeba da saiyawa alhj jamilu shak'ar da yakasheshi har lahira kuma yakashe banxa...


Ammi da wayar ke hannunta ,d'it taji alamar ankashe wayar...


Kuka yasmeen tasaki maicin rai ...afusace Anty lubna tace dallah malama yimana shiru da wannan kukan munafurcin naki na kar.... Kallon da ammi tayi mata yasakata yin shiru dan dama ammi tagama gane lubna batason yasmeen amma ta yi alk'awarin hankali ya kwanta xata take mata birki..


Sarki kuwa tsawa yyiwa lubna yanacewa da fadanki xataji ko kuwa  da rad'ad'in batan mijinta ,ki kiyayeni wlh zan sabamiki..


,,,dukawa tayi tace ALLAH yahuci zuciyar ka,sarkin kirari yace tuba take ALLAH yabaka yawon rai ,nan Sarki yace kowa yatafi yasallamesa,illah sageer.


Bayan duk an watse Sarki yakalli sageer yace kuje kaida security a bank kucuro kudin Ku kawomun nasaka akai musu k'ila da yardar ALLAH su badasa.


Cikin girmamawa sageer yace to ,hade mik'e wa yatafi dan bin umarnin Sarki...


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Wannan shafin nakine my sweet sister hauwa'u Usman lado (Jidda) kiyi yadda kkso dashi ngd da k'okarinki  akan wannan novel ina mugun jidake irin totally din nan.😍😍


🅿49&50


babu bata lokaci sageer befi 40minit ba da fita ,yadawo shida security da kudin ,nan Sarki yasaka waziri da driver sukai kudin inda sukace a aje musu.

     "haka kuwa akayi suka kai,amma basuga yarimaba ,suka tafi .

Suna tafiya Kawu bala da alh jamilu dke labe suka fito had'e da d'aukar kud'in."

Basu tsaya ko inaba sai get house din alhj jamilu.

"cikin jin dadi had'e da murna alhj jamilu yace abinda za'ayi shine mu aje kudin nan sai angama komai saimu kasafa abunmu!

bala yace eh hakane amma nidai abani ko dubu Dari 5nayi hidima ,alhj jamilu yace to had'e da xuge jakar yabashi.

dariya suka shek'e da ita."

Bala yace da naso mukashesa ,amma ga shawara,musaka ayimasa allurar dazai manta komai yakoma yaro sai abinda aka koya masa inaga inmukayi hkan baza'a zargemuba.

Alh jamilu yace eh gsky ne ,amma kacika macuci ,bala yyi dariya yace muncika macutadai.

Nan Alh jamilu yace kaga bayan yafito sai kaje kasaka adole yasaki yasmeen ka auramun ita tunda shine gatanta kuma mungama dashi,nikuwa nace lamanta da akwai ubangiji."

bala yace eh ai wlh sai Mariya tagane shayi ruwane aguna zata sani ,amma mubari xuwa jibi zankawo doctor yyi masa allurar sannan saimu kaisa gun da za'a zo adaukesa.

        "dariyarsu suoa cigaba da yi abinsu"


***** **** *****

Acikin gidan Sarki kuwa tun sadda akakai kudin suke sauraren xuwan yarima amma shiru.

        Duk sun damu har Sarki yakasa hakura yakira number su amma akashe ,nan Sarki yace bakomai  ubangiji yana tare da su ,sucigaba da addu a.

"Haka kuwa akayi suka cigaba da yi masa addu'oi."

Amma shiru ba labari har akayi kwana2 dakai kudin hakan Yakama kwanansa3 kenan .

Yasmeen gaba d'aya tayi baki tarame tayi zuru zuru aikinta ,sallah, Karatun kur'ani ,kuka,aikinta kenan ,akuma ranar kwana ukkun da safe ummanta tazo tayimusu jaje ta tafi gd.

duk Wanda ka kalla agidan Sarki to baya cikin kwanciyar hankali....


____________________

da misalin karfe 12:30 pm balane yakutsa kai gidansu yasmeen, bbu ko sallama,kamar yadda yasaba....


Mariya! Mariya!! Mariya!!!


"Yana kwalawa umma kira."


Umma dke kuryar daki ,tajisa Saida gabanta yafadi, hartafito ta tuna abinda yarima yace ,da sauri ta d'auko na urar takunna had'e da dasakawa a hijab dinta ta fito tsakar gd...


"" sama da k'asa bala yakalleta yace to munafuka ,ke har kin isa kija dani ,wai har kituromun wannan yaron kega mai suriki ko?"


Hmmmmm hahahahaha to yanxun yana ina ?


Aibari kiji ni bala nafi karfin ajadani wlh dan duk Wanda yaja dani ,hmmm saidai wani bashiba.


"Kinturamun surikinki ,wato kuna zargina ko?"


To kidaina zargi ma bbu tantama Nina kashe k'anina amadu nakashe  banxa, kiyi abinda kka gadama dan Wanda kike tak'ama dashi ma ,yanxun haka ba'an inda yakeba,bbu Wanda zakigaya mawa ya yadda cewa Nina kasheshi...


"" cikin kuka umma tace ALLAH ya isa tsakanunmu da kai kafitarmu dg gida kona taramaka jama'a .""


Murmushi yyi yace yanxun kuwa dama burina, na amaye abinda ke cikina,amma kisani bawai natafi kenanba ah ah zandawo ,yana fadin hakan fuuuuuiuuuu yafita dg gidan....


"Ajiyar zuciya umma ta yi ,afili tace Alhmdllh madallah ai inkasan wata bakasan wataba,amma anya ba akwai saka hannunsaba akan batan yarima....


Bala nafita yakira alhj jamilu yace yazo yasamesa agd suje sutaho da doctor yyi wa yarima allurar,yace to ..


Babu jimawa alhj jamilu yaje yadauki bala da mota sukaje suka dauki doctor, nan suka nufi karshen gari...


Bangaren yarima kuwa bawan ALLAH yyi duhu yarame acikin kwana ukkun nan,dan tunda yazo ruwa yake sha ..


Ayanxun haka zaune yake ,yana tunanin gd da yasmeen wacce ammi tace masa batacin abinci saikuka, kuma wai kwana tayi yimasa addua,azuciyar sa yace wayyo bewar ALLAH nasan tausayina taji,ALLAH Sarki indai nakubuta bazan sake batamata raiba,yafad'a had'e da lumshe ido, dan bbu wani karfi atare dashi sbd yunwa da galabaita,karar bude k'ofa yaji ,juyowa yyi yaga me kamasa abincine,atake ALLAH yasa wata dubara ta fad'o masa..


Kallonsa yyi yawani rufe ido yace kwanceni nashi ga bayi gudawa nake,har xai juya kuma sai yadawo. Yaduk'a ya kwancesa .


" yarima na d'agowa yyi saurin kaimasa wani wawan punch a wuya atake yasulale k'asa sumamme."


Cikin hanxari yacire kayansa ,yacire na mutumin yasaka harda safar fuskar da rufaffun takalmi,sannan yadauresa yafito dg dakin ..


Yana fitowa  yahango kattin nan majiya karfi sunkai su 20suna xagaye da gidan ,nan yanufi get,wani yace yah babah sai ina ?


Cikin adduar samun nassara da yarima keyi azuciyarsa yacanxa murya had'e da cewa eh mutumin  waya zanyi bbu net work aciki ,ko ina zansamu ,katon yace inkafita kamik'e kadan ,wato hanyar dazata sadaka da cikin gari ,anan zaka sami net work nima scan nake samu ...


To yarima yace ,had'e da bude get yafito,adedenan kuma alhj jamilu ya yi horn dan sushiga yanxun a yiwa yarima allurar.


Alhj jamilu yakalli yarima dake shirin wucesu  yace kai babah ina zuwa yanxun ,bacin kasan damun yiwa yaronnan allura Ku xaku kaisa gun da za'a daukesa?gashi kafito da safar fuska bacin kana waje bacikin gidaba....


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿51&52


"" cikin dakiya yarim a yace eh zancire yanxun waya zanyi Ku shiga yana ciki."

       batare da sundamuba ,sbd burinsu su aiwatar ta bak'in nufinsu suka cinna hancin motar cikin get din . parking sukayi suka fito suka nufi cikin d'akin da yarima  yake...

       "Yarima kuwa yana ganin sunshi ge get ,yyi saurin cire safar fuskarsa ,hanya dazata sadasa da cikin gari yabi da wani irin gudu da baisan ya iyasaba."

ko waiwaye bayayi can yafito bakin titi ,cikin sa'a yaga ke  x press yatsayardashi ,da mutumin bazai tsayaba ,amma yana ganin kamar yarima ne."

tsaya yyi yace ko yarima ne da ake nema ?ko amsa baibasaba yahau had'e da cewa kakure gudunshi  pls." nan kuwa suka tafi da gudu amma yarima jiyake kamar baya gudun".

Alh jamilu da Kawu bala kuwa suna shiga suka tararda babah kwance asume ga kayan yarima gefe dayacire..

Hmmmm kada kuso Kuga yadda bala da alh jamilu suka firgita had'e da rudewa ,Aida gudu suka fito suna tambayar kattin ina yarima yace zashi dazai fita?"

Sukace bbu Wanda yafita sai babah,atsawace alhj jamilu yace to aishine yyi basaja ,sokwaye dku bakusan aikinkuba....

da sauri alhj jamilu yabude mota suka shiga shida bala yajata atsiyace ,bala kuwa kamar yyi xawo sbd tsorata da yyi ganin asirinsu nashirin tonuwa ,cikin tsoro yace amma alh indai yaron nan yakubuta to gsky mu gudu kawai.

"Alhj jamilu yayimasa wani mugun kallo yace  bazaima kubutaba ...

       6angaren su yarima kuwa sunyi nisa har sun kusa fita daji ,da sauri yar ima yajuyo Aiko yahango su Kawu bala amma suna nesa da su ,addua kawai yake dan yasha alwashin muddin yakubuta saiyaga k'arshensu ko yanxun abinda yake tsoro besan ko akwai makamiba ,ko bindiga ajikinsu shiyasa ,amma yanajin zai iya gwada k'wanji dasu.

         su bala kuwa dasuka fara hango yarima kan acaba,har sun fara murna nan alhj jamilu yace wa yaransu dke baya su miko masa bindiga....

saidai me?" Motar sukaji ta tsaya cak ta mutu"

wata ashar bala yasaki da sauri suka fito had'e da tsaya bakin titi.

       Shikuwa alhj jamilu gani yake anya ba k'ar yarsu ta kareba."

wani me mota zai wuce suka tsaidasa yana tsayawa ,suka nuna masa bindiga yafito dg motar suka shiga da gudu suka bar gun ..

Su yarima kuwa gudu kawai suke har suka shigo cikin gari ,yarima yajuya baya yaga bbu alamarsu bala ,hamdala yyi ha ubangijinsa dan yasan ba wayonsa ko dubararsa ne suka kubutardashi ba."da hannu yyima dan acab'an nuni da sunufi police station dan yasan yanxun tunda basu ganshiba gida zasuje su gudu..

    nan dan acab'an yyi parking agaban police station, yarima yasauka had'e da yimasa godiya."

Mutane naganinsa akayimasa caaaaaaaa ko saurarensu beyiba yanufi gun d p o yasanar dashi yanxun atura get house din alhj jamilu akamosu ..

DPO yace me yayi?

Cikin tsawa yace katura naceeeeeeee!melaifine inhar kabari akaje yagudu wlh kaji narantse kaida dpo har abadaaaaaa!

Zare ido dpo yyi ya fita asukwane ,cikin minti 3yatura police mota2sukamo alhj jamilu bushasha...


"Yarima kuwa wayar wani dan sanda yakarba ,yasaka number Sarki ,yakira ,tana shiga aka d'aga."


Yarima yace Abba nah nine ganinan police station ta karshen gari azo ad'aukeni,cikin matukar farin ciki Sarki yace gamu nan..


Yana kashewa yatashi bbu batin gyara kintsi yanu part din ammi ya sanar da su,wayyo farinciki ammi har sujjada tayi,yasmeen kuwa harda kukan murna tayi ,bakinta yak'i rufuwa.nan aka dunga sanarda dangi nakusada na nesa...


,,,nan Sarki yyi mota2shida guards dinsa suka nufi police station.,,


Su Kawu bala kuwa koda sukaga basuga su yarimaba nan sukasan tasu takare insukabari aka kamasu..


Get house din alhj jamilu sukaje asukwane suka d'auko ganonin kudin da Sarki yabada akawo duk abinda alhj jamilu ke buk'ata suka dauka ,suka fito parking space dan shiga mota,saidai me?police ne sunfi ak'irga sun zagaye gidan had'e da yimusu attack da bindiga.,,,


Sbd tsabar firgita Kawu bala fitsari yasaki a wando.


Alhjamilu kuwa tsinewa bala yahauyi wai shine yabada shawar ayi hakan...


"" nan aka d'auramusu ankwa had'e da iza k'eyarsu zuwa police station. ""


       *******

Sarki kuwa ko parking ba agamaba yafito ,yarima da ke tsaye da gudu yaxo ya rungume mahaifinsa,jama'a sai kallon su ake ana tausayinsu.nanfa yan jarida sukayi musu caaaaaaaaa ko kallon su basuyiba suka shige mota  ,sai gida...


Tun a compound din gidan yarima yake ganin jama'a suna masa murna da jaje,har yashigo babban parlourn gidan,nan yaga duka familynsu da yan'uwa da abokan arzik'i...


Suna ganinsa ,ammi da hjy rahama ,suka rungumesa suna kukan farinciki,nanfa yan uwa duk suka taso suka rungumesa ana murna.


"gaba d'aya hankalin yarima baya gunsu ,dubawa kawai yake yaga ina zaiga yasmeen dinsa."


Cikin sa'a yahangota tsaye kanta aduke ,kallonta yyitayi kawai saitad'ago ,caraf idanunsu suka sark'e  da juna.


Cikin wani yanayi yarima yabud'e hannuwansa alamar yasmeen ta taxo garesa ,bbu musu da gudu tazo ta fad'a jikinsa,had'e da sakin kuka...


Hannuwansa yasa yagaye bayanta,murya k'asa k'asa yace yasmeeeeeeeeeee!


Jitayi sunan har cikin brain dinta dan yaune ranar da taji yarima yakira sunanta.


Lumshe idanunta ta yi tace ,dan yauce ranar farko dasuka rungume juna da yarima...jitayi yace  pls kidaina kukan haka kinji ainadawo ko,yafad'a cikin rarrashi,Wanda duka mutanan dke parlour kallon su ,suke had'e da jin tausayinsu dakuma jin sha'awarsu...


Yasmeen nason raba jikinta da nasa amma yaki saketa ,sbd taga ga idon mutane...muryar Anty lubna yasmeen taji tana cewa ,to chiweengum saiki sakesa yahuta ko kinwani bi kin ....tsawarda ammice tayi mata yasata yin tsit.


"Ammi ta kalli yarima tace my son kuje ciki ,kalallabata kuci abinci,kaji dan tunda abun yafaru Bataci abinci."


Sake yasmeen yyi Yakama ,hannunta,suka fara tafiya,Anty lubna da wata budurwa dke kusada ita suka bankawa yasmeen harara,kauda kanta yasmeen tayi,tana mamakin metayimusu suka tsaneta haka..


Hannunta da yarima yamurza yasakata dawowa haiyacinta.


"Ahankali yace zanyi wanka !


Kanta sunkuye tace to dan tatuna da ruwan yaud'on data zuba masa..


""" part dinsa yanufa da ita ,ahankali ta janye hannunta dg nasa tanufi toilet dan hada masa ruwan wanka"

Shikuma gun sif din kayansa yanufa ,yabude k'uri yyi yana kallon kayan duk ancanzasu da yadda suke ada ga wadanda yabari da datti a wanke kuma agoge koba a fad'a masaba yasan aikin yasmeen ne"wad'anda zai saka yafito ya aje kan bed ,cire kayansa yyi ya d'aura towel .d'akin yakalla yaganshi kal ko ina alamar kullum sai yasmeen ta gyarashi,afilili yace bewar ALLAH,ALLAH yyimiki albarka,adaidainan ta fito,batare data kallesaba tace kaje kayi wankan"ahanka li yamatso had'e da rungumeta tabaya yace um um saidai muje kitayani,cikin wani yanayi da kasala tace  nidai ah ah  kunya nikeyi,ta fada had'e da matsawa dg jikin sa,tana mamakin wai yau yarima ne yake sake mata fuska haka..


Murmushi yyi yace to naji innafito kezaki shirani,bejira amsarta ba yashige bayin..


Kayan dke kan bed tagani jitayi batason yasakasu ,wasu kananun kaya ,tafito masa ,jeans dark blue da yellow din shart,tafeshesu da turare ta fito..


Sarkin gida tasaka yyiwa wanzami mgn inyarima yaci abinci yazo yyi masa gyaran fuska,dan taga k'asumba tacika masa fuska..


"Awaiting parlour tazauna jiran yarima."


Yarima kuwa yana fitowa yaga bbu yasmeen ,girgiza kansa yyi yamatsa gabn dressing mirror yashafe jikinsa da mayukansa had'e da body sprays.


gun bed yaduba ,kawai yaga yasmeen ta canxa masa kayan dazai saka , tsintar kansa yyi dajin dad'in hakan hade da bin umarninta yasaka kayan .wato yasmeen d'insa naji dashi sosai fitowa yyi yasameta azaune kaf'eta yyi sexy eyes dinsa yana ganin irin ramar datayi cikin 3days ...


"K'amshin turaren sa dataji yasakata kallon gefen ,Aiko sukayi ido4dashi da sauri ta sunkuyar da kanta ,matsowa yyi Yakama hannunta suka wuce gun dinning table,kujera yaja ya zauna had'e da kok'arin aza yasmeen akan cinyarsa...


"" amma sai ta kiya,fuska bbu walwala yace meye haka? dg dawowana xaki fara b'atan rai ,yanajin haka da sauri ta zauna kan cinyarsa, wani lumshe ido yyi jin mazaunanta akan cinyarsa.""


Bayan tayi serving dinsa a plate1 tajawo wani dan yiwa kanta,saitaji yarik'e mata hannu ya girgiza kai..


"Bbu musu ta bari,amakinta saitaga yana feeding dinta ta karba ,amma shi yak'i ci."


Hannunsa guda  ta rike tazaibata ,takarbe spoon din tabashi a baki..haka sukayi ta feeding juna saida sukaji bbu guri tukum  sukayi hamdala ga ubangiji...


Tsue yasaka yagoge mata baki Yakama hannunta...knocking sukaji yarima yaketa yaje yabude sarkin aski na gidan yagani ,bayan yakawo gaisuwa yace dama gimbiyace ta aika nazo nayimaka gyaran fuska...


Yarima Besan sadda yasaki  murmushi ba ,sbd wani farin ciki dayaji lallai yasmeen mace d'aya ce tamkar4kuma nagari,cikin mamaki sarkin aska ke kallon yarima don yasan baya dariya ko murmushi agaban barorin gidan ko wasu jama'a na waje.sannan yasan baya  son yyimasa gyaran fuska dan k'yamar wanxamai yake...muryar yarima yaji yace jeka ganinan.


To yace yafita.


Shikuwa gun yasmeen yanufa....


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


Mmn sultan inatayaki murnar kammala littafinki MUBEENA, hakik'a yafad'akantar hade da nishad'antarwa muna godiya munsaka👀munajiran new novel din.😇😇


🅿53&54


,,,,koda yaduba bata parlourn, bed room dinta yanufa kan bed yasameta kwance."

         Kallo d'aya tayi masa ta juya ,cikin shagwaba ta ce nidai kaje ayimaka gyaran fuskar!

Bece komai ba nufarta yyi kan bed din ,bata auneba taji yarima samanta, runtse idanunta ta yi da sauri had'e da d'an turesa."

Murmushi yyi ganin alamar kunyarshi takeji dakuma tsoran yyi wani abu da ita.

"fuskarsa da tata yahad'e yana goga karan hancinsa kan nata ", cikin sweet voice insa yace meye na wani runtse ido ki bude ki kalleni ko kuma mubata yanxun ."

       dan turo baki gaba tayi..jiyayyi kamar yacafke bakin amma lurada yadda take tsorace yahanasa.

"Ahankali tabude idon tace pls yaya d'agani muje ayimaka gyaran fuskar", ware ido yyi yace hmmm kidai jirani ,amma bazamujeba yakallemunke.

      d'an murmushi tayi,shikuwa kafeta yyi da sexy eyes dinsa yana kallon wushiryarta Wanda sai yanxun yafara lura da ita.

" dagata yyi had'e da mirginota samanshi yasaka hannuwansa yazagaye bayan ta ."

       Cikin kukan shagwaba had'e da bubbuga k'afafunta ajikinsa tace nikaje agyara maka fuska!

hancinta yaja yace oh baby!to sai kin kalleni tukum sannan inkuma ah ah afasa gyaran fuskar.

d'an murmushi tayi had'e da danjamasa saje, y'ar k'ara yyi akuma lokacin sukayi ido4dashi.

     Wani killer smile suka sakarma juna ga wata sha'awarta dke fusgarsa.

Murya k'asa k'asa yace bara natafi ayimun nadawo kibani labarin abinda aka yi dabana gd.

"Ahankali tace to had'e da barin jikinsa ,tashi yyi yasunbaceta agoshi yace baby nah sainadawo".

Lumshe ido tayi batace komaiba ba yafita,amma har cikin ranta taji dad'in yadda yake kiranta da baby dan yana tuna mata da yah Omar d'inta.

       Afili tace hmmm yarima kenan dukda munshirya yanxun amma tunda kanabin abinda nike so tanan zanta garaka,dariya abinta tayi,tafi minti 10anan sannan taje tayi sallar l'asar ta wuce part dinsa.

      Atsakiyar bed d'insa tayi zamanta tana wasanta da burgima kamar yarinya..,,,,,


Yarima kuwa yana fita gun sarkin aski yaje yagyaramasa fuska sannan yawuce masjid yyi sallah yanufo part din su..


"" jin motsinta a bed room dinsa yasakashi,nufar can koda yashiga tsayawa yyi yaimata k'uri da idon dan shi yanxun duk abinda yasmeen tayi birgesa takeyi,kallon bak'in gashi kanta yyi me zawo Wanda yabaje agadon bayanta ga jibgegen k'ugunta me tafiya da imaninsa."";;


"Jitayi kamar damutum"


da sauri ta juyo ,yarima tagani yyimata masifar kyau gashi anyi masa gyaran fuskar gwanin sha'awa saiyafito a yarimansa sak maiji dakai da k'asaita.


"Ahankali yace zo muje kirakani part din ammi nasan ba'a rasa yan zuwa jaje mu gaisa", mak'e kafad'a tayi tace um um um inajin kunya .bece komaiba yajuya dan saiyaji bbu dadi in yatafi batare da ita ba,itama tashi tayi had'e da yin rolling kanta ,cikin sand'a tabisa saida tahada da gudu tukum dan yyi nisa kuma ta lura kamar beji dadin binsa datakiyiba.

        " ahankali tayi hugging d'insa tabaya tana dariya,juyowa yyi da ita agabansa yana murmushi yace ainazata d gske bazaki rakoniba hannunsa ta rike daya tace hmmm ai gashi nabiyoka,hancinta yaja,ihu tasaka ita saita rama ,agefen hanyar suka tsaya yakafeta da idanunsa yace tazo ta rama ,sai mik'e kai take takasa sbd yafita tsawo,kodayaga takasa dariya yyi ta mata ,fadawa jikinsa tayi tana masa kukan shagwaba ...muryar wasu k'awayen ammi sukaji da sauri suka rusuna suka gaidasu,nan sukayimusu jaje ,hannunta yarima yaja suka shige parlourn ammi..,,


Mutum4 a parlourn, Anty lubna da wannan budurwar ,jamcy(k'anwar mijin lubnace,kuma ita a haukanta San yarima take.) sai wasu k'awayen ammi 2zaune,ga kayan marmari agabansu.


"Duk'awa yarima yyi yagaidasu shida yasmeen, sannan suka zauna,ga k'ugunshi ga nata".


Sai harara lubna da jamcy suke aikoma da yasmeen.


Ita kuwa yasmeen ,azuciyarta tace wato kuna bak'in ciki kungammu tare....muryar kawayen ammi taji suna musu sallama suka fita.


Murmushi yasmeen tayi, da gayya dan ta k'ara basu lubna haushi,ta aza kanta gefen kafad'arsa had'e da zagaye hannunsa da hannuwanta har hannun nasa na gugar nashanunta,hakan kuwa bakaramin tsima yarima yyi ba..


" ahankali yace baby nah me kikeso ki ci?yafada yana nuna mata kayan marmarin dke tsakiyar parlourn. "


Cikin shagwaba tace ruwa zansha sai tuffa,tayi hakanne dan ta nunawa lubna ta isa ta juya yarima kogaban wama.


Tashi yyi yadakko ruwa yazuba a cup yabata tasha ,ya aje cup d'in, matsawa yyi dan d'akko mata tuffar ...Anty lubna dke mamakinsa wai yarima me aji da k'asaita har wannan me kama shuwa Arab din kesakasa aiki k'ila bata barshi hakaba,cikin haushi tace kai Ashman meye haka?


Agaban mu take juyaka ,kaikuma kana biyemata,


"Mitss ta bankowa yasmeen harara had'e da cewa aidama d'an talakka bai iyacin arzik'iba kinxo kingama dashi..jamcy ta karbe da cewa aidama duk yadda kke da jaki shege aisaiyaci kara...muryar yarima ta katsesu ,cikin tsawa da karaji yace ya isa Anty kinxo inda bazan iya jurewaba.


" me yasmeen ta kashe miki? Kika tsaneta hakane?


d'azun ma kin hantareta ,nak'yale yanxun kinsake harda waccan wawiyar data rako mata a duniya ita ma har zata saka baki ko?


To wlh duk Wanda bayasan iyalina nima bazanso saba.yana fadin hakan yaja hannun yasmeen da kanta ke duk'e tana jin dad'in yadda yarima yanuna tanada daraja agunsa,suka bar part din afusace...


Baki bude lubna ke kallonsu harsuka fice dg parlourn,tana mamakin yadda yarima ya yagaya mata mgn sbd matarsa,amatsayinta na yayarsa..


"Muryar ammi  taji tana cewa kadan ma Kika gani ,muddin bazaki rik'e girmankiba,d'an uwanki dg dawowarsa zaki fara bata masa rai kinyi dai dai ai...


" shiru lubna tayi dan tasan amma saita mata hukunci".


Afusace ammi ta kalli jamcy tace ke tashi kibamu guri zanyi mgn da ita.


"Tabe baki jamcy tayi ta tashi tafice."


Tsaki ammi tayi tace ke a haukanki wannan abarce marar tarbiya xakiso d'an uwanki ya aura ,ji yadda ta tabemun baki ta fita,inbaccin tare kuke harta isa tashigomun part bbu wani dalili hartayi hakan da jikinta yagaya mata,kuma last warning kada kisake xuwa da ita gidan nan.


"Kin ji ko bakijiba ?"


Ammi ta fada atsawace,lubna tace to pls ammi kiyi hku bazan sakeba,haranta ammi tayi tace ki sake ma.


Inaso ki sani muddin Kika sake Shiva harkar yasmeen koyimata tsawa da hantararta ban yafemiki ba tana fadin hakan ta shige bed room dinta......


Bangaren su yasmeen kuwa...


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿55&56


,,6angaren su yasmeen kuwa afusace yarima yajata suka isa bed room d'insa.,

Kan bed yafad'a had'e da kwanciya rigingine yalumshe idonsa yanajin zafin abinda Anty lubnah tayiwa yasmeen.

"yasmeen dke kallonsa dan ta lura ransa yabaci sosai",

Kan k'irjinsa ta kwanta .

         " ahankali tace pls kayi hkuri ",hannu yasa yashafi gashinta yace ,bazan taba barin wani ya wulak'antaki ba keda familynki  agabana ,inkyale dole nad'au mataki...wayarsa ce tayi ringing

Janye yasmeen yyi dg jikin sa yanufi gun mirror yadauki wayar dan me martaba ne ,jinayi yace yanxun?to ganinan xuwa,kashe wayar yyi yabude sif d'in kayansa yafito da suit bakak'e ,kallon yasmeen yyi yace baby xoki shiryani.

     " tasowa tayi fuska bbu walwala tace yaya ina zakaje?"

Kallonta yyi yace abbane yakirani naje governor da shugaban alk'alai nason mgn dani yanxun..

"batace komaiba " saidai sai wani d'aure fuska take tana turo baki gaba, tata yasa yashirya ,tayi saurin juyawa dan tafiya ..da sauri yarima yarik'e  hannunta,yajanyota jikinsa.

"Ahankali yace baby nah menene?"

Fad'amun kinji?turo baki tayi,saiga hawaye sharrrrr afuskarta,subhanallahi, yarima yace had'e da janta kan bed ya azata kan cinyarsa ,yanaso su had'a ido amma tak'i yarda.

Murya k'asa k'asa yace pls kifad'amun mekikeso?

"cikin kissa da Jan hankali tace nibanaso katafi kabarni ", kada asaceka.

Murmushi yyi yace oh baby rigima ,insha ALLAH lfy zandawo ai kina mun addua keda amminah kada kidamu kinji babyn yayanta...

Cikin shagwaba ta ce to muje tare.

       Ware ido yyi cikin rarrashi yace kizauna gun ammi nadawo akwai maza agun bazai yuyu mujeba...ihun da yasmeen tasaka yasashi yin shiru ,sai kukan shagwaba take ita bazai tafiba,da k'yar yashawo kanta tayi shiru ,yayi mata rollyn da mayafinta yaja hannunta zuwa gun ammi,amma azuciyarsa mamakin kansa yake wai yau yarima shine ke rarrashin mace,shinmeyasa bayasan  ganin ta tana kuka?meyasa yakeson abinda takeso,...hannunsa da yasmeen ta girgiza yasashi dawowa tunaninsa wasu tanuna masa sukayi masa jaje,sannan suka Shiga ciki.,,,,


Ammice a parlourn da kuyanginta ,suna ganin su yarima suka fita,murmushi ammi tayi tace oh my son sai ina kuma?


" nan ya sanar da ita gun dazashi "


Yasmeen ta kalla taga kamar tayi kuka,tunawa tayi da abinda lubna tayi msta k'ila shiyasa tayi kuka....muryar yarima ta ji yace ammi ga baby nan ki lallabamun ita nadawo sai koke koke takeyi wai kada asake saceni..


"Murmushi ammi tayi tace oh, xonan y'ata kinji yadawo,ai ALLAH yana tare da shi gakuma adduarki datawa kinji."


Zama yasmeen tayi gefen ammi,shikuwa yarima kasa tafiya yyi ,duk'awa yyi yayiwa yasmeen rad'a jinayi tace da gske yaya? yace eh ,dariya sukayi shida ita,itadai ammi na gefe dan ita aganinta summa manta tana gun ,tashi yasmeen tayi tace muje narakaka yaya...


,,,kafin yarima yyi mgn ,umman yasmeen tayi sallama da gudu yasmeen taje ta fad'a jikinta tana ihun murna.,,


Murmushi yarima yyi yace oh baby nidai kada kikayarmun da ummanah.


Umma cikin fara'a tace gskiyarka kuwa dan haryanxun tak'i girma..hararan yarima yasmeen tayi ta kalli ammi dkema umma maraba tace ammi kingansa ko yana Jana..


Yar dariya ammi tayi tace ALLAH ka kiyayeni,..murmushi yarima yyi yatsugunnah suka gaisa da Umma tamasa jaje,tukum yatafi...


Umma  kuwa bayan sun gama gaisa wa da ammi tamata jaje ,sannan yasmeen tajata wai tazo part dinta su gaisa,datak'i xuwa Saida ammi tasaka baki tukum tabita suka tafi.


Bayan sun sake gaisawa,umma ta fito da na u,rar da yarima yabata (takunna in bala yaje gdnta)


"Yasmeen tace name ne umma?"


Umma tace ki aje in mijinki yadawo kibasa,kinji ki Adana,nan tace to.


Cikin jin dad'in ganin yasmeen tana cikin kwanciyar hankali da zaman lfy da mijinta da danginsa ,taitawa yasmeen nasiha had'e da cemata ai Omar yace gobe zaidawo Nigeria dan ayi komai agaban idonsa.


Yasmeen tace ,aisai yahuta tukum sannan afara shariar,amma umma kina ganin da saka hannun Kawu a mutuwar abbanmu?


Umma tace hmmm yasmeen kenan,inmijinki yadawo kinji tabakinsa Nina tafi,jiki ba kwari tayiwa umma rakkiya tadawo part dinta ta shige bath room dan yin wanka..


      ***********

bangaren yarima kuwa koda yafita tare da Sarki had'e da security, suka nufi gidan Governor aka tattauna mgnar su waye sukayi kiddinapping dinsa?


Bbu boye boye yarima yyi ma governor da shugaban alk'alai bayanin farkon Shari arsu dakawu bala da alhj jamilu, sbd yasmeen ne,Yakima sanar dasu irin kamun dayyiwa alhj jamilu da yara 2zaisace.

         sannan yasanardasu zargin da akewa bala akan shine yakashe mahaifin yasmeen.

"nan aka aje magana tunda suna hannun hukuma to kawai ashiga kotu tunda akwai shedu ayi shara'a akan abinda ake zarginsu."

Maganar kiddinapping akyalesu kawai...sai in anyanke musu hukunci asaka su fito da sauran mutanan da su aikata kiddinapping din tare..

Badan yarima yasoba ya amince da hakan had'e da cewa jibi xa'a fara shariar zuwa gobe zai had'a shaidunsa...

Bayan sun fito ,yarima yacewa Sarki zai wuce police station, nan kowa yyi gun dazashi,dukda yarima bai waniso security suka biyosaba to dan dai Sarki yace subisane shiyasa...


Suna isa dpo yabashi ghanonin da aka kamasu da kud'i aciki,umarni yarima yyi da asaka kudin a boot .


Yarima yace akaisa gun da bash yake,bbu musu ,suka kaisa...


"Hmmmm duk Wanda yaga bash saiya tausaya masa yyi bak'i kirin yarame yafita kamanninsa sbd wahala da horo mai tsanani,ammafa da alama yahorun..


,,yana ganin yarima yazube yana tuba da Neman afuwa yasaka asakesa.,,


" shima yarima yalura da yashiryu yagane rayuwa,dan haka yace asakesa."


dg gun bash ,sell din dasu ahj jamilu suke yarima yanufa..kwance magashiyan yasamesu sunci duka na fitar hankali ,duk fuskokinsu akumbure,dan inba saninsu kayiba bazaka ganesuba,dan duk ancanja musu kamanni da dukan da'aka musu..


""" kalon tsana yarima yabisu dashi had'e da tafa hannuwansa ,yace sannunku masu iya dubara ,Ashe a iyanan wayonku yatsaya hmmmm inaso kusani jibi Ku shirya shiga kotu dan duk inda kukai wadanda kuka kashe kuma zakubisu...bala dan kunya kasa d'aga kansa yyi shikuwa ahj jamilu sai tsinewa bala yake wai shine yasakashi aikata hakan.


Tsaki yarima yyi yace ai kiddanapping nawa da kukayi shima bazan kyalekuba zan d'auki mataki Ku azatonku ,k'arshenku bazaizoba,hmmm kunyi kuskure.


Nasan kunyi mamakin yadda nagane June kukamun haka,sbd kunsaka safar fuska ko?


To bari kuji ko sau d'aya naji muryar mutum indai mugune to zanganeshi aduk inda naji muryar shi,yana fadin haka ya kalli dpo yace acigaba da azabatardasu su fad'i inda sauran mugayen suke akamosu..


Dpo yace to, nan yarima yyi tafiyarsa.


Bank suka nufa suka mayar da kudin tukum suka dawo gida ,alokacin anata Kiran magrib,masjid ya wuce be fitoba Saida akayi isha'i..


da kansa yaja mota yaje yasiyawa yasmeen nama gashashshe da ice cream, sannan yanufo gd.


bayan ya iso part din yasmeen yaje batacan,nasa yaje canma batanan ledojin dayazo dasu ya aje kan bed yawuce part din ammi.


Tafiya yake azuciyarsa yana jin haushin miyasa bazata jirasaba matsayinsa na mijinta sai dai shi yaje yakirata wato ita bata damu dashiba kenan..


"Tsaki yyi yashige parlourn ammi ,aikuwa tana can ,gaida ammi yyi had'e da cewa yasmeen yauwa,tana cema sannu da xuwa..


Kallon ammi yyi yace Saida safe ya fita..


Tab'e baki yasmeen tayi had'e da mikewa ,sukayi sallama da ammi ,tana tunanin lfy tagansa yana wani shan k'amshi da tunanin ta fita .


Jitayi anrungumeta ta baya,cikin shagwaba ta ce ,nika cikani sai wani d'aure fuska kakemun agaban ammi kana wani basarwa shine yanxun zaka wani r...rufe mata baki yyi da hannunsa yace muje sarkin shagwaba aikece wai bazakijiraniba sainaje natafi dke kin kyauta?


Ji yasmeen tayi batasan Bacon ransa,cikin sanyin murya tace to Yayana nabari,murmushi yyi yace ko kefa har naji dad'i muje ki karbi tsarabarki danamiki,bbu musu tabisa part din sa.


Bed room dinsa suka Shiga....


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿57&58


,,,bedroom d'in sa suka shiga,kan bed yajata had'e da bude mata ledar ga shashshan naman yatura mata agabanta.,,

Tuni yawunta ya tsinke sbd yadda k'amshi yadaki hancinta"

       "Ahankali yaciro yasamata abaki ,takarba had'e da lumshe ido ,sai dai aikin kallonta yake zuwa can taga beda alamar yaci,nanta nuna bata yardaba saidai suci tare.

Haka kuwa akayi sunci sun k'oshidg bisani yasmeen ta gyara gurin ,toilet ta wuce tahad'a masa ruwan wanka tayo brush ta fito.

" dg shi sai dan boxer tasamesa ,"kauda kanta tayi had'e da cewa yaya jekayi wankan kaji?

       "Ahankali yace to muje tare zamu yi ai", ware ido tayi tace nifa tuni nayi wanka,yace meyasa bakijiraniba?"

Cikin shagwaba ta ce to bakaine kayitafiyarkaba ni kaje kayi wanka ,bece komai ba yanufi toilet din.

Ita kuwa,vest da wani boxer ta fitomasa dashi ,har zata fita ta tuna da na'urar da Umma tace ta basa,fita tayi taje bed room dinta ta d'akko ,sannan tadawo.

"Tsakiyar bed din sa ta zauna tana jiran yafito tabasa taje ta kwanta."

Bbu jimawa yafito d'aure da towel ak'ugunsa wani kuma saman wuyansa yana tsane

ruwan jikinsa.

          gaban mirror yatsaya had'e da cewa baby zo nan!

Tashi tayi ta matsa kusa dashi,fara tayashi shafar,jiyayi wata kasala sakamakon lallausan hannunsa datake shafe masa jiki cikin dauriya yatsaya harta ida masa, ta juya ganin zai cire towel din sa.

         Kanbed ta koma ta bashi baya,shidai dan murmushi yyi kawai,bayan yasaka yazo gefenta ya kwanta had'e da rungumota ajikinsa

na'urar dke gefenta ya d'auka had'e da cewa baby ina Kika sami wannan?

Tace yauwa ummace tabani na ajiyemaka,Aida sauri ya kunna ,kafin yasmeen tace wani abu .... Jin muryar Kawu bala sukayi ......kaf Saida suka gamaji,kuka kawai yasmeen keyi ,shikuwa yarima hmdala yyi dan dama abinda yake son samu kenan,tashi yyi yaje ya Adana na'urar yadawo gun yasmeen.

share mata hawayen yyi yace indai ina numfashi to bala zaije gun da Abba yatafi insha ALLAH ,kinji kidena kuka.

"cikin damuwa yasmeen tace oh dama abinda duniya muke ciki kenan cin amana,yazama ruwan dare ,yanxun har d'an uwa zai iya kashe d'an uwansa sbd abin duniya...

Yarima yace hmmm wanima har ubansa yakashe sbd gado ma kinga k'arshe kenan..

Wani tsanar Kawu bala tasakeji yana shigarta,ananma yarima yasanar da ita cewa aishida alh jamilu suka yi kidnapping d'insa..

Kuka yasmeen ta sake barkewa dashi or dama tasanadinsu akayiwa yarima haka ,lallai bazata tab'a mantawa da yarimaba arayuwarta...rungumar da yyi mata ne yasaka ta yin shiru.

      " ahankali yarima yazameta dg jikin sa ya kwanta kife yadafe mararsa sbd ciwon datake masa."

Yasmeen dke kok'arin tashi taje ta kwanta, ta kalleshi zatayi mgn taganshi haka,da sauri ta shafa kansa had'e da cewa yaya lfy kobaka jin dadi ne??

cikin karfin hali yace yasmeennnnnnnnnnnnnnnnn!!

Marata pls kibani hakkina wlh komai zai iya faruwa dani pls na rokeki....rufemasa baki tayi tace to yaya amma  kada kamun me zafi dan  ALLAH.. da sauri yajanyota had'e da komawa samanta yarage hasken d'akin ,bbu bata lokaci yyi fatali da duk wata suturar jikinsu yaja blanket yarufesu...

Hmmm bewar ALLAH yasmeen yarima yasha mamakin yau batayi kukaba kota k'amemasa tadai rufe ido,haka yyita romancing dinta har suka Lula babbar harka.

Awannan dare yasmeen ta ji jiki gun yarima be sahirtamataba Saida yasamu gamsuwar dabaitaba samuba da ita Dan jun kwan biyu basu haduba..

gefenta yabaje yana maida numfashi, yarungumota ajikinsa,murya k'asa k'asa yace baby nah nagajiyar dake ko?

Tsintar kanta tayi da b'oyemasa ,dan yanxun haka gabanta zafi yake mata,amma saitace ah ah murmushi yyi yace to anjimama zan kara kinji tawan?

"cikin dauriya tace to ,ahankali yace muyi kwanciyarmu nan,dg yau tare zamu ruka kwana kinji ?kidena guduna pls...

To yasmeen tace, had'e da yin lub ajikinsa ,kayan baccinta take kokarin mayarwa ,amma sai yarima yahana ,wai baida ra'ayin sudunga kwana da sleeping dress..

       Haka ta hkura ta fasa ,har bacci yyi gaba da ita suna manne da juna,,,

gab da asuba,taji yarima na lalubarta ,haka ta hakura tabarsa yasake biyan bukatarsa da ita dg bisani yatashi yanufi toilet yahada mata ruwan dumi, yadawo da towel a hannunsa ,janye blanket din yyi yadaura mata towel din ,had'e da mikar da ita tsaye..

wata k'ara tasaki sbd yadda takejin azaba agabanta.

         da sauri ta zauna tana cewa yaya zafi gurin bazan iyaba,wani irin tausayi tabasa duk saiyaji bbu dad'i dukda yafiso yasaba mata watarana zata daina jin xafin tasaba dashi....

" kamata yyi yawuce da ita toilet din tana kuka da shagwaba ya gasata had'e da yima ta wanke ,yabarta tayi na wajibi da kanta.

Kwata kwata taki kallansa ,shikuwa bbu kunya wankansa yake hankali kwance bejin komai danta gansa zir bbu kaya...haka ta fito dg toilet din kafafunta aware kamar yaune first night dinsu,dan yarima namijine shi ba kad'anba."

gaban mirror ta tsaya tadan share jikinta da mai shikuma yafito,ahankali tace yaya dakkomun kayana ,nasaka...


Murmushi yyi yace hmm bazan dakkoba tunda baza'a kalleniba..


Marairai cewa tayi wai kada lokacin sallah ya wuce  ,wadrop ya bude yafito mata da jallabiyarsa tada masa kadan da sabbin inner wears yabata ,toilet taje tasaka tadawo taga hijab da prayer mat, atare sukayi sallar,sannan yajata suka sake komawa bacci...


""" basu suka farkaba sai karfe10:00am itace tafara tashi,k'uri da ido tayi wa yarima ,azuciyar tana cewa masha ALLAH Dan ganin tsantsar kyawunsa ,kokarin tashi take dan tana gudun kada yafarka yace sai sake wani abu da ita."""


hannuwansa ta kalla taga yawani riketa GAM ga k'afafafunshi cikin nata ,kansa agefen wuyanta ,numfashinshi na sauna abisa goshinta..


da gowa tayi ,jitayi kamar tashafi sajensa da ke kwance lub yak'ara masa kyau,hannu ta mika taja karan hancinsa dan itama yana Jan nata..


caraf yarima yarik'e hannunta, runtse ido tayi dan ta ji kunya.


Murmushi yyi yace good morning my baby ,itama murmushi ntayi tamaida masa gaisuwar.


Tashi yyi da ita wai suyi wanka,fafur yasmeen ta juya,Saida taga ransa yab'aci tukum ta bisa toilet din sukayi suka fita.


Hana zuwa part dinta yyi anan tashirya da mayukansa da turarukansa,amamakinta taga yafito masu da kaya sabbi iri d'aya ita gown ce dark blue mai hannun vest sai yar ciki fara..


,,,shikuwa suit ce dark blue ta saman da fara y'ar ciki,kamshi iri d'aya suke sunyi gwanin kyau ko makiyi yagansu yasan sunyi kyau bbu karya duk da bbu make up a fuskarta.


Tayi rolling da mayafi dark blue.


"Ammafa har yanxun tafiyarta ba daidai takeba ,daurewa kawai take,kuma yarima nalura da ita..


Tausayinta yakeji sosai ,wani gefen kuma yanajin nauyin ammi taganta dan yasan xata gane anya summa tafi tare kuwa...


Kallonta yyi yace baby muje muyi break ,amma kihakura da zuwa gun ammin tunda bakyajin dad'in jikinki.


Kuka yasmeen ta saka masa had'e da fudge hannunta daya rike ,tanufi k'ofar fita.


" gabanta yasha yace sorry yar gidan ammi ,nabari muje ,shikenan"


A dining area suka wuce sukayi break fast ,sannan yaja hannunta suka wuce part din ammi...


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿59&60


Hannunta cikin nasa suka isa,zaune suka sami ammi kan kujera tana Jan tasbaha kuyanginta na gefenta.

"Tunda suka shigo idonta ke kan yasmeen har suka gaisa", tana tunanin meyasa take irin wannan tafiyar.

      Muryar yarimace takatseta yana cewa ammi zanje office in had'a duk wasu shaidu gobe zamushiga kotu..

(kasancewar yyiwa ammi bayanin komai)

Cikin jin dad'in har yanzun yana akan gsky tace to ALLAH yabada sa'a, yakaimu yatsaremun kai aduk inda kake..ameen yace yana murmushi.

       " kallon yasmeen yyi yace baby natafi..cikin jin kunya ta ce adawo lfy "fita yyi dukda yaso tarakasa gun mota amma bayaso ammi ta fahimci wani abu.,,,

Bayan yafita ,ammi takalli yasmeen tace oh yau duk kinyi shiru shiru kamar marar lfy, ko wani abu ke damunki ta kafeta da ido,azuciyarta tana cewa ALLAH yasa cikine da ita..

Yasmeen tace ah ah bb komai."

"Ahankali ammi tace jiya wani abu na auratayya yashiga tsakaninki da son?"

Kai aduk'e yasmeen tace eh.

Batace komaiba ta nufi bed room dinta, azuciyarta tana tausayin yasmeen dan tagane cewa yarima yana da fitina,toilet ta shige da kanta ta had'a ruwan dumi had'e da wasu magunguna sannan tazo ta ja hannun yasmeen ,bbu musu tabita..

      adede toilet din ammi ta tsaya had'e da cewa yasmeen kishiga aruwan dumin karki fito saisunyi sanyi..

To tace ta shige toilet din.,,,

Ammi kuwa kafin yasmeen ta fito harta had'a mata wasu magunguna da damesu da madara,tana fitowa tabata tace maza shanye kinji y'ata bbu musu ta shanye duka,ammi tace to kwanta kiyi bacci kinji,cikin jin dadi yasmeen tayi kwanciyarta kan bed din ammi me rumfa na gargajiya irin na sarauta,bbu jimawa bacci Yy gaba da ita Dan da ma bata samu bacci sosaiba jiya..


      ******


Yarima kuwa duk wasu shaidu nasa yarigada yahadasu ,bayan yagama komai yakira umman yasmeen bayan sun gaisa yace mata gobe ne Shari'ar da karfe10:am.

To tace had'e da sanar da shi aiga umar nanma yadawo jiya da dare dan yanaso ayi shara'ar yananan..


Yarima yace umma inbbu damuwa inaso yazo yanxun yasameni a office dina dama bamusan junaba,cikin jin dadi umma tace to ,sukayi sallama..


Yarima befi20 minit dayin waya da ummaba yah Omar yyi knocking,yarima yace yes nan yah Omar yashigo da sallama..


"" cikin sakin fuska yarima yatarbesa ,kallo d'aya yyi masa yagane shi jinin yasmeen ne".


Bayan yah Omar yyiwa yarima jaje nan yasake masa godiya akan k'okarinsa akansu,murmushi yarima yyi yace bbu komai yiwa Kaine.


ahankali yah Omar yace ina yasmeen sarkin shagwaba Nasan kana fama da ita da rigimarta...


Yar dariya yarima yyi yace oh baby Ashe kodai agd ba umma kadai takewa rigimaba harda kai,murmushi yah Omar yyi,azuciyarsa yace shima baby yake cemata kenan.nan yahau basa labarin yasmeen da yadda ya shagwaba.,,,


Ahankali yarima ce Ashe Kaine ka shagwabar da ita kenan,murmushi yah Omar yyi bece komai ba.


"Yarima yakalli agogon dke d'aure atsintsiyar hannunsa yacewa yah Omar muje muyi sallah ko?" Saimutafi gd Ku gaisa da yasmeen dan intaji kazo har office dina bakaje guntaba saitayi kusa kuka.""


Nan suka mik'e ,sai firarsu suke,kamar dama sun San juna bbu wani jida kai ko isa da yarima yanunawa Omar,shikanshi yah Omar din yaji dadi sosai kuma yana mamakin wai shine yau zaishiga gidan Sarki.


       ********

6angaren yasmeen kuwa ,bata farkaba sai 1:00pm da yan mintina,wasai taji jikinta ga tafiyarta ta daidaita.


"Part dinsu ta wuce tayi sallah ta gyara part din yarima,sannan tayi wanka had'e da yin wata fitinanniyar kwalli tasaka pink lass Riga da sket yyi masifar karbarta .


A waiting parlour ta zauna tana jiran yarima yadawo suyi lunch dan jiyane suka fara cin abinci tare sai yau dasukayi break jitake inbatare dashiba bazaci abinciba...sallamar su Maryam da salim ce ta katse mata tunani..


Zaunawa sukayi suna fira abinsu suna dariya...sallamar yarima yasmeen taji juyowa tayi ta ga yabude mata hannuwansa da gudu taje tafad'a jikinsa ,suna dariya itadashi..


Sama yad'aga ta yana juyi da ita ...bata auneba taji muryar yy Omar dinta yana oh ni yah Ashman agaba ake soyewar? ,da sauri ta kalli gefen..


Ido 4sukayi da yah Omar, ihun murna tasaki,had'e da cewa yarima yayah saukeni...da gudu ta fad'a jikin yah Omar tana murna..,,


Maryam kuwa suman zaune tayi ganin wannan kyakkyawan santalelen saurayin,masha ALLAH take cewa azuciyarta dama wannan ne yah Omar din da yasmeen keyawan fadi' aibatayi zaton yawaye hakab...muryar yarima taji yace keeeeee!baki iya gaida mutaneba?


kallon gefen da yah Omar yake tayi cikin class tace ina wuni?


Shikuwa yah Omar lumshe ido yyi jin sweet voice dinta ,yace lfy atakaice dan kallo daya yyimata yaji ta tafi da imaninsa......


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿61&62


"" Ahankali Maryam ta tashi tabar parlourn, shima salim tashi yyi bayan sun gaisa da yah Omar. "

Yasmeen kuwa cikin jindadi tacika gaban yah Omar da kayan motsa baki.

       Sannan ta zauna gefen yarima ta na tambayar sa yah ummanta take?

Yace lfy take.

"Koda yarima yaga yah Omar yakicin komai,kama hannun yasmeen yyi yace baby muje muyi lunch kinga yah Omar d'inma bakunta yakeyi agidanki ko?"

cikin shagwaba ta .bisa had'e da cewa ALLAH nima zan rama innaje gidansa.

"Shidai Omar murmushi yyi yana ganin bala'in dacewar k'anwartasa da yarima azuciyarsa yace oh baby lokacin da za'ayi auren ta yita koke koke amma ji yadda suke zuba love....yarimane yakatsesa da cewa suje suci abinci..

         " haka kuwa akayi yabisu yasmeen tayi serving in su,itada yarima a plate daya kuma shike feeding dinta, shidai yah Omar cin abincin yake yana sha'awarsu wane gefen xuciyarsa yana tunanin yarinyar dasuka gaisa wacece ita agidan?"

Motsi kad'an yasmeen tayi, yarima yace menene?mekikeso ?ita kuwa sai tabararta take,yah Omar yarigasu tashi kan kujera yakoma yazauna ...

      Yasmeen kuwa shagwaba takama yiwa yarima wai bbu inda zashi sai gobe ita bazai barta yyi tafiyarsaba."

Lallabata yyi har suka ida cin abincin, sannan yarima yaja yah Omar yakaisa yagaishe da ammi,wadda bak'aramin dadi ammi tajiba sannan yadawo sukayi sallama dasu yasmeen akan sai sun hadu gobe a kotu..

Yasmeen dakyar tasake yaya Omar ganin kallon da yarima yyi mata tukum yatafi,yarima yadawo dg yimasa rakkiya,bed room dinta yanufa gaban mirror yasameta tsaye tana latsa waya rungumeta yyi ta baya..cikin tsiwa ta turesa had'e da cewa ni me ruwana da kai ,shine kaki bari naraka yah Omar har get ko?"

Hancinta yaja yace eh amma aikinsan barorin gidan na gun ,kuma ko alkhabba bbu ajikinki sai kawai kibisa..

dukansa tayi akirji ...rik'e mata hannu yyi yace lah lah lah ni aiko nima saina rama kuw...arcewa tayi yarufa mata baya zagaye bed room din sukayitayi dg bisani yasmeen ta gaji ,kan bed ta baje,biyota yyi ,kan kirjinsa ta kwanta tana maida numfashi, cikin shagwaba tace yaya nagaji tashi kagoyani,murmushi yyi um um ...birgima tayi ta yi ajikinsa da koke koke, gaba d'aya ta sakarma yarima kasala,murya k'asa k'asa yace baby

Nah rigimammiya d'agani na koma office kinga lokaci natafiya..

"Turo tayi tace ank'i din ,dan bakin yakalla yasha lip stick yace kinyi kyau,nidai kikayiwa wannan kolliyarko?"

Murmushi tayi had'e da shigewa jikinsa tace eh amma nifa bbu inda zakaje....bakinsu yahade gu d'aya yana Mata wani irin kiss kamar zai cinye bakin .....amamakinsa sai yajita tallabe kansa tana shafawa da sauri yadawo samanta had'e da xuge mata xif din gaban rigarta atake na shanunta suka bayyana kasancewar bbu bra aciki,bbu bata lokaci yacafkesu yana tsotsa sai maida numfashi suke,tun yasmeen na jurewa har ta fara masa kuka sbd yadda yake musu tsotsan fitan hankali sai xugi suke mata,da k'yar yasaki duk sunyi jajir..

Cikin kasalallar murya yace pls my baby kitsaya mana ai muna tare bbu inda zanje ko,cikin son faranta masa tace to jiki asanyaye dan tasan indai yarima ne ba gajiyawa yakeba.

Kayanta ya rabata dasu hade da rufesu suka Lula wata duniyar....saidai bataji wannan zafinba irin na jiya saidai gajiya da yayi..Saida aka kira la'asar tukum yarima yasahirta mata ,sukaje sukayi wanka sukayi sallah.

      "Rigima tasaka masa yagoyata bbu bata lokaci kuwa yatsaya ta d'ale bayan yahau zagaye parlourn da ita.... Maryam ce tayi sallama ta na ganinsu da sauri ta juya yasmeen tayi saurin dakatar da ita shikuwa yarima tsaki yyi aganinsa ta katsemusu jin dadi, zillo yasmeen tayi tayi yasauketa,sauketan yyi fuska a d'aure yabar parlourn ".

duk kuma saitaji bbu dadi tasan haushi yaji tunawa tayi inda da ne ta isa ma yakulata amma yanxun sun shirya shine take masa haka,kallon Maryam tayi tace kinga yayanku yyi fushi bara naje na rarrashi abuna,murmushi Maryam tayi ta ce wlh Anty ni azatona yafita shiyasa ma kikaga nazo nima na tafi aje asha love lfy...fita tayi,yasmeen ta nufi parlourn sa..

       "Yarima kuwa kwanciya yyi cikin jin haushin rashin damurda yasmeen bata nuna masa a matsayinsa nah mijinta,tsaki yyi a fili ce hmmm zanyiwa ammi mgn gsky mu koma gidanmu mubar gidannan gsky ina takura ,turo k'ofar da yasmeen ta yi yasakashi yin shiru,jikinsa ta fad'a tasaki kukan shagwaba...

Akasalance yace menene dan bayasan ganin kukanta,da hannu ta nunasa tace bakai bne kayi fushi kayi tafiyarka kabarni...

Fuska bbu walwala yace mekikeso nayi miki?yasmeen kwata kwata na lura baki damu dani ba ,tunda gashi muna tare ganin Maryam kinshareni.....katsasa tayi da cewa yaya bafa haka bane naga ta tafi bbu dad'i shine natsaidata,amma kayi hkuri nabari kajiiii tafada cikin shagwaba, matseta yyi ajikinsa had'e da radamata ALLAH yasa yau da dare mu sami rabon baby ..ware ido yasmeen tayi tace um um yaya bayanxunba nifa yarinyace kuma haihuwa da wahala akace....had'e rai yyi yace wato bakison had'a jini da ni komeye?

" ahankali tace ah ah ba nufina kenan ba ,ina nufi da wuya haihuwar",murya k'asa k'asa yace bbu wahala kunji aike kinama bacci zaki haihu...dariya yabata sosai,Saida tadara yayinda yashagala da kallonta...""


"Ahankali tace yaya gobene shariar ?"


Yace eh


Shiru tayi had'e da yin lub ajikinsa,can tace amma nima zanje.....Dan xaro ido yyi yace taf bbu inda zaki..ihun datayine yasakashi yin shiru ,kok'arin Barin jikinsa take shikuma yaki saketa..


Be auneba yaga tana kuka da hawaye ,aituni yarima yarude,share mata hawayen yahauyi had'e da cewa shikenan na yarda zakije pls kidena kukan kinji banason ganin kina kuka pls ya isa haka.


,,shiru tayi tanajin dad'in yadda yadamu da ita sosai.,,


Haka yarima yyi ta kokarin ganin yasmeen tayi dariya,aiko Saida tadara sannan yadena rarrashi nta basubar gunba Saida aka kira magrib kamar karsu rabu yawuce masjid ita kuma tayi sallarta a gd.


Yarima be dawoba sai bayan isha'iyasami yasmeen dg it's sau towel,kanbed yazauna ta d'ale kan cinyarsa wai yataso yayimata wanka,murmushi yyi yaja hancinta yace zanyi aiki a laptop kibari sai anjima saimuyi tare kinji yafad'a had'e da mika mata ledar dayashigo mata da ita ,karba tayi tabar jikinsa batace komaiba.... Ai tuni yarud'e ya a'jiye laptop din yayi saurin rik'eta sai fisge fisge take ita yacikata tunda aikinsa yafita mahimmanci ,gaba d'aya ta d'aga masa hankali dan gaba d'aya d'akin takes an bari sai kukan rigima take...


"yarima bawan ALLAH sai rarrashi nta yake dan yasan inta tafi rufe masa kofa zatayi,da k'yar ta hkura yaje sukayi wankan tare ,bayan sun shirya sukaci nama gashashshe,rigima tasaka saiyyi mata tausa bbu yadda ya iya yayimata har tayi bacci tukum sannan yyi aikinsa byn ya idar yyimusu addua suka kwanta...


         *******

Washe gari tun wuri suka shirya,uayansu iri d'aya ma yau,sunayin break fast part din ammi sukaje suka gaisheta ,tayimusu addua da saka musu albarka suka fita dan  sun sanar da ita atare zasuje gun shari'ar..


Bayan driver yyi parking yarima da yasmeen dke baya suka fito, yana rik'e da hannunta.


"" gaban kotun kuwa ,ummace yah Omar,inna atika da hassu ,makociyar umma,cikin sakin fuska yarima yagaidasu,yasmeen tafada jikin ummanta tana shagabarta,koda taga yarima zaishiga ciki da sauri tace yayaaaaa!


Tsayawa yyi ta iso ,rungumota yyi su shige cikin kotun ,yyinda su yah Omar suka biyosu abaya..


Kan kujera da yarima zaki zauna ya aje yasmeen had'e da shiga wani daki yasako rigarsa ta lauyoyi,masha ALLAH kawai yasmeen ke cewa dan yaune farkon ganinta dashi da rigai ajikinsa ,hannunta Yakama sai kallonsu ake cike da sha'warsu ,gunda yah Omar yake zaune yazaunarda ita inda zairuka hangota kenan.


"Ahankali yace Omar ga ajiyata ko kuda yatabamun ita nidakaine ko baby nah?"


Yasmeen tace eh yaya nah,kawo kunnenka kaji,dan tukowayyi tayi masa addua ,murmushi yatafi. yyi shidai yah Omar kamar wani sakarai haka yyi yanadai ta kallonsu da jamar gun,itadai umma kunya abinma yake bata dukda k'asan zuciyar ta taji dad'in yadda yarima yake nuna kaunarsa da kulawarsa akan yasmeen ko gaban wa...


Tashi akayi kasancewar alkali yashigo,bayan anzauna akashigo da Kawu bala da alhj jamilu daure suke cikin sark'oki sunyi bak'i sun ramee gwanin tausayi,kawunansu aduk'e sbd kunyarjama'a da iyalansu...


Bash dke cikin kotun Wanda yanxun yadawo bashir dinsa dan duniya ta koya masa hankali,yafashe da kuka ganin halin da mahaifinsa yake ciki...


Shima alhj jamilu iyalansa na kotun.


Me gabatar da k'ara yagabatar da karar farko wato ta Kawu bala da Mlm Mariya .


Bayan alkali yyi yan rice rubucensa yakalli Kawu bala yace yace yah sunanka?


Bbu gardama yagabatar da kansa,alkali yace mlm Mariya na zarginka da ka kashe mata miji kuma k'aninka shin hakane koba gsky bne?"


Share ps


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


🅿63&64


""" Cikin inda inda had'e da fad'uwa gaba k bala yace ah ah sharri tamun dama tace saita mun sharri ak..alkali yace ya isa haka,kokanada shaidar dazaka bada akan baka aikata abinda ake zarginkaba?"

Yah mai sharia banida ita..

Yan rubuce rubuce yyi yad'ago had'e da cewa a b'angaren louyoyi ko akwai tambayoyin dazakuyiwa bala?

Barrister Ashman ne yatashi cikin girmamawa yace eh yamai girmar mai sharia..

       Alkali yace kotu tabaka dama barrister...

Yarima yyi gyaran murya yakalli k bala yace, inaso kayiwa kotu bayani akan daran ranar da k'aninka ya mutu wacce sa'insa kukayi dashi?

"cikin rashin gsky k bala yace nibabu wani sa'insa da mukayi dashi...murmushi yarima yyi yace adaren dazai mutu antabbatar kazo gidan kuma kayimasa wasu maganganu marasa dadi,shin kozaka gayawa kotu wanne maganganu ne kagayawa k'aninka?"

Afusace k bala yace nibbu wasu mgn Dana gayamasa kawai dai ansanar dani mutuwarsa...

Yarima yace ashariar da akayi a baya kotu ta haneka da zuwa gidan Mariya miyasa kajeeeeeeee?"

Zaro ido k bala yyi yace nibanjeba!

Yarima yace kaje gidanmana....up jection yah mai girma mai sharia,barrister saminu yakatse yarima hade da cewa yakamata lauyan me k'ara yasan irin tambayoyin dazaiwa Wanda ake tuhuma ,zarginsa ake ya mai sharia babu tabbas akan yyi ko beyiba ,sai tursasa yake ya amsa laifin da baiyiba tunda yace baijeba inaga baizama dole ya amsa abinda baiyiba...

Alk'ali yace akiyaye barrister..

Wani mugun kallo brr saminu yyiwa yarima had'e da zama..

       Yarima yace yah mai girma mai sharia inaso kotu ta bni dama nayi mgn da Mariya?"

Alkali yace kotu ta baka dama,nan umma tafito tagabatar da kanta ,yarima yabukaci tayi bayanin akan abinda yafaru adaren da marigayi yarasu,da abinda taji yana fad'i kafin yarasu....duka umma ta zaiyanesu ai tuni k bala yafara gumi yana zare ido..

Barrister saminu yamike hade da Neman yardar akali zaiyiwa Mariya tambayoyi....

   "Kafeta yyi da ido yace meyasa kike zargin bala akan shiya kashe miki miji?

Umma tace alamomine suka nuna hakan.

Yace wanne irin alamomi kozan iya saninsu?

Yarima yace up jection my lord baizama dole lauyan Wanda ake tuhuma ba yasan alamomin dayasaka take zarginsa...alkali yace k'orafi be karbuba dole ta amsa wannan tambayar...

Wani killer smile brr saminu yyiwa yarima..

Umma tace sadda ya mutu munso ayi binkice akan suwaye suka kasheshi sai yahana sannan yakwace mana duka abinda margayi yabari....

Brr saminu yah duka had'e da cewa yah mai girma mai sharia inaso wannan kotu mai daraja da adalci tayi watsi da yawo da hankalin da Mariya keyi da ita dan batada shaidar dazata gabatarwa kotu cewar balane yakashe mijinta,kawaidai tanaso tayiwa bawan ALLAH sharri...

Alkali yakalli yarima yace barrister ko kunada shaidun dazaku gabatarda akan lallai balane yakashe mijin Mariya?

Yarima yyi murmushi azuciyarsa yace anxo gurin...ahankali yace inadasu yah mai sharia.

" juyawa yarima yyi suka had'a ido da yasmeen murmushi tyimasa had'e da alamar jinjina,lumshe idonsa yyi had'e da kallon alkali yace yah mai girma mai sharia inaso kotu takira inna atika da hassu agabanta...

K'uuuuuuuuuu!cikin k bala yyi k'ara ,Wanda duk wani motsi nasa yarima na lura da su ..

      Bayan su inna atika sunfito akasakasu rantsuwa da alkur'ani zasu fadi gaskiya ,sannan yarima yakalli atika yace ranar talata misalin karfe4:30 pm kina ina?"

Tace ina gidan Mariya ,yace meya faru da wannan lokacin ...nan tasanar da kotu xuwan bala dasurutan da yyi da ihun dasukayi masa ,itama hassu haka tafad'a kamar yadda atika ta fad'a sannan alk'ali yace suje su zauna...


Yarima ya fito da na'urarsa da recording yakalli alkali yace yah mai sharia ga shaidata ta gaba, nan alkali yasaka aka karb'o aka kunnna......

Tsit kotun tayi ana sauraren komai k bala kuwa kamar yasaki kashi dan yasan tashi tak'are sai zare ido yake kai duke..


Yah Omar kuwa shida yasmeen kuka suke had'e da tir da halin k bala Ashe da gske shine yakashe musu uba,abin kunya ace ka ga bayan dan uwanka.,,,,


"""hayaniya aketayi alk'ali yabuga guduma akayi shiru.""


,,yarima ya karbi na',urarsa yarusuna hade da cewa yah mai girma mai sharia da waddannan hujjoji da shaidu Dana gabatar nike so wannan kotu mai daraja da adalci tayiwa bala hukunci akan daidai abinda ya akaita nagode....


Alk'ali yakalli brr

saminu yace kokanada abin cewa ?yace ah ah dan kansa yadaure..

Dukawa alkali yyi yana yan  rubuce rubucensa...


Alhj jamilu kuwa takashi ta duri ruwa dan ya tabbata shima tasa ta k'areeeee.


Yarima yajuya yaga yasmeen tana hawaye,alama yyi mata kotayi shiru ko su bata.."


gyaran murya ak'ali yyi kowa yabada attention dinsa ,yafara mgn kamar haka bayan korafe korafe da nazarce nazarce had'e da hujjoyi da akasamu abakin lauyoyi musammun barrister ASHMAN ISMA'IL KHALID...


Wannan kotu ta yankewa bala hukuncin Kisa ta hanyar rataya .......


Wani uban ihu bala yyi atake yafadi su mamme.....


"Security sukayi ciki dashi"


Su bash da kannansa2hade da umman su sai kuka suke..


Umma kuwa dasu yasmeen hannu suka d'aya sukayiwa ALLAH godiya...


Wani irin kallo mai tare da shauk'i yasmeen ke aikawa yarimanta.,,,


Muryar alkali sukaji dan haka aka saurara,bayani yake kamar haka ,kotu zata tafi hutun awa2sannan adawo acigaba da shariar alhj jamilu Ibrahim,yana fadin haka akamike yatashi ana kotuuuuuu!


da sauri yasmeen ta tashi yanufi gun yarima bb kunya tayi hugging dinsa,tana hawayen farin ciki...


Rada mata yyi a kunne yace baby bakijin kunyar umma ko to muje mota kihuta ko?


"hannunta Yakama suka fito waje,anan suka sami su umma cikin jindadi umma tayima yarima godiya da saka mishi albarka,amminnanta suna tayata...


Shima yah Omar din sai godiya yakewa yarima.,,


"" sallama su umma sukayi dsu dan tafiyarsu zasuyi bazasu jira shariar alhj jamilu ba."


Yarima yasaka guards dinsa da mortar dasuke ciki su mik'a su umma gida har umma tace ah ah amma ganin kamar yarima beji dadiba yasa suka  shiga...


"bayan sun tafi yarima yaja yasmeen suka shige motar".


Shikuwa yah Omar kan wasu kujeru ya zauna kafin daya ta ida yyi salla dan yanason ganin sharia ta gaba.


,,,wani gefen na xuciyarsa tuna wannan baby girl din dayagani gidansu yarima yake (sunan da xuciyarsa tasawa Maryam kenan)


Tundayake betaba soyayya ba dukda mata da yawa nacewa suna sonsa amma baya kulasu,musammun alokacin suna fama  da talauci da kunci to mata basa gabansa..


Amma yanxun ganin yarinyar nan duk ta xuxutardashi,Dan gsky kafin yatafi zai tambayi yasmeen wacece ita inbbu damu yashigar da kansa...


B'angaren su yasmeen kuwa....


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Wannan page din nakune yan awesome writer's fans club kuyi yadda kkso dashi ina mugun yinku irin totally dinnan😍😍


🅿65&66


B'angaren su yasmeen kuwa,cikin farinciki suka zauna gidan baya.

Yasmeen ta aza kanta gefen kafad'ar yarima"ahankali tace my Prince bnida bakin da zangode maka sai dai inmaka addua".

      Yar dariya yyi yace baby bbu godiya atsakanunmu saidai adduar kuma nasan kinamun ko?"

d'aga kanta tayi tace eh kuma zanciga dayimaka sai illah masha ALLAH.

"Hugging dinta yyi sosai had'e da cafke pink lips dinta yana musu sha nafitar hankali,sai maida numfashi suke."

      "Ahankali yasaki jintana mutsu mutsu ,lumshe ido yasmeen tayi dan harwani zugi lips dinta ke mata.

Cikin kasalallar murya yace baby nah mekikeso kici? Ya fad'a yayinda yake shafa cikinta.

Lub tayi ajikinsa " ahankali tace um um yaya saimunje gida,murmushi yyi ya rad'a mata kinsanta amatse nake dan bangajiya dake da munkoma gd inaso inbaki ajiyar baby nah pls kinji?

Yafad'a kalar tausayi dan yarima akwaison yara ..

d'anturo baki gaba tayi tace um um yaya nifa ba yanxunba ....

Aransa yace hmmm ALLAH zaibamu...

"Afili kuwa sai yace baby nagane bakyasan had'a zuria dani da sauri ta d'ago kanta cikin shagwaba tace um um yaya inaso wlh ....katseta yyi yace to yau zambaki ajiyar baby, murmushi tayi tace to ALLAH yasa.

       Cikin jin dadi had'e da matseta ajikinsa yace ameen.

" firarsu suke suna soyewa hankali kwance ,har lokacin azahar yyi ",fitowa yarima yyi yana rik'e da hannunta dan tasaka rigima ita bazai bartaba.

gun tape dukaje yasmeen ta duka k'asa tacirema yarima takalminsa dan yyi alwarla sai wani killer smile yake sakarmata yanajin wani yanayi atare dashi .

Koda ta cire masa ,ta kama hannun sa ta cire masa agogo sannan yafara alwarla tana tsare da abunta.

      " har yagama cikin wasa yadan watsamata ruwa afuska ,cikin kukan shagwaba tace saita rama insunje gd dan gun da jama'a ana kuma kallonsu..

Masjeed yanufa itakuma tashige bayin dke gun acan tayi arwalla taje masallacin mata tayi sallah tana fitowa taga yarima da yah Omar suma sunfito suna mgn.

       gun yarima yasmeen ta nufa had'e da rike hannunsa cikin Jan hankali tace yayanah meka rok'amun dakayi sallah?"

Murmushi yyi yace  sirrine zangaya miki kinga yanxun ga Omar banaso yajimu ko?"

dariya tayi tace eh fa nima bana so yajima...yah Omar yyi yar dariya yace oh baby Niko?"wato kinsami yaya Ashman shine Kika manta daniko?"

gwalo yasmeen tayi masa tace eh.

Kwafa yyi yace ainima dai inada budurwata nakusa bin layinku..

Yarima ce amma naji dadi aigara kayi auren banaso kullum kana zuwa kana cinyewa ummana girkiba...dariya suka saka baki d'aya gab da zasu shiga kotun yasmeen tace amma naji dadi zanzo naga wannan antyn tawa,murmushi yah Omar yyi yace kinsanta..kafin yasmeen tayi mgn sun shiga ciki duk ga jama'a nan zazzaune.

    Alkaline yashigo akatashi,bayan yazauna kowa ya zauna.

Nan aka firo da alhj jamilu,cikin sarkoki,bayan angabatar da k'ara ,alkali yace lauyoyi inkunshirya?" kufito,,,


Yarima yatashi dan yin mgn muryar alhj jamilu yaji.. yana  cewa ayimun hukunci na amsa laifina tabbas nid'an mafiyane.....tsit kotun tayi sai kallonsa ake kamar ta babb'e ,brr saminu kuwa yyi mamakin alhj jamilu daya iya tonawa kansa asiri cikin bainar jama'a...


"" hayaniya kotun takaure da ita,alkali yabuga guduma aka nutsu,sannan yafara mgn kamar haka,bamu fara shariar nanba dama dasaida mukayi binkice munsan komai munasone ya amsa laifinsa kowa yasani tukum ayimasa hukunci to tunda ya amsa laifinsa wannan kotu ta yankemasa hukun Kisa ta hanyar harbi da bindinga....""


Nan Jami an tsaro sukayi ciki da alhj jamilu yana kukan danasani.


Yan jarida kuwa summa yarima caaaaa ko kulasu baiyiba ,yasmeen dinsa kawai yake kokarin rukewa su wuce....


Wata yar jaridace tayi saurin shan gaban yarima zatayi masa mgn wani mugun  kallo yasmeen ta watsamata cikin jin jaushi had'e da isa yasmeen tace my Prince bana bukatar kasaurari kowane dan jarida..


"Ahankali yarima yace to my Princess muje gida ko?"


Kama hannun ta yyi suka fice dg kotun,yar jaridai da sauran mutane dke son mgn da yarima jiki na k'wari sukayi baya tunda princess dinsa ta hana..


A parking spaces kuwa zasu shiga motar yah Omar yazo sukayi sallama yace musu gobe zai wuce amma anjima zai kira yasmeen nan yatafi,alokacin brr saminu yafito, kallo d'aya zaka masa kasan yana cikin bakin ciki..


,,murmushi yarima yyi yaja hannun yasmeen suka shige mota,hade da barin gurin suka nufi gida.


Bayan sun isa part din ammi sukaje  dan kaimata labarin shariar,suka sami tama gama kallo atb....


Tayi murna sosai da farinciki,nan suka wuce part din su...


Share pls


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


🅿67&68


"" A dining area straight suka wuce, yasmeen tayi zaune a tsakkiyar cinyar yarima tayi serving dinsu suka fara eating. "

sai shagwaba yasmeen ke masa harsuka  gama ,kiran sallar la'asar akayi .

"yarima ya tafi masjeed ita kuma tayi tata agd."

       yana idarwa gun shak'atawar yarima ta nufa ta shige a swimming pool tana wanka had'e da wasa da ruwa.

Shikuwa yarima bayan yadawo nemanta yyita yi be gantaba duk ya rud'e ,saiyaga k'ofar gun shak'atawar  abud'e da sauri yanufi can .

"alokacin kuma yasmeen ta fito jikinta ajike duk kayan sun lafe ajikinta."

     Atake yaji wata sabuwar sha'awarta ,da sauri ya nufeta yarungume suna murmushi cak yadauketa suka koma bedroom dinsa ,akan bed ya azata had'e da cire mata jik'kk'un kayanta yarage dg ita sai inner wear's

"Ahankali yace baby nah bacci zamuyi ", cikin shagwaba ta ce bafa ason bacci n marece...

      Kan bed din yahaye had'e da janyota jikin sa yace hmmm my Princess bafa wancan bacci n nike nufiba,sajen dke fuskarsa taja da k'arfi har yyi yar kara ,dariya yasmeen yabata ,aiko sai darawa take shikuwa yashagala da kallonta ,be auneba yaji tana masa cakulkuli tuni yafara dariyar shima, " ahankali tace yaya inada fa lectures yau murmushi yyi yace dni da lacture din wayafi muhimmanci? Tace kaimana...rada yyi mata akunne yace wai baby miyasa bakyamun abinda nike miki kullum nike kid'ana da rawata?"ahankali tace yaya nifa kunya nikeji..cafke bakinta yyi had'e da tura mata harshensa ta cafke tana tsotsa dg bisani salon yacanxa..

     Wanda ayanxun har yasmeen ta fara sabawa da fitinar yarima ,dukda wani lokacin daurewa kawai take .

yarima be kyale yasmeen ba Saida aka fara kiran sallar magarib tukum...

Sannan sukayi wanka had'e da sallah,bayan anyi isha'i suka kwanta agajiye ko part din ammi basujeba adaren.,,,,,


      ********

Bayan sati 1 yau Yakama Saturday

Yasmeen ce tsaye agan sif din kayan yarima tana had'a masu datti danta wanke..

Yarima dke tsaye yana kallonta Wanda batamasan dashiba ,tana d'agowa dan ta d'auki kayan idanunta tsab cikin nasa ,kafeta yyi da sexy eyes dinsa ,cikin shagwaba tace shine kashigo bansani saika tsoratani ko?

Matsota yyi had'e da karb'e kayan yace ki bari kinji baby nah sarkin gd zai wankesu...

Janye jikinta tayi dg nasa fuska bbu walwala tace hmmm kamanta aikinane nifa baiwarkace kaidai salmarka ....runtse ido yarima yyi jin sunan salma danko sunanta yatsani ji Balle ita.

"Ahankali yace pls yasmeen kifahimceni ko 'a baya bansan ke bace ,kidauki abun amatsayin haka ALLAH yatsara sannan kada kisake kiran salma agabana dan natsaneta kodama can niba Santa nikeba....yatsina fuska yasmeen tayi dukda har cikin xuciyarta taji dad'in kalamansa ,amma dayake tanason nemama kanta daraja sai tace hmmm nmj kenan Ashe katseneta?ita my salmar taka dakake ikrarin zanzama baiwarta hmm dole kace haka tunda kana amfanuwa dni ainasan dama tuni katsaneni jikina kawai kakeso,atsawace yace what mekike nufi yasmeennnnn?

       " nikike gayawa haka? afusace tace eh kuma kaya nixan wanke tunda ni baiwarkace tafad'a had'e da sakin kukan kirsa ....

gaba daya ta d'agawa yarima hankali kokarin rik'eta yakeyi taki  yarda...

Kayan yadauke yafita dasu ita kuma da gudu ta nufi part din ta tana kukan jin haushin sunyi fad'a wani gefen kuma dadi takeji na yace yatsani salma damacan b sonta yakeyi,amma tarasa miyasa take jin dad'in hakan ?"


       JORDAN


Salmace tsaye ta sha shirinta cikin kananun kaya, wad'anda suka fito mata da surar jiki ,sai hada kayanta take murna fal aranta ,zaka koma Nigeria yau taga momynta da daddy nta...

Wani gefen na xuciyarta kuwa ta kudurta tana sauka Nigeria zata fara binkice akan yarima dan saitaga bayan wacce yake ikirarin ya aura dukda tasan tanason yarimane dan kudinsa,kyau,sarauta,ajinsa ,miskilancinsa,uwa uba kuma isa d hadara dan baya d'aukar raini ga mata basa gabansa shiyasa take son aurensa dan dayi tunk'aho dashi acikin k'awayenta kanta yafasu..

dawannan tunanin ta ida had'e kayanta danta gama karatunta ,fitowa tayi sunata sallama da abokan watsewarta .

"Airport ta wuce bbu bata lokaci jirgin su yatashi zuwa Nigeria....


       ******

Bangaren su yasmeen kuwa ,yarima kamar yyi kuka ko abinci bawan ALLAH yakasa ci ganin yasmeen ta botsare masa yayi mata knock yafi akirga tasharesa...


"" sai part din ammi yake sintirin xuwa kasancewar yau week end bbu office,ita kanta ammi ta fahimci kamar yanada damuwa ta tambayesa yace ah ah tace ina yasmeen dan duk yau data shigo da safe gaisheni bata sake xuwaba lfy??"ahankali yace bacci take badan ta yardaba tace to.. ""


Yasmeen ma a bangarenta hakan take ,tasan tabbas son yarima take saidai tayi alk'awarin  bazata tab'a fada masa ba inbashi ya furta mataba kuma koshidinma saita ja masa aji dan bata manceba dayace yafi karfin yasota bazai tab'a sontaba har abada..


dan Saida sukayi fadan nan tagane tagama zurmawa asonsa danko abinci takasaci gaba d'aya cikin damuwa take jitake kamar taje  tabasa hkuri amma girman kanta yahana ta..


Da dare kuwa kowannansu yaji jiki dan tun bayan dawowr yarima basu taba raba gun kwanaba sai yau, musamman yasmeen dan tasaba akirjinsa take bacci...


Awahalce bacci b'arawo yyi gaba dasu....


"" washe gari byn yasmeen ta shirya part din ammi taje ta gaidata ,bata jimaba ta fito ,adede waiting parlour na part din su suhad'u da yarima yasha wankan kananun kaya yyi masifar kyau saidai fuskar nan bbu walwala...


"Ahankali yace yasmeennnnnnnn!


cak ta tsaya ,murya kalar tausayi yace kina ganin hakan daidaine matsayina na mijinki ki watsar dani kibar ni ina watangaririya ,naci ban Ciba bakida damuwa ,yanxun daban tsaidakeba tafiya tsakiyi?


Juyowa tayi tana hawaye ta fad'a jikinsa,atare suka saki ajiyar zuciya, matseta yyi ajikinsa kamar za'a kwace masa ita ..


" Ahankali tace yaya nah kayi hkuri kaji nadena bazan koma ba ".


Shafa kanta yyi yace baby nah bana iyayin fushi yanxun dke ,kwana d'ayan nan ma adaddafe nayisa ,goge hawayenta tayi tace nima haka cikin wani yanayi yace ai yanxun mundena fad'a ko?


" d'aga kanta tayi alamar eh ".


Ji yake kamar yace mata I love u ,amma girman kansa yahana....


" Jan ta yyi sukaje sukayi break fast. "


Bayan sun idar yace baby nah muje nakaiki kiyo shopping ko?"


Tsallen murna tayi tace to yaya,muje amma mucanza kaya,bakinsa yakai a kunnanta yace nima zancanza iri d'aya zamu saka ,cikin jin dadi tace to...,,,


Part dinsa sukaje,suka canxo kasancewar yasmeen akwai kayanta acan,cikin birgewa suka fito kamar jiya basu bataba...


Dogarawa da kuyangi sai kallonsu suke cikin birgewa ,da kansa yabude mata mota tashiga gidan gaba ,yazagaya gun zaman driver yazauna dan yasanar da guards dinsa kada Wanda yabiyosu..


"Awani had'add'en shopping male sukayi parking ,yabude mata ta fito yawani rukota had'e da rike mata hand bag dinta, adede kuma lokacin driven salma zai wuce da ita kuma taga yarima shida wata  shuwa Arab dan ranta yabata ba bahausabace...


Atsawace tacewa driven yatsaya,xuge glass din motar tayi tana kallonsu har suka shige cikin male din....


" afili tace oh wato yazama mijin tace tunda harda rik'e mata hand bag."


Jiki asan yaye had'e da mummunan kudiri aranta tacewa driven muje ka kaini gd nafasa yin shopping din,dan ta tsorata da kyawun yasmeen .


Su yarima kuwa suna shiga gun ,kayan lashe lashe suka wuce yasmeen sarkin shan xaki tana dubawa..


Tush! tush !! tush !!!


Sukeji alamar Harbin bindiga ,atsorace yasmeen tajuyo had'e da rungume yarima ta baya ta kwanta r da kanta abayansa jikinta sai rawa yake sbd tsoro...


"shikuwa yarima saikara boye yasmeen yake abayansa dan yafahimci yan fashine suka shigo zasuyi fashi....


Saurin Jan yasmeenyyi,suka matsa wani dan lungu dan yaji karar shigowarsu ciki  had'e da maidata  bayansa yaboyeta ,itakuwa jikinta sai rawa yakeyi,shikuwa yarima baya ta kansa adduarsa ALLAH yatsare masa yasmeen dinsa sai yanxun yaji haushin rashin xuwansa da guards dinsa...


Yan fashinne suka shigo da bindugu fuskarsu arufe idanuwansu kawai kake gani su5 ne katti majiya k'arfi.


" gun cashier suka nufa su ka Lodi kud'i son ransu ,suna niyar fita cikin rashin sa'a idanun ogansu yasauka kan yasmeen atake ya kwad'aita da ita...."


Yarima dke duke gaban yasmeen yajuyo dan ganin ko suntafi ,kawai yaga dan dashi daya ya nufo su yakure yasmeen da ido.


,,,wani mummunan fad'uwar gaba yaji,be auneba yaga  dan rashin na kokarin fisgo yasmeen dke bayansa...cikin rashin tsoro yarima ya mike afusace cikin isa yace lfy mlm kake kokarin rik'emun mata?


Cikin isa dan rashin yace Repin dinta zanyi,kafin yarima yace wani abu yan dashi biyu sun rurruk'esa ,ogan yaja yasmeen dke kuka tana kiran yarima ta...


Agun ya kwantar da ita yana k'okarin cire belt dinsa..


yarima cikin wani karfi da yazo masa yafisge dg gun su da gudu yyi wani tsalle had'e da saka gwiwarsa yadaki gaban dan fashin iya k'arfinsa...


Wata razananniyar k'ara dan fashin yasaki had'e da dafe gun yana cewa ya nakasani...


Yasmeen kuwa tayi mamakin jarumta da Saida ransa da yarima yyi agun wad'an nan marasa imanin..bats auneba yaji yarima yyi ka'ra sakamakon harbinsa dasukayi a k'afarsa ta dama da gudu yasmeen ta fada jikinsa tana jijjigasa tana kuka kamar ranta zai fita dan tasan dalilinta akayi masa haka...


Adede lokacin kuma..


Share pls


NIDA D'ALIBATA

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


Dedicate to all my fan's ana mugun tare,yan nida dalibata grp fan's 3 comments dinku na yau yafi nakowa ina mugun jidaku irin sosai dinnan.😍😍


65&66


Suna shiga sir Aliyu yyi sallama suka sami mommy da sa ada zaune ,sai Mubarak yyan zakiy ya abbansa ya aiko sa gun daddy nsu sir Aliyu,yasami daddy baya k'asarm a. Cikin fara'a mom my ta amsa sallam mar,kafin ta sake mgna taga wata kyakkyawar yarinya  na bayan sir Aliyu.


" murmushi mommy ta yi tace bakuwa mukayi."


Aida gudu sa'ada tazo tayi hugging din Hafsat tana dariya had'e da cewa oyoyo my friend.


Shikuwa Mubarak mutuwar zaune yyi ganin wannan sura ta Hafsat me d'aukar hankali.


Sa'ada ta kalli mommy ta ce mommy wannan ce Hafsat.


Da sauri Hafsat ta xube k'asa tana gaida mommy, ta amsa cikin sakin fuska had'e da k'ura ma Hafsat ido tana tuna kamar tasanta ko wani me kama da ita.


"""" shikuma sir Aliyu zama yyi gefen kujera yana me jin Dad'in yadda Hafsat ta girma ma mahaiyarsa,kuma itama mommy ta karbeta da hannu biyu.gefen da Mubarak yake ya kallah dan sai yanzun yalura da shima.kawai yaga yak'ure Hafsat da ido yana mata kallon k'urullah.wani mugun tsaki sir Aliyu yaja Wanda besan lokacin dayayisa ba,hakan yadawo da Mubarak haiyacinsa yadena kallon Hafsat cikin in ina yace yaya barka dah dah ....dare ina wuni? Wani kallo sir Aliyu yyi masa atak'aice yace lfy,na n Mubarak ya kalli mommy yace natafi mommy ,zan sanar da abban daddyn bayanan,nan mommy ta ce ok kagaida yan gidan,nan yafita sum sum.""";;


"Mommy takalli sa'ada tace bazaki kawowa bakuwar komai ba?"


da sauri tace ah ah mommy yanzun zankawomata drinks.


Mommy ta ce oh Hafsat kisaki jikinki kinji nan gidankune naga sai kunya kkeji,sir Aliyu yace hmm mommy haka takefa,yanxunma wai kunya takeji bazatazoba.murmushi mommy ta yi har cikin zuciyarta taji kaunar Hafsat dan ta lura yarinyar Nada tarbiyya da kunya had'e da kawaici,kallon sa'ada tayi tace Auta kuje da Hafsat d'akinki ta huta saikuzo muyi lunch ,nan sa'ada ta ce to takama hannun Hafsat suka mik'e koda zasu wuce saida Hafsat ta saci kallon sir Aliyu aiko shima yasaci kallonta suka had'a ido yakashe mata ido daya had'e da wani killer smile. Abinda basu saniba duk mommy na lura dasu,kuma tagane sir Aliyu da Hafsat suna son junansu, dalilin dayasa tace su Hafsat sukoma dakin sa'ada dan ta tambayesa meke tsakaninsa da Hafsat dan tana kwad'aita masa au  ren ta,co's yarinyar Nada kamun kai.


"Bayan su sa'ada sunbar gun mommy ta kalli sir Aliyu tace babana meke tsakaninka da wannan yarinyar kuma wacece ita??"


"Ahankali sir Aliyu yy gyaran murya yafara bawa mommy labarin Hafsat tun daga farko har yanzun da dalilin dayasa yakawota gidan ."


Be auneba yaga mommy na hawaye sbd tsabar tausayin Hafsat.


""""" ahankali tace insha Allah za'aga mahaifiyarta,kuma Laure aniyarta zata bita gara da kakawota nan sai ta zauna har babanta yadawo.sir Aliyu yace eh mommy Ai ankusa ma komawa Hutu dan yau saura8days sukoma,mommy tace allah yakaimu lfy,Amma babana kuna soyayya da Hafsat ko? da sauri yad'an zaro ido yace haba dai mommy d'alibata ce fa! Allah yakiyaye,nibanma San yaso yakeba.

    Murmushi kawai mommy ta yi batace komaiba dan ta lura sir Aliyu besan yafad'a tarkon so bane shiyasa yake haka ,Amma zata saka masa ido taga iya gudunsa.kallonta sir Aliyu yyi yace mommy bari naje Nayi wanka!ok kawai tace,amamakinta saitaga yanufi part din sa'ada."""


"da sauri tace baban a kaida zakayi wanka ina kuma zaka?


Waigowa yyi yana d'an Sosa k'eya yace am am dama..dama zansanar da Hafsat zanshiga ciki kada tajini shiru tayita nemana,ko tayi kuk...saurin yin shiru yyi dan yana Neman yin subutar baki.mommy data guntse dariyar datazo mata tace ai baza nemekaba tunda sunsaba da sa'ada.bece komaiba sum sum yy part dinsa.


************

Bangane sa'ada da Hafsat kuwa ,sun baje kan gadon sa'ada suna fira abinsu can sa'a taje ta had'a ma Hafsat ruwan wanka tace sis jekiyi wanka.

Bayan ta fito sa'ada ta fito mata da black arebian gown tasaka,wow sai Hafsat ta yi kamar balarabiya,sa'ada sai wasata take hade da kod'a kyawun datayi take.can sa'ada tace naso ace daddy na yana gari kikazo wlh dan inabashi labarin inada k'awa Hafsat.murmushi Hafsat ta yi tace Allah sarki, Dede nan mommy ta shigo tace yarana kuxo muje muyi lunch, ta kalli Hafsat hade da kama hannun ta tace y'ata kidena jin kunya ta kinji ki daukeni tamkar mamanki kinjiko?


" ahankali Hafsat ta ce to."


Nan suka fito suka nufi dining area, a can suka sami sir Aliyu yasha kananun kaya ,kyawunsa da kamalarsa sunsake bayyana atare dashi.


Murmushi yyi ya kalli mommy yace oh mommy naga baki wani damu dani ba yasu Hafsat da sa'ada kawai kike.


Murmushi mommy ta yi tace eh ta y'ayana nike mana,kai ai kazama tsohon yyi,sa'ada da Hafsat suka yi dariya atare,murtuke fuska sir Aliyu yyi yace kai ina wasa dakune wlh innarike yarinya hmm zata gaya masu,Hafsat ta faki idonsu mommy ta yi wa sir Aliyu gwalo,kallonta yyi yanuna kansa wai dashi take ?d'aga kanta tayi alamar eh, kwafa yyi yamata alamar zai kamatane.


Duk abinda suke mommy na lura dasu tadai sharene.


Nan suka zauna sa'ada tayi serving dinsu,suka fara cin abinci ,Hafsat naci akunyace .


Sir Aliyu ne yak'ara turakafarsa k'ark'ashin table din ,kasancewar suna pessing juna da Hafsat yatake mata k'afa da k'afarsa mai takalmi sawu ciki.


Wani mugun zafi taji,har zata fasa ihu ta tuna inda take  sai tayi shiru tad'an rintse ido alamar tanajin zafi.shikuwa sir Aliyu murmushin mugunta kawai yake ,yana satar kallon Hafsat,ita kuwa ta d'auka wani abu ne yadatse mata k'afa ganin  sir Aliyu yana murmushi kuma ita yake kallo yasa tagane shine.fakar idonsu mommy ta yi ta galla masa harara,kara take k'afar yyi,da ido take basa hakuri,sai can dayaga dama ya janye kafarsa,itakuwa ta murgud'a masa baki had'e da harararsa, ta had'e k'afafunta yadda bazai sake take mata suna .nan Hafsat ta ce ta koshi sir Aliyu yace aidama mommy haka take batason cin abincin sosai, murmushi mommy ta yi tace kiladai bakunta take mana. nan sa'ada ta ce ita ta koshi ,taja Hafsat sukabar gun.


"Shima sir Aliyu yatashi yatafi masjid."


___________________ Zakiyya ce zaune kan bed adakinta tanajin wak'ar music awayarta.


Mubarak yashigo yazauna kan bed side,yakalleta yace sis yasu nan yarinyar da kikaga yaya ALiyu da ita a shopping males?


"da mamaki Zakiyya ta kallesa tace lfy yaya?'


Murmushi yyi yace ki amsamun tambaya ta.


Zakiyya tace sunanta Hafsat!


Mubarak yace to naganta da yaya aliyu yau agidansu yaje da ita!, kutumar uba zakiyya ta fad'a cikin karaji,murmushi Mubarak yyi yace minene abun tada jijiyar wuya ,ni yarinyar tamun wlh danko bansame taba inason inhuta da ita dan kalar skin d'inta yamun,saidai inatsoron yaya Aliyu wlh dan naga kamar sonta yake.


Wata muguwar dariya irinta basawa Zakiyya tayi tace naji Dadi data maka dan nadau ki alk'awrin kota halin kak'a saina auri yya Aliyu.


" kabarmin komai zanbincike akanta ."


Mubarak yace to shikenan dan ni inzan aureta inaso inkuma bazan auretaba inason in lashi zumarta.


Wani mugun murmushi Zakiyya tayi tace kada  kadamu ko satota sai muyi ko mu nunawa iyayanta kudi su aura maka ita.


"Dan ina tunanin yar talakawa ce."


Nan Mubarak yace to shikenan yafita.


Da misalin 8:00pm sir Aliyu yashigo parlourn gidansu yasami sa'ada zaune a parlour ,yace ina mommy da Hafsat?


Sa'ada ta ce mommy na d'aki sallah take ,itakuma Hafsat ta na d'akina tana game.


Da sauri sir Aliyu yanufi dakin,yana shiga yasami Hafsat ta na game tana dariya ,kawai tagansa kamar daga sama.


Kusa da ita ya zauna ya kalleta yace wana kama?


Shiru tayi tana zare ido,can tace to bakaine kayita takemun k'afaba.


Murmushi yyi yace hmm saina gyaramiki wannan bakin da kike turowa.


"Ahankali tace yauwa yaya kiramun baban mu gaisa saika bani inyi game da wayarka.


Kallonta yyi yace bazan kiraba.


Aisaita hau kukan shagwaba harda dire dire ita sai yakira mata babanta.


Sir Aliyu kuwa lumshe idanunsa yyi ,azuciyarsa yanace wa yah salam sakamakon wani abu dayakeji ganin yadda Hafsat ke Wannan shagwaba r dan yalura akwai kuruciya da ita.


Share pls

NIDA DA'LIBATA

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿67&68


"""" Ahankali Hafsat ta ce bara naje nafad'awa mommy kak'i kiramun baban a."bud'e idonsa yyi yace hmm aibazaki iyaba ,abinda kunya r momin kike,marairaicewa tayi tana lallab'a sa sannan yakira baba n,Hafsat tayi mama kin yadda sir Aliyu ya saba da babanta ganin yadda suke fira dashi.

Sir Aliyu ya mik'a mata wayar yafita nan Hafsat suka sha fira da baba yyita mata nasiha tayi hakuri da rayuwa kuma ta rik'e mutuncinta.sannan sukayi sallama,tafit o dg dakin dan kaiwa sir Aliyu wayarsa."";;


A parlour tasamesu harda mommy, nan taje ta mik'ama sir Aliyu wayarsa sai kallonta yake da idanunsa dasuka canja kala.


Mommy ce tace suje ayi deener,Hafsat tace ta koshi,wani kallo sir Aliyu yabita dashi yace mekika ci da har kika k'oshi?


Sunkuyadda kanta tayi tace nasha fura gun sa'ada ai.


Girgiza kansa yyi yace banyarda fura zata k'osar dakeba oya muje kici abinci.


Murmushi mommy ta yi tana kallonsu cikin birgewada sha'awarsu ,tace kai babana kacika takura dole sai taci aboncinne?kallon Hafsat ta yi tace y'a ta zakici ko kin koshi?Hafsat ta saci kallon sir Aliyu taga yyimata alamar intace ta koshi in yakamata zata gayamusu ai da sauri tace eh mommy zanci!murmushi mommy ta yi danta lura da abinda  sir Aliyu  yanuna wa Hafsat. Dining area suka nufa,bayan sun zauna mommy ta yi serving in kowa,harsuka gama sannan ,sukayi sallama kowa yawuce makwancinsa.


Washe gari da misalin karfe 6:30am ,Hafsat ce ta fito da ga d'akin sa'ada,kasancewar bayan sun idar da sallah sa'ada ta koma bacci.itakuma ta kasa komawa Dan tasaba agidnsu da anyi sallar asuba Laure zatayi ta sakata aiki,zai zirga xirga take bata waiting parlour bata part din sa'ada,gash I tanason ganin sir Aliyu, kuma batasan inda yakeba,mommy dake part dinta taji motsin yyi yawa ta fito ta sami Hafsat zaune kan carpet ta yi shiru.


"Ahankali mommy ta ce y'ata yaya dai?"


Da sauri Hafsat ta gaida,ita ta amsa fuska cike da walwala,kan kujera mommy ta zauna ta ce zonan kinji,ba musu Hafsat ta je ,hannunta mommy ta kama ta zaunar da ita kusa da ita.tace kifad'amun mekkso?inde kin d'aukeni mamanki kinji?


"Ahankali Hafsat ta ce ina yaya yake banganshiba?"


Murmushi mommy ta yi tace, yana part dinsa ,k'ila bacci yake,amma ai lokacin motsa jikinsa yyi ,yanzun kingansa yazo,inkuma xakije ga kwana can inkikabi har part dinsa sai kije.


Da sauri Hafsat tace ah ah mommy basai najeba.


Murmushi mommy ta yi, dan tasan da k'yar taje,dan talura yarinyar akwai tarbiyya da kamun kai.


"Can kuma Hafsat ta mik'e tace mommy na tafi gun sa'ada!mommy tace to y'ata,nan ta nufi dakin,kafin ta ida isa taji kamshin turaren sa da sauri ta juya sukayi4eyes dashi yana sanye da kayan motsa jiki  wani killer smile yasakar mata ,itama tayimasa.


" murya k'asa k'asa yace my Hafsat kintashi lfy ?"


Turo baki tayi tace lfy had'e da duk'awa ta gaida shi  murmushi yyi ya amsa tare da cewa sarkin rigima to menene kike wani tura baki gayamun kinji?


"Ahankali tace bakaibane bangankaba sai yanzun."


Kallon ta yyi yace to sorry ina part dina ai yanzun gani ,mujema kirakani gun exersic . mak'e kafada tayi alamar ah ah bazata jeba.murmushi yyi yace shikenan zamu bata kuwa.....muryar mommy yaji tana cewa Auta sai yanzun kika tashi har Hafsat ta rigaki tashi,wata irin kunya sir Aliyu yaji,itakuwa Hafsat bata juyaba da gudu  ta shige dakin sa'ada, shima ko kallon mommy be iyaba sum sum ya wuce.


Ita kuwa mommy murmushi tayi ,axuciyarta tace allah yasa kunada rabon mallakar juna ,dan daga gani Hafsat saita canja maka ak'ida,gashi dama bakason raini ita kuma tana girmamaka ,ko dazata gaidashi saida ta duk'a fg ita harshi sun manta da ina gun ,amma zan cigaba da adduah allah yazaba abinda yafi alkhairi.


Bayan su Hafsat da sa'ada sunyi wanka ,sukayi break fast Wanda sir Aliyu be zoba  dan yanajin nauyin mommy sai dai  sadik , shikuwa kabeer yana skul. Nan sa'ada taja Fatima suka wuce islamiyarsu.


"Sir Aliyu da ke bed room dinsa yaga fitarsu ta window."


Basu jima da fitaba yaji k'arar anbude get ,da sauri yaduba yaga ko sadiq zai fita da mota dan anhanasa fita da mota yyi karanta aceawar sir Aliyu. Kawai saiyaga motar Mubarak yyi parking ,hakanan sir Aliyu yaji wani mugun fad'uwar gaba, yajikuma be yadda da zuwan Mubarak ba dan yasan dagashi har Zakiyya basa zuwa gidansu saida dalili,be auneba yaga sun fito mota tare da Zakiyya, nan yasake mamaki,amma sai yasake bude labulan windon dan yagansu sosai ,amamakinsa sai yaga sun nufo setin windon dayake da sauri yasaki labulen windon,har zai juya yakoma kan bed sai yaji muryarsu suna magana k'asa k'asa.


"da sauri yatsaya yafara sauraransu."


Ji yyi Mubarak yace kin gane sis inkinje ki nuna kinzo musu yini ne ,Nina kawoki zanzo na d'aukeki .

Kinsan sa'ada fa surutu sai kibigi ciki nta kiji inane anguwarsu da kuma iyayanta,kinga in talakawane ta kwana gidan sauki,sai muje muyi musu b'arin kudi ,kin gane? Wata yar dariya Zakiyya tayi tace babu damuwa Allah yasa zan iya dan mugun haushi suke bani daga Hafsat din har sa'adar.


"Ahankali Mubarak yace kinga inmun sami information akanta shikenan, sai mubita gidansu dg nan inta yarda zata aureni ba matsala."


Inkuma tak'i kawai sai insaka asatomun ita nabiya buk'atata da ita.


Dariyar mugunta Zakiyya tayi tace kaga ko yaya aliyu ya aureta bazata yi daraja gunsaba tunda abud'e zai sameta,ballema bazan bari ya auretaba.


"""" mutuwar tsaye sir Aliyu yyi agun ,sai wata irin zufa ke keto masa,innalillahi wa inna ilaihir raju un kawai yake maimai tawa,had'e da jin wani fad'uwar gaba da b'acin rai,Atake idanunsa sukayi jajir suka k'ank'ance,da sauri yaja glass din windown.


Arazane Zakiyya da Mubarak suka juyo sukayi 4eyes da sir Aliyu.


Ai take yan hanjin cikin Mubarak suka kulle dan tsabar firgita yatsorata da yadda yaga idanun sir Aliyu.


Ita ma Zakiyya ta tsorata sosai musammun data lura da sir Aliyu yaji duk firarsu da sukayi.


Basu auneba sukaga sir Aliyu baya bakin window din,arazane Mubarak yace muje mukoma mota wlh zagayowa zaiyi ,kinsan kuwa mukayi arba dashi kashina ya bushe asukwane suka nufi gun da suka yi parking.


Adede nan kuma Hafsat da sa,ada suka turo get suka shigo ciki.


Sir Aliyu kuwa da sauri yafito dg part dinsa, zai nufi k'ofar fita parlour n, da sauri mommy ta tsaidashi ganin yanayinsa dan tasan ba lfy.


Da sauri tace ina zakaje ne haka ranka bace?


Cikin damuwa yace pls mommy kibarni naje kada su gudu .


Mommy ta ce su wanene? Da sauri yace Mubarak da Zakiyya,kara su cutarmun da Hafsat mommy ki barni naje dan Allah yafad'a kamar zai yi kuka.


Cikin mamaki mommy ta basa hanya ya futa afusace kamar zai tashi sama.


Ya fita ya hango har get man yabud'e masu get zasu fita, da gudu yakoma ciki ya dauko key din motarsa ya fito mommy na tambayarsa ina zaije be kulataba ya fito asukwane.


Parking spaces yawuce,nan yahango su Hafsat zasu shiga ciki,da sauri yashige motar yabata wuta.


Dan yyi alk'awarin ko gaban abbansune karshe kenan sai yakoya musu ahankali.


Da mugun gudu ya isa gidansu Zakiyya,a parking spaces yaga motar Mubarak da alama suna ciki shida Zakiyya.


Azuciye yafito dg motarsa yyi cikin gidan afusace....



Share pls

NIDA D'ALIBATA

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿69&70


Ko sallama bbu ya afka cikin parlourn fuska ba annuri.yas amesu zaune a parlourn Mubarak yana shan lemo,ai yana ganin sir Aliyu yasaki cup d'in lemo n had'e da mik'ewa tsaye yana tari sbd k'warewar da yyi.

Shikuwa sir Aliyu gu n mubarak yyi gadan gadan,mommy na ganin haka afusace tace kai lfy zakashigo min gd bako sallama? Ko gun datake sir Aliyu be kallaba ,fisgo Mubarak kawai yyi yafara basa kyawawan maruka masu rai da lfy Atake Mubarak yasaki ihu had'e da cewa mommy ki ceceni dan Allah. Ita kuwa mominsu tsinewa sir Aliyu kawai take yi had'e da aibatasa.shikuwa ko ajikinsa,dukan Mubarak kawai yake yana cewa dakaji dukan dnayi maka a farko dabakayi yink'urin abinda kayi yanxunba ,bedena suburbudarsaba sai da yakumbura masa fuska tukum .sannan yanunasa da yatsa yace wlh wlh wlh duk abinda yasami Hafsat Kaine da Zakiyya dan wlh zan aje yan uwantaka gefe Nayi muku hukunci da abinda kuka aikata,ai inkacika tantiri basai kasaka asato maka ita ba kabiya bukatarka da itaba ah ah har gidansu zakaje  da kanka gaban kowa saika d'aukota ammafa in zaka iya.


Ita kuwa Zakiyya part dinta ta gudu ta rufe.


Koda sir Aliyu yajuya yaga bbu ita yasan guduwa tayi.


Cikin masifa mommy ta ce wlh saina dau mataki akanka dan kafi k'arfinsa saika rik'a zalintarsa ,kuma akan wata banzar mace ma .


"Ahankali sir Aliyu yakalleta yace mommy ina ganin girmanki kidena zagina haka,yaradai k'annena ne kuma na isa dasu insunyi laifi na hukuntasu. "


Wani tsaki taja tace wlh z....muryar abbansu Zakiyya taji yana cewa kincuceni Hajara kin b'atamun tarbiyyar yara gaba d'aya kuma Nayi duk abinda Aliyu yafad'a kinaji yace zaisa asato masa yarinya ya aikata masha'a da ita amma bazakiga laifinsaba,saikirik'a zagin Aliyu.cikin b'acin rai Abba yakalli sir Aliyu da kansa ke duke yace inaso kaje d'akin Zakiyya kazanemun ita,umarni na baka yafad'a had'e da mik'a masa wasu keys yace kabud'e dakin inta rufe.


"Da sauri sir Aliyu ya karba dan dama haka yake so dukda bayason dukan mace amma yaci ace Zakiyya jikinta yagayama ta."


Ita kuwa mommy ba bakin magana dan ta lura Abba ransa b'ace  yake.


"Bayan sir Aliyu yanufi dakin Zakiyya," Abba yakalli mommy yace hukuncinki zai biyo baya ai naga sadda aliyun yashigo gidan nikuma dawowata kenan nabiyo sa natsaya bayan labile naji koma.


Wata harara yaaikaea Mubarak dake kwance da k'asa da kumburarrar fuska yace Allah yashiryeka yafad'a had'e da barin parlourn.


""" sir Aliyu kuwa bude d'akin Zakiyya yyi yasameta kwance da earpiece akunnabta,saidai tagansa kamar dg sama beyi wata wataba ya zare belt d'in dake k'ugunsa yashiga jibgarta tana ihu hade da basa hkuri be k'yaletaba saida ta daku,sannan ya kalleta had'e da nunata da yatsa yace inaso kisani duk abinda yafaru da Hafsat kune kuma bazan taba k'yalekuba,sannan kince saikin aureniko?to bari kiji da in aureki gwara na tabbata bbu aure har k'arshen rayuwata.yafad'a tareda da Jan doguwar tsuka yabar parlon.""";;


Yaje yadauki motarsa yabar gidan.


Ko a hanya tunani yake azuciyarsa yace meyasa masa keson keta mata haddi ne?


Ko wanne gaja yanason b'ata mata rayuwa,wata zuciyar race sbd tana da kyawu had'e da k'ira me daukar hankali.


Wani mugun tsaki yaja ,koda ya isa gd straight part dinsa yanufa be kulasu sa'ada dake zaune parlour itada Hafsat suna firaba.


Mommy ce ta tashi tabisa d'akinsa dan ta lura yana cikin damuwa har yanzun.


Ta samesa kwance rigingine yyi tagumi yak'urawa seeling ido yana tunani.


Da sauri ta karasa gunsa ta hau tambayar lfy me yafaru dazu kuma me su Zakiyya suka masa??


Cikin damuwa ya zaiyane mata abinda yafaru,salati kawai mommy keyi tace lallai yarinyar da aka bamu amana suke shirin aikata hakan akanta,amma ai alhmdllh tunda Allah yatoni azirinsu.


"Amma bbna kayi hkuri kaje kayi break fast ."


"Ahankali yace na k'arya awaje na koshi ,yafad'a had'e da rufe idanunsa."


Fitowa mommy ta yi, ta isa kusada Hafsat ,ahankali ta dafata tace y'ata kije gun yayanku yana cikin damuwa ki lallab'asa ,sannan kixo kikai masa kayan break dinsa dan beyi break ba dan naga kunshak'u dashi kinji ko?


"To Hafsat ta ce ta tashi tanufi dakinsa."


Tana shiga tasamesa kwance idonsa arufe ,sallama tayi ta zauna nesa dashi,murya k'asa k'asa tace yaya shine na shigo d'akinka ka shareni?


Bud'e idanunsa yyi yana kallonta,ta sunkuyadda da kanta k'asa.


Cikin shagwaba ta ce yaya natafi tunda kak'imun magana ka shareni,ahankali yace ni ban sharekiba.


Murmushi tayi tace hmm hakane ,amma kasan kamun alkawarin dena saurin fushi amma naga kamar fushi kke yanzun badai nice Nayi laifinba ko?ta fad'a had'e da langabe kai tana kama kunnanta.


Besan sadda yyi dariyaba,yace my Hafsat bake bace kuma yanzun naji na huce nabar fushin murmushi tayi tace eh hakane amma meyasa bakazo mukayi break tareba ?


"Shiru yyi tanatunanin me zai ce mata?"


Can yace banajin yunwa,ai turo baki tayi race amma ni jiya ka tursasani saida naci abinci to yanzun zan kawomaka break kayi dan bakayi break ba nikuma banason yunwa takamamun kai ko?


Ai sai yyi kamar wani dolo dan besan sadda yace to kawomun my Hafsat innaci zakiyi farinciki?


Da sauri tace eh hade da fits.ba jimawa tadawo da plate chips ne aciki da cup din tea mai kauri ta aje masa gabansa.


Tace yauwa Yayana kacigaba da ci kaji ba musu yafara cin abincin sa tana masa fira har ya cinye komai Ta's,cikin jindadi tace yauwa ko kaifa.


Murmushi yyi yace gobe bayan sallar axahar zanmaidake gd dan lokacin baba yadawo ,dan munyi waya dashi dazun.


Murna sosai Hafsat ta hau yi,had'e rai sir Aliyu yyi yace wato ke murna ma kike ko bazakiyi missing dinaba kinfiso mu rabu?


Shagwabewa tayi tace Allah Yayana bahaka bane ,ai naga saura 6days mukoma skul kuma zan ganka a can shiya sa.


Shiru yyi bece komai ba.


Fita tayi takai dan kai plate din da cup din waje,koda mommy ta ganta taji Dadi sosai aranta dama tasan sir Aliyu bazaima Hafsat musuba kuma tasan yanzun yahuce daga Fushun da yake,sai murmushi mommy  keyi tanasa ma hafsat albarka.


Bayan ta kai kayan kitchen tadawo dakin tasamesa yana latsa waya gefensa ta zauna cikin shagwaba ta ce yayaaaaa!


Kallonta yyi da sauri yace my Hafsat yar rigimata kimun firanki kinji?


Tashi tayi tace barama nagyaramaka dakinka amma saika fita.


Murmushi yyi yafita ,cikin yan mintoci ta gyare dakin parlour da bed room.


Sannan ta koma toilet ta wanke shi Ta's,harzata fita taga fararen vest dinsa da jallabiyoyi guda biyu ajik'e a bucket, bbu bata lokaci ta duba taga bbu boxes aciki ,saita wankesu Ta's ta shanyasu a toilet din ta had'a masa ruwan wanka ta fito da ga toilet din .


Tana fitowa ,yanashigowa kallonsa tayi tace yaya kaje kayi wanka kaji?


Murmushi yyi yace to my Hafsat yaude anaji dani sosai.


Murmushi tayi ta fito,shikuma ya shige toilet.


Wani farin ciki yaji aransa,yaji Hafsat ta sake samun.matsayi me girma agunsa.


Yaji Dadi sosai da yadda yaga ta wanke masa kayansa sai murmushi yake har yagama wankan ya fito.


Bayan ya shirya ya fito cikin farin ciki dan yanason xuwa campaninsa,yaga ba kowa a parlour ,motsinsu yaji a kitchen can yanufa.


Yasami du Hafsat itada sa'ada suna aikii.


Murmushi yasakarma Hafsat ya ce sannunku da aiki, murmushin itama Hafsat ta yi masa tace yaya sai ina?


Ahankali yace  zan je office muje kirakini mota kimun addua.


Sa'ada tace haba yaya saita wani rak.... Hararar da ya aiko mata yasa tayi shiru.


Hafsat kuwa ba kunya ta bisa har parking spaces yayi masa adduar da yabukata ta dawo cikin gidan.


Washe gari....


Share plsNIDA D'ALIBATA

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿71&72


Washe gari.

Bayan sallah azahar sir Aliyu ne tsaye a waiting parlourn gidansu yana kallon Hafsat sun rungume  juna da sa'ada suna ban kwana,Hafsat kamar tayi kuka sbd sabon datayi agidan dakuma batasan rabuwa da sa'ada.

    Mommy ce tazo taja hannun Hafsat tasaka mata wata babbar Leda ahannunta ,hafsat zatayi magana mommy ta rufe mata baki,takalli sir Aliyu dake tsaye yana aikin kallonsu. Tace babana kuje dan Allah ka lallab'ata kaji?


"Yatsina fuska yyi yace haba mommy lallabata d'in me zanyi,ya kalli Hafsat yace oya muje."


"Turo baki tayi tabi bayansa."


Ya shige mota yabarta ,yak'i bud'e mata ,itakuma tak'i shiga sbd yasaba shike bud'e mata duk in zata shiga motarsa.


Shikuwa yana sane yyi hakan Dan yaji haushin yadda ta nuna damuwa kan zata rabu da sa'ada amma shi bata damu dan zasu rabuba.jin shirun yyi yawa yasa yafito ya kalleta fuska daure yace wai bazaki shi ga bane kome kkejira?

Kauda kanta tayi gefe tace cikin shagwaba tonika  bud'e mun nashi ga. Kallonta yyi yace keko kin rainani kwa nannan ko? batace komaiba can yabud'e mata sannan ta shiga yaja motar ,saida yabiya yasiya mata su ice cream da ga sassun kaji dasu biscuits da chacoolat,sannan suka wuce anguwarsu.


Bayan yyi parking da sauri ta kai hannunta dan bude k'ofar ta jita yasa lock,shiru tayi dan dama tunda suka shiga motar batayi masa magana dan zama da shi yasa takoyi miskilanci.


Kallonta yyi murya k'asa k'asa yace wato dan zakiga baba ki koma gunsa shine kikemun haka ko?


Mu hadu zuwa anjima

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Banida bakin gdiiya ga dukkan masoya wannan novel saidai addua agareku da fatan alkhairi ,ALLAH yabar kauna..love u all💋💋🌹


🅿71&72


Bayan sallar isha 'I yarima na toilet ,Maryam d salim suka shigo tare,bayan sungaisa dayiwa yasmeen ya mai jiki.

      "Ahankali yasmeen tace Ku ina fushi daku sosai saima yanxun kuka gadamar xuwa dubamin mijina Baku damu da shiba ko?

Maryam tace sorry Anty wlh kinsan muna islamiyya tun safe sai magrib muna dawowa mommy ta sanardamu shine nacewa yaya salim mu shirya mutafi....salim yyi saurin cewa waye yayan Anty Maryam?

dariya sukayi naki d'aya ,yasmeen tace oh ALLAH yashiryaku yaran nan ke kuma duk inda zaki yana biye dke kamar jela.murmushi salim yyi yace a skul ma twins ake cemana .

" yasmeen tace hmm intayi aure dole ka rabu da ita, hade rai salim yyi yace eh to amma ai can gidanta zan koma Anty...yasmeen tace sai kasaka niya ai..Maryam tayi saurin cewa wai Anty wannan yah Omar din dayazo gida rannan ana yake karatu?"

Yasmeen batayi tunanin komaiba tace ah ah ah yana kasar waye,barima nakirasa nafada masa my Prince bayajin dadi..

Maryam kuwa kuri tayi da ido tana tuna kyakkyawar surar yah Omar.

Yasmeen kuwa tana kira yashiga yadaga tace hellow yah Omar ina wuni dan acan marece ne ,yace lfy lau babyn yarima ..

dariya tayi tace hakama zakace ko?yace eh mana dama inason tambayarki wacece wannan yar farar yarinyar dana samu  a part din Ku rannan danaje gidanki?

Murmushi tayi tace oh wai Maryam kanwar my Prince ce....shiru Maryam tayi tana kallon yasmeen azuciyarta tana adduar ALLAH yasa yace sonta yake sbd tunda ta ganshi takasa sukuni...

Yah Omar yace oh to nahakura tafi karfina ni talakkane dariya yasmeen tayi ganin g Maryam agurin saitace mayi maganar da ma my Prince ne bbu lfy nan ta sanar dashi ,salati yyi hade da yima ta jaje yace zai kira yariman...

Adede nan yarima yafito dg toilet din ,su Maryam suka gaodashi dayimasa jaje ya amsa fuska asake bbu kunya ya zauna kusa da yasmeen hade da rike mata hannu yace  baby keda waye kike surutu?


"Tace yah Omar ne".


Yace zai kira ka anjima ,ok to shikenan.


Salim yakalli Maryam yace Anty Maryam muje ko ..harara yarima ya aiko masa yace oh yaronnan kazama nah mata ko ko ina tasaka k'afa kana manne da ita ai bari ba wannan year din zakayi  SSCE ba  Cairo zansaka Abba yakaika duk ahuta da wannan shigewar dakake mata...salim kamar yyi kuka shida Maryam sai hkuri suke bawa yarima,yyi musu banxa hade dayin kwanciyarsa kan cinyar yasmeen....


Ita kuwa yasmeen sai dariya take musu tsaki  yarima yyi yace dallah malamai kutafi kuncikamun kunne da surutun Ku,asannan yasmeen tayi mgn tace kada kudamu kunji kuna tare ,basuce komaiba suka fita sum sum sum.


" yasmeen ta shafa kan yarima tace oh my Prince kasaka ma yarannan ido ko?"


Murmushi yyi yace baby yarannan akwaisu da ban haushi ji dan ALLAH sai wani manne mata yake da ace kamar ba iyaye daya bane sai ya aureta...


Yasmeen tace to ba   kaninta bne."


Yace shekara fa 1 ne yabata ,yace yab ni gsky bazan iya auren K'ANINA ba (littafi na mai fitowa)


Kafin yarima yyi mgn Anty lubnah da hanan dsu munib d muneeba sun shigo room din.


Sai wani yatsina da yan harare harare Anty lubna keyi hade da cin magani.


Munib d muneeba kuwa gefen yasmeen suka tsaya suna mata surutu da gaida ita kota yarima basayi..


Bayan sun gama gaisawa da yarima ,Wanda ke mamakin yaushe twins sukasan yasmeen har sukayi irin wannan shakuwar?


Hanan ta kalli yasmeen tace Anty ina wuni yamai jikin?


Murmushi yasmeen tayi tace inayini mmn twins me jiki yasami sauki.


Hanan tace to Ku sarakan surutu bakuga uncle dinba saita antynku kuke..


"Yasmeen ta kalli lubnah tace Anty ina wuni,kamar adole atakure tace lfy hade da cewa hanan ke sarkin shishshigi kisameni waje gunsu ammi tana fadin hakan fuuuuuuuu ta fice.. ,,,


girgiza kai hanan tayi tace Anty bara muje gunsu ammi ,yasmeen tace to abarmin twins dina nan ,yar dariya hanan tayi ta fice..


Asanman yarima yad'aga cinyar yasmeen yaka kallen yanayin fuskarta kota damu da Anty  lubna,saiya bbu alamar komai,saima surutu suke d twins.


" Ahankali yace oh to tunda baza kuyimun mgn ba zandena muku shopping. "


Tsalle sukayi hade da cewa ai ko bakayi manaba Anty tana yimana kota aika mana dashi a gd ,kumafa har karatu ta koyaana tace bbu kyau yin zagi ko k'arya ,kuma maijin maganar iyayansa d'an aljannane ko Anty?


Yarima shiru yyi hade da yimusu kuri d ido yanajin dad'in auren yasmeen dayayi arayuwarsa tabbas yasmeenace ce ta gari ,yasan yaransa zasu sami tarbiyya mai kyau agunta ,wani sonta d kaunarta suka sake mamaye masa zuciya.


Sai dai wani gefen na xuciyarsa yana mamakin dalilin dayasa Anty lubna batasan yasmeen ,yasan yasmeen nasan danginsa kuma tna musu alkhairi wani yasani wani baosaniba sai anfada yake sani...


Muryar hanan ce tadawo dashi tunaninsa ,tana yiwa yasmeen sallama hade da Jan hannun twins tace yaya ALLAH yakara suusona.

..


Ameen nagode  suka fita ....


Kallon yasmeen yyi yace ni yaushe zaki bani babyn ?


Yafada fuska kalar tausayi, duk sai yasmeen ta ji yabata tausayi dan ta lura yanada son yara ..


Hannuwansa ta rik'e "ahankali tace insha ALLAH zamu sami yara kayi yayanah "

Inta kular maka dasu ko?amma zakatayani rainonsu?


Murmushi farin ciki yyi yace eh mana baby nah ai komai kikeso zan miki...i.. I lo ..ve .u..........


Ammice ta ta murdo k'ofar ta ce yasmeen had 9:pm tyi kixo g driver can zai kaimu gd mu wuce...


da sauri yarima yace ammi inkuma tatafi, wazaiyi jinyata gsky ni abarta anan....yasmeen tace eh ammi ni gunsa zan kwana na kula da shi. .....


Baki bud'e  ammi ke kallonsu tana salati hade da cewa son yaushe kazama marar kunya har ka koyarda yasmeen nidai nasan bahaka take ba wlh.


Kallon yasmeen ammi tayi tace srkin gd d guard's dinsa zasu kwana dashi..amamakinta sai taga yasmeen nayin hawaye ,yarima yaruke hannuwanta yace pls ammi kibarta ta kula dni na rokeki kinga kuka take pls yafad'a kamar zai yi kukan shima ..


Kwata kwata ammi basu bata haushiba saima sha'a wa dasuka bata dan bbu abinda yakai soyayya dadi aduniya  tayi mamakin wannan soyayya tasu .


Murmushi tayi tace yi hakuri kinji yata tsokanarki nke dama ke zaki tsaya ki kula d mijinki ,sallama nazo yimuku,tana fadin hakan ta fita..


Yarima yarungume yasmeen yana sinsinar wuyanta yace ILOVE U..


Shiru tayi batace komaiba ,arazane yadago ,azuciyarsa yana cewa kaddai ace bata sona.


Baby  do you love me, yes or no pls answer me..


Hawaye yasmeen kawai take ,ammafa na farin ciki saidai bata nuna na farin cikin bne,murya na rawa tace ka manta dakace baka sona ka tsaneni bazaka taba sonaba har abada kafi karfin hakan sai yanzun zakace kanasona...


Arikice yarik'e hannunta yace wlh yasmeen yake ki yadda dni ko alokacin bansa ke bace wlh Saida nadawo dg Jordan nasan kece na aura kuma ai dg lokacin ban sake yimki komaiba..


Wlh tun ranar dana fara ganinki a garden din nan nafara sonki,alokacin dana hango Ku keda k'awarki kuna sa insa dukda banajin abinda nike cewa nafahimci musu Luke shine naje na tsokaneki dan alokacin ina jin nauyin furta wata ya mace kalmarso sbd yanda  yan mata ke tururuwar cewa suna sons ,alokacin Kika watsamun lemo tabbas naji haushi kuma banyi niyar tafiya dkeba sai ,sai nayi wani tunani bara natafi dke na gwada tarbiyyarki tukum..


Shine naje dke kina kuka ,kina zagina har Muka Shiga ciki Kika fara bni hkuri namai dake gd ,fitar da Kika ga nayi parlour naje nayita dariya ganin yadda Kika tsorata bbu bakin tsiwa da rashin kunya ,shine dubara ta fadomin naje nace sai kin wanke ksyan kitafi ko ki kwana anan.


"" wankewar da kikayi ya tabbatarmun kinada tarbiyya bakisan kwana wani gu matsayinki na budurwa kuma kin tsorata kin dauka  Repin dnki zanyi. "


Yaci gaba da cewa bayan kin tafi ,sainaita tunani hanyar fa batada kyau kada wani abu yasamarminke d sauri na zagaya gun d me ba flowers ruwa yake nace yaje d mashin waje yakaiki gd yace kixo zai taimaka miki na fasiltamishi kalar kayan dke jikinki,amma sai nace masa nima ban sankiba ,naga kina bukatar taimakone shiyasa  nikuma banasan komawa cikin gari bbu musu yace to yatafi.


Bayan yadawo dg kaiki sai yacemun aike yar anguwarsu ce yasankima.


Nace ALLAH Sarki.


Sadda Kika ganni a skul na Ku tabbas bansanke bace bash yyima haka Saida nadago ki tukum,nima gun wani malami nje abokina bansamesaba,tabbas viju milk din d Kika watsamin naji xafin abun sosai har ga ALLAH da naso sake binkice akan ki ,sainafasa.


Ko a kotu bansanke bace nakare sai bayan naje Jordan nagane hakan sadda nje gaisheda umma.


Kuma alokacin kina raina har a jodan  ina tunaki sosai yasmeen kece first love dina kuma ta karshe insha ALLAH.


Salma dakikeji ina fadi wlh bna Santa kawaidai zan auretane sbd tana sona sosai tanamun biyayya kuma zata iyayin komai akaina.


Alokacin d naganki nayi niyar fasa aurenta sauna tuna namata alkawari ,to kuma sai Abba yatareni da cewa alhj tsoho kakana yamin mata shinefa gaba daya nashiga  rudani d damuwa .

Mata har ukku sainaji tsanar wacce aka auramin bansankebace...


AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿73&74


Yasmeen tayi ajiyar zuciya"ahankali tace ILOVE U too my Prince ",nima wlh tun ranar da na watsamaka viju milk tun ranar nafara sonka pls kada kaci amanata kaji..

    Janyota yyi jikinsa tare da hade bakinsa dnata yahau yimata wani special kiss"

Tallabe kansa tayi tana shafawa suna maida numfashi..knock d'in da akayi yakatsemusu hanzari,murya na rawa yarima yace waye?"

Sarkin gd yace nine,dan matsawa yarima yyi dg kusada yasmeen sannan yabashi izinin shigowa ,baya n yashigo yace dama mai martaba yace azo aji ko suna bukatar wani abu ?"

Yarima yace ah ah sarkin gd yace to hade da fita yasmeen ta tashi ta rufe k'ofar.

Kallonsa tayi tace my Prince ko kana bukatar wani abu? Murmushi yyi yace ah ah my Princess kixo dai mu kwanta shine abinda nike bukata ..

"ahankali tace pls ka kwanta kaga baka lfy kuma gadon yyimana kadan kada nafama maka ciwo zan kwanta k'asa..


"" shiru yyi bece komai ba ya kwanta,da sauri yasmeen ta hau kan bed din ,cikin sanyin murya tace yaya kayi hkuri in ranka ya baci bazan koma ba nadena."

      Juyowa yyi da ita gabansa yashafa kanta yace baby nah ke bakya laifi aguna kawai dai ba nason kinamun mus u kinji?"tace to nadena ,addua yyi musu hade da matseta akirjinsa ,atakure bacci yyi gaba dasu...


Washe gari bayan sun yi break har yarima yasha magani aka sake masa dressing hade d cewa yabari sai anjima yyi wanka amma kada yabari ruwa yataba gun ciwon.

"Kallon yasmeen yyi dke gefensa tayi shiru murmushi yyi yace my Princess kije kiyi wanka ko?

Mak'e kafad'a tayi tace um um nibazan iya yin wanka ba sai tare da kai duk sadda katashi nima zanyi..cikin jin dad'in kalaman nata yace to baby nah ai nasan nidake d'aya ne amma banason kifa takura ,murmushi tayi hade da aza kanta gefen kafadarsa cikin shagwaba tace um um bbu takura a tsakanunmu..lumshe ido yyi hade da cewa I'm proud of you.. k'ofar ammice ta bude itada kuyanginta suka shigo ,har kasa yasmeen ta sauka ta gaida ita ,cikin sakin fuska ammi ta amsa tare da tambayar mai jikin...


" tace da sauki".


,,,bayan sun gaisa da yarima yace ammi wai yaushe za'a bani sallama? "tace sai gobe insha ALLAH, yace nidai nafisan yau koda da dare ne,ammi tace to bari mugani.,,,


Kallon yasmeen tayi tace oh y'ata ,kije gd kiyo wanka mana...yarima yakatseta ammi d cewa ah ah ammi ba yanxunba zatayi sai anjima ,tace bn gane sai anjima?"


Yace eh nima ai doctor yace nabari sai anjima nayi shiyasa,shiru ammi tayi dan abun yagirmi tunanin ta ,yasmeen dai batace komaiba ,ammi ta fita bbu jimawa umma yasmeen ta zo itada inna atika suka duba yarima hade d kamasa mutuniyar tasa wato fura da tuwan masara ,aiko yji dadi kuma yaci sosai yasmeen tayi mamakinsa amma bata nunaba itama tasha furar dan mutuniyartace.,,,


       ********

Saude ce tsaye(yar Kawu bala) tareda saurayinta da ya aiko kiranta Wanda kitowarta kenan tayi masa sallama amma be kalletaba

"Ahankali tace musbahu lfy kaki mgn ?" afusace yace lfyar takawo hakan nazone nasanar dke nafasa aurenki sbd nasami labarin mahaifinki maciyin amana ne yakashe k'aninsa ,ayanxun hakama ankashe babanki ta hanyar rataya akotu...


sbd haka bazan hada zuria da maciya amanaba tunda nima wata ran xaki iya kasheni kigaje abinda nabari tunda mahaifinki nadason abin duniya kema zaki iya gadon hal.....da sauri saude ta katsesa atsawace hade da cewa ya isa hhhhh!cin fuskar yyi yawa,bazakazo har k'ofar gidanmuba kaci mutuncina d na iyayenaba, bazai yuyuba ,batun aure kuma sai me dan kafasa?"


Kaine autan maza ?


Saikayi tafiyarka ALLAH yahad'a kowa d rabonda....tana fadin hakan ta shige gida rai bace ....


"" bash d umman su ta samu a tsakar gd ,cikin kuka tayi musu bayanin abinda yafaru hade da cewa baba yyi mana bak'in fenti dabazai taba gogewaba har abada".


Bash yyi ajiyar zuciya cikin takaici yace nima haka mukayi d wacce nike xuwa gunta ,amma b komai wani ganin g ALLAH baiwane..


Nasiha mahaifiyardu taita musu d kwantarmusu d hankali,dukda ita daurewa kawai take yi dan maganar ta shigeta..


         ******

Su yarima kuwa haka yan dubiya sukayita zuwa dubasa har xuwa dare tukum akabasa sallama .


Koda suka isa gd part din su suka wuce ,sukayi wanka shida yasmeen sannan sukayi kwanciyarsu..


Washe gari  bayan sun gama kimtsawa ,yasmeen na zaune yarima yyi matashi d cinyarta saiga kubra tazo dubasa dan yasmeen ta sanar da ita.


bayan sun gaisa ta yi masa ya jiki ,sai kallonsu take tana tuna farkon haduwarsu ,koba a fada mataba tasan dai yanxun son junansu suke, kokarin tashi kubra keyi dan tafiya ..salis yyi sallama hade da shigowa parlourn.


Yah salam salis ya fada a zuciyarsa sbd arba da yyi d kubra atake yaji kaunarta ta shigewa dan yanasan mace wacce ta keda alaka d yasmeen kodan yasami irin so d kaunar da ake nunawa yarima...yarima kuwa tsab yaharbi jirgin salis ,cikin tsokana yace kai mlm kayi shiru kawani tsaremu d ido ko kayi mgn ko katafi,kubra data tsargu d kallon d salis kemata tace to friend sai anjima...


Tashi yasmeen tayi tadan takamata ,sai zolayarta take wannan ruwan love ai yyi yawa,itadai yasmeen dariya kawai tayi har sukayi sallama tadawo zata shiga ciki danta lura yarima bayason maza na kallonta.


"Salis yace gimbiya nidai gani d kokon barata gsky kawarki tamun pls kishigar dni."


Harararsa yarima yyi yace ni matata ba yar wani aikebace kashigar dakanka..murmushi yasmeen tayi tace g number ta saikashigar d kankan.


Bayan kwana biyu ...


Shin yasmeen ban cancanci kisoniba?


Yasmeen tayi ajiyar zuciya...


Share pls

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Masu min magana ta PC ko ta grps bbu replay kuyi hkuri wlh inada uxuri ,inaduba comments dinku  d fatan alkhairi agareni inajin dadi sosai..


🅿75&76


Bayan kwana biyu yarima ne kwance kan makeken bed din sa yana jiran yasmeen ta zo su kwanta tana part din ammi zata sha fura."

     Tsaki yyi ganin ta jima bata dawoba,afili yace nasan yarannan ne su Maryam suka tsaida ita",sai juyi yake kan bed din dan gsky yau bazai hakuraba dan rabonsa da yyi sex da ita yau 5days jiyake kamar yyi wata gashi kuma ciwonsa ya warke sai d'an abinda ba'a rasaba...

Jin kamshin turaren yasmeen yasakashi waigowa ,suna hada ido da ita tayi murmushi hade da fadawa jikinsa tana kukan shagwaba. "

        Shafa kanta yyi yace to sarkin rigima menene ?"turo baki tayi tace basu Maryam bne ...murmushi yyi yace oh Ashe keda  kannenki ne to bbu ruwana tsakanunku.

Cikin shagwaba ta ce wai dannace bana so afito da ankon ranar deener na yaya sageer kowa yasaka kayansa wai ah ah...


Hancinta yaja yace rabu da su kowa kayansa zai saka kedama bazakijeba ,dan kinsanma bazan barkiba ,hauka nake duk ga maza su kalle minke ai bazan iyaba..


"Ihu da koke koke kawai yasmeen keyi Wanda zallar shagwabace kawai,shikuwa duk yawani rikice yanata aikin rarrashi dg nan kuma yafara romancing dinta ,bbu bata lokaci ta biyemishi tana maida mishi murtani... saidai kuma tana fargaba dan indai yarima yawuce 3days basu haduba duk ranar da suka hadu sai ta ji ajikinta..


gaba daya yafita hayyacinsa hanyarsa kawai yake nema bbu bata lokaci yabi,tun yasmeen na jurewa har ta fara yan koke koke tana kokarin janye jikinta anasa ..hmmm ai sai hakan yakara masa karfin gwiwa ya riketa gam yanata aikin sa.,,,,


" sai shure shure take tana cewa pls yaya kamun ahankali zafi nakeji wayyo ummanaaaaaa!bakin ya cafke yahade d nasa daganan tayi shiru".


saida yasami cikakkiyar gamsuwa tukum yasarara mata ,yana maida numfashi... Itadai juyawa tayi ita kadai tasan yadda takeji dan ta gaji..janyota yyi jikinsa hade da azata kan kirjinsa ahankali yashafi kanta yace my Princess kin gaji ko ?wai yaushe zaki saba da abin nan?"

Ahankali tace nibanfa gajiba kawaidai bacci zanyi kara shigar da ita yyi a kirjinsa yace to kiyi baccinki kinji tawan.?

Shiru yyi yana bubbuga bayan ta dan tayi bacci,afili yace ALLAH yyi miki albarka yasmeen yabarmu tare nasan kin gaji sbd bakyasan in damu kikace baki gajiba ,ai nasami gamsuwa baby nah..


Ahankali tace ameen ,yaya muje muyi wanka,bbu musu ya sungumeta sukayi toilet...


Washe gari ,yasmeen ce tsaye gaban mirror tana parking gashinta ,taji anrungumeta t baya murmushi tayi dan tasan yarimane "cikin rada yace baby wai meyasa bakya saka bra?"


Turo baki tayi tace to ba ciwo kirjina keyiba,murmushi yyi hade da saka hannuwansa tasaman rigai yafara shafar na shanunta ,lumshe ido tayi hade da zuge masa xip din ..wani numfashi yasaki hade da cafkarsu yana musu wani irin tsotsa tuni tsayuwa ta gagaresu suka baje kan bed bbu kunya yasmeen ta rinka yiwa yarima wasu sabbin salon data kusa zautar dashi,Wanda yyi mamakinta sosai dg nan suka fada babbar harka....


Bayan sun kimtsa suka nufi part din ammi dan gaisheta ,samu sukayi anata hidima gasu hanan d anty lubnah sunxo,kuyangi d barorin gidan nata shige d fice ,bayan sun gaisa da su hanan,wadda lubnah fuska bbu walwala ta amsa ...yarima na lura da ita amma yasha alwashin xaiyi maganinta..


Hannun yasmeen yaja ,ganin ammi bata parlourn, can cikin parlourn ta na bak'i suka sameta.bayan sun gama gaisawa yarima yace wai ammi hidimar me ake ne?


Yar dariya tayi tace oh na mance banma sanar da kaiba ,hjy babbace  zataxo ita da alhj tsoho mijinta su ganka d jiki kuma suyimaka jaje....yatsina fuska yarima yyi dan har ga ALLAH beji wani dad'in cewa zata zoba sbd tsohuwar akwai mita d shishshigi alhj tsoho yafita kirki...hanance tayi sallama hade d cewa ammi aiga hjy babba nan ta iso,amma shi alhj tsoho sai bayan kwana4zaixo sai suwuce...


Tashi ammi tayi dan itama bataso hjy babban ta kwana dan tanada masifa d korafi...kallon su yarima tayi tace son kuje mana Ku gaisa dama batasan yasmeen ba!


Tashi yarima yyi beyi mgn ba Yakama hannun yasmeen wacce hakanan takejin faduwar gaba...


Tun kan su ida shiga ,sukejin muryar tsohuwar tana yiwa bayi mita itaga mahaifiyar Sarki..yasmeen kuwa cikin tsoro tasake matsawa jikin yarima shima kansa ganin kamar yasmeen ta Dan tsorata yasakashi jikinsa yyi sanyi,amma bai nunaba ,ahankali ya murza hannunta yace menene na damuwa?"kisaki jikinki Ku gaisa kakata ce kinji babyn prince?


Murmushi tayi ,shima yyi adedenan suka iso parlourn... Yasmeen ta saci kallon tsohuwar tayi saurin kauda kai dan bbu fara'a a fuskarta..


Zama sukayi a kujera daya hannunsa cikin nata,fuska asake yace tsohuwa mai ran karfe kece haka da safen nan?


dan murmushi tayi tace eh mana to yasan ranka,yanxun ya jikin naka?yace nasami sauki,yasmeen tace hjy ina kwana,ba yabo b fallasa tace lfy atakaice ta wani yatsina fuska tace wacece Wannan take wani shige maka kamar wani zai kamata haka bbu kunya ?ina matar taka take ne?hanan take ai hajjaju itace ,baki bude tace yoyabanganta da ciki ba ko karamine?


da sauri Anty lubna tace ai hjy juyace aure har yakusa shekara amma bbu ciki saidai taci tayi k'aton kashi ,gashi tagama da shi ,mijin tace ne  duk abinda tace shi yake bi ,bbu abinda suka aje sai jaraba butsu butsu yana gindinta ,kogaban wa basujin kunya sai barnar da kudinsa yake akanta...


Yarima ransa yyi k'ololuwa gurin back ,amma yanxun zaiyi maganinta dan shekara 2data basa take masa haka...


Yasmeen kuwa kanta aduke tsab take sauratensu rant bbu dadi amma batace komaiba..


"" cikin isa hjy babba tace to bazai yuyuba wlh bazan bari a mallakemun jika ba,dole ma yakara aure dan karuwa muke so ,aidama dan talakka be iya cin arzik'iba ,takalli yarima Wanda fuskarsa tayi jajir idanunsa ko bakin eye ball dinsa baki gani jijiyoyin kansa sun tashi sbd tsabar bacin rai...tace to da  sake dole ka kara aure kana jina koba kajina?


Asannan hanan tayi mgn tace haba mana hjy d Anty me Anty yasmeen tayi muku hakane?bisabilillahi tunda mijinta bedamu dayyi maganar haihuwar ba sai Ku barta dukafa 11 month kenan d auren kukasan ko rabon na gaba haba mana dan ...tsawar d hajiya babba tayiwa hanan yasata yin shiru tace rufemun baki ko ubanki dke Sarki be isa inyi magana yyimun musu ba Balle ke...


Lubna ta cafke da cewa ai haka take da shishshigi wai yarinya karama ita take cewa Anty ,hannan tace eh nace kindaiji haushi wlh kuma kin xubda girmanki.


Yarima dayagama cika yyi fom da cin fuskar da akewa yasmeen dinsa mace daya tamkar 4,hannun yasmeen yaja da niyar fita dan hawaye take, cikin masifa hjy tace kai baka bani amsaba nace kajini aure nakeson ka k'ara!afusace yarima yace eh naji kuma bazan k'araba sbd nizan zauna dasu ba wani ,wlh !wlh!!wlh !!!kinji na rantse d'aukewar numfashi kawai zaisaka nabi abinda kkeso....afusace anty lubnah tace bakada hankali hjy kake gayawa Wannan maganar?akan Wannan yar matsiyatan,tafad'a hade da nuna yasmeen dke bayan yarima tana hawaye..


Azuciye yarima yyi kanta hade da cewa zannuna miki rashin hankali ,kasheki zanyi kuma nakashe banza wawiya wacce batasan takama German taba..baki bude lubna ke kallonsa tana ja da baya ganin ya nufota...cikin tsawa da karaji hjy ta ce kai kada ka tab'ata ,ashedai d gaskiyarta datace tagama dakai...shiru tayi sakamakon cafkar dataga yarima yyiwa Anty lubna,Wanda tuni idanunta sukayo waje tafara kakari...yasmeen kwa da gudu tabar part din..


Hjy tsohuwa takasa komai dama masifar ce kawai dg zaune danta tsufa sosai.


Kallon hanan tayi wacce ke zaune hankalinta kwance bata damuba ma,cikin jin haushin ta hjy ta ce kina ganin zai kasheta bazaki hanaba inyyi kisan kai fa ?


dage kafad'a hanan tayi tace duk tsuntsun daya kira ruwa shi ruwa ka doka....muryar ammi sukaji tana cewa inhar baka kashemun lubnaba ban yafe maka dan nafitar da ita ajerin y'ayanah ALLAH yyi maka albarka Dan naji komai abinda ke faruwa nasaurari komai inma ka kasheta to ka kashe banxa dan bbu kowa anan dg ni sai hanan d hjy ,nikuwa d hanan bazamu bada shedaba....


Ihu hjy babba ta kurma iya karfinta dan inbatayi d gaskeba yarima zai oya kashe lubna atake....


Share pls

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿77&78


"" ihu hjy babba ta kurma iya k'arfinta dan inbatayi d gskeba yarima zai iya kashe lubna atake"

       Ihun datayine ,yasaka yhj rahama d yaya sageer saurin k'arasowa a parlourn.... salati hjy rahama tasaki ganin idanun lubna na Neman kafewa sbd tsabar shak'ar da yarima yyi mata, tsawa take masa amma ko ajikinsa ,baki bude take kallon ,ammi d hanan dke parlourn amma kamar bbu su ,cikin xafin nama ta tsinke yarima da Mari ,hade da Jan hannunsa amma yak'i saki ,asukwane sageer yasaka hannunsa da k'yar suka janye yarima sai huci yake yabar part din..

"Ita kuwa lubna data fara shak'ar k'amshin lahira tuni ta fadi gun asume"

cikin b'acin rai hjy rahama ke tambayar ammi meyahadasu ,bbu wani boye boye ammi ta sanar da ita komai....

Tsaki hjy babba ta yi tace aikin banza k'ila kema tagama dke tunda sbd ita har kina cewa ,wai inbekashetaba baki yafe masaba,aida dani kikace yahad'a yakashe tunda har dani amasu laifin.

      Mama (hjy rahama)dke zubawa lubna ruwan sanyi tace dan ALLAH hjy ya isa abar maganar ,lubna ta rugada ta zubda girmanta,sannan ammin yara ki janye maganar baki yafemasa in be kashetaba dakuma kincireta ajerin yayanki..adedenan lubnah tayi ihu tana cewa wayyo ALLAH zaikasheniiiiiii!harara mama ta watsamata tace yima mutane shiru..

Mikewa ammi ta yi tace ,maman yara na yafewa yarima ALLAH yyi masa albarka shida matarsa kuma insha ALLAH sai yasmeen ta xuba masa y'aya da yardar ALLAH maganata ta nanan na cire lubna ajerin y'ayanah,tana fadin hakan ta nufi ciki...

Hjy babba ta mike aikin banza saime to inkin cireta a jerin y'ayan naki ,aikowa yasan yarki ce ,bara naje ,isma'il din inban isadake d d'ankiba shi ai na isa dashi....da sauri mama ta bar parlour tabi wata hanya danta ruga hjy babba zuwa taje ta sanar da Sarki komai."

Parlourn yarage dg hanan sai lubna wacce keta faman kukan kalamin ammi agareta,tsaki hanan tayi tace kadan Kika gani badai tak'amarki hada husumaba ko..hmm ta tashi tabar mata parlourn ita d'aya..


    *********


Yasmeen kuwa koda ta fita d gudu part dinsu tanufa ,tafad'a kan bed tana rera kuka miyasa Anty lubna bata k'aunarta ko kad'an ?gashi tasakasa Wannan tujararrar tsohuwar itama bata sonta ,oh ashe dama  haka dangin miji suke,lallai d mutum keba kansa haihuwa data ba kanta kodan sbd mijinta dan tasan yanaso bayasan yyita matsa mata da maganar ne kada hankalinta yatashi..


"Tasan da yawan sex kesaka saurin samun ciki ,data samu,ALLAH Sarki yarima shiyasa take matukar kaunarsa ,ji yadda yashak'i lubnah sbd ita, oh ALLAH dai yasa kada ya aikata abinda yafadiiiiiiii!"


Wata zuciyar tace inya kashetafa?


"Zunbur ta mik'e dan fita tana bude k'ofar yarima na shigowa ,jikinsa ta fada ,amma batayi kukaba sbd tasan d'aga masa hankali zatayi..kan bed yajata yarungumeta" ahankali yace my Princess duk wuya duk dad'i duk rintsi inatare da ke ,kada kidamu da maganarsu matata inasanki aduk yadda kike kinji ?"aike nikeso ,inma bamu haihuba ga yaran dangi sai murik'e,balle inaji ajikina zaki haihu yasmeennnnnn,!


Hawayenta ta share tace nasan hakan mijina,amma kayi hkuri kayiwa kakarka biyayya kayi auren ,duk da bazanso hakanba sbd ban had'a ka da kowaba, ina kishinka,amma farincikinka shine naawa na yarda ka k'ara auren kaga ana zargin cewa wai namaka asiri..


Katseta yyi da cewa my Princess wlh kinji na rantse bazan iya adalci atsaka nunkuba koda na kara auren bazan gaji da fadamiki ina sonki bazan iya hada ki d kowacce mace ba...


Amma ki banni d hjy babba wlh tsoho zankira insanar dashi tazone ta d'agamun hankali b dubiya tazo munba,dan ai tasanshi in ya bude mata wuta..k'ofar da aka murd'o afusace ,yasakasu kallon k'ofar ...


"Hjy babba ce tsaye bakinta har kumfa yake tace oh ashe d gske dai maganar lubna ,jarabarce zakuyi kenan ko?"


Yarima da yahade rai yace eh itace dad'in abun dai halalina ne ,bada wata Kika kamaniba...


Salati hjy babba tyi tace nikake zagi ...to dama kiranka nazo yi d kaina basai naturoba,muje ayi magana gani g ubanka..


Yasmeen ,ahankali tace my Prince kabida kaji pls indai na isa kuma kada kayi musu da Sarki......


Tashi yyi yabita har parlourn Sarki,akuma lokacin har mama ta sanar dashi komai baidai nuna yasaniba,kuma beji zafin yarima dan lubna ta cancanci komai ,kuma dole yyi mata hukunci..


"har k'asa yasakko yagaishe d mahaifiyarsa ,yarima na gefe kai duke ...cikin kukan muna funci hjy babba ta zage da abinda akayi da Wanda ba'a yiba ta sanar da Sarki....


Azahiri yanuna ransa ya baci har yyiwa yarima fada yace kuma dole yabi umarnin...ringin din wayar  Sarki tasaka mai martaba kin karasa maganar...


dubawa yyi yaga alhj tsoho ne ,yana dagawa ,cikin b'acin rai yace bance kacewa yarima komaiba game d maganar Halima(hjy babba) gobe inanan tafe ,dama taxo ta hargitsa gidan ba dubuya tazoyiba to hanan ta kirani ta sanar dnikomai kuma ta kyauta ,xanxo gobe insha ALLAH bance ayiwa hanan komaiba,yana fadi d'it yakashe,tsaki hjy babba ta yi dan ta ji duka maganar ta tashi tabar parlourn..


Sarki ya kalli yarima yace karika bin hjy a hankali sbd ta tsuha da yawa,murna fal ran yarima yace to Abba tuba nake ,Sarki yace bbu komai,wlh matar ka da bbu alkhairi a aurenku alhj tsoho bazai aura maka itaba yyi ista hara yaga akwai alkhairi tun kafin ka aureta..


Tashi yarima yyi hade da yiwa abbansa godiya ya wuce part dinsu yana wani mugun kaunar yar uwarsa hanan dan dabata kira alhj tsohoba komai zai iya faruwa ,kuma yaci alwashin zai yima kyautar ban mamaki itada twins dinta kodan lubna taji haushi..


Salmace tsaye gaban motarta itada wani" ahankali tace...


Share pls

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿79&80


Salma ce tsaye gaban motarta itada wani "ahankali tace katabbatar anan skul din ta ke? yace eh ranki yadad'e tace to kana ganin Wanda zaiyi  aikin baza 'a kamashiba ?" yace ai zai boye fuska kafin ya aiwatar gsky dan bayada tsoro ko kadan."

        Tace to shikenan kaje kasamesa sai kuxo muyi dashi abinda zanbiyasa !yace to had'e da tafiya".

dariya salma ta kece da ita afili tace ai wlhy duk Wanda yyimun kan itace ni na kara zanmasa saina lalata tsakanunku kota halin k'aka.....


       ******

Yasmeen kuwa bayan yarima yafita taga lokacin sallar azahar yyi,alwalla tayi tazo ta yi sallar had'e da yin nafila,ta hawaye tna addua ALLAH yakamusu d'auki yabasu ikon cin wannan jaraba wa dayake jarabtarsu da ita,wadda dg wannan ta kunno sai wannan ta kunno kai,tana kuka tana shafawa..

       "Shikuwa yarima be shigo bed roomdinba sai da yyi salla", yana shigo yahangota tna addua tna kuka,wani irin tausayi tabasa sosai ."

Zama yyi kusada ita yatayata shafa adduar had'e da cire mata hijab din yace princess bana hanaki wannan yawan kukanba?

      "Ahankali tace  dena !mikar da ita yyi yace muje muci abinci kinji?" cikin sanyin murya tace yaya bazan Ciba yace ok nima bazan Ciba ,da sauri ta ce to zanci!murmushi yyi yace nima to,itama murmushin tayi ,suka wuce gun dining area ahanya yake sanar da ita yadda sukayi d Sarki dan yalura bazata tambayesa..

Wani farin ciki ta ji,duk saitaji bbu nauyin datakeji akirjinta nan tasaki jiki sukaci abinci....


Bayan sun idar parlour suka tsauna tayi zaune saman cinyarsa tana wasa da sajen fuskarsa  ,shikuma hankalinsa na gun laptop d'insa...


Ammice zaune akayafaren parlourn ta ,gefenta Anty lubna ce duke tana bata hkuri,cikin kakkausar murya ammi tace bazan gaji da maimaita mikiba ,bni kikayimawaba kije ki sami yasmeen d yarima kibasu hkuri inhar sun hkura zan janye kudurina akanki...


Tashi tayi sum sum sum ta fita sai fa bazata iyaba gsky yaron da yyi mata irin wannan shak'ar taje ta basa hkuri k'ila ma yakaramata...


"Tana fitowa tahadu d jakkadiya tace mata taje maimartaba nakiranta....cikinta Saida yajuya tsabar furgici,jiki ba kwari ta nufi fada.bayan tayi gaisuwa gun Sarki ,yyi mata Ta's had'e da cewa kada tasake zuwa gidan nan saiya nemeta kuma taje yanxun tabawa yasmeen hkuri kuma muddin ta sanar d hjy babba zata gane kuranta."


,,ko salma bbu ta kutsa kai ,cikin parlourn, tasami guri ta zauna ,azuciyar ta tana mamakin ani time suna manne da juna,duka sun lura da ita amma sai sukayi kamar basu gantaba,hakan yasa tad'an tsorata infa yasake shak'etafa?"cikin d'ar d'ar tace dama mai martaba yace nazo nabaku hkuri ...doguwar tsuka yarima yaja yatashi yasab'i yasmeen akafad'arsa suka barmata parlourn...


"Make kafada tayi alamar ko ajikinta ta fice abinta."


Yarima kuwa kan bed yake k'ok'arin aje yasmeen, amma taki sai tsillewa take tna shagwaba ita sai ya goyata ,murmushi yyi yace to sarkin rigima ni fitama zanyi yanxun ..,,


Kukan kissa tasaka ita sai ya goyaya kuma saita bishi bazai bartaba,dukowa yyi ta haye kan bayansa yyita zagaye bed room din da ita dan karan kanta tace ya sauketa haka..


Sauketa yyi yna maida numfashi, kan jikinsa tahaye sai shagwabarta take zubawa ...hancinta yaja yace oya rufe idon bacci zamuyi in la'asar tayi mutashi..bbu musu ta rufe idon lallab'ata yyita yi kamar yarinyar goye har tayi bacci ,ahankali yazare jikinsa anata ,yacanxa kayansa yafita dg gidan yanufi office insa...


"" mutane yasamu masu son ganinsa ,ciki kuwa harda bash,koda yagansa Saida yaji gaban sa yafadi amma be nunaba ,saima yace aturomasa shi."


Bayan bash yyi sallama yarima yabashi ixnin zama sannan yazauna ,wani pic yaba yarima had'e da cewa kasan wannan?

Wani mummunan fad'uwar gaba yarima yaji ganin salmace"yace eh lfy? Bash yace b lauba!, dan tanason ganin bayan yasmeen !dalilin dayasa nasani shine tasaka ayi mata binkice wanne skul take aka gano mata ,shine takes on tayi mata k'axafin xinaaaa!


"Cikin b'acin rai yarima yace what tttttttttt!"


Yace yes ,bazan boyemakaba abaya nayi rashin ji kuma na aikata hakan ,shine basusan cewa yar uwata bace kuma basu San nashiryuba aka nemoni ni xanyi aikin...tagumi yarima yyi yana salati Ashe salma ba iya lesbian mugun halinta ya tsayaba oh yaushe makiya zasubarsa su hutane shida yasmeen dinsa ALLAH yabasu ikon cin wannan jarabawa...


Kallon bash yyi yace to yanxun a ina tace kasami yasmeen har kayimata hakan?


"Yace a skul"


,,kuma tace zata bani dubu dari biyar inna aiwatarda aikin ,wani k'yallene tace zan goga mata a fuska to zata fita hayyacinta saina yima pics wadanda basu daceba sai na turamaka a what's app dan tabani number ka..


"Murmushin takaici yarima yyi yace kirata kace tana ina gakanan xuwa da akwai matsala."


Bbu musu yyi calling din salma hade da saka wayar a hans free,ta d'aga tana cewa lfy ina holewata d matana ka katsemun ?


Yace bbu lfy ai kina ina yanxun?"tsaki tayi tace gani agd ,amma muhadu a garden din jiya yanxun ammafa can baya zamu tsaya Inda bbu kowa....batajira me zaiceba takashe kiran...


Tashi yarima yyi yafita had'e da cewa bash I'm coming..


Yad'an jima tukum yadawo da wani dan bocket karami,yakalli bash yace yarik'e sutafi.


Wata karamar mota yarima yabude suka shiga yyiwa guards dinsa alamar kar su biyosa ,suna hanya salma ta kira bash tace gata nan agun yace eh yakusa karasowa...


Bayan sun yi parking ,bash yyi gaba yarima na biye dashi ,dan bucket din na hannunsa.


Can karshen garden din sukaje inda bbu mutane sosai ,yarima yacewa bash yyi gaba tukum.


Tana cikin mota ta fito ta kalli bash tace meye matsalar?


Beyi maganaba sai yasahannunsa yanuna mata gefen sa .....wazata gani?


Share pls

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿81&82


Beyi mgn ba sai yasa hannunsa yanuna mata gefensa...wazata gani?"yarimane tsaye yakafeta da firgitattun idanunsa dasukayi zajir yana watsamata kallon tsana..


"" wani kallon tuhuma tajefi bash dashi, "shikuwa mak'e k'afad'a yyi alamar ko ajikinsa".

       Cikin takunsa na k'asaita had'e da isa yanufota...tana ganin haka ta fara ja da baya dan guduwa dan tasan halin yarima in and out..

" wata muguwar damk'a yyi mata ganin zata shige mota ,tana juyowa ya wanke ta da maruka lafiyayyu guda2wanda Saida jinta na wucin gadi yad'auke."

Wata mummunan shaka yyi mata Wanda atake idanunta suka fara ruwa ta sark'e da tari ba k'akk'autawa ,Wanda shikanshi bash yatsorata daganin irin wannan shak'ar da yarima yyiwa salma."

       Saida yatabbatar ta jigatu yacika ta had'e da hankada ta kanta yabugi marfin motar,tasaki wani uban ihu....

"Cikin kakkausar murya ya nunata da yatsa yace ,natsaneki ,banason ki bana k'aunarki dana aureki gara natabbata bbu aure arayuwata. inaso kisani yasmeen ta fi k'arfinki ,yasmeen yar gatan ubangiji ce baki isa kiyi mata komai ba ,saidai sharrinki yakoma miki!

Wawiya fasik'a ke a tunanin ki na had'a yasmeen da wata y'a mace ?" Kinyi kuskuren da jakar brain d'inki kike tunanin yiwa yasmeen sharrin zina,inaso kisani nayarda da mamata dari bisa d'ari tanada tarbiyayya bakamar keba da Kika zubda darajarki atiti Kika zama kingi."koda kinci galaba akan wannan mugun gudirin naki to bazan rabu da yasmeen ba mata d'aya tamkar da 1000,bana aikata abu sainayi binkice,dan binkicen ne yasaka nagano yes kina nemanmu da sharri yanxun kuwa nazo hukuntaki,inafatan kin fahimta".

Zare ido kawai salma keyi dan duk ta ji yafitar mata arai ga zafin maganganunsa na cin fuska ga kuma wai zai hukunta ta ,kuma haushinta guda agaban bash aisai yarainata yaje yana yayata ta."

       Bata gama tunanin ta ba taga yarima na k'ok'arin bude dan bucket d'in dke hannunsa

atsorace tace meye aciki?"wata uwar harara yyi mata yace acid ne zan zubamiki afuska in lalata fuskar da dama bleaching yagama watsawa kixama abintsoro ga lalatattun mata irinki....

Atsorace tace pls wlh natuba kada kamun haka na rok'ek'a wlh nafita arayuwarku...tsaki yarima yyi atsawace yace kadama ki fita indai kincika y'ar halak!amma fa yanxun zan zubamiki na zubawa banxa bbu abinda za'ayi ....kuka tafashe dashi ta duka k'asa tanabashi hkuri...bash ne yazo yajanye yarima dg gefenta ,cikin girmamawa yace y'allab'ai dan ALLAH badan niba karabu da ita tunda da alama tayi nadama intasake yunkurin hakan saikayimata abinda ka gadama,ajiyar zuciya yarima yyi dan dama ba watsamata zaiyiba burgace kawai dan yatsorata "ahankali yace ok nabarta dan ALLAH saidai inaso kisani duk inda Muka hadu Kika nuna kinsanni,saina wulakantaki sakarya wacce ta zubarda da mutuncinta a titi...

Yana fadin hakan fuuuuu yabar gun .

      Kallonta bash yyi yace kiyi hkuri kada kiga naci amanarki ah ah na shiryune yanxun ina tsoron ALLAH, kema ALLAH yasa kigane gsky...

" yana kaiwa nan da sauri yabarta anan"

Yana zuwa gun dasukayi parking yasamu yarima acikin motar,nan yabude masa yashigo suka fara tafiya bbu mai mgn acikin su."

Can yarima yace gsky naji dad'in yadda ka shiryu,kuma na gode sosai da kasanar dani abinda salma kesan aikatawa!

Murmushi bash yyi yace ba komai.

Yarima yace aikin me kake yanxun?

Yace karatu nikeyi ina shekarar karshe  sai inama wani tsaron shago inasamun nacin abinci..

Cikin tausayawa yarima ce ok b damuwa gobe kasameni a office dina zan samarmaka wani abun yi mai kwari,godiya bash yashiga yi bbu kakk'autawa tun kan yasan me za'abashi."

Adede k'ofar gidansu yarima ya ajesa,shikuma yyi yar tafiya kadan yatsaya yyi sallar la'asar sannan yayo gd...


     *********


Yasmeen kuwa tana tashi dh baccin ta duba taga bbu yarima ,cikin jin haushi tace wato wayo yyimunko?"hmm zaidawone ai,tashi tayi ta yo wanka had'e da yin alwarla tayi sallah sannan ta shirya cikin purple din super exclusive Riga da zani tayi daurin daya fito da ita tayi kyau...


Harta zauna taji tanason shan furar ammi,amma me?"tasan wannan masifaffar tsohuwar tana sashen.


"Tashi tayi dan jitake inbatasha furarba ,kamar bazata iya baccin dareba".


Aiko tana zuwa ko tasameta hakimce akan kujera tayiwa tb k'uri kamar tanajin abinake cewa ,ammi na gefe kuyangi 2na matsa mata k'afa,sallama tayi cikin d'ar d'ar ,ammi ta amsa fuska asake nan yasmeen ta gaidasu ,wadda hjy babba ciki ciki ta amsa.ammi tace yayadai yasmeen kinyi shiru?" ahankali tace dama ammi zansha furane...tsaki hjy babba tayi tace oh to a can b'angarenku bbu ne saikin zo nan?"hmm gsky yarinyar nan da alama kingama dasu yodama jikar mlm,koda alhj tsoho yace wannan abar zai aurawa yarima nasan sai mlm yashiga yafito sun gama da.....ammice tace haba hjy dan ALLAH kidena hakan sbd cin fuska ne bbu dadi....


"Baki bude hjy babba tace banga laifinkiba angama dkene."


Ammi ta tsaida kuyanga guda dasuke shirin fita dg parlourn,tace ta dakko gidauniyar fura a frige.,,


"Yasmeen kuwa ko ajikinta da surutun hjy babba dan tasan dg gobe insha ALLAH zata tafi tabar musu gidan".


Karb'ar furar tayi ,ta aje gabanta tafara sha....jin sallamar yarima yasaka ta tafasa shan furar,dan yaje part din su bata can.


,,,,had'e rai yarima yyi had'e da yin kicin kicin da fuska sakamakon ganin hjy babba a parlourn, zama yyi yagaidasu ..tsaki hjy babba tayi tace ka rik'e abunka ,shiru yyi be tankataba,yakalli yasmeen yace my Princess ashe kina nan naduba bakyanan?

Turo baki tayi had'e da harararsa.

Murmushi yyi yace ninefa Prince dinki!tace eh d'in bakaine kayimun wayoba kayi tafiyarkaba ...azuciyarsa yace hmmm bakisan fitata alkhairi bace ba,amma afili sai yace fitarce tazama dole shiyasa my honey kiyi hkuri kinji tawan?"


Itadai ammi tana kallonsu,cike d burgewa da sha'awa dan tasan so ba karya bane ,ta fuskanci soyayya kamar haka gun me martaba Saida hjy babba ta tasota gaba waits mallake mata d'a ,Saida ya auri hjy rahama sannan ta barta tahuta shine yanxun kuma zata koma kan yarima..


Yarima yakalli yasmeen yace my honey zansha furar"make kafada tayi tace um um nidaya ammi tabamawa.dan murmushin gefen baki yyi had'e da matsawa kusada yasmeen yace nikuma nace sainasha b...maganar hjy babba ce tahana yarima kin ida maganarsa jiyyi tace oh ni halima wannan zamani bbu kunya ba tsoron ALLAH agabanmu da gyatumarka kuke wannan abu lallai bakuda kunya kuma yarinyar nan ta cuceni tabata maka tarbiyya tun....magana yarima keshirin yi ,ammi tayi masa alamar ah ah,afusace Yakama hannun yasmeen suna fita,yyinda ammi tasaka abisu da furar part din su.


"" Ahanya yarima yakalli yasmeen yace dg yanxun kada kisake zuwa part din ammi sai wannan masifaffar tsohuwar ta tafi kinji my honey nah?yar dariya yasmeen tayi tace nifa yaya yanxun nadena damuwa tunda kai baka canxamunba dan wani yacanxamun banajin komai..adedenan suka shige parlourn.


Suka tararda fura harta rugasu isowa kan carpet duka zauna yasmeen na tsakkiyar cinyoyinsa suna sha sna firarsu,knocking sukaji,yarima yace yesssss!aka shigo salis ne .


"Bayan sun gaisa,cikin tsokana salis yace to lailah d majnun,inkuna tare na luramanta wa d kowa kkeyi".


Yarima ya hararesa had'e da matse yasmeen gam datake shirin guduwa sbd salis,yace pls mlm yi tafiyarka banason takura lokacin iyalinane wannan.


Dariya salis yyi yace pls yasmeen kitaimakamin wlh kubra tak'i saurarena wlh,yafada  fuska kalar tausayi.


" Ahankali yasmeen tace ka kiratane?"


"Yace eh yafi akirga amma bata peaking".


Cikin rada yasmeen tace wa yarima yaya pls bara naxo kaji ,ok yace had'e da saketa ta shige  bed room dinta tanajin yarima na tsokanar salis..


Tana zuwa takira kubra ,kogaisawa basuyiba tace haba friend meye? haka wulakanci bbu kyau shine yaya salis yakiraki kikaki dagawa?


Ahankali kubra tace ke jamasa aji nayi ,nimafa yyimun ,tsaki yasmeen tayi tace to bari nasanar dashi hakan..d sauri tace ah ah yi hkuri pls zan daga kiransa ALLAH inmayimasa kwatancen gidanku.


Yar dariya yasmeen tayi tace oh anaso ana kaiwa kasuwa ,nan sukayi sallama, yasmeen ta je tasanar da salis cewa yakirata zata d'aga ,abinda yasa bata d'agaba ,bata daga bak'uwar number..


Cikin jin dadi salis yyi godiya had'e da hararar yarima ,yace to kaji kaimeyimun dariya,adaidai nan kubra ta d'aga kiran dan dama yasmeen na cewa yakira yyi calling d'inta,cikin xakuwa yace hellow baby yafad'a had'e da ficewarsa ,su yarima namasa dariya..


Kallon yasmeen yarima yyi yace baby muje nayi wanka bbu musu ta bisa tahada masa atare suka shige ta cud'asa sunata wassaninsu ,har aka kira magrib ,alwalla sukayi sannan duka fito ,yawuce masjeed,itakuma tayi tata agd...


Bedawoba sai da aka yi isha'i tukum yasamu yasmeen kwance tsakkiyar bed din sa dg ita sa yar have vest iya cibi da Dan mini siket..tana chat d friends d'inta....


Koda yaga hankalinta baya gunsa sai yahaye Samanta yakarbe wayar ,ihu tasaka itasaita karba,aiko yafara yimata cakulkuli sai dariya abinsu suke itama ta mirgina tadawo kansa ta ruk'a yimasa cakulkulin suna dariya dg nan salon yacanxa duka Lula wata duniyar...


Washe gari bayan sun gama kimtsawa,state duka fito dan gaisheda su ammi ya wuce office ita kuma skul dan yanxun itama da guards zata ruka zuwa skul din Wanda yajamusu kunne sosai akan su kula masa da ita..


Koda sukaje bbu kowa apart din ,parlourn Sarki suka wuce ,aiko nan suka sami hjy babba,ammi,mama,da lubna sai alhj tsoho zaune yana Jan casbaha.


Yana ganin su yyi murmushi, yace to Ku k'arasomana.


Sallama sukayi had'e da...


Share pls

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿83&84


"" Sallama sukayi had'e da samun guri suka zauna.

bayan sun gama gaisawa alhj tsoho yyi ajiyar zuciya yace yasmeen!

Ta d'ago kanta had'e da amsawa ,yace kiyi hkuri kinji?" da abinda yafaru  kidauka kamar bai faruba ,domin duk Wanda aka bawa hkuri to anxalinceshi."

        "Ahankali tace babu komai ya wuce wlh,alh tsoho yace ALHMDLLH to ALLAH yyi muku albarka ,gaba d'aya akace ameen.

Kallon lubna yyi yace ke kuma marar mutunci nadawo gareki, kifita harkar yarinyar nan tun  kafin iyayanki suyimiki baki...kibata hkuri yanxun!kinji kobakiji ba?" Yafad'a atsawace ,da sauri lubna tace naji,ta kalli yasmeen tace kiyi hkuri dan ALLAH da abinda yafaru "yasmeen tace ya wuce ,nan lubna ta rok'i Sarki d ammi gafara sukace sun yafe amma duk radda tasake shiga harkar yasmeen hmmm...


" nan alh tsoho yasallami kowa "yyinda hjy babba sai cika take tana batsewa,yakalleta yace halimaaaaaaa!

Halima !Halima!!


,,,har sau3 muddin Kika sake shiga shirgin yarannan wlh saina baki mamaki ,kitashi kishirya mu wuce gd yanxun.,,


Hjy babba baki ya mutu ,bata ce komaiba ta tashi tashige ciki dan hada shirginta su wuce gd...


    ** ** ** ** ** ** **


Su yarima kuwa suna fita,gun mota suka nufa ,gdn baya suka zauna shida yasmeen motar guards dinsa daban nabinsu abaya dan kai yasmeen skul shikuma yawuce office..


Yasmeen da kanta ke kan kafad'ar yarima" ahankali tace my Prince in antashi zanje gd na gaido ummana pls!


Murmushi yyi yace to my Princess, karfe nawa kke gama lecture's?


"Tace 1:00pm"


Yace ok to zanshigo gurin2:30gidan umma nima nagaida ita saimu dawo tare dan umman bataki bace ke d'aya "yafad'a had'e da Jan hancinta yana murmushi..


Itama ,hancinsa taja ,tace uhmm aidai narama ,kuma ai umman tafi ji dani akanka ai.


Hannunta ya matse yace ba kyau karya ,aixamuje atambayi umman kinyarda?"


"Tace eh"


Adede nan sukayi parking, yasmeen na k'ok'arin fita, Saida ya rungumota yyi mata kiss agoshi d kumatu.


"Ahankali yace kikulamun da kanki kinji Tawan?"


Cikin kissa tace to nawan nima haka,kuma banda kallon y'an mata,girgiza kai yyi yace in inatare da ke duk sauran mata muna matane kece mace kad'ai aguna .jinjina tayi masa had'e da dagamasa hannu har suka fice yyinda guards d'inta ketake mata baya ,nan tace su jirata zata gun lecture's..


Tana juyowa taga kubra namata murmushi, itama murmushi tayi tace Mrs salis ykk?"yar dariya kubra tayi tace uhmm wlh my one d'ina ya iya zuba love wlh gsky inbansami salis ba komai zai iya faruwa dani!


dariya yasmeen tayi ta mata tace oh friend sabon shiga kenan.


"Kubra tace hmm ai dace da masoyi dadi gareshi ...yasmeen ta katseta d cewa bbu abinda yakaishi dadi aduniya ,saiki rik'e salis dinki gam gam....


Suna gama lecture's yasmeen da guards d'inta sukayo gdnsu,saidaime?


Yasmeen ta sha mamaki ganin tun farkon shiga layin titine har kashe..bata auneba taga gidansu da tangamemen get harda bene ,zaro ido tayi cike d mamaki,sunayin parking agaban gdn tace suje ita yarima zaizo sukoma gida tare,nan ta fito ta tura get din gidan,get man zaune kan kujera ya kalli yasmeen yace hjy lfy?


Yasmeen tace banganeba?ina mutanen gdn ummana?


" asannan get man yagane cewa yar gidance,nan yace tana ciki,y'allab'ai ne yace saina tabbatarda kowanene zai shiga ciki umma tasan dashi..


Yasmeen tace hardani yasmeen? wanene y'allab'ai?


"da sauri ya sakko dg bisa kujerar yaduka had'e da cewa tubanake ran ginbiyya yadade,ALLAH shi taimake ki,wannan umarnin mai gidankine..


Wani farin ciki yasmeen ta ji had'e da k'arajin kaunar yarimanta dan yaga ma mata komai aduniya,murmushi tayi tace haba baba katashi kaji bb komai wlh..kudi ta fito yan 1000ajakarta batasan konawa bne tabashi yyita godiya.,,,,


Bayan ta wuce compound din gidan tabi wani dan corridor saigata a filin tsakar gd ,umma na zaune kan resting chair ga mai aikinta tana wanke wanke nan yasmeen tayi sallama d gudu taje tayi hugging din umma,sai murnar ganin juna suke nan suka shige ciki,bayan yasmeen ta gaishe da mai aikin..


Nan suka gaisa da Umma ,takawo mata wannan ta kawo mata wannan sai hidima take da ita..


Bayan ta zauna tace ina  d'ana yarima,kai yasmeen wannan yaro ALLAH yyimasa albarka yasa yagama da duniya lfy...cikinjin dadi yasmeen tace ameen umma,amma nayi mamakin baki fadamun ba my Prince ya gyara gidan nan ?"


Murmushi umma ta yi tace hakane wlh ASHMAN ne yace kada a afadamiki shidan ALLAH yyi ,ke nifa yanxun ko aiki banayi yadaukarmin me aiki ga store yacikamun da abinci d cefane  kai nidai sai hamdala shigowar yaran nan rayuwarmu alherine ,ALLAH Sarki YARIMA ASHMAN dan albarka kenan fatan shine yasmeen ALLAH yabaku zuriya d'aiyiba....kin k'arasawa tayi sbd wayarta na ringing d'agawa tayi had'e da yin sallama tace Omar faruq hakan take kiransa intaso nishad'i...


Murmushi yasmeen tayi tace Ashe yah Omar ne bani mugaisa!bata wayar tayi Takara akunnanta ,bayan sun gaisa yace my baby nanda 2weeks zanxo hutun shekara ina my girl dina take?


Yar dariya tayi tace hmm tana lfy ,yace pls ta taba yimiki mgn ta ?"


Tace eh


Yace d gaske ?dariya tayi tace inharkadawo namaka promise zanzo da ita agidan nan Ku shirya kanku..


Ahankali yace to ,amma umma najinmu ko?dariya tayi tace eh mana ,saurin kashe kiran yyi,umma tayi dariya tace oh Omar akwai kunya to ALLAH yatabbatar da alkhairi koma wacece..


Yasmeen tace ,ameen nan ta sanar da ita yarima na hanya zaixo sutafi tare yagaisheta,bari tayi sallah..umma tace ai gidan nan ba bakwansa bne asati yazo sau 3ko2yanxun haka furarsa na frige da tuwo akula dan dama yau rabonda da gidan nan kwana3ina tunanin xuwansa..


Cikin jin dadi yasmeen tace Ashe d gaske yake dayace kinfi jidashi akaina?murmushi umma tayi tace tabbas ...


Tashi yasmeen tayi ta na kukan shagwaba ta fita tayo alwarla tazo ta yi sallar azahar..


Zama tayi tace umma mekikadafa?"tace d'an wake ne ,bars akamiki,fita tayi tadawo da plate shake da d'an wake yasha  cabbage da kwai dafaffe ga man kuli d yaji..


Yasmeen nasaka hannunta yarima yyi sallama...


Share pls

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


Ina mik'a godiya ta ga masu kirana da turomun text nagode sosae ana mugun tare🤝🤝


🅿87&88


Batayi fushiba tabi bayansa har bed room d'in sa, ko juyowa baiyiba yakalleta kayansa yake k'ok'arin ragewa yyi wanka.

      "Ahankali taje ta rungumesa tabaya" tana kukan shagwaba cikin kissa ta wani langabe kanta tace Yayana kayi hkuri pls wlh tafiyar tafitarmun arai nafasa bazan jure zama kana fushi dani ba....tureta yyi dg jikin sa cikin tsawa yace kirabu dani kawai tunda Sarki yagama mgn aishikenan inkin tashi kiyi shekara acan ko ki dauwama a can aidama nibaki damu dani ba ,kinason murabu ko?"dama na matsamiki"tunda dakin damu dani bazakiso ko yini daya muyi bama tareba,ninasan bakya sona nine keta haukan sonki ...kuka tafashe dashi tace pls kada kayimun wannan fahimtar kasaurareni aihace nafasa tafiyarko tunda Wanda nike zaune danshi ransa bayaso gara na hakura...gefenta yabi yashige bath room.....

Wani bacin rai yasmeen taji wato bazai hkuraba yakullaceta ko?"

      Fita tayi jiki asanyaye,bed room d'in ta tashige tasami wayarta na ringin, kashewa zatayi saitaga yah Omar ne "ahankali tad'aga had'e da yin sallama,bayan sun gaisa yace oh baby bakisan yau nadawo bne?"

Tace ah ah

"Yace ok kinsani kenan?" Kika k'i kirana koxuwa tarbata!murmushin yak'e tayi tace to tuba nake yayanah gobe insha ALLAH zamuzo nida Maryam d'inka..

     "Lumshe ido yyi yace harnaji dadi gsky kin kyauta dan nak'agara naganta."

Murmushi tayi sukayi sallama.niyar kwanciya take taji knock tashi tayi tabude,jakkadiya ce tace taje ammi nakiranta..

"To tace tasaka alkyabba tafito,saidai kallo1zakamata kasan tna cikin damuwa."

Yana isa part din ta sami ammi zaune ,k'afafunta kan tuntu,kuyangi na mata tausa ak'afar..

Zama yasmeen tayi suka gaisa saidai tun shigowarta ammi ta fahimci tna cikin damuwa..sallamar kuyangin tayi suka fice dg parlourn.


"Ahankali ammi tace dama akan tafiyarkine ,shine nace dame dame kike bukata dazakiyi tsaraba dashi?"


Kanta aduk'e tace ah ah ammi ai nafasa tafiyar ma gsky.


"da sauri tace meyasa?"


"Tace bbu komai"


Ammi tace wato yasmeen nikike jiwa kunya ko nauyi zance?"bazaki fadamun damuwarki ba?


Tana hawaye tace ammi wlh nahakura da tafiyarnan bazanyiba tunda adalilinta mijina na fushi dani ,gara nabarta tunda Wanda nike zaune karkashinsa ransa bayaso ammi gara nabi abinda yakeso kuma wlh har cikin raina banji haushiba,kuma da nasan hakan zata faru wlh bazanyi maganar tafiyarba amma dan ALLAH ammi kisanar da Sarki cewa nafasa tafiyar sai wani lokaci yanxun inada exams ne na manta nayi mgnar tafiyar..


Shiru ammi tayi tanajin tausayinsa yasmeen wadda cikin maganarta bbu rashin kunya ko bakar mgn gsky yarima ne kyautaba dukda shima sontane yasakashi kinson taje wani guri ta d'ad'e..


"Ahankali tace kiyi shiru kidena kuka kinji yasmeen?" kije kirarrashe sa kushirya zakije insha ALLAH, tashi yasmeen tayi tace to ammi ngd ,tafice had'e da dafe kanta dan yana mugun Sara mata...


     ** ** **

Yarima kuwa haka yyi wankan xuciyarsa bbu dadi,wani gefen kuma bayason kukanta dan yasan k'ila yanxun tanacan tana kukanta...


Haka yagama shirinsa ,cikin milk din shadda tasha aiki da Orange din zare ga  wani fitinan kamshi dke tashi ajikinsa ,yyi kyau saidai fuskar nan bbu annuri ko kad'an..


"Jiyayi bayasan cin komai Co's yasmeen d'in sa bata ciba,part din ammi yawuce."


Yana zuwa yaga ammi ta kallesa ta d'auke kai,afili yace yah salam ammi naga kema fushi kike dani menayi?"


Tsaki tayi tace bansaniba!shine kayi fushi da yasmeen duk ta shiga damuwa tace tafasa tafiyar,ka kyauta kenan?"


Me tace naji mata?"


Nan ammi tasanar dashi yadda ta takurata harta fadamata.


Ajiyar zuciya yarima yyi yanajin kaunar matarsa da wani sonta nasake shigarsa hade da tausayinta dan yana mamakin ita batayi fushi dashiba burinta shi yadena fushi da ita ...muryar ammi ta katsesa gun cewa to yanxun Dan ALLAH kaje ka rarrasheta Ku shirya kaji my son?"


Murmushi yyi yace to amminah yafita.


Part d'insu ya wuce ,kaitseye bed room d'in yasmeen yanufa,yana murd'a k'ofar yajiyo kakarin amanta a toilet,arazane yashige toilet din yasameta ta tallabe kai tanata kwaraya amai tana hawaye,kamar zata amaye abinda ke cikin cikinta baki d'aya...


da sauri ya tallabeta yanajin tausayinta ,sai sannu yaketa mata"


Tana idarwa yaruka dobo ruwa d hannunsa yana wankemata baki d fuska ,ita kuwa zai maida numfashi take..


Yana gama wanke mata ,yasabota kan kafadarsa ,shima duk jikinsa yabaci da ruwa,kan bed yazauna had'e da rungumeta ajikinsa..


"Ahankali tace Yayana pls kadai na fushi dani kada mala'iku su tsinemun wlh na fasa tafiyar."


Rufe mata baki yyi yace, baby nah na hkura ainadena fushin ,munshirya ko ?"aiyawuce kawaidai banji dad'i bne kada kisake kinji matata?"


Cikin dadi tace to mijina na gode insha ALLAH bazan komaba...


Fuskarta yad'ago yace to yimun murmushi! kallonsa tayi idocikin ido tayi masa murmushi hade da cewa my Prince 2milion bucket can not wash your love in my heart...

Cikin jin dad'in kalamanta yace thank you my real one I'm pround of you, you are my special one in my life...


Hade bakinsa tayi da nata, ta zura masa lallausan harshenta bbu gardama yacafke yana sucking...


Wai numfashi suke mayarwa ,yana k'ok'arin tura hannunsa arigarta...jiyyi tayi saurin zare bakinta dg nasa d gudu ta nufi toilet, asukwane yabita cikin damuwa had'e da tausayinta..


Kamata yyi har ta idar ,yataimaka mata ta wanke baki da fuskarta ya dakkota suka fito,kan bed ya ajeta yaciromata gown ta atamfa "ahankali yacire na jikinta yacanxa mata ..


Cikin tausayi ya shafa fuskarta yace my Princess meke damunki?" dama bakda lfy ne?"


Ahankali tace ah ah ,nidai kawai d'zun bayan nadawo dg gun ammi ina kwance naji tashin zuciya dama kuma kaina namun ciwo..


Lumshe ido yyi yace oh ALLAH yabaki lfy my Princess kamar ciwon yadawo kaina ,yafad'a cikin damuwa,wayarsa yafito ykira doctor khadija(itace likitar dke kulada duk Wanda bashida lfy amasarautar) yace gashinan yanxun zai kawo yasmeen batajin dadi.


Yana kashe wayar yaduka had'e da cewa yasmeen ta hau bayansa su tafi,cikin tsantsar mamakinsa da al'ajabinsa dan yau ta k'ara tabbatarwa kanta yarima yana mata SO bana wasaba kuma natane ita d'aya ,amma bazata yarda ba ga barori d bayi suna kallon su Aida kuny...katseta yyi da cewa kihau princess dina mana!


"Ahankali tace innaho amai zanyi kadai kamani muje,bbu musu yatallabeta suka nufi hospital din  dke masarautar ...


Babu bata lokaci ,bayan doctor khadija ta mata tambayoyi ta hau treatment d'inta..


Nan tabata wata roba tace taje tayo fitsari " tashi tayi dg kan cinyarsa ta nufi toilet ,shima yamike dan binta ,doctor ta tsaidashi..


Tana sha'awar yadda suke kulada junansu dakuma soyayyarsu.


"Bayan ta fito ,nan ta auna fitsarin atake tagane yasmeen na daukeka d ciki ,shiru tayi tace ta kwanta ayi mata scanning b musu ta kwanta akayi mata.


Murmushi doctor tayi dan cikin duka sati3 ne kacal.


Kallon yarima tayi da yatsareta da ido tace ....


Share pls

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿89&90


     Kallon yarima ta yi da yatsareta da ido tace to masha ALLAH Alhmdllh, yasmeen nad'auke da juna biyu na 3weeks....what...yarima yyi exclaiming, doctor tace yes ciki ne da ita...wani uban ihun murna yarima yyi had'e da sungumar yasmeen yad'agata sama yana juyi da ita yana rawar murna,cikin tsantsar farinciki yace ALLAH nagode maka da ka nunamin wannan rana princess yau masucemiki juya zasuji kunya...itama yasmeen farinciki ne kwance fal aranta da fuskarta ALLAH yabasu abinda sukeso sai godiya ,fuskarsa yake k'okarin hadawa da tata sai sabbatun farinciki yake ....doctor tayi saurin yin gyaran murya gudun kada ayi tab'argaza agabanta ,garama tayi masa mgn dan talura fitina ne dashi kada yamatsa mata cikin yazube.

"Kallonta sukayi ,murmushi tayi tace to sauketa kuzauna nayimuku bayanin yadda zaku kula da lafiyar babyn naku..

      " babu musu yasauketa yazauna ,tad'ale kan cinyarsa yayinda bakunansu sunki rufuwa".nantabasu shawarwarin kanyadda za'a kula da da lafiyar yasmeen abata duk wani abu datace tanaso namasu ciki,kuma su jinkirta yawan yin sex sai cikin yyi kwari .

"Sun gamsu sosai da bayaninta ,dg bisani ,yarima yace yabata kyautar mota tukwuicinta ne.rissinawa doctor tayi tana zuba godiya bbu iyaka..

      " ita kuwa Yasmin dama yaya lafiyar giwa tayi shagwaba da tab'ara bbu dalili Balle yanzun dake da  dalili,sai ta wani shagwabe ,shikuwa sai wani nan nan yakeda ita...

Wayarsa yafito had'e da sabar yasmeen akafad'arsa yasaka kira bbu bata lokaci nayi yyi sallama had'e da cewa tsoho mai ran karfe Kaine farkon yiwa wannan albishir dankuma kafi kowa cancanta ,yasmeen nada juna biyu... Wlhy kuwa ,eh to kafadawa wannan  matar taka kotabarmu musarara yanxun tasan yasmeen dina ba juya bace....dariya naga yyi had'e da cewa muna godiya dan tsohonmu ALLAH yabar mana kai."

     Kashe wayar yyi ,suka ida barin cikin asibitin ,part din ammi suka nufa."ahanya yace my Princess kuma mommy n babynmu me kikeso kici?"pls gayamun kin ji ,turo baki tayi tace nidai sai munje gun ammi nah".yar dariya yyi yace yanxun zankira umma da Omar har da ma bash nagayamusu nakusa zama daddy...cikin mamakinsa tace bash kuma?"yace yes labarin maitsawone saimun zauna zan sanar dke dan yanxun haka bash ne manager na gidan manki dana bud'e miki a shekaran jiya kema kirika Sana'a kitaimaki bayin ALLAH.. wani dad'i da farinciki Yasmin taji wai itace keda gidan mai nata na kanta shin meyarage mata zata nema aduniya?"bbu gashi kuma yau taga ne tanada ciki ita ba juya bace kamar yadda wasu ke cewa ikon ALLAH kenan.

"Ashe ko lokacin da ake mata gorin ma Ashe da cikin jikinta tunda yanxun dayin abun2weeks kuma ance 3weeks ne cikin..

" kara mak'ale yarima ta yi tace oh my Prince banida abinda zansaka maka da shi sai addua na gode sosai ALLAH yabarmu tare ..

Murmushi yyi yace ameen ai princess kinbiyani tunda kike dauke da baby nah ajikinki gudan jinina kingama min komai  fatana ALLAH yaraba lfy ,kuma kyautarki sai munzauna dan saina yimiki kyauta ta musammun keda hanan insha ALLAH, murmushi tayi tace um um my Prince basaikamun kyautaba abinda kamunma dnida family nah wlh yyi adena b'annata dukiya hakanan kaji?"

      hancinta yaja yace hmm princess kenan zan iya batar da abinda namallaka sbd ke ko kinmanta ke ba'amiki kyautar first night ba...dan haka sainami kyauta sbd farincikin dakika jefani..adedenan sukashiga parlourn ammi saicewa yasmeen ta keyi yaya yaskeni kada ammi ta gammu,dariya yyi yace ko agaban Sarki ne bazan ajekiba aiyanxun kina bukatar kula sosai hutuma zan d'auka a office Inxo inta kuladake ko tawan?"muryar ammi suka ji abayansu tana cewa oh my son yanxun dai bakada kunya ko?"sokake sageer yyi koyi dakai tunda shima bikinsa ya matso kuma suma anan zasu zauna...


"Murmushi kwance a fuskarsa yajuyo ,yayinda yasmeen ta rufe idonta sbd kunyar ammi,yace hmm ammi nah yau muna cikin farin ciki bazan taba mantawa da wannan ranarba dan yasmeen nadauke da gudan jinina ammi zaki sami jika dg gareni ammi kiyi murna kema yau munhuce haushin masu kiran yasmeen juyaaaaa!


,,,cikin tsantsar farinciki da murna ammi tad'aga hannunta sama tace Alhmdllh ALLAH mungodemaka Kaine maji rok'on bayinka ,Yah ALLAH ka k'arawa annabi daraja ..masha ALLAH yasmeen y'ata ....kasaukemun ita manah!


" bbu musu yasauke yasmeen suka zauna kan kujera,hannunsa mak'ale da nata."


Murmushi ammi tayi ganin yasmeen nasoke kai,alamar kunyarta takeji,tashi tayi tace kujira naxo bara naje nakaiwa Sarki d hjy rahama labari, kafin autocina sunadawo dg skul(Maryam d salim kenan)suma suji dan burunsu kenan".


Bayan ammi ta fita yasmeen ta aza kanta akafadar yarima "ahankali tace yaya zanci awara da fura sai tsire mai kulli....murmushi yyi yace to my Princess har zaki fara kwadayin masu ciki to bara na duba miki furar sauran kuma bari ammi tadawo yanxun,kinga dama cikinki bbu komai...


" tashi yyi yaje gun frige yadakko gidauniyar furar."


Yazo yazauna gaban yasmeen yahau bata abaki,kuma ba laifi tasha ,sosai goge mata bakinta yyi da tissue, yace sorry bara ammin tazo kona kirata?"


"da sauri ta ce ah ah"


Zama yyi had'e da Ciro wayarsa yakira,yah Omar ko gaisawa basuyiba yagaya masa,wani uban ihun murna yah Omar yyi yace to gashinanma tafe gidan ayi dokin babyn dashi ,cikinjin dadi yarima yace to my broth ,umma nanan?"yace kaf tajimu itama murnar take ,ganinan xuwa dama yaunadawo!yarima yace eh nasani rannan yasmeen tace mun kakusa dawowa shiyasa nakiraka da wannan Layin..


Sallama sukayi ,yakira bash da salis yana fadamusu,kowamurna yake da farinciki dasamun wannan karuwa tasu.


Bayan sun gama wayar ammi ta shigo da fara'arta,nan yarima yafad'a mata abinda yasmeen keso,nan tace to shikenan da kaina ma zanshiga kicin nayimiki abinda kikeso y'ata..


Yarima yaji dad'in hakan tabbas yasmeen ta dabance agun ammi dan inba Sarki ba bbu Wanda takewa girki ,shima sai in ranar kwananta ne."


Ammi na wucewa kitchen ,su salim da Maryam suka dawo dg skul,ko zama basuyiba,yarima yace yan k'annena antynku nada kuna biyu....


Wani uban ihun murna sukayi har Saida yasmeen ta to she kunnenta sbd kararsu,salim kuwa shoki yacigaba da diba yanajin dadi zai d'aaaaa! Shima tabbas ranar da aka sauka akwai buduri amasarautarnan...


Maryam cire hijab da d'an kwali tayi ta zauna gab dasu yarima cikin murna tace oh antynmu munji dadi wlh kai gsky sainayi party dama this month is my bath day month dole inyi party ko my salim?"


Salim dke rawarsa yace tabbas ne Anty Maryam...


Yarima dke kallonsu cikin jin dad'in yadda yan uwansa keson gudan jininsa ,yace kada kudamu zanbaku dubu dari biyar kuyi abinda kukeso yan kannena..


Cikin murna sukace mun gode yeeeeeeeeeeee!"


Salim bb kunya yawani rungume Maryam suna murnar yarima zai barsu suyi party su cashe kenan.


Yasmeen sai kallonsu take tana murna ,itama dan ta ji dad'in yadda suka nunamumurnarsu ga cikin dke jikinta.


Sallamar da yah Omar yyi ce ta tsaida Maryam daga radar datakewa salim akunne...


Shikuwa yah Omar wani mahaukacin kishi yatasomasa ganin Maryam jikin wani hartana masa rad'a a kunne kuma wai yarima nagani yakyalesu ,to wanene wannan kuma?"


Yasmeen data lura..


Hmmmm to kunji yah Omar fa..

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿91&92


Yasmeen data lura tsantsar kishin dake cikin idon yah Omar"ahankali tace oh salim saikace ba yayarkaba kamar k'anwarka!tafad'a yayinda take amsa sallamar yah Omar tana kallon yanayin fuskarsa. "

Yarima kuwa tashi yyi suka rungume junada yah Omar sannan suka gaisa ,Wanda yah Omar idonsa k'yam akan Maryam,dan yafahimci salim k'aninta ne bbu tazara atsakanunsu,cikin doki yah Omar bayan sun gama gaisawa yacewa yarima yah Ashman yah babynmu?"

Murmushi yarima yyi yace baby yana lfy yanama gaidaka....

      "dariya akayi gaba d'aya, salim dke kusada Maryam yagaida yah Omar ita kuwa Maryam tsintar kanta tayi da jin kunyar yaganta bbu d'an kwali da sauri ta duka ta d'auki d'an kwalinta ta rufe kanta dke da kitso shuku yyi kyau yazubo mata dan tanada gashi...niyar tafiya takeyi, da sauri yasmeen tace oh Maryam bazaki gaisheda da yaya Omar dinaba kenan?"

Juyowa tayi sum sum kanta akasa ,yayinda yarima yakalli salim yace oya jeka kawoma yayanku drinks bbu musu yatafi,Maryam kuwa kasa kallon yah Omar tayi dan jikinta yana bata ita yake kallo...ahankali tace ina wuni?"

Yar dariya yyi kafin yyi mgn ,ammi ta shigo parlourn da kuyangi biyu a bayanta suna d'aukeda plate2 d'aya shake yake da awara taji kwai ga wani bowl agefe da yaji ciki,d'aya kuma tsirena yasha kuli ga tumatar da cabbage samansa ..

      "Yasmeen da k'amshin yadaki hancinta ,ta lumshe ido tuni yawunta yatsinke" ammi tayi umarnin su ajiye gaban su yasmeen ,kallon yah Omar tayi cike da kulawa tace  oh bakin turai Kaine yaushe kadawo??"

Murmushi yyi yace yau ammi, yaduka yagaisheta,byn sun gama gaisawa take tambayarsa umma yace tana lfy..

Kallon yarima ammi tayi ganin yana k'okarin feeding d'in yasmeen tace oh son pls kabimun ita ahankali"murmushi yyi yace to ammi nah nan ta fita,yayinda salim ya,aje musu drinks shima yabi bayan ammi...

Maryam wacce tayi shiru kanta aduke,ganin su 4yarage a parlourn tayi saurin d'ago kanta tsab idanunta cikin idanun yah Omar.... wani yarrrrrrrrrrrrrr!"taji ta saurin rufe fuskarta da tafikan hannunta.....


"Kallonsu yasmeen yyi yaga hankalinsu naga abincin dasuke ci."


Murya k'asa kasa yace to tunda bazaki gaidaniba dawo nan,yanuna mata gefensa ,Nina gaida ke...


Cikin jin kunya tadawo gefensa,murmushi yyi yace my baby girl ina wuni ?ykk?"


Wani yanayi na jindadi Maryam ta tsintsi kanta wai itace ake kira da wannan sunan ,burinta shine tasamu irin kula da soyayyar dasu yarima da yasmeen sukeyiwa junansu Ashe zata samu oh a....katseta yyi yace bazakimun mgn ba?"


"Ahankali tace lfy lau alhmdllh".


Murmushi yyi yace amma ni miyasa baza'a kalleniba ?kina kallon wani gu daban kina mgn " pls kalleni!kallonsa tayi tasakarma sanyayyen murmushi shima yyi mata ,ahankali yace yanxun kije kicire yuni foam kidawo sai musake gaisawa ko baby nah? "


Mak'e kafad'arta tayi alamar ah ah


Lumshe ido yyi dan yana bala'in son mace mai shagwaba,cikinrarrashi yace oh baby kinaso mubata?"


"da sauri ta ce ah ah"


Yace to jeki canxo kayan ,bbu musu ta tashi ,jiki amace dan duk kalaman yah Omar sun kashe mata jiki..


Yana juyowa yakalli su yasmeen saiyaga itada yarima suna mgn kasa kasa suna dariya...


Matsawa yyi gunsu yace oh wannan dariyar da kukeyi dawa kuke ne?"


Sake ke cewa da dariyar sukayi,yarima yace da duk Wanda yatsargu da kansa....Sosa k'eya yyi yace oh iyayan baby kunacin abu bbu tayi to sainaci nima ai ammin bataku bace ku kadai,yafad'a had'e da daukar awarar guda yakai bakinsa,wani lumshe ido yyi yana jin dad'in ta dan yasacinta..


Shikuwa yarima da yaune yafaracinta shima dan yasmeen ta fara yimasa rigima yasakashi yaci aiko yaji da dadi yacigaba da ci..


Sake daukar guda yah Omar yyi,kukan shagwaba yasmeen tasaka had'e da aza kanta a kafadar yarima tace yaya kaga yah Omar ko?"zaicinyemun kaya in so yake yasaka Maryam ta masa mana...


dariya yarima yyi yace gsky broth zamu bata da kai ,kaida kazo tayamu rainon cikin da jinya saikuma karika Sata tanamun rigima gsky kabari...


Hmmmm ALLAH yah Ashman kashagwaba yarinyar nan da yawa ,yo tayita rigimarta mana sai me?


Sannan naji kince Maryam kai tsaye ko ?"bbu sayi kin kyauta kenan?"


Hararar wasa yarima yyi masa yace lallai kadama kaja inmammari Maryam din,aibazata sabuba zanma gayamata ko bayan aurenku dole tacigaba da kiran my Princess d Anty..


Kafin yah Omar yyi mgn su kubra da salis sun shigo parlourn ,nanfa fira ta kaure da hayaniya  duk sun cika ma ammi kunne datake bed room, fitowa tayi suka gaisheta ,cikin dan murmushi tace to iyayen babyn dke ciki ,kukoma part din Ku kuyi murnarku a can....dariya sukayi ,kubra tace ai ammi wani abu ma sai an haihu ,tace to ALLAH yasaketa lfy ,baki daya sukace ameen.


Tashi sukayi ,adede nan Maryam ta shigo cikin gown ta las green tayi masifar kyau dan ba laifi duka gidan mata tafisu kyau dg ita sai hanan.


Salim yana mak'ale da ita sun jero,inkika gansu bazakice kaninta bane,wani killer smile yah Omar yasakamarta azuciyarsa yace oh wannan yaro duk inda zata yana manne like da ita...

Su yarima kuwa fita sukayi zuwa part din su ,shikuwa yah Omar tsaya wa yyi harsu Maryam suka k'araso yakalleta yace my baby girl kinyi kyau...cikin jin kunya ta dukar da kanta,salim yaturo baki yace ni yah Omar banyi kyauba?"


Murmushi yyi yace oh sorry k'aninmu kaima kayi kyau wollah,dariya yyi yace yes ,amma gsky zaku dace dakaida twins sister na,nikuma kaga k'aramine banida budurwaaaaa!!


dariya sosai yaya Omar yyi dan yalura salim akwaisa d barkwanci,ita kuwa Maryam jin kunyar maganarsa tayi,ahankali yah Omar yace my baby girl miyasa baza kimishi budurwaba ?"


Turo baki tayi cikin shagwaba ta ce ,aiyarone"kuma bayason mata ko sunce suna sonsa...


Murmushi yyi yace ok muje to kimun rakkiya zan wuce gd ko?"


Cikin shagwaba had'e da yarinta tace to muje ka gaishe da mama nah ko my salim ?"tafada tana kallon salim..


,,,salim kuawa cewa yyi eh gsky bara naje nafara sanar da ita,yana fadin hakan yajuya yatafi..


Shikuwa yah Omar "Ahankali yakalli Maryam yace my baby girl pls kibari zanxo saimu gaisa kinga k'anannun kayane ajikina yanxun kinji?"


Kukan shagwaba ta saka masa ita ah ah suje kosu bata...


Shiru yyi yakafeta da idonsa yana kallonta ganin yadda shagwabar ta mata kyau...


Murya kasa kasa yace to muje ko,amma sai kinmun dariya!


Kallonsa tayi ,had'e dayin dariyar,shima ita yyi yace ILOVE U my baby girl ...


Lumshe ido tayi ,suka jera suna tafiya,ahankali yace ko bakya sona ne ?"


Rufe fuskarta tayi,hakan yasakashi yagane tana sonsa ,har cikin parlourn hyj rahama suka shiga ,samunta sukayi zaune kan kujera salim yyi matashi da cinyarta yanata tabararsa,sallama yah Omar yyi kansa aduke ,yaduka har k'asa yakwashi gaisuwa ...


Cikin sakin fuska mama ta amsa had'e da cewa Omar kazauna mana kan kujera kasaki jikinka ai nan gidankune ,yasu umman ?"

Murmushi yyi yace lfy lau alhmdllh.


Kallon Maryam tayi tace oh kinyi wani tsaye kije kikamasa ruwa mana..


Cikin shagwaba tace to mama salim yatadamun cinya manah..


Girgiza kai tayi tace oh ko ina kuke baza by dena shiriritarkuba ko?"


Sai asannan yah Omar yyi mgn yace oh mama dama haka suke wannan shagwabar, suna hawa cinya Manya dasu..


Murmushi mama tayi tace wlhy kuwa Omar kagansu nan haka suke matsamin nida amminsu da fitinarsu,amma ai basayi gaban yarima dan sunci gidansu...


Maryam data aje lemo tazuba acup ta mik'a wa yah Omar yasha,kadan ya ajiye gaban sa..


Mama tace kije kisaka ashiryomasa abinci....da sauri yace ah ah mama wlh alhmdllh na gode sosai, murmushi tayi tace hmm kunyadai kakeji Omar.


"Tashi yyi yace natafi ,mama godiya ta masa had'e da cewa yagaishe da Umma,yakalli Maryam tace kije kirakasa mana.,,,,


Fita tayi dan rakasa.


Mama tayi ajiyar zuciya dan har cikin rants tayaba da tarbiyyar Omar fatan ta shine ALLAH yasa alkhairi ...


Bangaren su yasmeen kuwa...

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's )


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿93&94


Bangaren su yasmeen kuwa, suna can fira kawai suke da yadda zasu yita hidima inta haihu ,su kubra sunci sunsha itada salis da sauran abokanan yarima.


"Suna nan zaune saiga Maryam d yah Omar".


Murmushi yarima yyi yace oh broth badai tafiya zakayiba?"


Yah Omar yace eh lafiya zanyi sallama nazo miyi,shagwaba yasmeen ta saka ita ah ah bazaitafiba,girgiza kai yah Omar yyi yace hmmm aisaikiyita yi nikinga tafiyata ,cikin shagwaba yasmeen tace wato kasami Maryam ko ?"shine kadaina damuwa dani, dariya yyi yace eh,harararsa yarima yyi yace hmmm munbata dakai ,sudai su kubra dariyarsu suke d haka yah Omar yatafi gd cike da shaukin k'aunar Maryam d'insa.,,,,


Suma su salis basubar gidanba Saida aka kira magrib suka fita tare da yarima yawuce masjids..


Hmmm awannan dare yasmeen tayi baccin farinciki da jindadi Wanda bata tab'ayiba ,cos Daren nadaban ne arayuwarsu taga abinda ake kira gata agun yarima ,motsi kadan yace my Princess mekikeso ?"yah baby nah yake?"zaki sha kaza ko zakici kaza?"kulawa sosai yarima yabawa yasmeen had'e da lallabata kamar kwai...


        ** ** **

Washe gari byn sun gama shiryawa,Wanda yarima da kansa yyiwa yasmeen wanka da ruwan dumi waibayason  ta wahala itada babynsu,koda sukazo yin break kuka yasmeen ta saka masa ita bazataci komaiba sai tea da wainar fulawa".cikin rarrashi yace my Princess kinga wannan kukun be iyataba bara naje nayiwa ammi mgn tamiki ko?"kuka tafashe dashi... da sauri yajanyota jikinsa ,kansa agefen kafadarta yace menene kike kuka?"fad'amun kinjiko?"ahankali tace ni um um kai nikeso kamun da kanka...zaro ido yyi yace nikuma !aikinsan ban iyaba ko?"cikin kukan kissa tace muje a kitchen saina nuna maka ,yadda zakayi."tashi yyi ganin tana shirin masa kukan rigimarta da bayaso ,had'a mata tea din yyi mai kauri a cup sannan yasabeta a kafad'a suka nufi kitchen.

      Kukun na ciki yana goge goge yana ganinsu yaduk'a yakwashi gaisuwa yabar kitchen din."

Kujera yarima yajawa yasmeen ta hakimce samanta tana kurban tea d'in ta,nan tace yadebo fulawa da ruwa bbu musu yadebo tashiga nuna masa kaf yadda zayayi kuma yyi ,saidai tun gun yanka albasa yafara shan wuya idanunsa sai hawaye suke,sannan ya yanka tarugu ciki k'anana ,yagama hada komai sauran tuya nan tace ya kunna gas..


"Bayan ya kunna tace ita da pripan zai mata tuyar bbu musu ya aza pripan din kan wutar."


Tana dg zaune ta na kallonsa ,tanason yin dariya amma ta to she bakinta,ganin yyi wuri wuri dashi basabonba sai zufa yakeyi ,manja yazuba bayan yyi zafi yazuba kullun fulawar,nan tafara soyuwa ,sai ihu yasmeen keyi ita yyi sauri yagama taci babyn sa yunwa yakeji aisaita rud'asa gun juya wainar yasaka lallausan hannunsa aiko yad'askane atake hannun yyi jajir dama ga zunga yana masa dan ya yanka attarugu be wanke hannunba da albasa...


Yasmeen kuwa dukewa tayi tanata dariyarta ta mugunta dan sak abinda yyi mata a farkon zuwanta gidan yafado mata,wato guga da chakol da yadda taita d'askane hannuwanta aigashi nan shima yaji yadda akeji...kallonsa tayi taga yabata fararen kananun kayan dke jikinsa d fulawa had'e da manja..


"Murmushi tayi ,azuciyarta tace oh yanxun in kuyangin nan suka gansafa?"


Kallonsa tayi tace my Prince ka gamane?"


Cikin sauri bawan ALLAH yace ah ah sauran kad'an ko inkawo miki wacce nafara gamawa?"turo baki gaba tayi tace nidai um um,murmushi yyi yace to maman baby yi hkri saura kadan,ida shanye tea dinta tayi sannan taje ta rungume sa tabaya tana kukan shagwaba,ida kwashewa yyi yakashe gas din had'e da juyota gabansa ,hannunsa guda rike d plate din wainar yace muje ko?


"Make kafad'a tayi tace nika wanke hannunka tukum,bbu musu ya aje yawanke hannunsa Ta's Wanda yyi jaaa duk yadaskane g xingar dayake masa,kallon kitchen din yasmeen tayi taga duk yarima ya hargitsasa..


Hannunta yaja suka nufi parlour sai wannan lallabata yake, yazauna had'e da azata saman cinyarsa yarika bata yana lallabata, itakuwa saici take tana lumshe ido dan ta yi dadi sosai..


" gani tayi yaki ci,"ahankali tace yaya kaci mana girgiza kai yyi yace ah ah banma taba cintaba tunda nike,ai ihu yasmeen ta saka fafur bata yardaba,shikuwa bawan ALLAH yace to kidaina kukan zancu ai,akan dole yazauna sukaci ..


Suna nan saiga ,su Maryam d salim ammi ta aikosu da basket ,dke dauke d farfesun kaji ,da tuwon samanvita miyar danyar kubewa,sun sha mamakin ganin yarima haka,juyawa sukayi ganinsu haka musammun da yasmeen ke zaune saman cinyarsa suna firarsu ta masoya..azuciyar Maryam tace hmmmm nima haka zanyi wa yah Omar dina ...yarimane yyi musu mgn had'e da cewa su aje su tafi,yasmeen tarada masa akunne ita um um yabarsu ,yaje yyi wanka yacanxa kaya, tukum inyadawo sa tafi..


$suna niyar tafiya yarima yatsidasu,suka dawo,tashi yasmeen tayi dg jikin sa ta bud'e koolas din,lumshe ido tayi ganin wannan tuwon,wani son ammi d kaunarta taji yasake shigarta..


"Kallonsa Maryam tayi ,tace gsky ammi nah tanaji dani,dariyasukayi suka gaida ita had'e da tambayar babyn su,tace yana lfy,nan suka fara firar yadda bath din Maryam xaikasance dazasuyi jibi...shikuwa yarima ciki yawuce dan shiryawa."


Agogone yyi kara alamar 12:00daidai,alokacin kuma hanan d twins sukashigo parlourn, da ihun murna suka fada jikin yasmeen, salim kuwa hada rai yyi yace kai sarakan surutu kubi mana ita a hankali ba ita d'aya bace ,kada kufadawa babynmu..


Harararsa yasmeen tayi ,azuciyarta tanajin dad'in yadda dangin mijinta ke dokin cikin dke jikinta,ta ce ni karabu da su,zama hanan tayi tace ah ah Anty d gskiyarsa ai,bayan sun gaisa ,itama hanan sai murna take dan dama ammice ta sanar da ita, yayinda su twins sai surutu sukewa yasmeen had'e da tambayarta,wai zata haifi baby yazama kaninsu?"kuma zata basu baby ?"itadai murmushi take sukuwa su Maryam d salim nabasu amsa,ana haka yarima yashigo parlourn d gudu twins sukaje sukayi hugging dinsa suna dariya,sabarsu yyi yana juyi dasu ,yazo yazauna gefen yasmeen suka gaisa d hanan ,tayi masa murnar samun k'aruwar da yayi....


Nan yace mummyn twins ,dama kuwa zanje daa gidanki ,amma tunda kinso shikenan,dan murmushi tayi ta ce oh yaya tunda Anty yasmeen ta zo gidan nan bakasake xuwa gidanaba!murmushi yyi yace zamuje nida ita ko my Princess, yasmeen tayi y'ar dariya yace eh harma kigaji dmu,dariya akayi baki daya....


Yarima yatashi yashiga ,ciki bbu jimawa yadawo da keys din mota yabawa hanan kyauta halak malak dinta,ihun murna tayi kamar wata yarinya tanata jin dad'i had'e da yimasa godiya dan dama tanason acanza mata mota,cikin murna ta nufi part din ammi..


Su Maryam ma suntayata marna,nan suma yabasu kudin da yayimusu alk'awari dan suje suyi shopping din kayan yin bath din..


Bayan duk sun fita ,yasmeen tayita masa godiya da addu ar sake samun bud'i adukiyarsa ,Wanda ba karamin dadi yarima yajiba ..


Rungume yyi ajikinsa ,yana shakar k'amshinta ,anan yake labarta mata yadda bash yashiryu da yadda sukayi da salma har ALLAH yakubutar dasu dg sharrinta..


Hamdala yasmeen tayi tace ALLAH yak'ara tsaremu,yace ameen..sageer ne yyi sallama yashigo parlourn dan dawowar kenan dg Dubai yahado lefe na bikinsa Wanda da tuni anyi(kiddinaping din yarima da akayi yasaka aka daga bikin)shine mama ta sanar dashi yasmeen Nada ciki yazo tayasu murna..


Sallama tyi yarima ya mike suka rungume juna,cikin farin ciki yah sageer yace oh yaya Ashe mun sami baby ?"


Murmushi yarima yyi ,kallon yasmeen yah sageer yyi datake gaisheshi ,ya amsa had'e da cewa maman baby ya baby nah yake? "Tace lfy "yace to ki kulamun dashi pls,itadai sunkuyadda kanta take ,yarimayajashi suka zauna yake tambayarsa saura sati nawa bikin ?"yace2,firarsu suke Wanda duk firar ta babyn daza ahaiface  ...wayar yah sageer tayi ring in bbu bata lokaci yadaga ganin sweetynshi ce,hans free yasaka wayar dan su yarima suji.


Taslim(wato amaryar sageer)tace my blood Ashe matar yah Ashman cikine da ita, murmushi yyi yace eh wlh ,cikin tayasu murna race gsky naji dadi kace inatasu murna ina gaida babynmu da mominsa....da sauri yasmeen dke murmushi race aiko gamu muna amsawa kuma babynki yace fushi yake dke saikinxo zai amsa gaisuwarki...da sauri taslim tace oh my blood Ashe kuna tare ?" Har naji kunya d'it yakashe kiran..


Murmushi yarima yyi ,Wanda har cikin ransa yanajin Dadi d farincikin ganin yadda danginsa ke nuna farin cikinsu akan gudan jininsa ALLAH dai yanuna musu ranar da yasmeen dinsa zata Haifa masa babyn sa ,ameen...


Kiran sallar azahar yasakasu mikewa suka wuce masjid...


        ***

Bangaren salma kuwa...

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


Wannan page din nakune ,mmn fareesa fans page&awesome fans club kuyi yadda kukeso dashi kuna raina ina mugun jidaku over😍😍


Ina me bawa masoyana hkri aduk inda kuke na rashin jina kwana2inada uxurine nagode, masu zagi kuma na gode😂dan kunragemun xunubi kusani zagi ajinina yake be rageni sai kari ,grps na rufe bbu  yadda kuka iya dani saidai zagin nan kadai....


🅿95&96


Bangaren salma kuwa jiki ba kwari, tashige motarta ta nufi gd.

Saidai maganganun da yarima yagaya mata suntsaya mata arai da kuma bash yabata mamaki dukda batasanshi amma Wanda yahadata dashi yasanarda ita dan iskane na karshe."

      Ashe kuma yashiryu ,ita haushinta daya maganganun da yarima yagaya mata agaban bash yak'ara xubda mata kima, lallai Ashe duk abinda mutum keyi ko mekyau ko marar kyau,zaibika ko bayan kabar abun nan..

   "Jiki b k'wari ta iso gd ko abinci bataciba ana gama isha 'I tayi bacci bbu yi salla, dan dama bayitakeba." rabon datayi tama manta"

       da misalin karfe 3:00am salmace sai juye take kan bed idonta arufe ,tayi sharkaf d zufa ,kuma g hawaye na zuba....xuwa can tafara ihu tana cewa wayyoooooooo!

ALLAH nabar lesbian ,bazan sakebaaaaaaaa!


Bude idanunta tayi ta tashi zaune ,sai zare ido take tayi bala'in tsorata, afilili tace oh ni salma meke shirin faruwa dani?sai takama hawaye had'e da cewa dama haka akema masu lasbian azaba d marasa yin sallah oh nashi ga ukkunaaaa!sai waige waige take da gudu ta fito tana ihu hade da kiran mommynta."

Kicib'us sukayi d mommin da sauri ta fada jikin mommy ta na kuka mecin rai jikinta sai rawa da kirma yake".

     Itakuwa mommy cikin damuwa had'e da tsorata d ganin yadda ya'rta taburkice alokaci guda ,sai jijjigata take tana tambayarta lfy ?meke faruwane?"

Kuka kawai take taje mommy muje daki namiki bayani !ba musu ta bita har bed room ,bayan sun zauna cikin kuka ta sanar da mommy cewa tana lesbian kuma bata sallah...salati mommy ta yi, saikuma tafashe d kuka tace oh ni Habiba na cuci kaina nabatamuku tarbiya ta hanyar sangartaku kuyi yadda kukeso gashi kin lalace wai ko sallama bakyayi..


"" salma wacce kanta ke duke ,ta d'ago tana kuka tace yanxun nayi mafarki anamun azaba akabarina d macizai d kunamu ga duhu d zafi ga wasu irin hallittu nadaban ,kuma ana mun azaba d wuta sbd rashin yin sallah, wlh mommy na tuba nabi ALLAH nabiku.."


Ajiyar zuciya mommy ta yi tace to shikenan tunda kin shiryu kiyita istigifari ALLAHU GAFURUR RAHIM ne amma pls in daddy ki yadawo kada kisanar da shi kinji?tunda baya gari "


"Tace to"


Mommy ta ce yanxun kije  ki kwanta kafin asuba tayi,cikin tsoro tace ah ah mommy muje part din ki ,nan tabita sukaje...


Washe gari saida mommy ta koyawa salma alwalla d yadda ake sallah sbd ta manta.


,,,,acikin kwana biyun salma tayi bala'in yin sanyi ko mgn ba sosai takeyiba ,gashi tashiga islamiya ta matan aure anan anguwarsu burunta yanxun tayi aure bautar ubanjiji,sannan kozata fara aiki..koda daddynta yadawo shikanshi yaga canji atare da ita g islamiya tashiga Wanda yaji dad'in hakan sosai..


"Tun lokacin da salma ta shiryu ta dena amfani da layinta ta rufe dg baya kuma ta bude ta fidda number ta bash ,sannan ta karya layin tacanxa wani,saidai me ?tarasa dalilin dayasa ta cire number bash ta saka abason layinta.kuma take yawon tunasa....

  


   ** ** ** ** ** **

Su yasmeen kuwa sati biyu kenan da gane tanada ciki ,amma kullum gidan nan cike yake da jama a dangi da abokan arziki zuwa tayasu murnar samun wannan ciki." baba mlm har gd ya aiko da rubutu ajarka yasmeen ta yi ta sha kullum safe da rana,da ya kare asanardashi yyi mata wani insha

ALLAH zata sauka lfy..

     Uban gaiyar kuwa wato yarima saida yyi sati d'aya baya zuwa office yana lik'e da princess dinsa kuma mmn babyn sa,saida jama'a suka matsa tukum yakoma office sbdasu son ganinsa ko yataimaka musu."

Suma su salim d Maryam bayan sun yi bath day dinsu ,ai nan part din yasmeen suka tare ana rainon babyn dasu ....ayanxun haka shire shiren bikin yah sageer ake wadda yau akeyin kamu gobe deenar ,kuma a gobe hjy babba zatazo taga yasmeen tazo biki....


"" yasmeen ce tsaye ,ta kalli agogon hannunta taga 11am saura minti15amma Maryam shiru batadawo tazo ta sanar da ita tazo ayi mata kunshi d kitson biki.",,

Zama tayi gashi dama tanajin haushi yarima yyi mata wayo tayi bacci yyi tafiyarsa...k'arar bude k'ofar ne yasaka ta kallon me shigowa,maryamce, hararar ta yasmeen tayi tace shine Kika yi zamanki ko?"

Murmushi Maryam tayi tace sorry mmn babynmu"kixo muje ayimki lallen d kitson ni sai anmiki za'amun lallen ,bazanyi kitsoba saloon zanje yanxun..yatsina fuska yasmeen tayi tace naji muje!

Murmushi Maryam tayi tace hmmm nifa yanxun Anty ce saina gayama yah Omar nace kina yawan aikena,dariya tayi tace Kisa niya ai,abunda ma bazaizoba gun kamun."

Turo baki Maryam tayi tace lah Anty yace zaizofa pls d gaske kike?"dariya yasmeen tayi jar beautiful point dinta ya lutsa tace tsokanarki nake ...ihun murna Maryam tayi tace wlh da har najini kamar marar lfy,tafad'a yyinda sukabar parlourn ,suka nufi part din ammi, ahanya Maryam kesanar d yasmeen gobe hjy babba zatazo,shiru tayi batace komaiba, amma cikin xuciyarta bataso zuwan wannan fitinannar tsohuwarba...


"Suna isa suka sami parlourn du baki yan biki da yan'uwa,zama yasmeen tayi yayinda me kitson ta matso dan farawa yasmeen ga maiyin lalle gefe itama zata mata ga kuyanginta agefenta ko in tana buk'atar wani abu.,,,,


Bayan yasmeen ta zauna sun gaisa da mutane ,lura tayi da wata Budurwar ,amma dg ganinta ba yarinyabace sai wannan hura hanci take tana shan k'amshi tayimata k'uri da ido,itama yasmeen kicin kicin tayi da fuska dan bata d'aukar raini wlh gun kowane sakarai..


" har anfara tsagar kitson tace adakata"


Ta shi tayi ta bi bayan Maryam dazata tafi gun saloon ta tsaida ita sukatsaya gefen hanya..


"Ahankali tace Maryam waccen me light blue in atamfar wacece?"


Tsaki Maryam tayi tace ,y'ar kanin ammi ce itawai yaya Ashman take so.....what!


Yasmeen ta katseta tana zaro ido dan wani mugun kishine yataso mata ,dariya Maryam tayi tace maida wuk'ar wlh yaya bayasonta ko kad'an ke ko fuska baya sakarmata itada yayarta sukazo yau gun biki nasan k'ila suyi kwana3,sunanta elham..


Ajiyar zuciya yasmeen tayi tace naga sai wani harara ta take,Maryam tace k'ila haushinki tajeji,yatsina fuska yasmeen tayi tace hmmm zankuwayi maganinta wlh dan my Prince na yasmeen ne ita daya."


Murmushi Maryam tayi tayitafiyarta abunta ,itakuma ta shigo ciki aka fara mata kitson d lallen .


"Kadan kad'an ammi ta lek'o tazo gun da akewa yasmeen Kitso tayi ta tambayarta metakeso?" Zataci wani abu?"


Saidai tayi murmushi cikin jin kunya tace ah ah.


Ita kuwa elham dayake zaune kan kujera tana kallonsu kuma tsab yasmeen ce matar yarima duk da basuzo bikinba sbd tana kishi kuma ko yanxun tana kan bakanta na sonshi..


Tayi shiru duk da ta tsorata da yadda taga kyawun yasmeen ,amma wani gefen na xuciyarta tanajin dad'in ance ai bayasonta akayi auren dan haka ,afili tayi doguwar tsuka tace hmmm aikin banxa cusa kai ba kwarjini Wanda akeyi danshi bedamu d mutumba,shara tafisa daraja ....


"" shiru akayi mutanan dke dakin suna mamakin ta todawa take ?Wannan maganar."


Yasmeen kuwa tsab tagane da ita take ,murmushi tayi ta kalli agogo taga befi awa guda yarima yadawoba ,tasan dayaje part dinsu yaga batacan nan xaixo,azuciyar ta tace zanbaki mamaki yarinya..


Tashi tayi tace wa kuyanginta suje a wanke mata kunshin tayi sallah dg baya a ida kitson,bbu musu suka bita.


Bayan anwanke tayi sallah tadawo aka cigaba da yarfamata kananun kitsonta da yyi masifar kyau yazubomata agadon baya..


Kad'an kadan ta duna agogo ,karfe 2:26pm aka gama kitson tasan yarima na hanya,sallamar kuyangin tayi da masu kitson,parlourn yarage dg ita sai kuyangin ammi d ilham sai wasu baki su2adedenan Maryam tashigo tadawo dg gun saloon,tana faraa tace Anty g yayacan yadawo b....baya idaba yarima yashigo cikin parlour ..


Tashi yasmeen tayi tana turo baki ta juya bayan ta ...shikuwa bawan ALLAH bedamu da mutanan dke parlourn ba ta yasmeen kawai yakeyi  ,da sauri yasaki jikkar hannunsa murya asanyaye yace my Princess waya tabamunke ?"kike fushi haryashafeni.


"Nufarta yyi tana janyota jikinsa sai shagwaba take ta rufe ido ,d'agoya yyi fuska bb walwala yakalli Maryam d kuayangin dke parlourn atsawace yace Ku fadamun waya batarabun raina rai ?" Ko yanxun Ku fuskanci Bacon rai...


Ita kuwa elham mutuwar zaune ta yi tana kallon ikon ALLAH ,lallai anya mutumin nan haka ta bassa?"Amma kuma akwayar idonsa tagane son tane kwance ciki..


Yasmeen kuwa ganin zaitara mata jama 'a acikin taron yan biki tasa tafad'a jikinsa tayi masa rad'a ,dan dama abinda takeso elham ta fahimta kuma ta fahimta..


Ita kuwa Maryam tsab tabani yasmeen amma sai waske d cewa k'ila taya bananba gsky Dan bbu Wanda ya isa yabata mata rai ina agun banganshiba ,inafatan katafomata d tsarabarta?"


Murmushi yyi yace eh my sister naji dad'in yadda kike kulamun da antynki ,zo muje namiki kyauta ...


Ihun murna Maryam tayi tace to taya muje natake muku burki daddyn &mommy n babynmu ,murmushi yasmeen tayi suka nufi k'ofar fits asannan yarima yaga yayar elham da wata kawar ammi suka gaisa ko elhm din be kallaba kuma yaganta..


Ficewa sukayi...


Kuyi hkuri da typing errors d spelling mistake, bana editing nagode..

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


Wannan page din nakine maman khadija kiyi yadda kikeso dashi ,nagode sosai da kaunarki gareni anatare🤝🤝


🅿97&98


"" ficewa sukayi  dg part din suka nufi nasu,awaiting parlour suka sami lodoji guda biyu kan kujera ,d'aya yarima yadauka yaba Maryam ,baki washe takarb'a had'e da cewa ngd sosae yaya ALLAH yasauki antynmu lfy .

     "Yar dariya yyi yace ameen yah ALLAH" nan ta fice ,kallon yasmeen yyi wacce sai turoba ki take gaba..murm umishi yyi yakalli hannayenta da santala santala kafafunta ,afili yace wow my Princess masha ALLAH gsky yyi kyau lallen nan ,wace tamiki shi inmata kyauta ?"xo in gani mana,mak'e kafad'a tayi ita bazatazoba."

Yar dariya yyi yace niko big baby ?"yana nuna kansa ,dariya yabata aiko ta dara had'e da fadawa saman cinyarsa ,lumshe ido yyi dan dama yana jinsa cikin buk'atauwa tunda akace yasmeen nada juna biyu yau 2weeks besake yin sex da itaba."

     "Ahankali yace my Princess nayi missing naki sosai" sake shigewa jikinsa tayi,yyinda hannunta na cikin nasa yana wasa dasu dan lallen yyimasa kyau.

    "Murya kasa kasa tace nima haka ai yanxun kadawo muna tare har zuwa lokacin da zamu tafi gun kamun amarya ko?" yatsina fuska yyi yace kamun amarya fa kikace Aida kunya naje yana k'anina kuma kema bazakijeba gsky sbd bazan iyaba kawai wasu gardawa su kallemun ke aidasake wlh zan iya k'walkwalewa mutum ido inyana kallonki....cikin shagwaba tace nidai um um tare zamuje ALLAH kuwa ,kana like dni ,ina like da kai kaji yaya..sinsinarta yake ,cikin wata murya yace um um ban yardaba....ihu takama yi d burgima ajikinsa wai ai babyn sa nasan yaje gun kamun uncle dinsa...shikuwa kamar wani yaro yace to my Princess tunda Small baby nah yanaso nahakura ...

Cikin jin dad'in maganarsa tace yauwa kokaifa!muje kayi wanka...am inama tsarabata?"yar dariya yyi yajawo ledar dke gefensa yace gashi hade da zame d'an kwalinta yana yaba kitson da akamata."

Ledar ta bude dan k'waleliyar kaza ce gasassu guda biyu g ice cream nan sukaci sukayi kat had'e da aza drinks sama ,janta yyi wai suje suyi wanka.

     "Bbu musu ta bisa dan yanxun mugun shagwaba ta yake da kansa yyi mata wankan ,tarigasa fitowa bayan ta gama shafa yafito ,akuma lokacin wayarta tayi ringin,d'agawa tayi ganin maryamce nan naji tace ok gani nan xuwa.kallon yarima tayi tace yaya bara naje ayimun kwalliya..lura tayi yawani yi kicin kicin d fuska bece komai na ,shiru tayi itama,kallonta yyi yace kije mana.. "Ahankali tace yaya nafasa naga kamar ba kaso dama sbd kai za'amun tunda bakaso inaga abarshi dama akwai zama wlh.tafad'a fuska sake dan ta lura kishine yasashi yin haka...shikuwa tausayinta yaji ganin amaganarta bbu tsiwa ko rashin kunya ,shiyasa yakesonta sbd bata masa musu ko gaddama ," ahankali tazo ta yi hugging dinsa ta baya..


"Lumshe ido yyi jin nashanunta na gugar bayansa ,Wanda dama ko a toilet jurewa kawai yyi." Cikin kasalallar murya yace baby kije ayimiki kwalliyar ina jiranki  kinji?"ahankali tace to yaya amma wanne kaya zansaka?"be juyoba yace zan fito miki dasu,batace komaiba ta fita dan ta lura kamar yanada bukata ,dan ita tausayinsa takeji dan tasan yanada yawan b'ukata..


Haka taje akayimata kwalli me kyau bata haukaba su kabsu masu make up din sun yaba kyawun datayi ana idarwa ta nufi bed room tasami yarima yagama shirinsa cikin suit dark blue sunan kansa yasha gyara sai wani k'amshi ke fita ajikinsa tuni yasmeen kanta yafasu ganin mijinta yyi kyau kuma ko ina yakai mijin da za'a fita dashi tsara,shikuwa murmushi yyi ganin yadda take kallonsa yasan yyi mata kyau ,bude mata hannunsa yyi b musu tafad'a jikin sa cikin shagwaba ta ce yaya nidai banaso yan mata su kallarmin kai,kaji?"ta fad'a had'e da sakin kukan shagwaba ,cikin dubara d rarrashi yatayata tasaka kayanta fitted gown dark blue tayi rolling ,yo ai shima tuni kishi yataso masa dan inba Wanda yasan yasmeen tanada aureba to bbu Wanda zaiganta yace wai tanada aure sbd tayi kyau ga k'uruciyarta ta fito sak kuma bawai shigar yan mata tayiba dan ta rufe jikinta tafukanta d fuskarta ake gani..


"Shikuwa yarima duk gani yake mazan gun zasuyita kalle masa ita."


,,,hannunta Yakama zaiyi mgn wayarsa tayi k'ara ...bayan yyi sallama naji yace ok to gani nan xuwa yakashe wayar had'e da kallon yasmeen yace baby muje  cikin gida kutafi kedasu Maryam nasameku a can ana nemana a office.,,,


Make kafad'a tayi had'e da cewa niban yardaba!


"Hannunta Yakama yace kiyi hkuri nadawo kinji baby nah nemana akeyi ,kuma bansan sadda zan dawoba da sai mutafi tare " ahankali tace to yaya muje ,hancinta yaja yace to mmn baby ,murmushi sukayi atare..


Acikin parlourn ammi suka sami Maryam tana selfie tayi kyau cikin gown purple, duk mutanan dke gun kallon su yasmeen suke gani n kyawun dasuyi d matuk'ar dacewarsu.


Maryam naganinsu tace wow perfect mach,pls yaya bara na selfa Ku ,murmushi sukayi ,adedenan elham ta fito cikin gown maroon sai iyayi take ,idonunta suka haskomata yasmeen d yareema rungume d juna Maryam na musu pics ...


Tsaye ta yi ,can kuma tayi tsaki ta fita, Wanda yasmeen na lura da ita, wayar Maryam tayi k'ara ,dagawa tayi cikin kashe murya tace my heat beat ,eh ganinan xuwa nan takashe kiran tad'ago da niyar mgn taga yarima d salim sunmata k'uri da ido dariya tayi ta na Sosa kai, yarima yace oh wato gabana kike soyewa ko?"


Yasmeen tace hmm my Prince yah Omar ne muje kai katafi gunda  zakaje ,mukuma muwuce .


"Fitowa sukayi ,yayinda hannun salim na cikin na Maryam tana masa fada yyi tafiyarsa gun ball sai yanxun yadawo .


guards din yarima suka bude masa mota zai shiga, yahango yah Omar tsaye cikin suit purple yyi kyau nadaukar hankali sai jifar tauraruwarsa yaje da wani killer smile.


" karasowa yyi ,Yasmin tayi ihun murna, wani kallo yarima yyi mata ta nutsu ,gaisawa sukayi da yarima ,yajashi gefe yyimasa gargadin ga big babyn sa d small babyn sa yakula masa dsu kafin yazo."


Yasmeen kuwa mijinta tabi saida yyi mata kisses zafafa yatafi,had'e da Barin guard din da zasu bi yasmeen zuwa gun kamun.


Bayan yarima yatafi ta matsa kusadasu yah Omar d Maryam sai salim dke gefensu.


Murmushi tayi tace to kuxo muje ko!Maryam tace ai my man yazo d motarsa saidai muje d my salim gsky nishi zan bi..


Baki bude yasmeen ke kallon Maryam,shikuwa yah Omar murmushi yyi yace yes kuje keda my salim.


Turo baki salim yyi yace nagaji nima soyayya nike so wlh kowane nada burdurwarsa ni banida ita gsky Anty Maryam kiyimun budurwa kinyi?"


"gaba daya sukayi dariya ,yasmeen tace guards din su shiga motar subisu abaya ,sai sushiga motar yah Omar din."


Haka kuwa akayi ,Maryam ta hakimce gidan gaba ,yasmeen d salim gidan baya,saidai yasmeen tayi mamakin ina yah Omar yasamu wannan zuk'ekiyar motar...


Suna isa gun da za'ayi kamun...


Tofa 😍😍


Mmn fareesa ce✍🏻✍🏻

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


Wannan page din nakine salma Muhammad kiyi yadda kikeso dashi ina mugun jidake over😇😇


🅿99&100


Suna iso gun da za'ayi kamun sukayi parking, yesmeen d salim suka fito suka bar Maryam itada yah Omar dinta..

       "Masha ALLAH gurin kamun yyi kyau yasha decoration ", nan guard din suka fito yasmeen tace su tsaya anan ai suna hangenta ."

Salim kuwa yaji haushin barinsa da Maryam tayi ,kallon yasmeen yyi yace Anty muje ciki ko?" Bbu musu ta bisa suna hira suka shige cikin dan akwai mutane amma amarya d ango basu isoba...

      Kuri da  ido akayiwa yasmeen dan wad'anda basu santaba, sunyi zaton itace amaryar sbd tsabar kyawun datayi"...

Wani iri taji ganin idon jama a akanta ,awasu fararen kujeru salim yace su zauna.zama nta yasa aka gane b amaryar bace ...

gefenta ta kalla taga elham sai cika take tana batsewa yatsina fuska tayi ta cigaba da kallon wasu yan mata dke sanye d ankon kamun."

Nan suka fara fira d salim ,mutane nata shigowa can saiga maryam,ta shigo had'e da nufarsu,murmushi yasmeen tayi tace kungama love d'in? "Ahankali tace ah ah kixo ga amarya can d ango zasu shigo yanxun ,to mune zamu take musu burki kowace mace d partner dinta ke sai my salim yazama partner d'inki tunda yaya bayanan ...tafad'a tana dariyar tsokana,hararanta yasmeen tayi tace kin manta!aiba dauwama zayayiba yanxun zaidawo ,nakirasa yanxun bata shigaba nasan gunda yake bbu network me kyau ...

      " tashi sukayi ,ahanyar fita salim yace wato ni ga Wanda bashi akowa zakice nine partner d'in Anty ko?"dariya Maryam tayi tace sorry my salim ayau zanmaka budurwa kada kadamu..itadai yasmeen batace komaiba hankalinta naga jama'a da kuma ango d amarya dan ba karya sun wanku sunyi kyau d sheki ,yah sageer bakin nan yaki rufuwa..

Gefe suka bi,Maryam ta matsa kusada yah Omar dinta yana gefe tana gefe,yasmeen kuwa ganin mazan kurin subsaka mata ido yasa tayi gaba gabdasu yah sageer ta tsaya shikuwa salim ganin yasmeen ta bace masa yasakashi komawa baya dan MC  yafara bayani anutsu ,yanxun amarya d ango zasu shiga cin hole din ...

Muntasir wato babban aminin ango saurayi metashe da naira yahadu b laifi ,shine abayansu yah sageer sai aka kirasa a waya ,saiyabar gun yaje yyi wayarsa yagama yanufo gun ,by surprise yaga wata balarabiyar yarinya ko shuwa arap lolx..

gaba daya yasmeen ta tafi da imaninsa dan shi yacika jin kai yana ganin bbu wacce ta kai matsayin dazai kulata agun bikin kawai yaga yasmeen wacce betaba ganin bahausa kyakykwa kamartaba.lolx..

     Matsawa yyi gefenta beyi mgn ba yana kallonta akuma lokacin suka fara shiga hole din.. Itadai yasmeen taji k'amshin turare agefenta ,kawai ta juyo suka had'a ido da shi ,yasakarmata murmushi ,saurin kauda kanta tayi gabanta na dukan Tara Tara dan tasan yarima yaga haka akwai rikici dan fashima be raga masaba Balle wannan...

Suna ida shiga tayi maza ta nufi gun kureru ta zauna tana kallon masu shigowa...

     Shikuwa muntasir yakudurta zai shigar da kansa gun wannan xuk'ekiyar Budurwar,zama yyi yana hangen duk wani motsi nata.


Ita kuwa yasmeen ta na ganin kowa yazauna ya nutsu tasake kiran yareema cikin sa'a tashiga ,bbu mgn tasakarmasa kukan shagwaba rta me rud'asa ..."ahankali yace sorry mmn baby ganinan ina hanya kinji dena kukan..bbu dai Wanda yatakuraki ko?"yah Omar bemiki komaiba?"cikin shagwaba ta ce eh ni kai nakeso kazo yanxun ko wacce da mijinta ko saurayayinta bandani.....


Cikin rarrashi yace ganinan baby nah kinji ?"


"To tace ta katse kiran"


Adedenan kuma MCyabukaci ango d amarya had'e da abokansu d yan'uwa afito fili....


Nan kuwa yah sageer yafito rike d hannun tasleem ,nan aka tashi ana musu Barin kud'i .


Maryam dataga bbu yasmeen ta fito ta zo tajata ,suka shigo filin rawar ,ita kuma ta fito da kudi tanama yasmeen like...kafin yasmeen ta yi mgn taga mutumin d'azun namata lik'i da dollars...


Kokarin fita takeyi dg cikin filin rawar tana juyowa taga yarima yana nufosu ......


Hmmmmmm


Mmn fareesa ce✍🏻✍🏻

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN


Story &written by mmn fareesa


Wannan page din nakune masoya wannan novel naga comments bbu adadi agrps daban daban had'e da fatan alkhairi agareni ,musammun mmn fareesa fans page&mmn fareesa fans club nagode sosae.love u all💋💋🌹🌹


🅿101-102


K'okarin fita takeyi dg cikin filin rawar tana juyowa taga yarima yana nufosu..

"Wani mummunan fad'uwar gaba yasmeen ta ji", sbd yadda taga yarima fuskar nan tasa bbu annuri kamar be tab'a dariyaba kallo d'aya zaka masa ka gane ransa abace yake ,idanunsa sunyi jajir jijiyoyin kansa sun tashi rad'o rad'o sai hucu yake" domin tunda yashigo hole din idanunsa suka hangomasa wannan guy d'in yanama yesmeen lik'i zuciyarsa ke tafasa wani kishi mai zafi yataso masa..

      "Nufarsu kawai yakeyi zuciyarsa na cewa kawai ka kashesa ka huta...

Ita kuwa yasmeen jikin ta sai rawa yakeyi ganin yarima gab dasu..shikuwa muntasir ko ajikinsa dan besan abinda ke faruwaba ,k'okarin fito da wasu dollars yakeyi ganin na hannunsa sun k'are yaji anmasa wata irin fincika d sauri yad'ago kansa yaga yarimane yayan sageer...huci kawai yake kamar mayun wacin zaki yasaka hannuwansa yyiwa muntasir wata muguwar shak'a...cikin tsantsar bacin rai yace kai wawan inane ?" mekake nema agun mamatane?" dakake mata lik'i da dollars ,kokanaso kace banida arzik'in yimata lik'ine ?"iyeeeeee!yafad'a atsawace hakan yasa mutanan dke gabansu kallonsu..

   Shikuwa muntasir sbd shak'a ko mgn baya iyawa sai tari yake yanasa hannuwansa dan kwatar k'ansa...

Ita kuwa yasmeen ta tsorata gudunta kada yakashesa ya watsa taron bikin ...muryar salim taji yana cewa pls yaya sakesa kaga bikin d'an uwanka akeyi kada ka lalata masa taro ,in angama kamasa hukunci kaga hankalin jama'a yafara dawowa kanku...yana huci ya hankad'a muntasir har sai da yabige wasu mata dke gefensa,azafafe yaja hannun yasmeen kamar zai tashi sama sukabar hole din....

"Shikuwa yah sageer besan wainar da ake toyawa ba " salim kuwa fita yyi ganin ALLAH yasa yarima beyi bannaba."yanufi gunsu Maryam d yah Omar..


Yarima kuwa ko kallenta beyiba ,yabude mota yasaka yadawo yashige atsiyace yaja motar d mugun gudu ,guards d'insa suka bisu a baya da sauri ganin irin gudun da yarima keyi...


"tuk'i yakeyi zuciyarsa na masa zafi ,kaddai ace yaronnan son yasmeen yakeyi ", dole yad'auki mataki ,miyasa ma yaji maganar salim?" yakyale muntasir ,doguwar tsuka yaja beyi mgn ba dan kansa kewani irin Sara masa har bibbiyu yake gani,ga wani haushin yasmeen yanaji...


"Ita kuwa ta rakub'e tsoronta kada yahad'a da ita".


Cikin muryar kuka d kissa tace my Prince pls kayi hak...tsawar da yarima yyi mata ne yasakata yin tsit..


Ikon ALLAH ne kawai yakawosu gd yanayin parking yasmeen ta fito ta nufi ciki,shikuwa fita yyi zuwa masjid sbd anata kiran magrib...


Yasmeen kuwa duk taji bbu dad'i dama tasani batajeba ,gashi yarimanta na fushi da ita, jiki asan yaye ta wuce toilet ta yi wanka had'e da alwarla, tazo ta yi sallah,batabar gun ba sai bayan isha'i ..


,,,dukjinta take wata iri ga yunwa tanaji, amma ba abincinne gabantaba burin yarima yasauka dg dokin zuciyar da yahau..tunda tasan shima beci abincinba ,tashi tayi tasaka kayan bacci tafeshe jikinta d turare ta nufi part dinsa .,,,


Shikuwa be dawo gidanba sai bayan isha'i ,saidai zuciyarsa tarage rad'adin datake masa ,amma dai fuskar nan tasa ad'aure ,bath room ya wuce yy wanka ,bayan ya shirya yazo ya kwanta rigingine ya lumshe ido, bbu abinda yake gani azuciyarsa sai muntasir nama princess d'insa lik'i ....karar b'ud'e k'ofar yasakashi bud'e idanunsa yaga yasmeen ce ,maidasu yyi yarufe ,ita kuwa ta na shigowa tafad'a ajikinsa tasaki kukan shagwa...


" yana jinta tsab yyi mata banxa,Wanda yanxun haka wannan shagwabar tata tana tadomasa sha'awa dama yau yasha alwashin karb'an hakkinsa ,wannan abun daya faru yasakashi fasawa "ita kuwa jin yyi shiru ,alamar bazaice komaiba saitakama tarin k'arya da kukan kissa..d sauri yabude idonsa yarik'e mata hannu had'e da cewa menene kikeso?" fad'amun ko baki lfy ne ?"nakira dr, cikin shagwaba tace bakai bane kke fushi dani..


Hannunta yasaki,yajuya mata baya ,koda taga haka ,saita fara yimasa wasu irin abubuwa masu wuyar fad'i ajikinsa ...hmm tuni yasaki layi yabiye mata suka cigaba da romancing din juna dg nan komai yakankama ,Wanda yarima hardasu Sabbatu ,ammafa yasmeen ta ji ajikinta dan yarima nmj ne bakad'anba....


Bayan sun sami nutsuwa ,tana ajikinsa "Ahankali yace my Princess miyasa kikatsaya wannan sakaran yyimiki lik'i ?" Kina matar aure hakan yadace?"


"Cikin ladabi yasmeen ta yi masa bayani tun sadda suka hada ido da shi yyi mata murmushi har zuwa sadda taga yyi mata lik'i."


,,,ajiyar xuciya yyi yace shikenan dg yanxun nik'ab zaki ruk'a sakawa inzaki fita,sai inmuna tare ne mu fita baki sakaba ,gobe gun deenar kafata kafarki..


Murmushi tayi tace to nawan ,hakan yyi ni nama zata goben bazanje deenar ba..


Hancinta yaja yace to bazakijeba ,itama hancinsa taja tace ai my Prince dina baya mgn biyu ..


"Ahankali tace oh yaya wlhy salim nada hankali ,jiyadda asaukak'e maganar da yyimaka yasaka ka sakesa da kayi d'anyan aiki,ajiyar zuciya yarima yyi yace hmmm hakane gsky yyi kaifin tunani inmaryamce bazata iyaba ,nikaina dg baya nagane gara d nahakura kawai...


Firarsu sukacigaba da yi,kamar bbu abinda yatab'a shiga tsakanunsa ,dg hakan bacci yyi gaba dasu...


   ** ** ** ** ** **


Washe gari byn sun gama shirinsu ,yasmeen na rike da jikkarsa dan yomasa rakkiya ,suna hanyar zuwa part din ammi saiga Maryam ta fito ,tsayawa tayi ta gaidasu had'e da zolayar yasmeen ta na cewa shine jiya bbu ban kwana to suje ga hjy babba can tazo tace akirasu..


" yasmeen taji gabanta yafad'i amma saita dake".


Yarima kuwa b'ata rai yyi yace my Princess muje kirakani gun mota baza mujeba..da sauri ta katsesa d cewa ah ah yaya muje pls bbu matsala insha ALLAH, kallonta yyi dan dama sbd ita yafasa zuwa ,amma ganin tace suje b musu suka shige parlourn ammi..


Kan kujera suka sami hjy babba zaune ga kayan marmari gabanta da drinks da break fast ,su ammi d hjy rahama agefe d alama sun gama gaisheta..


Fuska bbu yabo bbu fallasa ta amsa sallamar su,nan suka gaisheta amutunce,kallon yasmeen ta yi tace ke zo nan!b musu yasmeen ta je taga me za'a mata ,wata y'ar kwalba tabata tace ungo kirik'a shafawa da dare da safe ko ina ajikinki harda bisa cikin insha ALLAH nmj zaki haifa,tafad'a tana washe baki..


"Kicin kicin d fuska yarima yyi yace oh hjy nidai duk abinda ALLAH yabamu inaso ai albarka akeso ba wani mace ko nmj ba ,ni wlh azab'ina ma nafison tahaifi mace..


Cikin mamaki sa hjy babba,ta yi masa dakkuwa tace karb'i nan gidanku nace ,to nmj zata haifa insha ALLAH.


" su ammi dai basu tankaba ,amma sun San abinda tafad'a be daceba ko a musulunce."


Yarima kuwa tashi yyi yakalli yasmeen yace my honey muje kinji?"tsaki hjy babba tayi tace aikin banza ,ke kuma ki yi abinda nace yar hocin kilbabbu wai hoci!hmmmm"shidai yarima bece komai ba suka ficewarsu sukabar part din...


Da dare kuwa haka yarima d yasmeen suka wanku ,kaya iri daya suka tafi gun deener yana like da abarsa ,kuma har sai da muntasir yazo har gun dasuke zaune yabasu hkuri akan avunda yafaru jiya ,yarima yace bbu komai yawuce ..


Haka aka ci aka sha ango d amarya suma sunsha kyau ,hade da shan pics da video har akatshi.


Washe gari d misalin karfe 11:00am daruruwan jama'a suka shaida d'aurin auren sageer isma'il Khalid d amarya tasleem Ahmed akan sadaki dubu100,taro yatashi lfy.


Hakafa su yasmeen sukayita hidima da jamaa har dare aka kawo wa sageer amaryarsa,yasmeen dg gaisuwa bbu abinda yasake shiga tsakanunta d hjy babba kuma magani yarima yakarb'e yazubar...


Salma ce zaune a bed room dinta...


Mmn fareesa ce✍🏻✍🏻AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's,)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


🅿103&104


Salmace zaune a bed room d'inta ,tayiwa wayarta k'uri da ido ga number bash tanaso ta kira amma kuma tanajin nauyi to inma takirasa tace masa me?"tabbas tasan tanason bash akan wad'annan dalilan",na farko itadai yanxun tasan b budurwa bace tarabu d budurcinta asanadin lesbian ,duk Wanda zai aureta bata da daraja agunsa."

       Amma in ta auri bash kar tasan karc e bazai goranta mataba zasu zauna lfy insha ALLAH. "

Saidai me?"ita gsky bazata sake furtawa wani nmj kalmarso ba dasunan tanasonsa sbd taga darasi ayarima.wata zuciyar tace hmmmm to kiyi amfani d damarki ta y'a mace kijanyo hankalin bash mana akan ki."cikin jin dad'i tace yesssss!nan tayi calling din bash....

      Bash dke kwance d'akinsa dke soron gidansu  kafin yafita gun aiki yaji wayarsa na ringing, dubawa yyi yaga bak'uwar number ",kamar kar ya d'aga sai kuma yad'aga yyi sallama

Jin muryar mace yyi tace slm bash ykk?"

Lumshe ido yyi dan yaji dad'in muryar saidai yasan kowacece tasansa,gabansa yafad'i daya tuna abubuwan dayyi abaya k'ila ma cikin abokan watsewarsane wata ta kirasa...muryar ta ta katsesa d cewa hellow kana jina?"

da sauri yace eh ygd?"amma bangane mai mgn ba?"murmushi tayi tace salmace!cikin mamakin kiranta yace ranki ya dad'e kwana2,tace alhmdllh dama nakirakane nabaka hkuri d kaida yarima akan abunda yafaru pls kace nace yyi hkri wlh natuba nagane rayuwa batada tabbas yanxun lahirata nake nema tayi kyau...ajiyar zuciya bash yyi yace to alhmdllh ALLAH ya yafe mana gaba d'aya, gsky naji dadi kuma insha ALLAH zangaya masa.."ahankali tace ok sai anjima ....d sauri yace wannan number ki ce?"cikin jin dadi tace eh new sim card dinane yace ok to ngd nan sukayi sallama....


Bash kuwa ajiye wayar yyi afili yace oh wlh da yarinyar nan zata soni dana aureta sbd dg ni har itadai munshiryu to inaganin anya zata soni?"dukda ni yanxun baza'a kirani talakaba inada rufin asiri na...ita kuma yar masu kud'i ce"wata zuciyar tace hmmmm saika gwada tukum inbata sonka saika hakura..


"Seving number ta yyi yaduba a what's app yaganta ,amma bata online murmushi yyi yakashe datar."


Itama salma anata bangaren bayan sun gama wayar taduba taga yana what's app,amma baya online ,addu arta ALLAH yasa bukatatta ta biya.,,,,


***  *** *** ***


Yasmeen ce a kitchen tana girkawa yarima tuwo dan yanada son abincin gargajiya ,hartagama komai ,miya zata kad'a sai sauri take sbd yakusa dawowa ,tana cikin kad'a miyar taji anyi hugging d'inta ta baya ....murmushi tayi dan tasan yarimane,kansa ya aza bisa kafad'arta yace mmn baby yunwa nikeji"ahankali tace sorry daddy baby yanxun zakayi lunch shima babynka yunwa yakeji..


Tayata yyi suka kwashe komai suka kai atsakkiyar parlour suka ajiye sbd yasmeen batason zama a dining area.


Serving d'insu tayi ,suka faraci sai santi yakeyi ,tana masa dariya.....turo k'ofar akayi juyowa sukayi hjy babbace ta shigo, haransa tayi tace to shanyayye mijin tace kananan lakafe to ni natafi gd sai inmatar taka ta haihu zanzo insha ALLAH. "


Murmushi yarima yyi yace hmmm hjy kenan kinmanta ai kafin tace nake yin abu ,dan haka sai ki kirani mijin kafin tace ko?"tsaki tayi ta hararesa ,had'e d kallon yasmeen wacce kanta ke duk'e tace keeeee!bansan muna funci Nina tafi gd sai kin haihu tukum zan dawo,kin wani duke kai kinadai shafa maganin dana baki ko kuwa?"da sauri yasmeen ta d'ago fuska asake tace eh ALLAH yatsare kigaida gd d alhj tsoho....


Hjy babba tace hmmmm duk zasuji nasan murna kuke zantafi ko?"to ai zandawo....da sauri yarima yace pls kada kixo kinji?"baki bude take kallonsa ,d mamaki wai kada tazo oh,cikin fad'a tace kada nazo ko?"to sainazo aikin banxa aikin wofi bbu yadda kuka iyayi dani dole ak'yaleni xuwa kuwa sainazo nagyarawa marasa ji zama ,tana fadin hakan fuuuuu ta fita.,,,,


Murmushi yarima yyi afili yace agayas can dai ai wlh naji  dad'in tafiyarki wlh ,kinxo kintasa mutane gaba d ikonki....rufe masa baki yasmeen tayi tace my Prince ida cin abincin kamun tausa bacci zanyi...kallon so had'e da kauna yyi mata yace to mmn baby nah badai babynmu ne yamatsa miki ba k?"


"cikin shagwaba tace eh"


Abincin sa ya ida cinyewa ,yasmeen takira kuyanginta suka gyara gun.


Kan kujera taje had'e da hayewa saman cinyar yarima tace yaya zanci nama ga shashshe!kanta yashafa yace ai yanxun 4batayiba kibari saitayi kinji alokacin angama ,ihu tasaka ita wlh ah ah yanxun take so kobaisan cewa inmai ciki nason abu ba'a bataba cikin xai iya zubewa,tama sa karya....


Shikuwa gogan duk yarude, sai rarrashinta yake tana kara botsare masa....ana cikin hakan yah sageer d tasleem suka shigo yana ruke d hannunta sukayi sallama...


Amsa sallamar yarima yyi yace ahhhh amarya kece d kanki?"murmushi taslim tayi ta kwace hannunta dg na sageer sbd taji nauyin yarima,zama sukayi yah sageer yakalli yasmeen da  kanta ke saman cinyar yarima yace mmn baby yaya babynmu?"naga kinyi shiru me kikeso?"


Murmushi yasmeen tayi tace ba komai yah sageer ,bakuyi fushi dani ba ?"naso inshigo d'azun wlh...yarima yakatseta d cewa wlh broth rigima take ita adole nama zataci gasasshe to yanxun ba'a gamaba shine niketa aikin rarrashi..


Tasleem tace oh gsky my man kaje kasamomata sbd babynmu ,kasan masu ciki anaso abasu abinda sukeso d wuri..


Murmushi sageer yyi shida yarima ,sukace bakin Ku daya ko?yasmeen tace eh mana ,ai munxama twins yanxun nida taslim,taslim tace hakane antynmu.


Yah sageer yace to nidai bara naje d kaina innemoshi yanxun bama zan aiki kowaba,taslim tace yeeeee!yauwa kokaifa tana murmushi..


Yarima d yasmeen na kallonsu sunajin dad'in yadda suke kaunarsu hade d son gudan jininsu tun kafin yazo duniyar..


Tashi sageer yayi ya kalli taslim yace baby muje ki rakani gun mota ko?"make kafadarta tayi,murmushi yyi yakalli yasmeen yace antynmu kingani ko takimun rakkiya bacin ke har mota kike raka yaya ?"


Murmushi yasmeen tayi tace Anty amarya kirakasa kinji?bbu musu ta tashi tana turo baki ,yarima da sao yanxun yatanka ,kan yasmeen yashafa yace oh kin koya mata shagwaba d turo baki gaba ko?


Murmushi yah sageer yyi yace ta kyauta ai sbd inason hakan,bejira amsarsuba suka fice shida tasleem......


        *****


da dare bash ne zaune wayarsa na hannunsa yabude data ,kawai yaga salma online ,da azama yabuta mata"


Slm"


Ykk?"


Sarai tagani saida tayi minti 3sannan tayimasa replay da


"wslm lfy lau"


Sai yaturo mata.


😍😍


Saita tura masa.


😇😇


Sai yace da wa kk chat?"


Tace d friends d'ina "


Ok yace yabar online.


da dare saiga text message yaturomata yanasonta d gske kuma da aure meye amsar ta game dashi?"


Cikin jin Dadi tace zatayi tunani.

dan murna salma saida tayita nafilfili nagodiyarta g ALLAH dayabata bash yakarbi adduarta ALLAH yasa alkhairi awannan taraiya tasu..d farinciki t kwana..


Washe gari  tun 8am bash yakirata bbu wani yanga tace ta amince ,sukayi sallama akan zaixo zance d dare..


Shikuwa bash har office din yarima yaje yasanar dashi komai game d salma d shiryuwarta harda yafiyarsa datace yanema mata agunsa dg karshe yafad'a masa suna son juna meye shawara?"


,,,yarima yaji dad'in hakan sosai ,nan yace ba komai yayafe mata ALLAH yasa alkhairi a auren sannan  dg karshe yace insha ALLAH ka aureta zata maka biyayya sbd ko da can gsky yarinyace me biyayya, cikin jin dad'in maganar yarima bash yace to ai haka akeso nan sukayi sallama.,,,,


koda yarima yaje gd yagaya ma yasmeen tayi murna sosai had'e da masu fatan alkhairi ...


-----------------------------------


Kwance tashi bbu wuya gun uban giji yasmeen yanxun cikinta haryyi 5month yafara turowa ,shagwaba d rigima kuwa sai abinda yyi gaba yin abunta take yarima yana biye mata,inkikaga yad'a rigarta yana shafa  cikin yana surutu  wai  da babynsa yake fira ,wani lokacin saidai yasmeen tayi dariya t girgiza kai sbd yana bala'in burgeta hakan nakara mata k'aunarsa.


Ayanxun haka antsida maganar auren yah Omar d Maryam inyadawo dg Cairo dan Yakima sadda zai gama ita kuma Maryam tayi SSCE dan yanxun ss3 take.

dan haka yarima yabukaci bash yabari ayi bikin su tare dsu yah Omar bbu damuwa yasanar d salma iyayenta suka amince..


Salis kuwa d kubra shirye shiryen bikinsu akeyi befi 5days ba dan yanxun haka yasmeen ce zaune tana jiran yarima yazo suje tayiwa kubra siyayyar kayan kitchen takai gudun muwarta ta biki,to shima yarima hardashi a hidimar matsayinsa na babban abokin ango wato salis..


Bata jimaba d zama taji horn din motarsa tashi tayi da cikinta da yyi girma dan ta tarosa.


Murda k'ofar yarima yyi y...


mmn fareesa ce✍🏻✍🏻AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿107&108


Sukuwa suka nufi gd hankalinsu kwance.


    Hakafa rayuwar tayita tafiya inda yanxun har cikin yasmeen yashiga watan haihuwa tayi duhu d kumburi ,ga cikin yyi girma sosai gaba daya yanxun part din ammi take yini tana kula da ita, gogan kuwa wato yarima acan yake yini shima ,gaba d'aya tausayinta yakeji sbd yadda cikin ke takurata ga girman da yyi ,shiya

sa yanxun yakura da bukatarsa ta auratayya da ita ",any time ammi da kanta ke matsawa yasmeen k'afa wani lokacin yarimanta dan yanxun ba sosai yake zuwa offi

ce ba sai da dalili mai k'arfi...

Ita kuwa yasmeen tanajin dad'in yadda ammi d mijinta ke kula da ita ,shagwaba sai abinda yyi gaba ,ita taslim tana d'aukar kwas din shagwaba r yasmeen."

Akuma lokacin yarima yazo yakawo mata kudinta na ribarta na gidan man daya bude mata million 3yace tayi yadda takeso dasu natane halak malak....

      Taji dad'in hakan sosai dan Dadi har kuka tayi ,nan takira umma ta sanar da ita itama tayi murna da hakan nan yasmeen tace ta yanke shawarar taturama yah Omar million 2inzai dawo yahad'owa Maryam lefe acan dan Maryam ta cancanci komai garesa tunda ta zabesa amatsayin miji bata duba shi matsayinshi na talaka kuma Maraya...

Umma tace wannan gsky taita saka mata albarka ,nan tace million guda zataba ba bash yasiyawa inna atika gd...umma taji dad'in wannan tunanin d yasmeen tayi sbd atika ta cancanci amata komai sbd ko yar uwarta ta jini iya abinda zata mata kenan..

   Haka kuwa akayi yasmeen tasaka bash yatura ma yah Omar kudin ta bank ita kuma inna atika akasiya mata gida..

dan  dad'i inna atika har kuka tayi tazo har gdn yasmeen tayi mata godiya.,,,


     ***** ***** *****

Yasmeen ce kwance a bed din ammi mai rumfa tana chat da kubra,sai murmushi take..sanye take da doguwar Riga ta atamfa , red tayi parking gashinta da ribbon red kasancewar kanta bbu dan kwali akanta tulelen cikinta yafito yyi das ajikinta.,ita kuwa ammi tana kicin hadawa mai martaba deener kasancewar girkintane...


     Yarima da shigowarsa kenan bed room d'in,tsaye yyi ya hard'e Hanna yen yakafeta da lumsassun idanunsa yanata kallonta cike d so da kauna saiyaji ta burgesa...ita kuwa yasmeen batasan dashiba ,d'agowa tayi dan taje kan mirror ta dauki agwalumarta kawai taga yarimanta yana sakar mata lallausan murmushi, lumshe ido tayi ,sbd wani irin tausayinshi taji tasan yyi k'okari sosai kusan 22days rabon da yyi sex da ita har yar rama yyi kuma tana lurada ciwon ciki yake kwana..""


Katseta yyi da cewa my Princess kibude idon mana!"ba musu ta bud'eidanunta tana murmushi, takowa yyi yadaukar mata agwalumar dan yafahimci ita take so ",kan bed din ya haura had'e da kwanciya gefenta..agwalumar ta amsa had'e da cewa yaya sannu ka gajiko?" Murmushin gefen baki yyi yace um um my Princess ganinki yasamun na nemi gajiyar na rasa ykk d baby nah ?"ahankali tace yana gaidakai kuma yyi missing naka..murya qasa qasa yace nima haka my honey baby yahana daddynsa jin dad'i ajikin momynsa yafad'a had'e da kashe mata ido,yar dariya tayi, cikin shagwaba ta ce oh nifa baya wani takurani ,zan iya yimaka komai(tafad'i hakan sbd farin cikinsa )"ahankali yasa Zara zaran hannayensa yamikar da ita had'e da cewa pls my Princess muje part din mu banaso ammi tasani sai mudawo tunda zaki iya ko?"cikin k'arfin gwuiwa tace to nan suka fito wuf suka nufi part din su..


"Bed room d'inta suka wuce akan bed suka yada zango ,yarima jikinsa har kirma yake ita kuwa tausayi yake bata";;


,,,hakafa yadunga lallab'ata yanabinta ahankali had'e da canxamusu salon kwanciya ,itakuwa bewar ALLAH daurewa kawai take yi batason yimasa raki tasan kyaleta zaiyi ," ita kuma tafison yabiya bukatarsa agunta sbd bayada wacce zata biyamasa bacin ita ,kuma yarimanta yaci darajar tayi masa komai na rayuwa aduniya...


     Be kyaleta ba sai da yasami cikakkiyar gamsuwa ,tukum suka baje suna maida numfashi dg bisani yataimata mata suka nufi toilet Wanda da k'yar take tafiya sbd yadda gun kemata zafi hakadai suka kimtsa suka nufi part din ammi alokacin kuma gab ake dayin sallar magarib..


"Ammi kuwa tana gama abinda take tazo a bed room d'inta da farfesun kifi had'e da awara takawowa yasmeen ta ga wayam ,saida ta tambayi kuyangin dke parlourn sukace sun fita tare da yarima ,zama Ammi tayi ,tafi awa guda zaune bbu su bbu alamarsu ,azuciyar ta tace oh d'an yau ba'a iya masa wato yanacan zai matsa mata da fitinarsa bacin ga abinda take d'auke dashi sai yaje yatado mata nakudar dole hmmm ALLAH shi kyauta....... sallamarsu ce ta katse ma ammi tunani ,kallo d'aya tayiwa yasmeen ta gane wani abu yafaru atsakanunsu,shikuwa yarima ganin harararsa da ammi keyi yagane taganosa sarai,sai yadukar d kai yana Sosa k'eya....


Zama yasmeen tayi had'e da dukar da kai tace ammi sannu da hutawa ,atakaice tace yauwa,had'e d kallon yarima tace bakaji ankira magrib ba ne?" Sum sum yafita cikin jin kunya..


Bayan ya fita ammi ta kalli yasmeen fuska d'aure tace wato shine yazo yyimiki wayo Kika bisa yabiya bukatarsa ,sai yaje yatado miki nakudar dole ko?"hmmmm nmj da dad'in baki inhar yabiya bukatarsa ai ke zaibari da wahala..hkuri yasmeen ta bawa ammi ,nan tace to kada tasake binsa taje tayi sallah ,farfesun kifi d awara na kan mirror ta ajiyemata cikin murna yasmeen ta yunkura ta tashi ta nufi bed room..


      Bayan ta idar da sallar sai jin wani bakon yanayi take ,amma sai daurewa take sbd umma tace kada ta zama mai yawan raki d k'orafi tunda suna bakin k'okarin su akanta.


"jitayi awarar d kifin sun fice mata arai ,tayidai zaune kan prayer mat"


Zuwacan dai taji abu nata gaba ,cikin sai juyi yake ga ciwon Mara d k'ugu,zuwa can taji wani ruwa na fitarmaya agaba ,adedenan ammi ta shigo d'akin ganin shiru yasmeen bata fito parlour ba ,kallonta ammi tayi taga ta runtse ido ta dafe ciki kuma ta lura batamasan tashigoba"ahankali ta matsa kusada ita tace yasmeeen lfy?"me kkeji ne?"


Kallon ammi taji cikin jin azaba tace ammi marata ,bayana ,k'uguna ciwo suke mun..


Salati ammi tayi afili tace oh wlh nakudace ,kuma nasan yaron nan ne yatado miki ita mttss,taja tsaki..


Wayarta ta d'auka ta kira Dr tace suhadu acan asibita yanxun zasu kawo yasmeen ta na nakuda...


Bayan sun ida wayar ,ammi ta kalli yasmeen baki bud'e ganin tana addua kuma tana kiran sunan yarima...


Wani irin tausayinta taji dama haihuwar fari sai hakuri sbd baka sababa ,lallai ayau ta jinjina soyayyar dke tsakanin yasmeen d yarima..


Cikin tausayawa ammi ta kira jakkadiya awaya dan tazo su kama yasmeen ,amma me ?"sai yasmeen cewa take akira mata yarimanta...


Cikin tausayi had'e da rarrashi ammi tace kinsan yana masjid baya dawowa sai anyi isha'i muje kinji ,adedenan jakkadiya ta shigo dakin nan suka kama yasmeen ta mike tsaye sai sannu suke Mata ganin tafara galaibaita amma kuma sai daurewa takeyi....kuma tana kiran yarimanta...


Ko taku  biyu basuyiba yarima yasjigo d'akin da sauri yesmeen...



mmn fareesa ce✍🏻✍🏻AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿107&108


Sukuwa suka nufi gd hankalinsu kwance.


    Hakafa rayuwar tayita tafiya inda yanxun har cikin yasmeen yashiga watan haihuwa tayi duhu d kumburi ,ga cikin yyi girma sosai gaba daya yanxun part din ammi take yini tana kula da ita, gogan kuwa wato yarima acan yake yini shima ,gaba d'aya tausayinta yakeji sbd yadda cikin ke takurata ga girman da yyi ,shiya

sa yanxun yakura da bukatarsa ta auratayya da ita ",any time ammi da kanta ke matsawa yasmeen k'afa wani lokacin yarimanta dan yanxun ba sosai yake zuwa offi

ce ba sai da dalili mai k'arfi...

Ita kuwa yasmeen tanajin dad'in yadda ammi d mijinta ke kula da ita ,shagwaba sai abinda yyi gaba ,ita taslim tana d'aukar kwas din shagwaba r yasmeen."

Akuma lokacin yarima yazo yakawo mata kudinta na ribarta na gidan man daya bude mata million 3yace tayi yadda takeso dasu natane halak malak....

      Taji dad'in hakan sosai dan Dadi har kuka tayi ,nan takira umma ta sanar da ita itama tayi murna da hakan nan yasmeen tace ta yanke shawarar taturama yah Omar million 2inzai dawo yahad'owa Maryam lefe acan dan Maryam ta cancanci komai garesa tunda ta zabesa amatsayin miji bata duba shi matsayinshi na talaka kuma Maraya...

Umma tace wannan gsky taita saka mata albarka ,nan tace million guda zataba ba bash yasiyawa inna atika gd...umma taji dad'in wannan tunanin d yasmeen tayi sbd atika ta cancanci amata komai sbd ko yar uwarta ta jini iya abinda zata mata kenan..

   Haka kuwa akayi yasmeen tasaka bash yatura ma yah Omar kudin ta bank ita kuma inna atika akasiya mata gida..

dan  dad'i inna atika har kuka tayi tazo har gdn yasmeen tayi mata godiya.,,,


     ***** ***** *****

Yasmeen ce kwance a bed din ammi mai rumfa tana chat da kubra,sai murmushi take..sanye take da doguwar Riga ta atamfa , red tayi parking gashinta da ribbon red kasancewar kanta bbu dan kwali akanta tulelen cikinta yafito yyi das ajikinta.,ita kuwa ammi tana kicin hadawa mai martaba deener kasancewar girkintane...


     Yarima da shigowarsa kenan bed room d'in,tsaye yyi ya hard'e Hanna yen yakafeta da lumsassun idanunsa yanata kallonta cike d so da kauna saiyaji ta burgesa...ita kuwa yasmeen batasan dashiba ,d'agowa tayi dan taje kan mirror ta dauki agwalumarta kawai taga yarimanta yana sakar mata lallausan murmushi, lumshe ido tayi ,sbd wani irin tausayinshi taji tasan yyi k'okari sosai kusan 22days rabon da yyi sex da ita har yar rama yyi kuma tana lurada ciwon ciki yake kwana..""


Katseta yyi da cewa my Princess kibude idon mana!"ba musu ta bud'eidanunta tana murmushi, takowa yyi yadaukar mata agwalumar dan yafahimci ita take so ",kan bed din ya haura had'e da kwanciya gefenta..agwalumar ta amsa had'e da cewa yaya sannu ka gajiko?" Murmushin gefen baki yyi yace um um my Princess ganinki yasamun na nemi gajiyar na rasa ykk d baby nah ?"ahankali tace yana gaidakai kuma yyi missing naka..murya qasa qasa yace nima haka my honey baby yahana daddynsa jin dad'i ajikin momynsa yafad'a had'e da kashe mata ido,yar dariya tayi, cikin shagwaba ta ce oh nifa baya wani takurani ,zan iya yimaka komai(tafad'i hakan sbd farin cikinsa )"ahankali yasa Zara zaran hannayensa yamikar da ita had'e da cewa pls my Princess muje part din mu banaso ammi tasani sai mudawo tunda zaki iya ko?"cikin k'arfin gwuiwa tace to nan suka fito wuf suka nufi part din su..


"Bed room d'inta suka wuce akan bed suka yada zango ,yarima jikinsa har kirma yake ita kuwa tausayi yake bata";;


,,,hakafa yadunga lallab'ata yanabinta ahankali had'e da canxamusu salon kwanciya ,itakuwa bewar ALLAH daurewa kawai take yi batason yimasa raki tasan kyaleta zaiyi ," ita kuma tafison yabiya bukatarsa agunta sbd bayada wacce zata biyamasa bacin ita ,kuma yarimanta yaci darajar tayi masa komai na rayuwa aduniya...


     Be kyaleta ba sai da yasami cikakkiyar gamsuwa ,tukum suka baje suna maida numfashi dg bisani yataimata mata suka nufi toilet Wanda da k'yar take tafiya sbd yadda gun kemata zafi hakadai suka kimtsa suka nufi part din ammi alokacin kuma gab ake dayin sallar magarib..


"Ammi kuwa tana gama abinda take tazo a bed room d'inta da farfesun kifi had'e da awara takawowa yasmeen ta ga wayam ,saida ta tambayi kuyangin dke parlourn sukace sun fita tare da yarima ,zama Ammi tayi ,tafi awa guda zaune bbu su bbu alamarsu ,azuciyar ta tace oh d'an yau ba'a iya masa wato yanacan zai matsa mata da fitinarsa bacin ga abinda take d'auke dashi sai yaje yatado mata nakudar dole hmmm ALLAH shi kyauta....... sallamarsu ce ta katse ma ammi tunani ,kallo d'aya tayiwa yasmeen ta gane wani abu yafaru atsakanunsu,shikuwa yarima ganin harararsa da ammi keyi yagane taganosa sarai,sai yadukar d kai yana Sosa k'eya....


Zama yasmeen tayi had'e da dukar da kai tace ammi sannu da hutawa ,atakaice tace yauwa,had'e d kallon yarima tace bakaji ankira magrib ba ne?" Sum sum yafita cikin jin kunya..


Bayan ya fita ammi ta kalli yasmeen fuska d'aure tace wato shine yazo yyimiki wayo Kika bisa yabiya bukatarsa ,sai yaje yatado miki nakudar dole ko?"hmmmm nmj da dad'in baki inhar yabiya bukatarsa ai ke zaibari da wahala..hkuri yasmeen ta bawa ammi ,nan tace to kada tasake binsa taje tayi sallah ,farfesun kifi d awara na kan mirror ta ajiyemata cikin murna yasmeen ta yunkura ta tashi ta nufi bed room..


      Bayan ta idar da sallar sai jin wani bakon yanayi take ,amma sai daurewa take sbd umma tace kada ta zama mai yawan raki d k'orafi tunda suna bakin k'okarin su akanta.


"jitayi awarar d kifin sun fice mata arai ,tayidai zaune kan prayer mat"


Zuwacan dai taji abu nata gaba ,cikin sai juyi yake ga ciwon Mara d k'ugu,zuwa can taji wani ruwa na fitarmaya agaba ,adedenan ammi ta shigo d'akin ganin shiru yasmeen bata fito parlour ba ,kallonta ammi tayi taga ta runtse ido ta dafe ciki kuma ta lura batamasan tashigoba"ahankali ta matsa kusada ita tace yasmeeen lfy?"me kkeji ne?"


Kallon ammi taji cikin jin azaba tace ammi marata ,bayana ,k'uguna ciwo suke mun..


Salati ammi tayi afili tace oh wlh nakudace ,kuma nasan yaron nan ne yatado miki ita mttss,taja tsaki..


Wayarta ta d'auka ta kira Dr tace suhadu acan asibita yanxun zasu kawo yasmeen ta na nakuda...


Bayan sun ida wayar ,ammi ta kalli yasmeen baki bud'e ganin tana addua kuma tana kiran sunan yarima...


Wani irin tausayinta taji dama haihuwar fari sai hakuri sbd baka sababa ,lallai ayau ta jinjina soyayyar dke tsakanin yasmeen d yarima..


Cikin tausayawa ammi ta kira jakkadiya awaya dan tazo su kama yasmeen ,amma me ?"sai yasmeen cewa take akira mata yarimanta...


Cikin tausayi had'e da rarrashi ammi tace kinsan yana masjid baya dawowa sai anyi isha'i muje kinji ,adedenan jakkadiya ta shigo dakin nan suka kama yasmeen ta mike tsaye sai sannu suke Mata ganin tafara galaibaita amma kuma sai daurewa takeyi....kuma tana kiran yarimanta...


Ko taku  biyu basuyiba yarima yasjigo d'akin da sauri yesmeen...



mmn fareesa ce✍🏻✍🏻AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


Wannan page din nakine halak malak my Hafsat kiyi yadda kikeso dashi nagode sosae d yadda kike comment akan wannan novel😍😍


🅿109&110


Ko taku biyu basuyiba yarima yashigo d'akin da sauri yasmeen tace yayaaaaaaaaa!azabure yanufeta had'e da cewa ammi lfy ?"meke damun princess d'ina ?"yafad'a had'e da k'okarin taba yasmeen... Tsawar da ammi tayi masa yasashi takatawa,gaba d'aya yarude jin yadda yasmeen ke kiransa bbu tambaya yasan haihuwace zatayi tunda gashi sun rurruk'ota..maganar ammice tadawo dashi tunaninsa inda take cewa zaka matsa kabamu gu ko kuwa?"kake wani tambaya ta ,bakaine katado mata nakudarba.....karar da yasmeen tayi yasaka ammi yin shiru,cikin damuwa kamar zai yi kuka yace pls ammi kubari nadauketa sai muje asibitin wlh ina masjid jikina yabani b lafiya shine nataho plssssss!ammi ,batace komaiba ,tacewa jakkadiya ta karbo kayan haihuwar gun hjy rahama tasamesu a asibitin..yarima kuwa arikice Yakama yasmeen yasureta sai sannu yake mata had'e da cewa pls Princess kiyi addua kinji zaki haihu lfy insha ALLAH.. ammi tabisu abaya da jarkar rubutu ahannunta dan insunje takara bata tasha.

Yasmeen kuwa bewar ALLAH daurewa kawai take ita kad'ai tasan me takeji,duk tayi zufa ,shikuwa yarima ji yake inama ciwon yadawo ajikinsa dama haka mata keshan wahalar haihuwa hmmmm shi yasan dai ana cewa da wahala amma beyi tunanin ta kai hakaba..har cikin lobour room d'in yarima ya shiga ya aza yasmeen akan gadon".idanunsa sunyi jaa kamar yyi kuka kallon yasmeen yyi wacce ke rik'e da hannunsa gam sai juyi take sbd azaba ga uban gumi datakeyi...kamar zaiyi kuka yakalli Dr khadijat yace pls kubimun ita a hankali kinji?"ammi ta karbe d cewa to ai saika fita ko ,kajiramu..zaro ido yyi ,kamar zaiyi kuka yace ammi bazan iyaba ina waje yasmeen nanan tana wahala ni wlh bbu inda zani mamata tana cikin wannan halin...k'ara yasmeen tayi had'e da salati dg karshe takira sunan yarima ,rik'e mata hannu yyi yace sannu kinji?"ya jikin?"Dr tace pls zansaka miki hannu ki gyara ,ammi tace abari tasha rubutu ,nan tabata tasha had'e da shafe mata cikin ,aiko kamar an k'ara tado nakudar sai komai yarikice ,shikanshi yarima yyi zufa, sai surutai yake ,ammi data lura ba a hayyacinsa yakeba saita fita tabarshi ,tareda Dr ,bayan tafita Dr tasaka mata hannu..yyinda yarima yajuya sbd tausayi ,bawan ALLAH saiga hawaye..muryar Dr yaji tace insha ALLAH takusa sauka  gab take d sauri yarima yace ALLAH yaraba lfy Dr tace ameen.....


    Yarima juyawa yyi had'e da rike mata hannunta "ahankali yace sannu kinji princess d'ina " ahankali tace yaya pls ummanah kakirata mutuwa zanyi  pls kayafemun...tafad'a tana hawaye,shima hawayen yake yace bazaki mutuba kinji mamata zaki haihu lfy, akyale umma kinga kada hankalinta yatashi...


Dr kuwa dke tsaye k'uri da ido tayi musu azuciyarta tana yaba irin wannan tsantsar so d k'auna tasu"matsowa tayi ganin yasmeen din na juye juye tace ta yi nishi bbu musu tayi,atake tasaki wata razanan nar k'ara adedenan baby gils ta fad'o had'e da tsantsara kukanta tashaki iskar duniya..


Yarima kuwa cikin farin cikin dabai musaltuwa yyi saurin d'aukar babyn dko cibi ba ayankeba duk jini...d sauri Dr tace pls tsaya mana karbar ta ta yi tayanke mata cibi ...yarima yakalli yasmeen dan yimata mgn yaga tana runtse ido had'e da dafe cikinta ,kafin yyi mgn tayi wani uban nishi atake baby boy yafad'o.


"" wayyo murna atake yarima yad'a ga hannuwansa sama yyiwa ALLAH godiya da wannan babbar kyauta da yayimasa ....itakuwa Dr tana yankewa macen cibi tayankewa mnjin sannan ta ajiyesu ta fita had'e da cewa yarima kada yatab'asu...


Yasmeen kuwa rufe ido tayi tana maida numfashi, cikin farinciki d murna yarima yamatsa gunta "ahankali yace my Princess kingamamun komai aduniya ALLAH yabarmu tare da zuriarmu..bude ido tayi tana murmushi, sai sannu yake mata had'e da tambayarta yajikinta tace lfy takejinta yanxun,murmushi yyi yace mmn twins,itama murmushi tayi tace daddyn twins,matsawa yyi gun yaran yyiwa macen k'uri da ido ganinta sak kamanninta na yasmeen ne ,shikuma nmj kamanninsa ne kafin yace wani abu Dr d ammi had'e da wasu nursing suka shigo dakin nan suka kama gyara yaran yyinda ammi take cike da farinciki,tanata ma yasmeen sannu da tambayarta jikinta,nan Dr tahau kimtsa yasmeen shikuwa yarima kamar yaro d gudu yafita zuwa fada dan sanar da maimartaba.


Ita kuwa ammi waya tayi tace ashirya mata d'aki guda nan yasmeen zata dawo bazata barta a part d'inta ba sbd yareema gara takoma can.


Acikin yan mintina gaba d'aya masarautar suna cikin murna da farin ciki kowa yasani,yarima kuwa waya yacigaba da bugawa na nesa da na kusa ,wannan haihuwa...


Salim kuwa bayanan yana kallon ball ,Maryam ta kirasa yazo tasanar dashi ,ihun murna sukayi had'e da rungume juna suka kama rawa wai sunyi y'a y'a twins oh sudai twins sun karbesu gashi bacin Anty hanan tayi gashi shima yah Ashman yyi,sai murna suke suka nufi part din ammi dan ance kowa yajirasu yanxun zasuxo..


Acan asibiti kuwa bayan angama kimtsa yasmeen da babies ,nan suka nufo part din ammi gaba d'aya, da yasmeen dasu ammi ,hjy rahama ,anan suka sami taslim d yah sageer sai su salim d Maryam,yarima kuwa yana part dinsu yana waya da jamaa dan shi yad'auka anan zatazo besan a part din ammi zata zaunaba...


Koda yaji shiru yakira dr tace ai suna part din ammi ,atake yaji gabansa yafad'i afili yace taf da sake dan bazan yardaba haba yo minene na cewa acan zata zauna ...tashi yyi ya wuce part din ammi, yasamu parlourn tamkam da jam'a wani Dadi yaji ga babies din daya hannun Maryam itada salim sai pics suke mata namijin nagun taslim d yah sageer ,ita kuma yasmeen tana zaune kan pillow aakan carpet ta matse kafafunta bbu kunya yarima yazo yazauna kusada ita had'e da ruk'e hannunta ,murya qasa qasa yace my Princess yajikin ?"murmushi tayi tace da sauki,yace umma nagaidake,kallonsa tayi tace lah yaya Kaine kasanar da ita?"yace eh ..adede nan ammi tashigo ,bayi na bayanta da trays da Kula's samansa had'e flax na ruwan zafi,kallon yarima ammi tayi ta girgiza kai ,akuma sannan wayarsa tayi ringing tashi yyi yafita dg parlourn..


Ammi kuwa da kanta tahadawa yasmeen tea mai kauri tabata had'e da zuba mata farfesun kaji da ruwan semonvita miyar kubewa ,tasaka agaba tace ta cinye ,bbu laifi kuma tasha ta ci tayi kat had'e da hamdala..


Sannan ammi ta kaita dakinta,had'e da cewa ta kwanta kafin yaran su bukaci nono nan ta fice ,yasmeen kuwa wayarta ta janye ta bude data tana hawa online ta dubs status taga salim maryam, kubra,yah Omar,bash duk sun aza pics na twins din a status nan taciga d chat da mutane ,jitayi ankarb'e wayar ,d'agowa tayi ,yarimane ,duk yayi kicin kicin da fuska ya zauna agefenta yaran na hannunsa yyimusu k'uri da ido.


"Ahankali tace daddyn twins meye ne kke fushi" haba nawan ai murna zakayi ko?"ahankali yace wace murna bacin ammi ta rabamu ni daku ,yanxun fa sai ace said kinyi arba'in sannan kikoma part dinmu haba mana nibazanji d'umimin jikinkuba kenan?"


Murmushi tayi jin ba wani abu bane cikin rarrashi tace pls yaya kabari ayi suna tukum sai kawai nasace jiki na bika kawai ko yakace?"(tafad'a ne dan abar maganar)


Murmushi yyi yace yauwa my Princess ,yanxun kibasu nono ko su sha ,nama gani zakiyi kyau da shayarwa ma,turo baki tayi cikin shagwaba tace ni um um da zafi fa!dariya yyi yace lallai princess Ashe ke matsoraciyace to bari na taimaka miki kibasu ..


Ajiyesu yyi ,yajanyota jikinsa had'e da zuge xif din gaban rigarta ,aiko duk sunciko suyi girma sosai, k'uri yyi musu d ido ,can yamiko mata mace ,rigima yasmeen tasaka ita nmjin zata faraba ,rarrashinta yyi tukum sannan tayi addua had'e da bissimilla tafara bata ,yar k'ara tasaki,tana cewa wayyo yaya zafi...shafa kanta yyi yace sorry zai bari kinji."bayan ta gama bata yakarbeta had'e da mik'o mata nmjin shikuma ya aza macen akafad'a yana rurrugata hartayi gyatsa tukum .


Zama yyi agefen yasmeen ya aza babyn acinyarsa yyi mata k'uri da ido afili yace yes koda inji....itadai yasmeen batayi mgn ba tanadai kallonsa..


Shikuwa wani  tunani ya fad'o masa arai sbd ganin wannan babyn ,abun da dadewa.


Shekaru coma sha Tara dasuka wuce...


mmn fareesa ce✍🏻✍🏻AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


🅿111&112


Shekaru goma sha Tara dasuka wuce...


Alh ismai'l ne wato mahaifin yarima alokacin yana magajin gari bezama Sarki ba,yana rik'e da hannun yarima Wanda alokacin yana dan 14years .

Bayan sun fito dg mota ,yyinda dogarawa nagun motar suna jiransu.

      Cikin asibitin suka shiga suna tafiya suna fira a hanya ,office din wani Dr suka nufa abokin abban yarima  ne yazo suyi wata shawara gameda rashin lafiyar dayake fama da ita....suna shiga office din suka sami jaririya kwance kan gadon da'ake duba marasa lfy",ai da sauri yarima yanufi gunta yana murmushi yad'auketa had'e da kissing nata.... Abban sa kuwa cikin mamakinsa yake kallonsa har yazauna suka gaisa da Dr din ,suka cigaba da mgn yyinda yarima hankalinsa naga babyn wato yasmeen (alokacin tana jaririya)Abbansa yakallesa yace oh my son bazako zo Ku gaisaba?" dg zuwa said'aukar y'ar mutane kadafa ka kadamusu y'a...murmushi Dr yyi yace oh wannan baby ,yanxun mahaifinta yaje yakarbo allura za'ayimata ta BCG dayake sabuwar haihuwace shine yabarta nan yaje yakarbo allura yadawo in anmata yakaita gun mamanta tana can bin layin ganin likita..yarima ne yakatsesa da cewa pls uncle kubani ita natafi d ita gidammu,murmushi abbansa d Dr sukayi kafin suyi mgn ,baban yasmeen yashigo d sallama abakinsa."

bayan sun amsa yagaida abban yarima cikin girmamawa kasan cewar yasan shine magajin gari...Dr yadubi yarima dketa ma yasmeen wasa yace to ga abbanta nan saika tambayesa inzai baka ita..da sauri yarima yakallesa yana murmushi yagaidashi,ya amsa cike d kulawa had'e da cewa Ashe yasmeen ta sami wani yayan bacin yayanta Omar?"kai duke yarima yace pls kabani ita natafi da ita gidanmu gun ammina!murmushi yyi had'e da dafa kafadarsa yace kayi hkru kaga jaririyace batafi wata2 ba in anyayeta zan kamaka ita har gdnku kaji ....mika masa ita yarima yyi had'e da cewa to kayi alkawari ko?"abbansane yace oh haka kake dama?"aiyace zaikama ita bashikenan ba muje gd ...shiru yyi abban yasmeen dai baiyi mgn ba yamik'awa Dr ita dan ayi mata allura ,shikuwa abban yarima hannu yaba mahaifin yasmeen sukayi sallama had'e da sakamasa kud'i wai na yasmeen ne da yak'i karb'asaida Dr yasa baki tukum yakarb'a yyi godiya... shikuwa yarima saida yaje yasake kallon yasmeen tukum yataho had'e da cewa abbanta saika kamun ita,murmushi yyi yace insha ALLAH yasmeen batada miji sai kai.....nan abbansa yace ALLAH yasa sukayi sallama suka tafi....


Ajiyar zuciya yarima yyi a fili yace oh ALLAHU Akbar wato ubangiji ya amsa ,tabbas tunda naga photo na abbanki nasan duk inda nasan shi nasansa,yafad'a had'e da kallon yasmeen...


Cikin rashin fahimta tace oh sai surutu kke kai d'aya kayimun bayani dan infahimta ni yanxun ban gane ina kadosaba?"murmushi yyi yace my Princess wlh kuna kama da yarinyarnan sak kamanninkine tun kina jaririya! Turo baki tayi tace hmmm ni kasanni ne da ina jaririya ne?"ahankali yalabarta mata sadda yaganta a asibiti..murmushi tayi tace oh ikon ALLAH Ashe yan ameen sun karba....kafin yace wani abu ammi ta shigo dakin, tana ganinsa tayi salati had'e da cewa wato kana nan bazaka barta ta hutaba ko ?"to maza ka tashi katafi kafin ran...yasmeen ta katseta da cewa ayya ammi muna sallama ne shiyasa...da sauri yarima yace eh wlh,baki bude ammi ke kallinsu dak'k'uwa tayimusu had'e da kora yarima ,sannan tagyrawa yaran kwanciya had'e cewa yasmeen yanxun zata turo jakkadiya tazo ta kwanadasu ,bata jira amsartaba ta fita...


       Yasmeen kuwa kwanciya tayi tana tuna labarin da yarima yabata ,azuciyarta tace oh dama Ashe tun tana jinjirarta yarima ke k'aunarta ,wani irin son mijinta da k'aunarsa suka sake dabaibayeta ako ina nan jikinta ,lallai ta yarda aurensu had'in ALLAH ne gashi har sun fara da haihuwa d'aya yara2 oh to wama yasan iyakar zuriarsu?"sai ALLAH da wannan tunanin bacci yyi gaba da ita.,,,,,


    *** **** ****


Washe gari misalin karfe 7:am yasmeen ta farka da adduar tashi dg bacci abakinta ,bude idonta tayi taga jakkadiya nawa macen wanka ,inna atika nayiwa namijin shafa...mamaki take yaushe inna atika ta zo?"muryar ta taji tana cewa yasmeen kintashi?" nan tace eh inna ina kwana?"bayan sun gaisa tace to tashi muje namiki wanka kinji,bbu musu ta tashi ta cire kaya ,nan akace tabasu nono za'a kaisu fada gun maimartaba yagansu...


Bayan ta shayar dasune,suka shige toilet inna atika tayimata wanka sosai ta gasheta ,yasmeen kuwa yaji dad'in jikinta saidaifa taji zafin ruwan zafin hakadai ta fito ta shirya ,sannan tayi break fast mai rai da lafiya..


"" bayan ta idan ne taduba wayarta taga miss call 126na yarima ne 3na yah Omar 3na umma ,umman takira suka gaisa ta tambayeta lafiya dai take ko?"tace eh nan tayita mata nasiha akan taruk'a nuna kawaici akan yaran,sannan banda musu d kowa sannan sukayi sallama nan takira yah Omar shima sukasha fira sannan sukayi sallama..""


Bata aje wayarba yarima yashigo d'akin da sallama fuska asake tashi tayi ta fad'a jikinsa tana kukan kissa da shagwaba"ahankali yace mmn baby lfy me aka miki?"fad'amun kinji tawan,cikin shagwaba tace ba inna atika ce tamun wanka da ruwa masu zafiba !had'e rai yyi yace oh dama wait dole wankan sao anmike?"nifa gsky banaso ayita kalleminke bbu kaya gsky !Amma zancewa ammi arik'a bari ruwan yaf'an sha iska tukum ayimiki kinji?"ahankali tace to yaya, zama sukayi suka gaisa yatambayeta kotana bukatar wani abu ?"tace ah ah ,yaran yatambaya tace suna gun maimartaba afada ,ahankali yace my Princess nakira naji shiru baki d'agaba lfy dai?"tace lfy lau yaya ina wanka alokacin.... Jakkadiya ce ta shigo da yaran Maryam d salim nabiye da ita wai sunxo suyi wasa da fira da yaransu...shidai yarima murmushi yyi ya karbesu yahad'a d yasmeen yacigaba damusu pics ,sai fara'a yake bakin nan yaki rufuwa,yyinda Maryam d salim keta lissafa budurin daza'ayi na suna ,saiga Anty hanan d twins dinta sun shigo..


Bayan sun gaisa ta musu barka ta karbi yaran twins d'inta kuwa sai murna suke suna surutu wai sunyi kanne dasu zasu tafi gidansu ....wayar yarima tayi ringing yad'aga ganin salis ne murmushi yyi yace ok had'e da datse kiran,yakalli yasmeen yace bars naje da yaran nan ga abokaina can part dinmu su gansu sai na maidosu!tace to nan hanan ta miko masa su ya karba adaidainan kubra ta shigo dakin, tana ihun murna tayi ya'ya koda taga yarima saitayi shiru dan tare da salis suke ya wuce can part dinsu yace ta nufo nan yasmeen tana nan,cikin kunya tagaidashi hade da masa barka murmushi yyi yace babies d'inki sunyi fushi dke sunxo duniya tun jiya sai yau kikazo ganinsu,ware ido kubra tayi tace all yaya ai yanxun bata baciba ina nan har ayi suna tare dasu ,murmushi yyi yace dakin kyauta ,nan yafice ta fada kan bed din suka rungume juna da yasmeen suna farin ciki ,nan suka cigaba da fira dasu hanan d Maryam da salim suna nan kuma saiga salma ta shigo bash ne yakawota yawuce part dinsu yarima dan yakirasa yace sunacan...


Bangaren su yarima kuwa ,suna can fira ta Barker shiga salis dan wasu dg cikin abokan bayan sun ga yaran tafiya sukayi,sukabarsu suda salis .


Salis yakalli yarima yace kai mutumin bbu sauki kowa yaga yaran nan yasan nakane sbd kamarku ,musammun nmjin ,kana bada himma gsky yafad'a hadeda yin dariyar shakiyanci...murmushi yarima yyi yace to yasan ranka ai indai wannan fanninne bana wasa da harka ,kai aigashi duk jarabar taka matar taka bbu ciki ko?"hararansa yyi yace hmm to bars kaji tana da ciki 2month dandai mu namu ba mai laulayi bane ,dan ranar da najefa kwallona araga aranar Muka sami Rabin baby...


Cikin tsokana yarima yace hmmm kayi kokari dan duk yadda nike ganin inada fitina to wlh gara ni dakai ,kodayake ai gudunka tarukayi saida my Princess ta tsorata ta dazaka mata kishiya sannan taba da kai bori yahau,murmushi salis yyi yace eh naji ai dan tanasona ne shiyasa tayi kishina Ashe haka akayi?"yarima yace eh mana hade da labartamasa komai ...


Suna haka su mukhtar da wani kamal abokansu sukazo ganin babies bbu jimawa bash yashigo shima ,nan sukayi ta fira basu maida babies dinba saida ammi ta kirasa tukum yamaidosu sbd jamaa nason ganinsu yan barka...


Yinin ranar yarima be fita ba yana gd shida abokansa suna tayasa murna ,abinci kuwa dg hotel akayi Oder, ana bawa jamaa,shima yarima Maryam ta kaimusu nasu shida tauwagar abokansa.


Hakafa aka cigaba da zaman jego gidan cike d mutane a kullum kubra kuwa saida tayi kwana anan sannan ta koma gdnta 2 washe gari tasake dawowa nan aka cigaba shire shiren suna dan su Maryam har anko akayi kuma a hotel za'ayi taron sunan ..


Ayaune aka kawo kayan yaji na babies d na uwarsu hmmm fadin yawan kayan ko tsadarsu bata lokaci ne ga harda gold dana babyn mace dana yasmeen ,dan Tsabar murna yasmeen bar kukan Dadi tayi yau ALLAH yashare mata hawayenta ta haihu kuma alokaci guda 2ta Haifa ta huta da gorin wasu dg  dangin miji ...


Yau Yakama Daren suna akuma yau d safe hjy babba ta sauka ...


mmn fareesa ce✍🏻✍🏻AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


Wannan page din nakine Aisha Aliyu kiyi yadda kikeso dashi ina mugun jidake irin sosai din nan😍😍


🅿113&114


     "Yau Yakama Daren suna akuma  yau da safe  hjy babba ta sauka agidan sbd tun farkon haihuwar taso xuwa alhj tsoho yahana yace sai Daren suna washe garin suna ta dawo..


          Yasmeen ce zaune ,ana Mata lalle da Kitso nasuna ,masha ALLAH wannan lalle yyi kyau over ,yyinda kuyanginta ke gefenta suna rik'e da babies d'in..

Lubna dke zaune kan kujera ta kalli yasmeen tace mmn babies ankawo kayan printing d'in?" Yasmeen tace eh "nan tace ok bara agama miki sai amun,sannan Maryam....bata rufe bakiba saiga Maryam d'in da salim sun shigo,kallonsu kubra tayi tace oh ikon ALLAH kaidai kazama na mata ko ina Maryam tayi kana manne...murmushi Maryam tayi tace ALLAH Sarki my salim bacci kawai ke rabamu dashi gsky Anty lubna kinsaka masa ido..yar dariya yasmeen tayi tace hmmm inkinyi aure ai dole yahakura...sallamar hjy babba ta katsemusu fira ,sai yan harare harare take tasamu guri ta zauna nan suka gaisheta ta amsa hade da cewa amiko mata baby boy din nbu musu akabatashi taita kallo nan lubna tace hjy badoshi kidauki macen...wani mugun kallo tayiwa lubna tace ke wacece ne dazaki gayamun San ranki?" Yasmeen azuciyarta tace oh lubna kintab'o jaraba"da sauri maryam tace yi hkuri hjy mstar abokin yah ashmance kuma batasankiba...tsaki tayi tace to dg yau aita sanni ,itadai kubra bata k'ara mgn ba ...ana cikin hakan yarima yyi sallama cikin takunsa na k'asaita yasha askin suna da guaran fuska yyi masifar kyau wani lallausan boyel ne milk ajikinsa sabo fir sai kamshi yake dalagansa kaga angon jego,kai tsaye gun yasmeen yanufa kuma cikin sa'a angama mata ,fuskarsa asake be amsa gaisuwar da kuyangin kemasaba yadai daga musu hannu ya tsugun na gefen yasmeen hade da rike mata hannu d'aya yace wow my Princess kunshin nan yamun kyau gsky,murmushi tayi tace ALLAH nawan?"yace eh mana amma zanbasu kyauta ta mu.....salatin d hjy babba ta yi ne yasashi yin shiru dan sai yanxun yasan tazo shibema lura da ita ba azuciyarsa yace to ga fitinanna kawai,jiyayi tace gsky bakuda kunya kota miyan bacci ,ace agabanmu kuma tana jego kake tab'ata to wlh zansaka da anyi suna amaidata gd yo wannan ai kafin tayi 40kasakeyi mata wani cikin ta fada hade da tashi tsaye ....yyinda kubra tayi shiru tana mamakin mita da jarabar wannan tsohu wa tana shiga inda ba huruminta...


Yarima kuwa tashi yyi azuciyar sa yace bara na lallabata dan tabbas zata iya sakawa amaida my Princess gd da sauri yabi bayan hjy babba yasameta zata shiga parlourn baki da sauri yarungumota yace haba matar kisaurareni mana ,turesa tayi tace rufemun baki marar kunyar banza da wofi...kudin daya azamata ahannu yakata yin shiru saita fara murmushi to kokaifa yaron kirki jeka aidama kishine yasani yin fada ,amma tunda kabiya na kwalliya shikenan, yarima dke gimtse dariyar data tasomasa ganin hjy sbd kud'i tabar masifa ,yace to matar kije ciki na tafi to tace hade da Barin gurin ..


,,,shikuwa yarima fita yyi yaje ya larboma yasmeen dinkunan dazasu saka shida ita a gobe,bayan yakarbo yakaimata sukayi sallama yawuce part dinsa.,,


    Washe gari kuma suna yara sunci sunan ,mace rahama ana cemata (arfat)nmj isma'il ana cemasa (arfan)

gaba daya hidima ake bbu kama hannun yaro ga gefe anyanka raguna da shanu na suna..

Cikin bed room d'in da yasmeen take na kutsa kai na hangota cikin wata arniyar shadda dark blue tayi masifar kyau yyinda arfat d arfan suma sunsha gayunsu cikin riguna da wando masu kyau da tsada, su kubra d salma hade da wasu kawayensu na a gefe,yyinda kuma part din ammi ma can cike yake da yaran gidan da yan uwa anata hidima ,Maryam kuwa d salim sunacan suna casu kafin atafi hotel anjima..

Su yasmeen dke cikin bed room suka ruka juyo busa d kida irindai Wanda suka saba ji nasarauta sai kirari akewa yarima ana kodasa ,nan yashigo cikin dakin fuskarsa wasai sai murmushi yake masu video nadaukarsa da masu photo ,duk matan dke d'akin suntaya yasmeen murnar mallakar Wannan had'adden mijin nata,shima shaddarce dark blue ajikinsa sunyi iri d'aya, yasmeen bbu kunya ta makale abinta akayita musu pics suda babies d'in dg bisani yarima yarad'a mata akunne zaije yataho da bakinsa wad'anda sukazo suna ,murmushi tayi batayi mgn ba adaidai nan kuma akayimusu pic yafita..


Salma dke kallonsu tayi ajiyar zuciya ,lallai ikon ALLAH kenan dayanxun itace haka take cikin wannan matakin saidai kah!sanadin lesbian yajamata ,har yar kwallah taji ,amma tadauki hakan amatsayin kaddararta..


    ****  ****  *****


Da misalin karfe 4:12pm motocine da yawa keta d'aukar jama'a ana kaisu gun dazaayi taron sunan dan tuni yarima da yasmeen suka Dade da bayyana acan..


Acikin hotel dinkuwa guri na musammun akaware musu yasha decoration ,gefe ga masu asharalle da police bam ,can nahango yarima d yasmeen hakimce kan kuje sun saka kaya iri d'aya hannunsa cikin nasa, kowanne gefensu ga body guards dinsu nan tsatsaye abayansu yyinda babies d'in suke gun Anty lubna da hanan...gefe guda kuwa Maryam ce lubna ,salma sun saka kaya iri daya ,gefensu kuyangine da buhu na suna biye dasu suna zagaye gun dkeda jama'a suna raba jikka dkeda photon yaran ajiki da kalanda sai memo d tissue d robar ruwa d lemo sai take away aciki dkeda snack's anataba rabama jamaa...nan nahango yanMMN FAREESA FANS PAGE agefe da AWESOME FANS CLUB da MMN SHUKRA NOVELS duk suna zaune akan fararan kujeru ko waccensu taci wankanta lolx...suna tayasu yasmeen murna nan naga Maryam nata mikawa kowaccensu Jakarta..


Abokanan yarima kuwa yanxun suka bayyana agun ,salis ne gaba yyimusu jagora ,nuraddeen d Zarah (SONE)yana rik'e da hannun zararsa ,abayansu kuwa sir Aliyu ne da Hafsat (NIDA D'ALIBATA) abayansu kuma  sultan ne da raudah (RAMIN MUGUNTA) abayansu kuma mubeen ne nah mubeena(MUBEENA)duk suka sami guri suka zauna gefen su yasmeen nan me video d masu camera suka cigaba da aikinsu yyinda suma masu kida suka saki kids nanfa guri ya cika makil da jamaa sai ruwan lik'i akemusu wasu da dollars suke musu likin,yyinda wasu suketa zuwa gun wad'annan taurari suna gaisawa wasu na karban numbersu ...


Anci ansha anrak'ashe su babies sunsha kyaututtuka suda yasmeen ,nan fa aka cigaba da jidar mutane ana maidasu gd dahaka taro yatashi lfy ...


Bayan duk andawo kowa agajiye yasmeen kuwa itada babies wankansu sukayi suka kwanta,yyinda kubra itama tayi ta kwanta hade da kashe wayarta dan kada salis yamatsa mata yace sutafi gd tasan xai iya yadda ta kwaso gajiyarnan zai iya k'ara mata wata...


     Bangarensu yarima kuwa suna can part din baki shiga su salis ,tunda suka dawo dg gun sunan.


Zazzaune suke ,saidai bbu Wanda yyi mgn sbd duk miskilaine dukasansu ,salis ne ya yatsina fuska ta ce oh malamai kunyi wani shiru to niba ma wannan ba ,katashi kaje kafito mun da matata wlh dan amatse nake inkai taka tanada laluri Toni tawa batada komai yafad'a hade d kallon yarima,sir Aliyu ne yyi dan murmushin gefen baki tace yadubi yarima yace friend dakaifa yake ..tsaki yarima yyi tace tabu da d'an iska yanxun yasan ko karfe nawa ne ,kosoyake naje muhadu da ammi tayi zargina kogun yasmeen nazo...sultan ne yace hmmm wlh danine kaiko friend wlh yar zagaye zanrikayi ko romancing juna ne muyi narage zafi ...nuraddeen yakarbe da cewa hmm kaima kasan ajene dan friend bbu sauki tanan fannin, dariya sukayi mubeen tace nidai bbu ruwana...sir Aliyu yace kai friend aigara kowa dakai..salis yakatsesu d cewa dallah malamai kuyi dani wlh dan yadda nikeji to wlh ko wata nakama kada kucemun komai ,dariya sukayi gaba daya yarima yace mlm in kanakwanciya ka kwanta bbu inda zanyi dg nan sukayi kwanciyarsu .


Salis yyi tsaki ya kwanta abinda badan yasoba..


Washe gari...


mmn fareesa ce✍🏻✍🏻AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


Dedicate to my lovely jammy&mummy's ped


🅿115&116


Washe gari byn su yasmeen shungama kimtsawa harsunyin break saiga yarima yashigo ko gaisawa basuyiba yakalli kubra yace to ga mijinki can yana fushi sai kije ki rarrashi abinki yana Neman yadawo kaina nikuma bani na kashe zomanba rataya akabani!"yafad'a had'e da dariyar tsokana ,murmushi kubra ta yi tace to shikenan yanxun yana ina?"yace kije part din mu yana can dan sauran abokanmu suntafi shiyarage",tashi tayi tafita..

Yarima yakalli yasmeen yace mommyn twins nima gsky azo ajidani ,dama jiya ban ga lallen nan nakiba da kitson bara naxo nagani ko

yafad'a had'e da kashe mata ido..

      Itadai murmushi tayibatace komaiba kan bed din ya hauro had'e da cewa ina yarana?"ahankali tace suna gun ammi ,murmushi yyi yace kinga bazamu takuraba yafad'a had'e da janyota jikin sa, cikin shagwaba tace in ammi tazofa?"rad'a mata yyi akunne aibazata zoba ...

daga nan yamirginota had'e da hayewa samanta yahad'a bakinsu guri d'aya yana aikamata da hot kiss....sai numfashi suke mayarwa nan suka cigaba da romancing juna azafafe dan yarima yama fita hayyacinsa sai murzata yake son ransa gaba d'aya duk sun hargitsa bed sheet d'in dake kan bed...


   Ammice tafe ita d'aya tana sabe da yaran kowanne hannu,kasancewar duk kuyangin gidan da bayi sunacan b'angaren da ake girki suna soyen naman suna,tun a window ammi da ta kallah kasancewar anyaye labulen windown tafahimci kamar yarima na cikin d'akin..


" matsawa tayi dan ta tabbatar ....salati tayi ganin irin jarabar yarima dayake kokarin cirewa yasmeen riga had'e da saurin Jada baya ta rufe idonta tana mamakin fitinar d'an nata gsky dole ta hanasa shigowa kada ya afkama yar mutane kafin tagama wanka ta koma samun wani cikin ta fada azuciyarta ."


Da azama ta zagaya had'e da yimusu knock da k'arfi... da sauri yarima yatashi dg kan yasmeen ,yana cewa my Princess ALLAH yasadai ba ammi bace!"yasmeen dke kokarin mayarda rigarta tace ameen...


Sake knock din akayi da azama yaje yabude ammi tasako kai....tanama yarima kallon tuhuma ,shikuwa duk Yakama kansa sai Sosa kai yakeyi ,cikin rashin gsky yace ammi naje part din ki bakya nan....tsaki tayi had'e da matsawa ta mikawa yasmeen wacce kanta ke duke arfat ,sannan ta kwantar d arfan,takarewa bed din kallo koba'a fada maka kasan abinda akayi kan bed din...


Juyowa tayi taga ita yarima ke kallo suna hada ido yadauke kansa girgiza kai tayi tace kasameni a part dina..bata jira amsarsaba tafice...


Yasmeen kamar zatayi kuka tace oh yaya kagani kajamun gashi ammi tagane ko?"ahankali yace sorry kinji bara naje gunta...


Koda yaje Ta's ammi tayimasa had'e da gargadinsa tasake kamasa hmmm saitabashi mamaki.,,,,,


***** ***** *****


Hakafa Rayuwar tacigaba da kasancewa inda yasmeen d yarima sunaji suna gani ammi tayi katutu tahanasu keb'ewa da juna ko dakin taga yashiga dayawuce Monti 5zata shigo ta koresa ,sannan da kanta tacigaba da tsuma yasmeen dan tasan d'an nata ba sauki ,agefe kuma arfat d arfan sunyi bul bul sunyi wayo abinsu suna cikin koshin lfy kowa son yaran yake acikin gdn salim kuwa d Maryam suna like da su koda yaushe ,ana cikin hakan yasmeen tayi 40 hmmm kada kuso kuga zumud'i agun yarima bawan ALLAH sai murna yake dan bak'aramar takura yyiba ,amma me ?"koda yaga har tayi 45bata komaba wato takara 5days sai yyi zuciya harda ammin gaba d'aya ko part din yadaina zuwa har yar rama yy... Ita kuwa Yasmin ganin yyi 2days be xoba takirasa yaki dagawa dg bayama sai ya kashe wayar gaba d'aya, ai sai yasmeen ta saka kuka dama itama gun mijinta takeso ta koma ta gaji ...


    Koda taci kuka mai isarta aita tashi ta nufi gun ammi ,tasameta a parlourn ta da arfan d arfat ajikinta sunata mata dariya ,zama yasmeen tayi batayi mgn ba ,nanvammi ta sallami kuyangin,suna tafiya yasmeen ta barke d kuka ...


Hankali tashe ammi ke tambayarta meke faruwane?"bbu kunya yasmeen tace pls ammi kimaidani gun daddn su dan ALLAH wlh yyi fushi damu yau kwana 2rabona dashi....tafada tana hawaye....


Cikin mamaki d al'ajabi ammi tace ok bbu damuwa hakan yyi kyau ai Baku daya yake fushinba hardani nima amma yau basai anjimaba zaku tafi part din Ku dama dalilin jinkirina sbd Ku koma gidanku kubar cikin gidan nan amma bbu matsala....


Tashi ammi tayi bbu jimawa tadawo tasami yasmeen naba arfat nono,zama tayi batayi mgn ba...


Sallama yarima yyi yashigo...ada ammi tayi niyar yimasa fada amma koda taga yanayinsa tasan atakure yake yadai hakurane kawai dan har rama yyi ,kuma tagane yasmeen tasan halin mijinta shiyasa take so su koma..


Zama yyi kusada yasmeen kansa aduke yace ammi gani!


Ahankali tace to dama nakirakane dan nabaka hkuri sbd nayimaka laifi na rike maka mata ko ?"da Saudi yagirgiza kai ,murmushi ammi tayi tace kada kadamu kazo da dare kajata da yaranku kutafi ALLAH yyimuku albarka...


Sukace ameen gaba d'aya ,nan fa yarima baki yaki rufuwadan murna..


   Hakafa akayi da dare yazo yatafi da familynsa hmmmmm wannan dare yasmeen d yarima jinsa sukayi kamar first night dinsu ,sbd yanuna mata tsantsar kaina da kulawa ta musamman.


      *********


Bayan 8month yasmeen ce tsaye gaban dressing mirror tana rolling din mayafi akanta ,arfat dke tsayuwa ta rarrafo had'e da dafa yasmeen ta mike tsaye daukarta yasmeen tayi tana dariya hade da dagata sama tana mata wasa...


Yarima dke zaune kan bed arfan nasan cinyarsa ,yakallesu yace mommyn twins mujeko?"akaisu gun ammi sai muwuce ko?"murmushi tayi tace eh hakan yyi dan nafiso naje naga lefen nan anatse kada su rudanikafin akaisa gobe.....


Ta shi yarima yyi suka fice dg gidan Dan yanxun suna gidansu masu nakansu bagidan ammi sukeba ,agidan ammi sukaje suka ajiyesu sannan suka dauki hanyar gidansu yasmeen dan tagano lefen yaya Omar kafin jibi akai dan biking saura 10days ayi tare damasu bash..


Suna isowa k'ofar gidan....


mmn fareesa ce✍🏻✍🏻AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story &written by mmn fareesa


Wannan page din nakune zainab Othman & sury baby kuyi yadda kukeso dashi ina mugun yinku😇😇


🅿117&118


Second to the last page


Suna isowa k'ofar gidan yarima yyi parking, cikin azama yasmeen ke k'okarin ficewa yyi saurin ruk'ota "ahankali yace oh my Princess ko sallama bazamuyiba abani ko dan kiss ne saiki gudu ko?" Murmushi tayi tace lah yaya bahaka bane ...be bari ta ida mgn ba yacafke bakin nata Wanda be sakiba saida yashanshe lip stick d'in dke bakinta duka"murmushi tayi cikin shagwaba tace to yaya nibara natafi anjima kadawo saimutafi ko?" Cikinta yashafa yace to mommyn twins ,ammafa inaga kamar nayi ajiyata anan ko?"turo baki tayi tace um um yo dukafa 10month su arfan garesu ace kuma ciki yanxun aika tausayamun..

         Murmushi yyi yace hmmm ai yanxun y'an ukku zaki haifamun ko ?"marfin motar ta bude ta fito had'e da cewa yaya ALLAH yatsaremun kai ,cikin jin dad'in addu arta yace ameen had'e da tada motar itakuma tashige cikin gidansu...


"" kaya masha ALLAH sunyi nagani na fada,masu kyau da tsada Wanda a kasar waje yaya Omar yahad'a lefen ."haka yasmeen yarima yazo daukarta tanata santin kayan .


Bangaren su salma ma bash yyi mata lefe  shima hadad'e Wanda akwai taimakon yarima aciki arana daya akakai lefen bash dana yayah Omar Wanda kowane bangare sun sami tarban mutunci ....


     ******


Yau Yakama Friday kuma Yau ake dinner su yah Omar da bash dan komai tare akeyi."da misalin karfe 7:30motocin gdn sarkine keta zaryar daukar jama a ana kaisu gurin dinner.

      Su yasmeen ne ,da kubra wacce itama ta haihu tana sabe da baby boy ,tsaye sai taslim itama da tsohon cikinta kowaccen su zata shiga motar mijinta ....yyinda salim yaci gayunsa cikin fararen suit yyi masifar kyau saidai ransa adagule yake sbd gobene zai rabu da Maryam wacce tunda suke ko awa biyu basu tabayiba batare da sunga junaba ko jin muryar juna dan a skul class nasu d'aya ....yasmeen data gama karantar salim kuma ta tausaya masa ,nan tahango yarima d salis had'e da yah sageer sun nufosu,kowannensu yaja matarsa suka shige mota ,shikuwa salim fau fau fau yace shi motar da Maryam zata shiga zai shiga ,haka ko akai bbu jimawa yah Omar yazo da wata had'add'iyar jib ,Maryam tafito suna like da juna itada salim,shikuwa yah Omar tausayinsu yaji ,agidan baya suka zauna aka saka Maryam atsakkiyarsu yyinda driver yaja motar..


"Ahankali yah Omar yasa lallausan hannunsa cikin na Maryam ....atake sukaji wani shock dan wannan ne karo na farko da yatab'a tabata, k'okarin kwace hannunta ta ke shikuma yarik'e gam"murya qasa qasa yace baby yau baamun mgn ko y'ar gaisuwar bazan samuba ko?"

dukar da kai tayi had'e da gyara rufin lullubinta ,shikuwa salim bemasan me akeyiba yalula tunanin rabuwarsa d gudan jininsa wato Maryam..shiru sukayi duka bbu mai mgn acikin su ,shikuwa yah Omar yyi mata uxuri kunsan amarya da Jan aji ,amma azuciyar sa yace sun had'e gobe wato tazama mallakinsa ,saidai yaki sake mata hannu sai murzawa yake da hakan su iso gun da zaayi dinner din atare suka fito aharabar gun suka had'e d salma da bash nan sukayi  ciki ,suna shiga tun kafin su zauna aka fara musu barin kudi hmmm fad'in irin kyawun dasukayi bata lokaci ne abin sai Wanda yagani..

       Bayan sun zauna aka bukaci aminin ango  yafito yabada tarihinsa ,nan yafi to ,bayan yabada aka bukaci na amarya kawai MC yakira salim isma'il Khalid .....nanfa akayita tafi da ihu nan salim yafito cikin nutsuwa yaba tarihin Maryam atakaice ,bsyan yagama ,aminin bash yafito yyi d kawar salma dg nan suka yanka cake suka ciyar d junansu masu video d camera akayita dauka ana pics ,nan MC yabukaci ganin anguna d amare afilin rawa ,nanfa suka fito akayita musu barin kudi ,su yasmeen k'irjin biki tana makale da yarima ta ko ina zata musammun dataga yan matan gun nata kallonsa dan yarima akwai farin jinin yan mata...yasmeen tayimusu liki sosai hakan yasa marok'angun kod'ata da wasata itada yarimanta atake yarima yyi musu kyautar mota,hakan kuwa yasa duk mutanen dke gun suka San yasmeen nada daraja agun mijinta...


Suma sa Anty lubna da hannan da Anty sameera ba'a barsu abayaba gun liki dan yanxun lubna ta aje makaman yakinta  tadawo hanya ,saidai fa yasmeen bata wani saki jiki d itaba bacin gaisuwa bbu abinda ke hadasu dan duk Wanda yace baya k'aunarka bazakata taba mantawa da kinsa agarekaba.....salim kuwa sunan sa duk yana bakin Maroka sbd  irin Barin kud'in da yyiwa twins sister tashi ...


da hakadai taro yatashi lfy kowa yadawo gd agajiye ...


Washe gari da misalin karfe 11:30am aka d'aura auren Maryam isma'il Khalid da Omar Ahmed akan sadaki dubu dari, bauan angama nasu aka d'aura na bashir bala d salma kabeer akan sadaki dubu dari ,daurin auren da ya halarci dubban jamaa kosu alhj tsoho d baba mlm sun harta dattijan kirki kenan,har cikin gidan Sarki sukaje suka gaisa da jamaa,yasmeen kuwa ta hannun Damar alhj tsoho bayan sun gaisa da ita tayi masu kyautar turare d goro ,sukayi ta saka mata albarka sannan sukayi sallama.


Hakafa akayita hidima da jama'a ab'angarori dana su yah Omar da nasu salma d gidan Sarki ,yasmeen kuwa anayin azahar gidansu ta tafi ....


Da misalin karfe 5:30ne motocin daukar amarya suka bayyana ak'ofar gidan Sarki ....nanfa jamaa sukayi ta fitowa dg ciki suna shiga motar..


      "Acikin gida kuwa salim d Maryam sun rungumeta juna sai kuka suke anyi anyi arabasu amma sunki rabuwa ,dan ita kanta ammi duk daurewarta saidatayi hawaye sbd tabbas sun shak'u da autocinta ta saba da kiriniyarsu da shagwabarsu dasuke zubawa ajikinta ,dan haka bata galaifinsuba dan sunyi kuka...yarima ne da kansa yarabasu had'e da yima salim dubara da cewa ai yayah Omar Wanda yace yyimasa daki agidan sai Yakoma can da zama dan yalura da Maryam sai cewa take ita inbada salimba zasu tafi to ta fasa auren...


Hakafa aka rabasu akatafi da Maryam gidan yah Omar ,gd masha ALLAH yyi dan yah Omar yyi kokari sosai dan harda get gidan dagun shak'atawar su,bayan kowa ya watse akabar su kubra da yasmeen suka d'an kara gyaramata gidan suka sataka tayi wanka ta shirya ,sukuma sukayi sallah nan driver ya aiko su fito.


" gaba d'aya Maryam ta rude hankalinta yatashi ganin gidan yarage saura ita daya,aisaita saka musu ihu ita saidai sutafi tare ....maganar yah Omar taji hakan yasakata jin fad'uwar gaba d gudu tashige bed room itadai yesmeen dariya tayi dan dama tasan duk amarya a irin wannan ranar atsorace take ...


Shikuwa yah Omar bakin nan yaki rufuwa ,koda yashigo yaga su yasmeen ,yawaniyi kicin kicin d fuska had'e da cewa yaya dai malamai?"aiyakamata kutafi gd haka ko?"murmushi sukayi state sukace hmmm yah Omar kenan bakaga driver awajeba yana jiranmu ai tafiya zamuyi basaika koremuba"!murmushi yyi yace to saida safenku....dariya sukayi had'e da ficewa shikuma yashige bed room din Maryam.


Washe gari d misalin karfe 8:am salim yafito d trolley dinsa,zai fice ,ammi dake zaune kan kujera tana lazimi tace kai Auta ina zuwa haka harda trolley? "Fuska asake yace yo gidan Anty Maryam mana can zankoma sbd yah Omar yyimun daki a can!


Salati ammi tayi tace oh kajimyn yaro Ashe har yanxun baka girmaba ,kai bakasan wasaba dan ancemaka haka saika yadda to ahir d'inka nasake jin maganar nan abakinka zan sabamaka yo yanxun ko tashima sunyi ne  mitts taja tsaki...


Ihu salim yasaka ,kamar wani yaro shi sai yatafi ,anacikin hakan yarima yyi sallama.....


mmn fareesa ce✍🏻✍🏻

AWESOME WRITER'S ASSO..🏮


(palace of excitation and pleasant writer's)


YARIMA ASHMAN

🐾🐾🐾🐾🐾🐾


Story & written by mmn fareesa


wannan page din nakune my bestie & mmn sultan kuyi yadda kukeso dashi ina mugun yinku amminnan kwarai ALLAH yabar tare🤝🤝


🅿119&120


🔚🔚🔚🔚🔚🔚


Ihu salim yasaka kamar wani yaro shi sai yatafi ,ana cikin haka yarima yyi sallam.!tsit salim yyi koda yaga yarima ,ammi kuwa kallon sa tayi tace yauwa gara da kazo !ashe yaron nan bashida hankali?"wai gidan Maryam zaikoma....kafin yarima yyi mgn wayar ammi tayi rin

ging, dubawa tayi taga maryamce ,cikin murna ta daga had'e da cewa autata kuntashi lfy? "Yah bakunta?" Maryam cikin shagwaba had'e da kuka n tace ammi wlh yah Omar mugune ni ALLAH gida zandawo wlh tun jiya yake tamun...tsawar d ammi tayi mata yasaka yin shiru "cikin rarrashi tace ya isa banason ji kuma bance kifadawa wani ba kina jina?"ahankali tace to !nan ammi tace to yanxun zanturo jakkadiya tazo ta kula dake takamuku break fast, cikin kukan shagwaba tace to ammi ina my salim?" Murmushi ammi tayi tace gashi kuma bance kifad'a masa maganar da mukayi yanxunba ,nan ta mikawa salim wayar yakarba yanata kumbure kumbure yabar parlourn...

Shikuwa yarima tsa

b yagama fahimtarsu ammi yyidai shiru azucoyarsa yace oh ina amfanin auren karamar yarinya?"ammi ce tace my son inasu arfat ?"murmushi yyi yace suna lfy ,nan yaduka yagaida ita had'e da mata ya gajiyar biki ....suna ta fira salim yashigo yabawa ammi wayarta dan dama Maryam takirasa bata samesaba.

       Yarima ne yakallesa yace kai zonan!bbu musu yaje yaduka gabansa...cikin kakkausar murya yace dg yau nasake jin kace wai gidan Maryam zaka koma hmmm wlh jirgi zansaka dogarawa siyimaka nayima ka dukan tsiya kaiko kunya bakaji?"k'ato dakai kanada 16years kana abun yan4years hmmm to kabi ahankali inba hakaba sai mata sun rainaka wlh...ammi ce tace aigara kayi masa fada ya gyara nibara naje ciki dg haka tadauki alkyabbarta tasaka ta fice..

Shikuwa yarima Ta's yyiwa salim had'e da cewa ko wannan yawan rungumar yaga yana yiwa maryam sai yagane kuransa...nan dai yyita bada hkuri...


***** ****** *****

Yasmeen ce zaune kan 2seeter yyinda arfan keta sukuwa ajikinta,tunani takeyi itafa rabonta da ganin al'adarta tun month na bikinsu yah Omar gashi yanxun watansu 2da aure tana cikin hakan yarima yyi sallama yashigo parlourn d gudu twins sukaje gunsa yad'aga su sama yyinda yasauke arfan ,nan yarika kuka da gwaranci yana nufin asauke arfat adaukesa....murmushi yarima yyi dan sun tuna masa salim d Maryam in sunama ammi rigimarsu", wucewa yyi gefen yasmeen yazauna dan yafahimci kamar tanada damuwa"ahankali yasha fuskarta yace my Princess meke damunki pls ?"konima kinaso nashi ga adamuwar ne?"ahankali tace ah ah yace to menene?"hawaye sharrrrr!ne suketa zuba afuskarta ,arikice yace bazaki yaganba?"cikin shagwaba tace yo ba 2month kenan ba rabon danaga period dina ba ,kuma da k'yar inba ciki bane gashi yaran nan duka shekararsu daya d wata2....ta fada had'e da fashewa da kuka!"ajiyar zuciya yarima yyi ,cikin farin ciki yace ALLAH yasa shine ameen dan wlh inaso .....ihu tasaka had'e da cewa haba ai wlh d sake kaiko so bakayi na huta to inma shine gsky sai dai azubar....

Azabure yarima yace whatttttttt!?mekike nufi yasmeen ?"yafada atsawace Wanda har twins saida suka tsorata da tsawar ,afusace tace abinda kaji !cikin tsantsar mamakinta had'e da jin haushi yace yasmeen ni kike ikrararin zaki xubarwa d gudan jini ?"hmmm lallai bakya sona, son dakikemun k'aryane ,baki tsoron ALLAH dazaki zubarda cikin d'an halak?"cikin kuka tace ai lalurine pls muje abincika in shine sai a zubar wlh haihuwa d wahala bece komai ba yafita afusace...


Bbu jimawa yadawo tare da Dr khadijat yace ta bincika masa yasmeen, nan tayimata yan tambayoyi tasakata tayo fitsari a wata yar rober, bayan takarba ta tafi,bata jimaba d fita yarima yabita ....


Koda yafita yasmeen tabe baki tayi race oho dai haka kawai ina shekarar karshe askul sailawai ka kunsamun ciki d sake wlh dan nafiso nayi service dina wasai bbu wani ciki...yarima ne yashigo bbu ko sallama fuska a d'aure kamar be tab'a dariyaba ..


"" cikin bacin rai yace to yasmeen cikine dke har wata2 inaso kisani wlh duk abinda yasamu gudan jinina kece!kuma bazan taba yafemikiba,ashe baki son had'a zuria dani hmmm to zan auro wacce zataita haifamun yara...ai tuni su yasmeen wani kishi yatasomata ,shikuwa yafad'ane dan yyimata barazana dan yasan ko yyi aure bazai iya adalci atsakanunba cos yanawa yasmeen wani SO nadaban.... Muryarta yaji tana cewa oh naji ciki saina zubar kuma kaima banasonka gidanmu zani saika auro wacce kakeso aidama ance d'a nmj bashida tabbas tana fad'in hakan ta ture su arfat dke gabanta had'a da cewa kuma na tsaneku d gudu ta wuce bed room dinta ...


Shikuwa yarima gaba d'aya yasmeen ta hargitsa masa tunani ta daga masa hankali ,bawan ALLAH saiyaji dama rarrashinta yyi ,twins yadauka ganin suna kuka bed room din yashige....mamaki yakeyi gani yasmeen na kuka tana shirya kayanta acikin trolley da alama dai gd zata tafi kenan..


Fita yyi yaje yakaisu twins parlour yabazamusu kayan wasansu Yakima a bed room din yasmeen."


Samunta yyi tana k'okarin saka hijab nata da azama yanufeta had'e da rungumota ajikinsa...afusace ta kwace jikinta ,shikuwa gam yarik'e ta "cikin rarrashi yace pls my Princess kada kitafi kinji?" nida yaranki muna bukatarki pls....aisai ta ida haukacemasa tanata zizzile zizzille da ihu d koke koke ita sai tatafi afusace yad'aga hannunsa ya wanketa da mari.....dafe kuncinta tayi ciin itsantsar mamakinsa,shikuwa fita yyi had'e da saka key yarufe k'ofar....


"Taja taja amma taki budewa kan bed ta fada tasaki kuka mai cin rai"


Shikuwa yarima mota yahau yawuce gidansu,bayan ya isa  part din ammi yawuce idanun nan nasa sunyi jajir ,kallo d'aya ammi tayi masa tasan bbu lfy ,cikin rudani ta tambayesa meke faruwa ,shiru yyi beyi mgn ba ,sake tambayarsa tayi...cikin damuwa kamar zaiyi kuka yace ammi yasmeen ce ,ammi zata zubarmin d cikina ammi wai gidansu zata tafi bata sona nida yaranmu bakiga yadda ta turesuba ,yazanyi ne?"yazanyi d rayuwata takasa fahimtar haka ALLAH yatsara!


Ammi tace subhanallahi! Tana ina yanxun?"nan yace tana gd a cikin bed room dinta na rufeta nan ammi tace kaje gani nan xuwa nan jiki b kwari yafice ...

Kai tsaye motar yashige ya koma gd.


Bakin k'ofar bedroom din yatsaya,taba jiran zuwan ammi anan ammi tasamesa ,nan yabude suka shiga ,yasmeen nakan bed tana kuka ,kallo daya ammi ta mata tagane cewa yarima yamareta ,tashi tayi ta fada jikin ammi tana kuka had'e da cewa pls ammi kisaka yasauwakemun bazan iya zama dashi da wataba ,atake ammi tagano k'ila cewa yyi zai zai kara aure..


Nan ammi yakamata suka fito parlour ,bayan sun zauna ,ammi ta tambayi yarima meke faruwa ,Ta's yazayya nemata komai,ajiyar zuciya tayi bayan ta tambayi yasmeen ta ce eh hakane..


,,,nan ammi tayi musu nasiha da cewa ada bahar gorin haihuwa akewa makuba har juya ancemiki ,sai yanxun kikeson butulcewa ubangijinki  to tun wuri kituba ga ALLAH kibawa mijinki hkri,sannan indai dan yara ne ni dg yau zan karbesu in maidosu guna yaye...har sai kin haihu ..


Shiru yasmeen tayi dan jikinta yyi sanyi ,wani k'aunar ammi tayi da son mijinta ,dan yanxun maganar da ammi tayi ta tunamata d gorin dasu hjy babba d Anty lubnasukayimata ,nan taita bawa ammi hkri.


Nan ammi race bbu komai yawuce ,tadai nawa mijinta hkri,nan yakalli yarima taga yyi mata kuri d ido yyiwani wuri wuri dashi,"ahankali tace yaya kayi hkuri ka yafemun bazan koma ba"ahankali yace ba komai yawuce nima kiyafemun Marin danamiki nan tace ta ya femasa,cikin jin dadi ammi tasaka musu albarka had'e da saka kuyanginta dke waje su dakko mata twins ,nan su ammi suka bar gdn tare da twins ,yasmeen ko bbu kunya ta rungume yarima duka fada wata duniyar...


BAYAN SHEKARA 6


Agidan yasmeen na leka ,wasu kwawawan yarane nagani zaune a waiting parlour d yuni foam na light blue ajikin mata 2,farare kal kuma jikin maza3 sai wasansu suke .


Arfat dke babba wacce ke yar 8years ta kalli arfan tace kanina muje islamiya lokaci yyi ,make kafada yyi yace um um sai mommy ta zo tamana addua sai driver yakaimu ....sallamar da yarima yyine yasaka yaran  da 3gudu xuwa gunsa, wato elham wacce akasakawa marya (sunan umman yasmeen) sai sadeeq da imran ,dagasu yyi daya bayan d'aya sai dariya suke nan su arfat sukazo suka yimasa sannu da zuwa... hmmm su yarima Manya kenan matashi maiji d kudi d ilimi kuma d'an gatan matarsa yakara frash fatarsa tayi had'e da shek'i ,alamar Hutu na jikata ...


Wata sweet voice naji tana cewa oyoyo my man yaushe kadawo?"juyawa nayi wow Masha ALLAH su yasmeen anxama manyan mata tak'a kyau da wayewa tayi yar kiba ,murmushi yarima yyi yace eh my Princess gashi kuma yaranki zasu kayar dani ..turo baki tayi kamar yarinyar ta kallesa had'e da cewa kuxo maza nayimuku addua g driver can najiranku yakaimu islamiyya....nan sukazo tamasu suka fice ..


Kan kujera taje hade da hayewa saman cinyar yarima ,yar kara yyi yace oh my Princess gsky kinyi nauyi d yawa kidagani ,dariya tayi ta ce oh ka rama ko  ?"murmushi yyi yace ni na manta ammi race afadami gobe ake saka bikin autanta ...ware ido yasmeen tayi ta ce oh salim yadai rantse sai yyi auren nan ,cikin rad'a yarima yace ai gara ayimasa yasha gara yafada hade da daga mata gira ,yamikar da ita dg jikin sa yace muje ciki ki sallameni tunda yara basa gd ...


Bed room d'in su suka nufa kan bed suka kwanta da Sauri yarima yaja musu blenket yace my Princess mu rufe jikinmu kada mmn fareesa taganmu tasamu abin fad'awa fans d'in ta...


Tamat bi hamdilillahi..


Anan nakawo k'arshen wannan littafi kuskuren danayi yah ALLAH kayafemun abinda nayi daidai ALLAH kabani ladar..


AFUWAN! AFUWAN!! AFUWAN!!!

Yaro ko babba duk Wanda na batamawa a wannan littafi ya yafemun.


GODIYA

Nagode! Nagode!! Nagode !!!ga kamar dasuka fara bina tun dg farkon fara wannan novel har xuwa wannan lokaci ALLAH yabar kauna...


GODIYA 2


Ina godiya ga duk grps d'in da ake posting wannan novel ,kunyi yawa sunayenku ,alkalamina bazai iya rubutawa ba saidai yabo d jinjina agareku ,insha ALLAH mmn fareesa natare daku Dari bisa Dari dg karshe sai mun hadu asabon novel dina mai zuwa insha ALLAH🤝🤝😍😍


gaba d'aya wannan novel nasadaukar dashi gareki halak malak my lovely sister Hauwa'u Usman lado (Jidda)


Mmn fareesa ce ✍🏻✍🏻

No comments