Miwasmiti Complete Hausa Novel




🕌🕋🐄🐄🐄🐄

📝💫Bismillahirahamanirahim***🌳🐄

Mi'wasmiti. Page 1⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🕌🐄🐄🐄🐄🐄


Tafiya take cikin sauri sauri da Dan sassarfa tana tafe tana Dan mita da holo irin Na tsofaffi da sauri Na dan qarisa gunta Na Dan kalleta a nitse a take Na gano tsohur ba fillatace cikin hikima Na gaidata da yaren fillanci cikin Dan sakin fuska ta amsamin ba tare da ta tsayaba a hankali Na bita gami da cemata kakata ina zakije haka da sanyin safiya gashi sai sauri kike kamar wacce jirgi ke shirin tashi ya barta .. 

Ta Dan juyo ta kalleni tare da ci gaba da tafiyarta tana mai cemin ba doleba nai sauri ai ko faduwa zanyi Na fasa bakina Na zubda haqaran robar sai Na hamzarta .ai shi yafi jirgi shi sama da jirgi yake in ya shirya baya jiran kowa kuma shi jirgi ai yana  bada lkci. toshi bai bada lkci shi tamkar hadari yake inya fito tofa ba jira kuma shi kamar guguwane sarkin birkita taro....

Cikin mmk nace keko kakata waye wannan ? kuma a ina yake? Cikin surutunta da  mita tace gidan kamannin zani zanyi aikene Dan yau zasu gembu cikin mambila ..da Dan sauri na bita nace gidan kamanni kuma ?su haka sunan gidan yake ? Wannan wacce irin kamace dasu ? Na jera mata tabbayoyin  aiko ta fara bani lbri tiryan tiryan🐄🐄🐄


Zuriyar Alhj Muhammad babayo Wanda akafi sani da Mlm babayo kuma sarkin shanu Dan asalin jihar tarabane can cikin mambila.  Matansa 2  yayansa 5  maza 4  mace 1 uwar gidan innayi tana da Yaya 3 maza 2 sai mece 1 babban dansu barrister Muhammad Bello Muhammad sai mai binshi doctor Aliyu Muhammad sai qanwarsu Aysha.Muhammad


Sai amariyar yayanta 2 duk maza Amadu shine babban danta sai hamisu 

Duk da kasan cewar mlm babayo ba fillatanine baiyi qasa a guiwaba wajen ilmantar da yayansa ilimin zamaniba sunyi karatu mai zurfi 


Barrister M.B.M Wanda suke kira baba bello yana da matarsa daya Nenne Aihuwarta 12  Amman yanxu haka yayanta 3 ne kadai sabida aihuwar wabi take Sadiya itace babba bayan aihuwar sadiya sai da tayi aihuwa 5 duk suna komawa sai Na 7 in ta sami da namiji mai suna Ahmad tokoran qaninshi Amadu bayan Ahmad ta kuma aihuwa 4 duk suna rasuwa sai ana 12 ta samu Allah ya barmata shi sunanshi Rabi,u...


Sai  doctor Aliyu Wanda suke kira Abba da matarsa Ummi yayansu 4 Yusuf shine babban dansu sai Abubakar da Usman sai Autarta Aysha .


Sai Goggo Aysha wacce take Aure a Yola tana auren doctor Umar babban Abokin yayanta doctur Aliyu Abba kenan yayanta 3 Adam sai hydar sai Maryam 


Sai Amadu Wanda suke kira baba matarsa 1 yayansu 2 Abdul sai Amira.


Sai baba Hamisu matarsa 1 dansa 1 Sadiq .


Kamanni Family zuriyace da ta samu wadata da rahamar ubangiji Allah ya musu baiwa tako ina ga ilimi ga kyau ga arziqi ga zaman lfy da qaunar juna da tsantsar shaquwa da tausayawa 


Su yayan inna basu karatu sosaiba sai suka Koma makarantar Dan gote baba bello da Abba su suka budemusu wani katafaren filin seye da sayarwa mai suna kamanni family kuma su Amadu da Hamisu suna zaunnene da iyayensu acikin garin mambilan yayinda

 bb bello da Abba suke cikin taraba da zugar iyalensu sai dai alqawarinsu ne duk weekend suke zuwa gaida iyayensu da qannensu 


Years en Adam da Yusuf da Ahmad dai daine Sa.annine su randa akayi 40 en Adam a ranan aka aifi Yusuf ran sunan Yusuf kuma aka aifi Ahmad rayuwarsu Ahmad Abin Sha.awane da burgewa rayuwace mai tsafta sun kasance masu qaunar juna ga wani irin kamanni da suke fiye da tunanin mai karatu mutane da dama sukan dauka yan 3 ne sabida zallan kama fararene tas irin farinnan mai daukar hankali gasu kyawawa tamkar larabawa ga tsantsar cikar haiba gashin kansu tamkar indiyawa kamanin su kuma ya samo asaline sabida dukkansu da iyayensu suke kama sukuma iyayen kamane Na haiqan a tsakaninsu 


Sabanin abinda ke sakaninsu sai  hali haqiqa halinsu ya banbanta dana juna kamar yadda wasu al.amura suka banbanta a tsakanin su Adam irin mutanenane da zan iya cemusu fadi garas mgn dai da zaran tazo ransu toh fa zata fito yana da yawan surutu da abin dry gashi da raha 


Ahmad bawan Allah damo sarkin haquri haka Allah yayishi shi mutumne mai haquri da tawakkali ga sauqin kai ga iya zama da jama,a gashi da fara.a ko yaushe fuskarsa Na dauke da murmushi Sam bai iya fushiba shi....


Ayagi sarkin fada mishkili kafi mahaukaci ban haushi muqu baya dry sai Abu ya baci Yusuf yadda wasu Al,amura Na rayuwarsa yasabawa sauran jama,a hakama halinshi shi Yusuf irin jarirenane da ake aifarsu da kaciya a jikinsu shi da kaciyarsa ya fito duniya  tun tashinshi bai da yawan mgn haka kuma baison yawan surutu gashi da ra.ayin riqau ba,a juyashi yana da zuciya ga iya horon yara baison shishshigi da Sa ido ko Kadan madafacine sosai zakayi zaman shekara dashi bazakaga dryarsa ba haka kuma ko shekara 4 zakayi dashi da wuya kaga qwoyar idonshi kuma kab wanan halin bb bello ya gado yayinda shikuma Ahmad ya dauki haqurin Abba danshi Abba tamkar ba mai suna Aliyu bane. Amman duk da fadan Yusuf bayayi da su Adam sun shagu shaguwar da ba adadi tare suka tashi gida 1 daki 1 don dole mahaifin Adam ya haqura ya barshi a taraba tare sukayi marantarsu tun daga primary har xuwa university innada sukayi digiru ensu Na firko a qasar India Yusuf da Adam sun karanci medicine shi kuma Ahmad Abba ya sashi ya karanci business Amnan shi Yusuf  yanxu haka yana karatu a jami.atul Madina enda yake qara karantar likitanci a musulunci Sai in sun Dan samu Hutu yake zuwa kamar yanzu tun cikin Ramadan yazo duk ya buwayi qannenshi mu samman Aysha da basa hada inuwa daya tamkar wuta da audiga haka kuma su Usman da Abdul d Rabi,u suma duk ya fara gungurarsu Amira ko dama cewa take suna zuwa bikin sallah bazata dawoba sai ya Koma Dan ita Amira a gaban bb bello take  haqiqa kowa najin takaicin yadda Yusuf da Aysha basa shiri qiyeyyace sosai Yusuf yake mata wasu lukutan ji yake kamar ya karyata Ahmad kuma wata soyeyyace mai qarfin gske ke tsakaninsu hakama Adam da Amira 


Kumuje zuwa dai Ku biyoni a hankali lbr Na can gaba  🐄🐄🐄


By garkuwan fulani

[4/9, 1:47 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI.....page 2⃣        Na Aysha Ali Garkuwa 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 


Taci gaba da bani lbr su Usman da Rabi,u da Abdul ma Sa,annine hakama Aysha da Amira da Maryam  ...

Yusuf ya kasance mai zuciya tun yana dan yaronshi sanadin zuciyarshi yanzu haka yana da matsalar ciwon zuciya💔 tun suna primary school yana dan shekara 6 makarantar su da aka shigar dasu yinifom en makarnar dan gajeren wondone da yar riga Amman tunda aka dinka musu kayan Yusuf yake ta faman cin rai shi ala tilas bazai Sa gajeren wondo ba dan shi ya kasance mai kunyar bayyana jikinshi tako wanne bangare ne ba yadda ba,ayi da shiba yaqi Abba yace sai a shigar dashi wata makaratar nanma yaqi yace shi dai inda su Ahmad suke nan zaije dole akayiwa shugaban makarantar bayani da yake abokin bb bello basu samu matsala ba 

Yusuf ya kasance mai kwarjini agun abokan kara tunshi kowa so yake  yarabesa ko dan ilimin da Allah ya bashi 


Wata rana a makarantar yayi fada da wani yaro Mujaheed  aiko suka rinqa gudu dan ya samu ya yarama Amman ya kasa kamo Mujaheed ga mlmansu da suka shiga tsakaninsu shi kuma yace dole sai ya rama da aka hanashi ramawarne ya rinqa kuka cikin xuciya da takaici kuka yake har numfashinshi Na yankewa basuyi auneba ya fadi sumemme 


Kai tsaye gida suka kawoshi Abba ya dugufa coto rayuwarsa da qyar aka samu ya farfado yana tasowa da kuka ya farka yana wlh ni sai Na rama bazan yardaba abi dai yaci tura dole aka nemo yaro yazo da iyayenshi yana zuwa Yusuf sai cewa yayi yazo gabansa ya duqa zai rama Abban mujaheed ya tura masa shi yana jeka ya rama aiko ya samu tsakiyar bayan shi ya rinqa dakamar duka gami da cemai wlh in baka ban haquriba bazan bar kaba yaro ya juya ya bashi haquri 

To daga nan suka zama abokai 


Ta dan zagaita surutun nata ta kalleni anitse tace to abinda yasa kikaga ina saurin Yusuf yazo nasan zai azalzalamusu su tafi ba tare da nakai aikenaba.""""

Na danyi dariya a raina nace hajia Zubaida ikon rabbi daga tabbaya daya taban bayanin da ya zarce zatona 

Tacemin jikata ban sankiba gashi har mun saba daga ina kike haka nadan kalleta a nitse nace ni bakuwace daga jihar Adamawa nake sunana Aysha Ali Garkuwan Fulani kuma dama nazone gun Fulani yan uwana saiko nai Sa,ar cin karo da zuriyar sarkin shanu nima zasu barni Na kaimishi gaisuwar sallah ko? a madadin babana 

tace sosaima kuwa ai suna son baki 


⭐⭐⭐⭐⭐⭐


Babban gidane Na gani Na fada acikin babban birnin taraba  gate en gidan ma kawai abin kallone ga ma aikata tako ina jamin sarone masu tsaron barrister M B M cikin gidan muka nufa kai tsaye wani babban parlor mai kama da dakin taro cike yake da mutanen gidan cikin hikima Na zuba musu  ido 👀 dan naga wani abin al,ajabi kamace ta gsky a fuskokinsu gaba dayansu shiga iri daya sukayi galilace mai kyau da tsada bb bello da Abba suna zaune kan kujera daya tamkar tagwaye sai dai Abba ya dan fishi tsawo sai Nenne da Ummi suma suna zaune wuri daya cikin shiga ta alfarma da ka gansu kaga jin dadi da kwanciyar hankili haqiqa Nenne macece mai mutunci da kawaici da tsantsar qawaunar dan wani ga alkunya bata iya gwada son yayanta sama da sauran yaran Ummi Na mutunta ta matuqa 

Daga can gefe kuma su Usman ne suna dan hiransi.


Ahmad kuma da Adam suna tsakiyar porlon kan wani tattausan carpet Sai Amira da take ta zirga zirgan zuwa tadda Aysha wannan zuwanta Na 3 kenan sai ta tashi ta zauna da zaran Amira ta fita sai ta sake nadewa a borgo 


Muna shigowa ba jimawa 


Naji wani irin qamshi mai ratsa zuciyar dan Adam nan take parlon ya hargitse da qamshin mai dadin shaqa gaba daya Na maida hankalina kan qofar danafi zaton tanan qamshin ke shigowa

 

Cikin nitsuwa yake tfy da cikar kamala taku yake da salon girma hasken fuskarsa kamar tauraro⭐ komai najikinshi tamkar shi ya tsarawa kanshi kai tsaye gaban bb bello ya dan duqa ya gaidashi ya gaida su Nenne ya dan miqe yana gyara riqon da yayiwa briefcase enshi da woyoyinshi ya miqawa Ahmad hannu suka gaisa Adam ya dan harareshi cikin tsokana yace kai yaro ninefa babba ka fara gaida kanina ya qarishe mgnar yana dry

Ya dan kalleshi cikin salon ka isheni da shegen son girma


 Abdul dake gefe yace good morning Hamma Yusuf a hankali  yace morning Usman dake zaune gefen Abdul yace da kyau ba gaisuwaba ai yayi mgninka shi ko gaisuwar baiso dan haka ni bazan wahal da bakinaba Rabi,u ya danyi dry yace ni bari in gwada ya dan kalleshi da kyau yce Hamma Yusuf..... da sauri ya daga mai hannu ya yimai nuni da su taso su tf ya dan kalli bb bello yace baba mu tafiko 


Sagal kaka ta amshe mgnar tana mai cewa kai Yusufa ni ban kai ka gaisheni bane komeye kana tafe kana yamutsa fuska kai dai har Abadan baza,aga fara Arkaba 

Rabi,u ya ce toh ma ai  Aysha muke jira tun dazu bata fitoba ya dan juya ya qarewa parlon kallo bata gun Amira dake manne jikin Ummi sai yanxu tace Hamma Yusuf ina da sauri ya dakatar da ita gami da cewa cikin mishkilanci da Alamun bacin rai yana mgn da dan fada fada ke tashi kije ki kirata in kuma ba hakaba wlh zan shigo Na babbalata muna fukar yarinya sai baccin tsiya ta iya da sauri ta nufi dakin 

Kaka kuma taci gaba dacewa Amira kije kicemata jirgin✈ ya iso kuma har ya fara dirin tashi ta dan juyo ta kalleshi kanshi a qasa tace mutum baida aiki sai sababi ni wlh ai wannan turaren daka zubbuda zai sani mura Abu kamar anyi barin motar turaren ta kuma shaqar qamshi tai ajiyar zuciya tace gsky ka tsammin turaren dan wlh yamin dadi ya kalleta cikin murtuqe fuska ya dan tabe baki

 Adam ya kwashe da dry yace kai kaka sharrinki yafi ta tsohuwar mota yanxufa kikace zai kasheki da turaren zai saki mura sai kuma kice ya baki duk sukayi dry yace Allah biyaye karka bata ta dan harari Adam tace toh dan hassada kada Allah yasa ya banin mana ga mai gidana zai sayamin ta fada tana kallon Ahmad ya danyi murmushi yace zanma dauko miki nashin matar 

Tai dry cikin jin dadi Usman yace toh yaukuma menene saqon naki?

 tce kai da Allah tafi daga can mai muryan mata kai sai shegen made Amman dai duk da hakan kafimin yusufa kam ta maida hankalinta kan Ahmad tece Ahmadu in kaje kace innayi ta baka naman raqumi nakeso..... aiko su

 Rabi,u sun sami abin dry Yusuf ya kalleta yana cewa Aku kawai baki da aiki sai surutu sai shegen kwadayi ke dai nama nama kowa ya gaji da nama Amman banda ke 

Edin tace nayi surutun so kake naita baqin hali irin naka baki kamar dinkekke andai ji jiki wlh kuma sai kaban turarenan ehe 

⭐⭐⭐⭐

Kwance take ko a jikinta kamar ba ita ake jiraba cikin sauri Amira ta daka mata duka ke Aysha toh wlh ga hamma yusuf ya fito 

Da sauri ta bude ido gami da zazzarosu 😳 ta diro daga kan gadon tana qoqarin cire kayan jikinta gaba daya jikinta bari yake tana shiga toilet tana Na Shiga uku 🙉 dan Allah Amira fitomin da kayana da mayafina da takalmi yau kam Na kade mugu ya samu dan dalilin jibgata 


By garkuwan Fulani 


Ku biyoni masu karatu wannan goron sallarkune daga gareni

[4/9, 1:47 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 MI,WASMITI.....page 3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


9:55 PM*12-09-2016


Bayan ta gama yan gyare gyarenta ta fito sab da ita gonin sha,wa Doquwar rigace ajikinta tayi kib da ita cikin sauri ta dauki ribbon enta da dan kwalinta a hannu ta fito parlon tfy take cikin sauri sauri hankalinta gaba daya nagun Ahmad shiyasa bata lura da shi a gunba tana isa ta miqawa Ahmad en ribbon en gami da dan juya bayanta tce ya Ahmad gashi tufkemin gashina ga yan kunnena ma ka samin da sauri kasan yanzu za,aitamin masifa Karba yayi yana murmusawa ya dan matso yana tattara gashin da ya kwanta har kan kafadunta 

Rabi.u ya dan kalleta cikin jin takaici yace wlh kedai kinji jiki kina mace Amman wai sai maza ke shiryaki....cikin tsiwa tace endin aiba kai nace kaminba ehe Yusuf dake tsaye a gefensu takaici ya gama cikashi yarinya ta bata musu lkci sannan ta fto tana musu rasar kunya  cikin jin haushi ya ware tafin hannunshi zai shimfi da mata mari da sauri Ahmad ya dan jata jikinshi ya tura fuskarsa aiko marin ya sauka kan lallausar fusakarsa Adam ya dan juyo dan jin sauqar marin kai biyaye lfyarka kuwa ?  a harzuqe Yusuf en  yace wlh yau zakici dan banxan duka kaji muna fukar yarinya ya kalli fuskar Ahmad a take tai jawur abinka da farar fata hatta zanen yatsunsa sai da suka bayyana a kuncinshi ita kam tuni ta gudu gun Nenne cikin jin tsanarta ya kalleta ya kadai kai gami da cije lips enshi ya fita a fusashe

Amira ta kalleta shike nan Aysha kin kade wlh saikinfi fura kirbuwa agun Hamma Yusuf kika Sa ya mari ya Ahmad ai kinshiga tara..tai rau rau da ido tace dan Allah Ummi ki bashi haquri. Usman ya harareta yace Wlh ya dakakin dai Munafuka ba  bakya tsoron kowaba tun yaushe muke jiranki sai kace kece uwarmu gaba daya..

Nenne tace yi shiru abinki bazai dakekiba 

Bb bello ya miqe hadi da cewa kutaso mu tfi..


Motocin 3 ne a harabar gidan daya  Usman ne ke jansu  bb bello da Nenne sai Abdul da yake kusa dashi daya kuma Rabi,u ne ke jansu Abba da Ummi suna baya sai Anty Sadiya dake gefenshi a hankali suka fita harabar gidan sai dayar kuma  Yusuf ne xaune a ma zaunin driver Adam ya zauna a gefenshi sai Amira da Aysha a baya Ahmad Na daga tsakiyarsu Aysha Na maqale da hannu Ahmad a jikinta  duk ta rude 


Kusan minti 20 da fitarsu bb bello Amman shiru yana zaune sai danne danne yake a lap top enshi  tamkar ba masu shirin tfy ba Adam ya dan kalleshi cikin yanayi yadai yace haba biyaye tfy fa zamuyi kuma kai zamanka ai ya kama mu tfi ko shiru kamar badashi akeba sai gyara zamansa yayi ya dan kishin gida da jikin kujera Ahmad ya danyi mirmushi cikin muryar lallashi yace tuba muke yayana aimana afuwa a huce plss mu tf kasan Abba zai ta jiran isowarmu ya juyo ya kalleshi ya maida kanshi a hankali phone enshi ya fara suwa ya balle marfin motar ya fita gindin wata bishiyar manqoro 🌳ya zauna kan wasu kujeru da aka tana dan zaman mgn yakeyi kamar baison ya dan hada fuska yana mai cewa Rashida ni fa bana son fitina ai sauri kikayi aiki ne yamin yawa ko zaman kiranki zanyi cikin muryar gudun matsifarsa da tsantsar qaunarsa tce ayyah Yusuf yau kwana nawa bamuyi mgn ba kai baka kirana saidai in ni Na kiraka sallah guda bazaka kiraniba mu gaisa cikin gajiya da mitarta da surutun nata yace ya isa ya isa haka badai gashi yanxu mun gaisaba ni yanzu ina da abin yi da sauri tace dan Allah kar ka katse kiran Yusuf yaushe zakazo ne ? Barana ya bata amsa a gajarce ya katse kiran cikin jin takaici ta qurawa phone📱 nata ido a fili take cewa ya Allah ka mallakamin zuciyar 💛Yusuf ka juyomin hankalinshi gari Allah ka sassautamin sonsa a raina Rashida yar kano ce kuma tare sukayi karatu dasu Yusuf a India allah ya jarabceta da qaunar Sa a ranta shi kuma mishkilanci da taurin kai da ra,ayi sun hanashi maida hankali kan ko wacce mace 


A hankali Ahmad ya zauna gefenshi biyaye ya kirashi cikin sanyi muryarsa tashi mu tfi ko ido ya zubawa fuskarsa hannu yasa ya shafa fuskar yace biyaye meyasa meyasa zakasa hannuna ya mari fuskarka Kasan kimar fuskarka gareni kuma kasa Na cutar da zuciyata bana qaunar duk wani abin da zai tabamin gangarjikinka da lfyarka wlh naji tsanar ta araina dan ta sani Na mari dan uwana da hannuna.

Cikin sakin fuska Ahmad yayi ajiyar zuciya ya shafa fuskartashi cikin murya mai nuna gskyar abinda yake fada yace biyaye zafin marin a fatata ya tsaya bai shiga cikin 💘 zuciya taba hakazalika komai kamin duk zafinshi bazanjiba Amman da marinnan ya taba fuskar Aysha Na da zuciyata zata soku da dafi 💘ya daura hannushi kan kafadarsa yaci gaba da cewa biyaye komai nakeso a  duniya kana tayani son abin ya akayi ka kasa tayani son Ayshana meyasa zuqatanmu suka samu sabani kan Aysha ni duk zuqar numfashin da zanyi a duniya da nauyin qaunar Aysha nake janshi yayinda kai kuma da tsanarta kake Jan naka numfashin meyasa ya tsura mai ido cikin yanayin tabbaya idonsa sunyi jaa shi bai saniba mganganunshi qara samai tsanarta suke a cikin zafin nama da sauri ya nufi gun motar 

Da garfi ya fixqota waje ya watsa mata mari ciki jin radadi tasa kuka ta dafe quncinta da gudu ta fada qirjin ya Ahmad tace Hamma Yusuf dan Allah kayi haqiri wlh bazan qaraba Amira kam tuni ta rakube jikin glass A hankali Ahmad yace ngd biyaye mu tafi tunda kayi abinda ranka ke so ya jata suka shiga 

A fusashe ya figi motar

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

MAMBILA


Bayan isarsu baba bello da kadan suma suka iso parlon cike yake maqil da zuriyar bappa yaya bayan gaishe gashen da sukayi shidai yusuf su babba Amadu kawai ya gaisar ya koma can gefe ya zauna ya bude lap top enshi yai ta dan danne danneshi Sadiq yazo kusada shi ya zauna suna dan dubawa tare dan haqiqa yana qaunar yaron duk da ba wani mgn dashi yakeyi sosaiba 


Abba ya kalli Ahmad dake zaune kusadashi yace Ahmad meya tsayda ku ? ya danyi murmushi yace Abba kawaidai mun tafi a hankaline ya jinjina kai yace toh kun kyauta 

Bappa yaya ya dan kalli Yusuf daya murtuqe fuska yace kai Dudabe har yanxu baka Koma bane ya daqo ya zuba mai harara dan ba abin da ya tsana kamar kiransa da Dudabe da bppa yaya yakeyi yaci gaba da cewa Ahmad shi har yanxu hutun nasu bai qare bane ? Ehh da sauran lkci dai ya bashi amsa

 Adam yace wai kai menaka da komawarsa ne ko a kanka yake zaune baba bello yace Adam haka naka dama kai inkazo dai toh sai kai ta sokano mana su     innayi tamiqe tana nasan yusufa da tea bari Na kawo maka ta dauko flask en da cup ☕ta dire mai a gabanshi tace ga shayinka dan nasanka kananan kamar balarabe ya dan kalleta ya motsa bakinshi a hankali yace sai anjima zan Sha.ko Sadiq dake gefenshi Badon yana kallon bakinshiba da bazai San me yaceba inna ta dan tabe baki tace yayi ai In dai Yusuf ne ya iya gwatsale mutane Bappa Yaya yace Dudabe har baki 3 bai amsaba bai kalleshiba ya danyi dry yace Allah sarki Dudabe am mu muna sonka kamar mu mutu kai kuma kana qinmu kamar ka mutu duk suka danyi dry Adam ko dry yake hard a buga hannu yace madallah biyaye toh Bappa Yaya mu da bakwa son kuma ko zaku kaimu bola😂 haka dai sukai ta hira da nishadi hirar zumunci 


By garkuwan Fulani

[4/9, 1:47 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇MI,WASMITI.....page 5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

A hankali ya direta kan kujera hadi da manna mata kiss a goshi Nenne ta kallesu cikin qauna ta murmusa tace kai Abubakar kamar dama ita kadai kai kewarta da sauri cikin dry ya duga gaban bb bello ya gaidashi da Abban su Ummi farin ciki take sosai tanajin dadin yadda Abubarkar ke mu,amala da qanneshi tamkar abokan watsanshi zafi sosai takeji a ranta in taga yadda Yusuf ke hantarar su da donqofarsu Sam baya zama  dasu yayi hira Sam abin bai mata dadi amatsayinsa Na shine babba 

hira suke sosai tana maqale jikin ya Abubakar ga Ya Ahmad a gefensu Nenne ta kalli Amira tace toh kunyi ta mai hidima yanxu kuma kun xo kuna ta surutu Baku kawo mai abincin ba da sauri ta miqe gami da dauko abincin Yusuf dake gefensu mamaki yakeyi sosai a ransa kome su Ahmad keji da maqalema yara qanana basa ko jin kunyarsu da gudun karsu rainasu abin haushi yake bashi sosai ya sake kallon yadda Abubakar ya ke ta lallaba yarinyar har abin kyamama yake bashi ga uban surutu da suke zubawa kamar parrot  ko bakinsu bai gajiya da cokoikoiwa cikin qosawa da surutun nasu ya miqe ya zai tafi a lkcin Kuma Abubakar ya dan ture Aysha a jikinshi yace Auta baki kawomin ruwaba fa ta miqe kenan sukayi ido 2 da dodon nata cikin razana da tsantsar tsoronsa jikinta har bari yake bata San sanda ta furta إنا لله وإنا إليه رجعون،الله‍م اجرني في مصيبتي وأخلف لي خير منه‍ا ya kalleta da kyau yana qoqarin gano me take nufi shine matsifar ko qaqa ai bata bari ya idda tunaninsaba ta juya da gudu tai dakinsu hakanne ya tabbatarmai dashi din take qoffa yayi ya girgiza kashi gami da cije lips enshi ya fita  Sukama sukaci gaba da hiransu Ahmad dai ya gano Abinda Yusuf ke nufi Aransa yake mmki wai ace mutane uwa daya uba daya Amman basa taba haduwa gu daya kamar wuta da auduga 


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ 


A hankali take tfy har ta iso qofar gidansu dai dai baking get in taga wasu maza su biyu zasu kai Sa,annin ya Ahmad kanta a kasa tana tfy cikin gaji tana kai gidan kaka sai shegen nisa in bakajeba tai ta mita tazo daidai gunsu da sauri dayan yace yauwa qanwata yaki ta dan kalleshi a nitse ta iso ta gaidasu suka amsa da fara,arsu dayan yace aha qanwata in kin shiga kicewa yayanki Yusuf ya fito mu tafi 

Ta dan kallesu a yatsine tace ni bani da wani Yaya mai wannan sunan ehe ban sanshiba ta qarishe mgn tana qoqarin tfy da sauri suka kalli juna har suna hada baki wajen cewa ina ke yar gidannane ehh ta basu amsa da mmk sukace kuma kice baki San Yusuf ba ?

Ta dan juya ido tace ehh ni yayuna ba Yusuf sai ya Ahmad da ya Adam kuma basannan ta juya  da nufin tfy a firgice ta zaro ido 😳ta dan ganinshi a bayanta juyawa tayi da sauri zata Koma inda ta fito cak ta tsaya sabida tsawar da ya watsa mata maza kixo ki wuce gida yarinya sai shegen yawon tsiya zan kamakine ya kada kai suka shiga mota itako tai cikin gida  

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ 


Bayan sallan 🕌isha Ahmad ya shigo gida a lokacin tare suka shigo da Abba ya ajiye mar jakarsa ya fito a parlor suka hadu da Aysha su Ummi Na zazzaune ya dan kalketa cikin salon tsantsar qauna ya dan shafa cikinshi yace Aysha yunwa nakeji a kawomin abinci dan Allah toh tace cikin zumudi tace ya Ahmad me zan dafa maka ?hankali cikin murmushi yace matayassara Ummi ta danyi dry tace inbanda abinka Ahmad gani ga Nenne duk baka tabbayemu abincinba sai itta zaka tabbaya ya dan Sosa qeya yace uhum Ummi ai gwara tun wuri ta koyi kula dani dan nasan Abbbana kam ya bani ita sai dai bansan me baba kuma zai ceba ya dan kalli Nenne yace Nenne inason Aysha inasonta a raina bana iya boye sonta a zuciyata💛 da Zahirina cikin wani yanayi Nenne ta kauda kanta daga kallon dan nata

 abin qaunarta Tanajin Ahmad tamkar bugun zuciyartane ya matso gabanta ya rusuna yace Nenne banason yadda kikemin in namiki mgnar Aurena da Aysha 

A hankali ta daura hannunta a tsakiyar kanshi tace Allah ya maka albarka kai da sauran yan uwanka baki daya Amin yace cikin jin didi ya juya ya tf part ensu 


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

A harabar gidan ya samu Adam da Amira suna hira cikin nishadi SLM kawai ya musu ya wice ciki  a parlor ya tadda Yusuf zaune kan kujera ya miqe qafafunsa kan Center table ya daura laptop enshi kan qafafun yana daukar lacturer ta online Jallabiyace a jikinshi ya gyara gashin kanshi gonin Sha,awa Sai qamshi yake kamar fure cikin qaunar juna suka gaisa da Ahmad ya dan kalleshi yace biyaye ina ka tsaya haka sai yanxu tare muke da Abba ya fada yana cire kayan jikinshi yaci gaba  da cewa bari naje Na dan watsa ruwa ya tafi bedroom enshi kai tsaye toilet ya wuce 


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ 

A hankali tai SLM gami da dire tiren abincin kan dining ta juyo cikin sanda ta tsaya saitin kanshi duk a tunaninta Ahmad ne dan komai Nasu iri daya hatta gyaran gashinsu Sam bata gane shine a gunba a hankali ta sunkuyo kanshi tasa bakinta daidai kunneshi ta dan hura issaka ta dan tura yatsunta cikin lallausar gashin kanshi mai qamshin gaske cikin rada tace I love u ya Ahmad tana maici gaba da wasa da gashinshi cikin daqiqa daya ya gano itace ya San ba mai haukannan sai ita a take ji wani malulun baqin ci da takaici duk illahirin tsikar jikinshi sai da ta tashi gaba daya ya harxuqo cikin fushi da zafin nama ya juyo kamar walqiya ta ganshi gabanta  tunda ya juyo   fuskarsa ta saki qara tana baya jikinta bari yake sosai gaba data ta fiddo idanta woje Ahmad dake toilet da sauri ya dauro towel ya fito cikin xafin nama yana ai dama nasani za,Rina sai ya sata kuka  

Shikuma Yusuf hannushi har rawa yake cikin daga murya yace zonan bakince baki da nitsuba ba dama inada cikinki yau sai Na babbalaki gutsi gutsi ya fada yana gwada yadda xai ballatan ya daga hannushi zai yarfa mata marinshi mai bala,in zafi da Sauri Ahmad ya shiga tsakaninsu yace cikin salon kar ka daketa yace huce a kaina ninace ta kawimin abinci yasa hannushi ya dan balleta a jikinshi yace tf Aysha sai da safe ko  aiko a guje tai cikin gida Amira kam dama tunda taji qaranta tai cikin gida cikin 

Fushi sosai ya kalli Ahmad da Adam wlh kun isheni kun isheni abin yayi yawa ko kunya bakwaji qatti daku Ku liqewa yara qanana salon Ku jamin raini kallekafa biyaye da girmanka ka wani dauro towel a ququ girjinka duk yana woje yanzu da daurin ya kwance shikenanfa ka kade a gaban qanwar qanwar bayanka den tasoka ko ta rainaka Adam yayi dry sosai Yace toh me a ciki ba shikenan ba tasan German abinda zata aura ba 🍌 shi dai Ahmad shiru yayi sosai Yusuf kuma ke fada yayinda Adam ke qara tunzurashi A qufule yace Wlh Ku daina kiramin su nan in bakusan kunyaba Ni inajin kunya bira girma ya fadi Yaya Yaya ase yayun banzane 


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐


          Mambila

Yau  lahadi tun da sassafe suke shirin komawa cikin Tarawa dan sunyi hutunsu Na qarshen sati gaba dayansu daga kan Adam har zuwa kan Aysha suna zaune kan dining suna karyawa yayinda sukma manyan suna tsakiyar Palon sun da tattaunawa Aysha da Amira ke Serving ensu duk sun xubawa kowa suna tunani ya zasuyiwa Yusuf shi ba ,amai gwaninta Ahmad ne ya dan kalli Aysha cikin mgn da ido ya nuna mata shima ta hadamar tea cikin dan jin tsoronshi ta jawo cup ☕ta zuba mai tea duk hankalinta Na kanshi ta ina zaiyi matsifa Koma taji mari cikin tsoron har ta zuba mai gishiri a madadin sugar a cikin tea en 

Shi kuma tunda ta fara yake kallon farshen dan qaramin yatsar hannuta Na hagu ta barshi  wai ita gayu shi kuma kyamar farce yake a rayuwarsa 

Ya kalli sadiq dake gefenshi yace kai. Sadiq Kawomin scissors enka toh yace gami da miqewa ya lura Sarai gishiri tasa shiyasa ya jawo cup en ya dan kurba dai dai lkcin Sadiq ya mi qamai ✂ ya karba ya tura mata cup en yace gishir a madadin sugar kasheni kike shirin yi ko toh ke zaki shanye yasa hannushi ya kamo dan yatsar ya dan dannan  scissors en da niyar yanke farcen aiko ya hada da kan dan yatsar 


By garkuwan Fulani

[4/9, 1:48 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 MI,WASMITI.....page 4⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐


Gaba dayansu suna cike a porlon cikin shirin komawa 

Sunyi sit dan bppa Yaya zai musu Nasiha da Addu,a kamar yadda yake musu ko yaushe in sunzo komawa i dan da wani mai buqata ko uzuri ko umurni toh duk a wannan lokacen yake bawa yayanshi damarsu 

Shiru sukayi cikin maida hankali kanshi 

Sadiq ne yayi slm tare da shigowa da sauri Aysha ta juyo gunshi cikin harara tace Allah Sadiq ka kawomin kayana ko baka dinkaba ni gsky Na gaji Amira tace gsky kam kaya kusan shekara baka dinkasuba Usman dake gefenshi ya kaleshi a yatsine yace gsky dai Sadiq ka shiga tara tunda Sam baka da cika alqawari duk halayen teloli kai ka hada ga shegen son kudi Kaine dinkin yan mata kaine dinkin samari har Na tsofaffi baka bari....

Innayi ta amshe zance da cewa ai Sadiq kam sai a hankali wlh nima tun bayan sallahn bara Na bashi fatarina ya dinkamin aljihu a jikinsa Na samu gun ajiye yan canji da woyata Amman har yau bai baniba

Mixxixx Rabi,u ya ja tsaki sai da duk suka juyo gunshi yace kajifa kaji shirmanta ko ana mgnan kaya masu rai kekuma kina mana mgn bujenki Duk sukayi dry Adam yace tab innayi kawai ya batar miki da fatari .

Tab tace aiko sai ya biyani shidai Sadiq sai dry yake Abdul ya kalleshi yace ai ba dry kakeba biyan fatari zakayi 

Ya dan gyada kanshi ya ajiye wata qatuwar leda yace toh kudai ga naku dan wlh dama nasan su Aysha Anty masifa jiya ko bacci banyiba saida Na gama hada muku ya kalli su Usman yace Yaya Usman kuma ga naku.

Abba ya danyi gyaran murya yace toh Ku saurara ai mana Addu,a Bappa Yaya ya rinqa musu nasiha da sanya musu albarka daga qarshe ya musu Addu,a 

........ Duk suka fito suka shishshiga mota a hankali Yusuf ya yafito Sadiq da hannushi da sauri ya iso gunshi cikin kulawa yace kai Sadiq anya kuwa kana maida hankali kan kara tunka ? Cikin girmamawa yace sosaima Hamma Yusuf nama kusa try Universityn zariya yace ka dai kula dan naga gaba daya so kake ka zama mai dabi,ar mata shiyasa bansoka da dinkin nanba dan mafi akasari telolin mata da masu daukan photo dabi,ar mata suke dauka haka dai ya dan mai nasiha 

Suka tfy suna kewar juna 


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐


Yau kusan satinsu 3 kenan da zuwa mambila amma Yusuf bai kuma zuwa ba kuma duk weekend sai sun je yau jumma,a bayan sunyi sallan la.asar duk suna hallare a babban palonsu suna ta hira bb bello ya dan gyaran muraya yace toh Yusuf kunsan gobe Saturday ko dan haka duk Ku shiyarya da wuri dan tfyar sassafe nake son muyi..

Ya dan tura hularsa qeya kadan yace hmm baba nifa ina da taya goben Ummi ta dan kalleshi cikin jin haushi tace wai kai kam wanne iron mutum ne kai Sam bakason shiga yan uwanka kowa mararin zuwa yake Amman banda Kai su kullumu basu da mgn sai taku Amman a fili kake nunawa Baka damu da suba Duk baqin haline hakan da mugun mishkilanci wlh bakaji dadin rayuwarka ba..ta qarishe mgnar cikin fada

Nenne ta dan kalleshi tace ina zakaje ne Yusuf ?.

Ya dan yamutsa fuska yace Yola zamuje dan tunda nazo bamu jeba gashi har klcin komawata ya fara matsowa Goggo jiyama saida ta kirani tana ta fada bamu jeba 

Adam ya kalleshi da kyau yace wai kai ban ganeba fa kanata xakuje bakujeba kai dasuwa kenan zaku ? Ya dan harareshi ta wutsiyar ido yace toh da dasuwa nake zuwa ? Atoh nikam bazaniba ban saniba wataqil Ahmad zaije

Ya kalleshi a yatsine yace wlh sai kaje dole kaje mutum baison jiharsa ta aihuwa ko kadan 

Ahmad ya danyi murmushi yace toh Abba mu dai gobe Yola zamu Abba da su Nenne su kace toh Allah ya kaimu lfy 


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐


Haka kuwa akayi Adam badon yaso ba suka tfy Adamawa 

bayan sallah azahar kada suka isa A hankali Ahmad yayi parking a harabar gidan hydar da Maryam dake qoqarin fitowa da sauri suka qarasa gunsu cikin jin dadin ganinsu hydar ya karbi briefcase en Yusuf da miqamar hannu suka gaisa Maryam ko da sauri ta fada jikin Adam tana welcome ya Adam sai yau kuka zo ya dan subbaci goshinta yace ya zafin garinku tai dry dai dai lkcin da ta fada jikin Ahmad ta dan dago kanta ta kalli shi tace kajifa ya Ahmad wai garinmu wato shikam bandashi murmushi kawai ya iyayi yana dan tureta daga jikinshi dan wani mugun Abu yaji yana yawo a jinshi  abinda bai tabajiba dan ya runqumi su Amira ga kuma Yusuf dake ta watsa musu harara 

A hankali ta nufi jikin Yusuf tana Hamma Yusuf yaus.....

Da sauri ya katseta ta hanyar daga mata hannu da murtuqe fuskarsa tamkar sojan dake filin daga Atake  tasha jinin jikinta 

***********

Bayan sun gaggaisa gogga ta cika musu abinci a gabansu suna ci suna dan hira ba laifi yau yadan sake Amman dai baici Abinciba har baba Umar ya dawo ya jasu palonshi sukai ta hira yana musu da nasiha ya kallesu da kyau cikin qaunar yaran nasu yace Ahmad kunci abinci kuwa ? Alhamdulillah baba munci mukam Amman biyaye baiciba ya fada yana nuna shi OK yace ya kwallawa Maryam kira yace ta kawo mishi abinci ..

da kanshi ya zuba mishi ya bashi yana maza cinye banason dabi,arkannan ta zama da yunwa da gyar ya danci kadan  ya kalli Goggo yace Goggo nonofa mai dan sanyi tana dry ta dauko mar mai sanyin gsky toh nanne ya danci 

Haka sukai ta hira kashe gari suka dan zaga dangin babansu Adam 

Da a zahar suka kama hanya sai jaligo


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐


Aysha kam tunda tasan yana dan zaman palon ta daina fita da zaran tasan yana gun bata fita duk da bawai mgnarsa take jiba qamshin turarensa ke fadamata yana palon 

Dan gudun bala,inshi da duka 


Yau tunda safe suke ta dan girke girken dan yau babban soja xai diro daga Abuja ya Abubakar kenan sosai take farincikin zuwansa dan yana gwada mata kauna ta haqiqa

Qarfe 2 dai dai ya dira a babban palonsu tana tsaye gefen dining area tana ta shirya mai abinci Sam bata lura tare suka shigoba da qarfi tasa dan qara ta fada jikinshi yako tallabota yana dan juyawa da ita a tsakiyar palon sai dry take sosai tana miss U ya Abubakar juyi yake da ita sosai tana maqale a jikinshi Ahmad dake gefensu farinci yake sosai a ransa ganin ayshansa Na cikin happy aduniya duk abinda zai sata farinciki to shima zai sashi farin cikin


Muje zuwa masu karatu aiki Na gaba Na Gode da kulawarku da qaunarku gareni Nina kuna raina 😍😘


By garkuwan fulani

[4/9, 1:48 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇MI,WASMITI.....Page 6⃣ Na Aysha Ali Garkuwa🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Da garfi ta saki qara gami da fizge hannunta dan azabar da ya ratsata jini kuma a take ya rinqa tsirtowa abinka da farar fata gata da laushi kamar auduga kuka take sosai tana yarfa hannun  tana bubbuga qafafunta a qasa Ahmad kam tuni ya kamo ta ya riqo hannu yana matse kan dan yatsar da niyar tsaida jinin amman abin yaqi Adam ya jawo handkerchief en Yusuf dake kan cinyarsa da sauri ya yagi gefen handk en ya kamo hannu ya daure kan dan yatsar Amman ina jinin zuba yake Abubakar kam da Ahmad tamkar a jikinsu jinin ke zuba kuka take sosai jin kukan yasa Ummi da Nenne suka shigo a tare da sauri sukayi gunta tana lafe jikin Ahmad cikin mmki Nenne tace kai Ahmad meya yankata haka shiru yayi yana girgiza kai yana damqe da hannun ba abinda yake furtawa sai sorry Aysha cikin jin takaici da tausayinta  a hatsele Ummi ta buga musu tsawa kai ana muku mgn duk kunyi shiru ke Aysha waya miki muguntarnan dan ita tuni tasan mai aikata aikin dan duk suna zagaye da ita suna ta tausarta shiko oga ko a jikinshi ko inda suke bai kai idonsaba kamar baya gun kanshi a sunkuye yana ta danne danne a phone enshi ga cup en coffee a gabanshi yana dan Sha Ummi ta sake daka musu tsawa tace wai kuna jinmu kunyi shiru Rabi,u ya dan kalleshi yaga a sunkuye yake ya maida dubanshi gun su Ummi gamida gyaran murya ya dan dunqule hannushi  ya miqar da dan babban yatsarshi ya nuna Yusuf in gamida dan musu alama shine yana gedawa Ummi kai da dan furta haaa Nenne tace toh Koma waye yanzu dai kai Yusuf zoka San yadda zakayi ka tsaida jinin kanshi a qasa yace Nenne ni kuma ? Ummi ta jinjina kai tace a a ba kaiba wani mugun da ban da ya yanketa wlh ka kiyayeni ka fita harka yarinyar nan dan banga me ta tsare maka ba tunda kai zuciyar dutse Allah ya maka baka da qaunar  yar uwarka bare tausayi kullum sai mugunta fada sosai takeyi 

Shiru yayi zuciyarshi najin zafin yarinyar da tsananta a ranshi shi kullum a kanta sai ranshi ya baci cikin jin takaici ya shiga dakin innayi ya fito rike da kwalbar turare da qarfi ya fizqo hannu ya matse ya danna bakin kwalbar fesss ya fesa cikin yankan 

Da qarfi ta saki qara dan jin yadda azabar zafin ke ratsa jikinta har cikin zuciyarta sosai ta qanqame ya Abubakar tana wayyo Ummi ya qasheni ya Ahmad zafi nakeji gaba daya hannu sai bari yake Ahmad ya zagaya ya kamo hannun yana huramata iskar bakinshi mai sanyi yana dan shafa kanta Abubakar kuma yana dan buga bayanta a haka dai jinnin kam ya tsaya sai ajiyar zuciya take  

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐


Gaba daya porlon sunyi shiru suna sauraron Bappa Yaya A hankali yayi gyaran murya ya dan jinjina kanshi irin Na manyan mutane ya kalli yayan nashi daya bayan daya cikin muryar gsky da gsky ya kalli baba bello yace bello mgnarmu akan yarannan lokaci yayi da ya kamata ace duk mai shirin aure ai masa Sam banji dadin ganinsu a haka kun xuba musu ido suna abinda sukaga dama ya dan yi shiru sannan ya kalli Aliyu yace Aliyu inason mako mai zuwa Umar yazo da qanwarku Aysha dan insha Allah zamu San matakin da zamu dauka akan abin cikin girmamawa yace to Bappa insha Allah zan kirashi 

Juyawa yayi gunsu Ahmad cikin yanayin tabbaya yace kai Adamu kai ka fidda matar aureko ? Ehh ya bashi amsa yana mai nuna Amira yana ko dai baza ka ban ita bane a a Na isa nine mai badasu oho nasani ko zaka gwada ikonka..

 Dudabe ya kira Yusuf ya dago cikin jin haushi yace meye kuma ? Ehh akwai batun aure fatan ka shirya dan bazaka bar qasannanba saida matar aurenka uhum kawai yace dan yasan tsohonnan da iya kalen fitina shi kuma Bappa Yaya cewa yake wlh kunji kunya kune manya kan Abubakar Amman gashi dayin aurensa shekata 2 kenan da da saurin rabo da har an samu qaruwa 

Ahmad ya danyi murmushi yace toh ai shikenan muma zamuyi yanzu kam cikin kallon Ahmad din yace shiyasa Na yarda da kai Ahmad kai mutum ne sosai Na tabbata bazamu samu matsala da kaiba shisa matarka ta musammance Adam ya dan kalleshi yace mukuma ba mutane bane ko eh ai Ku kam gwara ma kai akan sarkin fadannan kam ya nuna Yusuf haka dai yaitawa zuriyarsa addu,a da fatan Allah ya maidasu lfy har bakin gate ya rekasu 

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐


Tun daga bakin qofa yakejiyo hayaniyarsu duk sun cika gidan da sowa a hankali yayi slm ya shiga pictures suke ta dauka dasu Ahmad da Adam Abubakar kam duk ya gama biye musu sosai suke ta dauka harda kaka da ta zo yanxu Usman shike daukarsu harda nunamusu yadda zasuyi cikin mmki yake klnon yadda yake tawani lonqwosa kamar mace Aysha fake tsaye tsakanin Ahmad da Abbakar duk sun dan sunkuyo Suna kallonta suna murmusawa itako ta dan dago kanta tayi kalan shogoba da sakalci Ahmad yasa hannushi ya dan tallabo fuskarta good Usman yace kunyi kyau ya daukesu

 ahankali ya karisa tsakiyar palon duk da baya ta bashi qamshi turarenshi ya sheda mata ya shigo dan haka ba tare da sun juyaba sukayi cikin wani parlon da sauri 

Kaka ta kalleshi cikin tsokana tace toh fa watsa taro duk ka watsasu ya dayamutsa fuska lokacin da yauzauna gefenta Ahmad da Adam suka sashi tsakiya Usman ya kallesu sunyi ras dasu gwanin Sha,awa ya dan kalli Yusuf a marairaice yace plss Hamma Yusuf bari Na daukeku daya wlh kunyi kyau harara ya watsa masa kaka tace Abubakar maza karbi ka daukesu ai shi photo tarihine wataran zaka tuna da dan uwanka Camera ya karba ya rinqa daukarsu duk motsin da sukayi sosai sukayi kyau kamarsu ta fito Sak da Sak suyi tamkar taurari kaka ta kallesu tace toh ko kufa ya dan yamutsa fuska yace kai nifa banson fitina da surutu ke Sam bakya iya shiru eh din nayi surutun bakinka ko nawa haka dai suka wini hira su Nenne Na musu dry Sam shi Yusuf da kaka in sun hadu sai fada  


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Yau asabar tun da safe suke ta shirin tafiya mambila su Goggo Aysha kam da su hydar da Maryam da maigidanta baba umar tun jiya jumma'a suka wuce mambila 


By garkuwan Fulani

[4/9, 1:48 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI.....page 7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Gaba dayansu kusan a porlon suka wuni sunata hirar zumunci sukuma su bappa Yaya da 'yayashi da surkinshi suna can parlonshi Na mu samman suna ta tattauna mgnarsu ta mu samman 

Tafe suke bayan sun fito masallaci yin sallan la.asar har sun danyi cikin gida Adam ya kallesu cikin raha yace biyaye muje cikin rafi mana mu dan Duba yanayin wajan Ahmad ya dan kalli Yusuf yce biyaye zamuje ? Kai ya dan gyada mai alamar bazashiba wlh sai kaje mutum kamar mai iska in kai kadaine ai kullum sai kaje amman dayake kaga su Rabi,u ma zasu sai ka wani ce bazaka ba cewar Adam kenan usman ya dan kallisu cikin salonsa Na dan rigima yace toh fili da fadi ai ba saimun zo gunkuba.. 

Haka dai suka jashi suka tfi 

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Rafine babba mai dubbin sirrai da qworamai ga duhuwa da qamshin furanni ga wani sanyi mai sanyaya zuciyar dan Adam ga yanayin shauqi da tsuma zuqatan masoya wurine mai dubbin tarihi tun na iyaye da kakanni suna kiran wurin da funa rafi 


Suna shiga duk suka watse cikin rafin kowa da abinda yake buqata Yusuf mutum ne mai son yananin sanyi da qamshi wurin Na tsuma zuciyarsa gaban wani qwarama mai ruwan garai garai qarqashin sirran bishiyiyin ayaba ga qatuwar bishiyar bangoro da wata bishiyar kashu da jijiyoyintama cikin tabkin suke ninqaya ga kukan tsuntsaye masu kama da sautin sarewa a hankali ya taka ya qarisa kan daya daga cikin kuyerun da aka jera a wurin masu dan tsawo Wanda sunfi kama Dana kwanciya 🌳 

A hankili ya kwanta tare da yin wata sassanyar ajiyar zuciya gamida lumshe idanshi duk Wanda ya ganshi yasan yana cikin nishadi 

Cikin yanayin tsokana Adam ya dan yafito Ahmad ya nunashi da ido yace shi dai har abada haka yake son kasan cewa ba kowa kusa dashi ya lumshe ido kome yake gani ranine.? sai Allah Ahmad ya bashi amsa yana dan murmusawa

 cikin shauqi ya fara zagaya wurin yana dan ciren yayan itatuwan cikin zuciyarshi Aysha ce ke yawo phone📱enshi ya zaro gami da kiranta bugu daya ta daga Cikin muryar tsantsar qaunar Ya Ahmad dinta take mgn jin muryarta da shauqi ya jingina jikin bishiyar 🌳 hadi da lumshe ido cikin sanyin murya yace Aysha kina ina ? .

Ta dan qara magalewa jikin innayi ta danyi ajiyar zuciya tace 

Ya Ahmad gani a kan gadon innayi 

Cikin sanyi ya fesa munfashi yace toh kizo lambu gani ina jiranki 

Toh tace gamida da cewa ya Ahmad ta wanne gefen kake ?

Bakin gwaramannan ya bata amsa 

Aiko cikin zumudi ta figi mayafinta ko Amira da Maryam bata nemaba ta fita da Sauri sauri  ta nufi rafin 

Ahmad ya nufi gun kenan yaci karo da hydar da sauri ya miqa mai phone enshi yana ya Ahmad Abba Na nemanka tun dazu yake kiranka layinka bai Shiga shine yace Na kawo ma 

Da sauri ya kara phone en a kunne 📱👂🏻cikin biyeyya ya ke mgn toh Abba ganinan zuwa ehh yanzu zanzo cikin sauri ya katse kiran ya miqawa hydar phone en ya nufi gun su Yusuf fuskarsa dauke da murmushi yace biyaye ni Abba Na kirana ZAmu tf bakin kogi gun dabbabi 🐄🐪 da sauri Adam ya miqe yana muje Nima xani har sundayi nisa Ahmad ya dawo ya dan kalli Yusuf yace biyaye kai bazaka jebane ?

Kai ya gyada mai alamar bazashi ba Adam yace kai da Allah zo mu tf ai kasanshi ba zuwa zaiyiba ya fada yana hararanshi shi ko sarkin hali ko idanshi bai budeba da sauri suka tf abinsu 

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Tunda ta shigo cikin rafin sanyin iskar da qamshin furannin suke ratsata ta lumshe idanta hadi da ware hannayenta tana tfy cikin rausaya tana shaqar qamshi kai tsaye gun da ya Ahmad dinta ya gayamata ta nufa tana dan ratsewa shuke shuken har ta qarisa wajen duk idanta a rufe cikin nitsuwa take dan tsallaka kujerun a nufinta zataje bakin ruwan ta zauna aiko a hankali qafarta ta dan zame zata antaya cikin ruwan da sauri ta ja qafar baya tana shirin juyowa taji ta afka kan kujerun

 Yusuf dake kwance a rigingine idanshi a rufe ba abinda yaji sai fadawar mutum a kan faffadan girjinshi cikin mmk da sauri ya ware idanshi gami da dan yunqurawa zai tashi 

Ita kam tun da ta fadi cikin razana ta yunqura sai tajita jikin mutum da sauri cikin fara.a tace ya Ahmad yau kam Dana karye ta dan saki murmushi gami da dan manna fuskarta kan  girjinshi ta zagaya hannuta ta bayanshi duk abinnan da take idanta a rude

Shiko cikin takaici da jin haushinta ya ware manyan idanunshi kan fuskarta cikin fushi da takaici ya danna mata tsawa keeee Baki da hankali ko jin muryar dodonta  cikin tsoro ta bude idanta dan tsawace mai rikita mutum ya sakarmata har sai  da cikin rafin ya dauki sautishin da sauri ta yunqura dan ta tashi bata gama firgicin tsawarba taji wani irin axabebben mari daya yarfa mata cikin jin zafi tasaki qara aiko ya miqe cikin zafin nama ya rinqa zuba mata Maruka tun tana tsaye har ta fadi qasa nanko yasa qafarsa ya rinqa bol da ita tana kuka tana wayyo Hamma Yusuf dan Allah kayi haqri wlh ban saniba ne plss Na tuba 

 su hydar dake can gefen bishiyoyin goiba da sauri suka nufi gun amman suna zuwa ganin Hamma Yusuf ne ke tabkarta yasa gaba daya suka tsaya hydar ya kallesu cikn jin takaicin Yusuf yace wai me ya tsaiya daku ? Rabi,u yace tab wazai qarisa wannan mugun yahada dashi shi dama in dai baiyi dukaba baya jin dadi cikin jin tausayin ta ya Shiga tsakaninsu ya sunkuya ya dagota ya dan juyo badan ya soba sai dan kar Yusuf yace ya rainashi yace dan Allah kayi haquri Hamma Yusuf 

Cikin fushi da murtuqe fuska yace maza Ku bacemin da ganan aiko da sauri ya jata suka tf 


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Abinka da farar fata tuni fuskarta ta kumbura tayi jawur ga wani azabebben zazzabi daya rufeta tun kafinnsu isa gida jikinta sai bari yake

 tab aiko Ummi kam ta hatsala fada take tamkar zata aro baki har zuwa bayan maggariba fada take sosai Nenne sai  bata haquri take amma ina fada take har su Abba da Ahmad suka shigo gida yayinda bba bello da Yusuf ke binsu a baya .


Yan uwana musulmai ina barar addu,arku ga dan uwana ya Abubakar Wanda Allah ya mai rasuwa  ya Allah ya jiqanshi da rahama 👏🏻😭😭😭


By garkuwan Fulani 090,,,,,,

[4/9, 1:48 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI.....page 9⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🙏🏻Bayan ya bude taron da addu,a ya dan yi gyaran murya ya jinjina kanshi jikin kushin ya dan kalli illahirin Family enshi din haqiqa shi da kanshi yanajin nauyin furicin da zaiyi zuciyarshi Na samun rauni idan ya kalli idanu jikokin nashi yana samun fargaba sosai yanajin tsoron kar yau ta kasance ranar nadama ko ranar baqin ciki ko ranar daukewar farin cikin wani sashi daga cikin sashikan zuriyar tasa jikin jinjina kai ya dan dago kanshi Ya dan zuba musu ido gaba daya a hankali ya danyi gyaran murya ya bude baki cikin sanyin lafazi da taushin baki yace 


Bello da kai da sauran qannan ka da matanku da qanwarku da maigidanta da dan uwana da iyayenku mata Yau gashi mu dukkanmu Allah ya kawomu wannan rana da muke fatan isar da wani alqawari da muka dauka idan Allah ya nufa yai shiru ya dan zuba musu ido

 sukuma yara daga kan Adam har xuwa kan Aysha ido suka zuba musu cikin yanayi tabbayar wanne alqawarine wannan Ahmad tun wayewar garin bugun zuciyarsa ta zarce tunaninshi sai yanxu yaji abin Na sauqa shiko Adam kallon kakan nasu yayi cikin dan zaquwa yace gsky mu bama son Jan rai kana mgn kana jinkirtawa da sauri baba Umar ya daga mai hannu alamar ba batun wasa ganin haka yasa gaba daya sukayi shiru sai yusuf shi dama baiyi mgn ba asalima kanshi a sunkuye yake Aysha da ke dan manne jikin innayi ta maida kanta tai lamo yayinda Amira ke gefen Adam maryam kuma Na jikin Nenne duk suka maida hankalinsu kan Bappa yayan a hankali yaci gaba da cewa Ahmad  

Bai Amsaba sai ido daya zuba mai bugun zuciyarsa Na tsananta 💗Ahmad ya kuma kiransa da gyar ya iya amsawa Na,am jin yadda sautin muryar Ahmad din ta fito yasa Yusuf da Aysha dagowa a tare suna klonshi sai yanxu su duka sukaji wani baqon yanayi ya darsu kan zuqatansu sautin muryar kakan Nasu ya katse musu Al,amarin yana mai cewa Ahmad A kullum duk zuriyarmu tana alfahari da kai haqiqa Na tabbata kai mutum ne mai cikir haiba da nazartan hilin da ake ciki Ahmad ina alfahari da kai a zuriya ta Na tabbata kai dayane mai fahimtar kalemen mutum duk kaushinsu da dacinsu 

Tun kana yaro baka taba kaucewa 

Umurnin iyayenka ba ko yaushe kai mai biyeyyane a garemu 

Baki daya shiru ya dan kumayi yayinda duk parlon sukayi sit Yanayin Ahmad kuma yafi kama da wanda tsoro ya cika zuciyarsa sukuma iyayensu gaba daya sada kansu qasa sukayi 

Cikin qarfin hali yaci gaba da cewa Ahmad a yau Alfarmanka nake nema kuma da yafiyarka dani da iyayenku baki daya Ahmad muna masu tausar zuciyarka muna kuma buqatar haquri daga gareka 

Cikin rashin fahimta yace bappa yaya ni kuma muryarsa har rawa take yaci gaba da cewa ya isa tunda tun forko kace iyayena toh mgna ta kare ba wani neman alfarma tsakaninmu a hankili ya daga kanshi ya kalli qanin mahaifinshi  yace Abba ni dai ni din Abba me kuke buqata a gareni da har kuke ban haquri ni Ahmad danku meye rage da baku minba a duniyarnan 🌍  ya maida dubanshi gun mahaifinshi da mahaifi yarshi yace baba da Nenne kun gama min komai Nenne am Na Dade ina Neman abin da kike buqata in miki a duniyar nan da kema zakiji bakiyi asarar yaranki da suka rasuba cikin 'yaya 12 da kika aifa sai mu 3 Allah ya bar miki Nenne ni Ahmad ki gayamin meye buqatarku yaku iyayena ya qarishe mgnar

 Yana mai zubda qwallah😭 ya dan kalli kakanshi yace bappa Yaya gayamin meye buqatarku ko zanji sauqin abinda ka dauramin haqiqa zuciyata ta soku 💘in dai bazaku sani Abu kai tsayeba sai kunce kuna Neman alfarma 

Ahankili Abba ya daura hannushi kan tsakiyar kanshi cikin wata iriyar murya yace Ahmad Allah yamaka albarka ubangiji ya jibanci Al,amuranka 

Cikin muryar kuka nenne tace Amin yusuf kam tuni zuciyarsa ta fara tafasa ganin hawayen biyayenshi Aysha ko kuka takeyi sosai innayi Na tausarta 

Gyaran murya yayi yace Ahmad alfarman da muke nema a gareka batun Aurenka da Aysha sai kuna ya sunkuyar da kanshi ganin yadda gaba dayansu jikokin nasa suka zuba mai ido

Haqiqa yusuf yasan wannan zaman kalen fitinane shiyasa ya dago kai fuska a murtuqe yace dan Allah kai mgn kana gasamin zuciya da maganganunka da suke Sa dan uwana zubda qwallah 


Ayijar zuciya ya danyi 

Yace Ahmad batun aurenka da Aysha babushi dan ita Aysha tana da mijin 😳😳😳

Cikin razana da fargaba da bugawar zuciya ya katse shi da meyasa ? Waye mijin tadin ? A ina yake ? Hannunshi Na dafe da qirjinshi yake wadannan tabbayoyin a take sukar zuciyarsa ta tsananta wani nauyi ya danni maqoshinsa 

Zufa ta fara ketomai tsoro mai tsanani ya rufeshi har cikin hanjinshi yake jin sanyi Na ratsashi 

Itako Aysha tunda taja wani numfashi sai ta zama mutum mutumi a zaune sai barin da jikinta keyi cikin mmk abin yusuf yace ai wannan mgnar hogice wayeshi da za,a hana dan uwana farin cikinshi akan wani can banxa tun tana qarama yake wahala da ita wlh ni dinnan a matsayina Na yayanta ni zan aurar da ita ga dan uwana Adam ya dan kalli Bappa Yaya a fakaice yace cikin yanayin kaji tsohonnan da zance shirme ai wanan ba huruminka bane sai ka bari iayenmu suyi ikonsu a kanmu       Allah sarki Ahmad duk sun rikice sabida bidar farin cikinsa dama Ku hausawa kunce nagari Na kowa 

Su Usman ma duk sunyi zurui Abdul mai saurin kuka shikam da Sadiq kuka suke sosai Rabi,u kuma sai kada kanshi yake a hankali yace (nayeku Na ko jibare ) tsufa ko rikicewa ne 

Baba bello ne ya dan rinqa musu fada cikin qarfin hali yana sabida me  zaku samu a gaba kuna kuka ko ance muku mutuwa akayi da gyar dai suka dan tsaqaita sai yanxu Bappa Yaya yaci gaba yace Ahmad tabbayoyinka harsunmin yawa duk da dai zan amsa ma ka su yanxu wasu kuma sai wataran zakuji amsar sai batun aurenka da Aysha babu shi domin kuwa ita tana da miji

 Amman duk da haka ba hanaka sure za,ayiba tunda an dakatar dakai  kan Aysha haka nan kuma an mayarma ka da yar uwarka Maryam a madadinta

Sai yaxu Usman yace toh wai waye ne wannan da za,abashi Aysha a hana ya Ahmad ita ?

Yusuf ne shine mijinta shine Abokin rayuwarta shine tsohon alqawarin zuriyar nan ya basu amsa

 

 daram  duumm ras ras zuqatansu suka rinqa amsawa cikin firgici da razana ta dago kanta a take zufa ta keto mata bakinta har rawa yake tana waye kace?

 dan uwanki yusuf nake nufi Adam ido ya zazzaro waje cikin dimuwa yace (hey ado andi ko a yeccata bo) kai Kasan abinda kace kuwa shiru yayi bai bashi amsaba 

😭💗😱 

Cikin dimuwa da fargaba Ahmad ya dan ja guiwarsa ya qarisa gun Abba hannushi ya daura kan guiwowinshi ya dago kanshi ya zuba mai ido cikin wani can ji da muryarsa tasamu yace Abba gskanta min furucin mahaifinku shin zancenci gsky ne ya kuma batun haramcin auren nasu Abba ko ya mantane Aysha da yusuf uwa daya uba dayane ?  Abba matuqar ka gskan tamin toh nayi alqari koda zan rasa raina nane 

Da sauri yusuf ya qarisa gunda yake yasa tafin hannushi ya rufe bakinshi 


Toh masu karatu Ku biyoni muji wannan wanne irin rikitaccen Al,amarine wannan sarqakiya ya zata kaya 


By garkuwan Fulani 85

[4/9, 2:23 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI.....page 8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Da sauri Ahmad ya qarisa kan kujerar da take zaune  zama yayi daf da ita yana klon fuskarta cikin yanayin damuwa da tabbaya hannushi daya yasa yana shafa fuskarta da tayi jawur yayinda ta dan manne jikinta da nashi tasa hannuta daya ta sankalo hannushi ta daura dayan kuma kan hanun nashi ta dan ranqwafar da kanta kan damtsenshi 

Cikin zaquwa yace Ummi meya sameta ? Cikin fushi da jin haushi Ummi ta nuna Yusuf dake zaune can gefe kan dining table ai kasani Ahmad ba mai salon muguntar nan sai shi din shugaban mugaye ko yaushe mutum bai da aiki sai cin zali nan taci gaba da fadan kamar forko qara matsowa kusa dashi tayi cikin fada tace wlh ina gaya maka ka fita harkar yaranan idan duka kake son yi toh dole sai ka haqura sai randa ka haifi naka 'yayan amma bamu zaka yi ta dakawa yaraba daga yau sai yau ko mugun klo ka kuma yiwa yarannan ranka zai baci 

Sosai Ummi take mai fada gaba daya shi kam ya gama cika yadda take mai tsababi a gaban qannenshi kanshi ya. Sunkuyar duk da hali irin Na Yusuf baison bacin ran iyayenshi baison yaga ransu Na baci a kanshi cikin yanayinshi dayafi kama da baya son mgnan ya kalli Ummi a hankali ya bude bakinshi yace dan Allah kiyi haquri Ummi daga nan bai kuma mgn ba 

Ahmad kuma dake klonsu duk ya fahinci abinda ya fada da kuma abinda ke zuciyar sa💛ya tabbata tsanar Aysha fadannan ya qara mai shiyasa bai fiye son ana mai fada a kan lmrin taba  

Hankilin shi ya mayar kan Abba da yayi shiru ya zuba mai ido cikin ta kaici ya bude baki kamar maiyin fada sai kuma yace Yusuf am Allah ya shir yeka ya tausasa maka zcyar ka 💛 yasa maka qaunar yan uwanka  Allah sarki Abba shi bai iya fada da mugun baki ba a rayuwarsa shiyasa komai lamarinsa yafi tfya da Ahmad 

Borkono 🌶sai Baba bello gaba daya halin Yusuf halin wan mahaifinshi ya dauka bba bello shiyasa duk bala insu da masifarsu su suna shiri da juna lkta da dama ganin Abba da Ahmad suke a matsayin su kamar basu damu da raini ko wani abu ma kamanci shiba Shiyasa kuma ba komai Yusuf keyiba bba bello zai fadaba sai dai ya zuba musu ido yana dan fara,a

Bayan sun kam mala cin abinci kamar yadda suka saba in sunzo mambila duk haduwa suke a parlon aita hira 

Yanzuma duk suna ta hira sai Yusuf da Adam da suka fita yayinda Ahmad kuma yau jinya yake tuquru duk ya susuce a kan abar qaunarsa itako sai zuba shogoba da sakalci take tun dazu yake ta faman lallaba mata koda tea ne ta dan Sha taqi ya dan kalleta cikin jin tausayin ta yace plss Aysha tashi ki dan Sha ko kadanne a hankali ta qara male hannushi tai rau rau da ido cikin sanyi mirya tace ya Ahmad ni ya isheni bana jin yunwa hannushi daya ta kamo ta daura kan wuyanta tace kaji jikina fa zazzabi nakeji 

Jikin kam yayi zafi sosai shiyasa da sauri ya miqe ya dan debo ruwa a dan roba da dan qaramin towel a hannishi ya dawo gun ya zauna ya dan kamo hannuta ya zaunar 

Daidai lkcin su Adam suka shigo Adam ya kallesu da kyau yace sannu da qoqari  biyaye 

Usman dake gefensu tun dazu yake binsu da ido ya dan ja tsaki ya juya kanshi yana wlh ya Ahmad yarinyar nan tama rainaka kai kuma sai wani biye mata kake Rabi.u ya dan harareta yace ai ni nafijin haushin me biye matan ai wlh ba mgnin ta sai Hamma Yusuf

Bki ta dan tura gami da dan hararsu tace ehdin 

Da sauri  ya dan juyo gunta gami da watsa mata harara cikin murtuqe fuska yace (hey Ummuh hado moi on qworgima hado de a tonta ta amin ) ke tashi daga nan waye Sa,anki anan da kike bamu amsa 

Cikin dan jin haushi da tsanarsa ta miqe tana klon Ahmad hannuta ya kamo ya ranqwafar da ita yace biyaye (anon on wari tawi amin hado mai ko ?) Ku kukaxo kuka samemi a nan din ko ?_toh dan haka kuyi gaba ..

Dry Adam yayi yaja hannun Yusuf yace (en dillu)  mu tafi suka tafi suma su Usman tfya part ensu sukayi 

Shiko sai da ya samu ta danyi bacci ya zame hannushi ya dan gyara mata gashin kanta ya dan shafa kan kuncinta da yasha maruka yayi jawur ya dan kalli Ummi da Nenne da suke dan hirarsu qasa qasa yace Ummi tayi bacci ya dan qarisa gun Nenne yace Nenne am (sai fajira ) good Night Nenne Na ya juya ya tf Murmushi tayi tana jin dadin yadda dan nata gudan jininta yake gwada mata qauna sosai 

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Yau Sunday kuma yaune zasu Koma cikin taraba su baba Umar kuma gobe zasu nufi Yola tun wayewar garin ranan Bappa Yaya da yaranshi da matanshi da qaninshi gaba dayansu suke babban parlonshi suna ta tattaunawa

Su Nenne kuma Suna ta shirinsu yayinda su hydar da Usman suka tfi cikin rafi Adam kuma da Amira gidan kawun amiran suka tf sai Ahmad dake kula da Aysha Suna parlon su Ummi nata xirga zirgansu a hankili ta kirashi 

Ya Ahmad cikin kulawa yace Na,am Aysha meke faruwa ?

Ta da sunkuyar da kanta tace ya Ahmad wai pisa bilillahi me nayiwa Hamma Yusuf ne ya tsaneni haka ?har baya iya boye qiyeyyata kowa Na sona Amman bandashi meyasa ne 

Murmushi ya danyi mai dan sauti yace Aysha ina kika tabajin dan uwa ya tsani yar uwansa  biyaye yana sonki shi dai kawai haka halinshi yake yana da mishkilanci kuma baison raini 

Da sauri ta kallishi gamida sake hannishi ya Ahmad kenan ni Na rainashi ne ? Dry ya danyi ta kuma dan kauda kanta ta dan tura baki tace wlh ai dama Na ganeka ya Ahmad wlh kafi son Hamma Yusuf a kaina kai akan kowama ko yayi laifi baka gani kuma ka sani sarai ( o kallu do ) shi mugune bai da tausayi 

Shirun da taji yayine yasa ta dago ta kalleshi ita ya zubawa ido cikin wani yanayi duk yanayinshi ya sauya a hankali yake dan girgiza kanshi ya maida bayanshi ya jingina jikin kjra ya dan lumshe idanunshi da sukayi jaa cikin sanyin  murya yace 

Yusuf da Ahmad da Adam wasu abune guda 3 da Allah ya halitta wadanda suka kasance tamkar hanta da jini a jikin juna farin cikin daya cikin mu 3 dinnan ya wada cemu yayinda bakin cikin daya zai mana illah a zuqatan mu 💘 baki daya rayuwarmu zata kasance ne tamkar taurarin nan guda 3 da suke nuna alamun lkci Aysha ina son yan uwana bana taba jurar baqar mgn a kansu haqiqa ina son yusuf amma duk da hakan shi yafi sona yusuf da Adam jinina ne ya dan tsaya ya bude idanshi ya zuba matasu itama din gaba daya shi ta warema NATA idan da sukafi kama Dana maijin bacci a zahiri ta ga gskyar abin da yake fada a kwayar idanshi a hankili ta nuna kanta tace ya Ahmad harni bankai Hamma Yusuf a zuciyar kaba ? kai ya girgiza yaci gaba da cewa shi Yusuf da Adam jininane su ke kuma bugugun zuciya tace 💗💘 tabbas in babuke toh ba Ahmad cikn wani irin sauti yace Aeeeshahhh ni da kaina bansan wane irin so nake miki ba Aysha sonki a zuciyata babban sukane 💘 Na tabba ta in ance babu ke  a a cikinta to bani a duniya 🌍 jawota yayi ya manna kanta kan girjinshi yace kinji bugun zcyta toh duk numfashin da zan shaqa a duniya da qaunarki nake shqarsa a hankali tayi sassanyar ajiyar zucya tace ya Ahmad har abada ZAMU kasance tare 

A haka sukayi ta jaddawa juna son da qaunat da sukewa junansu har su yusuf da Adam dasu hydar suka dawo 


⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐


Banyan sunyi sallan LA,asar duk suka hallara a parlon da shirinsu Na tfy kamar yadda suka saba komai Na zuriyarsu a daidai wanan lkcin suke tsara komai da duk wani hukunci ko umurni da zasu bayar a zuriyar tasu toh hakama yanxu duk sun nitsu  dan jin ta bakin Bappa yayan 

Nima kaina Aysha Ali Garkuwa Na nitsu sosai dan Na tabbata yanxune ZAmU ciga cikin lbr


By garkuwan Fulani 97 📱

[4/9, 2:23 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI....page 🔟 Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Hannushi Na kan bakinshi ya dago kanshi ya rinqa girgiza mai kai da zuba mai manyan idanunshi da suka qanqance sukayi jawur 

Shi kuma sai dafe hannushi yayi a qahon qrjinshi a hankali ya ciro hannushi daya ya zame hannun yusuf daga rufe mai baki da yayi ido yusuf din ya zuba mai cikin jin ta kaici yace haba biyaye meye amfanin furucinnan ina tunanin ka ya tfi me amfanin yarintarka shin kai yarda kayi da ( talol ) tasuniyar Bappa Yaya ya za ayi kwanyarka Na aiki kake bin shirmen qoqolwar tsohon da ya gama birkicewa kai ka gaskanta zancenshi ya dan dakata ya dan kalli iyayenshi cikin yanayin bada shawara da dan rusuna kai yace bba bello tun tini nake CE muku ku rinqa kula da yanayin zantu kan mahaifinku amma sai kuke ganin Sherri nake mishi to ai yau kunji kun kuma gani kuma ya muku ta yadda dole ku yarda tabbas ni nasan tsufa ta birkita tunaninshi zancen gsky ku kaishi likitan sakatiri ya dubashi............

Baba Hamisu ya daga mai hannu da sauri yayinda yake mai donqolo yace kai yusuf ya isa haka mahaifin namu a gabanmu kake cewa ya zauce 

Kai ya daga ya kalli baba bello ya kirashi cikin Neman qarin bayani yace wai baba ku kun yarda lfyarsa lau kun kuwa ji abinda yace ko a lbrin films da novels kun taba jin inda yan uwa uwa daya uba daya sukayi aure kun tabaji ? 

Ya qarishe mgn cikin tabbaya yaci gaba da cewa toh haqiqa wannan al.amari yana Neman wani duhu da zai kawo cikin wannan zuriya tamu 

Abba ne ya dakatar dashi da cewa ba kai muke sauraro ba kuma ba hukuncinka muke jiraba dole tsarin mahaifinmu xamu bi 

Cikin sauri Usman yace Abba koda ya sabawa sheriyarmu  ta  musulunci ?

Baba bello ne ya katseshi ba tare da ya bari Abba ya bashi amsaba

Shikam Ahmad tamkar robot ya zama 


Cikin yanayin jimami Abba ya dafa kafadar Ahmad ya dan sun kuyo ya kalleshi cikin sanyin jiki da murya yace eh Ahmad Aysha tana da miji kuma yusuf shine mijinta kai kuma a madadin family enmu gaba daya ina mai baka hqri ha kazalika ni Na zabarma matar aurenka Ahmad Na zabama Maryam yar uwarka mu kuma yar qanwarmu 

Ido kawai ya zuba musu sai duk mai mgn ya bishi da ido ya rasa me qoqolwarsa ke tunawa ya manta meye farin cikin rayuwa ga wani azabebben nauyi da ya tokari qahon qirjinshi da maqoshisa tunani  yake ko mafarkine 

abba ne ya kuma katseshi da kiranshi cikin yanayin Neman alfarma 

Ahmad ya zuba mai ido ba tare daya amsaba yaci gaba da  cewa Ahmad ka amince zaka Auri yar uwarka Maryam ka amince ka haqura da Aysha ido ya qurawa Bappa Yaya a zahirin ranshi baya qaunar Maryam kuma furucin yake da niyar furtawa kai Bappa Yaya ya gyada mai cikin yanayin kayi mgn 

A hankali baba Umar ya kalli Ahmad cikin taushin lafazi yace Ahmad ba dole in baka son Maryam ka fada insha Allahu bazan bari a hadama zafi biyuba rashin abin sonka da kuma samuwar Abinda baka so idonshi ya sake maidawa kan goggo Aysha nauyin furicin ya sauqa kan harshenshi taya zai kalli qanwar mahaifinshi da baba Umar sannan qanwar biyayenshi Adam yace bai qaunarta bazan iyaba ya bawa kanshi amsa 

Yusuf kuma da Aysha dama illahirin mutanen porlon shi suka zubawa kunne da ido👂🏻👀 dan jin mai zaice yusuf hatta jijiyoyin hannushi motsi suke dan tsabar bala,I gashi ba daman yin matsifar jin tsanar kakan nasu yake sosai duk da shi a badirinshi baima ji mgnarba bare ya yarda da ita. 

Ka Abba qanin bappa yaye kenan shi ya katse shirun da cewa gsky ne Ahmad kana da damar da zaka auri duk wacce kakeso tunda baka sami zabinka Na forko ba cikin

Yanayin jin haushi yusuf ya kalleshi yace wlh ni ban son jin zancenka da Na dan uwanka zanceku zai sai zuciya mai rauni da ciwo irin tawa  zuciyar 💗 ta buga 

Shi kam baba Amadu mahaifin Amira sai yanxu ya danyi mgn cikin sanyi yace ba komai yusuf komai Alkhairi ne.

Alkhairi kuma ? ya tabba yeshi 

ehh alkhairine yusuf mitarka ta fara isata kar ka hatsalomin da fushi Na baba bello ke bashi amsa  kanshi ya sunkuyar cikin qunar rai 

Cikin taushin lafazi Hydar da Abdul har suna hada baki suke cewa Baba bello wai ina mgnar nan ta dosane aure tsakanin Hamma Yusuf da Aysha cikin tausasa lfzi Rabi,u yace karfa garin yiwa iyaye biyeyya mu aikata haramci a zuriyar mu 

Kai Nenne take girgizawa cikin qunar rai da gyar tace ya isa kun ishemu da tabba yoyinku marasa amsa 

 A hankali bappa Yaya ya danyi gyaran murya ya dago kanshi yabi dukkanin illahirin zuriyar tasa da ido yusuf yake kallo sosai yayinda ya fahimci zuciyar Sa Na dab da fara tuna mai shin to a cikinsu waye binqelawo kai ya jinjina ya maida dubanshi kan Adam daketa murtuqe fuska tamkar sojan da aka bugawa tabbarin yaki idosa cikin idinsa ya sauqa da sauri cikin birki tecciyar murya da mgn kuma ta gsky da gsky da kaga yadda yake mgn kasan har cikin ransa hakane yace  kai Bappa yaya .....


By garkuwan Fulani 32

[4/9, 2:24 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI....page 1⃣1⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Kai Bappa Yaya wlh ka daina klna cire idon 👀 ka a kaina Sam ni bana wani qaunar ka kalleni 

Duk suka  juyo suna klnonsa cikin mmk shi kuma da iya gsky Sa yake mgnar ya kalli baba bello yana Abba gsky ni ku gayawa tsohonnan ya daina zuramin ido danni wlh banaso ya maida hankalinshi kaina 

Tunda Na riga Na gane cewa kwanyarsa ta toshe tunaninshi ya koma hada auren mu harraman juna 

Ya juyo ya kslleshi cikin harara yace ( mi do yecce fa accu larugo am mi yida hala bema ) ina gayama fa ka daina klna dan bana son mgn da kai 

Dan ba mmki yanzu kace ni ma din ka fasa ni zan auri Maryam tunda abin naka ya Koma wa da qanwa tsufarka ta baka shawaran hadawa ya 

Ya kuma murtuqe fuska ya girgiza kai ya cije lips enshi yace tam ni dai wlh mutum bashi ya haifeniba kuma bai isa ya sarrafamin tunanina ba eh kayi ikonka iya kan yayan ka 

Yusuf dake qufule yace a barshi ai shi ji yake duk shi ya aifemu 

Baba Umar ne ya  kalli dan nashi cikin hada fuska yace kai Adam ya isheka haka kafa kiyayeni 

Kai ya sunkuyar ba tare da yakuma mgn ba 

A hankali Abba ya kalli Ahmad yace 

Ahmad ka yarda da auren Maryam ?

Cikin nitsuwa ya qarewa iyayen nashi kallo ya tabbatar da gsky mgnarsu a qowayar idansu 👀 cikin sanyin murya 

Yace 

Abba Na Amince zan auri Maryam ina sonta tunda ku iyayena ita kuka zabamin Na yarda 

Na kuma 

Haqura da Auren Ayshaaa 

Zanci gaba da klonta  a matsayinta Na qanwata ta jini cikin dimaucecciyar murya yaci gaba da cewa 

Duk da tarin tabbayoyin da suke tare a zuciyata wadanda banda amsarsu bani da kuma mai ban amsarsu sai ku 

Kukuma  kun wuce matsayin da zaku sani Abu intsaya bincike akan isarku a kaina Abba ngd da zabinku a hankali ya rufe bakinshi yayinda yayi qasa da kanshi 

Abba ya dafa kanshi ya rinqa jero mai Addu,oi Ahmad Allah yama albarka yasa ka gama da duniya lfy kaima Allah ya baka Yaya masu yimaka biyeyya fiye da yadda kake mana Allah ya jibanci Al,amuranka 👏🏻

Gaba daya suka amsa da Amin ya rabbi

Aysha dake zaune tayi mutuwar zaune sai yanxu ta samu kuka ya kwofce mata 😭 cikin kuka take mgn 

Ya Ahmad me kake nufi kace ka Amince kana nufin kafi son a rabamu anya kuma kalaman Na baya gsky ne 

Da rarrafe ta qarisa gaban Ummi ta riqo hannuta ta fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro 

Jin kukanta yasa nauyin dake zuciyar 💗 Ahmad karuwa da hannu bibbiyu ya dafe girjin dan azabar da yake jin 

Yusuf ko gaba daya qoqolwarsa ta hargitse ta birkice yama rasa me yake tunawa ga sautin kukan ta da yakeji kamar sauqar aradu duk ya gama cika yayi tab fashewa kawai ya rage yayi kuma ba hali gasu Abba 

Juyawa yayi ya kalli Ahmad a daidai lkcin da ya yunqura ya miqe a lkcin kuma woyoyinshi dake kan cinyarsa suku zube a tsakiyar parlon 

Duk suka tarwatse a gun sabida haduwarsu da tayis  qafarshi yasa ya cure. Laptop enshi dake gabanshi 

Ya nuna Ahmad a lkcin da fitar numfashinshi ya fara korar juna cikin wata iriyar murya yace ( a hafdi biyaye am ) ka keuta dan uwana 

Kana ganin wai jarumta kayi kenan to mu ka naqasawa rayuwa ya juya a fusace zai fita 

Cikin fada Abba yace kai yusuf dawo nan 

Da sauri Bappa Yaya yace barshi gwara ya fita dan tuni numfashinshi ya fara birkicewa ka sanshi da zuciya tunda ba samun yadda yake son zaiyiba in ya zaunama sai zuciyar tasa ta buga jarabebben yaro Kawai 

Haka sukayi Addu,a 

Suka watse 

Taronsu 

Shi kam yana fita ya figi motarsa ya nufi taraba ikon Allah ne kadai ya kaishi 

Sukuma suka dawo a tare 

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

               HALIN RAYUWA  

Yanayin zaman kamanni family ya canja rayuwa ta juya musu farin ciki ya musu qaura duk wani hayaniya da zaman parlo aita hira ya canza 

Yau kusan kwanansu 4 da dawowarsu Amman har yau dinnan Aysha bata kuma ganin ya Ahmad ba hakama yusuf duk da dai shi kam dama bai fiye shigowaba Adam ma tunda suka dawo bai shiga ba


Zaune take kan kujera ta duqunqune ta tura kanta cikin cinyarta tana sana ar tata a hankali Amira ta dafa kafadarta ta zauna gefenta 

Cikin sanyin murya tace Ayyah Aysha ki tausayawa kanki ki tausayawa umminki mana baki ga duk damuwarki ta kama zuciyarta ba ta danyi shiru ganin Ummin a gefensu cikin damuwa hannuta dauke da cup en nono ta zauna gefenta cikin rarrashi tace Aysha karbi ko da nononne ki Sha kinji ko 

Kanta ta dago ta zuba musu jajayen idanunta cikin takaicin rayuwa tace Ummi ni banjin yunwa Na qoshi 

Haba Aysha yaufa kwana 5. Bakici abinciba so kike kijawa kanki cuta ne 

Kanta ta manna jikin Ummi ta fashe da kuka cikin kukan tace Ummi wai da gskne mgnar aurena da Hamma yusuf Ummi kuma da gaske bani ba ya Ahmad 

Ta dan zuba mata ido tace Ummi Amman bakya sona ko girgiza mata kai tayi cikin sanyi tace Aysha ina kika taba ganin uwa taqi yarta nima wannan abin ba a son raina za ayishiba Amman bari in gaya miki gskyan Al,amarin ...............👂🏻👀 duk ta zuba mata ido dakunne danjin meye gskyar abin


By garkuwan Fulani 76

[4/9, 2:24 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI...page 1⃣2⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Cikin lallashi taci gaba da cewa Aysha nima kaina wannan abin yafi qarfi nane shiyasa banda iko ko damar hanawa shiyasa wlh da ina da iko da Na hana ko dan farin cikin Ahmad inajin quna a raina sabida halin da Ahmad ya kasance a ciki ina jin tausayin mahaifiyarshi da Abbanku dan duk duniya sune Na forkon shiga matsala in damuwa ta dameshi 

Ta daura hannuta a kanta tana shafa gashin ta cikin taushin lfzi tace Aysha kiyi hqri da gddarar ubangiji ki daure kiyiwa iyayenki biyeyya kibi umurninsu 

Kuka sosai ta saki cikin jin zafi tace Ummi shikenan ni kam bani da wani sauran farin ciki ko ?

Kina dashi Aysha am me zai hanaki ai rayuwa juyawa take wata ran sai lbr rayuwa zata kawo miki farin ciki zuciyarki ta Koma tamkar bata taba riskar takaiciba 

Haka dai taita bata baki Amman duk da hakan taqi cin abinci sai kuka da ta sake suna zaune a haka har bacci yaci qarfinta tai baccin 

Gudun kar a tadda ita taci gaba daga Inda ta tsaya dole Amira ta dawo parlon suka kwana tare

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

              Yau 

10 days kekan da jin wannan sabon salon rayuwar da suke ciki damuwa da kuka su suka zama abincin Aysha yayinda Ahmad da yusuf sukayi wuyar ganuwa 

Adam dai yakan dan chigo kadan kadan 

 

Misalin qarfe 9 Na dare Abba da ummi ke zaune a parlon Abban suna dan tattauna wa cikin damuwa Abba 

Ya dan kalli Ummi yana mai  cewa Ahmad fa kwana 3 kenan ni ban ganshiba kuma yawanci a kwanakin zai kirani da safe muna gaisawa zai katse kiran kuma ko Na sake kiranshi sam layukan nashi basa shiga abinfa Na damuna sosai ya qarisa mgnar cikin damuwa 

Ummi ta danyi ajiyar zuciya cikin sanyi tace wlh ni kam ma yau kwana goma kenan

Ban ganshi da idona ba sai dai kullum zai kirani mu gaisa kam 

Haka kuma shima yusuf bai shiga kuma dukkansu ko abinci yadda aka kai musu haka za,a dauko 

Kanshi ya jinjina gami da zaro wayarsa number Usman ya kira yana dagawa ko gaisuwarsa bai amsaba yace (hey Usman ya 'youni nam ya Ahmad Mon) kai Usman je ka kiramin ya Ahmad enku

Toh ya amsa da sauri gamida katse kiran 

Ya kalli Nenne da suke parlonta suna ta dan hira yace Nenne ya Ahmad fa ?

Abba ke nemansa kai ta dan kada tace wata qil yana dakinshi 

A dakin ya sameshi kan sallahya yana kwance yayi rigigine hannushi ruggume da Al,QURA,ANI mai girma Amman kuma idonsa a lumshe yana ta rera karatun cikin narkekkiyar sauti baki 2 yana mai mgn bai jiba saida ya qarisa gun ya zare AL,QURA,ANIN 

Da sauri ya bude idonsa 

Shima din shi ya zubawa ido cikin yanayin tuhuma dan ganin yadda ya koma tam kar ma jinyaci yace ya Ahmad (dume hebima) meya sameka 

Kai ya dan gyada mai cikin qarfin hali ya dan murmusa yace kai ba komai lfy ta lau ya fada a lkcin da ya miqe tsaye 

Ba dan ya yardaba yace toh masha Allah tunda lfy kaje Abba Na kiranka 

Da sauri ya kallishi yace yana ina 

Yana parlonshi ya bashi amsa lkcin da ya juya ya fita 

       ⭐⭐⭐⭐

A hankali cikin nitsuwa yayi slm Abba ya amsa mai  

Shigo ya cemai 

Ya shigo cikin girmamawa ya zauna inda Abba ya nuna mai kusa dashi a kan carpet yayinda Abban kuma ke kan kujera 

Cikin mmk suka zuba mai ido 

Ummi ce ta fara mgn cikin kaduwa tace Ahmad baka da lfy ne ?

a,a.  

Ya bata amsa a taqaice 

Cikin damu tace doctor kallifa yadda yaronnan ya zama cikin dimuwar Abba ya xuba mai ido ya dafa kanshi 

Yace Ahmad meyasa baka cin abinci gafa yadda yunwa da damuwa da tunani suka galabaitar da kai 

Ya dago kanshi ya kalli shi cikin qarfin hali da murmushi a fuskarsa yace Abba inafa cin abinci 

Kanshi ya dan kawar ya kalli Ummi yace Fatima kawo min abincina 

Toh tace ta juya da sauri ta nupi kan dining dan dauko abincin 

Kanshi a gefe ya kirashi cikin taushi yace Ahmad tsoronmu kakeji ko? shiyasa kke buya kar mu sake zaluntarka 

Da sauri ya daura kanshi kan cinyar Abban ya dafeshi da hannu Bibibbiyu yace cikin rawar murya 

A,a. Abbana baku zalunceni ba bare naji tsoron kar Ku kuma 

Mun zalunce ka mana Ahmad am banda yadda zanyine shiyasa Ahmad qaddara ta rigayi fata ka gafarcemu hqqa mun zama masu tauye haqqi a  gareka dana 

Ummi ya kalla a lkcinda ta dire tiren abincin a gabansu gamida dan sunkuyar da kanshi yace ummi ki tunawa Abbana matsayinsu a guna mana in yana fadar haka zafi nakeji sai inga kamar ganisuke basu isa daniba 

Ummi kam sai hawaye cikin muyar kuka tace ga abincin ta dan zuba mishi ta miqa mai Abbane ya karbi pilet en ya zame qasa kusa dashi 

Tuqeqqen tuwon shinkafane da miyar taushe sai qamshin man shanu yake 

Sa hannu kaci kaji ko Ahmad ba musu ya danci abincin badon yanajin dadinshi ba

Sai dan ya faran tawa Qanin mahaifinshi 

Bayan ya dan mishi nasiha da qarfafa mai guiwa da sanya mai albarka 

Sukayi sai da safe har bakin part ensu Abban ya rakashi 


A bin mmk a palonsu ya samu ..........


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:24 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI...page 1⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Yusuf Ne zaune yana riqe da cup din black tea yana dan Sha gefenshi yaje ya zauna cikin yanayin happy ya dan murmusa ya kalleshi yana kai biyaye yaufa kusan kwana 5 ban gankaba 

Klonshi yayi cikin harara ya miqa mai cup en yana gashi karbi kasha karba yayi ba musu yana Sha ya dan tsaya zaiyi mgn da sauri ya dan daga mai hannu yace gama shan tukun sai kayi farfa gandan naka kar kayi ka qware 

Ajiye cup din yayi ya kalleshi da kyau yace biyaye farfaganda kuma ni din 

Yes ya bashi amsa kai din dai ba waniba ya dan girgiza kanshi da dan gyada kan cikin yanayin muryar da tafi kama da zaka qwaremu yace 

Biyaye bazan iya fushi da kaiba bazan iya rayuwa cikin happy bayan kai taka rayuwar ta cabe ba

Hannushi ya dan daura kan qirjinshi yace kana son soya zuqa tanmu da biyeyyarka mara amfani a wannan karon cikin jin takaici yace nifa banda matsala dan banma ji zancen tsohonan ba bare Na wani yarda da tsarinsa Na gaibu ni kwannan zan barmusu qasar 

Amman damuwata nasan zasu yimaka daurin kazar kuku 

Dry ya danyi yace tab guduwa zakayi kenan ? ehh ya bashi amsa tunda ban da mafita iyayena sun Sa baki kan zancen zauceccen tsohonga ai dole Na bar qasan

Zan fadawa Abba murmushin takaici yayi yace Na tabbata bazaka iyaba shiyasa Na fadama 

Haka suka danyi ta tattaunawa har zuwa qarfe 11 sukayi shirin kwanciya 

Dama shi yusuf tunda suka dawa da yake bai son kayan takaici injishi da fada sai yakan wuni gidan kaka Zubaida sarkin surutu sui fada su shirya 

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Yau kusan 2 weeks kenan da dawowarsu mambila amman har yau Aysha batasa ya Ahmad dinta a qwoyar idantaba 

Duk da fama da take da azabebben ciwon girji Sam bata iya cin abici sosai qirjinta ke  suqa kuma dai dai  kan dukiyar fulaninta har taji tamkar zasu tsage 


Kwance take a dakin Nenne dan ta dawo nan dan fakon ya Ahmad din 

Can cikin bacci taji sautin muryarsa cikin sanyi yana dan mgn da Nenne shi bakin qofa tazo ta tsaya ta dan yaye lblen kadan yadda zata hanqoshi da kyau a hankali ta zuba mai ido duk ya canza ya wani rame fuskarsa tai sakau ya bar dan sajenshi ya dan baje ya qara fadi sabanin da dayake siriri yanayin shi gaba daya ya sauya zaune yake qasan carpet yayinda Nenne ke kan kujera ya dan miqar da hannushi kan kujerar ya kwantar da fuskasa kan damshe hannushi inda ya kasance kamar wurin baccin Aysha 

Cikin sanyi Nenne 

Ta kallishi gami da cewa Ahmad tashi kaci abinci kar yayi sanyi 

Kai ya dan qara kwantarwa ya lumshe idansa a hankali ya motsa lips enshi yace Nenne naci abinci da Abba banjin yunwa 

Kanshi ta dan dafe tace Ahmad ka dawo da wolwolarka mana tashi yayi yadan qara matsota ya daura kanshi kan cinyarta yace Nenne am bazan iyaba Na rasa farincikina dole wolwolata ta bace ya dan damqo hannuta yace Nenne wazan gayawa in as on Aysha har abadan in ba keba kullum nauyin zuciyata qaruwa yake suka mai zafi nakeji 

A hankali Aysha taji kukan da take dannewa ya kwafce mata cikin sauri da kuka ta qarisa gunshi 

Ganinta yasa ya miqe cikin wata iriyar radadi zai fita da sauri ta bishi ta fada bayanshi ta runqumoshi jikinta ta manna kanta tsakiyar bayanshi dumin hawayenta naratsashi da gyar ta iya budan baki ta juyo gabanshi cikin sautin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro tace ya Ahmad...


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:24 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI...page 1⃣4⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Murya Na rawa tace ya Ahmad guduna kake? meyasa ? Baka son ganina ko ? Cikin kuka mai tsuma rai tace ni dai har Abadan xan kasance mai yarda da zancen zuciyarka ce ta daura hannuta kan qirjinshi tasa daya hannunta kan fuskarshi ta ware yan yatsunta 

A hankali ya lumshe qwayar idansa zafi Na ziyartar qoqon zuciyarsa da qyar yake fidda numfashi taci gaba da cewa zance fuskarka ba zahiri bane kai kace 

Aysha bugun zuciyarkace 💗

A.yanxu kuma sai ka shimfida ja rumtanka kan fuskarka Dan kawai kayiwa 

Kakanmu biyeyya kan abinda bashi da iko a kai

Da qarfi ta riqe kafafunshi tana jijjigawa tana kuka 

Ya Ahmad haqurinka zai cutar da rayuwarmu 

Tuni jikinshi yayi sanyi sonta da yake dannewa qasan qoqon ransa da ruhinsa suka rinqa tsirgowa rauni sosai ya ziyarci zahirinsa 

Hannunshi yasa ya runqumota tako manna kanta cikin qirjinshi tana sakin ajiyar zuciya hannunshi yasa yana share mata qwallar idanta sosai suke sauqe ajiyar zuciya Nenne kam tuni tabar porlon

Can kuma zuciyarsa ta darso zancen gskyar da aka rigada aka fada mai bashi ba ita kamar cikin razana ya balleta a jikinshi ya Dan tureta zai fita ta sake kamo hannunshi 

Juyowa yayi cikin sanyin murya yace Auta Abba Na kirana ya janye hannunshi ya fita ranshi Na soyuwa 

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

               A hankali ya shiga parlon ya kwanta kan tattausan kujerar kaka ya harda qafafunshi ya daura laptop enshi kan ruwan cikinshi phone enshi kuma ya ajiye kan hannun kushin din ya lumshe idansa 

Maganganun kakansu ke masa yawo a kai a ranshi yake gskanta jibewar Bappa Yaya numfashi ya furzar a hankali yaci gaba da cire abin a ransa 

Kaka dake kitchen tana girke girkenta Na tsofoffi duk ta cika gidan da qamshin man shanu girki take tana ta zirga zirga kuma sai mita take ita kadai 

Missxx ya Dan ja gajeren tsaki ita dai wannan tsohurwa bakinta bai iya shiru 

Tazo parlon kusan sau 3 Amman bata ganshiba sai yazu da ta shigo riqe da akoshi sai qamshi yake 

Tana ni bana son iyayi in zaki fito kici abinci ki fito irinku nawa akayi daga baya a dawo kamar za a hadiye juna...

Tsaiwa tayi da sauri ta kalleshi cikin da tsorita tace kai Dudabe yaushe kazo ban saniba ? Ai saikasa nai ihu mutum ko slm bazaiyiba 

Shiru bai kulata ba ta sake ta kalleshi tana kai hannuta kan qafarshi da yake ta kadawa tace kai da Allah banson isa ehe Dan kai kazo ka sameni har gidana kuma inama mgn kamin banza

Duk dai bai kulataba ta juya ta ajiye akoshin kan santer table ta Dan matso tana ai nasani ba bacci kakeyi ba mutum sai baqin hali ni yau har ina murna bazaka zoba jarabatu kawai😏ta ja dogon tsaki ta juya zata tafi da Dan sauri ya kamo hannunta ba tare da ya bude idonshiba cikin rashin son surutun 

Yace 

Dan Allah ki nitsu mana shin ke bakya iya Abu a hankaline 

Ya tashi ya zauna ya jawota gefenshi yana gsky ni 

Yau ba fada zamuyiba mgnar gsky nakeson muyi dake kaka ta Dan harareshi tace kar kawani min zaqin baki ban da masaniya kan tabbayoyin da kakemin kullum batun aurene dai ba fashi kuma dolenka ita zaka aura 

Ya Dan kauda kanshi daga gareta Dan yasan zai harareta kuma yana son ta Dan bashi wani qarin hske kan batun birkiceccen auren da suke ta tunanin zai yiwu

Hakan yasa ya kalleta a daqile yace wai ke gani kike zakumin dolene ni zancen yayanki kamar tatsuniya nake ganinshi wlh kin San bashi ya haifeniba bare ya wani haqiqance a kainaba 

Tace aiko tunda ya haifi ubanka zance ya qare 

Da sauri yace (hey oyani handebo hala mai habe kudina) ke hajia yau kuma abin naki harda zagine 

Edin ai naga kaima zagemin Yaya kake da niyar yi 

A a Na isa Na zageshi gaban qanwarsa 

Da yafima kam ta bashi amsa 

Kaka ya kirata cikin tausarta yaci gaba da cewa mgnar gsky ni dai yayanki bai isa ya Sani abinda bana soba Dan bashine ubanaba

Amman matsalata Dan uwana sun cusa tarin damuwa a rayuwar Dan uwana klonta yake cikin neman mafita yace ni shawara nake nema a gunki Dan ni kam kwanannan zan Koma gun karatuna Amman nafison sai Na tabbata Na bawa Dan uwana farin cikinsa cikin raunin murya yace wlh kaka komai zai iya faruwa da Ahmad Ku tausaya mai tunda shi mai biyeyyene a gareku 

Duk yanayinshi ya sauya azahiri ake gane tausayin Dan uwanshi dake cikin ransa 

Kai ta Dan jinjina tace Dudabe ( no mi watta be alkawal be wadi daga dubi cabfande tati e tati ) ya zanyi da alqawarin da akayi 33 years da suka gaba ta bazan iya hana komai ba 

Kallonta yayi cikin jin haushi yace ke kullum abi daya kike gayamin bakya tuna haramcin auren da kuke cewa za,ayishi 

Yarinyar da muka fito ciki daya da ita insha nono in barmata da yake duk kun jibe shine kuke ta babatu a kai toh wlh zan shiriya zanje Yola gun baba Umar da iyayen Ummi Na tunda kunfi son sai wasu sunji barnar da kuku tutiyar aika tawa zanje nace baba Umar ni banaso kar a kuma hada koda sunana da wannar mayyar yarinyar  ni Na tsani koda ganintane ban ko qaunar tunata ya qarisa mgnar yana tattara phone enshi cikin klon yarinta da take mai tace Dudabe kar kaje zafa kaji kunya wata ran harara ya watsa mata yace dudabo

Wlh in baki daina kirana hakaba bazan sake zuwa gidankiba ai dama bani Na kiraka ba tabashi amsa

Aysha dake jin duk hirar da sukeyi tana tsaye qofar shigowa  dama tunda safe tazo kafin ya shigone taje gun matar mai gadin gidan kakartasu itama kanta kaka bata San bata nanba tsaye tayi idanta tab hawaye bata lura dashiba sai jin da tayi ya yarfa mata mari yasa loptop enshi ya hanka deta ta fada qasa shiko yayi wucewarsa


By Garkuwa Fulani 09097853276📱

[4/9, 2:24 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI...page1⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Tunda ya fita taje ta kwanta kan cinyar kaka tanata kuka mai shiga rai da gyar taita lallashinta 

Cikin kuka tace ba gashiba ai kuna gani da idonku kaka wlh kun Sani sarai mugune 😡bai qaunata kuma shine kuke wani cewa zaku qullamai ni kaka gajiya dani kukayi shine kuke Neman Mae kasheni ko ???

a,a Aysha insha Allah bazai kashekiba da yardar Allah zaki zama Zahra ⭐a gareshi 

Tashi tayi ta gyara mayafin jikinta ta tura Dan bakinta tace Sam kaka buku duba haram ko halal kan batun aurenan shiyasa ba amfanin sauraronku

Cikin kunar zuciya tace 

Ni ya riqada zuciyata ta bushe zan daina tsoron Hamma Yusuf koda ko kasheni zaiyi ta juya tai tfyarta kaka Na kizo Aysha tace anqi zuwan 

⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐

Yau jumma,a kuma yaune baba bello da ya Abubakar suka dawo daga qasa mai tsari daga aikin umrah da sukaje gaba daya suna cike a babba parlon suna ta Dan hira Adam ma dayaje Yola jiya ya dawo Shiyasa suke cike a parlon sunata hira sai Aysha ne da take dakin su tayi shiru cikin tunanin. Ko meyasa ya Ahmad ke gudunta 

Idanta a lumshe hawaye Na bin gefen fuskarta a hankali 

Abubakar ya Sa hannunshi ya share mata qollar cikin lallashi ya dagota yana gyara mata gashin kanta daya Dan baje cikin tausarta yace ayyah autan Ummi meyasa kike kebe kanki daga cikin mu banajin dadi Sam nafison ganinki kina raha da walwalah Aysha ki yarda da qaddara ki jure zafin da kikeji duk abinda kikeji baikai abinda ya Ahmad ke jiba baki ga yadda ya dawoba Amman 

A hakan yake bawa iyayenmu qarfin quiwar yiwa nasu iyayen biyeyyeh 

Kanta ta manna a jikinshi taci gaba da sheshsheqar kuka tana ya Abbukar kafasan waye Hamma Yusuf kasan baida wani buri a duniya daya wuce yasani baqinciki ya Abubakar ko ka manta uwa daya uba daya muke a ina aka taba irin aurenan 

Kai ya jinjina ya jawo hannuta suka nufi palon yana Aysha kada ki tsananta bincike 

Ni zuciyata tsinkewa take sabida bansan meye a qasaba banson jin wani mugun qulli shiyasa banason binciken haka ya jata suka tfi 

******* suna shiga tana maqale da hannuta cikin hannu Abubakar suka zauna ta daura kanta kan damtsen hannunshi 

Ahmad dake sunkuye da kanshi sai yanxu ya dago ido cikin ido sukayi da qarfi yaji zuciyarsa Na duka Tara Tara 

Cikin qarfin hali ya miqe ya Dan kalli Yusuf dake murtuqe da fuska yace (biyaye in dulliko) mu tafiko kai ya Dan girgiza mai bazaka tafi ba eh yace yaci gaba da latsa phone enshi shi kuma cikin hikima ya zame ya bar gun 

 Dakin shi ya tafi 

Duk abinda yake binshi da kallo kawai take bayan fitarsa kadan ta Dan saki hannun Abubakar ta miqe tayi woje


A hankali ta murda qofar dakin ta shiga can ta hangoshi kwance kan gadonshi yayi ruf da ciki matsowa tayi ciken sanda tasa hannuta ta zare picture enta daya kifu a kai idansa ya rumtse gamida cije lips enshi cikin Dan dakewar murya tace bude idonka budesu ka kalleni ka gayamin meye a zuciyarka shin xaka gskanta zancenka Na baya ko zaka qaryata kanka da kanka 

Kai ya rinqa juyawa cikin disashewar murya yake ta maimaita a,a 

Hannu tasa ta dafa kafa dunshi tace ya Ahmad wlh kashemu kake son yi kallifa yadda ka dawo da rayuwarmu 

A hankali yace Aysha nine da laifi meyasa kike qara azabtar da zuciyata?

Ehh kaine da laifi Ashe dama yaudara gsky ce maza nayi sannan kai sai ka rasa wacce zaka yaudara saini qanwarka  kasan dama ba aurena zakayiba meyasa ka cutar da zuciyata💔 

Ya Ahmad ka cucemu ta fada cikin kuka kan qirjinshi ta fada tana kuka 😭

Sosai tana Dan bugaga girjinshi tana dama baka sona ashe zancenka qaryane dakace Aysha ce bugun zuciyarka 💗 

A hankali zaciyarsa keta cushewa zancenta ke ratsashi idanshi ya fara budewa bakinshi ya fara motsawa zafi da yakeji ya fara bunqasa cikin rauni ya kamo hannuta ya daura kan qirjinshi 

Yace kinjin har Abadan bazan miki qaryaba haqiqa ke Aysha kece buguzucita💗 Na gayamiki duk numfashin da zan zuqa da sonki nake zuqarsa wlh ina mai sheidamiki rayuwar Ahmad sauran kadan tunda aka tirsasawa zuyata fidda qaunarki Ayshaaa ki sani wlh duk randa Na gama cireki a raina toh tabbas a ranar zan barduniya🌍 

Cikin sanantar kukan tace OK zaka ciren a ranka kenan ?

Eh Aysha ya zama dole naiwa iyayenmu biyeyyah da qarfi ya danna hannuta kan qahon zuciyarsa yace kiji har abada zan mutu da qaunarki hannushi 2 ya hada yace plxx Aysha( burtinam ha sudu am  usenifu ta loru waru ha am)

Fitamin a dakina ina riqonki karki qara zuwa guna 

Klonchi tai sosai cikin zubda qollah tace fitar numfashinka shi zai yanke nawa numfashin yayinda muka mutun zuciyar Dan uwanka dakafiso zata buga Dan rashinka ta sake kallonci tai murmushin takaici tace Allah sarki duniya su Abba zasuga tarin qawarwaki wataqil rashinka yasa Abba na barin duniya ayyah baba bello zai qunci takaici da dacin rayuwa 

A hankali ta matsoshi tace yau zanyi ban kwana da kai kiss taimai kan kumatunshi yayinda shi kuma ya lumshe ido a hankali ya manna kanta kan qirjinshi can kuma ya Dan daqota ya manna mata kiss a goshinta ta kalleshi cikin yin murmushi takaici ta sake shi tafi tana suyar zuciya 


By Garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI...page 1⃣6⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


----------------------------------

Haka dai rayuwa taci gaba da juyawa cikin quncin rayuwa 

Yau jumma,a 

Bayan an sauqo daga sallan jummaa 

Duk sukayi gida 

Cike suke a parlon 

Sai Yusuf da Ahmad da basa gun 

Baba bello ne ya dan kalli Usma dasu Rabi,u ya danyi gyaran murya yace kai Abdul tashi kuje parlona ku fitomin da kayayyakin dake ciki 

To suka amsa gami da miqewa sukayi part inshi din 

Aysha ya kalla a dan fizge gamida dan yafi tota da hannu a hankali ta dan saki hannun ya Abbakar ta miqe taje gabanshi ta dan duqa 

Wani dan leda mai sheqin gaske ya miqa mata yana gashi ki kaiwa Yusuf kuma kice ina kiranshi dum zuciyarta ta Nada wani sauti

😳😳😳ido ta zaro cikin firgici tace baba ni kuma ? 

Eh ya bata amsa gami da gyada mata kai 

Cikin firgici da razana da bugun zuciyarta da ya tsananta 💓 da gyar ta miqe dakin Ummi ta nufa riqe da laidar 

Kaka da tazo bikonsu su duk sun daina zuwa gunta 

Ta kalleta cikin wasa tace ke figi ruga yau ba mgn ne 

Baki ta dan zunbura ta zauna gefen 

Umminta tana rau rau da idanta tace ayyah  Ummi dan Allah ki ajiye wannan in Hamma Yusuf yazo ki bashi wai inji baba 

Kai ta dan girgiza mata 

A a ni ban isaba ko ni ya aika dole nakai aiken ba wani nawa den ke kiwani ce sai ni zan bayar 

Kaka tayi caraf ta karbe da cewa ai wannan ma rashin kunya ce 

Kallonta tayi a lkcin da tamiqe tasa bayan hannunta tana goge qollah tana wlh Na Sani sai ya zageni kun sanshi sarai mugune 😡 banje inda yake bama Yaya ke kaka badai burinki ke da dan uwanki ku naqasamin rayuwa ba kusani kunci da takaici 

Da sauri Ummi ta dan yimata don qolo 

Kaka tai dry tace 

Barta Fatima ai randa zatayi alfahari da hadinmu nanan tafe 

Ita dai fita tayi tana dan qunquni


Zaune yake a dakinshi a qasa kan carpet jikinshi sanye da 3 qtr sai dan riga mai hade da hula ya Daga dukkan alamu woya yake 

Ita kuma a tsakiyar parlon ta dan tsaya tana tunanin ya zatayi tayi slm shiru toh ko bayananne ta tabbayi kanta sabida tayi SLM yafi a qirga shirun da taji yasa 

Ta danyi tinanin shiga dakinshi ta ajiye mai kawai 

Cikin nitsuwa kanta a sunkuye tayi cikin dakin ba tare da tunanin ko yana cikiba sai xuciyarta dake bugawa 

Bugun zuciyar ya tsananta a lkcin da ta shiga dakin kanta a qasa tana nufin ajiye mai kan gadonshi sai ji tayi tayi tuntube da qafarsa aiko tai taga taga ta fada kan kirjinshi 

Da sauri cikin mmk da jin ta kaici ya hanka data duk da bai gama gano wayeba sabida duhun dake dakin 

Itako tuni hancinta ya sheida mata shine qamshin turarensa yasa ta ganoshi shiyasa cikin sauri ta miqe gami da miqa mai aiken jikinta har bari yake cikin tsoro da rawar murya ta miqa mai ledar  tace (da Hamma baba on vi mi waddine ) gashi Yaya baba ne yace in kawo ma 

Fuska a murtuqe ya zaro ido ya buga mata tsawa yana ( salu vurti nam hado )  wuce ki ficemin daga nan 

Tsoron sawar da masifarsa yasa ta dan saki laidar 

Wasu yan takardu masu kyan gani suka watse a gun har kan qafarsa 

Iskar pankar dake kadawa ya rinqa watsa su 

Mmk sosai ya bayyana a fuskarsu su dukka cikin al ajabi da dimuwa yasa hannu ya dauko daya yana dubawa da fargaba sosai cikin minti 2 kamanninsa suka qara sauyawa bugun zuciyarsa ya tsananta numfashinsa ya fara dabur cewa idansa ya sauya daga yan qanana farare suka koma manya jajaye hatta jijiyoyin kanshi dana hannushi suka taso sama da wani irin yanayi ya tako ya nufi inda take 

Cikin tsoron da take ta Sa hannu ta toshe bakinta da hancinta🙊 da nufin hana kukanta fita sai hawayen daketa kwaranya a hakali ta rinqa takawa tana baya baya shi kuma yana binta har suka pito parlon 

Ganin zatayi waje yayi saurin fizgota har saida ta fada jikinsa 


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Mi,WASMITI..page 1⃣7⃣to2⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 

Cikin takaici ya rinqa sakar mata maruka 

Zuwa yanxu tsoro ko gudun dukan ya fita a ranta firgicin ganin i,v din Auren sun da suka gani yafi komai bada tsoro a gareta jikinta da zuciyarta duk sun qageshe 

Zafi sosai Yusuf keji a ransa ya gama makancewa da bacin rai shiyasa baiji bai gani yaketa bugarta kallonta yake ido cikin ido a fili yake cewa badai ke kince taurin kaiba ba tsayuwa kikayi kina tsuramin shegun idanunki 👀 kamar Na matsafaba toh wlh kanki zakici mayya fitinenniya ya kuma hambararta tai baya 2 ta fadi bakin qofa a dai 2 lkcin Ahmad da Adam suka shigo parlon 

Da sauri Ahmad ya sunkuyo ya dagota yayinda Adam ya nufi gun Yusuf din yana fadin 

Haba biyaye me hakan anya kana cikin hankalinka kuwa ko dai ka fara shaye 2 ne 

A harzuqe yayi kan Adam yana zazzaro ido woje yana eh giya nasha Adam ko kana da maganin buguwarnan tawane cikin mmk Adam yake klonsa kamar dai a bigen yake kam da sauri ya dakatar dashi hannushi ya jawo ya ajiyeshi kan kujera Goran Faro mai sanyi ya ballo ya miqamai karban Goran yayi ya cillata kan Aysha da sauri Ahmad yasa hannushi zai tare Goran cikin qeqashewar zuciya ta ture hannun ta kalleshi ido a bushe cikin yana yin dacin rayuwa tace barshi barshi ya Ahmad wlh ni a yanxu nafi buqatar azabar Hamma Yusuf ina dai sau daya ake mutuwa toh kubarshi ya kasheni ko duk ma huta wlh nafi buqatar zalumcin Hamma Yusuf din Don gwara nashi ai Ku naku boyeyyen zalumci kukemin wanda zai iya fasa zuciyata ta qareshi mgnar tana mai zubda qollah😭

Cikin sanyin jiki Ahmad ya kamota ya rugumota ya mannata a girjinshi yana Dan shafa kanta yana bubbuga bayan ta 

A hankali ta rinqa sheshsheqan kuka mai tsuma rai 

Yusuf da yake ta numfashi kamar zaki Dan zabar bala,i da zuciya cikin daga murya yace wlh kar nazo Na sameki a nan Dan wlh sai na lahira ya fiki jikin dadi 

Da jin haka Ahmad ya jata sukayi cikin gida 


Adam ne ya rinqa yiwa Yusuf din nasiha kan ya tausasa zuciyarsa 

Haba biyaye shin a duniyarnan akwai mai wuce qaddararsane ?shin muke tsarawa kanmu rayuwa ne ko mahaliccinmu? haba Yusuf rayuwafa komai asannu mutum zai bishi matuqar kana son cin ribar rayuwar..... 

Cikin sauqe ajiyar zuciya ya kalli Adam din cikin rawar murya da hardewar harshe yace Adam ya zanyi ya zanyi da burin Dan uwanmu Ahmad nafi jin makomar rayuwar Ahmad ya kamo hannushi yaci gaba da cewa shin kai baka tunanin yadda Ahmad ke son yarinyar nanne biyaye haqiqa kakanmu ya kasance mai zalumci a kan jikanshi Ahmad da yafi mu dukamu haquri da biyeyya a garesu cikin rawar murya yace Adam wlh so suke su kashe rayuwarmu da bakinciki Adam ya zanyi Plx biyaye ka tayani samawa Dan uwanmu Ahmad farin cikin Sa 

Sosai jikin Adam yayi sanyi ya kalleshi cikin sanyi yace insha Allahu yau dinnan zamu samu mafita Yusuf zamuyi tunani daga yanxu xuwa dare gobe da safe sai mu isar da manufarmu a haka ya samu ya Dan lafar da fushin 

A cikin gida kuwa Ahmad ne a gaban Nenne bayan ya samu Aysha ta lafa da kukan ya barta tare da Abubakar yana ci gaba da tausarta 

zaune yake a gaban nenneshi ya daura kanshi kan cinyarta sai fidda wani nannauyan numfashi yakeyi cikin zuciyarsa sai tafasa takeyi da ka ganshi kaga tashin hankali 

Allah sarki uwa da dan ta sai rabbi tuni Nenne ta gano yanayin da gudan jinin nata ke ciki a hankali tasa  hannuta cikin sumar kanshi mai tashi da sheqi ta rinqa shafa kan nashi tana Dan shafa kumatunsa da daya hannun nata dai 2 kain kuncinshi taji damshi alamun hawaye😭 da sauri ta dago kanshi ta zuba mai ido shima itan yake kallo ya Sa hannayenshi 2 y daurasu kan nata da ta tallabe mai fuska 😭cikin zubda hawaye da muryar kuka bakinshi har yana rawa kamar maijin sanyi 

Yace Nenne Na kingako nikuma kinga yadda rayuwa ta juyamin ya zanyi Nenne inason Aysha kuma Bappa Yaya ya hanani ita Nenne ke kadai zan gayawa naji sanyi ya kuma kamo hannuta yaci gaba da cewa wlh inasonta tana sona kuma an rabamu Nenne duk duniya bayanke da Abba ba Wanda nakeji kamarta 

Itama hawayen takeyi cikin salon ni nacuceka ya kai Dana tace Ahmad ba laifinka bane ba laifin kowa bane laifi nane Nina kawo wannan irikitaccan al,amari Amman ka gafarceni D'ana da  Sauri ya katseta da cewa ni baki min komai ba ni zan nemi gafararku

a haka baba bello ya shigo ya samesu suka hadu sukayi ta bashi baki da samai albarka 


Da slm marsa da shigansa duk kusan a tare yayisu kuma duk batajiba har saida ya zauna gefenta daga dukkan alamu yanxu ta Idar da sallah

A Dan firgice tace kai me hakan  wlh dudabe sai nakai qararka gun Aliyu Dan ka isheni ji yadda ka shigomin a fijajam bako slm cikin harzuqa yace ancemiki ni alulkitab ne da zanshiga wuri ba slm toh ai nidai banjiba 

Hmm toh nidai nayi slm 

bakadai yi da qarfiba kam

 toh ni maroqine da Zan kama ihu a gari

 oho dai tace masa ai tunda kin ga nine  shikenan ga baki ga tsoro harara ta cillamai shi kuma yaci gaba da cemata dama   baki ya Dan tabe ya kalleta a cukushe yace ke ni dama zuwa nayi ki...da sauri ta katseshi in baka lbrin ko toh nima bansan komai ba kan batun aurenku da akeson hadawa 

Cikin qulewa yace keda Allah fadi ba,tambayaba ai duk surutn siya kin iya Amman da yake kinga INA roqonki shine kiketa wani jirgani toh ni bashixan tabbayeki ba zuwa nayi ki rakani mambila yanxu kafin manqqariba mun dawo baba bellone ya Aiken 

aiko dajin haka ta miqe tana yauwa Dama inason zuwa toh mutafi Hajia a yawe 

Oho dai sainaje Dan baqin ciki murmushin mugunta yayi aranshi yake cewa kedai komai fada


A hanya kaka sai bala,I take dan ganin hanyar Yola suka kama fada take ase Dama baka da mutunci INA zaka kaini ?

 Sama zan kaiki ya bata amsa 

fuskarsa Na kan titi yanata tsula gudu mita kam da masifa ya shashi Amman dayake mishkiline kafi mahaukashi ban haushi ko a jikinsa  5:00 pm suna cikin porlon baba Umar 


By Garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI...page2⃣1⃣to2⃣5⃣......Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Bayan yan gaishe gaishe da sukayi sai suka Dan tsagaita 

Kakace tace kai Dudabe ka bada aike Dan dere yanayi.

 toh yace mata gami da Dan kallon baba Umar cikin yanayinshi  Na rashin surutu ya Dan sunkiyar da kai gami da Dan sake dagowa ya kalleshi ido cikin ido yace 

Baba dama zuwa nayi kamin taimako ka Duba Al,amarinmu ni da yan uwana sai kuma ya danyi shiru Dr Umar ya Dan jinjina kai yace fada min ba komai gayamin menene matsalar 

Ya Dan kalleshi gami da cewa baba Dama ni batun Auren nan ne sai kuma ya kurawa kaka ido Dan jin wani uban salati da ta dago haydar ma idon ya zuba mata ta kalleshi a yatsine tace wlh Allah ko Yusufa (a wasmitan ) zakafa yi nadama ka kama bakinka Dan gaba wlh kana dab da jin kunya zakayi nadama gabafa wlh ka iye bakinka.....

Ke da Allah wayasa bakinki cikin zancen nan me hadinki dani bafa cewa nayi kirekoni kimin gatsali a zancena ba kuma wlh ki kama bakinki ni da wadanda suka isadani nake mgn badake karere ba ya qarisa mgnar yana mai watsa mata harara da zazzaro idansa woje Dr Umar yadan murmusa Dan Sani dama haka zata iya faruwa shi mmk mayayi sosai dayaga wai Yusuf ne da kaka a mota daya kuma tafiya mai nisa gashi ba Dan rabiyar fada a tsakaninsu 

Yusuf ne ya katsemai tunanin nashi yana mai fadin baba 

Wlh tallahi kaji nayi rantsuwar musulmi 

ko baba bana son Aysha wlh Na tsaneta ko ganin ta bana son yi Sam banjinta a raina baba wlh Auren da kukeson hadawa wlh masiface baba ni wlh Na yarda ko mahakaciya Ku samo Ku hadani da ita matuqar zan tsira ban Aure Aysha ba 

Kaka kam baki ta sake tana ware ido tana fadin wataran zakaji kunya wlh sai kunya ta hanaka ganin abinda ke gaban ka ni kam baza,ayi tijarar nan daniba barima ka gani woje zanyi 

Hydar da shima Sam bai farinciki da Auren da suke son hadawan ya harareta yace kifi ruwa tafiya ya koma ya kalli mahaifin nashi yace gsky baba niba banason wannan hadin naku nafison ya Ahmad ne ya auri Aysha

Goggo Aysha dake gefe najin muhawararsu ta bisu da ido tana mai cewa Yusuf ai banan ya  kamaceka kazo ka furta qiyeyyar da kake yiwa Aysha ba gun Umminka zakaje ka fada

 ido ya Dan zaro yace wlh tace duk randa Na kuma furta mata wani zance akai zata tsinemin cikin kaduwa Dr Umar yace

Subahanallahi 

Meyayi zafi haka insha Allahu bazata tsinema ba 

Cikin yanayin lallashi ya dafa kafadarsa yace 

Yusuf kayi haquri

Qaddara ta rigayi

Fata 

Bani da wani zabi bayan Na Bappa Yaya

Yusuf nima cikin qarqashin ikonsa nake

Kayi haquri ka ruggumi qaddara 

Kayi biyeyya ga iyayenka zakaga sakayya mai kyau 

Wlh bani da ikon watsa Auren ka da Aysha da ina da iko da tuni Na watsashi 

Ya kuma dafa kafadanshi yace abinda baka saniba Yusuf ya rigada an Dade da daura aurenku kai da Aysha

Tun Aysha nada shekara 8 aka daura aurenku 

Cikin firgici da mmk tsosai haydar kam dake zaune kan hannu kujera bai san lkcin da ya zameba Yusuf kuwa baki ya bude kawai yana binshi da kallo a rensa yake cewa wadannanfa sun Dade da kamu da cutar haukannan bamu kula da wuriba

 muryar hydar ce 

Ta kuma bashi wani sabon tsoro 

Hamma Yusuf toh ai Abu yazo da sauqi yoh ba sai ka saketa ba kawai

Cikin kaduwa ya kalli hydar cikin murmushin takaici yace yoh in banda abinka 

Hydar ai Auren da ya halatta ayishi shi ake iya sakarsa toh kai ka yadda Auren ya daurune?

Kai ya jinji yace haka nefa Hamma Yusuf 

Dr Umar ne ya kallesu cikin Solon yaro mankaza 

Ya kalli hydar yace haba Aliyu ase kaima kna da baqin tinani wannan wacce iriyar shawara kabaiwa Dan uwanka Ali ban sanka da haka ba ya kuma maida dubansa kan Yusuf yace wlh Yusuf ina jiyemaka tsoro fushin iyayenka kaji tsoron Allah kayiwa iyayenka biyeyya shin kai bazaka yi koyi da Ahmad ba ka ganifa shi aka gwara Amman ba Wanda zaice ga qorafin ko furuci mara dadi dayayi kayi koyi da Dan uwanka

Haka dai yaita musu nasiha 

Daga bisani suka kama hanyar taraba a motako yasha mita gun kaka 

-------------------------------------------------------------------

8:27 pm ya sauqi kaka a qofar gidan ta kai tsaye gidan Anuty Sadiya ya wuce 

A Can kuma gidan Anuty sadiyan tun bayan isha Ahmad yazo yana shiga bayan slmar da yayi bai kuma mgn ba 

Ikram yarta tai gudu ta shiga bedroom tana mami ga uncle Ahmad yazo 

Tare suka fito da ikram tana zuwa kan cinyarshi ta dale tana uncle xamuje gidan zoo ko kai ya Dan gyada mata ba tare da ya bude idoba 

A hankali Sadiya ta kalli Dan uwan NATA cikin sanyin murya tace Ahmad ka rinqa mai maita innalillahi ka yawaita hamdala kaji Dan uwana ?

 toh yace muryayarsa Na rawa hawayen da yake boyewa suka samu damar zubowa Allah sarki Ahmad duk jarumta irin tashi ga so Na maidashi rego ko yaushe idansa bai bushewa da qollah😭 haqurinshi ya fara gazawa cikin sanyi ya zame daga kan kujerar ya komai gefen Anuty Sadiya ya riqo hannuta ya daura kan qahon zuciyarsa yana mai Jan numfashi da qarfin yace Anuty numfashina tafiya yaketi kiji qahon zuciyata kamar zata stage ina tausayawa rayuwarta INA taushayawa biyaye a INA kuma tausayawa Maryam Dan zan aureta ne kawai Amman ba batun so kam gashi matsalar Aysha ko

tafi komai damuna a duniya wlh Anuty da mutuwa nayi da yafi min da wannan rayuwar gomin ko nasani Nanda Dan  wani lkci zan mace Na barku ya daura hannushi kan jinyarta yana mai cigaba da cewa Ayyah   

Anutyna zan mutum Na barki nabar Aysha zan barki da Yusuf da Adam Na tabbatar duk abinda zan miki zasu miki toh Amman Anuty duk duniya ba mai yiwa Aysha abinda zan mata biyaye baya Sonta bare ya riqemin amanart Anuty zanbar Amanar Aysha a gunki keda ummina ku kadai ne zaku iya riqemin  amanrta  bazan ba Yusuf amanar Aysha naba Dan nasan bazai riqemin ba Niko banason abin da zai gasamin Dan uwa

Kuka

Sosai sukayi cikin kuka mai tsuma Sadiya take fadin bazaka mutuba Dan uwana zakarayu zamu rayuwa tare zamu zamewa Nenne mu 3 tamkar da  30 Ahmad banda qawa ko aminiya kune kawayena kai dasu Yusuf 

Ahmad ni INA gidan miji in kamutu zakabar Nenne mu da kewa 

Rabi,u bazai iya mata kula da biyeyyar da kake matanba 

Da Sauri yace Anuty banso Rabi,u ya kasance mai irin halina gashi ni yanxu hiyayyarce ke shirin rabani da duniya 

Bazaka mutuba Cewar Abba cikin mmk Sadiya ta kalleshi tana Abba yaushe ka zo ?

Tun dazu nazo Sadiya duk naji hirarku Sadiya Yusuf Na Haifa Amman Ahmad shine jigona insha Allahu Ahmad bazai mutuba Shi  daya da nake gani naji sanyi Abba kuka yakeyi harda hawaye Ahmad ya kalleshi cikin dauriya yace Abba dama kana zuwa gidan Anuty Sadiya ne ehh gashi kuma ka gani aini yawanci Abba kanxo muyita hirarmu Amman Sam baba shi baya zuwa ko kadan suka danyi dariya 

Abba yace toh ai dama ni ya kamata Nazo bashi ba tunda shi yanaga gidan surkine ni kuwa gidan ma,aikacin asibitinane kuma mijin y'ata 

Haka dai sukayi SLM suka tafi suna fita daga layin Yusuf kuma Na shiga Amman basuga junaba da yake akwai cikowar ababen hawa

Cikin tsoro da firgici Yusuf yayi kan Anuty Sadiya jikinshi har  bari yake ganin halinda take ciki


Kuyi haquri masoyan wannan littafin insha Allahu zan Duba qorafinku nason Na yawaita Sa fillanci a ciki haka kuma INA Baku haquri da jinkirin da kuka gani 

I love all makaranta wannan littafin

 Fasaha Writers INA gaidaku Auntys din kamaluuuu

😝

By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI...page2⃣6⃣to3⃣0⃣  Na Aysha Ali Garkuwa 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Cikin kaduwa yace Anuty meke faruwa? ya Na ganki haka kiga yadda fuskarki ta kumbura ?meya sameki ? Haka ya jero mata tabbayoyin 

Cikin qoqarin boye damuwarta tace 

Kai Yusuf me haka ka firgice gaba daya kawai ciwon idone ke damuna kuma yanzuma Abba ya kawomin mgni 

Hannuta ya kamo suka zauna kan kujera ya kalleta da kyau ya Dan kauda fuskarsa gami da yamutsa fuska 

Cikin kula tace Yusuf meke damunka 

Lips din shi ya Dan ciza gamida Dan kamo Na kasan yana tsotsa 

Yusuf meke faruwa ne ka gayamin mana 

Qara matsar lips din yayi yace Aunty Na tsani Aysha Na tsani Auren Anuty

 Aysha fa burin Ahmad ce 

Eh ita burin Ahmad ce Amman kuma zabin iyayenmu ne da suka zaba maka ita 

Cikin takaici yace Anuty hardake bakya tuna makomarmu ba komai Yusuf insha Allahu ba wani Abu 

Hmmm 

Anuty ba haka naso ji daga  garekiba Amman naga kema layinki daya da tsofaffinan 

Cikin sanyi ta rinqa mai nasihar da shidai lebenta kawai yake ganin yana motsawa alamar mgn take 

Can dai yace ni zan tafi har baking gate ta rakashi yaja mota ya tafi 


Allah sarki yau kusan duk ba wanda yayi bacci Abba gaba daya ya karaya Nenne kuma kan sallahya ta kwana tanayiwa gudan jinin nata addu,a Yusuf kam abin ba,a cewa komai a jikin shi yakejin alamun ciwon zuciyarsa ke shirin dawowa  Adam shima cikin tunani ya kwana shiko Ahmad ciwon da yakeji a zuciyarsa ne ke qaruwa kullum dare Anuty Sadiya kam kusan kuka ta kwana yiwa Dr Bashir mijinta kenan Dr Umar ma lamarin ya dameshi Ummi kuma tabbas tanaga an cutar da Ahmad haka dai kowa ya kwana zuciya a quntace


*************"*"""****** Yau Monday bayan maqqariba duk suna tare a parlor kowa da abinda yakeyi su Abba ma duk suna nan

 lami  mai aikice keta kacaniyar ta a kitchen

Abba ne ya kalli Usman yace je ka kiramin Ahmad toh yace gamida miqewa ya fita,,,,,,,,

Tare suka shigo kai tsaye gaban Abba yaje ya zauna baba bello Na cemai Ahmad Yusuf fa ?

Yana wonka ne baba.

 toh yayi kyau 

Cikin gyaran murya Abba ya kalli duk kan mutanen parlor ya zaro wasu document dinsa daga cikin jakarsa 

Ahmad ya miqawa yace ingo duk inda kaga za,asa hannu ka saka cikin mmk ya kalli abban  yace toh Abba bari Na jira biyayena 

Ido ya Dan qura mai gami da cewa kai nasaka ba shiba

Ahmad bai iya musuba ko da abokaima bare da iyaye 

Duk ya shiga budewa yanasa hanu daya bayan daya ya gamasu tas ya dagasu ya hada ya miqawa Abba 

Cikin tsantsar qaunar Dan Dan uwan nashi yace toh mutanen parlon nan ku zama shaida bayan shaidawar Allah ☝🏻ni Aliyu Muhammad Aliyu Na baiwa Dana Ahmad company Na dake birnin Abuja Na bashi halak malak Na kuma malla kamai gidana da yake anquwar fada nanan cikin taraba 

Gaba dayansu farincikine ya cika fuskokinsu ba abin da suke fadi sai

Masha Allah kai Abu yayi kyau Abba Allah ya qara budi Nenne kam kukan farinciki takeyi sosai baba bello kuma fada ya kama haba Ali kasan abinda kakeyi kuwa ?

Da Saudi Abba ya katseshi da cewa Dan nayiwa danka kyauta shine laifin 

Cikin jin kunya baba bello yace a a wlh ba haka bane Ali Ahmad ai dankane Aliyu .

Toh inko kasan da haka barunka kasa albarka kawai haka kuwa akayi 

Ahmad kam da ya zama mutum mutumi sai yanxu yaji bakinsa Na furta 

Jzkllahu bil jannah👏🏻 Abba ubangiji ya jibanci lamuranka gamida yin sujjadah yayiwa rabbi godiya  murya Na rawa ya miqa mahaifinshi yace baba ganifa kyautat da Abba yamin Abba Na ya gamamin komai a duniya gaban Abubakar yaje yana kalli Sadip 

Na gani ya fada gamida cewa ya Ahmad ka wuce haka a gun abbanka runqumarsa yayi sukayi ta farin ciki kowa yaji dadin wannan kyautar Usman kuma cewa yayi ya Ahmad tukuicina mata nakeso

Ka samu Usman key din motarsa ya cilla mai gamida cewa ga tukui cinka 

Wow Rabi,u da Abdul ke fadi usmanko rawar choki ya kama harda juyi 

Dai2 lkcin Yusuf ya shigo da Sauri Ahmad ya runqumasa gamida nunamai kyautar da ya samu gsky farin cikin Yusuf tamkar yamafi Na Ahmad Adam kuma cewa yayi dole ayi walima a gongoje

Wunin ranar dai farin ciki ya dawo cikin family din saka makon farin cikin Ahmad din sun shirya kan cewa ran jumma zasuyi waliman shiri sukeyi sosai sun gayato manya manyan   mlmanmu  Dr Ibrahim jalo jaligo dasu alaramma malam Sulaiman gasu shehk Kabir Gombe su isa Aliyu fantami duk dai anata shiri  

Gaba daya shirin walimar yadan kauda damuwarsu kasan  su Bappa Yaya tuni anxo Dr Umar ma da iyalansa abokan Abba Dana baba bello da dai dukkan yan uwa musulmai 


Qaqa qara qaqa


Taro yayi taro gaba daya duk girma irin Na farfajiyar qofar gidan kamanni family ya kasa daukar jama,ar dole wasu har bakin laying anquwar 


2:12 pm kowa dake cikin anquwar ya shaida daurin Auren Maryam Umar ardo da Ahmad Muhammad Aliyu saikuma  Adam Umar ardo da Amira Ahmad Muhammad Aliyu 😳😳wasu fuskarsu mmk yake nunawa wasu kuma figicine sosai aurenda ansa sai nan gaba 1 month shine yanxu lkci daya a hargitse Abu cikin tsananin firgita Yusuf ya nufi gun Ahmad

Cak ya tsaya jin ana  cewa ayi addu,a ga ma auratan asaka da Aysha Aliyu Muhammad Aliyu da kuma Yusuf Aliyu Muhammad Aliyu

Toh fa gaba daya kowa da abinda take fadi Wanda bai sansu bama jin sunan su ya kansa  mutum 🤔 


Bugawan 💗qirjin Ahmad kuma da Yusuf ba,a magana dukkansu ko qwaqwaran motsi sun kasa 

A cikin gida kuma jin wannan lbrin yasa Aysha dake shirin Shan ruwan ta qware takoyi muguwar gwara a take a gun ta fadi ba..


😍😘ina alfahati daku matan group din DABITAL FALAKU soyeyyarku sadidan zee Abba gaisuwa gareki da fatan masu son a saka fillanci suna ganewa 

Kowa tamba Yaya wai zan kashe wani daga  cikin star dinko toh nima INA nasani kuma banceba 😄


Dan 

Allah Ku rinqa haquri da typings errors da muke samu 


By Garkuwan Fulani🐄🐪

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

MI,WASMITI..page 

3⃣1⃣to3⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Jiki Ba 

Qwari ta zame ta zube kan gado ta fara rera 

Kuka mai tsuma ran mai sauraro 

Su Nenne dasu Ummi da mama matar baba Ahmadu mahaifiyar Amira kenan 

dasu kaka da wasu qannen Ummi cikin su ko harda innah mahaifiyar lamido on top Dan Baban lamidon yayane ga Ummi mahaifiyar su Yusuf din 

Gaba daya lallashinta sukayi 

Nenne ce ta jawota kan cinyarta tana shafa kanta 

Aysha ki bar kukan nan haka dan Allah ko so kike muma ki samu kukan kinga Ummin ki kam tunda gari ya waye kukan itama take ki daure Aysha am kowa inya yaga kin sake muma duk zamuji dama dama 2

Sheshsheqa takeyi har kamar zata shide ganin haka yasa Ummi kam juyawa ta fita tana cige lebenta da zubda qollah😭 a ido 

Cikin hatsala kaka tace 

Ke 👈🏻Aysha zakici kanki nace wlh kanki zakici (Minin  kam ha alari amin do ha doddo a accata amin) 

Mukam inda kika ganmunnan an an zaki barmu ehe 😡😏 (anon bikkoi jotta saro enmon be fotai bemon ) ku yaran zamani wai iyayenku basu isa dakuba) 

Wlh ina gaya miki matuqar dai baki gyara halin kin nan Na taurin kaiba toh wlh zakisa baqin ciki cikin rayuwarki.

 

Bayan hannuta tasa ta goge gwallar dake bin fuskarta cikin rawan murya da disashewar voice dinta tace kaka ni kuma wanne farin cikene ya regemin a rayuwata ai bani da wani sauran haske sai duhu ta dago ta kalli Nenne tace Nenne insha Allahu bazan sake saku kukaba kuyi tamin addu,a Allah ya dauki raina kowa ya huta da sauri 

Innah tace kul👈🏻 Aysha kar ki kuma irin wannan furucin Anuty Sadiya Ce ta zauna gefensu taci gaba da bata baki a haka dai suka samu ta Dan tsagaita kukan 

            

          🔆🔆🔆

Bayan an gama daurin Auren

Sai akaci gaba da gudanar da liyafar da aka shirya

Daga nan kuma akayi sallan LA,asar 

Sannan manyan malamai suka rinqa bada tasu gudumowar a inda suka rinqa bada shawar wari ga angwayen da amaren 

Sune ba ,a tashi a walimarba sai goshin maqqariba nan kuma akayi sallah akaci abinci aka kumayo ishaa daga bisani 

Fagan ya zama Na alaramma malam Sulaiman ne ya hau ya rinqa rera karatun alqura,ani mai girma inda sautinshi mai dadin sauraro ya rinqa rasa cikin anguwar tako ina 


9:25 pm 

Yusuf Na kwance a parlon shi kadai abin duniya duk ya isheshi Amman kuma yana qoqarin nemawa kanshi da biyayenshi mafita ne kuma a tsarinshi ya samo musu ma fitan


 Adam da Ahmad kuma  suna can suna fama da abokansu da suka samu hallaruwa wajen  bikin 


Daga nesa yakejin surutunsu alamar nan part din shi suke zuwa 

Dan gajeren tsaki ya ja gamida juya kanshi ya lumshe idansa kamar maiyin bacci 

Iska ya Dan furzar cikin ransa yake cewa 

Ko waye ya gayyato min wadannan parrots din mutane bakinsu baya iya shiru nasan kuma ba aikin kowa bane sai Adam duk 

Yanxu zasuzo su matsawa rayuwata 

Ya kuma Jan tsaki dai2 lkcin suka is a tsakiyar parlon 

Mmk nayi sosai ganin wadanda suka zo din 


Su  LAmido on top ne Na ruwan kashe gobara 

Gefen shi kuma kamal ne anqon yusra Dalibina 


Daga daya gefen kuma Modibbo ne  angon Bilkisu meke faruwa 

Bayan shi kuma Yaya habeeb ne nida Yaya habeeb can kuma gefen jalal ne Na  jalaluddin 

Abin mmk sai ga wasu masu kama sak 🤔lah Na gane su ase Hassan da Hussain ne  na littafin yar Fulani Na Aysha Ali Garkuwa  

Cikin gajiya suka zazzauna lamido ne ya zauna gefen Yusuf ya Dan harareshi yana wlh kadai ji jiki mutum sai baqin halin....

Kai kuma sai shegen surutun siya eh anyi din bakinka ko nawa 


Nan kuma ya juya gun kamal ya Dan yi daryar tsokana yace kai kamaluuuuu dama ase kana iya barin asran taka kazo wani woje 😜


Kai dai lamido Dan duniya ne toh duk nacina Na kaiku ne kai da modibbo cewar kamal kenan gaba daya sukayi dry 

Cikin qasaita modibbo ya hararesu wlh kundai kunji jiki yara qanana daku sai baqin jaraba

 hararanshi  lamido yayi yana Nikam nafi qarfin yaro sai dai ko en kamal ne yaran  Dan wlh ni kam Na wuce yaro 


Hussain ne ya karbe zancen da cewa ai wlh kamal kam da lamido da modibbo layinku daya Habeeb ne yace kamal ai shi ba daga qafa 

Harara kamal din ya watsa masa yana aiko wlh ni kam Na daqa qafa kusan shekarun biyu ina haquri 

lamido ne yace toh shiyasa kaso ka cinye baking yar mutane tsabar kiss ne harda kumbura mata lips 😀yoh da an barka cinye bakin zakayi ko  kamaluuu 😝😀

Adam ne yace kaifa on top layinku daya da kamal Dan wlh Baku da sauqi 


Yusuf ne ya kalli hasaan yace yane  sarki hasaan kayi shiru ko daya ke nasan kai ba irinsu akukkuturunan bane iyayen jaraba basu da aiki sai Na zance mata

 lamido ne ya watsa mai harara yanxu kai kuma Yusuf har kana da bakin mgn ne duk jara barmu mun kaima ne dry sosai sukayi 

kamal yace har kai da modibbo bai kai kuba 

jalal ne yace ji Dan iska kamal kai ware kanka kake a cikin jara babbun ai Ku duk mota data CE ta deboku

Lamido ne yace kunsan Allah mu ture batu zoleya kawai dai mu jarabarmu ake gani da yake mu bama iya boyewa ko daurewa ya Nuna hassan da Yusuf yace wlh kunga wadannan muna fukan masu qiffqifta idanu sun fimu 

Yusuf ya kai mai bugu ya kauce da sauri 

Jalal Na kai lamido abin kuma harda yar   Sherri ne

Da sauri ya kalli Yusuf yana nuna lips enshi yace ka Ganshi ko wlh zabar fitinarsa CE tasa baya taba bude idansa ya woresu ya kalli gari dan da zaran yaga mace  yake daburcewa yai ta rawan sanyi 


Cikin dry Habeeb yace kai lamido dama rawan sanyi da Yusuf ke yawan yi lkuta da dama ase abin ne ke motsowa?


Sosaima kuwa kaga yan qananan inda nunshin nan da baya budewa ya ga gari ko toh wlh Sha,awarsa Na tashi zakaga sun fiffito sunyi woye a take zakaga idan yayi jazawur leben bakinsa jajayennan sai kaga suna ta rawa kamar mai jin sanyi sai ya wani kamo lebenshi Na qasan ya rinqa tsotsa sai sunyi fari tas ya wani Sa hannushi ya damqe mararsa ya rinqa mammatse cinya yana hanata tasowa😝🙈ya rinqa rawar sanyi gaba dayansa ya rinka yiwa mutane barin baki sai kaji shi yana wani shiiiiiiiiiiii hahhhsh 

Jara bebbe kawai wai a hakan kuke cewa Yusuf Nada dauriya 

Duka Yusuf din ya kai mai tare da miqewa yana qoqarin shiga bedroom yana miqa yana mammah 


 Mujahedin da yanxu ya shigo yace wlh zancen ka gsky ne Dan yanxu miqar nan da yake abinne yake motsawa Dan an kira sunan mata kawai yanxu haka mgni zaije ya Sha.


Duk sukayi dry suna tafawa 

Ido lamido ya kashewa Yusuf yana kadai San ba qariya muke makaba ko😉

Hassan ne yace komai dai menene ai muna iya control din Sha awarmu bama danne yayana mutane kam 😡

Kamal ne yace aiko

 kwa kashe kanku wataran 

Habeeb yace bar yan rainin wayo ai shikam 

Hassan yasan azabar daya Sha da yar Fulani ta qauracemai 

Jalal yayi dry yace kasan wai su sun iya fulaku 

Kamal yace wayace ma ana fulaku kan abinnan😉 

Hussain ya kalli Ahmad yace wannan kuma da ya wani tsamure zai iya tsinana wani abin kirkin ko dai sai mun kawo kafi doki mun baka kasha duk suka kece da dry


Cikin sanyin yanayinshi yace  kai dai Mayya kawo idanka kaina ni ko Na gazama qanwatace zatayi haquri dani 

kamal yace ka banu gwara ka miqe  Dan wlh mata basa son lusarin namiji😝

Yusuf ne ya katse musu dry da suke tayi Dan ceqiyanci

Kai biyaye INA mgnina ? Adam yace tab yoh ni nasan inda ka ajiye abinka 

 cikin hada fuska

 yace ka Sani kam kasani sarai ai dama Kaine kullum kake kwashemin abinna kana zubar

Dry sosai modibbo yakeyi yana nuna idan Yusuf da suka firfito sai zaresu yakeyi sai wani sheqi sukeyi da qwalla tab aciki kamar mai shirin yin kuka 

Kamal yace Abun ya motso  kenan 

Lamido yace in ka masu in dauki maka amariyar ka dan mu kam baqin sauqine zamu Baku fili😜😀😀😉haka dai sukayi ta yiwa juna  Tsiya 


Bayan an gama biki duk baqi sun kokkoma sai yan kadan da suka rege



GIDAJEN AMARE


Masoyana masu kira da masu gaisuwa ta chart INA godiya da kulawarku kuma INA jin dadin yadda kuke ban qarfin guiwa😍😘👍🏻

 

By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

Mi,WASMITI page

3⃣6⃣to4⃣0⃣ 

Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

        Gidan Adam 

A hankali yayi SLM tare da shiga cikin bedroom din nasu 

Cikin nishadi yayi ajiyar hrt Dan wani sanyi da qamshi da yaji yana ratsa gabban jikinsa 

Daki kam ya hadu iya haduwa 

Amariya Amira ce ke zaune kan gadon tana sanye da kaya Na alfarma sai qelli goshi takeyi cikin takun shauqi 

Ya isa gareta 

Hannu ya miqa mata alamar ta kamashi zai jawota ta sauqo 

 

Cikin jin kunyar da bata tabajin tana yiwa Dan uwannata ba yayanta kuma mijinta a yau 


Cikin Yanayin mmk yace meerah yau kuma kunyata kikeji  ya Dan ronqofo ya jawota tsaye suna fuskantar juna ya Sa hannushi ya tallabo fuskarta ya Dan zuba mata ido cikin wata iriyar muryan da bata tabajin ya Adam din nata dashi ba sai yau 

Yace  

Plx meerah kar kibari wata baquwar kunya ta cutadar damu 

Shiru dai tayi

Dan haka kawai ta sinci kanta da jin kunyarshi

Kinji ko meerah ?

Kai ta gyada alamar eh 

Hannuta ya jaa ya kaita bakin  qofar toilet 

Yace shiga kiyi alwala 

Toh tacemai gamida shigewa ciki 

Shima alwalan yaje yayi a gefenshi 

Yana shiga 

Ya sameta a zaune 

Darduwa ya shimfi da musu 

Sukayi nafila raka,a 2 

Bayan yayita jero musu addu,oi 

Suka shafa 

Zata tashi ya jawota ta zauna lader da ya shigo da ita ya bude

Gaseshiyar kazace mai Dan romo 2 sai juice kala 2 masu sanyi kai tsaye shi ya rinqa bata a baki cikin kuya take karba  haka dai sukaci sukasha


11:15 pm  Adam ya jawo amariyarsa cikinsa gami da kashe hasken dakin 

Cikin Dan jin tsoro ta fara Dan tureshi 

A hankali ya kai bakinshi dai 2 kan kunneta 

Yana furta mata zantuka masu kama da darasi mai wuyar fahimta nan

Kuma hannushi ya fara isar da saqonshi gareta 

Sosai ta tsorita jin yadda yayan nata ya rikice mata a yau din 

Hannushi ya zira cikin rigar jikinta har ixuwa qirjinta 

Firgita tayi sosai jin yada yake sarrafata 

Cikin muryar tsoro da qoqarin yin kuka ta kamo hannushi tana kayi haquri

Wlh tsoro nakeji ya Adam Na tuba 


Kai ya rinqa girgiza mata yana mgn cikin wuya da tsananin buqatuwa 

Kiyi haquri meerah bazan iyaba 

Wlh bazan iya jure wannan Daren ya kau cemin ba 

a haka dai cikin hikima ya rabata da budurcinta


Garfe 3 dai 2 Adam ya samu nitsuwa yayinda itako Amira tasha Kukanta shiko yayi ta faman lallashi da gyar ya samu Ya lallabata tayi wonka bayan ya Dan gasa mata jikin ta 

Anan suka samu sukayi bacci mai dadi da nishadi 


       Gidan Ahmad 


Tinda ya shigo gidan  ya wuce dakinshi 

Kan gado ya fada cikin 

Kunci zuciya da zafin

Rayuwa 

A hankali yake furta 

Ase dama haka rayuwa zata kasan cemin ase wannan Daren da nake tayiwa tanadi da shiryawa da burin Mallakar Aysha ase hakan bazai kasan cemin ba 

Sannan qaddara ta hadani da Maryam yar uwata a matsayin mata 

Wani daci yaji yana tuqarsa daga cikin maqoshinsa 

Cikin murya mai rauni yace 

Am so sorry 

My Aysha 

Ki gafarceni qanwata 

Dana San bazan aurekiba da bazan dasa miki sona a ziciyarki ba 

Wlh da nasani da nabar abin a zuciyata ni 

Kadai

Da ko ba komai ban cutar da keba 

Cikin zafin rayuwa

Da tajuya mai baya 

Yake ta fadin 

Wlh da inada yadda zanyi 

In sawa biyaye Na sonki a ranshi  da Na saka mishi Dan da koba komai zai kulammin dake

Amman ban da damar Sa so ko qiyeyyah a zuciyar Dan Adam 

Zogi sosai zuciyarsa ke yi hannushi ya saka ya danni kan qahon zuciyarsa 

Yadda  gaba daya jikin shi ya dauki bari ga wani zufa da yake ta keto mai tako ina 

Sosai yake jin azabar ciwon zuciya cikin rawan baki ya rinqa surutai masu ban tausayi kusan a haka ya kwana sai sunan Aysha da yaketa kira yana ki gafarceni 


Amariya Maryam kuma dama tayi zaton haka 

Dan tunda aka hadata da ya Ahmad Wanda tasan ba itace burin ranshiba tabbas ta sawa ranta wannan Abu zai iya faruwa

Shiyasa tunda taga  12 yayi bata ganshiba ga soron da takeji gida shiru sai ita kafai

a haka ta fito parlor cak ta tsaya 

Jin sautin kukan da Ahmad din keyi da sabbatun da yakeyi cikin  raunin murya da halin quncin rayuwa

A hankali ta qarisa baking qofar 

Lkci daya kuma tausayin Dan uwan NATA kuma mijinta  ya rinqa ratsa qahon zuciryata

Nan ta zame a wurin ta rinqa kuka mai tsuma rai  a haka suka kwana shi yana ciki yana nashi kukan itako tana baqin qofarsa 


A haka kuma rayuwa taci gaba da Tafiya agaresu 



Yau kwana 7 kenan da yin bikin 


Kuma lamido shi basu komaba 

Shiyasa 

Yusuf ke Dan jin dama2 tabbas yaji kewar yam uwana Amman lamido Na debe mai kewa sosai  

Suma kuma su Ahmad sukan xo suyita hira Adam ne ma bai cika zuwaba da yake shi rayuwar aurenshi dadine ke tafiya


    Yau asabar kuma yau su lamido zasu komai Yola shi da innarshi 

Tafiyar yamma zasuyi 

Shiyasa basu tfi ba har yanzu


Bayan sunyi sallan azafarne suna dawowa gida 

Lamido ya kalli Yusuf yace kai bazanfa koma banje gidan su Ahmad ba 

Toh me nawa da kake gaya min zan hanaka zuwa ne ?


Banson iskancifa Yusuf ai dai ka Sani tare zamuje kam ko 


A a ni kam bazaniba

 

Haba Yusuf gidan su Ahmad din kake cewa bazaka jeba ka tunafa kasan ko suwaye Ahmad  dinka nefa biyayenka da Adam dinka yan uwanka abokanka aminan ka shin ko ka manta matsayinsune a gareka

Yusuf ko zarginsu Ahmad kake da laifin da ba nasu ba 

Hannun shi ya kamo cikin tuna sarwa yace Yusuf ka dawo cikin hayyacinka ..

Kai ya jinjina gami da cije lips enshi ya kalli lamidon yace 

Hakalina tashi yakeyi ako da yaushe in naga halin da Ahmad ke ciki kaga fa lkci daya yadda biyayena ya fita hayyacinsa gaba daya ya birkice farin ciki ya bar rayuwarsa 

Toh in banda abinda Yusuf ai yanxu ya kamata ka nunawa Dan uwanka kulawa 

 

Kai ya dan jinjina yace 

Toh shi kenan mutafi 

Gidan Adam suka fara zuwa 

A parlo suka samesu  Adam Na zaune kan 3str Amira ko Na konce tayi pillow da cinyarsa suna hira jin SLM marsu yasa Adam miqewa 

Da sauri ya bude musu qofa suna ganin juna Adam ya miqawa Lamidi hannu cikin wasa suka tafa lamido ya kalleshi da kyau yace kaji Dan duniya kana Sha,aninka shiyasa ka wani sheremu yau kwana nawa bakaje gidaba 

Kai 

on top banson Sherri shekaran jiyan cammafa naje ko biyaye ai ka tuna

 ya fada yana kallon fuskar Yusuf din harara Yusuf din ya watsa masa gamida cewa toh ni dai ka kama kanka Dan wlh naga alama zaka jamana raini gun yarinyar nan 


Yoh raini kuma Na nawa tunda ta ga gadon baccinsa ta kuma yiwa mararsa kallon tsaf ai raini ya qare anan cewar lamido 

Kenan 

Adam yace bar Dan iska shima zai worene wannan wuri in kasan dadin da ya qunsa ai bakayi taurin kaiba dry sosai lamido yayi 

Shi kuma cikin ta kaici yace wallah tallahi kunji Na muku rantsuwar musulmi ko toh wlh ni kam har a bad a bani ba Aysha kam kodako mata sun qare a duniya koda zan rasa rai nane

 Adam ya kalleshi cikin mmk yace ni kuma Na tabbatar kana tare da wahala wotarana 

Dai2 lkcin suka zazzauna kan kujera cikin jin kunya Amira ta kawo musu dirings masu sanyi ta gaidasu ganin yadda hamma  Yusuf din ya murtuqe fuska yasa ta wuce kitchen dinta taci gaba da aikinta

 Basu dade ba Yusuf ya miqe yace su tafi gidan Ahmad 


A baking gate sukayi qaro dashi yana kokarin shiga mota cikin tsoro da firgici da tsananin kaduwa suka isa gun shi 

da sauri Yusuf ya kamo hannushi.......


FAHIMTARWA 

Da yawa suna min qorafin basa fahimtar me sunan littafinnan  yake nufi sabida ganin sunan da yaren fullancine ana yawan cemin menene ma,anar MI,WASMITI toh 

Manar mi wasmiti dai yana nufin 

NAYI NADAMA

Fatan masu karatu kun gane sunan novel din nayi Nadama 

Kuma insha Allahu zanci gaba da hada sunan da hausan 

Ina godiya da kulawarku 


KINA RAINA  UMMI Garkuwa marubuciyar Jennifer fatan alkhairi a gareni 


Gaisuwa ga dukkan marubutanmu inai mana fatan alkhairi 


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


NAYI NADANA

MI,WASMITI page 4⃣1⃣to4⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Hannunsa Ya riqe cikin mmk da kdma da tsabar firgici cikin kaduwa yace 

Biyaye meke damunka ?

Baka da lfy ko?

Shiyasa yau kwana 2 bakaje gidaba ko ? 


Shiru dai baiyi mgn ba 

Cikin damuwa yace 

Haba Ahmad ya ina mgn kayi shiru 

Ji yadda gaba daya ka rame 

Ase dama shiyasa kake yawan Sa manyan kaya 

Dan ka boye yadda ka sauyane ? 


Cikin yanayin shi Na sanyin hali da kawaici da haquri yayi murmushi Garfin hali da qoqarin boye halin da yake ciki 

Yace 

Ni wlh matsala ta da kai  kenan  saurin 

rudewa jifa yadda ka wani gigice kana ta jeromin 

Tabbayoyi 

Toh wacce tabbaya daya nasan 

Zan amsa maka 

Adam ne yace ka gaya mana gsky ya fada  cikin son gane me Ahmad din ke son  boyewa musu

Dry yayi cikin qarfin hali yace 

Bani da wata matsala ni kam


Cikin kura masa ido Yusuf yace ka tabbata? 

Yes bani da matsala ya fada yana kamo hannun lamido 

Yace on top mu isa kunzo kun tsaidashi a  woje 

Yusuf ne ya kirashe biyaye 

Na,am ya amsa masa 

Yace juyo ka kalleni 

Cikin dryar tausayawa Kansu da Kansu yace anqi juyo wan 

Da sauri Yusuf ya Sha gaban shi yace nace ka kalli qoyar idana ka cemin baka da matsala 

Cikin sauri yayi gasa da kanshi 

Dan yasan muddin ya bar idon Yusuf cikin nasa toh zai gano halin da yake ciki 

Dan su tun suna yara sukan laqanci halin da Dan uwansu yake ta cikin qwayar idan juna koda ko ya boye a fuskarsa


Part dinshi ya nufa riqe da hannun  lamido 


Cikin karaya da yanayin cushewar tunani Yusuf ya kalli Adam cikin rawar murya yace biyaye inajin tsoro 

Wlh tsoro nakeji 

Adam kalli yadda Ahmad ya dawo 

Adam kasani Na Sani iyayenmu sun Sani su Kansu su  Bappa Yaya

Sun San cewa Ahmad Aysha yakeso 

Itace burin ranshi 

Sun kuwa San zai iya zaucewa in aka hanashi ita 

Adam meyasa 

Suke son 

Sabautamin rayur Dan uwana

Kanshi yake ta jijjigawa da juya idan shi yasa lips enshi Na qasa a baki ya ciza da qarfi 

Hawayen da suka cuko a idonsa yakeson su kwaranyo ko zai dainajin nauyin da ya danni qirjinshi

Amman ina abin yaqi 

Da qarfi ya riqe hannu Adam yace 

Biyaye ni 

Banajin kaina banajin Aysha 

Dan uwana nakeji 

Adam ni 

Yanxu Na gama tsara komai Na komawa cshool 

Ba Wanda zan gayawa sai kai da Ahmad

Dan banson su Abba su San zan tafi nafiso sai naje Na kirasu Na gaya musu 

Amman Adam kaga halin da Ahmad yake ciki 

Adam ko dai Na fasa tafiyar Nanne  

Adam in natafi Na bar biyaye da kai kadai zaka iya kula dashi 

Cikin rawan murya Adam 

Yace kaje insha Allahu ba komai yadda zaka barmu lfy haka zaka dawo ka samemu lfy

Duk kulan da kake tunanin zaka bawa Ahmad zan hada da nawa 

Cikin murmushi takaici yace 

Ya ja hannushi suka bi bayan su a parlo suka yada zaggo suna ta Dan taba hira

Har aka kira sallan LA asar Adam ne ya fara shiga yaje yayi alwala sai lamido yana fita yace 

Yusuf kuyi saurifa kunsan innah tanan ca tana jirana kuga dare yanayi 


Tare suka miqe Ahmad dinne ya fara shiga yayi alwalan sai Yusuf din ya shiga sauri sauri yayi ya fito 

Har yazo baking qofar fita 

Sai kuma ya dawo da sauri ganin abin mmk 

Da sauri ya fito parlon ya kira Ahmad din hannushi ya jawo har gaban gado ya kalleshi cikin 

Tuhuma yace 

Biyaye jinin menene wannan a kan shimfidarka har kan pillows dinka ? 

Shiru yayi 

Cikin kaduwa yace Ahmad tabbayarka fa nakeyi 


Cikin inda inda ya kama cewa A.a 

Ai dama

Damafa 

Biyaye ka Dane inda inda ka gayamin gsky 

Lamido ne ya katseshi da cewa wlh kai dai bakaji

Dadiba Yusuf

Ka fiye bincike da qididdigar mutane 

Kazo gidan sabbin amare Dan kaga jini a makwancinsu ka tsaya dogon bincike kai Amman dai anyi surkin banxa 

Cikin jin dadin zance Ahmad yace qyaleshi dai duk suka fita suna dry Amman banda Yusuf Dan shi ya zargu da jinnan da ya gani 

Har zasu fita Adam yace bamufa ga qauwar tamuba 


Ras Ahmad yaji gabansa ya fadi har sai da ya fafe qirjinshi danshi har ga Allah mantawa yakeyi da wata a cikin gidan 

Lkci daya kuma yaji kunya ta rufeshi ko ba komai Maryam bata cenceci haka daga gareshiba Dan ba laifinta bane


Muryar tane ta katseshi da tunanin da yakeyi 


Cikin Dan sakin fuska tace laa ya Adam Hamma Yusuf ya lamido sannuku da zuwa 

Da sauri ta nufi kitchen tana bari Na kawo muku abinci Yaya

Ta fada tana kallon fuskarAhmad din shi kuwa da sauri ya kauda ganinshi daga gareta Dan kunyarta yaji sosa

Yusuf ne yace a a Alhamdulillah mun gaisheku wucewa masallaci zamuyi


Cikin Dan tsoro tace  

Ayyah Hamma Yusuf da sauri haka 

Ko ruwan Baku shaba 

Toh mubar sallan kenan ya fada fuska a daure 😡

A ranshi kuma yace ba gashi ba har sun fara tsare mutane da raini 


Cikin sanyin murya tace A,a

Toh Ku gaida su Ummi 

Harara ya kuma watsa mata yace suwayen yan Aiken naki mu zaki aika 

Kai ta girgiza gudun kar ta kuma mgn ya zama laifi

A ranta tace shi kenan Aysha am ke kam kin kade zama da wannan masifeffen 

Tare suka fita 

Ahmad Na bayan su 

Har yazo baking qofar sai ya kuma komawa yazo dab da ita ya Sa hannushi ya tallabo fuskarta cikin rauni da 

sanyin murya yace 

Maryama kiyi haquri ki gafarceni 

Rau rau tayi da ido alamar kuka da sauri ya zaunar da ita kan kujera yace ki yafemin ba nufina kenan Na cuxguna miki ba kimin afuwa yake yar uwata 

Cikin sanyin murya tace 

Ni baka min komaiba ya Ahmad kuma ko ka minima Na yafe 


Cikin farin ciki ya subbaci goshinta ya 

fita yana cewa rabbi ya miki albarka 

Amin tace cikin jin dadin addu,arshi gareta


3:30 pm su inna sukayi sallama da su Ummi suka kama hanyar Yola sun tafi suna kewan juna 



Yau saura kwana 2 Yusuf ya bar  Nigeria


Da yamma su Abba da baba bello Na zaune a harabar gidan nasu Yusuf ne yashi cikin nitsuwa ya isa gunsu 

Cikin biyeyya yace sannuku da hutawa baba 

Abba yanxu naje hospital baka can anata nemenka kawai suna ganina suka tsareni 

Baba bello yace a to kace yau ka Sha aiki kenan 

ehh wlh baba har C,S nayiwa wata mata 


Ayyah me aka cire 

?

Da namiji  


Masha Allah rabbi ya raya


 amin yace 

Ya Dan kalli baba bello yace baba 

Yanxu zan wuce mambila Dan Na kwana biyu bamu hadu da Bappa Yaya ba 

toh yayi kyau ka gai dasu yaushe zaka dawo ?insha Allahu  Gobe  zan dawo 

Abba yace (Allah yare jam wartira on jam)

Allah ya kaika lafya ya dawo da ku lfy 


Ameen ya rabbi yace gamida miqewa ya je ya sallami su Ummi ya kama hanyarshi shi kadai 🚗


 Gembu Mambilah 


Garfe 6 dai2 ya isa farfajiyar gidan ba kowa sai  Dan hirarsu da yake juyowa daga cikin parlon baki ya Dan table gaida cewa badu da aiki sai surutu cikin gajiyar  hanya 

Ya bude Qofar kenan ita kuma tazo da Dan gudu gudun ta kawai sai ji yayi ta fada cikin girjinshi a take yaji jinin jikin shi ya dauke  duk yaji tsikar jikishi Na tashi qoqolwar shi tayi dip duk network dinshi ya dauke 

Cikin qarfin halin ya sunkuyar da kanshi Dan ganin wacce  wannan 

dai dai ya tabbatar ko bai ga wayeba yasan macece Dan yaji suka guda biyu a qirjinsa alamun qirjin macece ya have da NASA 

Ido ya zaro woje Dan mmk da ganin....


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA 

MI,WASMITI page 

4⃣4⃣to4⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Yarinyar da ya tsana kamar yadda ya tsani abinda zai cutar da biyayenshi 

Da sauri cikin jin haushin ta ya yarfa mata mari 

Cikin jin zafi da sauri cikin raxana ta dago 

 Sosai ta qara tsorita ganin fuskar da bata qaunar gani da sauri ta juya dafe da fuska 

Cikin zafi nama ya miqo hannu zai cabkota ya dirka mata Na jaki 

Sadiq dake gaban ta 

Yace kin banu 

Aysha kauce 

Da sauri ta ruga 

A guje bata tsaya ko inaba sai cikin dakin innayi kan gadon mai rumfanta ta dale tana mai kukan takaici 


A parlor kuma zama yayi bai kula kowa ba sai faman murtuqe fuska yake da huci 

Bappa Yaya ne ya Dan kalleshi da kyau a ransa yake mmkin halin irin Na Yusuf shi har abada ba,a gane far in cikinsa da baking cikinsa ko yaushe fuska ba walwalah 

Cikin kula yace 

Kai Dudabe  meke damunka kaketa huci 

Anyi din 

Toh yau kuma da bala,i kazo kenan?


Ehh da  bala,i nazo 

yanxu kai kuma kana da bakin mgn ne 

Bala,I da fitina ya wuce wanda ka janyo mana

An janyo din nace an janyo ko 

Aikin kawai Dan kaga ina binka ina sonka 

Shine kake son ka samin hawan jini


Ka sawa kanka dai 

Innace ta kalleshi cikin tsokana tace ayagi sarkin fada ka iso har ka fara daga shiga 

Da dukan matarka kayi slm 

Sannan ka sauqo kan Bappa an da kuma kanwa zaka kuma hawa


Kanki zan hau nai ta surface miki bala,i matuqar kika qara kiran waccar yar yarinyar kuma muna fuka a matsayin matata


Innayi ce tace toh dibino gwara muyi axumin mgn in ba so muke a hanamu baccin dare da sababiba 



Oho dai can ta matse muku ya fada gami da daga kafada 

Bappa Yaya ne yace 

Toh tashi mu tfi 

Masallahci Dudabe am 

Bazan je da kaiba haka kawai kai ta wani kirana 'Dudabe 

Nacema bana so Amman taurin kai da son ka konamin rai ya hana ka bari 😡


A haka dai sukaje sukayi sallah 

Basu dawoba sai da sukayi insha

A parlor suke ta Dan hira yanxu ya Dan sauqo 

Cikin kula ya kalli kakan nashi 

Yace Bappa Yaya jibi in Allah ya kaimu zan koma wurin karatuna 

Dan an nememu kwanannan 

Cikin Dan jin sanyi yace 

Ayyah dudabe zaka tafi kuma sai mai Nisan kwana 

Ko zaka dawo ka samemu ko kuma shike nan an rabu 

Duk da halin irin Na Yusuf yana qaunar kakannishi sosai a ranshi yana sonsu fiye da zaton mutum

Cikin qarfin hali yace ba komai kakana zan dawo Na samemu lfy 

Innayi tace hmm Yusuf am ai dolene watara kam ka dawo ka samu bamu kan doron qasa 😱

hannun ta ya kama ya hada Dana inna yace insha Allah ba komai 


Suna cikin hiran Bappa Yaya ya miqawa Yusuf din phone dinshi yace hingo kamo min babanku 

Da sauri ya kalleshi cikin tuhuma yace 

Me zaka cemai 

Kafasan ni bansan gulma 

Dan basu San jibi zan komaba Na kuwa sanka da barin zance yanxu zaka shafa musu zancen

Cikin mmk da Al,ajab yake kallonshi 

A ranshi yake cewa wato so yake ya zulle ya bar matar shi a nan toh lallaiko yaro shirinka yayi nitsa 

A daqile yace 

Ina mgn kayi banza dani 

A Dan fir ya dawo daga nunanin da ya tfi 

Dry yayi irin ta yaro man kaza kenan 

A fili kuma cewa yayi toh Na FASA kiranma ba shike nanba?

 ehh gwara kam 

Ya fadi tare da miqewa ya nufi dakin innayi yana innayi zo kiban tea 

Toh tace gamida bin bayan shi 


Suna shiga ya hau kan mairumfanta ya kishin qida yana kallon rumfar gadon da yasha kolliya a ranshi yake cewa tabbas wannan gado yayi  a rayuwarta kuma insha Allah sai Na shigarda gadonnan cikin tarihin rayuwa

Haka kawai shi kam yake son gadon kakar tasa  haka kawai yake jin nishadi in ya hau gadon  da farin ciki 


Innayi CE ta katsemai 🤔da yakeyi tana toh ga shayin ko a kan gadon zakasha ne?


A a zan sauqo mana Amman ajiyeshi ya Dan huce 

Toh tace gami da dire cup din a qasa 


Itako Aysha tunda ta shigo ta.kwanta kan gadon

tana kukan marinta da yayi a.haka bacci ya saceta 

Baccinta take cikin jin dadin gadon 

Shiko Sam bai lura da ita a kan gadonba

Shiyasa yayi kwanciyarsa


Can cikin bacci ta Dan fara juyi a hankali ta daqo hannuta daya cikin sanyin baccin ta dire hannun kan qirjinshi 

Lkci daya kuma ta mirgino da qafarta ta daura kan ququnshi cikin sekon 10  duk ta kanainayeshi 


Cikin firgita ya bude idan shi da sauri ya tashi ya zauna har jikin shi Na bari 

Cikin takaicin gani wacece ya 

Daga hannushi sai da ya dubu kan fuskarta ya watsa mata maruka har 3  ajere cikin kidima da firgici ta saki kuka mai qarfin gami da bin bayan shi ta diro daga kan gadon 

Cikin kuka dataje baking qofar ta juyo ta kalleshi cikin tsana tace mugu azzalumi Allah ya isana wlh bazan yafe maka ba ko qabarinka naci da wuta

 

😳😡ya zaro mata cikin zafin nama ya diro daga kan gadon yana fadin ke 👉🏻ni kike zagi ?

Ehh din an zageka azzalumi 

Aiko cikin zalumcin ya nufi kanta Dan yana iya babbalata in ya kamata ganin yadda ya nufuta kamar wani ma yunwacin zaki yasa ta arta a guje 🏃🏻‍♀cikin 

Zafin nama ya rufamata baya


 bata tsaya ko inaba sai cikin dakin Bappa Yaya 

Da sauri ya riqota yana ke Ayshatu lfy kuwa ke da waye

Ita dai ihu take da.iya qarfinta tana 

Hamma Yusuf ne Bappa Yaya wlh ka tare shi ka Sani baida imani  zai kasheni 

Toh me kika masa 

Wlh.ni ban masa komaiba shine ya sameni INA baccina kawai yakama dirkata

Shi dai Yusuf huci kawai yake Yayea qoqarin fixgota 

Cikin tsawa kakan nasu ya jawata ya turata bayanshi yace je kiyi zamanki kai kuma ficemin a daki ko yanxunnan Na kira ubanka nace kazo dukana 


😡👉🏻baki ya ciza gamida kada kai yace wlh zaki shiga hannu Na kuma zaki gane kurenki yayi woje yanata huci


Bayan fitashi ne ya miqowa Aysha woya yace kamo min bello 

Karba tayi ta ki rasa sai da ya daga sannnan ta miqa mai ta shige toilet 


bayan sun gaisa

Cikin rada rada yace kai bello kasan Dudabe nata shirin tfy jibi jibinnan ko 

Ehh yace mai Na Sani Amman shi yana tsamman ban saniba Adam ya zo ya gayamin 

Toh batun matarsa fa ?

Ehh ai tare zasu tfi ko baya so Dan yanxu haka Na gama mata shirin tafiyarta kab

Dry yayi cikin jin dadi yace yauwa Allah ya muku albarka daku da zuryarku baki daya

Amin ya rabbi ya fada cikin jin dadi

 

Sannan yace toh ka kirashi gobe da safe kace ya taho da ita Dan in Nina fada bazai yardaba 

Toh shi kenan Bappa 

A haka sukayi SLM ya kashe woya yana dryar cin nasara 


Da safe bayan ya gama shirinsa ya shigo ya ya rinqa binsu innayi ko wace har dakinta yana basu kudi da yi musu slm yana ce musu Allah ya sadamu da alkhairi

Duk sai yaji ba dadi

 

A farfajiyar gidan yaga Sadiq ya bude but din motarshi yana zuba kaya 

Ga Aysha kuma a bayan Bappa Yaya tana kuka 

Cikin tsoro take cewa wlh zai dakeni ni bazan tafi da shiba 

Cikin mmk da take baki yace ke da Allah can ki rufe mana baki nima motata ba ta daukar mahaukata bane 

Kai Sadiq 

Rufemin mota Wanda ya kawoki yazo ya maidake ai ni ba bawan kubane 

Cikin isa Bappa Yaya yace toh ai bani nace Ku tafi taraba ubankune ya fada kuma tunda kace kai kafi qarfi bari Na gaya mishi

Miqawa Sadiq woyar yayi yana maza kamomin bello 

karba yayi ya kirashi bugu daya ya daga ko slmarsa bai amsaba yace toh bello ga isheshshen Dan naku yace bazai taho da itaba 

Dry ya danyi Dan yasan anacan ana shan rgima tsakaninmu Yusuf da mutanen gidan baki daya.

 katse kiran yayi ya kira Yusuf din 

Bugu daya ya daga cikin takaici Dan yasan mgnar da zai mai 

Toh kawai yace 

Ya fito cikin motar woyar Na kunneshi daga dukkan alamu mgn yake mishi har yanxu 

Da garfi ya fizgo hannuta da ita da jakar tata gaba daya ya cillasu a gaban motar gamida maida marfin gib ya rufe cikin fushi ya shiga ma zaunin   direba ya figi motar da qarfin duk abinnan da yake baba bello Na jadda da mai Yusuf karfa kasa yarinyar nan kuka


 cikin takaicin ansashi daukar ta a dole yace 

Ni ba ruwan Na da itafa baba,,,,,,,, cikin mota ko a zuciye ya dago,,,,,,,,


Ina gaida dukkan ma karanta novel dinnan inai mana fatan alkhairi



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA 

MI,WASMITI page 4⃣6⃣to4⃣8⃣Na

Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Jakarta ya danna mata kan cinyarta cikin mugunta

Daga nan bai sake kallon ko gefen da taken ba 

Titi ya zubawa ido 

Yanata sharara gudu

Kafin 9:11 Am 

Sun isa 


Kashe gari 

Tun da safe 

Aysha ke kuka wuy wuy da hawaye da suka kasa tsayuwa 

Saka makon bayanin da Abba ya mata Na tafiyarta tare da Hamma Yusuf din 

Kuka take sosai tana pita parlorn Abban nata kitchen ta nufa 

Ummi dake qoqarin hada musu breakfast  ta fito da sauri gami da kama hannuta cikin tausaya mata da cikar takaici 

Dan Sam Ummi bata son abin da zai taba mata autar  tannan 

Daki ta wuce da ita kan gado ta zauna gamida jawota 

Cikin kuka ita kuma ta zame ta zuba guiwowinta a kasa ta kifa kanta kan cinyar umminta cikin tsananin kuka tace 

Shi kenan Ummi nikam Na shiga ukuna Ummina

 cikin Neman alfarma tacigaba da cewa Dan Allah Ummi Ku gafarceni Na tuba kumin afuwa dan son Annabinmu Dan Allah kar kubari ace tare zamu tafi da Hamma Yusuf wlh tsoronshi nakeji Ummi zai kashe miki nifa

Haka tai ta kuka tana surutai 

Ummi ta dago fuskarta tace kalleni nan Aysha 

Na miki alqawari 

Indai Na isa 

Da Hamma ku

To insha Allah bazai cutar da keba 

Kisa ido kigani ni nasan iya koki da dokokin da zan bashi a kanki 

Haka dai tai ta bata baki da kontar matada hankali

Dama tuni an qarisa mata shirinta


Ahmad kuma da Adam tun da sukayi sallan asuba suka taho gida Dan yiwa biyayensu rakiya zuwa airport 

Suna tare a farfajiyar yar gidan bayan an gama dura jakukkunansu a but 


Cikin nitsuwa 

Yusuf yaje gaban baba bello ya Dan duqa gamida cire hular kansa cikin sanyin murya 


yace toh baba zan tafi fatan Allah ya qaddara saduwarmu kan alkhairi ya Dan yi shiru kadan ya Dan kuma dago kanshi cikin rawan murya yace Ku gafarceni baba in akwai abin da Na muku cikin rashin Sani 


A hankali baba bello ya dafa kanshi cikin son Dan Dan uwanbnashi yace baka mana komai ba Yusuf Allah ya maka albarka Yusuf mu iyayenku

 xuqatanmu baza su iya yin fushi da kuba duk da kaso ka boye min tafiyar Amman ya zama dole nasan duk woni motsinaka shiyasa tun jiya Na sanar da kai munSan da batun tafiyar taka Dan kar da safe ka shirya ka tafi ba tare da ka nemi afuwar iyayenka da sanya albarkan suba 

Allah yayima albarka 

Hannun shi ya Sara kan hannu baba bello da ke cikin sumar kanshi yace 

Amin ya rabbi


A hankali ya taka yaje 

Gaba mahaifinshi 

Cikin biyeyya ya duqa gaban shi ya dago ya kalli ma haifin nashi yace 

Abba ka gafarceni ka San yamin albarka ko zan samu sauqi cikin rayuwata 

Ya kuma Dan duqar da kanshi Yagi gaba da cewa yau zan tafi ina mana fatan saduwa cikin alkhairi


Kai Abban ya jinjina yace ba komai Yusuf Allah ya muku albarka baki dayanku da kai da yan uwanka INA maka fatan alkhairi cikin karatun ka 

Amin yace cikin jin dadi

Haka yaje gaban Nenne ita ta samai albarka 

A gaban Ummi ya tsaya   cikin mmk ganin tana riqe da hannun Aysha ita kuma sai kuka take fuskarnan duk tayi jazur da ita 

Ba tare da ya qara kallon inda Ayshan takeba yace toh Ummi ni kam zan tafi sai kuma Allah ya gaddara saduwarmu 

Toh Allah ya kaiku lfy ya kuma  dawo daku lfy 

Amin yace cikin rashin gane me zancen Ummi yake nufi Allah ya kaimu lfy to shi da waye kenan 

Cikin ransa kuma yace toh me ruwanka kai da zaka bar musu qasar 

Cikin Dan sassarfa ya qarisa gun Adam rungume juna sukayi cikin qaunar juna 

Adam ya Dan kai bakinshi dai2  kunneshi cikin sanyin jiki yace 

Zamuyi missing dinka biyaye 

A hankali yace insha Allah kamar yau zan dawo muci gaba da rayuwar mu mu 3 dinmu 

Har yanxu suna ruqqume da juna cikin jadda dawa Yusuf ya Dan bubbugi bayan Adam yace 

Adam nabar amanar Ahmad dinmu a hannuka Dan Allah ka kukan mana dashi ka Samar mai farinciki insha Allah nima inna isa zan aiwatar da aikin ummra zan roqi mahaliccinmu da ya cikawa Dan uwanmu farin cikinsa 

Cikin qarfin hali Adam yace Na karbi wannan amanar 

A haka ya sakeshi tare suka nufi gun da Ahmad din yake tsaye yana jingine da jikin mota Anuty Sadiya Na gefebshi wanda yanxu kenan isowarta


Ya

Isa gaban shi kenan Abba ya iso riqe da hannu Aysha cikin muryar umurni ya kamo hannu Yusuf din ya damqa mai annum Aysha cikin nasa ya hada ya rumtsesu 

Cikin mmk ya dago ya zubawa Abba Ido cikin Ido sukayi 

Cikin kaduwa ya bude baki zaiyi mgn 

Da sauri Abba ya dakatar dashi dacewa 

Bana son jin komai daga gareka Yusuf a yanxu haka umurni nake baka kai tsaye ka kama hannun matarka tare zaku tafi wannan umurnine kuma kab mun gama yanke wannan hukuncin 


Cikin razani da kidima ya maida dubanshi kan baba bello da alamun tabbaya 

Kai ya jinjina mai cikin alamun yes umurnine

 Ummi ya kuma kallah cikin daure fuska tamai nuni da amanace 


Cikin tsananin bugawar qirji ya maida dubanshi ga Ahmad dake gaban shi da ya zama tamkar an dasashi 

Girjinshi ke duka 3 3 a take zufa ta fara keti mai tabbas yasan da tfyar Yusuf Amman baiyi tunanin za a hadashi da Aysha ba 

Cikin sauri ya dawo kanshi ya kalli fuskar Aysha Ido cikin Ido sukayi cikin wata iriyar narkekkiyar murya ta saki kuka mai tsuma xuciyar mai sauraro

Kuka take tana wayyo ya Ahmad dina shike nan kun rabani da ya Ahmad dina 

Cikin azama ta fizge hannuta daga cikin hannu Yusuf din da ya zama tamkar ruwan ya cinyeshi 

Da qarfin ta fada qirjin  Ahmad din ta Sa hannuta ta qaqumishi ta mannashi da qirjinta tamkar zasu chige cikin juna 

Gaba daya shiki kam ya zama tamkar takarda jinshi yake a tsakiya shi ba sama ba shi ba qasaba tabbas badan a jingine yake da jikin motoba da tuni sun kai qasa

Bugun zuciyarsa kuwa tamkar zata balla girjinsa ta fito woje qoqol warsa ko gaba daya ta cushe mai ji yake kamar zai zauce 

Allah sarki Ahmad damo sarkin haquri 

A hakan yayi murmushin qarfin hali yasa hannushi ya dagota cikin ciccijewar voice yace Aysha ai tafi ya ba mutuwa bace koba  Dade ko banjima zaki damo ki samemu 

Kuma muma zamuna kawo muku ziyara 

Ita dai kuka take harkamar zata shide 

Hannuta ya kamo ya miqawa Yusuf cikin qarfin hali da juriya yayi Dan murmushi yace 

Biyaye ko zaka iya riqe wannan amanar da zan baka cikin takun jarumta ya matso gareshi yace 

Yusuf bazan taba gane kana so naba sai ka tayani son abinda nakeso fiye da kaina

Dry ya danyi kuma cikin dacin rayuwa yace INA nufin Aysha kuma INA nufin so Na Dan uwanta ka

Cikin mmk Yusuf ya zuba mai I do shi tunda suke da Ahmad bai taba kiran shi da woni sunan da ya wuce biyayeba Amman yau ya kirashi da yusuf kenan yana nufin amanar dai yake bashi da gsk


Da qarfi ya jawoshi ya fada jikin shi runqume juna sukayi kamar zasu shige jikin juna 

Cikin rada yace Ahmad nayima alqawari zan dawoma da farin cikinka 

Cikin juya kai yace Na yarda Amman in kasa Aysha farin ciki ne koda INA cikin qabarina zanyi farin ciki biyaye am

Da sauri cikin razani😱 Yusuf yasa hannu ya rufe mai baki cikin  firgici ya rinqa ja da baya  yana fadin a a 

A a kam 

Ahmad zamu rayuwa tare kuma 

Zamu mutum tare 


Shiko Ahmad Abba ne yazo ya jashi sukayi cikin gida yana juyawa yana kallon Yusuf dinncikin sanyi ya daga mai hannu tare da furta mai zanyi kewarka Dan uwana 

Usman ko da Rabi,u gaba daya jikin su yayi sanyi 

Abdul ka mai saurin kuka tuni yake ta sharbar kuka


Baba bello da Adam ne  kadai suka yi masu  rekeyi 

Basu dawoba har saida jirginsu ya tashi 


    Allah sarki Ahmad ko ya rayuwa zata kasan CE mai ne ?

Abinda masu karatu suka rinqa kirana suna tabbaya ta kenan ko ya Yusuf zai yi da amanar da aka bashi ?  Duk dai am soshinku Na gaba kunbiyoni dai a hankali 


Fatan alkhairi ga dukkan daukacin alummar musulmai 

Inai mana barka da jumma,a



Dan jin ra ayinku masu karatu qofar a bude take da shawarwarinku ina alfahari daku 



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

MI,WASMITI.. page 4⃣9⃣to5⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Maryam kam tun ran dasu Hamma Yusuf suka zo musu ziyara 

Suka fita tare da ya Ahmad har yau bata kuma sashi a idonta ba 

Haka kuwa rayuwa ke tafiyar musu kullum dare 

Ahmad zaiyi ta kukan zuci da zantuka cikin tsananin quncin rayuwa

 Haka kuwa sukaci gaba da rayuwa 


Sai dai al,amarin Na yau din ya firgita 

Maryam sosai 

Misalin 

Garfe 8:30 Pm 

Maryam Na cikin kitchen tana Dan tafasa indomi  

Dan tunda gari ya waye batasa  komai a bakinta ba 


Daga cikin kitchen din taji sautin da ta saba ji matuqar dare yayi 

Cikin fargaba da tausayawa Dan uwan nata 

Ta fito ta nufu qofar dakinshi 

 A hankali ta zame a baking qofar 


Cikin fitar hayyaci take jin zantukan da ya Ahmad din yakeyi 

Cikin kuka yake ta nanata innalillahi wa,inna ilaahi raji,un 

Cikin muryar kuka sosai kamar yaro 

Yake cewa ya Ubungijina ka kawo min mafita Allah Na ka dubeni da idon Rahama rabbi ka bani ikon cinye wannan jarrabawar da ka jarab ceni da ita yaci gaba da fadin

Woyyo Allah 

Wayyo yar uwata Aysha ko cikin wanne hali zaki kasance 

Allah sarki Dan uwana biyaye Na kamin adalci ka luranmi da burin raina 

Ki gafarceni Yar uwata Na cutar da zuciyarki 


Cikin tsananin kuka yaci gaba da cewa 

Ya Allah menayi gareka ka hukuntani da wannan baqin cikin rayuwa ya ugaban gijina kowa Na cikin farin ciki sai ni zuciyata ke suyuwa

 

Ya Allah ka jibanci lamuranna 


Kukan da yakeyi ya sata kuka sosai tun tanayi qasa 2 cikin sheshsheqa har kukan yaci qarfin ta ya kufce mata 


Can cikin kukan tajishi cikin rawar murya yana 

Astaqafirillah  Astaqafirilah 

Haka yayi ta Nana tawa  har zuwa woni Dan lokaci can kuma tajishi cikin kuka mai tsananin da alamar toshewar numfashi

Yana fadin ya Allah kai kaso ka ganni a haka ya ubangijina kai kafini sanin matsala ta  ya Allah ka karemin imanina ya Allah ka kawo min sauqi tako wacce hanya  

Cikin Jan numfashi yace koda ajalinane matuqar dai shine waraka ga rayuwata Allah ka bani Sa,ar tafiya kawai 

Ya Allah ka gafar tamin kura  kuraina Allah ka bani ikon sauqi haqqin matata maryama da ya rataya a wuyana 

Yana cikin haka

Wani irin tari mai garfi ya sarqa fe mai wuya 


Trin yake yana fadin ase dama bazan rayu dakeba Aysha 

Ayyah yar uwata ko zaki gafar tamin nan kuma tari ya rufeshi mgnar ta tsaya sai tarin da yakeyi cikin jin daukewar numfashi ya rinqa zagaya cikin dakin kamar mai yin dawafi



Cikin tsananin kuka da firgita da fitar hankali

Maryam ta zame a baking qofar ta konta kuka takeyi sosai 

Kukan takeyi irin kukan da Dan Adam zai iya suma da kaji kukan kasan bata cikin hayyacinta 

Qofar take bugawa da qarfin cikin rawar murya

Take ta kwada mai kira tana 

Ya Ahmad

Zo ka bude min qofar ya Ahmad Ka budemin wayyo Allah Na Dan uwana wayyo Abba Na wayyo Nenne na


kuka take sosai tana buge buge kamar ta bebbiya tana ya Ahmad ka bude dan Allah kazo ka budemin qofar


Cikin rike cewar ya rinqa salati yana lalabu qofar Dan Sam idonshi bai gani da gyar yake furta 


Ina kike Maryama ban gankiba Na rasa qofar 

Ita dai kukan takeyi tana buga qofar da iya qarfin ta 

Da gyar ya samu ya lalubo qofar ya bude 

Yana budewa yaji ta


 konce a qasa  tanata kuka mai qona zuciya 


Da sauri ya durqusa guywa bibbiyu hannushi ya Sa ya kamata 

Yana fadin 

Maryama kiyi shiru kiyi haquri zo ki fadamin waya taba min ke

 ita dai kukan take da cure cure tana tuttureshi gashi da iya qarfin ta take kukan a nata tunanin tanayi da qarfine Dan a kawo mata dauki


Da gyar ya tattaro iya sauran qarfin shi ya matseta a cikin qirjinshi 

Amman Sam ta kasa tsaida kukan nata 

Cikin tausayi yace maryama ban so cutar dakeba ya yar uwata idan laifin nawa ne kimin afuwa banson Na mutum da nauyin cutar da ke a zuciyata kanta ya qara mannawa kan qahon xuciyarsa cikin karaya  yace Maryama kiji bugun xuciya tako maryama ba zanyi tsawon rayuwa ba shiyasa gwara Na nemi gafararki 

Zancenshn ya qara ingizata ta qara rushewa da kuka tana qamqameshi cikin tsoro tana fadin bazaka mutuba ya Ahmad insha Allahu zamu rayuwa tare mu mutum tare ya Ahmad in ka mutum nima zan mutum 

Ganin ta rude sai surutai takeyi duk yayi iya yinshi ta kasa barin kukan 

Shiyasa cikin 

Hikima 

Ya tallabo 

Fuskarta 

Cikin tausayawa Kansu da Kansu ya tsurawa bakinta Ido yadda take kuka baji ba gani 

A hankali qoqolwarsa ta rinqa bashi umurni 


Cikin sanyi ya manna bikinshi da nata 

Da dabara ya samu ya zira harshenshi cikin bakinta 

A hankali yaji jikinshi

Ya fara sakewa tako ina yaji kamar ana watsa mai ruwan zafi a take idanshi ya fara canzawa 

Cikin zafin nama ya samu ya cabko harshenta ya rinqa tsotsan harshen cikin wani yanayi ya fara sarrafata 

Itako gaba daya jikin ta ya Debi bari da firgici jin irin karatun da yayan nata yake qoqarin biya mata nanda nan ta fara tureshi cikin tsoro da son zaro bakinta daga nashi Amman Ina ta kasa


A hankali ya zare bakinshi daga Nata ya nufi kan gado ya zube sai faman maida numfashi da mishi yake tayi 


Da hamzarita ta sake miqewa a karo Na 3 ta samu ta miqe din bata fadiba ta nufi kan gadon 

Zama tayi a gefen kanshi tana 

Ya Ahmad tashi mu tafi asbiti 

Hannushi yasa ya kamata ya kontar da ita a gefenshi 

cikin 

Rada yace maryama bani haqqina ko zan samu sauqin zogin da nakeji

Zuba mai indo kawai tayi tana zubda qollah😭

A hankali ya ronqofo kanta cikin hikima ya zare rigar jikin ta ya rinqa sauqe mata  salo kala kala


A hankali naji sautin kuka guda biyu Na tashi 

Ita kuka take Na tunanin irin shirin da Aysha take yiwa derennan ga ya Ahmad  din ase abin zai canza ya dawo gareta 

Shiko kuka yake yana ya Allah ka zama sheidana Na sauqi haqqin maryama da ya rataya a wuyana rabbi ka bani ladan biyeyya da nayiwa iyayena


Bayan sun gama dawowa haiyacinsu 

Ya tashi ya hada mata ruwan zafi ta Dan gasa jikinta tayi wonka ta fito ta kinga gefen shi


 shima wonkan yaje yayi gamida yin alwala yazo yayi ta nafilfili 

Sai da akayi kiran salah ya tasheta shi kuma ya nufi masallaci 


Bayan ya dawo daga masallacin ya samu bata nan

Cikin mutuwar jiki ya konta 

Zuciyarsa Na bugawa 

 a ranshi yaji bai yiwa maryama tashi Adalciba a fili yace da Aysha ce da bazan mata hakab da zan bataba kulawa t sosai


Da gwarin guywa ya nufi dakinta tun da tazo gidan bai taba shi gaba sai yau  

Sosai yayi mmkin ganin ta konce hawayen Na bin fuskarta da sauri ya qarasa gunta cikin Dan kula ya tallabota ya daurata kan cinyarsa 

Maryama ni nasaki kuka ko ki gafar ceni kar kijamin Allah ya isa 

Kai ta rinqa juyawa tana zubda qollah😭 cikin sanyin murya tace ya Ahmad ba kamin komai ba kuma ko kamin ma Na yafe 

Toh meyasa saki 

Kuka 

Kaine ya Ahmad

Da sauri yace kuma kince ban mki komai ba

Ehh bani kake yiwaba 

Toh me NAYI gayamin yake yar wuta Na baki haquri


Cikin kuka tace ya Ahmad meyasa bazaka Sa haquri a rankaba ya Ahmad ka ruqwumi qaddara mana ka dena azabtar da zuciyarka da ta maso yanka da halin da kake ciki


Cikin cije lebe yace maryama ba yin kaina bane bani da yadda zanyi 


Cikin kula tace ayyah ya Ahmad duk da nasan ba sona kakeyiba Amman zan roqeka alfarma ka daina rufe qofar ka gareni

Da sauri ya katseta da cewa waya CE miki ban sonki kin tabajin inda Dan uwa yaqi yar uwarsa 

Cikin kukan tace 

Ya za ayi in yarda kana sona

Cikin qarfin hali da qoqarin ganin ya fatan ta mata yace zo zonannki gani 

Bakinshi ya hade dannata ya rinqa tsotsar harshenta sai da yaji tayi nuqui ya zare bakinshi ya dan nunata yace 

Maryama zabin Allah kece zabin da Allah ya min kuma bazanngi zabin mahaliccina ba cikin Dan jin sanyi tayi ajiyar hrt tace I love U so much my dear Broz 

Me 2 

Yace mata gamida fita ya nufi dakinsa

Kai tsaye toilet ya nufa Dan amai yakeji mai bala,in zafi yake jin yana  tuqarsa daga qahon zuciyarshi 

Sosai yaketa kakari ga wani zazzabi mai zafi da ya rufeshi a take 


Cikin tsinkewar zuciya da frigata da tsantsar azaba ya zubawa a man da yake kwara wan ido 😳


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

MI, WASMITI page5⃣1⃣to5⃣3⃣

Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Jini ne guda2 baqiqqirin dashi aman 

yayi sosai

Cikin wahala da dimuwa ya koma cikin dakin kan gadon shi ya fada 

Cikin maida numfashi a hawale cikin tausa yawa kanshi yake qoqe qollahr😭da ta cicciko mai ido 

A ranshi yake tunanin wannan karo Na biyu kenan yana aman jininnan ran da Maryam ta tare da yau kuma


Cikin tunanin da azabar da yakejin baccin wahala ya saceshi Dan wannan lkcin ya kasance kamar shine dare a gareshi daran kuma yakan zame mai tamkar rana da wuta a cikin zuciyarsa 


Tin daga wannan rana Maryam take shigewa rayuwar Ahmad sosai Dan qoqarin qanin ta debe mai kewa ta Dan kawar mai da matsalolinshi 

Ba laifi kuma iya dai dai gorgodo ya sake 

Yana boye damu warshi Dan ganin Maryama manshi Na shiga ciki. Damu sosai

Sai dai banan gizo 

ke saqanba

Ase a hankali ciwon zuciya ya gama raraka qarkuwar jikin Ahmad


Wata rana da aman ya sashi a agaba

Dole ya shirya cikin sirri yaje hospital gojin forko da akayi aka gano zuciyar Sa ta samu mugun raunin dr Jabir ne ya kalleshi cikin kula da tausa yawa yace Ahmad  dole sai anma dashen zuciya


Kai ya sunkuyar cikin siyayar da qollah😭 ya Dan kuma daqowa yace Dan Allah doctor ina Neman alfarmanka plx wannan mgn ta zama sirri tsakani Na da kai karka gayawa Abba Na 

Cikin mmk Dr yace 

Ahmad me kake nufi zaka boye musu abinda ke damunka ne shin sai ciwon ya kasheka ne kakeson su Sani 

Ko nufinka bazaka nemi mgni ba 

Na gayama dole ayi dashen zuciya kuma mu anan ba,ayi dole zamu fidda kai India ne Dan acan muke da qorarrun likitocin zuciya


Zan nemi mgn Dr kuma zan fidda kaina India a bincikeni in takama ajene ma Na tabbatar zaka tsaya min a mddin Abba Na 

Toh meya baka son shi din ya Sani ?


Sabida zai cutu nikuma ban son abinda zai cutarmin dashi 

In yaji shima zai iya kamuwa da ciwon Na tabbatar Abba zaisamu matsala matuqar yaji cutar dake jikina kaima da kanka kasan rayuwara ta azgara ai shiyasa 

  nafi son sai nasamu sauqi

Ko kuma sabanin n hakan 

 inyaso a gaya mai daga baya  

 

Cikin sanyin jiki Dr yace haba dai Ahmad aishi cuta ba mutuwa bane zafin ciwo bai kawo qarshen numfashi 

Haka dai yai ta kontar mai da hankali

Cikin wota 2 suka kammala shirye shiryen tfyar cikin sirri ba Tate da kowa ya saniba 


Kullum Yusuf sai ya kira Ahmad da Adam dama wannan Al,adarsu kenan ko basa tare sai sun Kirayi juna da safe Dan jin lfyar juna da dare suyi sai da safe


Sosai Ahmad ke qarfin halinsa kan baya son kowa ya gane ciwon dake tare dashi   

Lkta da dama in yaje gida yakan zauna yasa Nenne shi a gaba yana tuna wanne irin hali zata shiga ran da babu shi sautari in yaji haka yakan fita kawai ya komai part dinsu da a yanxu ya zama nasu Usman yai ta kuka


Wata rana da yamma yana zaune a parlon shida Maryam Na konce a gefebshi tayi pillow da cinyarsa 

A hankali cikin hikima ya tura hannushi cikin rigarta cikin tafiyar tsutsa y sauqe hannun akan qirjinta 

Ya rinqa shafawa 


A hankali ta lumshe idanta  gamida sauqe gajiyar hrt 

Kanshi ya Dan ronqofo saitin kunnetan yace maryama tawa  shin tsaka Nina da ke waye rego ya fada yana shafa mararta 

A Dan kunyace tace 

Ya.Ahmad me mukayi na raqunta

Biki ya Dan ciza yace yoh har yanxu ban samu Na baki rain on Magaji naba INA tsorofa kar bazan samu mai min addu,a ba 


Da sauri ta tashi ta zauna kan cinyarsa tana fuskantarshi tace nacema bansan iri zancen   nan naka ko 

Toh nayi shiru

Masoyiyata maryama 

Cikin jin dadi ta sanqalo wuyarsa ta hada bakinsu wuri daya ta rinqa bashi keutar kis masu zafi 

Cikin bugatuwa yace Maryam mutafi daki 

A kuyance tace 

Kai ya Ahmad me zamuyi a daki kuma


Bakinshi ya kai saitin 

Kunneta yace  farauta zamiyi Na farauto baby's

A kunyace tayi cikin daki

cikin fatan Allah yasa ta samu ciki a yau dinnan ko zai samu mgji Dan yau saura 1 week su tafi shi da Dr  

Bayan komai ya LFA sun dawo hayya cinsu yana shafamararta yana Allah ka  inqatamin  


A hankali woyarsa ta fara suwa da sauri ya daga ganin Abba Na a rubuce a fuskar woyar

Toh ganin zuwa Abba yamxuma kuwa

Sauri sauri yayi wonka ya nufi gida 



Cikin sanyi sanyi yayi  slm gami da shiga parlon abban


Baya ya zauna gefenshi kadan daga qasa kan carpet 

A hankali yace abba barka da gida 

Barkadai 

Ahmad

Abba gani 

Cikin wani irin yanayi Abba ya dauki duk takardun binciken lfyar Ahmad din ya ajiye mai a gaban shi


Cikin mmk ya daqo kanshi ya zubawa abban Ido 


Shi kuwa Abba komawa yayi ya zauna gamida dafe qirjinshi cikin cijewar voice yace Ahmad me wanna Ahmad ase a duniyan zaka iya boye min wata matsala taka 

Cikin salqewar qarshe yace 

Tun yaushe kake tare da wannan mugun ciwon ni dai Ahmad ka boye mun cutar dake jikinka


Cikin zubar qollah😭 ya kontar da kanshi kan cinyar Abba ya rinqa zubda qollah😭 cikin jin zafi azuciyarshi ya kalli abban yace Abba toh ya zamuyi ya rigada rayuwa ta zo qarshe dole 

Kunasona INA sonku dole mutuwa zata rabamu zan tafi Na bar Yusuf da Adam cikin kadaicina Abba zakayi rashina dole da nasan wannan ciwon bazai barniba 

Ina tausa yawa nennena ko ya zatayi ran da taga gawata a miwe a gabanta

Nan kuka yaci qarfin su su duka biyu aka rasamai bawa woni haquri a cikin su 

Can dai Abba ya rinqa shafa kanshi cikin kontar da hankali yace Ahmad cuta bata kawo mutuwa ba mmk yanzu wanda ke da lfy ya mace Allah ya barmana kai din 

Tun randa kukayi mgn da Dr jabeer bai bariya qara koda kwana dayaba  har gida yazo ya  gayamin matsalar taka kuma duk shirin tafiyar nan da akeyi dani akeyinta tare zamu tafi insha Allahu zamu dawo cikin nasara


Ka kontarda hankalinka 

Haka dai sukayi mgnarsu su biyu suka rufe 


Yakarbi takardu ya tafi dasu 

Part din Nenne shi ya nufa yayi SLM bata parlon Dan haka kai tsaye ya wuce cikin bedroom

Tana konce gefen gado cikin fara ta amsa slmar gami da nuna mai gefen ta a hankali yazo ya durqusa a gabanta ya manna kanshi kan cikin ta 

Razana sosai Nenne tayi Dan wani irin sanyi da taji cikin cikin ta irin  sanyi da taji a kwana kin da mahaifinta zai rasu hannuta ta Dora a kanshi hannu har bari yake tace Ahmad baka da lfy ne meke faruwa da Kaine ya kai Dana


 cikin qarfin hali yace ba komai 

Shiru sukayi Na Dan wani lkci can dai ta dago kanta ta leqa fuskar dan nata 


Cikin razani da mmk ta taso zaune  😳🙉😱😰


Ku biyoni a sannudai yanxu zamu fara ninqaya cikin lbrin 


A gsky INA Alfa hari daku Tabital Fulaku group ban manta da  kuba novels group 

Dan gyaran kanmu INA jin dadinku😍😘😍😘


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

MI WASMITI page5⃣4⃣to5⃣5⃣ Na  Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Cikin mmk tace kai Ahmad yanxu muna mgna yanxu kuma kayi bacci a take 


Murmushi ya danyi gamida miqewa yace wlh baccin yaci qarfinane shiyasa Nenne am 

Toh koma gidan ka kayi baccin ka 


Toh yace gamida yi mata slm ya fita ya tafi 


Yau Monday kuma yaune da yamma su Ahmad da Abba zasu tafi 

Tin safe Maryam take Dan harhada  damai kayanshi adan ma daidaiciyar jakarsa🎒 

Ta Dan bude zip din bayan jakar kenan da nufin zata samai turarenshi a ciki taji takardu a ciki 

A hankali ta jawosu Dan gyara shirin zamansu 

Cikin mmk da zare ido ta nufi 

 parlon

Da sauri ta qarisa gun shi cikin tuhuma 

Tace ya Ahmad

Me wannan me nake gani ya Ahmad ciwon zuciya ase dama abinda zai kaika India kenan 

Sai hawaye da yake bin fuskarta cikin kukan tce ya Ahmad meyasa kayi shiru 

A hankali ya daqo 

Cikin sanyin jiki yace 

Toh maryama in Na gaya miki ma mai muka iya bawai Na boye miki Dan wani abu bane 

Kawai dai banson kowa ya sanine Dan gudun kar a gayawa Nenne Na 

Cikin muryar kuka tayi dakinta 

Da sauri ya bita 

Tana shiga ta rufe qofar kan gado ta fada ta rinqa kuka mai zafi cikin firgici


A bakin kofa ya tsaya yana kiranta cikin salon lallashi da waqa waqa ina kikene masoyiya ta

Na duba gabas ban gankiba Na Duba yamma ban gankiba naje a arewa banga ya tamkarkiba 😜😝

naga yammata kala kala  bbanga kamarkiba maryama tawa pito kixo gareni 

Cikin kuka da Dan gudu gudu ta zo ta bude qofar 

hannu ya bude mata cikin goge qollah😭 ta fada cikin girjinshi 

Ajiyar hrt yayi gamida meda hannushi ya matseta cikin jikin shi yana sauqe numfashi


 cikin raunin muryar tace ya Ahmad tare zamu tafi ko ?

Ido ya lumshe gamida dagota yana kallonta a hankali ya rinqa shafa fuskarta hannushi daya kuma Na kan qirjinta yana Dan canza salon zance a hankali ya rada mata kiyi haquri ba Dadewa zamuyiba kuma kinga tare da Abba zamuje

Cikin zuba mata ido ya manna bakinshi da nata ya rinqa tsotsar lips dinta saida yaji gaba daya ta sake 

Tana ta qoqarin kaisu qasa 

Cikin qarfin hali

Ya Dan zame bakinshi daga nata ya jata suka koma daki kan gado suka zube cikin dabur cewar murya da buqatuwa yace 

Maryama Na roqeki kar ki gayawa Nenne batun ciwona kinjiko kimin alfarmannan yake matata 

Cikin sanyin jiki tace nayi alqawari bazan fadawa kowaba 

Cikin ji. Dadi ya jawota cikin jikishi daga nan kuma suka shiga fagen yaqi suka rinqa kaiwa arna hari suna kashesu😜😝


A ranar jirginsu ✈ya daga  sun isa lfy har an fara binceken lfyar Ahmad din..


Gasar saudiya 🕋

Cikin birin madinatul 

Munauwarah


Yau kusan 3 weeks kenan da dawowar Yusuf da 

Ciggam dinshi injishi da fada daga zuwa Nigeria Hutu aka manna mai ita 


Duk sawon kwana kinnan Tun randa sukazo bata qara Sa Yusuf a idantaba 

Tinda suka isa cikin gidan ta zauna a parlon cikin gajiya da yunwa

 

Tunda ya shiga part dinshi bata sake yin motsinshiba 

Har aka kira sallan maqqariba 

Sosai takejin kiran sallan da akeyi daga cikin masallancin Madina Dan gidansu ba nisa da masallacin zakaji duk abinda akeyi radau 

Hatta hasken fitulun masalacin ana gani ras 

Cikin tsoro da jin Dan jimamin gidan 

Ta nufi cikin dakin komai nanan ras dakin tsaf anyi mai gyara sai qamshi yakeyi 

Lkci daya kuma tunanin gida ya fado mata sai kuka 

Cikin kuka take fadin shike nan haka zan rayu ni kadai duk an rabani da yan uwana ba uwa ba uba ba yayu ba qanne kuka sosai ya kofcemata duk da zuwa yanxu hawayen ta ya fara qafewa 

Cikin kukan taje tayi alwala tazo ta gabatar da sllahn maqqariba bata tashi a wurin ba har aka kira isha 

Sallan kawai tayi ta kuma ci gaba da Kukanta 

Haka ta zauna ba ci ba  Sha sai tunani da tsoro da firgici da suka isheta 


Koda qari ya waye bata fito ko parlon ba haka ta wuni cikin tsoro da kadaici 

Haka ta wuni ba abinda ke daga ta kan carpet din sllahnan nata sai alwala 

Haka ta rayu tsawon kwana 3 in banda ruwan da takesha ba abinda takeci 

Duk tagala bata hatta jikinta in ta tashi tsaye sai taji tana bari kamar zata fadi ga Dan banzan yunwa da jiri da takeji  

Dole ganin tana qoqarin rasa ranta  a rana 4 ta fito parlon cikin tafiyar gala baita ta nufi wani Dan steep Wanda daga dukkan alamu kitchen ne 

A hankali cikin jin yunwa ta zubawa kitchen din I do komai Na buqatar rayuwa akwai can 

Gefe ta hango firij da sauri ta qarisa gun cikin tasan hannu ta bude Da sauri ta rinqa ballot inabin ciki masu sanyi ta rinqa ci sai da taji haqwaranta sun mace da sanyi a  hankali ta rinqa sauqe ajiyar zuciya


A wurin ta zame ta  konta Dan jin cikinta Na murdawa konciya tayi cikin sheshsheqar kuka tana fadin ko mutuwa zanyi ba ruwan Hamma Yusuf mugu azzalumi ya ajiyeni a gida kamar karya ni kadai 

 Cikin qunci tace  da ya Ahmad da sai  gata ya isheni 

 Can kuma ta rinqa sake numfashi bacci mai dadi ya kwasheta a gun 

 Itace bata farkaba sai kiran sallah da ya tada ita 

Cikin Dan jin qarfin ta dabi inabin da tufa ta fito takaishi dakinta ta dawo parlon ta Debi kayanta ta shigar

Dakinta 

 

Tun daga ranan haka take rayuwarta sai tayi kwana 3 ana 

4 ta fito ta danci fruits tun yana mata dadi har ya dena mata dadin sai dai taci kawai Dan kar yunwa ta kashe ta

Tuni kuma yuwwar ta shiga jikin ta duk ta Dan jeme Kuma ga rashin qarfin ko wonka tayi sai tayita haki 


shiko Yusuf zuwa yanxu yana ma man tawa da wata halitta a cikin gidan duk da kullum yayi woya da mutananen gida sai  sun tabbayeshi ita 

Haka zai ta musu kone kone ko yace yana cikin makaranta ko gani yanxu Na fita gida ko kuma wlh INA cikin masallaci 

In ance woyartafa sai yace ai ita tace bata buqatar woyar tawama ta ishemu 

Haka dai rayuwa tayi ta juyawa


Ranar wata jumma,a tun da safe 

Yusuf yayi wonka cikin shiga ta alfarma irin shigar larabawan Riga da wondone masu taushi bugun pakistan   yayi rasa ya fito cikin haiba  ya Dan kifa yar pulannar da suke sawa gashinshi mai laushi da bakinan sai sheqi yakeyi 

Ya fesaturare mai qamshi gaba daya ya debi qamshi fa sheqi ya fito cin nitsuwa ya nufi masallahci Dan wannan dabi,ar shi kenan duk ran jumma,a  

a masallacin yake wuni


Ita kuma Aysha tun safiyar ta tashi da wani irin ciwon mara mai tsananin Wanda ko motsi mai qarfin tayi sai taji kamar marar zata balle ga azabebben ciwon kai da zazzabi mai zafi 

Cikin jikinta takejin sanyi Na ratsa hanjin ta 

Haka tayi ta rawar sanyi cikin kuka 

Haka ta wuni cikin azaba ko sallah bata samu ta tashi ta tayiba


Qarfe 3:00 pm Na Nigeria Wanda yayi dai dai da 5:00 pm Na saudiya

A hankali woyar yusuf ta fara suwa kamar bazai dagaba sai ya kuma daga yaga Ummi CE ke kiran shi 

Cikin sauri sauri ya fita cikin harabar masallacin 

Cikin mmk yake kallon sararin samaniyar hadarine baqiqqirin  ya hado ga iska mai sanyi ta fara kadawa alamar forkon damina

Gaba daya  ya zaman sararin samaniyar ta canca kala iskamai dadi keta kadawa yana sauqe nishadi cikin zucuyar duk wata halitta dake rayuwa a wurin


Suwar woyar ne ya kuma katseshi cikin duniya nishadin da ya tafi


Da sauri ya daga gami da yin sallama


 cikin biyeyya yace yi haquri Ummi bana kusane 

Hmm tace gamida cewa ka bawa Aysha woya 

Cikin Dan yin Jim yace

Ayyah Ummi ai bana gida 

Kana ina?

Kinsan yau jumna,a INA masallaci 

Cikin Dan fada fada tace kai kaga shiga hankalinka rainin wayon ya isa haka ka kama kanka

Kullum nakira ka hadani da yarinya sai kai tamin kauce kauce

Ina gayama yanxunnan nakeso ka kaimata woya 

Cikin Dan yamutsa fuska yace 

Kiyi haquri Ummi in NAYI sallar maqqariba da insha zan kai mata


Ka kaimata kawai dai yau dinnan kam  nace 


Toh yace gamida katse kiran


Bayan an idar da sallan insha ya fito ya nufi gida cikin nishadi dajin dadin iskar dake kadawa idanshi ya lumshi gami da yin ajiyar zuciya sosai yanayin ke sashi nishadi


 aduk lkcin da yaji irin yanayinnan shi kadai yasan yadda yakeji a ciki jikin shi jininshi kan carke  ruwan kanshi Na sinkewa ta yadda yake sauqar mai da Sha,wa mai qarfin da fiddashi hayyacinsa

Cikin tsotsar lips dinshi da Dan rawar sanyi ya qarisa gidan......

 

Fatan alkhairi a gareku masoyana INA jin dadin irin😍😘 kulawar da kuke bani 


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


NAYI NADAMA


MI WASMITI page 5⃣6⃣to5⃣8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Cikin takun mishkilanci ya qarisa cikin parlon 

Ido ya Dan wore gami da qarewa parlon kallo 

Cikin Dan mmk 

Yace kamar ba 

Wani bani Adam dake 

Rayuwa a ciki parlon 

Baki ya kuma tabewa gamida Dan buda hannu da Dan daga ka fada alamar ko oho shi dai bai shafeshi ba

Kai tsaye 

Bakin qofar bedroom dinta

Ya nufa 


A hankali ya rinqa Dan buga qofar 

Har zuwa Dan woni lkci baiji motsinta ba 

Gashi sai wolqiya da iska dake kadawa tako INA 

Cikin fara harzuqa 

ya murda marfin qofar gamida turawa da qarfi


Tsayuwa yayi can a tsakiyar dakin 

Yana yan dube dube 

A ranshi yake cewa toh ina ta shiga 

Yarinya sai shegen kadifiri

Kofar mashigar toilet nata ya nufa 


Da sauri ya tsaya gamida qara zubawa gefen gadon ido 


Can ya hanqota a kasa konce kan carpet ta wani duqunqube sai karkarwa takeyi 


Da Dan sauri ya isa gun cikin Dan mugunta yayi murmushi gamida Sa qafarsa ya cureta 


Taba tan da yayi da qafarsa hakan yayi dai2. Haskawar wata iriyar walqiya mai tsananin haske a take kuma tsawa mai qarfin ta ratsa dukkan illahirin fadin garin 

Ruwan kuma mai qarfin kamar da bakin qoriya ya kece


Abin yayiwa Aysha yawa ga firgici zazzabi ga tsoron kadaici ga abin da take tsoro kamar mutuwarta tsawa yana firgitate fiye da zaton mai karatu 

Shiyasa cikin 

Tsananin firgita 

Ta miqe 

Da qarfi ta fada jikin Yusuf din 

Tasa hannuta bibbiyu ta qaqumo bayan shi qirjinta ta manna kan nashi qirjin cikin kidima gamida tura kanta cikin wuyan shi 


Cikin wani irin baqon yanayi Yusuf ya nemi qarfinsa da kuzarinsa ya rasa gaba day sassan jikinsa sun mace ba wani abinda ya rege a jikinsa maiyin aiki sai zuciyarsa 

Hatta numfashin Sa da jinin jikinsa sun dauke Na Dan woni lkci


So yake ya  taqarqara ya samu ya hanka data Amman ba qarfin yin hakan

Cikin yanayi da ya hade mai 

Ga yanayi Na sauqan ruwan dama yanayin da yafi komai tayar mai da Sha,awa

Ga qirjin mace da yake ji cikin NASA qirjin  

A take ya fara fita haiyacin sa  

Lkci guda ya fara rawan sanyi lips dinsa suka rinqa motsawa a hankali 

Cikin kidi memmeyar

Sha,awa

Ya kamo lips dinshi 

Na qasa ya rinqa tsotsa cikin fitar haiyaci


A hankali yaji sautin numfashinta Na sauqi kan wuyanshi 

Dumin jikinta ya rinqa ratsashi 

Kamar 

A mafarki 

Ya tuna wacece a jikinsa 


Cikin tsananin jarumta 

Ya tatara gaba 

Daya sauran qarfin shi ya hanka data kan gado

Cikin juya mata baya Dan gudun kar ta gano halin da yake ciki 

Ya fara surfa mata masifa

Can kuma ya juyo yana nunata da Dan yatsa cikin hada fuska 😡yana fadin

Waike wacce irin fiti nenniyar yarinya CE 

Shin baki da hankaline 

Dan tsabar raini zaki woni shaqoni 

Da gangan ko so kike ki kasheni ne 

Toh wlh ki bude idanki da kyau ki ga waye a gaban ki 

Ni Yusuf nake 

Ba Ahmad bane ma rainin wayonku da zakuyi ta cakudashi


Ita kam tunda taji ya hanka data ta dawo cikin haiyacinta ta kifa kanta kan guiwowinta ta rinqa sheshsheqar kuka 


A hatsale ya matso gab da ita dai lokacin da kiran Ummi ya shigo woyarsa 

Cikin nuna mata yatsa yace 

Ki rufewa mutane baki kinsa Sam ni bansan muna furci kekuma kince ke uwar muna furci CE wlh kika kuskura kikamin ba dai dai ba babbalaki zanyi ko a jikina

Nan dai ba Nigeria bane bare kina da masu goyon bayanki 

Woyar ya miqa mata gamida 

Cewa

(Da jabu leqquru do Ummi on yidi volugo be ma lutti a wanna am nafi kaku )

Ingo karbi phone dinnan Ummi ce ke son yin mgn dake saura kuma kimin muna furci 


Hannuta har rawa yakeyi ta karba gamida karawa a kunneta 

Cikin kewar juna suka kira sunan juna Na,am Ummi Aysha tace 

Sai kuma kawai ta saki kuka mai cin rai ciki kuka 

Tace Ummi 

Banda lfy Ummi zan mutuwa 

Ummi kince wa Hamma Yusuf

Ya dawo dani gida ni Na gaji 

Cikin lallashi tace kiyi haquri Aysha ki nitsu ki saurareni mana ki daina kukan .

Toh tace gamida da bayahannuta ta qoqe fuskarta da ta cika da qollah😭


Kina jina ko Aysha in dai zakinayin kukan in an kirki to ba mai kiranki Dan nima yanxu haka a boye Na kiraki Dan Bappa yaya yace kada aita kiranku Dan zaki rinqa yiwa mutane korafe korafe .


Cikin shan majina tace 

Shike nan Ummi yanxu ni kam haka Zanyi ta rayuwa ni kadai cikin uquba😭

Dan Allah Ummi ki taimaka kamin kince a dawo Dani


Cikin  jin dadin zanceta yace nima den Na huta wlh in sun yarda a satinnan zai maida musu kayansu 

Ko nima Na samu Na huta da jarabar tsiya

duk anbi an matsamin da kiraye kiraye 

Kowa sai yace min fatan dai tana lfy wato ni kam ko oho in naga dama Na muuu bai da mesuba 

Mayya kawai 

Ya fadi a fili dai2/ lkcin da ya fizgi woyar 

Cikin hikima yace Ummi 

Kinji abinda naketa fama dashi ko ni kullum cikin lallashinta 

Ko karatun ban samun inyishi yadda nake so wlh da kun yarda na maido muku da abunku in yaso in Na kammala karatun sai kuyi yadda kukace din

 

Cikin qosawa da zancen nasa tace

Kai saurara  

Toh yace 

Kana jina ko 

Ehh ya fadi  da  Dan yamutsa fuska Dan yasan kwanan   zance

Cikin umurni tace INA gayama ka kula da yarinyar nan 

Toh yace gamida cemata toh 

Ummi sai da safe

Allah ya bamu alkhairi tace mai 

Amin ya fadi tare da katse kiran


Yusuf da Ahmad yawanci suna woya kullum

 amman kwana biyunnsn  Sam ko ya kirashi Abba ke daqawa 

Yusuf yasan suna India Amman Ahmad cemai yayi sunje har kar business din sune 


    A CAN INDIA

Kuma kwana biyu kenan anata Duba lfyar Ahmad anyi nasarar gano zuciyarka ce ta stage sakamakon yawan damuwa da tunani da cushewar qoqolwa da numfashi 

an kuma dora shi kan mgni duk da cutar tamai mugun kamu ta yadda dole cikin biyu za ayi daya ko ya rayu ko a rasa shi 

Saka makon binciken da ake ta mai dinne yasa ko Yusuf ya kira dole sai Abba ke daqawa


Abin ya Sa Yusuf a tunani ga yawan mafarkin da uwan nashi da yaketa damunshi sai dai in bai konta bacci ba


     Yau alhamis 

Tun da gari ya waye Yusuf ya tashi da wani irin kasala ga tsinkewar zuciya a kai akai 

Gaba daya jikin shi ya sake shiyasa ko fita bai yiba 

Yana konce 

Kan 3 str dagashi sai Dan 3 qtr da yar farar sheet

A hankali yaji phone dinshi nata Neman a gaji a karo Na  7 kenan ta yanke bai dagaba

Duk lkcin da kiran ya shiga sai yaji wani irin tsinkewar zuciya

A karo Na  8

Ya Sa hannu cikin kasala ya daga woyar mujahedin ya gani cikin dan jin tsinkewar zuciya ya daga..........abinda mujahedin ya gaya mai shi yafi komai qara kashe 



 Ina Alfahari daku masu karatu  


By garkuwan Fulani😍😘

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


NAYI NADAMA


MI WASMITI page


5⃣9⃣to6⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Mutuwar jiki 

Cikin tsoro 

Ya katse kiran 


Baba bello ya kira cikin rudani 

Yace

 baba meke damun Ahmad

Baba meyasa Baku gaya min ba 

Baba ya za ayiku boye Min abin da ke damun Ahmad

Cikin mmk

Baba bello ya tsaidashi yana 

Fadin kai Yusuf ka nitsi ka tsaya 

Wai shin waye ba lfy 

Kuma waya gayama 

Ni nasan lfy lau Abban Ku ya tafi da Ahmad

Cikin tsoro yace baba boyema sukayi ko Kaine kake son boye min 

Cikin Dan rudewa yace waya gayama ?


Mujahedinne ya kirani yanxu yace min ya qansu a asibitin jinyar zuciya kuma yace yaga an shigar da Ahmad dakin aiki 

Shi yaushe yaje India ?

Shima kwanan nan yaje ya kai mahaifinshi .

Cikin 

Kon tarmai da hankali yace toh 

Bari Na bincika 

Naji 

Da sauri ya kira 

Adam bayan ya katse kiran baba bellon


Ko slmar Adam bai amsaba 

Yace Adam 

Ina Ahmad?

Cikin da Jim yace 

Yoh 

Ai basu dawoba

Tukun .

Toh me suka je yi a can ?


Dan tsaki yaja gamida jawo Amira dake konce a gefensa 

Yana shafa mararta yace kai 

Miraah kinyi yar lukutafa ji yadda kikayi nauyi 

Cikin salon motsa love ta Dan shafa nashi marar har zuwa Dan qasa 

Da qarfi ya matsota gamida sakin yar qara wash miraah zaki zauta yayanki fa 

Yusuf dake jin duk abin da sukayi ya hatsala iya hatsala 

Cikin ta kaici 

Da tsawa yace 

Kai biyaye ban son halin akuyanci fa kaji Dan iska Na kiraka zamuyi mgnar kirki ka woni tsayawa kana bunsuranci a gun yarinya qarama 

Dan iska 

Na mamajo kawai ka gayamin me Ahmad yaje yi a India


Cikin muryar Sha,awa ya lumshe ido yace Sam wlh kai banzane biyaye kai ka takura rayuwarka muma zaka takuramu 


Cikin muryar gsky da gsky yace 

Adam ko kasan Ahmad bai da lfy ne ko kasan ciwon zuciya Ahmad ke fama dashi

Cikin muryar karaya yace 

Adam ina amanar da Na baka 

Cikin zaro ido da tsoro Adam ya ture Amira ya tashi tsaye yanata fadin innalillahi wa inna ilaihi raji un 

Gaba daya jikinsa rawa yakeyi

Cikin tsoro yace 

Biyaye waya gayama ?

Cikin Dan fada yace ban saniba 


Cikin tsoro ya koma ya zauna kan kujerar 

Ahmad din ya kira 

Kiran forko bai dagaba sai ana 3 ya daga 

Cikin fargaba yace 

Biyaye 

Na,am ya amsa 

Cikin qarfin hali 

Ahmad Kaine ?

Ehh nine mana 

Da qarfi yayi ajiyar zuciya


Kamar yana ganin shi yace Ahmad ka kalleni ka gayamin meke damunka ?


Cikin qarfin hali  da qoqarin danne tarin da yake son taso mai yace 

Ni ban da matsalar komai 

Kai sai yawan tuhumar mutum ko yaushe ai shiyasa INA ganin kiran ka nake qin dagawa


Kai ya rinqa girgizawa kamar yana gaban shi yace 

Ba gsky ka fadamin ba 

Biyaye qrya kake min Na tabbaya matuqar muna Raye kuma muna halin lfy duk tsananin laifin da Na maka Na tabbaya zaka daga kirana 

Ahmad meyasa kake son boye min muguwar cutar da take tare da kai 

Gaba daya muryarsa ta rinqa carkewa 

Ahmad ciwon zuciya ko 

Ahmad an gayamin fa Sai kuma ya kasa ci gaba 

Ahmad dake konce kan gado Abba Na gefenshi 

Hannu yasa ya kamo hannu abbansu ya rinqa kuka kamar yaro

Kukan yake yana fadin Abba Yusuf yaji banda lfy

Abba meyasa batun ciwona ya isa kunnen Dan uwana 

Abba INA tsoron halin da Yusuf zai shiga 

Cikin ajiyar zuciya 

Yaci gaba 

da cewa 

Abba Na INA sonku kuma Kuna  sona Amman dole  zaku rasani 

Abba kamin alqawari zaka bawa Yusuf da Aysha da Adam ga maryama  kulawa ta mu samman da zata dauke musu quncin rashina 

Abba shima kuka yakeyi sosai

Yana zaka rayu Ahmad am  

Zafin ciwo ba shine mutuwa ba 

Cikin alamar tabbaya yace toh Abba ko Na rayuwa yanxu ai gaba dole zan mutun ko ?

Hannushi ya kama cikin kuka yace eh Ahmad mutuwa dolece Amman muna roqon Allah ya rufa mana asiri mu gaba ceku


Girgiza kai yayi cikin Roqo yace 

Dan Allah Abba Na 

Mu koma qasarmu ta aihuwa 

Abba tun yaushe aka sallan memu Amman kace sai mun qara ganin wani doctor

Abba kayi haquri ba taurin kai nayi ma ba Abba Na mukoma qasarmu Na mutum acan a gabanka  a gaban mahaifiyata a gaban baba Na

Abba kamin alqawarin muna komawa

Zaka kira Yusuf da Aysha suzo in musu kallon qarshe Abba INA son Yusuf da Adam su kasance sune masu Sani cikin makoncina

Kuka sosai abban keyi 

cikin kukan yace nama alqawari insha Allahu jibi jibinnan zamu koma kuma zan hadaka da yan uwanka


Can kusan 9:00 pm 

Yusuf ya kira Abba cikin rawan  murya yace Abba insha Allahu jibi zan taho gunku Dan Allah Abba kar kace zaka hanani zanzo naga Dan uwana 

Cikin sanyin jiki yace Yusuf bazan hanaku ganin junaba 

Amman muna jibin zamu dawo 

Kawai ka taho Nigeria mu hadu a can

Abba meyasa zaku koma ya samu sauqi ne ?

Eh Yusuf jikinfa da sauqi Amman dai  kazo tare da Aysha. 

To yace cikin cushewar tunani 


Yana katsewa

 Adam ya kira ya sheida mai yadda sukayi da Abba dan dama  suyi zasu hadu a can


🌏🌏🌏🌏🌏🌏


    KASHE GARI

Tun da safe Yusuf komai  yake cikin sikewar zuciya yakeyi komai 

a hankali ya fito cikin mutuwar jiki ya shiga mota da niyan tafiya airport Dan kammala  shirya shuryen tfyar tasu 

Cikin sanyi jiki 

Ya fito cikin motar cikin gidan ya komai cikin woni irin sanyi da yakeji a jikinsa 

Kai tsaye dakin Aysha ya shiga 


Jikin qofar ya jingina ya zuba mata ido cikin ta kaici 

Zaune take kan gado sai kuka take kamar wacce aka yiwa rasuwa 

Masifa yakeson yi mata a ranshi Amman bai da garfin haka bare kuzari 

Cikin ta kaici ya isa gaban ta 


Hannu yasa ya dago kanta 

Da sauri cikin razana ta wore idanta cikin ci gaba dakukun


Rai a jagule ya nunata da Dan yatsa

Gami da cewa 

Wlh kina ban tsoro ke ko yaushe kina cikin kuka toh insha Allahu zakici kanki banga me ake mikiba banga da me Na regeki ba 


Ido ta tsura mai cikin sake Sakin kuka

A kufule yace mayya 

Ni ki tashi ki bani passport dinki banza

mayya gobe dai insha Allahu Iwar haka kina can

Gun su Ummi kiyita masifar kukanki


Cikin sauri ta miqe jikinta har rawa yakeyi 

Beed side din dake gefen ta ta jawo miqa mai passport din tayi da sauran takar dunta gaba daya 

Cikin harara ya karba gamida tsince wadanda yake da buwata ya watsa mata sauran


Kafin azahar kab ya kammala musu shirin tafi yarsu jirginsu zai tashi shida Na safe


Suma su Abba duk sun gama shirinsu tsafa suma tashin asuba zasuyi


Yusuf kam tunda ya fita bai dawoba   sai 9:12 pm  

ya shigo kai tsaye dakinshi ya nufa shirin shi yayi cikin sanyin jiki bayan ya gama hada komai ne 

Ya Dan shiga toilet ya Dan watsa ruwan 

 Yana fitowa ya zauna a bakin gado  

Cikin jin yiwa ya shafa cikinsa yunwar yakeji kamar zata kashe shi Amman kuma bazai iya cin komai ba duk da kuwa tun shekaran jiya da dere rebonshi da cin wani abu


Cikin sanyin jiki ya daga woyarsa

Ahmad ya kira a wunin yau wannan shine kirashi  na 23 da ya kirashi Dan jin ya jikin shi 

Abba ne ya daga woyar 

cikin Dan fada fada yace haba Yusuf

Baccinma bazaka barmu muyi bane?


Cikin sanyi yace kayi haquri Abba 


ajiyar zuciya  Abban yayi gamida katse kiran

Da sauri ya kamo Ahmad dake ta tari da amai cikin azaba ya kamo hannushi yace Abba meyasa kake yiwa biyaye Na fada?

Kai ya jinjina yace 

Haba Ahmad shi Yusuf ya fiye nacin tsiya ne wlh


Cikin Tari yace Ayyah Dan uwana ya zamuyi abinda muke tsoro shi zai faru

Zama Abba yayi a gefenshi cikin dauriya ya rinqa mai nasiha kan ya daina irin zantu kannan

Murmushi kawai yayi gamida konciya 


A firgice cikin razani da rudani Yusuf ya farka daga mugun mafarkin da yayi 

Addu ya rinqa yi da Neman tsari da wannan mugun mafarkin


A hankali ya rinqa jin sautin kukan Aysha daga dakinta kuka takeyi sosai harda sheshsheqa


Da jin haushi ya nufi dakin nata


Abin mmk duk kukan nan da takeyi cikin bacci take yinshi

 

Da sauri ya qarisa gunta 

Ke  ke 

Ke ki tashi sokuwar banza kin konta bakiyi addu,a ba gashi kinzo kina ta mafarkin kina ta yiwa mutane hihu a gari 


Ko motsi bata yiba kuma bata bar kukan ba 

Da qarfi ya ware yatsun shi ya zuba mata mari a fuska


Cikin razana ta miqe gamida sakin kuka mai tsuma rai Wanda har muryar ta ta fara dashewa

Sai tirje tirje take a kan gadon tana wayyo ya Ahmad dina 

Ya Ahmad kar ka tafi ya Ahmad ka dawo 

Sosai take sabbatu da sauri yayi kanta cikin kamata Amman Ina sai zullewa take 

Tana ya Ahmad 

Cikin mmk yace menene hakan ?

Meya samu ya Ahmad 

din ? hannushi ta riqe da qarfi  tana bubuga qafa ya Ahmad ya rasu Hamma Yusuf ya Ahmad dina zai tafi ya barni  ya Ahmad dina ya mutum 

A kidime da zafin nama ya rinqa zuba mata maruka yana fadin ke ki dawo hayya cinki ki bude idanki kiSan abinda kike fada kuma ?


Ahmad yana Raye duk shedanin da ya raya miki ya mutum to yayi qarya 

Abin ya bashi mmk Dan duk da marukan da tasha Sam bata dawo hayyacin taba sai faman qaqumoshi takeyi tana kuka tana rirriqeshi 

Da qarfin take jijigashi 

shi ko gaba daya jikinshi ya mutum tsoro ya rufeshi dan shima  irin mafarkin da yayi kenan

Da qarfin ta kuma janyoshi tana wlh Hamma Yusuf an cemin ya Ahmad ya mutu

Cikin qarfin hali ya jawota jikin shi ya matseta cikin qir Jinshi 

Cikin qarfin itama ta runqumishi tana mai ci gaba da kuka 


 Bakinshi yasa dai dai kunneta ya rinqa mai maita mata innalillahi wa inna ilaihi raji un


Sosai take qara shiga jikinsa hannuta ta daura kan qirjinshi tana ta Dan bugawa 


A hankali ya farajin sanyi Na ratsashi lips dinshi suka rinqa bari

A hankali ya jawo blanket ........



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 


NAYI NADAMA

👇🏻

MI WASMITI page 6⃣1⃣to6⃣3⃣Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Blanket din ya jawo 

Ya rufe su iya qirjinshi 

Hannu shi ya Sa ya jawota jikin shi Cikin hikima ya dago kanta ya daura kan qirjinshi kanshi Na daidai saman  kanta yana shaqar kam shin kanta Cikin wani baqon yanayi ya daura hannushi daya kan Kuma tunta yana Dan shafawa 

Gaba daya jikinsa Kuma Sai rawa yakeyi

Sai wani irin sautin numfashi yake ta fesarwa 

Bugun zuciyarshi Kuma gaba daya ta angizo 

Ita kam Aysha batama San me ake cikiba 

Kukan takeyi tana ta kiran ya Ahmad din nata 

Kukan Na ratsa kunneshi a zahiri shi Yusuf ya tsani kuka a rayuwarsa 

Cikin. Sakin ajiyar hrt ya Dan tura mata yasarsa Cikin bakinta da niyar danne harshenta ta bar kukan 

Amman wani yanayi da yaji tana yi da yatsar tasa yasa shi jin jijiyoyin jikin shi tamkar ana binsu ana tsistinkasu ne 

Yatsar ta kama Cikin qoqarin yin baci ta rinqa tsotsar yasar tashi tana lasarsa a haka bacci ya kwasheta 

Shi kam Yusuf rawan sanyi yake sosai gaba daya jikin shi Sai Bari yake ya kame Dan lips dinshi yana hucewa a kai tsotsor lips dinshi din yake sosai yana mai damqe mararsa gaba daya idanunshi sunyi wuqi wuqi

Sai fam matse cinyarsa yakeyi 

Cikin 

Wahalan ya rinqa zaro yatsar 

Ita Kuma Sai faman tsotsar yatsar take 

A haka suka Dan dauki tsawon lkci 

Sai can ya Dan samu bugun ziciyarsa ta fargar dashi da qarfin ya zare yatsar tashi

Dakinshi ya nufa 

Yana jan tsaki 

A ranshi yake cewa ba ga irin ta ba 

A wani hadaka da yarinyar qarama ta zamarwa mutum damuwa ta wani maqalemin yatsa 

Tana ta tsotsa kamar wata sabuwar mayya 

Hannushi ya Sa ya Dan shafi kanshi gamida shafar hamtsar wondonshi 

Tsaki ya kuma ja 

Aikin ban za yace Cikin quluwa ya nufi toilet dinshi yana fadin 

Ji sokuwar yarinya tasa gaba daya Na jiqe


😝😉 lol su Yusuf anji harshe me taushi nanma harshen kadai akaji tukun😝🙈😂


     NIGERIA

Qarfe 3 daidai Su Yusuf suka dira a tsakiyar gidan su 

Abubakar da ya dauko su yana riqe da jakar yayanshi 

Ita Kuma Aysha tana maqele da hannushi a haka suka isa parlon 

Gidan a cike yake 

Cikin tab zuriyarsu su Dr Umar Ardo ma sunzo 

Suna shi ga parlon Aysha ta saki hannu ya Abubakar din nata cikin kukan  ta fada kan umminta Sai kuma ta saki kuka  su Amira da maryam kam sai murna suke yi suna ruggume da ita usman ne ya harareta ke da allah can ke bakya girma da kuka  kaka ta kalleta cikin yatsina baki tace barta dai mutum kullum kuka kamar wanda aka hada da baqin cikin rayuwa  cikin kukan tace eh ni ba ruwana da ku dama ai kekam kaka nasan matsayi na a gunki ta dan juyo ta kalli Nenne  a hankali tace Nenne INA ya Ahmad ?


Suna hanya Aysha suma sun iso tintini Adam ya tafi dauko su ne da yake su a Yola suka sauqa 

 

Yusuf kam zama yayi can gefen su bayan gaida su Ummi da yayi bai Kuma mgn ba kaka ta kalleshi a yamutsa tace (wairego Na wailego )


Shi dai bai kula taba Sai table baki da yayi a ranshi yace ai nasan so kike nayi mgn ki samu abin fadi 

Mutum bakinsa bai iya shiru 

Ehh din yaji tace eh din ba zanyi shirunba 

Cikin Dan mmk ya kalleta yace kekuma ke da waye ?

Da kai mana ta bashi amsa 

Niko me namiki ?

Ai nasan abinda kake fada a ranka

Toh kin koma Allan musuru kenan?

Oho koma dai me zakace ka fada.


Zaiyi mgn kenan su Abba sukayi slm suka shigo


Gaba daya parlon suka miqe Cikin tsananin mmk da kaduwa ganin yadda Ahmad din ya rame gaba daya ya can za

Sai wani fari da kyau da ya qara yi 

Adam ne ke dafe dashi suna tafiya a hankali hannushi daya Na kan qirjinshi 

Abba da baba bello Kuma Na biye dasu a baya 

 

Cikin sauri da razana Yusuf ya nufi gunsu yana zuwa Ahmad din ya bude mai hannu haka Adam din su duka 3 suka ruqqumi juna  

A hankali Ahmad ya rinqa ayin ajiyar zuciya yana wani irin wahalellen numfashi 

Yusuf ne ya  tallabo fuskar Ahmad Cikin rawan murya yace biyaye 

Meyasa meyasa zaka boyewa zuciyata halin da taka zuciyar ta ke ciki hannushi ya kamo suka taka a hankali Adam Na riqe dashi ta gefen shima Yusuf yana riqe dashi ta daya gefen gaban Abba suka je suka zauna 

Da sauri Nenne tazo kusa da Dan NATA ta zauna Cikin tsoro tace Ahmad meyasa ka boye min abin da ke damuna Wai kana gudun kar hankalina yatashine Ahmad?

Kai ya geda.mata alamar ehh

Cikin tausayin Dan nata tace toh in banda abinka Ahmad

 wane tashin hankali ne ya wuce wannan ga yadda ka dawo 

Cikin qarfin hali ya Dan ja quiwarsa ya qarisa gun Nenne tashi a hankali ya daura kanshi kan cinyarta gami da Sa hannushi ya riqo NATA

Cikin murmushin qarfin hali yace Nenne ke dai ki kasance mai min addu ,a har ranar da zaki zo ki taddani 


Dum zuciyar Yusuf ta buga jin irin furucin da biyayenshi ke furtawa 

Itako Nenne bata fahimci komai ba 

Sai shafa kanshi ta rin qayi tana insha Allahu zan rinqa maka addu Kuma dama kullum Cikin yimaka ita muke 


Maryam ce ta dauko abincin da suka shir ya musu ta rinqa jerawa a gaban su 

A hankali ta matso kusa da Ahmad din 

Cikin sanyi tace ya Ahmad ya jikin 

Hannushi yasa ya jawo nata kanta ya daura kan qirjinshi 

Yace maryama tawa kinga Allah ya nufa alqawarin da Na miki ya cika ko 

Cikin jin kunya tace ehh ya Ahmad

Amman yazu dai tashi kaci abinci


Yusuf ne ya matso kusa dashi shi ya zuba mai abinci ya matsoshi Sai faman tura mai abincin yake kamar yaro qara mi 

Da gyara ya danci loma 4 

Sai kuma ya fara nishi yana ture hannu Yusuf

Yace ya isheni haka banafa iya cin abinci ko kadan

 biyaye Amman kaga yau da ka bani abinci da hannuka Cikin  qaunar Dan uwan taka gashi naci


Aysha dake maqale a hannu ya Abubakar ta Sa hannuta 2 ta sanqalo nashi ta daura hannuta kan damtsen hannushi 

Cikin mmk da qaunar zuciya ta fashe da kuka 

Gaba daya hankalinsu ya koma kanta

Cikin 

Harara Yusuf ya buga mata tsawa yace 

Wlh ko ki rufe mana baki ko nazo Na takamiki wuya

Banza kawai mai kama da mayya 

Dan iskanci ki tasamu a gaba kina ihu

Munafuk...

Bai qarisa zancen nashiba yayi shiru gamida sunkuyar da kai Dan jin furucin Ahmad

Cikin zuba mai ido da alamun tuhuma

Yace 

Biyaye amanar kenan ?

Hannu ya miqa mata Cikin lallashi yace autan Ummi zo nan ki gayamin waya tabaki 

Cikin kukan ta fada kan girjin shi Sai da yayi wani irin ajiyar hrt

Cikin kukan 

Tace ya Ahmad tunda ka dawo baka kula ni ba 

Ka tabbayi kowa ni baka tabba yeni ba 

A hankali ya ronqofo kan kunneta Cikin Rada  

Yace ai 

Ke Aysha matuqar INA Raye a duniya toh INA tare dake ba sai Na tabbayi woni ba

 Amman kuma 

A yanxu lkci ya qarato mana

Rabuwar Na gaba towa 

Da sauri ta daqo Cikin mmk ta zuba mai ido 

Cikin alamun eh gsky nake fada miki 

Yace gatar da nakeso ki min bayan rabuwar itace addu,a 

Cikin sanyi ya kuma kalli Yusuf yace biyaye 

Haka mukayi da kai 

Meyasa ka kasa cika min burina 

Meyasa kake yiwa Aysha tsawa har yau baka bar hantararta ba 

Cikin sanyin jiki yace 

Ahmad yanxu wannan ba shine matsala ta ba 


Ni kuwa itace matsalata

Hannushi ya riqo Cikin kula ya kalli Abba yace Abba meyasa kuka dawo? bayan jikin Ahmad har yanxu na ciwo?


Cikin nitsuwa Abban yace Yusuf Ahmad dinne ya matsa da Sai mun dawo

Gida

Toh a satinnan zamu koma ya fada yana mai kallon Ahmad din 

Kai ya geda mai Cikin cewa toh Allah ya kaimu lkcin  

Amin suka amsa baki dayansu


Baba bello ne ya miqe gami   da cewa toh duk Ku fito mu tafi masallacin maqqariba tayi


A hankali Cikin hikima Ahmad ya rinqa qoqarin tashi Amman INA abin yaki 

Cikin sauri Adam ya kamo shi ya miqar dashi 

Fuskar Yusuf ko fal tsoro ya kalleshi Cikin tabbaya yace bakama iya tashi da kanka ne biyaye Sai in an dagaka?.

Dry yayi wace tafi wuta ciwo a ranshi yace a ni kam INA tashi wlh kai matsalar ka kenan Sa ido

Kai ya jinjina Dan gani quru quru Ahmad ke nunawa shi lfyarsa lau 

Daki 

Nenne suka shiga 

Cikin davara ya kalli Yusuf yace kai turomin maryama kaima jekayi taka al walar

A a muje dai in samaka ruwan

Kai ya Dan juya  yace nave zan iya Malam turomin matata ita nakeson gani kafa San INA hannu kusan wata 3 fa ban jitaba bata jiniba gwara kai taka matar tana katararka


Kallon shi yayi a gyatsine yace toh


 Ayu uwar jaraba bari Na turoma ita ni ban nemi dogon zanceba ka dai tuna a dakin Nenne kake .

Eh ai nasani anan din nakeso Na sama mata jika da zai zame mata madadina kai Kuma ka samu abin gani a matsayina 

Cikin mmk irin mgn ganun Ahmad Yusuf din  ya juyo yana kallonshi  

Ya bude baki Zaiyi mgn kenan 

Maryam ta shigo 

Cikin farin ciki Ahmad din yace yauwa maryama tawa zo nan zo yayanki yaji dumin jikinki

Cikin qaunar mijin nata ta fada qirjinshi 

Hannu bibbiyu yasa ya ruggu mota yana sauqe numfashi 

Ita kam Maryam tama manta da wani Hamma Yusuf a wurin

Shiyasa Cikin shogoba ta maqalo wuyanshi gami da furta mai 

I miss u so much my dear broz

Cikin tau saya musu yace 

Allah ko?

 ehh mana ta fadi gamida narkewa a jikin shi 


Cikin Dan murmushi yace toh daqo daqo kanki ki gani ......

  

Yusuf kam dake tsaye yana kallon su ganin halin da Ahmad din ke ciki😳 yasa shi fita Cikin sauri har yana qoqarin faruwa....


Kuyi haquri masu karatu 

INA jin qorafe qirafenku kan batun Ahmad  Dan Allah kukam kiyi haquri kawai Ku biyoni a hankali zakuga Yadda abin yake 


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA 

👇🏻👇🏻👇🏻

MI WASMITI. page

6⃣4⃣to6⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Ganin da sauri Ahmad ya hada bakinshi da Na Maryam yana mata wani irin kidi memmen kiss 

Yasa Yusuf ficewa 

Da sauri

A ranshi yake cewa kome su Ahmad sukeji a jikin yara qanan nan ne 

Oho musu


A daki kuwa tabbas Ahmad yayi missing din maryama haka  Kuma ya nuna mata hakan a aikace 

Sosai yake ta kissing dinta tako ina 

Itama biye mai tayi 

Gaba daya sun mance da cewa a dakin 

Nenne suke

Cikin buqa tuwa Ahmad yaja hannuta suka fada kan gadon 

Wasa yakeyi da  iya son ransa 

Cikin zaquwa ya fara qoqarin zuge zip dinta 

Da sauri tace ya Ahmad a dakin Nenne fa 

Na Sani maryama Na San a inda nake 

Kiyi haquri yau kawai daga yanxu fashike nan

Gaba daya ya birkice mata ala dole ya samu ya biya buqatar Sa 

Bayan komai ya lafa ne ya daddafe ya shiga toilet wonkan tsarki yayi yayi yishi Kuma suffatul kamal so hade da alwalarsa ya fito


Tin da ya watsa ruwan a jikin shi yaji woni irin sanyi ya ziyarceshi gaba daya jikin shi Kuma yaji kamar an rufe shi da danyen fata 

A take jikin shi ya fara rawan sanyi 


Yana fita rigarsa ya dauka yana zurawa a jikin shi gaba daya jikin shi rawa yakeyi


A Dan firgice Maryam ta matsoshi tana fadin ya Ahmad sanyi kake jine ? ko zazzabi ne ke damunka? 

Kai ya rinqa juyawa Cikin cijewar voice yace shim fidamin darduma 

Zanyi sallah a gida bazan i iya iya iya zuwa masallacin ba gaba daya muryar shi Sai fizga takeyi 

Da sauri ta shimfi da mai 

Yana tada kabbara 

Cikin ikon rabbi duk ya nemi sanyin ya rasa 

Ganin ya daina rawar yasa itama tafada toilet din tayi nata wonka 


Shi Kuma Ahmad yana idar da sallan gaba daya 

Yaji jikin shi ya sake 

A hankali ya rinqa jin suqar zuciyarsa Na tsananta

Lkci daya zazzabi mai qarfin ya rufe shi ga tari 

Yana Cikin haka Maryam ta fito 

Da sauri ta nufi gunshi 

Dai 2 lkcin da ta isa a dai dai lkcin ya fara wani irin amai jinine yake amayarwa guda guda 


😳😩😭😱 da qarfin ta riqoshi Cikin ki dimewa ta rinqa kiran shi ya Ahmad ka tashi tashi mu tafi asibitin Nenne Nenne kuzo wayyo Allah Na ya Ahmad

Gaba daya ta rude Cikin tsoron 

Taji yana kiranta da qarfin 

Cikin fizgar mgn

Yace 

Maryama je ki kiramin Nenne Na da Yusuf da Adam kiyi sauri kice Abba Na da baba bello su zo 


Cikin tsoron da kidima tafita a guje babban parlon ta nufa 

Gaba daya suna zaune shi gowarsu kenan 

Tana zuwa hannu Abba taje ta kamo Cikin 

Kasa mgn Sai nuna mai hanyar dakin Nenne take 

Cikin firgita Yusuf yace Maryam INA biyaye Na 

Ba mgn Sai komawa tayi ta kamo hannu Yusuf din tana ja 

Da qer tasamu ta iya bude baki tace 

Hamma Yusuf

Ya Ahmad zai zai

Bai tsaya ya qarisa jin zancen ta ba ya nufi dakin a guje 

Gaba daya suma suka rufa mai baya


Yana shiga ya hanqoshi konce Cikin galabaita 

Yana ganin Yusuf din ya miqa mai hannushi yana mgn da qar yace biyaye Na zo zo gareni zo inji dumin jikinka Na qarshe 

Da sauri ya qarisa gunshi tallaboshi yayi ya ruqqumeshi a girjinshi Cikin kidima yace 

Baba bello mu tafi hospital

Ya yunquro zai tashi dashi 

Kenan 

Yayi mgn da Dan qarfin yace biyaye barni barni a gida barni Na cika a dakin mahaifiyata a gaban idanta 

Hannu ya miqawa Adam

Wanda tuni yaketa sharar qollah😭

Riqe hannun juna sukayi Cikin tsananin firgita 

Shi Kuma Yusuf ruqqumeshi yayi da qarfin kamar mai tsoron kar a kwaceshi kai kawai yake juyawa yana 

A a a a ba inda zaka

Tafi biyaye muna tare 

Aysha ko riqe da hannushi daya Sai kuka take kamar ranta zai fita 


Cikin qarfin hali yace 

Abba Ku gafarceni ya kuma kallon Nenne da ta fara zama mai daqushewar tunani yace Nenne da sauri ta matsoshi 

Yace shin ba INA gaya miki cewar Allah da ya bakini ya fiki sona ba Nenne ya nake ga alamar kareya a idonki  da qarfin ta riqo hannushi tace Na yarda Ahmad Na San Wanda ya bani kai ya fini sonka .

Toh Nenne inko hakane addu,arku kawai nakeso 

Dan Allah kar ki bin da kuka

Ina ita kam a NEnne  tuni ta fashe da kuka 

A hankali ya juya kanshi gun baba belle mahaifinshi kenan Cikin murmushin qarfin hali yace

Baba Na zan tafi Na barka

Ga Nenne Na ka kulanmin da ita


  hannushi ya kuma riwewa

Baba ka gafarceni idan Na taba yima wani laifin 

Cikin qarfin hali baba belli ya daga kanshi yace Ahmad baka min komai ba Kuma koda kamin Na yafe maka duniya da lahira 

Ahmad Allah ya bada Sa,an tafiya


Cikin sanyi yakira Abba 

Abba Na kuka kake min ? Ya tabba yeshi 

Kai Abban ya jinjina Cikin kuka tsosai yace a a Ahmad kaina nake yiwa kuka Ahmad kaina nake kokawa


Da qer ya daga hannushi ya goge qollah😭 da ke bin fuskar Abban yanan murmushi 

Cikin sanyi yace Abba Dan Allah INA da tabbayoyin  da zan muku 

A yau dinnan Ku daure Ku bani amsar su

Kai ya geda yace INA jinka Ahmad tabba yeni matuqar Na sani to zan gaya maka


Cikin gajiyar hrt yace Abba meyasa kuka hanani Auren Aysha?


Meyasa kukace Aure ya haramta  a tsakanin mu?


Abba meyasa kuka hadata da Yusuf bayan shi uwa daya uba daya suke da ita ?


Kuma yaushe aka daura Auren Aysha da Yusuf?


A hankali ya kamo hannushi yace wadannan  sune tabbayo yin ka ?


Ehh Abba 


Cikin sanyi yace toh Ahmad zan amsa makasu kamar yadda ka buqata

 

Da forko dai Aysha yatace amman ba ta cikina ba cikin gsky da gsky ya nuna Dr Umar Ardo yace wannan shine mahaifin Aysha ma haifiyarta Kuma itace qanwata khadeeja wacce ta rasu 

Da sauri Adam yace Abba me kake cewa? 

Eh abinda dai kaji Na fada 

ya bashi amsa 

Cikin dimuwa yace kenan Aysha qanwa tace uwa daya uba daya

Ehh sosai ma kuwa

Nan ya fara basu amsoshin tabba yartasu


Kamar yadda kuka Sani khadeeja qanwa tace uwa daya uba daya dama a cikin mu mu  6 ne maza 4 mata 2 a gurin maHaifi yarmu mu  3 ne bello Sai ni  Aliyu Sai Khadija 

Itama inna yayan ta  

3 Maza  2mace  1Ahmadu takwaran Ahmad kenan Sai hamisu Sai Aysha 

Khadija qanwata ita aka fara aurawa abokina Dr Umar Ardo bayan sunyi Aure Allah ya azur tasu da namiji shine Adam Sai hydar kamar yadda kuka Sani ana tare kuka girma da Adam

Daga kan hydar bata Kuma aihuwa ba kamar yadda kuka Sani khadeeja Na matuqar qaunar Yusuf a ranta shiyasa tayi alqawari duk ran da ta haifi ya mace to matar Yusuf CE ta bashi duniya da lahira

Ku 

Kuma bayan kunngama primary school dinki Sai aka sama muku makaran ta a bauchi

Inda kukaje kun Sani sai hutu ke dawo daku hutun ma Sai shekara shekara

Kuna js 1 khadeeja ta samu Cikin Aysha 

Cikin ikon rabbi ta goya cikinta lfy ta aihu lfy 

Tana aihuwa ta kira mahaifinmu tace ta aihu Kuma ta samu ya mace tace Kuma yarinyar yar nan matar Yusuf CE Na bashi duniya da lahira

Bayan awa daya da ahuwar jini ya yanke mata a take kafin minti  30 tace ga garinku

A haka mukayi kuka muka haqura bayan wata biyu aka aurawa Dr Umar Ardo goggonku Aysha tana zuwa da shekara data ta haifi Maryam 

Inda itama Kuma tace ta bawa Ahmad  ita amatsa yin mata



Dama a lkcin Kuma  da aka haifi Aysha  Nenne Ku ta aihu yaro ba rai tsaka ninsu sati  3

Shiyasa Sai ta karbi Aysha ta shayar da ita kaji  dalilin da Aure ya haramta tsaka Ninka da Aysha kunsha nono daya mahaifiyar kace ta Sha yar da ita har tsawon shekara daya da woya

6 kafin ta yayeta 

Batun daura Auren Aysha da Yusuf Kuma a lkcin kuna India a inda kuke hada digri dinki Na forko

A lkcin Aysha Nada shekara 13

Bappa Yaya yayi woni irin ciwon da ya firgita mu

Gaba data muka karaya to a nanne yake cemana batun daurin Auren Aysha da Yusuf a lkcin yasa aka daura Auren a tunanin Sa kar ya mutum bai hada Auren ba mu zo muqi cikawa khadeeja wasiyar da ta bashi


Tarin da ya sarqafe Ahmad ne ya tsaida Abba daga lbrin da yake basu

Da sauri Yusuf ya talla boshi Cikin azaba ga aman jini da yaketa kwarawa

Murya Na rawa yace 

Yusuf kaji ko kaji abin da nake gaya maka Na tabbata

Su Abba bazasu hada haram taccen aureba 

Cikin sanyi da daukewar numfashi ga wani zufa da yake ta keti mai 

Yadamqo hannu Aysha ya kamo Na Yusuf ya hada su wuri daya ya tura hannu Aysha Cikin Na Yusuf din da qer Cikin wahala da fixgar numfashi yace... ..


Gaisuwata gareki 

Hajiya Ramatu Allah ya jiqan mahaifinku da rahama👏🏻



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI,WASMITI page 6⃣6⃣to7⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Cikin carkewar murya yace 

Biyaye

Ga amanar da zan bar maka. 

Sai kuma tari ya Dan carkeshi 

Hannushi Yusuf ya riqe da qarfi ya kai kan qirjinshi ..

Tarin yayi sosai kafin ya da lfa gaba daya jikin shi ya sake idansa duk sun fiffito kan goshinshi Sai zufa ke tsatsafo a take fuskarsa ta dauki sheqi da qelli 

A wahalce yaci 

Gba da cewa 

Ban saniba Yusuf ko zaka iya karbar amanata ?ban saniba ko zaka iya riqemin amanar tawa ?

Ban saniba ko zaka iya Sa farin ciki a rayuwar Aysha ?


Yusuf kam tamkar icce ya zama a wurin ya kasa koda qifta idan shi Sai zuciyarshi dake bugawa 

Da qollah😭 da ke bin fuskarsa  

A hankali ya daqo hannushi ya shere hawayen dake bin fuskar Yusuf din ya kamo hannu Aysha ya jawota

 kanta ya daura dai2 kan qahon zuciyarshi

Cikin rawan murya yace 

Aysha kiji bugun zuciyata da zanyi Na qarshe a duniya

Ki ji lkcin da sonki a matsayin matar Aure zai bar jikina kiji lkcin da numfashi zai rabu da gangar jikina 

A yau zaki gsknta cewar kece bugun zuciyata

Kanta ta daura kan qirjinshi ta Saki kuka mai ban tausayi 

Tana ya Ahmad bazaka mutuba numfashi ka bazai bar gaggar jikin ka ba 

Toh ya zanyi dole zan tafi Na barku 

Hannushi ya daqo ya kalli inda Maryam ke 

Durkushe Sai 

Kuka take jikinta duk bari yakeyi 

Cikin qarfin hali da kawaici da haquri da jarumta irin Na Ahmad

Ya miqa mata hannu Cikin sautin qarfamata zuciya yace 

Maryama zo Maryama zo Maryama zo masoyi yata

 cikin kuka ta tsura mai ido tana kallon yadda yake fizgo numfashi Amman wai a hakan yake qoqarin sata farinciki 

Hannu ta Sa ta kamo nasa 

Cikin sakin wani irin numfashi ya jawota ya daura kanta kan daya gefen qirjinshi 

A hankali yace 

Maryama tawa kin zamani Na zamake 

Komai zanyi in babuke bazan ji dadiba 

Maryama kontar da kanki a  jikina inji dumin jikinki Na qarshe Maryama matso gareni ki ga fitar raina a take Sai ga wani irin tari mai qarfin ya turkeshi numfashin ya fara fizqa in ya shaqa baya fitarwa da qarfin yasa hannu daya ya qara damqe hannu Yusuf da Aysha da ya hada wuri daya 

Ya Sa daya hannu Kuma ya damqi hannu Adam Wanda tuni yake kuka kamar mace


Kuka 😭😭😭😭😱sosai Maryam da Aysha keyi Nenne ko miqewa tayi Cikin dimuwa kamar wacce hankali ya bar jikinta zata fita 

Da qarfin Cikin tarin yace Nenne kiyi haquri zaki rabu dani Nenne ki kalli Rabi,u a madadina 


Baba bello ne ya matsoshi Cikin qarfin hali da jarumta irin ta maza Sai kai yake juyawa yana cije lebe 

Yace Ahmad Na yafema duniya da lahira ubangiji ya maka raya Allah ya sadaka da Mala ikun rahama

Ahmadu Cikin cijewar voice ya rinqa maimaita mai LA ila haillah muhammadura sulillah s a w 


Cikin  sanyi ya karbi Kalmar shahadar da maifinshi ke mai 

Abba da yake ruqqume dashi kanshi a kan cinyarsa 

Da qarfin ya ruqqumeshi gami da rumtse idanshi 

Yana fadin innalillahi wa ibailaihi raji um

A hankali Yusuf yaji hannun Ahmad ya saki nashi 

Cikin zaro ido ya kalli fuskar 

Ido Cikin ido 

Sukayi 

Murmushi Ahmad din yayi Cikin sanyi yace 

Biyaye ga amanar Aysha 

Sai kuma ya daura da Kalmar Shahada 

Idanshi suka koma suka kafe murmushin da yayi yana kan fuskarsa


Dr Umar ardo ne ya rinqa mai mata kullu nafsin za ikatul maut


Nenne dake gefe cikin gigita tace shike nan Ahmad kaima kabi yan uwanka Ahmad Na rabu da kai Sai kuma ta saki wani irin kuka mai ban tausayi 

Gaba daya dakin ya rude 

Hatta Abba kuka yake sosai ringume da gawar Ahmad din 

Adam kam 

Tuni ya fada kan Yusuf Cikin riqe hannushi 

Yana 

Shike nan Yusuf Ahmad ya tafi ya barmu Yusuf mun rasa Ahmad

Sh kenan yanxu dagani Sai kai Yusuf Ahmad ya tafi ya barmu 


Maryam kam da Aysha qaqqame qawar sukayi Cikin firgici da rudani 

Suke kuka kamar ransu zai fita 


Baba bello ne da Dr Umar ardo sune suka samu Dan qarfin jikin miqewa baba bello kam Nenne ya kamo ya ruggume Cikin rawar murya yace haba ruqayyatu kar kibi Ahmad da kuka mana shin baki ga Rahamar da Allah ya mishi ba cikawafa yayi da kalmar shahada 

Allah sarki Nenne Sai fafawa tayi jikin mijinta ta rinqa kuka mai ban tausayi


Cikin kuka Abubakar ya riqo hannu marya da Aysha da nufin ya jasu su fita 

Da qarfin Maryam ta fada qirjin shi Cikin n kuka tace ya Abubakar da gaske ya Ahmad ya rasu Na rasa ya Ahmad

Kai ya rinqa juya mata yana zubda qollah😭ya jata suka fita 

Ummi CE ta matso Cikin kuka tasa hannu ta rufe mai idanshi

Su Usman da Rabi,u kam da abdul dama tuni suka koma parlon kuka suke kamar yara 

Ummi CE ta miqe gami da kamo hannu Aysha da nufi su fita 

Tana janta Sai gani tayi tayi yuu

 Sai fadawa kan Yusuf tayi a sume

cikin firgita Ummi ta rinqa kiranta tana jijjiga ta Amman ina 

Goggo Aysha CE tayi tunanin debo ruwan ana Dan shafa mata a fuska Amman INA ko matsi bata yiba 


😱😫dimuwa. Da firgici da tsoro mai matuqar tsananin su suka sauqa kan rayuwar Yusuf inda ya zama tamkar mai Ciwon mantuwa 

Lallai kuka ma Rahama ne 

Shi kam Yusuf yau yake buqatar kuka a rayuwarsa Kuma a yau kuka ya mai tsada 

Zuciyarshi ta kasa tuno komai qoqol warsa Kuma gaba daya ta tsaya bata aiki kanshi da jikin shi duk jinsu a juye suke🙃 

Ido kawai Yusuf ke binsu dashi Sai hannushi da yasa ya damqi hannu Ahmad din 

Su Ummi yake klo Cikin zare idon fuskar Aysha yabi da idonshi Cikin yanayin rashin sanin abin da akeyi


Hydar ne ya zo ya ciccibi Aysha yayi dakin Ummi da ita kamar gawa 


Yusuf kam yana zaune a gun riqe da hannun gawar  

Dr Umar ya ja Abba ska fita tare 

Fuskar Ahmad din ya zubawa ido Sai ya juya ya kalli Adam dake durqushe a gefen shi yana ta kuka 

A haka har zuwa tsawon wani lkci 


           Allahu Akbar 

Lbrin rasuwar Ahmad

Ta kasance tam kar sauqan aradune a zuqatan yan uwa da abokan arziqi 

Lbrin ya zama tamkar sauqan qanqarane  ne a jikin mutane 


Kafin wani lkci gida ya cika tab da yan uwa da maqota da abokansu 


Baba Ahmadu ne da Dr Umar 

Suka shigo 

Daukar gawar Dan 

Aje ayiwa gawar wonka ayi mata sutura a kaita makoncin ta


Cikin tsoro baba Ahmadu ya daqo yana kallon yadda dr Umar ke ta yin qoqarin cire hannu Ahmad Cikin Na Yusuf Amman .......



Allah sarki rayuwa Dan Adam Dan mutuwa  nima kaina Aysha Ali Garkuwa rasuwar Ahmad ta zame min fami a zuciya ta ta famimin rasuwar yan uwana shiyasa wlh bazan iya ci gaba da  typing ba har Sai zuwa gobe 😭😭😭


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI,WASMITI page 7⃣1⃣to7⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Amman gsky Baku kyautamin ba masu karatu ya kamata ace tsakaninmu Marubuta da ma karanta a ringa yiwa juna uzuri 

Daga jin   Ahmad ya rasu Sai wasu suka rinqa qananan maganganu wasu harda kirana a woya Wai meyasa zan kashe Ahmad ai wanna NAYI rashin imani Haba masu karatu kukam kuyi Haquri maNa Ku Biyoni A  hankali  ai zakuga yadda zan tsara mana abin masu bina ta prvt chart kowa da irin qorafin da yake min

Dan Allah mu rinqa yiwa juna uzuri

Wasu harda cewa ai gwara  akashe Yusuf😫

Ina Baku haquri wasu nace Na sasu kuka sosai  karku damu zakuyi dry a gaba fiye da yadda kukayi dry a baya zaku Sha nishadi fiye da zatonku

Ku dai Ku hira Yusuf ya shigo hannu😍😘🍌🙈😝




Jan hannu Yusuf din yakeyi yana qoqarin rabewa a na Ahmad din shiku ma Yusuf Sai damage hannu da yayi yana mai zuba musu ido 

Kamar zaucecce a hankali Dr Umar ya zauna kusa dashi Cikin tausasa zuciyarshi yace 

Yusuf saki hannu Ahmad

Kaji sakeshi a yanxu ba wani gata ko 

Alfarma da zamuyi mishi sama da mu kaishi Cikin qabarinshi 

Baiyi mgn ba bai Kuma sakiba Sai zuciyarsa da ta rinqa bugawa da qarfin qarfi 


Hannu nashi ya jawo ya dawowa kan qawar yasa yatsunshi ya rinqa bude tafin hannu da Yusuf do ya damqe 

Shi kam Yusuf kallon shi kawai yakeyi 

So ya yake yaji shi shima a mace ko zaiji wani a bu a ranshi ji yake dama haukacewa yayi 

A hankali zuciyarsa ta fara tuno mai abinda kalaman baba Umar ke nufi a take Kuma Sai jikin shi ya rinqa karkarwa 

A haka suka samu suka dauke gawar 

Cikin kuka Adam yabi bayansu 

Shi kam Yusuf a wurin ya zauna kamar dasashi akayi 


Acan Kuma akayiwa gawar duk abin da ya kamata kafin ma gari ya waye anyi komai an gama 


Washe gari da safe wannan lbrin ya iski Anuty Sadiya 

Duk da mijinta ta ya ji dashi akayi komai Amman ya rasa ta INA zai fara kawo mata wannan zance 

Sai da safen yace ta shirya suje gida 

Su gaidasu 

A mota ta kalli mijinta Cikin sanyi tace Abban Yumin.

Na,am ya amsa mata Cikin sanyi 

Sai kuma tayi shiru gamida dafe qirjinta 

Hannushi yasa ya kamo nata yace 

Kin kirani kin Kuma yi shiru 

Kai ta daqo ta kalleshi Cikin rawar murya da alamar kuka zatayi 

Tace Abban Yumin

Zuciyata Na tsinkewa tsoro nakeji ban San meyasa ba tun jiya nakejin faduwar gaba 

A hankali ya jawota ya manna ta a jikin shi cikin fargaba yace ki rinqa addu,a ki Kuma kasance mai yarda da gaddara 

Dai dai nan yayi parking a farfajiyar gidan nasu 

A hankali ta zame jikinta ta fito 

Cikin tsoro da firgita ta bude idanta da kyau ganin gaba daya harabar gidan a cike yake da mutane a take qafarta ta fara rawa Cikin tsoro ta juyo gareshi tana Abban Yumin me ya faru me kake boye min 

Hannushi ta riqe tana jijji gawa da qarfi tana ka fada min INA Abba ban ganshi anan ba 

Allah sarki

 ita Sam bata kai tunanin ta kan qaninta ta rasa ba 

Rabi,u dake gefe ne yayi saurin isowa gareta durqushe wa yayi a gaban ta Cikin kuka yace Anuty Sadiya ya Ahmad ya tafi ya Ahmad ya tafi ya barmu 

Ido ta zaro Cikin tsoro Sai kuma tayi Cikin gida kai tsaye dakin Nenne ta nufa 

Can ta hango Ummi da sauri taje gaban ta ta fada Cikin kuka tace Ummi 

Me nakeji Ummi meya samu Dan uwana wayyo Allah wayyo Dan uwana wayyo Nenne Na wayyo cikina Ummi shike nan Na rasa Dan uwa 

Adam ne ya kamo hannuta Cikin kuka yace Anuty Sadiya mun rasa Ahmad Anuty Sadiya Ahmad ya tafi ya barmu 

Gaba daya suka ruda parlon kakace ta tashi itama Cikin kuka ta kamo hannu Sadiya 

Da Adam tayi Cikin daki dasu 

 

Suna shiga Sadiya ta hango Yusuf Wanda tun jiyan bai tashi a wurin ba sai sallan asuba da ya tashi yayi da taimakon hydar

Tana hoggo shi ga Nenne a gefenshi 

Tana riqe da hannushi tana fadin 

Haba Yusuf kayi mgn mana Yusuf katashi kaje qun baqin da sukazo yi maka gaisuwa 

Haba Yusuf fushi kakeyi da yin ubangiji ne 

Shin ase bazaka rungumi qaddara ba 

Yusufa mufa musul Maine 

Shi kam Yusuf ido ya zubawa Anuty Sadiya

Ita Kuma gabanshi tazo ta durqusa ta kamo hannushi ta kifa kanta kan cinyarsa ta saki wani kuka mai ban tausayi 

Tana kuka tana fadin Yusuf ya zamuyi Allah shi yabamu Ahmad Kuma shi ya dauke shi 

Dama kullum haka Ahmad ke gayamin ai Wanda ya Baku ni yaga fiku sona Anuty Sadiya ki dena damuwa da halin da nake ciki ase Ahmad duk maganganu da yakejin wasiyace


A hankali ya daura nashi kan kan kafadarta 

Yasa hannushi ya riqe nata Sai ya kuma kura mata ido 

Yana jujjuya kai 

A hankali tace Yusuf kayi min mgn ma ko zanji sanyi a raina dama kullum Ahmad cemin yake ko ya mutum kar Na damu gaka ga Adam da Abubakar duk abin da nake so zaku min 

Kai ta juya cikin kuka tace Ummi INA Abba Ummi a wane hali Abba yake ?


Cikin duseshewar murya tace Sadiya 

Abba tun a Daren jiya ya tafi Abuja shida Hydar Kuma yau dinnan zasu wuce  India

A Dan tsorace tace Ummi Abba ne ba lfy ko ehh Sadiya abbanku baya Cikin hayya cin sa 

Hawan jinisa ne ya tashi

Sai hawayen ke bin fuskar ta 


Adam ne ya kalleta Cikin sanyi yace anty sadiya ko zakizo kije dakin Ummi ki zauna da su Maryam da Aysha da Amira suna can Sai kuka sukayi ba mai lallashin wani

Cikin sanyin jiki ta nufi dakin Ummin 


Ayyah Maryam da aysha suna zaune tun jiya da Aysha ta farfado suke ta kuka abin tausayi Aysha abin ya hadu mata jiya tasan ba ummi

bace mahaifiyar ta kuma a jiya ta rasa ya Ahmad dinta Kuma a jiya tasan mahaifiyata ta rasu a lkcin aihuwarta 

 Ganin Sadiya yasa ta fada jikinta tai ta wani sabon kuka

Ta ruggumi meta nan sukayi ta kukansu 

Da dyar dai suka samu suka tsagaita 

Da kukan 


Rayuwar gidan ya canja musu gidan ya koma tamkar ba kowa Sai masu zuwa gaisu da zaran bakin suntafi kuma to shike nan gidan yayi shiru

Rayuwar Yusuf ta sauya ta koma abin tausayi baya mgn da kowa komai za acemai da kai ko ido yake bada amasa duk masifar Na ta Yusuf da bala,I da mishkilanci yanxu babu su 

Ya koma abin tausayi Baya iya mgn 5 lafiyeyyu 

Komai ya rigada ya gama sauyawa 

Aysha kam ko yaushe Sai ta shiga toilet tayi ta kukanta Sai fuska ta kumbura Maryam Kuma yanxu bata iya kukan ya rigada zuciyata ta bushe 




Yau ne akayi sadakan  7  gaba daya baqi sun waste su Bappa Yaya ne kadai suka rege basu tafi ba 


Yau kwana 10 da rasuwar Kuma yaune su Bappa Yaya ya zasu koma 

Shiyasa da safe ya Tara zuriyar tasa

Bayan ya gama musu nasiha 

Ya kalli Yusuf da Adam yace 

Dudabe 

Na,am ya amsa cikin

sanyi 

Ido ya zuba mai cikin tausayawa yace 

Yanxu me kakeyi a qasarnan ?

 Kai ya sunkuyar gami da cije lips enshi yace me zanyi Kuma a qasarnan bani da abin da zanyi 

Toh ka shirya kaida matarka Ku koma kaje kaci gaba da kara tunka

 Aysha dake takure a jikin Nenne Cikin kuka tace Dan Allah Bappa Yaya Ku barni ni bana son komawa can 

To me zaki zauna kiyi a nandin ?


Ni dai banson komawa canne 

Ta bashi amsa Cikin kuka

Shi dai Yusuf shiru yayi Dan yanxu qoqolwarsa bata fiye gane me ake yiba 


Haka kuwa akayi randa akayi kwana 15 da rasuwar a ranar baba bello ya kamma lawa su Yusuf shirin tafiyar su 

A Kuma ranar ✈ jirginsu zai tashi


A hankali suke fitowa daga parlon suna zuwa harabar gidan  

Bayan su Rabi,u sun gama Sa musu kayansu a but 


Cikin sanyi Yusuf yaje ya durqusa gaban baba bello  murya Na rawa yace baba zan tafi 

Kanshi ya dafe Cikin qarfafa mai guiwa yace Allah ya kaiku lfy Yusuf

 amin yace 

Gami da miqewa yaje gaban Nenne itama ta mai addu,a 

A hankali ya qarisa gaban umminshi 

Ya durqusa guiwa bibbiyu yace Ummi zan tafi Amman bazan sake zuwa qasarnan da wuriba 


Cikin

 ajiyar hrt

Ta kamo shi ta tsaida shi 

A hankali  taja hannu Aysha ta samai Cikin nasa tace to ga amanar  da Dan uwanka ya baka

Yana Cikin qabarinshi 

mu kuwa mune masu ganin irin yadda zaka riqe amanar da ya baka a dai dai lkcin da ransa yake fita a jikin shi 


Hannu yasa ya kamo Na Ayshan ya juya Cikin Rashin sanin me zaiyi 

Ya jata 

Suka qarisa gaban Adam ya ruggume juna sukayi musabaha 

Ya kalleshi Cikin sanyi yace biyaye Allah ta sadamu kan alkhairi 

Amin yace dai 2 lkcin da suka shiga mota 


Usmanne da Rabi,u suka kaisu airport


3:37 pm jirginsu ya tashi 



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI,WASMITI page 7⃣4⃣to7⃣5⃣ Na Aysha s Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Allah sarki rayuwa mai juyawa 

               A

 cikin jirgi 

Yusuf ya  zauna kan kuje rarsa ta number 24 yayinda Aysha Kuma nata number 23 ne 

Nata kujerar itace kusa da window jirgin 

A hankali Yusuf yake takawa har ya isa wurin zaman nasu 

Jiki a sanyaye ya zauna 

Gamida yin taqumi da hannushi daya ya Sada kanshi qasa 

Bai tuno komai Sai ran da suka dawo India a lokcin da suka kamma la kara tunsu

A wannan jirgin suka dawo a wadannan kujerun suka zauna inda ya ke zaune anan ya zauna a wancan lkcin Na gefenshi Kuma biyayenshi ne 

A hankali ya zubawa sit din ido 

Zuciyarsa Na suya 

Sai cije lebenshi yakeyi sabida kuka yake son yi Amman kuma ya kasa samun kukan 


Yana Cikin wannan halin  

Yaji abi Na diga kan wuyanshi 

Hannushi yasa ya shafo wurin kamar ruwa yaji 

Kai ya dago ya zubawa Aysha dake tsaye a gefenshi dafe da kan kuje ranshi  

Hawaye wannan Na koran wancan 

 Kallonta yayi Cikin shawa,a 

A ranshi yake cewa 

Kinji dadi da kika samu kina kuka kina zubda qollah😭 nasan koba komai zakiji sauqi a ranki


Sanarwan da akeyi Na koma ya koma gun zamansa jirgi zai tashi shine ya dawo dashi daga tunanin da yakeyi 

Ido ya sake zuba mata

A hankali ya daqo 

Hannushi ya kamo nata 

Ya jawota

Gami da Dan Jan qafafunshi 

Dan ta samu gun wucewa

Kan sit din gefenshi ya yaja hannuta ya zaunar da ita 


Ita kam Aysha ido cike da qollah😭 ta bi fuskar shi da kallo

Lkci guda Kuma ta tuno 

Lkcin da zasu tafi wancan karon 

Da ta tsaya a kanshi haka tana kuka

Cikin masifa ya rinqa surface mata bala,I harda yarfa mata mari yana mayya kawai kin wani tasa mutane a gaba kina kuka toh kanki zakici ai tunda kikayi kuskuren yadda kika biyoni toh  wlh baqin jaki Sai ya fiki jin dadi

Cikin tsawa ya jawota ya tura  a wancan lkcin


Tana Cikin tunanin taji jishi 

Cikin wani irin voice yace 

Kija bel dinnan ki saka 

Kai ta sunkuyar Cikin zubar qollah😭

A hankali 

Jirgin ya rinqa 

Qugi da Dan diri

Cikin tafiya a hankali ya rinqa Dan tashi sama 

A hankali  Yusuf ya maida kanshi jikin sit din ya lumshe idansa jikin jin wani irin azaba a karo Na forko da yaji yana qaunar barin qasarsa ta aihuwa

A karo Na forko da yaji ya qagu ya daina shaqar iskar qasar 

 A ranshi yakeji to me y rege masa a qasar nan

Babu ya fada a bayyane 

Gami da bude idanshi da jin zafi a ransa

Ita kam Aysha ta window take yiwa qasar ta wani irin kallo da jirgin ya gama tashi sama 

Ta kifa kanta jikin window ta saki kuka mai ban tausayi 


Ido ya zuba mata gami da jinjina kai

A ranshi Kuma cewa yayi kuka ma Rahama ne bazan hanaki ba 


A haka Cikin kukan bacci ya debeta 

Yayinda shi Kuma Sai ajiyar hrt da yake tayi 

9:00 Am agogon Nigeria

Dai2 da 11:00Am saudiya


Jirginsu ✈yayi  landing Cikin birnin Madina

A hankali fasinjoji suka rinqa fita

Ido Yusuf ya rufe a sannu Kuma ya budesu

Kan fuskar amanar Ahmad dinshi 

Cikin sanyin murya yace 

Ke 

Ke tashi mun iso

Kamar a mafarki taji muryar shi 


Sai kuma taji tsoro Dan tuna wancan Zuwan nasu inda ya rinqa zuba mata mari Cikin fushi yace ko ki taso ko Na tafi Na barki 

Bira alaqaqai kawai

Banza mayya..a wancan lkcin

 

A hankali ya katse mata tunani da takeyi

Muryar shi ta kumaji 

Cikin Dan kauri yace 

Ke INA mgn kinyi shiru

A hankali ta miqe 

Tabi bayan shi 

Har inda aka ta naji motici Dan ma tafiya wani ma aikaci Na biye dasu riqe da jakarsu 

Har zuwa gun motar

Suka shiga suka tafi 


A dai dai harabar wani qaton gida mai kama da ma aikata part part sun kusa 7 


Abakin qofar su direban ya tsaya dai2 bakin qofar shiga 

Suna fita

Yaja motarsa ya tafi 

Jakar ta ya zubawa ido Cikin ranshi yasan bazata iya dagawa ba Amman kuma shima ga nashi 

Sai kuma ya kalli inda take ta tsaya Sai rawan sanyi take Dan daga dukkan alamu anyi ruwan samane ya dauke Sai walqiya akeyi da iska mai sanyi da take kadawa 

Hannu yasa ya dauki jakar tata yasa qafa ya tura mata nasa


Ya juya yayi gaba a hankali tabi bayan shi


A parlo ya ajiye mata nata ya karbi tasa ya juya yabi Cikin Dan koridon da zai Sa dashi da parlon shi

Yana shiga ya fada kan 3 str Cikin 

Yanayin shi da yafi kama da maraya 

Ido ya lumshe ba tare da yayi bacci ba zafi yakeji sasoi a rayuwarsa 

A hankali ya daqo phone dinshi Nenne ya kira 

Tana dagawa tace Yusuf kun isako ? ehh yace mata

Gamida cewa ki gaida baba Sai da safe 

Toh Allah ya bamu alkhairi tace dashi gamida katse woyar 

Shi kuwa a nashi gefen kashe phone din nashi yayi gaba daya


Ita kuwa Aysha da qyer taja jikinta ta tafi bedroom dinta 

Kan gado ta fada Cikin kuka a haka a ranan ta kwana kuka 

Shi kuwa Yusuf kukan ya nema ya rasa shiya sa ya tashi Cikin rawan jiki yaje yayi alwala yazo ya rinqa nafilfili 

Idan yayi sujjada ba abin da yakeyi Sai nemawa Dan uwan shi gafara


Washe gari da safe 

Abokan Yusuf laraba suka rinqa zuwa mai taziya da dama daga cikinsa sun San Ahmad 

Wasu sunsu Kuma insun zo kuka sukayi kamar zasu suma


Akwai wasu abo kansu su 2 Sulaiman da Bashir Wanda tare sukayi karatu a inda

Kuma suma yanxu suna Jami,atul madinan ne suna kara ilimi

Bashir Dan Katsina ne Kuma tare da matarsa sukazo 

Mai suna Zakiya

Tunda sukazo 

Sulaiman yake kuka kamar mace dan shi ya shaqu da Ahmad sosai kusan halin su iri daya 

Bashirne ya rinqa Dan bashi baki yayinda dashi ma yake ta sharar qollah😭

Shi kam Yusuf Sai cije lebe da yakeyi 

Cikin daburcewar murya yace Zakiya ki isa gun qaunar Ahmad tana ciki 

Ku gaisa 

Toh tace mai gami da miqewa

Tayi candin 

A hankali tayi SLM Cikin parlon ba kowa 

Ido ta Dan bude Cikin zubar hawaye tana kallon parlon a shirya yake tsafta ba datti ko kadan komai Na parlon farine  da jaa gashi labulayen suna sasake shiyasa Sai parlon yayi dubu kamar dare 

SLM ta kumayi gamida zuwa jikin gini ta kunna wutan tsakiyar parlon 

Ba kowa har ta juya zata fita Sai kuma taji sautin kukan a cin bedroom din 

Juyawa tayi ta shiga dakin 

Kan gado ta hangota tayi rufa da ciki Sai kuka takeyi tana 

Ayyah ya Ahmad yanxu mun rabu kenan bazan Kuma ganin ka ba

Zuwa tayi ta zauna gefen ta Cikin sanyin murya 

Da qoqarin danne nata kukan tace 

Kiyi haquri Aysha ki daina bin Dan uwanka da kuka kiyi ta masa addu ,a shi yafi buqata a gareku ba hawayen ki ba

Dagowa tayi tana kallonta Cikin rashin Sani 

Fahimtar hakan da Zakiya tayi shiyasa ta kamo hannuta

Tace 

Ni suna Zakiya ni matar abokin Yusuf ne sunan mijinta Bashir 

Muma muna qasar nan Kuma tare muke da mijina yana can gun Yusuf dinne .


Allah sarki Aysha rashin Dan uwa shiyasa a take taji zaki tamkar Maryam da Amira 

Cikin hawayen tace kinsan ya Ahmad dinako ?

Eh Na sanshi Aysha

!

Ayyah to shinefa ya rasu.

 ehh Na Sani Aysha 

Kibar kukan Dan Allah

Wlh nima zaki Sani kuka

Kai ta jinji na gami da share hawayen ta tace 

Ni ma banson yi mishi kukan kasawa nake in banyi kukan ba ji nake kamar zan mutu

Cikin tausa yawa tace ki rinqa addu,a kinji ko Aysha 

Toh tace Cikin  goge qollah😭

Haka dai Zakiya tayi ta lallashinta

Har ta samu ta jawota suka shiga kitchen

Suka danti girki mai Dan sauki 

Dan dama ba abin da babu a cikin kitchen din

Ita ta dauka ta kaiwa su Yusuf

T juya zata tafi Bashir yace in kin gama kizo mu tafi 

Toh tace Cikin sanyi Dan tanajin tausayin yadda Yusuf da Aysha zasu kasance su kadai


         A 

Parlon ta zuba abinci ta matso ayshi cin lallashi tace 

Ayyah Aysha ki matso kici abinci kinji ko 

Kai ta girgiza tace bazan iyaba bakina daci nakeji

Ta Dan sunkuyar d kai tace Aysha bakya son nazo gobe ko ?

Da sauri tace a a wlh inaso 

To kici abinci 

Ayyah Zakiya nima ina son ci bazan iya bane shi yasa

Miqewa tayi gamida yin Cikin kitchen din furts ta dauko ta kawo mata

 tace gashi ki daure kici koda inabinnan da Dan dabino ga Apple 

Karba tayi ta danci 

Sannan sukayi sallan insha


A parlon Yusuf Kuma shi da sulamai sun kasa cinnkomai shima Bashir sai dan tea ya Dan Sha


Bashir dinne ya miqe gami da kallon Yusuf

Cikin sanyi yace 

Yusuf zamu tafi Sai gobe in Allah ya kaimu insha Allah zamuzo

Amman dan Allah Yusuf ka rinqa Sa dauriya a ranka Yusuf ka rege tunani Dan Allah kar ya maka illa

Kasan kana da matsalan zuciya

Kai ya sunkuyar Cikin ceje lips dinshi da gaba daya yanxu sun kubbura sunyi jazur sabida rashin kukan da bai samu yayinba

 Sai yayi ta cizon lips din nashi

Haka dai Bashir ya rinqa bashi baki 

Sannan suka wuce parlon Aysha 


Sulaiman kam yana ganin ta Sai hawaye Dan shi yasan irin son da Ahmad yake mata 

Kuma itama tasan Sulaimanu

Durqusawa tayi a gabanshi tana zubda qollah😭 Cikin rawan murya yace 

Sannu Aysha sannu da rashi  Allah ya jiqanshi da Rahama 


Amin ya rabbi ta fada Cikin kuka shima Bashir ya gaida ta sannan suka fita suka tafi


Shi kam Yusuf parlon shi ya koma Cikin kuncin zuciya 

 Yadda ya kwana jiya hakama ya kwana yau

Washe gari da safe Bashir da Sulaiman sukazo Zakiya kuwa sai da ta tsaya tayi musu girki sannan ta taho

Daga ranan haka sukayi tayi Sai randa suka cika kwana 7 da dawowa sannan suka daina zuwa 

Su wuni Sai dai duk da haka kullum zakiya ke musu girki ta bawa Bashir ya kawo musu duk da baci sukayi ba yadda  Bashir ke kawo shi haka yake zuwa ya

 dau keshi


Sannu a hankali yau watansu daya da dawowa 

Rayuwa ta juya ta canxa 

Yusuf Dan qolisan nan gaba daya ya zama abin tausayi  banda wonka ba abinda yakeyi ko mai bai shafawa

A hankali Dan sirinrin sajenshi Na ya rinqa qaruwa yana yawa yana bajewa ga wani irin rama da yayi duk ya canxa sai dai kyau kam kamar qara mai akeyi

kullum da safe yana dawowa masallaci Sai ya leqa gun Aysha a cewarsa amanarsa CE ita

Duk da ita kam bata ganin shi


Wata ranar jummah da daddare misalin qarfe 2

Na dare Aysha dake parlo Wanda a yanxu parlon ya zama dakin kwananta Dan 

Da zaran tayi bacci a bedroom sai mafarkin ya Ahmad dinta ke bibiyarta

Shiyasa ta dawo parlon

Inda zata kwana kuka yayinda zata kwana jin sautin karatun Yusuf Kuma a parlon shi

Sai dai abin tsoro da firgici jin a yau ba sautin karatun  Yusuf din take jiba Cikin firgita ta tashi da sauri ta nufi parlon bashi..... Tsoron ta ya qaru ganin abinda Yusuf din keyi

 ta kidime ta rude ta kidime da sauri tayi kanshi..........


I love you all my frns😘😍😘

Allah ya barmu tare


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI,WASMITI page 7⃣6⃣to7⃣7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Kina raina Asma,u Adam admin din zauren guzurin gobe alqiyama😘😍

 I love you all my frns😘😍



         Kuka yakeyi cikin fitar hankali kuka mai ban tausayi gaba daya ya fita hayyacinsa 

Jikinsa kab zuface ke tsatsafo mai tako ina 

Ya zaune kan sallayah runqqume da qur,ani mai girma a jikinsa ga qaton photo su su 4 Shi da Ahmad din da Adam da Abubakar 

Hannushi yasa ya dafe kanshi da hannu bibbiyu

Cikin kuka 

Da ya samu rabbi ya sauqo mai dashi a  yau 

Cikin dashewar murya yaketa nanata wayyo Allah Na 

Wayyo Allah

Ya rabbi ka bani ikon cin jarra bawar da ka jarab ceni da ita ya ubangiji kayiwa bawan ka Ahmad Rahama rabbi ka haskaka mai qabarinshi 

Kanshi ya dafe da hannushi daya gaba daya jijiyoyin kan nashi sunyi rudu rudu

Hannushi daya Kuma qirjinshi ya dafe da qarfi

Gaba daya jikin shi rawa yakeyi 

Sai zamewa yakeyi a kan carpet din 

Cikin wahala ya rinqa kiran Ahmad shi kenan mun rabu 

Ayyah biyayena 

Bani da wani masoyi kamar ka bani da mai gayamin gsky kamar ka bani da Wanda nakeji a jikina kamar ka Kaine maisani farin ciki


Tsoro sosai ta ring a ji ganin yadda ya fita hankalinsa 

Da sauri itama Cikin 

Kukan taje 

Gaban shi ta zare qura,anin a jikin shi 

A hankali ta zo gaban shi ta durqusa 

Cikin kukan 

Ta rinqa kirashi 

Hamma Yusuf kayi shiru Dan Allah ka daina kuka 

Meyasa bazaka yiwa ya Ahmad addu,a ba 

Wayyo Ummi Na ya zanyi kuka ta kamayi sosai Cikin kidiman 

Ya jawota jikin shi 

A yau yanaji bai da kowa a duniya Sai 

Ita tunda itace ke kusa dashi 

Gani yake ba Wanda zai San irin zafin da yakeji Sai ita 

Shiyasa 

Ya matseta da qarfi a jikin shi 

Kukan yakeyi kamar yaro 

Itama kukan takeyi kamar zata zauce 

Cikin kukan tace 

Wayyo Ummi Na 

Wayyo rayuwa ta mana dubu 

Wayyo Hamma Yusuf ni dai ka maida ni 

Gida 

Kanta ya manna kan qirjinshi 

Yana nima Sai dai su Ummi suzo suga gawata zuciyata zata fashe ban San ya zanyi ba 

Kanta ta daqo ta zuba mai ido lkci daya Kuma numfashin shi ya fara daukewa 


Cikin tsoro ta miqe tana tsakiyar parlon tana bubbuga qafa 

Tana kuka sosai ganin gaba daya kamar mutuwa shima zaiyi 


Gaba daya ya fara murdewa kanshi Sai juyawa yakeyi da sauri ta zauna gami da Dora kanshi kan cinyarta

Gami da sakin kuka 

Woyar ta ta laluba a wurin 

Zakiyi ta kira 

Kiran forko har ya tsinke bata dagaba Sai a nabiyu 

Kiran Na shiga 


Bashir da yanxu ya fito wonka bayan ya gama shanawa da matarsa ita Kuma yana shiga tayi 

Bacci 

Shisa har kiran ya tsinke bata   dagaba

Kiran Na qoqarin katsewa 

Bashir ya daga 

Woyar 

Cikin 

Kuka tace 

Hello zakiyi

Zakiya Hamma Yusuf ki gayawa Bashir Hamma Yusuf bai da lfy Na rasa yadda zanyi 

Da sauri 

Bashir yace 

Aysha 

Kuna INA meke damun Yusuf din 

Cikin kuka tace Bashir kazo Dan Allah kazo kawai

Toh yace gamida katse kiran


Da sauri sauri  ya zura Riga hannu kawai yasa ya daqo zakiya Cikin tsoro ta miqe tana lfy honey ?

Tashi tashi kisa kayanki Yusuf ba lfy 

A tsorace ta shirya suka fito 

Suka nufi anquwarsu Yusuf din mai suna Ibrahim Khalil Wanda Ya kasance yana Dan kusa da masallacin Annabi 

Shiyasa anquwar ba kewa darene kamar rana 


Suna shiga Aysha ta juyo Cikin zubda qollah😭 tace Bashir kalli kalli yadda yakeyi 

Da sauri bashir

Ya zauna gami da kamo shi 

Kanshi ya rinqa shafawa wani Dan farin mgni gamida zaro wata yar allura qarama ya zira mai 

A take Sai ya kuma rinqa mimmiqewa kamar Wanda ranshi zai bar jikin shi 

Sai  daddamge hannushi yakeyi

Yana juyawa 

Ganin haka yasa Aysha qara rudewa Cikin kuka ta durqusa a gaban shi tana hama Yusuf ka tashi katashi bari in kirana mana su Abba su zo su dauke mu

Phone dinta ta Kuma karba a hannun zakiya 

Baba bello ta kira 

Cikin 

Mmkin wake Neman shi a Daren nan

Da sauri yayi pikin ganin Aysha CE 

Cikin kuka tamai bayanin a bindake faruwa

Sosai yaji zuciyarsa ya tsinke  A ranshi yace ya Allah ka rufa mana asiri 

Allah ka hanamu sake ganin wani duhun a wannan rayuwar

A fili Kuma

Da sauri yace 

Yanxu ina Bashir din 

Gashi nan ta fada gami da miqa mai phone din 


A tsorace yace hello Bashir waimeke faruwa ne 

Ina Yusuf dinne

A hankali yace 

Baba ga shi yana konce yanxu ya Dan samu ya fara lafawa Na kuma yimai alluran banci yanxu ya samu yana Dan lfwa

Toh Wai Bashir meke damunshi ne ?

Wlh baba Yusuf damuwa CE ta mai yawa ga kadaci Yusuf yana buqatar kulawa baba wlh rayuwar Yusuf Na Cikin hadari gwara a dauki mataki tun wuri kasan Dama yana da hrt problem

 Cikin firgita da baya nan Bashir din

Yace  

Insha Allahu bashir a satinnan zan shirya mana zamu taho zamuzo mu ga halin da yake ciki

Toh bba Allah ya kawoku lfy 

Amin ya amsa gamida cewa ka bashi duk kulawar da ta kamata

Ba komai baba insha Allahu zai samu sauqi 

Allah yasa yace gami da katse kiran


A hankali ya fara nitsuwa Cikin sanyi ya fara lumshe idon shi 

Bacci mai qarfi ya debeshi

Lkci daya ya fara sauqe numfashi mai nauyi 

Cikin ajiyar zuciya Aysha ta matso gefenshi tana gyara mai konciyar tasa 

Zama tayi a gefen tana Dan mai kallon tausayi

Bashir Kuma shima gefen ya koma gamida rungume matarsa 

A haka bacci ya debesu 

Ita kam Aysha gani take tana rufe idanta zai mutum shiyasa ta zauna Sai zubda qollah😭 da takeyi


Sune basu tashiba Sai 5:00 Am

A hankali Yusuf ya fara bude idanshi Cikin dan sauran mayen allurar baccin 

Ido ya qura mata 

Yayinda qollah😭 ke bin fuskarta

A hankali ya tashi ya zauna

Ya jingina da jikin 1 str


A dan

Firgici ta miqe tana 

Bashir ya tashi tashi ka gani 

Da sauri shima ya miqe gefenshi ya zauna 

Cikin sanyin murya yace 

Yusuf ya jikin dai ?

Kai ya jinjina gamida Dan motsa lips dinshi yace da sauqi bash

Masha Allah

To Aysha kinga Dan uwanka ya miqe Sai hankali ya konta a daina kuka

Ita dai Sai hawayen ta kalleshi tace ai baba yace zai zo a satin nan Kuma tare zai koma damu

Ido ya qura mata Cikin mmk yace waya gayawa baba banda lfy?

 bashir ne yace yo wannan ai kasan mai fada 

Zakiya ta kalli mijinta cikin kulawa tace ai gwara da ta fada nimafa jiya naji tsoro sosai

Juyawa yayi ya zuba mata ido 

A hankali ya sauqe idanshi kan qirjinta 

Rigar bacci CE a jikinta mai taushi Sai dai doguwace har qasa 

Amman gaba daya ta koma ta manne a jikinta

Ido ya sake lumshwa ganin girjin nata yayi wani cur a tsaye 

Lkci daya idanshi ya fara worewa suna Dan yin jaa 

Kanshi ya sunkuyar Cikin kamo lips dinshi na qasa ya fara tsotsa a hankali 


Bashir ne ya Dan kalleshi a fakaice 

Baki ya taba a ranshi yace kaji Dan banza mai idon ganin mata mutum kamar maye

A fili Kuma miqewa yayi gamida kamo hannu zakiya yace 

Toh mu kam zamu wuce gida Sai anjima Zan zo Na qarisa ma allurar taka 

Kai ya geda mai alamar toh 

Bayan sun fitane ya Dan sunkuyar da kanshi Cikin sanyi yace 

Kinyi sallan ne ? 


Kai ta girgi zamai Cikin zubda qollah😭

Kallonta ya kuma yi Cikin rauni yace toh tashi kije kiyi sallan 

Bata dai tashi ba shima Kuma ya kasa tashi Dan baijin qarfi sosai

A karo Na forko ya Sa hannushi ya damage mararsa lips dinshi yake son ciza ko zasu bar barin da suka farayi Amman ina a take gaba daya tsikar  jijinshi ya fra tashi 

Sanyin jarabar tasa ya fara ka dashi 

Har haworansa Na dukan juna kat kat

Cikin qarfin hali ya miqe ya fada toilet

Ruwan ya sakarwa kansa Cikin  ajiyar hrt ya rinqa murza jikinsa da samulu 

Sai da ya watsa ruwa sannan yayi alwala ya fiti 

Yana fita ya samu bata parlon sallah yayi Cikin 

Kushu,I ya rinqa jero addu,oin nemawa Dan uwanshi gafara

Bayan ya idar da sallan ne ya zame kan carpet din ya konta

Idanshi a rufe 

Yaji ta shigo dakin 

Gaban shi tazo ta durqusa 

Cikin sanyin murya tace  Hamma Yusuf ya jikin baiyi mgn ba bai Kuma bude idanshi ba 

Phone dinta ta miqa mai 

Tana fadin gashi baba nason mgn da kai Kuma yace layukanka basayi



Tsaki yaja da qarfi gamida bude idanshi da tashi zaune 

Hannushi yasa ya fizgota da qarfi har Sai da ta fada jikin shi cikin sauri Kuma ya tureta

Cikin masifa ya daqo hannushi zai yarfa mata mari 

Sai kuma ya tsaya da sauri saka makon abinda  yaji take fur tawa 


By Garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI,WASMITI page 8⃣1⃣to8⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Wayyo Allah Na 

Da sauri yasa tafin hannushi mai laushi 

Ya rufe bakinta 

Ido ta zazzaro Cikin qoqarin kauda kanta

Tana baya baya 

Cikin mishkilanci 

Ya rinqa daga qafarsa yana takawa a hankali yana qara matsota ita Kuma tana qara yin baya2 

Har saida taji ta jikin 

Garu


Ido ya tsura mata Cikin hada fuska 

Ya dago hannushi ya kamo kunneta ya matse 

Da qarfi 

Da qarfi tayi qara Amman sautin bai fitoba sabida tafin hannushi da yasa ya to she bakin nata

Qara matse kunne yayi

Cikin yanayin gargadi 

Yace 

Kin San Allah ki kiyaye ni 

In kuwa ba hakaba wlh zan babbalaki

Kaji yarinya da rainin wayo wato har kin samu damar murgudamin baki ko😏 toh wlh Allah ki rufawa kanki asiri in ba hakaba kuwa

Hmmm ya fada gamida jinjina kanshi alamun zaki daku 😡

Sake matse kunne yayi yana kinji ko bakijiba?

Kai ta gyeda alamun taji 

Qara matsota yayi 

Gami da manna girjinshi a jikin nata 

Sake nauyin shi yayi kan qirjinta 

Gami da matseta ya hadata da jikin ganin idon ta  rumtse Cikin wahala jin yadda ya hadata da gini 

Hannu bibbiyu tasa kan qirjinshi tana Dan tureshi

Kanshi ya sunkuyar Cikin boye halin da ya fara shiga

Lips dinshi ya kamo ya matse da Dan qarfi Cikin dauriya

Yace kina jina ko?

Uhum ta fada Cikin Neman iska Dan gaba daya ya matseta

Qafarshi ya daga gamida taka nata qafan Cikin mugunta

Yaci gaba da cewa 

Wlh karki ga 

Su baba sunzo 

Kice zaki kasa min 

Rashin 

Kunya 

Kin sanni sarai 

Wlh ko sunanan dakaki zan 

Barema ai kin Sani sarai 

Tafiya zasuyi su barki 

Tare dani

Ita dai Sai zaro 

Ido 😳

Take hannushi ya daga 

Daga kan bakinta yace 

Muna fuka 

Da manyan idan nunki a wurin Na rashin kunya

Ita dai numfashi ta rinqa sauqe a hankali

Ta sunkuya ta dauke  robar madarar 

Har takai 

Bakin qofar 

Yace ke

Tsayawa tayi ba tare da ta juyoba

Cikin tsurawa gugunta 

Ido yace 

In Kuma kika yarda kikamin halin munafurci 

Kinsan abinda zai biyo baya

Kinjini kam ko 

Ehh tace 

Cikin  jin haushi

Toh me kika tsaya yi anan maza kauce daga nan

Da sassarfa ta fice 

Tana Allah ya isana mugu kawai



10:00 pm 

Suna parlo gaba dayansu suna ta hira 

Yusuf Na zaune gefen baba suna ta dan hirarsu

Usman Kuma yana zaune tsananin Sadiya da Aysha suna ta hira yana nunawa Aysha pictures din Maryam da Amira da dai sauran  mutanen gida 

Cikin mmk ta kalli Usman tace kai

Ya Usman 

Ga yadda Maryam ta qara fari yanxufa ta kaini fari Sai dai Kuma ta rame

 Sadiya CE ta dan kalleta Cikin Dan jin bacci tace 

Aysha

 Maryam ai dole ta rame Cikin  yana wahal da ita sosai

Kai ta daqo cikin rashin fahimta

Tace Anuty Sadiya wake da ciki?

Da Dan fara tace yoh 

Cikin abin tsoro ne naga kin wani zazzaro ido 

Yusuf dake gefen Sai a yanxu ya Dan kalli inda suke Cikin murtuqe fuska ya harareta da salon ai ita kam Sai zaro idan ta iya

Baki ta tura Cikin maida kanta gun Nenne 

Tace 

Nenne Wai da gsk Maryam Nada ciki 

Fuska dauke da murmushi tace 

Ehh Aysha da gsk Maryam Nada ciki ?

Cikin fara,a ta koma jikin Usman tace yes

Muma mun kusa mu zama iyaye wayyo Allah Na wayaga Maryam da baby 

Da sauri ta Kuma tashi taje 

Gaban baba bello 

Cikin farin ciki tace 

Baba 

Tare zamu koma ko kaga kar ayi suna

Bana can 

Dan kasan dole ni zanje Na rauni da ko yar ya Ahmad

Usman ne ya kalleta Cikin mmk yace da Allah can a reni muje biki ni mijiba baya fada

Bafa cemiki akayi ta aihu ba 

Cikinda gaba daya watanshi 2  da  sati 3 

Mutum Sai shegen son yawo

Ehdin ANSo yawon 

Ai ba kai Na tabbaya ba ehe 

Gun baba takuma maida dubanta Cikin Neman alfarma 

Tace Dan Allah baba kar a hanani 

Zuwa 

Kai ya geda gamida kallonta Cikin 

Tuno Dan nashi 

Yace 

Insha Allahu zakije Aysha 

Amman Sai Maryam din ta aihu kinga kafin satin suna 

Sai kuje

Kai ya juya gun Yusuf

Dake sauqe numshi a hankali Dan furucin Aysha ya famomai ciwon rashin da uwan shi

Yusuf

Baba ya kirashi 

Cikin bada umurni 

Yace Yusuf in Allah ya sauqi Maryam lfy

To ka tabbatar Aysha taje

Kai ya jinjina Cikin jin daci 

Murya Na rawa yace 

Baba in ban jeba wa zaije 

Baba 

A yanxu Dan Ahmad ai baida wani uba da ya wuceni

Baba wannan ai dama nauyi nane Na jibanci dukkan lamuran rayuwar wannan

Da 

Baba me zance da ubangijina 

Ya dauke min Ahmad Sai ya kuma amsar addur Ahmad da yayi aloka cin da baifi  awa 2. Baya bar duniya

A wannan rana ya roki Allah ya bashi da da zai zama madadin shi a gareni a wancan lkcin INA daukan zance Ahmad a matsayin  wasa ase dgske Zai tafi ya barni 

Sai kuma muryarsa ta carke 

Yai shiru yanata cijjije lebe

Aysha kam tun i Sai hawayen 

Cikin kuka tace baba har Sai ta aihu kafin inje?

Ehh Sai ta aihu kafin kije a nan din ma Sai inki min alqawari

Zaki daina yiwa Dan uwanka 

Kuka ki Kuma yi qoqarin

Sa Dan uwanshi Yusuf y daina damuwa 

Den Na tabbaya koda Ahmad Na makoncinsa toh zanyi alfahari daku

Cikin share hawayen tace Na bari baba bazan sakeba inason ya Ahmad yai alfahari dani


Cikin jin dad yace Aha haka nakeson ji 

Allah ya muku albarka baki dayanku

Amin suka amsa gaba dayansu

 Haka sukayi ta hira

Har zuwa 

1:00 Am

Baba ne ya mike Cikin tattara phone dinshi yace toh ni kam zan chiga Sai da safe

Shima Yusuf miqewa yayi Cikin kallon Usman yace kai tashi muje mu shiga

Baba ne ya juyo ya kalleshi Cikin Dan jin bacci yace a a Yusuf

Usman yazo tare zamu kwana

Kai ya Dan daqo yace to baba muje mu kwana tare kawai mana

A a yace kai dai jeka kawai kai Usman tashi mu tafi

Wannan dakin ya ishemu ya nuna dakin daya da yake gefen dakin Aysha wanda da toiler a ciki yace ku kuma Sai Ku shiga nan din ya nuna dakin aysha


Toh su Nenne sukace gamida shigewa dakin Ayshan

Itama tana biye dasu a baya riqe da laptop din Usman Dan tace a dole zai bar mata har Sai in sunzo komawa


Shi kam yusuf a parlon shi ya yada zongo 

Kan 3 str ya zauna Cikin Dan jin bacci a yau ya danji sanyi a ransa Dan ko ba komai yan uwan shi sun Dan debe mai kewa duk da shi ba hiran yakeyi ba yana dai jinsu kawai



A dakin Aysha kuwa 

Suna shiga 

Anuty Sadiya ta fada toilet ruwa ta dan watsa a gaggauce 

Tana fitowa tace

Aysha ga ruwan dumi Na hada miki maza jeki danyi 

Wonka

Cikin jin dadi tace yauwa Anuty Na Allah ya bar manake 

Amin tace Cikin dry 

Ke dama Aysha son ruwane dake kamar kifi Amman kuma tsoron ruwan sama Kuma kike

Kome yasane oho

Tana shiga toilet din gamida cewa wlh Anuty ni tsoron tsawa da walqiya da iska nakeji shiyasa Amman in badon suba  inason yanayin damuna

Dry tayi gamida konci tana to maza jekiyi ki fito


Tana fitowa humra tamurza mai balain qamshi gashinta ta Dan saki Dan in ta tubkeshi zai hanata jin dadin konciya 

rigar bacci ta

Ta zira a jikinta mai Dan siririn hannu iya kan gugunta ya tsaya

Sai Dan wondonshi Dan madaidaici 

Shi Kuma iya kacinsa

Guywarta


 Kan gado ta nufa tana fadin Anuty kinyi bacci ne? 

A a idona  2inaga yadda kike ta wani shan qamshine 

Kai Anuty Wai gamshi 

Eh mana tace Cikin CE mata to Sai da safe

Ki jamana qofar

Toh tace Cikin rashin gano zancen

Qofar ta jawo gamida dawowa zata konta a tsakiyarsu

Da sauri Sadiya ta mike Cikin mmk tace ke Aysha me haka  a INA zaki konta maza tashi ki tafi gun mijinki

😳ido ta zaro Cikin kaduwa tace kai Anuty Dan Allah me haka nifa gsky Ku daina wani cemai mijina

Ni ba ruwan dashi Kuma ban zuwa dakinshi nake yiba bare ma wannan mugun banje inda yake bama  yana cin zalinah bare Kuma ace INA zuwa inda yake

Tashi tayi ta zauna Cikin kamo hannuta parlo ta fito da ita Cikin hada fuska tace maza tafi gun mijinki 

Aysha ase anamki kallon mai wayo ase babu Sam 

Auto indai irin wannan zaman kukeyi tofa dole kuita zama Cikin kunci haka Kuma bazaku taba man tawa da Ahmad ba in Kuma kunyi haka to Baku kyauta masaba


Ita dai Sai tura baki take tana 

Ni wlh baruwa bat dashi 

Fuska a hade tajawo hannuta Sai da ta kaita bakin qofar ta tura ta bude qofar

Hannu tasa ta tura bayanta tayi ciki 

ita Kuma ta juya ta koma tayi konciyarta


Shi kuwa jin an bude qofarne ya  sashi ya dago kanshi da sauri Dan ganin mai shigowar....


Barka da jumma,ah 

Masu karatu inafa jiran barka da jumma,ar😀😍😘



By  garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇

MI,WASMITI page 7⃣8⃣to8⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


A hankali ya sauqe hannushi 

Ido ya tsurawa fuskarta 

Mmk yake 

Yadda ta wani 

Rumtse idan nata gamida qaqqame jikinta 

Dan qara min bakinta 

Ya kuma zubawa ido 

Cikin sautin tsoro

Take fadin wayyo

Allah Na wayyo ya Ahmad

Zai dakani 

Jin sunan Biyayenshi da ta kira ya sauqe mai sanyin  jiki 

A hankali ya Sada kanshi qasa fuska a daure 

Yace toh

Menene me Kuma akayi miki kike ta ihu 

Ni wlh kinsan banson ife ifenki Na banza nan Dan Allah 

Ki barni inji da abinda ke damuna


Ido ta Dan bude a hankali 

Da sauri ta Kuma kawar da kanta ganin yadda ya qura mata ido fuskar nan a murtuqe

Phone dinta ta miqa mai 

Tare da cewa 

Anuty Sadiya CE take son yin mgn da kai 


Shiru tajishi bai karba bai Kuma mgn ba 

Sake juyowa tayi 

Tana kallon shi 

Hannu ya miqa kamar mai karban phone din Sai kuma kawai taji ya kama kunneta 

Ya Dan matse 

Da Dan qarfi ta saki qara

Cikin Dan fada fada yace 

Ke Wai wacce iriyar sokuwace 

Ke baki San abinda kikeyiba 

Waya CE miki banda lfy da zaki rinqa bazani a duniya ban da lfy ki kira wannan ki kira wancan 

Kina tace musu ban da lft

Sam ke  hankalinki baya jikin ki

Ji yadda kike tafiya 

Ko tsari babu ya fada yana mai qoqarin kauda  idanshi daga kan qirjinta

Gami da miqewa yana can da Allah tafi can da  shirmenki 


Jiki a sanyaye ta miqe tana fita tana qunquni 

Mugu kawai azzalumi danma kaga INA jin tausayin ka ne shiyasa ka 

 mutuma in kaga dama 

Da sauri yace ke me kikace ?

Baki ta Dan turo tace a ni cewa nayi 

Allah ya baka lfy 


OK insa zaton ai

Qunquni kikeyi min 

A haka ta fita 

Ta tafi 


Da rana

Bashir ya qara dawowa ya dubashi gami da bashi

Magunguna 


Shi kuwa Yusuf tun daga wannan  ranar

Ya kamu da ciwon kai 

Dare nayi 

Bacci zai qaura cemai ciwon kai mai tsananin zai rufe shi 

Da zazzabi haka zai ta fama ga tsananin tunanin Dan uwan shi


            A 

Nigeria kuwa 

Tun randa Aysha ta kira baba bello ta shei da mai halin da Yusuf ke ciki .

Gari Na wayewa

Ya karbi 

Passport din Nenne

Da Na Sadiya 

Dana Usman ya hada da nashi 

Yayi ta musu shirin tafiya a cikin satin komai 

Ya kammala


Ran da zasu tafi 

Nenne ta maida maryama gun Ummi Dan kula da ita 

Gashi tana fama da laulayin ciki 

Allah sarki duniya 

Randa Ahmad zai rasu a ranan rabbi ya albarka cesu da samun Cikin

Maryam kam takanyi kuka sosai gaba daya ta jeme Sai Dan fari da hancinta da ya qara fitowa

                 

          Su Nenne sun 

Insa lfy 

Randa suka iso murna a gun Aysha kam ba,a mgn 

Dan basu gaya musu sun tasoba 

Kawai 

 Da yamma tana zaune 

A parlo

Yayinda Yusuf ke Cikin daki

 Yana konce ne Amman hankali shi baya jikin shi

Konce yake yayi rigingine idanshi a lumshe 

Hawayen ne ke ta bin gefen fuskarsa 

Ba abinda yake tunawa Sai rayuwarsu ta baya 

Kamar mafarki ya rinqa maimaita shi kenan yanxu 

Ahmad ba kai a doron qasa yanxu bazan kuma ganin kaba 

Bazan Kuma jinka ba 

Yanxu dagani Sai Adam 

A take ya rinqa jin daci Na tokareshi a maqoshi

Yana Cikin wannan 

Halin yaji 

Ihun Aysha dake parlo 

Tsalle takeyi kamar qaramar yarinyar tana maqale da Sadiya

Jin tana ya Usman ase Dana kaima zaka zo 

Ayyah inasu ya Rabi,u 


Da Dan mmk

A fuskarsa ya fito jiki a sanyaye 

Yana 

Shiga parlon yaga baba bello a zaune kan 1 str Nenne da Sadiya suna kan 3 str Aysha Kuma Na maqale dasu a tsakiyansu 

 Usman Kuma Na shigo da kayansu 

Da sauri yaje gaban 

Baba Cikin Dan jin dadin gani su 

Ya zauna a gefenshi Cikin sanyi murya yace baba 

Dama yau zakuzo 

Ni ban saniba.


Ehh ya CE gamida daura

Hannusha a kanshi 

Cikin qashinshi ya tura yatsunshi 

Daya hannushi Kuma fuskar shi ya shafa gamida shafa har kan sajenshi 

Ido 

Ya zuba mai Cikin kulawa 

Yace 

Haba Yusuf

Wannan  wacce iriyar rayuwa kakeyi 

Ne Yusuf kaga yadda ka maida kanka 

Fa  

Kanshi ya kontar kan cinyarsa 

Gami da rumtse idanshi 

Murya Na rawa  

Yace

Baba ya zanyi 

Ya zanyi ne 

Baba bazan iya manta Ahmad ba 

Baba mutuwar Ahmad bazata wuce  A rainaba

Nenne dake gefen tuni ita ma ta fara zubda qollah😭

Aysha CE ta fada kan cinyarta gamida sakin wani 

Irin kuka mai cin rai

Sadiya CE ta dagota 

Cikin zuba mata ido 

Tace Aysha 

Kuka zai dawo da Ahmad ne 

A a tace Cikin kuka 

Toh kukan zai mana mgnin zafin rashin shi da muke cikine a a tace  Cikin share qollah😭

Murmushi tayi mai zafi tace toh mu daina yiwa Ahmad kuka muyi mishi addu,a

Ba gata ko so da zamu nuna mishi Sai addu,a

Usman dake gefen Yusuf yace wannan gsky ne Anuty a man kinga fa yadda 

Hamma Yusuf ya maida kanshi

Baba bello ne ya miqe gamida cewa 

Yusuf maza tashi mu tafi muje a gyara maka gashin kankan nan da fuskar nan taka 

Jiki ba qarfi ya kalli baba yace baba Bari a yi muku 

Othern abinci

Sadiyace tai maza tace 

A a Aysha zata tashi zamu shiga kitchen zamuyi duk abin da ya kamata 

Toh shike nan ma kajiko


Suna fita basu tsaya ko inaba Sai wurin gyaran kai

Shi kam Yusuf ido kawai ya wore yana kallon yadda ake ta gyara mai kai badon yana soba  

Dan shi komi yafi son yayiwa kanshi 

Gyaran akayi mai sosai 

Gashin nan Sai sheqi yakeyi dama gashi da yawa da sulbi tamkar valarabe 

Sajennan yayi luv a sufkarsa 

Gashin girarsa da suke kusan a hadewa

Suma sunyi ras sun qara qawata fuskar tashi

Lkci daya yayi rasa haibarsa ta fito gonin Sha ,awa

Daga nan suka wuce masallacin 


Aysha kam yau tana Cikin gata 

Girkinma 

Usman ne da a Sadiya sukayi 

Itako tana jikin Nennen ta 


Sai faman cin inabi takeyi tana ta zuba surutun ta da rakadinta

 daya bayan daya take ta tabbatar kowa 


Bayan sun gama girkinne 

Sadiya ta shigo itama suka zauna sukaci gaba da hirarsu 


Usman Kuma ya dage Wai zai hada musu kunnun aya

Yanata kiciniyar tace marka den ayar ne 

Su 

Yusuf suka shigo 

Bayan sunyi sallan insha

Cikin mmk Yusuf ya kalleshi a gyetsine yace toh Usman abin naka Kuma har ka kai nanne

Kana namiji ka wani zage Wai girji kakeyi 

   Dry ya danyi yace kai hamm Yusuf nifa ba girki nakeyi ba kunun aya nake hada mana


Kai da Allah tafi can kai dai dabi,ar  mata duk ka iya ya fada tare da zama kusa da Baba belloN


Sadiya CE tace yoh to ba dole muyi girkiba tunda matar gidan bata 

Ma San ta yadda zatayi wani abinba 

Dan gani NAYI gas dinkun nan ko sau daya tema ba ayi Amfani da shiba


Baki ya tabe Cikin gyatsina fuska yace 

Wannan me taiya in banda kuka da ihu 

Dan tsabar iskanci 

Girkinma Wai bazata yiba sai dai zakiya ke aiko mata

Baki ta Dan tura Cikin fakaice idansu ta watsa mai hara da murguda mai baki😏


Ido ya Dan zaro mata Cikin tsawa yace 

ke waye kikeyiwa harara🙄

Oho tace mai ai ni ba da kai nakeba ehe😏

Ya gane sarai yasan shi tayiwa hakan 

Shiyasa Cikin 

Dabara ya miqe 

Gamida juyowa ya kalleta 

Yace zo ki dauko 

Madara ki kawo wa baba

 baki ta tura 

Cikin shigoba tace 

Toh 

Ba ga Yaya Usman ba ya dauko mana ..


Tab lallaima yarinya kin rainani toh Dan nazo gidanku Sai aka cemiki ni Dan aikenku ne

Cewar Usman kema ya fada yana gyara koncinyarsa kan 2 str 

Nenne CE tace ke Aysha ai wannan aikin kine mu kam baqin ne ai 

Tashi ki dauko


Toh tace gamida miqewa ta nufi kitchen

Tana tafiya tana leqa fuskar Yusuf din 

Dan tasan dai tayi mai abin da ya tsana shiyasa da sauri sauri ta dauko madarar 

Tana uhm gwara nayi sauri 

 ( ta Lamido kallube do wara tawa am hado)

Kar sarki mugayen Nana yazo ya sameni anan


juyowa tayi da sauqi Dan fita kitchen fin

Gim taji ta fada jikin mutum har saida robar ta  fadi

Da sauri ta daqo 

Ido ta zaro Cikin tsoro murya Na Dan rawa tace ....


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI,WASMITI.page 

8⃣4⃣to8⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Idanshi ya qara budewa 

A take yaji  yarrr gaba daya gashin jikinsa Na tashi

Kanshi ya kawar da sauri 


Ita Kuma tsayuwa tayi jingine da qofar

 

Phone dinshi ya jawo 

Yana Dan daddan nawa Amman Sam hankalisa baya jikin shi

Tsawon wani lkci bai Kuma kallontaba bai Kuma yi mata mgn ba

Itako tana tsaye a haka har bacci ya fara fizgarta

Sai tayi

Yuu kamar zata fadi Sai ta Kuma miqewa 

Shiko 

Yusuf bai qaunar ya sake daqo idanshi ya qara ganin abinda

Zai zame mai fitina ya hanashi bacci

Kai ya mayar jikin 

Kujerar gami da lumshe idanshi

Tsaki yaja

Tare da miqewa ya nufi daki 

Koncita 

Yake sonyi.

Amman ya kasa samun nitsuwa

Tuni ya Dan

Fara tsotsan 

Lips dinshi

Yana Dan tsurawa garu ido


Itako Aysha yana tashi ta dawo kan.3 str tai konci yarta


A haka tai baccin ta 

Cikin konciyar hankali


Shi kam Yusuf acewarsa yayi baqin gani garin gane ganensa ya tado da azabebbiyar Sha,awarsa gashi 

Tbs dinshi sun qare 

Haka ya kwana Cikin 

Matsi



Tun daga ranar Aysha a parlon shi take shi kuma yana cikin dakinshi 

In gari ya waye ko zasu Dan zauna a parlon Aysha ayi ta Dan hira duk da ma shi Sai ido kawai yake binsu dashi ita kuwa harara ke 

Hada su

A haka har sukayi 

Kwana 8 


Yau jumma 

Dabi,ar Yusuf tun da safe ya shirya Dan tafi masallacin da wuri

Yasa Usman ma ya shirya 

Dan shi kam baba tun da yaje sallan asuba bai dawo ba yana can


8:00 Am

Yusuf ya fito cikin shigar larabawan

Yayi ras dashi gonin 

Sha,awa ga yar qibarsa ta fara 

Dawowa Dan yanxu yana Dan samun konciyar hankali

Dan yanxu Aysha bata ife ifentan nan Kuma ko zatayima shi baruwanshi sannan yana samun kula ta gefen abinci ga baba da yake ta yawan shige mai Dan debe mai kewar Dan uwan shi


Fuskarsa cike. Da haiba 

Yayi luu da idan nushi Cikin shafa sajenshi 

Ya kalli Usman yace kai tashifa mu tafi lkci Na tafiya


Sadiya dake gefe ta kalleshi a fakaice tace

Ha Yusuf

Toh batun zuwa 

Hilton dinfa 

Kadai San ban gama sayeyya taba 

Kuma gashi gobe zamu wuce 

Makka

Gashi duk mun shirya kai muke jira


Kai ya jinjina Cikin gyatsina fuska yace

Haba dai Anuty ni gsky kin San ban fiye son yaeon nanba Kuma ma haka kawai Sa kuyita duruwa Cikin garadai Wai zakuyi tsaraba

Toh 

Yusuf ai dolece sayan wani abin 

Kai ya juya yace toh gsky yau dai frayed ne

Kuma ni banson  banje masallacin da wuriba

Toh kaje mana in ka dawo Sai muje 

Da yafi kam ya fadi Cikin ransa kuwa cewa yyin in kin ganniba

Har zai fita 

Aysha tace wlh Anuty Sadiya inya tafi yanxu Sai dere.


Allah ko tace tare da zura hijabinta 

Tana toh wlh kawai ka tsaya mu tafi tare in yaso Sai mu dawo da wuri

Kai ya juyo Cikin watsa mata harara yana kada kai


Gaba daya su Anuty Sadiya kam an nitse Cikin Hilton

Sai debo koya suke kamar ba gobe 

Aysha kam qananan kaya tayi ta jida da dogayen riguna masu Shep

Ga su da taushi da sulbi


Shi kuwa Yusuf gefe dayaya koma ya zauna ma aikatan ciki da suka saba Sai hira suke tayi

Cikin larabci

Har zuwa Dan wani lkci

Ya kira Usman yace kcefa su fito Dan wlh xan tafi Na barsu


A gaggauce suka gama hada kayan 

Usman yayi gaba da wani itama Anuty Sadiya ta dibi wosu

Aysha  ko  bakos guda biyu 

Cike da kaya

ta dauko ruggume dasu a qirjinta tazo ta wuce ta gaban shi inda yake tsaye yana biyan kudin kayan nasu

Kanshi ya kawar Cikin jin hau shin sun bata mai lkci

Tana fita yana binta a baya

Su Usman kuwa tuni sun fita suna Cikin mota 


A hankali take tafiya kanta a qasa

Dai2 lkcin wani 

Bature ya fito Cikin motarsa

Da woni karensa qato mai jikin kura 

Karen yana 

Fitowa kai tsaye gun Aysha ya nufa

Ita Sam bata luraba 

Sai kawai ganin abin da take tsoro kamar mutuwarta tayi a gabanta

Cikin tsoro da razani da firgici

Ta watsa kayan dake hannuta

Ta cillara ihu mai ban tsoro idanta ta rumtse gamida ware hannuta

Duka biyu

Gaba daya jikin Sai bari yake 

Shi mai karen dry ma ta Mashi shi Karen Wai hakan gaisuwa ne ihun da takeyi Kuma shi a gunshi wasane

Gaba daya hankali mutane ya komo kanta ihun takeyi a firgice

Yusuf dake binta a baya da fari

Cewa yayi da kyau

Karen ya yayyagu sheki dai ba son yawoba

Sai kuma yaga gaba daya ta firgice ihu take da iya qarfin ta ta tsaya a wurin Kuma kamar wacce aka dasa 

A take ya tuna wata rana da irin haka ya faru

Ahmad har kamar zaiyi kuka saida ya kai qaran masu Karen 

Kamar a kunneshi yaji ana rada mai amanar Dan uwanka nefa

Cikin sauri ya tsinci kanshi da qarasawa

Gunta

 Qirjinshi ya manna a bayan ta

Tare da bude hanna yenshi ya zagayota dasu ya matseta a jikin shi

Itama jin mutum a jikinta yasa da sauri ta sauqe hanna yenta da ta bude

Ta daura kan nashi 

Ta qaqqameshi

Tanata goga jikinta a nashin

A hankali ya Dan sunkuyo 

Ya manna wuyanshi Cikin tsakanin nata wuyan da kafadarta

Gemunshi Na kan kafadarta

Bakinshi ya saka dai2 kunneta

Cikin rada rada da sanyin jiki

Yace

Ke da Allah kina Tara mana jama,a 

Ke baki iya addu,a bane Sai ihu

Kinitsu ko nace ki bude idanki 

Karene fa ba kuraba

A hankali ta bude idan

Kai ta sunkuyar Sai kuma ta Kuma qaqqameshi Dan ganin Karen Na shinshina qafarta

Qara matseta yayi a jikin shi gami da dan daga ta ya tsalla kar da ita daga gaban Karen

Yasa qafa ya ture Karen

Da sauri mai Karen ya matso yana bawa Yusuf din haquri

Ba tare da ya kalleshi ba yaceba komai

Aysha kam quluwa tayi sosai

Abu Na Neman kasheta Amman Wai shi cewa ma yakeyi ba komai

Baki ta tura Cikin zubda qollah😭 ta qarisa gun motar shiga tayi ta zauna tana ta kubbura baki

Usman kam dry

Yakeyi

Sosai harda riqe ciki

Yana ke zo zo kinga yadda kika rinqa zunduma ihu har kina watsa musu tattabarun su

Phone dinshi ya miqawa anty Sadiya yana Anuty ki gani duk motsin da tayi Na dauketa 

Dan inason inje in nunawa su Rabi,u kai nama fasa yau dinan zan tura musu ta

WhatsApp

Anuty Sadiya kam dry takeson  amman ta sani tanayi

Zata kama kuka shiyasa tayi shiru Sai murmushi

Kaway

  kyau sukayi sosai a pictures din 

Yadda sukayi abin tamkar masoya ga wani kyau da sukayi kamar larabawa

Bayansu ga tattabarun da sukayi musu rumfa

Yana isa  kuwa ya shiga mota ya ja suka tafi

A cikin mota ko Sai tsaki yake tayi

Yana faman danna mata harara


Suna isa gida

Usman ya kalleshi Cikin girmamawa yace Hamma Yusuf ai ba sai mun shigaba kawai mu juya mu tafi masallacin ko

Bai kulashiba Sai wani dogon tsaki da yaja 

Gami da fita

Kai tsaye dakinshi ya nufa

Yana shiga

Ya fara zare kayan jikinsa

Toilet ya shiga Cikin jin haushi yayi wonka tare da alwala ya fito ya sake wani sabon shirin

Kai ya rinqa jinjinawa a fili kuwa Sai Jan  tsaki yakeyi 

Yana fadin wannan yarinyar Sai kace mayya ga shegen naci da iya maqalewa a jikin mutane 

Munafuka fitinenniya bata San irin fitinar da take Sa  mutun a cikiba

Amman Bari zanyi mg ninta

A haka ya fito ya nufi masallacin shi da Usman

Sune basu dawoba Sai bayan insha

Suna dawowa suka samu suna ta hada kayansu

Ita kam Aysha Sai faman zubda qollah😭 take tana ayyah yanxu gobe i war haka bakwanan 

Ni kam ma Na gata kaina tunda aka kwasoni aka kawoni

Nan

Ayyan Nenne Dan Allah kice baba ya barmu mu tafi tare

Cikin lallashi Nenne tace toh ki tabbayi mijinki mana in dai ya barki to shike nan Sai mu tafi taren


Baki ta tura Cikin fushi tace

Wlh ni ni ban da wani mai hanani kawai dai bakwa son na koma ne

Toh bisu mana Dan Allah tashi ki tafi yanzuma 

Jeki kije kfi ruwa tafiya

Wato kinga zasu tafi zaki dawo da iskan cinki Na ife ifen nanko

Toh wlh ki kiyeni

Banza kawai sokuwa


Aiko haka ta faru Dan tun jiya taqi cin abinci sannan yau Kuma ta fara kuka

Haka ta kwana kuka da safe ma da kukan ta tashi

Taqi cin komai

Har

Zuwa yanxu da suke 

Gun da motocin su baba zasu debesu su tafi Cikin makka Kuma daga can zasu dawo 

Nageria

Sosai baba yayiwa Yusuf fada da nasiha kan ya riqe amanar Dan uwanshi  sannan yasan shi Aure ba wasaba 


Hakama Nenne tai tamai nasiha

Sadiya Kuma dama tunda sukazo take ta faman nusar da Ayshan 

  

9:30 Am 

Moticin suka gama shirin su

Su Nenne duk suka rinqa miqawa Aysha hannu suna musabaha ta Sai mun hadu Kuma

A hankali Sadiya ta rugumota Cikin sanyin jiki da rawar murya tace 

Aysha Sai wata rana fatan Allah ya hadamu kan alkhairi

Dan Allah Aysha am Ku daina yiwa Ahmad kuka

Kinji ko ?

 Lkci daya Kuma 

Kukan da take dannewa ne ya kufce mata

Itama Aysha Sai kukan takeyi 

Da gyara ta saketa suka shiga mota 

Gun Usman ta Kuma komawa

Fa dawa tayi jikin shi tana

Kuka tana ayyah ya Usman Sai kuma yaushe ne 

Kukan kunji dadi zaku koma Cikin danginku gatanku ni kuwa bani da kowa a nan Sai Allah na

Shima Usman sosai yaji kewar  qanwarshi abokiyar fadanshi Dan da yake kamar ita ke binshi shiyasa ta rai nashi

Cikin lallashi yace haba dai Aysha kina da kowa mana tunda ga Hamma Yusuf kiyi haquri wataran

Zakizo

A haka ya saketa ya shiga mota suka tafi suna daga musu hannu


Allah sarki Aysha a wurin ta tsuguna gami da sakin kuka

Cikin kewar yan uwanta

Shi kam Yusuf komawa yayi gefen yana kallonta Cikin jin hau shin kukan 

Yace 

ki tashi mu tafi ko kuwa na koro miki karnuka

Da sauri ta tashi Cikin tsoro ta shiga mota suka tafi 

Kafin su isa gida kuwa tayi bacci Sai ajiyar zuciya take sauqewa

Bayan yayi parking ne ya juyo ya zuba mata ido...


Gaisheku manyan matan Fasaha Writers

Halima Auwal gaisuwata mai tarin yawa a gareki😍😘



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI WASMITI page 8⃣6⃣to8⃣8⃣Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇




Ina alfahari daku iyayena Allah ya biyaku da mafificiyar sakayya😍😘



Ido ya tsura mata Cikin fidda numfashi a hankali hankali

Ko qefta idon ya kasa 

Kai ya dan Kuma juyawa Cikin sauqe qwayar idansa kan

Qirjinta rigace da wondo a jikinta sun matuqar amsarta Sai Dan hula da ta tattara gashin ta ta tura ciki

Sai yadin laffaya mai matuqar kyau ta yane jikinta a cikinsa 

Baccin da takeyi yasa ta Dan zame daga jingu nuwan da tayi  ta Dan konto ta kanshi hular kanta ta zame ta fada kan cinyarsa

Hannuta daya ta daura kan cinyarsa

Daya Kuma ta daura kan kafadarshi

Ta Dan motsa gamida Dan qara konciya a kanshi 

Motsin da tadanyin ne ya taimaka wa laffayar wurin worworewa ta bar jikinta

Shi kam Yusuf

Gaba daya ya jishi Cikin wani irin yanayi 

So yake ya dauke idanshi daga kan ta Amman ya kasa a hankali lips dinshi Na sama ya Dan rebe da Na qasan 

Harshe yasa ya Dan  lashi lips dinshi Na qasan

Da qarfi yayi wani irin ajiyar hrt

A lkcin da ta qara kontowa kan cinyarsa

Gaba daya yaji tsikar jikin shi ya mimmiqe qwayar idanunshi suka fara budewa da kyau

A karo Na for a rayuwarsa da ya tsurawa qirjin mace ido

Yadda kanta ya danyi kan cinyarsa Sai ya bawa qirjinta damar daqowa sama

A take yaji jikin shi ya fara kerma

Kai ya mayar jikin sit din yana fesa numfashi

A ranshi yake cewa

Toh me hakan me abin gani a jikin wannan rikitecci yar shi yanxu matsala larsa 1 yana tada ita ya tabbata da kuka zata tashi duk ta hanashi bacci 

Tsaki ya Dan ja gamida daqo kanshi Cikin samo mafita 

A hankali ya daqo hannuta Na kan qafadarshi ya hada da daya hannu da ya tafi Neman tsokana kusa da  hajia🍌

Ya Dan dago kanta ya hada ya Dan jingina ta da jikin sit din da take zaune

Fita yayi 

Ya za gaya gunta 

Kanshi ya zura Cikin motar gami da ruggumota Cikin jikin shi

Kamar yarinya

Da bayan shi ya koma ya rufe murfin motar

A haka ya isa qofar shiga part dinsu

Qara ruqqumota yayi 

Da hannu daya daya hannu Kuma ya bude qofar ya shiga da ita

Kan 3str ya nufa da ita Cikin sanda 

Ya kontar da ita gamida Dan tattato gashin ta ya mayar matashi baya

Duk yanayin abin ne Cikin gudun kar ta tashi 

Dagowa yayi

Cikin ajiyar hrt da

Cilla mata harara yana

Aikin banza 

Jifa gaba daya yadda aka hadani da matsala

Yarinya Sai kukan tsiya

Tsaki ya kuma ja gamida tabe baki ya juya ya 

Nufi 

Part dinshi

Kai tsaye 

Toilet ya shige ruwa ya watsa a jikin shi 

Yana fita ya sanya kayan baccin shi

Rigace da wondo wondon har qasa Sai rigar iya qugunsa

Daga samanta Kuma zip ne kalan fari da Dan ratsin

Yellow

A jikin shi

Turare ya feshe jikin shi dashi

Jikin window ya qarisa Cikin shaqar iskar da ta fara kadawa mai sanyi labulayen ya sassake gamida kashe wutan dakin

Kan gado ya nufa Cikin ajiyar hrt ya konta ya jawo blanket ya rufe kanshi 

A hankali ya rumtse idanshi a take photon fuskarta ta fadomai

Da sauri ya bude idanshi Dan 

Jin ihun da ta saki daga parlon 


Tsaki yaja gamida cewa sheke nan kuma mayya ta tashi ba zatayi baccin ba bazata barni nayiba

 Komawa yayi ya kontar da kanshi da nufin shareta

Sai kuma yaji Sai qara surutai 

Take qara ta saki da qarfi

Tana wayyo Allah Na kare wayyo ya Ahmad ka taimakeni

Sosai take surutan da qarfi

Kiran Ahmad da take ya tuni mai da amanarsa 

Shiyasa da sauri

Ya miqe Cikin 

Yanayin shike nan ai Na kade


A parlon konce take kan kujerar Sai faman riqe hannu kujerar take tana kuka tana qoqarin faduwa

Da sauri ya kamota Cikin fada fada yace 

Wlh ke sokuwace ke kullum baza kiyi addu,a ba in zaki Konta kizo kiyi ta yiwa mutane ihu a gari  

Ita kam batama San yanayi ba sai faman shigemai jiki takeyi

Tana qaqumoshi

Yana tureta tana qara maqaleshi Cikin tsoron mafarkin da takeyi Dan har yanxu ganin Karen yana binta takeyi

A fusace yasa hannushi ya rufe bakin nata

Jin haka ita Kuma tasa hannu bibbiyu ta tura Cikin rigarsa 

Yarrr yaji tsikar jikin shi gaba daya ta miqe

Idanshi ya rumtse da qarfi gamida 

Tallabota ya hadata da qirjinshi 

Dakinshi ya nufa da ita kai tsaye kan gado ya kontar da ita

Ya daqo da niyar janye jiki shi daga NATA tai wani irin ruqqumoshi

Da bude bakinta da qarfi ta sakemai qara Cikin kunneshi

Sosai yaji qaran ya ratsashi ta Kuma bude baki zata Kuma cillara wani qaran

Da sauri

Cikin rashin sanin halin da yake ciki ya manna bakinshi kan nata 

Harshenta da ta daqo zatayi kukan ya cabke a kidime

Hannushi ya Sa Cikin rawan jiki ya qara manna qirjinta da nashi 

Gaba daya yaji jijiyoyin jikin shi sun tsaya cak jinin shi ya tsinke bugun zuciyarshi ta tsananta harbawa a take zuciyarshi ta rinqa harbawa tana watsa saqonni a jikin shi zuwa qoqal warshi

Lkci daya jikinshi ya fara Bari kamar mai rawan sanyi

Lips dinshi suka fara qoqarin aikin su da suka saba Sai 

Wani irin sauti yake sauqewa hannushi bibbiyu yasa ya tallabo kanta ya qara mannawa da bakinsa Cikin wani irin salo da fitan hankali 

Ya rinqa tsotsar harshen ta

Gaba daya ya manta waye shi ya manta a wacce duniyar yake ya manta da waye yake rayuwa ya rasa tunanin shi baki daya

Sosai yake sarrafa bakinshi Cikin nata

Ita kuwa 

Tunda ya kame harsheta 

Ta fara dawowa Cikin hayyacinta

Hannuta tasa ta rinqa tutttureshi

Amman ina  Yusuf baima San tanayiba gaba daya ta tsorita dashi ba abinda yafi bata tsoronma irin yadda taji gaba daya jijinshi rawa yakeyi da garfi ta samu ta zaRo harsheta daga tsotsar da yake mata 

Da saurinshi yasa hannushi yana kamata yana qara matseta Cikin 

Kuka da tsoro ta rinqa tureshi

Tana Dan bugunshi 

Tare da cewa 

Bana so wlh bana so ka barni mugu kawai wayyo Ummi Na 


Shi kam Yusuf kai ya rinqa juyawa yana ta danna ajiyar zuciya gamida matsota jikin shi da sauri ya samu ya

Laso 

Pink slip dinta masu matuqar taushi tsotsar su yake yana ta susucewa

Ita kuwa Aysha dukunshi takeyi sosai

Tana mugu kawai azzalumi 

Jin haka ne ya Sa ya zare bakinshi daga Nata gami da matsota ya daura cinyarsa daya kan mazaunanta hannushi Kuma ya qara rufe bakinta dashi

Ba tare da yayi mgn ba tayi tayi ta motso ta kasa 

Sai zare ido takeyi

Tana sauqe numfashi

Shi kuwa da qarfi qarfi yake sauqe ajiyar hrt

A haka bacci mai nauyi ya kwasheta


Shi kam Yusuf rayuwa yayi a iya wannan lkcin Cikin azaba ba abin da yake buqatar irin ya samu mai debemar kewa ko zai samu ya kauda ruwan fitinar dake cinsa

A wani gefen xuciyar Sa Kuma haushin kanshi da kanshi yakeji  a wani banqaren Kuma kunya mai tsananin ya rufeshi

Cikin Jan tsaki ya zare jikinshi daga Nata

Gaba daya haushin kanshi yakeji

Toilet ya fada ya sakewa kanshi ruwan sanyi 

Wai ko zai samu hajia ta koma ta kama kanta 

Da qer ya samu ya fara nitsuwa 

Dole yayi wonkan sarki

Yana fita ya kimtsa 


3:25 Am ya fito 

Masallacin ya tafi Cikin 

Jin takaice da kanshi yakewa kanshi fada toh me kayi hakan Yusuf

Ya za,ayi ka kasa konturol din Sha,awarka

Me  ajikin yarinyar nan mitsss yaja dogon tsaki

Dai 2 lkcin da ya shiga Cikin masallacin

Nafila yayi raka 2 ya dauki qur,ani ya fara karatu

Koda yana Cikin karatun Sai abin yake tunowa 

Cikin takaici 

Ya rinqa addu,ar

 

Allah ka bani ikon kauda kaina kan wannan yarinyar  rabbi ka hanani jin kunya Allah ka sauqaqamin yawan buqatar da nake ciki

A haka yaita addu a har akazo akayi sallan asuba

Qur ani ya kuma dauka yaci gaba da karatu

Har zuwa 12:20 pm 

Har dai akazo akayi azahar

Yana son komawa gida bai San da wanne yanayi zai shigaba

Haka ya zauna har akayi LA asar

 sannan 

Ya kama hanyan gidan

Cikin murtuqe fuska wai shi karma taga qofa ta rai nashi


Lol 😝


Ita kuwa 

Tunda baccin ya dauke ta bata farka ba sai 6 dai dai

Da sauri ta miqe gamida fira daga kan gadon

Cikin mmk ta Kuma wore idanta ta zubawa dakin ido

A fili

 tace me ya kawo ni nan kuma

Nan take Kuma ta tuno su Nenne sun tafi

Ahankali ta sunkuyar ta kalli jikinta Riga dai da wondo sunanan Sai dai ba laffayan ba hula

A hankali ta fara tuno mafarkin da tayi Na karnuka Na binta

Kai takuma dagawa Cikin kallon dakin a fili tace toh kenan zuwana dakin nan Kuma ya akayishi ko dai abin da Na gani a mafarkin da gsk ne

Kai a a ta bawa kanta amsa  Hamma Yusuf dinne zai wani abin a a dama dai ya Ahmad ne

A haka dai ta bar abin a matsayin mafarkin

Tana idar da sallan asuban ta Dan Sa yar qaramar Riga Wanda iya ka cinta guiwa kalar read da hulanta sabida Dan yanayin zafin garin gashinta ta mayar ta baya 

Tana gamawa

Yunwa Kuma tace assalamu alaikum

Sosai takejin yuwar harda jiri jiri takeji

 Cikin ta kaici ta kira Sadiya amman Kuma layin bai shiga

Parlo ta dawo ta zauna bayan ta Duba Cikin kitchen din ba wani Abu deffefe


Zama tayi kan kujera tana riqe da jikinta hawayen Na bin fuskarta

A hankali take fadin wayyo Allah Na yunwa nakeji wayyo Ummi Na

Haka fa ta zauna har zuwa yanzun duk ta jeme

A haka ya shigo ya sameta tana ta kuka


Fuska ya qara hadewa😡gamida

Watsa mata harara

Ya ja tsaki ya wuce parlon shi

Ganin haka yasa takaici ya kuma cikata

Tashi tayi ta bishi  tana kuka

Da sauri ya juyo ya kalleta Cikin tsawa 

Yace me hakan zaki wani rinqa bina a baya kinata kuka

Me akayi miki

Qara matsoshi tayi Cikin

Yanayin ta Na shigo bar da ta sabayiwa Ahmad dasu Adam 

Tace yunwa nakeji

Ido ya Dan bude Cikin mmk

 yace toh yau kuma sabon salon iskanci ne 

Me kike nufi kenan 

Ni xan miki girkinne?

Ita dai Sai kuka takeyi tana qara matsoshi sabida jiri takeyi

Cikin kuka tace wlh yunwa nakeji  Hamma Yusuf yau kwana 3 banci abinci ba  

Tsaki yaja gamida shigewa Cikin dakin yana fadin Sai kuma akace kizo kiyi tamin kuka

Binshi tayi a baya duk inda yaje Sai ta matso gefenshi tana kuka

Tana dire dire 

Sosai ya hatsalo da qarfi ya juyo Cikin zafin nama

Ya matso dab da ita ido ya tsura mata gami da qara matsota........🙈



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻Mi WASMITI .page 8⃣9⃣to9⃣0⃣Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Kuka ta Kuma saki gamida kamo hannushi ta matse a tsakiyar qirjinta Dan jin wani irin suka da yake mata

Ga jiri da takeji gaba daya bata gani sosai

Mmk 

yakeyi sosai

Dan gaba daya ya lura ta daina tsoronsa kamar da

Hannu yasa zai hanka data

Sai kuma jin kanta yayi ta daura kan damtsen hannushi

Cikin muryar kuka

Take fadin

Wayyo Allah Na wayyo cikin qirjina kaina yunwa zata kasheni

Ido ya tsura mata cikin hade fuska

Yace 

Ke da Allah can gafara 

Ni ban son koke kokenki Na banzan nan

Hannu yasa yana daga kanta Amman INA ta maqaleshi

So yake ya zuba mata mari amman Kuma zuciyarsa ta tunamar anar Ahmad ce 

Hannushi ya Dan zame cikin Dan

Fada fada yace

Toh ai saiki sakeni

Inyaso nasan yadda zanyi

Qara kamo hannun tayi 

Da Dan qarfi ya janye hannushi Dan jin ta fara sauya mai yanayin gudun jininsa

Toilet ya shige

Gamida rufe qofar 

Ita kuwa a bakin qofar ta tsaya tanata kukan

Wonka yayi gamida maida kayan shi ya fito Dan yana jinta 

Yana fita tabi bayan shi

Gaban madubi ya zauna

Yana goge sumar kanshi

Ita kuwa tsayuwa tayi a bayanshi tana zubda qollah😭

Shi dai bai kulata ba a hankali ta qara matsoshi tana 

Cikina

Yunwa nakeji

Tsaki ya ja cikin jin haushin ta ya miqe ya koma parlo

A falonma zuwa tai gefenshi kan 3 str ta zauna gamida kamo hannushi ta kontar da kanta a damtsen hannushi

A hankali ya sunkuyar da kai 

Ya zuba mata ido

Dan jin gaba daya jikinta Sai rawa yakeyi

Sai wani numfashi tafe sauqewa

Hannushi ya zame gamida miqewa 

Ya kalleta afakaice yace toh ki sakeni mana zan fita Na seyo miki abincin.


Ni dai mu tafi tare. tace dashi cikin kuka

Da kaji mgnar ta kasan tana tare da yunwa

Janye hannun yayi gamida ficeea 

Da sauri yana yarinya Sai koken koken tsiya


Yana fita masallacin ya wuce Sai da yayi insha ya biya rstr

Ya saye mata abinci 

Gida ya nufa da qafa yake tafe da yake ba nida tsana ninsu


A bakin qofar shiga ya sameta jingine da qofar Sai kuka take yi

Ganin ya wuce ne ta bishi da Dan  sauri

Gamida kamo hannushi

Juyowa yayi yace Dan Allah ki daina takuramin kije kitchen ki dauko pilet.

Cikin rawar murya tace

Ni bazan  iyaba 

Jiri nakeji

Kai ya jinjina gamida miqewa ya dauko ya zuba mata ya tura mata gaban ta

Da sauri ta ture pilet din. Tana

Ni bazanci wannan kayan tafarnu wannaba

Ni dai ka dafamin ko tea ne 


Zuwa yanxu kam ya gama hatsalowa 

Shiyasa ya miqe cikin fushi yana kar kici Dan Allah karma kici cikina ko naki 

In kinga dama ki tabbata a haka kaji iskanci 

Ni nema zan miki girki

Daki ya nufa yanata mita

Itama tashi tayi ta bishi a baya 

Tsayuwa tayi a gefebshi ta rinqa rusa kuka

A fili yace wlh bappa Yaya kun cuceni

Miqewa yayi kitchen ya shige inda yake jinta a dakin tana ta rusa kukan

Da sauri sauri ya hada mata komai

Ya kai mata

Karba tayi da sauri cikin jin yunwar ta kurba Sai kuma tai maza ta kamo hannushi gamida Sa qara 

Cikin kufula yace Allah shi qara ai kina sane yanxu Na tafasashi

Anan kuwa ta tasashi fafur dole shi ya fifita ya bata tasha

Tana gama shanyewa ta daura mai cup din kan cinyarsa

Ta Sa kanta jikin hannushi

A take Kuma

Sai zufe keta tsatsafo mata tako INA

Lkci daya Kuma ta fara rawan sanyi 

Sai karkarwa takeyi.cup din ya dauka ya daura kan beed side 

Ya zame ya ja baya daita gamida tura mata pillows gabanta da bayanta

Shiko yaje ya rurrufe ko INA gamida kashe filun 

A hankali ba tare da tuna komai ba yazo ya konta a gefenta

Phone dinshi

Ya zaro

Adam ya kira cikin 

Sanyin murya ya daga gamida cewa wlh kai banza ne Yusuf ko yaushe Sai kadaidaci inajin dadin rayuwarta da mata ta Sai kawani matsamin

Tsaki yaja cikin kufula yace banza kawai Na mamajo

Kashe woyar in bai maba.

dry ya danyi cikin tsokana yace gsky ka Bari da safe muyi mgn Dan yanxu kam inajin dumin matata.

Mitsssss 

ya ja tsaki gamida katse kiran

Lumshe idanshi yayi gamida shaqar sanyin da A,C ke fesa musu

Ga wani irin qamshi da dakin keyi

Lkci daya tunanin shi ya fara juyawa

Blanket ya jawo ya rufe jijinshi

Sosai yayi nisa cikin tunani

Can ya rinqa jin 

Yadda take rawan sanyi Sai qara matsoshi takeyi

A hankali ya Dan ja baya 

Ita kuwa jib dumin blanket yasa Sai qara matsoshi takeyi

A hankali ta mirgina ta isa cikin jijinshi

Qara matsoshi tayi Dan jin dumin jikishi Na ratsa ta

Kam ta kamo shi 

Cikin a zabebben zazzabi da takeji

Kanta ta tura cikin wuyanshi

Tana sauke numfashinta

Wayyo Allah shi kam Yusuf ya koma tamkar zaucecce Sai numfashi yake tafixga da ajiyar hrt da qarfi qarfi

Sosai yaji sanyin jikinta Na ratsashi

Duk da jallabiyar dake jikinshi Dan bai samu yashirin baccin ba

Hannushi ya Dan Sa da niyar tureta Amman Sam baida qarfin hakan 

Dan duk jinin jikinshi ya tsaya

Konyarsa kuwa tamkar an cunna mata wutane

CiKin rashin sanin halin da yafada ya jawota jikinshi da qarfi ya matseta lkci daya Kuma ya Riga ajiyar hrt

Lips dinsa suka fara motsawa a hankali jikinshi ya fara jarkin


Ita kuwa jin dumin shi yasa ta qara maqaleshi gamida qara juyowa kanshi gaba 

Daya

Hannuta ta Dan dago cikin  yanayin mai fama da zazzabi

Ta sauqe hannun kan mararshi

A take yaji wani irin Abu ya ziyarceshi wata iriyar guguwar Sha,awa ta yunquro mai 

Shiyasa bai San lkcin daya saki Dan wani irin sautiba wayyooooi

Shihhhhshi gami da 

 matsota jikinshi  ya rinqa shafa ma zaunen ta

Burinsa yaji fatarta Na gogar tasa Amman ya rasa ta yadda hakan zai kasance

So yake yajishi a sabuwar duniya Amman ya rasa ta Yaya 

A zuciyarshi kuwa cewa yake me  kake sonyi haka Yusuf

Tsaki yake ja Amman a cikin ranshi

 a fili kam Sai lips din Shi da suke ta motsawa

Cikin kidima ya manna qirjinshi 

Duk da a ranshi wai ai so yake ya Kore mata sanyi da takejin.

 zaiyi

Gaba daya ta fidda shi cikin hayyacinsa

Dole tasa ya rinqa cakudata cikin jikinshi

Da azabar da taurin kai ya samu baccin azabar ya debesu


Asuban faru ya zame jikinshi cikin jin haushin kanshi da kanshi

Qarin takai cinsa ma Sai yayi wonka

A haka dai ya shirya ya tafi massalaci


Ita kuwa tana tashi ta samu baya nan ta koma dakinta tai wonka da  sallah gamida dawowa parlon

Zazzabi kuwa har yanxu yana Dan damunta

Shi kuwa Yusuf daga masallacin

Makarantasu ya nufa 

Bai dawoba Sai bayan sallan insha


Yau ma kamar jiya haka ta tasashi agaba da kuka tana yunwa takeji Dan tun jiya bata Kuma cin komai ba

Shi kuwa fada ya rinqa yi 

Dan takaici kuma ba yadda ya iya a dole ya fita ya seyo mata

Sannan Kuma

 tace ita abinci su d tafarnuwa bazata Ciba 

Dole yauma ya shiga kitchen

Ya Dan mata abinci mai Dan sauki



🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

A hankali yanayin zamansuya fara can zawa wani irin 

Zama ya fara zama musu sabo

Zuwa yanxu Yusuf qarfi da yaji ya zama shike kula da Aysha sosai

Sun kuwa Dan saba dukda kullum Sai yayi ta mata masifa

Wasu lktan Kuma da dama tana  haddasa mai tashi muguwar Sha,awarsa ta yadda yake kwana da axaba



Yau jumma,a 

Tunda Yusuf ya fita da safe bai dawo ba sai yanxu da 

Yake tafiya a hankali cikin yanayin shi Na nitsuwa 

Yake takawa

Iskar damuna mai dadi da qamshi ke ta kadawa sosai yaji nishadi ya fara dibarsa

Iskace mai sanyid a qanshin furannin

A hankali walqiya ta rinqa haskawa

Rugugi ya fara a hankali 


A haka ya iso tsakiyar parlon

Ita kuwa Aysha gaba daya ta gama firgita da razana 

Wani irin walqiya akayi da sautin qaran aradu mai matuqar tsawa da rikitarwa dai dai

Lkcin ........



 Ina Alfahari daku members Na

Gaishe ki Aysha s bayero

Fatan kina lfy



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

Mi,WASMITI page

9⃣1⃣to9⃣2⃣Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Ina godiya da kulawarku rdrs da addu,oinku garen 



Ya rinqa jin sautin kuka a cikin parlon

Daga can gefen 3 str phone dinshi ya zaro gamida kunna torch din ta 

Hasken ya Dan gauraye parlon duk da ba wani haskene sosaiba 

Dan yanayi Na dare ga Kuma duhun damuna Sai in andanyi walqiya ne Sai a Dan ga hasken

Can

Ya haggota kan 3 str ta lafe ta jikin hannun kujerar 

Gaba daya ta qaqqame jikinta

Sai faman karkarwa takeyi 

Ta rumtse idan ta Kuma gam Dan tana bala,in jin tsoron walqiya

Kuka kawai take 

A hankali ya qarisa gun nata 

Ido ya Dan zuba mata cikin tabe fuska yace mutum Sai shegen tsoron tsiya 

Ita kam Sam bata jishiba Dan duk ta firgice

Kai ya Dan kawar Dan ganin surar jikinta Na bashi tsoro

Kukanta ya kuma jin ya qaru.

 Dan wani rugugin da akayi kusan 3 a Jere irin mai kamar nishin nan

Tsugu nawa yayi a hankali 

Cikin sanyin murya yace 

Ke bude idanki me hakan

Jin muryarshi yasa ta dan

Bude idan da sauri 

Gami da zuba mai idon cikin hawaye 

Tace tsoro nakeji injin tsoron ruwan sama

Toh ruwan cinyeki

Zaiyi?

Murya na rawa tace 

Hamma Yusuf ni ko a gida in ana ruwa Ummi bata barina ni kadai

Kuma ko ya Ahmad ma ya Sani wlh inajin tsoron tsawa

Sai hawaye shar 😭a idanta 

Gaba data Sai yaji jikinsa yayi sanyi tabbas yana iya tunawa

Muddin ana ruwan sama duk abin da sukayi Ahmad yakan zame jikinshi ya koma kusa da ita ya ruggumeta ya rinqa shafa kanta 

Da taji tsawan Kuma Sai tai ta qaqqameshi

Kuma ya lura tabbas tsoron tsawa take har cikin ranta

Cikin sanyin jiki ya dago hannushi ya daura kan wuyanta gamida Dan tallabo bayan kunneta babbar yatsarsa Kuma ya daura kan kuncinta a hankali ya rinqa murza yatsar tasa kan habarta yana goge mata qollah😭

Ido ya qura mata cikin wani irin yanayi yau a fili yake gano kamar da ake cewa sunayi da ita a zahiri Kuma yaga kamar da ake cewa sunayi da Ahmad

Qwayar idanta irin Na Ahmad ne sak

Qara zuba mata ido yayi cikin Dan kada mata kai alamar ta bar kukan.

Gaba daya yaji Ahmad ya dawo mar lkci daya yanayin shi ya sauya


Ita kuwa cikin tsoron ta kamo hannushi ta riqe 

Tana mai zubda qollah😭

Wani irin walqiya akayi mai hasken gsk 

A lkci gida Kuma aka saki tsawa mai firgitar wa

Da qarfi cikin razani ta abka jikinshi har saida ya koma ya fadi qasa kan carpen  dirsham

Da qarfi Kuma ta rinqa qwaqumoshi tana tura kanta cikin qirjinshi

Shi kam Yusuf ya gama macewa a zaune bai iya tabuka komai ba 

Sai sanyi da ya farajin yana ratsashi

Gaba daya qarfin jikinshi ya bace

A take Kuma ruwan ya kece kamar da bakin qorya

Sai iska mai sanyi da take busawa

Da gyer cikin qarfin hali ya tattaro sauran jarumtarsa 

Ya yunquro 

Ya Dan koma jikin kujera ya jingina

Ita kuwa kanshi ta qara mirginowa 

Gamida Sa hannu bibbiyu ta sanqalo wuyan shi

A hankali ya rinqa furta mata Addu,oi cikin kunneta   hannushi yasa ya qara matsota jikinshi 

Ita Kuma Sai faman qaqqanda rewa takeyi

Hannushi yasa gami da tallabo fuskarta 

Gaba daya ta birkice

Cikin qarfin hali ya miqe ruggume da ita kai tsaye bedroom dinshi ya wuce da ita

Yana ruqqune da itan ya juya ya rufe qofofin gidan 

Gami da ajiye hasken phone dinshi kan beed side 

Zama yayi gamida jawo pillows ya jera 

A bayanshi ya Dan jingina dashi

Ita kuwa jawota yayi ya daura ta kan qirjinshi

Yasa hannu ya tattaro gashin kanta ya mayar matashi bayan ta

Hannushi daya Kuma hannuta ya koma ya saka cikin nashi gamida harde yatsunsu

Ita ma ta sanqalo daya hannuta a bayanshi

Daya hannushi Kuma kan fuskarta ya daura ya rinqa shafawa har zuwa kan gadon bayan ta

Yayinda daya Hannu kuwa da yake cikin hannuta ya rinqa Dan murza yatsunshi a hankali cikin tafin hannun nata 

Ajiyar zuciya ya rinqa sauqewa Dan jin wani irin taushi da laushin hannun nata 

Lkci daya Kuma ya fara daburcewa 

Lips dinshi suka fara Bari ga sanyin gari ga sanyin A,C 

Ga wani irin buqatuwa da yakeji

Sosai ya qara matsota jikinshi ya rinqa shaqar qamshin kanta

Sai faman tsotsar lips dinshi yake tayi makar zai tsinkesu ya hadiyesu ko yaji sanyi


Ita kuwa zuwa yanxu ta samu bacci ya debeta

Yayinda shi kuwa

Yake ta faman azab tuwa 

Lkci guda yaji mararsa ta fara wani irin harbawa

Qara matsota yayi wai ko zaiji sanyi Amman ina a haka ya kwana cikin azabar

Bugata 

Kafin qari ya waye ko gaba daya ciwon Mara ya isheshi gashi yasha tabs din Na shima a banza

Ko sallan asuba a gida yayi Dan bai iya mike tsawonsa

Bayan ya idarne 

Ya Dan matso bakin gadon 

Cikin cije lips dinshi yace 

Ke 

Ke tashi kiyi sallah.

A hankali ta bude idanta

Cikin muryar bacci tai addu a ta yawo ta dawo bakin gado qafaqunta Na qasa

Kai ya sunkuyar ya qurawa qafar tata ido yatsunta kab irin nashi ne

Hatta farcensu iri daya ne har zuwa sharabarta Sai dai shi 

Jikinshi a kawai gashi Zara Zara masu laushi da baqin

Mu samman ma qirjinshi da hannushi 

Sauqa tayi cikin Dan bacci 2 ta juya ta tsaya ta bashi baya 

Ta yi miqa ta yadda rigar jikinta ta qara yin sama 

Qirjinta ya taso 

Ido ya sauqe kan ququnta

A hankali take tafiya Amman ququnta Sai wani juyawa yakeyi mazau nenta ya tsurawa ido

Har ji yake kamar idanshi zasu manne a jikinta cinyarta ya kuma qara tsurawa idan 

A dai2 lkcin ita Kuma tayi woje


Kai ya mayar jikin godon gamida lumshe ido

A ranshi yake tunani ya zama dole NAYI Aure matuqar INA son Na kare mutum cina da lfy ta bazan iya jumre wannan uquba ba 

Hannu yasa ya damqi mararsa gamida miqewa ya koma kan gadon ya konta


Ita kam Aysha Sai da tai wonka sannan tai sallah 

Ta zauna gaban mirro

Mai ta Dan murza gamida Dan shafa turaruka masu sanyin qamshi

Atamfa ta dauko Riga da siket ne kalan atamfar ya amshi jikinta yayi ras a jikinta

Siket din ya Dan matseta 

Dan kwalin ta Dan tubke kanta dashi 

Miqewa tayi 

Ta nufi dakinshi


Kan gadon taje ta zauna ta kamo hannushi cikin tura Dan bakinta tace

Hamma Yusuf ka tashi mana yunwa fa nakeji ka ganifa rana tayi


Cikin wahala ya bude idansa da suka rine sukayi jazur

Tsura mata idan yayi cikin kamo gefen lips dinshi Na qasa. ya fara tsotsa 

Jikinshi dake rawa ya rinqa Dan kamewa

A karo Na 2 tace ni ka tashi yunwa nakeji


A hankali yace bazan iyaba 

Kije kitchen kiyi duk abin da kikedo kici jogolgolenki

Qara matsoshi tayi ta kamo hannushi tana jawo shi

Ji dumin tafin hannuta ya qara ingizo halin da yake ciki

Gaba daya ya cika da takaici Dan ya rasa mafita

Shiyasa ya miqe cikin fada yace zo xoki ficemin a daki yarinya sai naci kamar mayya

Ko so kike ki kasheni tun kwana bai qareba

Ki barni naji da abinda ke damuna mana

Tasowa tayi cikin sanyi da Dan tsoro tace Hamma Yusuf baka da lfy ne ?

meke 

damunka?

Bansani ba yace da ita

Toh meyasa baka iya miqewa?

Me ruwan ki da miqewata.

Cikin sanyi tace wlh baka da lfy gafa yadda idanka sukayi gashi baka iya miqewa 

Ka ganifa gaba daya 

Jikinka rawa yakeyi

Gashi Sai faman cije lips dinka kakeyi..


Harara ya watsa mata gamida yin parlo kan 1 str ya zauna Sai zufa keta keto mai 

Ita Kuma phone dinta ta dauko

Ta zauna a parlon ta

Cikin sanin murya ya jiyita

Tana cewa

Hello

Ya Adam ka gani ko Hamma Yusuf bai da lfy.

Sai kuma ya jiya tayi shiru alamun ana mgn daga daya gefen

sai Kuma yaji tana fadin 

Ya Adam wlh ko tsayuwa bata iyawa Sai cikinshi yaketa riqewa

Gashi Sai rawan sanyi yakeyi

Jin haka 

da sauri ya shigo parlon phone din ya fixge

Cikin fada yace 

Ke ni nace miki banda lfy da zaki wani zaqe ki rinqa yadani gun wannan yayan naki mai bakin tsiya

Yanxu ya isheni da surutun banza

Da sauri ya daqo phone dinshi Dan jin ana kira yana dubawa ko yaga Adam ne

Mitsssssss yaja godon tsaki gamida matsota cikin murtuqe fuska😡 yace 

Ni lfy ta lau Sai dai in kece baki da lfy

Asalima ni lfyarce ta jawomin haka

Amman tunda gani kike banda lfy toh zan tabbatar miki ni lafiyeyye ne  kuma zaki gane kurenki

Banza kawai  sokuwa


Ya qarshe mgnar cikin daga woyar tashi yana

Dagawa

Adam ya kece da dry 

Cikin dry yace wlh ka kusa ka kashe kanka

Dab kake da ka resa ranka matuqar baka bar wannan baqin halin da mishkilanci ba kasanka sarai Allah yayika fitinenne Sai bakin jaraba sannan ka wanisa taurin Kai

Banza jarabebbe 

Ustazu kawai

Ka bada kai bori ya fada.


A kufule yace Kai da Allah tafi daga nan ancema kowa irin kune jarabbabun tsiya 

Sai matse qanana yara kuke tayi

Dan rashin abin yi


Dry Adam ya kumayi tare da cewa toh Allah ya sauwaqa in Kuma mganinka ne ya qare ai Sai ka kuma saya.

wai kaima Yusuf har zaka cewa wasu jarabbabu

Ai gwara kowa da kai kam

Katse kiran yayi 

Tare da juyowa kanta cikin 

Takaicin............


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

Mi,WASMITI page

 9⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇



Gaisuwa ta mai tarin yawa gareku

Yan uwana matan group din MUSAN JUNA MARUBUTA

Allah ya barmu tareya😍😘😍😘


Ina jidake Ummee Garkuwa Jennifer👍🏻😍😘



Ido ya tsura mata cikin takaici Dan shi sosai yakejin takaicin yawan koke-koken da takeyi

Gashi Sai tai ta bibiyarsa tana shigemai

Cikin takaici

Ya isa gabanta

Kai ta dago ta kalleshi cikin zubda qollah😭

Tana Hamma Yusuf yunwa nakeji.

Cikin fada yace 

Toh gani cinyeni

Nace tashi ki cinyeni

Tunda dai ke kin maida kuka abincin ki

Ni wlh kin fara ban 

tsoro dan

Haka kikayi tayin wannan kukan a lkutan baya baki bar yiba saida kika ciyemin Dan uwa mayya kawai fiti nenniya 

Kin cinyeshi kin huta saura nima kin cinyeni

Dan da kullum kukun kike kina kiran sunansa yanxu kuwa kin dawo kaina ko?

Kai ta rinqa girgizawa tare da sakin kukan takaici wai ita Hamma Yusuf ke kira da mayya harda cewa itace ta cinye mai Dan uwan shi.

A kufuli yace ba zaki bar kukan bako?

Cikin rawar murya tace 

Nifa yunwa nakeji

Juyawa yayi ya nufi kitchen Cikin 

Takaici

Fruits ya debo a pilet gami da Dan lalla besu

Ya fito da nufin kai mata Dan ta barshi yaji da abinda ke damunsa

A kan steps din haurowa kitchen din ya sameta a zaune

Sai zubda qollah😭 takeyi

A hankali ya zauna gefen ta

Cikin sanyin murya yace gashi kici wannan 

Anjima in na danji sauqi

Zan miki abin da zakici

Hannu tasa a hankali ta sanqalo nashi hannun kanta ta kontar kan damtsen hannushi 

Tare da sauqe ajiyar zuciya

Inabi ya dauko ya miqa mata 

Karba tayi da hannuta daya daya Kuma tana riqe da nashi

A haka ta danci

Yana zaune yana kallonta Cikin mmk

Ita a kullum bata da wani abinci Sai fruits Kuma Sai Dan tea 

Sannan shima bazata Ciba dole Sai ta takurashi

Kai ya Dan sunkuyar gamida leqo qwayar idanta

Kai ya jinjina gamida take baki da sauqe ajiyar hrt

A hakan tayi bacci a jikinshi ta Dan konto kanshi kanta Na kan damsten Hannushi

Ta lumshe idanta gashin ta yayi lub a baya 

Sosai ya tsurawa fuskarta ido

Ta yadda a hakan Kuma in kana Kansu bazaka ga qwayar idanshi ba

Dan dama duk da Dan girman idan Yusuf Amman ganin idanshi yana wuya sabida koda yaushe kanshi a kasa yake Kuma a lumshe suke.

 A hankali yaji wani Abu na shigemar Cikin zuciya

Lkci daya Kuma yaji jinin jikinshi ya tsinke yana wani irin harbawa,

Da gudana,

A fili ya rinqa sauqe ajiyar hrt

Lkci daya Kuma yaji tausayi ta Na ratsashi

A hankali ya Dan qara talla bota

Gamida lumshe idanshi 

Jikinshi ya Dan rinqa sanyi Sai kuma bacci mai dadi ya debeshi.


Basu tashi ba sai 9:35 pm 

A hankali Aysha ta bude idanta

Da sauri ta matsa ganin yadda shima ya qwaqwumota hannushi daya kan qirjinta duk da ba wai bres dinda ya taba ba.

 Amman Sai taji haushin abin

Dan yawanci duk abinda Yusuf keyiwa Aysha bata Sani Dan Sai in tana Cikin tsoro ko firgici ko bacci ne yake Dan shi shige mata duk da shima yakan ji 

Takaicin kansa


Idanshi ya bude Dan jin motsin ta

Kallonta yayi a fakaice 

Gamida Dan daqo hannushi da ta maida pillow

A hankali ya danyi qara Dan zafin da yaji Dan hannu ya Tara jini

Hannushi daya yasa yana Jan dayan

Cikin qoqarin tashi dakinshi ya nufa 

Har yaje baqin qofa Sai kuma ya Dan juyo 

Itama shi take kallo

Ganin ya juyo yana kallonta ne yasa tai sauri tayi dakinta.


Bayan ya  gama kimtsawa ya hada mata tea ya bata tasha shi Kuma 

Ya wuce school.


            

           🌹🌹🌹

Kwanaki sun ja mokonni sun ja

Har ya koma watanni sun ja


Bayan watanni 7 

 

             Yau tun

Da safe Yusuf bai fi taba

Yakuma yaqi ko tafasa ruwan tea din ma yau yace bazai

Yiba 

In taga dama ta shiga tayi

Ita Kuma 

Sai nadewa tayi

Kan 3 str 

Tace wlh

Ita bazata iyaba 

Shi kuwa zaune yake can gefen

Kan dining table

Ya Sa laptop a gaban shi yanata 

Aikin karance- karance sa


Can ta daqo tace 

Hamma Yusuf

Wlh yunwa nakeji har qirjina ya fara ciwo.

Bai kalleta ba bai Kuma yi mgn ba

Hakan ya cikata a Dan qasa qasa tace mugu kawai azzalumi

Sai kuma ta miqe ta nufi inda yake 

Jawo kujera tayi ta zauna kusa dashi

Cikin tura baki tace

Hamma Yusu!

 Bata qarisa mgnar ba ta tsura mai ido Dan ganin yadda ya wani tsura mata ido Cikin yanayin zanfa saba miki


Juyawa yayi yaci gaba da aikin shi.

Ita kuwa kuka ta fara a hankali da ta lura bai kulata ba yasa ta saki kukan da qarfi

Don ta cika shi da takaici


Kallonta yayi Cikin harara ya mige tare da tattara phone dinshi da laptop dinshi ya ja kujerar 

Ya fita yana juyawa

Phone dinshi ya dauki suwa alamar ana buqatar mgn dashi

Dagawa yayi Cikin nitsuwa da biyeyya yake gaida baba bello

Cikin farin ciki 

Baba bellon ke sheida mai.

 maryam ta aihu ta sami da namiji

Farin ciki ne sosai ya ziyarci rayuwar Yusuf

Ba abin da yake fadi Sai Alhamdulillah

(en yetti tak domen)

Mun godewa ma haliccinmi.


Ita dai sai ido take binshi dasu

A can Kuma baba bellon ne yace INA Aysha? 

Gata nan baba ya bashi amsa 

Toh bata woyar

Toh yace Cikin miqa mata

Phone din karba tayi ta kara akunne

Bayan sun gaisane 

Yake cemata Aysha Maryam ta aihu.

Daga jin Maryam ta aihu kawai Cikin Salle ta 

!qaradi da tsantsar farin ciki ta cilla woyar gefe 

Ta tsaki qara mai qarfi gamida tsalle kamar yarinya

Ta rinqa juyi a tsakiyar parlon 

Tana rawa Sai faman juya ququnta takeyi

Tana Alhamdulillah

(Amman hade do mi seyi)

Amman yau dinnan nayi farin ciki

(Mi yetti Allah mi hotai leddi am dayirdi am)

Na godewa Allah zan koma qasa ta ta aihuwa

Juyi takeyi sosai

Gaba daya jikinta Sai rausayawa takeyi

Duk ta gama kashe Yusuf kam a tsaye

Bai taba zaton yarinyar nan ta cika hakaba Sam bai taba tsura mata ido irin na yau ba gaba daya ya wore idanshi kan mazauneta da suketa juyawa tana ta faman happy 

Ko idanshi ya kasa qiftawa

A hankali ya zaro harshensa ya Dan lashi lips dinshi da suka fara motsawa


Ita kam juyawa takeyi sosai har jiri ya fara diban ta

So take ta tsaya Amman ta kasa

Da qarfi ta rinqa yin baya-baya 

Zata fadi 

Cikin zafin nama da tsinkewar zuciya

Yusuf ya tallabo ta fada qirjinshi

A tsorace ta rinqa fadin 

Hamma Yusuf zan fadi rami a gabana

Wayyo ka tai make ni wlh zan fada Cikin rami 

Sosai take surutai

Hannu yasa ya dago kanta Cikin tsurawa pick lips dinta ido

Yace ke bude adanki

Ba dai bakya jiba 

Ke haka kikaga ya dace ki nuna farin Cikin ki 

Ba godewa Allah zakiyi ba sai rawa da ihu

Ita kam Sam idanta a rufe yake ganin hakane yasa ya qara kontar da kanta kan kafadarshi ya rinqa shafa kanta zuwa bayan ta

Har zuwa tsawon wani lkci

Sannan ta samu abin ya saketa

Tureshi tayi da Dan qarfin tayi cikin bedroom dinta 

Shi kam Yusuf ya gama macewa a tsaye dagyer ya samu ya koma kan 3 str ya zauna yana maida numfashi da qarfi-qarfi

Jim kadan ta fito

Cikin doguwar Riga baqa wacce tasha aiki da pick din zare

Kanta ta yane da siririn mayafi shima pick

Tayi tarha dashi fuskarta ta fito rasa a ciki

Ga wani Dan ma daidaicin jaka rataye a kafadarta  hannuta

Daya Kuma janye da trolley mai Dan girma

Cikin fara,arta da nishadi tace 

Hamma Yusuf ni kam fa na gama shirin,

 sannan kai Kuma kana zaune.

Ido ya zuba mata cikin mmk

Trolley ya kalla Cikin 

Jan tsaki yace lallai baki da kai bakima San abinda kikayi

Ba

Yana kai nan ya tafi part

Inshi,

Aiko da sauri ta bishi a baya gamida riqo hannushi

Cikin karya suya da Neman alfarma tace Dan Allah Hamma Yusuf kar kamin mugunta ka hanani zuwa wlh Na gaji da garin nan ni nafi son in koma can qasa ta


Baki ya Dan tabe gamida daga kafada da Dan ware hannu alamar bai shafeni ba,

Aiko ta rinqa nacemai duk inda yayi tana biye dashi a baya 

Ita dai su tafi

Can dai ya juyo ya kalleta Cikin murmushin mugunta yace 

In kinaso zakije mana.

Ehh in a so ta bashi amsa da sauri.

Ko ?

Ehh takuma cewa.

Kai ya kada gami da cewa

Toh Amman fa da shara din zakibi dokana shike nan in kin qi kuwa bake ba zuwa

Ehh na yarda tace dashi Cikin zumudi tace 

toh gayamin menene shara din naka?

Kai ya jinjina yace daga yau ke zakina.....



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

Mi,WASMITI. Page9⃣4⃣,Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Fuska a murtu qe yace

Daga yau ki raba kanki da koke-koken

Da kikeyin nan sannan 

Ki daina takuramin kin iya, girki bawai baki iyaba ki shiga kitchen kiyi girkin ki

Ni ban damuba bance kiyi daniba Dan ni ba zanci kwabenki ba 

Sannan karki matsamin da batun tafiyar in kinqi kuwa,

Kina gani zan tafi Na nabar ki.

Cikin zumudi tace 

Na yarda zanyi

Girkin

Kuma nama bar kukan

Ta fada tana mai goge fuskarta

Tabe baki yayi Cikin cewa da kin kyau tawa kanki...


Tun daga ran Kuma Aysha ta bar koke-koken Dan dama tanayi ne da gaya Dan ta cikashi Kuma tai tamai dry a fakaice in taga ya zage yana ta fifita mata tea 

 Ta rinqa cewa mugu tunda dai kabar cin zalina da sauqi.


Tun ran da  ya gaya mata sharudansa

Kullum da safe zata tashi tayi wonka da sauri sauri

Dan ta shiga kitchen  tayi musu breakfast Amman Sai tasamu ta makara shi har ya shirya ya fita

Sai dai taci sauran abin da ya bari ta Kuma nadewa kan 3str tai ta woya da mutanen

Gida pictures din baby Maryam Kuma tamkar dansu aka buga woyar ta

Duk wani shirin ta ta gama Sai jiran Comandan nata take kullum tanason ta  tabba yeshi Kuma tana jin tsoro kar allaura ta to no mata garma. Shiyasa dole takeyin shiru.



Yau Alhamis wanda yayi dai dai 

Da kwana 5 da aihuwan Maryam

Da yamma 

Liris 

Yusuf ya shigo

Parlon Aysha

  

Kai tsaye kan  carpet ya zauna a tsakiyar parlon laptop yasa a gaba yana ta aikin latse-latse


Ido ta zuba mai Cikin yanayin son mgn Kuma tana jin tsoro shiyasa Sai ta kalleshi Sai ta Kuma kauda kai can dai ta gaji 

Ta sauqo daga kan kujeran ta matso kusa dashi Cikin hikima 

Ta fara mgn 

A hankali

Tace Hamma Yusuf.


Bai amsa bai Kuma dagoba

Hakan tasa ta qara matsoshi Cikin

Qarfin hali tace 

Hamma Yusuf

Kaga pic din boy dina

Ko ?

kalleshi ka gani kekkewa dashi mai

Kama da ya Ahmad

Kai ya daqo Cikin tsura mata ido 

Yace boy dinki

Kuma

Yaushe kikayi cikinsa?

Har kika aifeshi?

duk ban saniba?


Baki ta tura Cikin jin takaici tace d'anane mana ai in munjema Zan roqi 

Maryam ta ban shi.


Hmmm yace gamida harararta yace waya CE miki zakije?

Da sauri ta daqo kai tace Dan Allah Hamma Yusuf kayi

Haquri

Wlh in banjeba zan mutu

Kai ya jinjina yace toh ai naga ko sau daya baki aikata shara dinaba sannan Dan abinda Na ajiye in Na dawo zanci Sai ki tattareshi ki cinye.

Haka mukayi

Dake?

Da sauri ta gyeda kai tana a,a 

Dan Allah kayi haquri wlh gobe kam zanyi na tuba 

Ta fada tana qoqarin zubda qollah😭

Da sauri ya daga mata hannu cikin murtuqe fuska yace ki hadiye hawayen ki

Allah kika yarda kika zubda qollah😭 bazaki jeba.

A zahiri har Cikin zuciyarshi Yusuf bai san meyasa ba Sam baison ganin fuskarta Nata tsiya yar da hawayen da zaran ya ganta tana kuka jikinshi ke macewa burunshi ya ruggumota a ranshi zai ke ji kamar ya lashi hawayen Dan tausayi ta da yakeji.


 a nashi ganin fa wai tausayi ne shiyasa ya dakatar da ita 


Ita 

kuma sai ta fara rau rau da ido Dan maida qollar

Miqewa yayi.

Ya fice daga gidan bai dawoba Sai dare.kafin ya dawoma tuni tayi bacci

A parlon ta ganin haka yasa shima ya konta a parlon shi gamida bude qofar da daga labulen ta yadda zai ke hanqo ta.

A haka ya kwana badan yaji dadiba Dan gaba daya yanxu ya saba da kwana da ita a girjinshi baccin dai yayi badan dadi ba.



Kashe gari Jumma,a kam tun 5:00 Am

Ta tashi tai wonka tana fita tayi sallah ta  dauko wasu Riga da wondo black color Sai Dan rats in fari kadan 

Wondo. Dan gajere iya karsa guy warta rigar Kuma ta Dan rufe mata cibi yar ta kadan

Amman daga baya bayan ta ya Dan bayyana ta kasan mazau nanta

Sai gashin ta da ta kitse ta saki jelar ta gefen kafadarta

Kai tsaye kitchen ta nufa  

Tana zuwa ta fara kici niyar fere doya

Tana gamawa ta kunna gas ta daura shi daya gefen Kuma ta daura ruwan tea 

Lkci daya sukayi dai-dai yadda take buqatar

Ta sauqe tea din ta daura a filas 

Sannan ta daura kaskon tuyan 

Ta fasa qoi da samai kayan qamshi sannan ta matso da niyar fara tuyan.

 ta debo zata zuba Cikin kaskon kenan

Sai taji kamar motsin mutum

Gaba daya jikinta ya bata ana kallonta


Shi kuwa Yusuf tun sanda ta fara firan

Ya zo bakin kitchen din Dan so yake ya fita da wuri yaje masallacin gashi yau zasu wuce 9j 

Yana isa qofar kitchen din yayi baqin gani injishi da fada Dan gaba daya ta watsa mai tunanin shi

Lkci daya ya zamo tamkar an dasashi ba abinda yakeyi Sai

Bin qugunta da Ifo ko qefta idan ya kasa 

sosai yake mmk yaushe yarinyar nan ta cika haka gaba daya jikinta Sai kadawa

Yakeyi

Zuciyarshi ke raya mai ya qarisa gunta ya shafi bye bye dintan ko zaiji sauqi 

Aiko yabi umurni hrt dinshi a hankali ya fara takawa har yazo dab da ita

Gashi dama gaba daya jiya ya kwana da kewar ta

Ya daqo hannushi kenan ita Kuma ta juyo

Ganin yadda yanayin shi ya sauya

Lips dinshi Sai bari sukayi ya bude idanan ras Sai faman kadasu yakeyi.

 hakan ya bata tsoro ta juyo da sauri Dan matsawa baya.

 aiko

Hannuta Sai Cikin kaskon mayin


Cikin jin azaba da  radadi

Ta saki qara gamida xillowa tayi bayanshi

Salle takeyi kamar yarinya qarama lkci daya kuma yatsarta ma nuniya da tashiga cikin mayin tayi jazazur

Gaba daya hannun nata sai karkarwa yakeyi


Ihunta shi ya dawo dashi cikin hayya cinsa

Da sauri yayi kanta ita kuma sai zillewa takiyi tana jawo qasan rigarta tana goge yatsar

Da qarfi ya samu ya komo hannun gaba daya shima ya rikice 

Ita kuma sai yarfa hannu take tabs wayyo Allah wayyo Hamma Yusuf hannuna ya nuna

Ganin taqiyin shirun ne yasashi

Kamo yatsar cikin wani irin salo yasa yatsar cikin bikinshi

A hankali yasa harshen shi ya rinqa zagaye yatsar gamida Dan tsotsar ta

Da fare taji zafin dubin bakinshi sai kuma a hankali taji sanyin harshen nashi Na ratsa yatsar tata

Shiyasa a hankali ta rinqa sauqe ajiyar hrt cikin tsura mai ido

Shi kuma 

Gaba daya hankalin shi ya koma kan qirjinta 

Dan dukiyar fulaninta ya zubawa ido ganin yada suke tsaye cur kamar zasu tsone mai ido 

Da qarfu yayi ajiyar zuciya sanadin tuno yadda ta rinqa tsalle a gabanshi qirjinta Na kadawa ma zaunen ta Na juyawa


Sosai ta zuba mai ido gami da sunkuyar da kanta Dan taga me yake gani

Ido cikin ido sukayi

A take taji jinkita ya fara rawa ganin yadda idanshi suka qara yin ja ya wani kamo lips dinshi sai tsotsa yakeyi

A hankali ta fara zaro yatsarta daga kan harcensa

Shi kuwa sai qara cabke yatsar yayi

Cikin rawan murya tace

Ha Ham Hamma Yusuf

Zafi nakeji

Jin yadda take mgn ne ya sashi komo hannuta ya zaro yatsar daga

 bakinshi

Ido ya tsura mata cikin lasar lips dinshi da yin piki piki da idanshi

Jan hannuta yayi ya wuce da ita har bedroom dinshi a baking gado ya ajiye ta

Robar zam-zam ya dauko mai sanyi


Gabanta yazo ya durkusa gamida kamo hannun.

 ya balle bakin

 robar

Ya rinqa zuba mata ruwan zam-zam din

 yana shafawa 

A take taji wani irin sanyi Na ratsa hannu nata gaba daya.

lkci 1 ta nemi zafin qunan ta rasa

Sai sauqe ajiyar zuciya takeyi


Tashi ya kuma yi ya jawo mata pillows

Cikin wani irin murya  yace 

Konta bari naje Na qarisa aikin

Kai kawai tageda mai gamida lumshe idanta

A ranta take tunani menene a kan harshen Hamma Yusuf

Ko ya yake iya sarrafa harshen sa

Da tunanin tayi

Bacci


Shi kuma zuwa yayi ya kashe gas din 

Ya koma parlon ta ya konta kan 3 str yayi ruf da cikin

Ya rinqa matse kanshi wai ko zai samu nitsuwa Amman ina 

Sai wahala kawai da yake Sha

Shi baison ta gane halin da yake ciki

Da qer dai ya samu hajia ta Dan konta🙈


Sannan yaje ya hada sauran aikin

Sai da ya hada mata tea sannan yazo ya tasheta 

Tayi breakfast

Shikuwa toilet ya shige yaje yayi wonka 

Kafin ya fito ta koma parlo.

 bayan ta tattara wurin



      10:27 Pm 


Ya fito cikin shiga ta alfarma

Manyan kaya ya saka farare tas sai hularsa CE da takalmin shi ne baqaqe

Sai aqoqon hannushi Na Axurfa da yaketa shegi


Ya kifa hular nan tayi Ras a kanshi ta gefe gefe kuma da qeyarsa gashine kwonce lub 

Sai wani irin qamshi yake fita daga jikinshi

Ido ta zuba mai Dan ganin yau kamarsa da ya Ahmad tafi ko yau she fitowa

Gabanta yaxo ya Dan tsaya

Cikin

Kauda kai Dan gani yake kamar zata gane halin da yake ciki

Dan dolece  ta sashi Sa jomfa Dan baiso ta gani a sana yake😜


Cikin kauda kan yace ki shirya

 ana sauqowa sallan jumma,a zamu tafi 

Eprt

Dan qarfe 2:20 pm jirgin mu ✈zai tashi


Wayyo dadi gun Aysha ba,a mgn

Qara tayi cikin tsantsar farin cikin da

Rakadi ta buqa tsalle ta fada hikinshi hannu bibbiyu tasa ta sanqalo wuyanshi

Cikin murna ta manna mai lafiyeyyen kiss a kumatun sa Na dama 

sai kuma ta arce a guje tayi

Dakinta tana 

Alhamdulillah (habde kam mi hota tai)

Yau kam zan koma.


Shi kam Yusuf dole ya fada kan kujerar Dan ya samu ya saita kanshi tukun

A ranshi kuma zafi yakeji meyasa take farin cikin komawa?


 Toh fa Yusuf anya Kansan menene a zuciyar ?

Ni dai Garkuwa wannan tabayar nayiwa   Yusuf kuma banda amsarta


Amman kumuje zuwa


2:30 pm jirginsu✈ Yusuf ya dage xuwa qasarmu ta aihuwa

Nigeria


Qarfe bakwai dai-dai...


By garkuwan fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI,WASMITI, page 9⃣5⃣Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Suka shigo

Babban parlon gidan Adam da Yusuf suna jere riqe da hannun juna farin cikin fal zuqatan su 

Aysha ko tana shiga Amira tayi kanta da sauri cikin fara,a da tura katon cikin ta

Cikin mmk Aysha ta ruqumuto

Gamida shafa cikin 

Da alamu tabbaya 

Ta kalleta cikin zumudi tace 

Amira cikin kema har kin qunsa shine ko ki gayamin Na tayaki addu,a Allah ya raba lfy

Amira kan sai murmushi da sune kai Dan kunya sosai Aysha ta bata ga Hamma Yusuf da take jin tsoro yanzu zaice sun ishesu da surutu

Da sauri ta kuma sakin Amira jikin Maryam ta fada cikin kewar juna suka ruqqumi juna

Sun kasa mgn sai dai su kalli juna su sake fadawa jikin juna.

Ummi ce

 tai dry cikin qaunar Aysha tace 

Yau naga ikon Allah Aysha ase kinfi kewar yan uwanki damu

Da sauri kuma ta saki Maryam ta konta jikin umminta cikin qaunarta tarinqa sinsinar ta tana I miss you so much my lovely Ummi Na 

Gaba daya suka kwashe da dry daga gun Ummi ta koma gun Nenne 

A haka dai duk ta bisu da gaisuwa.


Shi kam Yusuf suna shiga ya zauna kan kujera 2 str bayan ya gaidasu daya bayan daya.

Kaka dake ruqqume da jaririn tazo ta miqamai 

Hannu bibbiyu yasa gamida karbar yaron

Cikin tsantsar son yaron ya zuba mai ido

Lkci daya tunanin Dan uwanshi ya fadomai

Qaunar yaronne ya rinqa ratsa zuciyarshi

A hankali ya daqo yaron ya mannashi a qirjinshi

Cikin sanyin murya da alamun quna a zuciya

Ya kalli Maryam yace maryam Allah ya raya  manashi da imani,

Amin ya rabbi ta fada cikin muryar kuka

Tare da qoqe qollah

Aysha dake jikin Nenne ta miqe da sauri tayi gun Yusuf 

Cikin zaquwa tace 

Hamma Yusuf banishi

Bai kalleta ba bai kuma Ciro 'Dan ajikin shiba

Cikin jin haushi tace kabani yarona

Mana 

Kaka dake qefensu tace toh in banda abinki

A hakan zaki karbi Dan Ki xauna mana.

Naqi in zaunan 

Ke wlh ai kuma mutum ya boni da shishiginki

Da sa ido

Ehh nayi Sa idan shegen baki Na kin samu kin miqe

Harda wasu duwaiwuka da kika ajiye kin kasa daukan cikin sai she gen kadifiri


Gaba daya kuma sai mgnar kaka ta Dan sasu murmushi Amman banda Yusuf

Da sai yanzu kaka ta darso mai wani Abu a ransa

Wani Aysha ta kasa daukan cikin


Tofa Yusuf😜


Nenne CE tace Aysha zauna ko ki karbi danku

Toh tace 

Gamida zama kusa da Yusuf din har hips dinta Na gogan cinyarsa

Hannu tasa a hankali ta tura ta qasan jaririn daya hannu kuma ta sama

Cikin qoqarin dago yaron ne ta yi kuskuren tura hannu har ya shafo oga Yusuf

Da sauri ya matse cinyarsa gami da sauqe wani irin nannauyan ajiyar zuciya

Itako batama San tayiba

Daqa yaro tayi ta zuba mai ido cikin 

Sanyin murya tace photo copy ya Ahmad

Kai ta sunkuyar ta rinqa subbatarsa 

Cikin rawar murya take fadin

Maryam ina son yaron nan maryam zaki banishi

Sai hawaye shar a idanta

Shima jajari kamar ya sani sai ya rinqa kuka

Hannu Yusuf yasa ya karbeshi ya sashi kan kafadarshi

Cikin murya qasa qasa yace 

Kayi haquri dan

Uwana banson jin kukan ka

Randa 

Baban ka  zai  rasu ya gayamin kaine madadin shi a guna a hankali yaro kam ya fara shiru

Ita kuwa Aysha cikin kuka

Ta Dan roqqofo

Jikin Yusuf har qirjinta Na gogar kafadarshi

Tana tayar mai da tsikar jikinshi

Da son samune duk ya hadasu ya ruqqume da jaririn

Dan ya tabbata da Ahmad yana Raye da haka zaiyi,

Hawayen

Ta ne suka rinqa diga kan habarsa

Cikin kuka tace

Hamma Yusuf kawoshi ko yunwa yakeji

Ido ya tsura mata cikin miqa mata shi ya hada da hannuta

Ya riqe ta kasan blanket din  yaro

Ya rinqa murza yatsunta cikin salon lallashi

Kai ya kuma dagawa cikin alamun kibar kukan

A haka suka riqe yaron

Yana kan cinyar Aysha Yusuf kuma idanshi Na kan yaron


Baba bello ne yayi gyaran murya cikin girma yace

 Yusuf dama kai muke jira kayiwa yaro huduba da bakinka

Dan wannan shine fatan Ahmad

Kai ya jinjina cikin sanyin jikin ya daqo kanshi yace baba wanne suna za,a samai?

Sunanka zaka samai!


A hankali yace baba nikuwa da sunan biyaye Na zan mayar mai,

A a 

Shi Ahmad dama yace matuqar

Dai Allah ya bashi d'a namiji toh sunanka zai sanya mai

Kai ya sunkuyar gamida karbar yaron ya mai huduba

Da sunan Sa

Aysha kuma sai sharar qollah take A hankali ya zaron hankicif dinshi mai laushi da taushi sai qamshi mai dadin shaqa yake fitarwa ya miqa mata

Karba tayi ta share qollar

               *******

A haka sukai ta hiran yaushe gamo 

Har zuwa 11 Na dare Yusuf yasa su

 Usman da Rabi,u suka dauko akwatunan da ya ciko da kayan jaririn ba wani abin da bai yiwa wannan yaro ba yaro kam yasha gata

Sai 12 sannan suka waste Adam ya dauke matarsa suka tafi

Shi kuwa Yusuf

Dama an gyara mai part dinsu

Can ya tare

Su Usman kuma suka koma dakin

Adam

Aysha kuwa ta dage ita dai tare zasu kwana

Da yaron ta da yar uwarta

Qanne babansu ma Dr umar sunzo daga Yola 

 

              *****

        Kashe gari 

Ran Sartudey 

Akasha biking sunan Yusuf qarami

Ba wani shagali da akayi sosai sai walina da aka gudanar

Yaro da mahaifi yarshi sunsha gata a gun yan uwa da abo kan arxuqi

Anty Sadiya ma ta taka rawar gani

Hatta su Rabi,u sun yiwa yaro kaya sosai

Bare aje ga lodin kayan da tokwaranshi ya mishi wasuma sai ya kai shekara 9 

Yana sawa

Anyi suna lfy an waste lfy


           "-"-"-"-"-"-"-

Yusuf ne kwance kan gado gaba daya yarasa abinda ke mai dadi a rayuwarsa

Da ya rumtse idanshi ba abin da yake gani sai fuskar Aysha

Sam ya rasa meke damunshi

Ya rasa bacci mai dadi ya rasa sukuni

Ba abin da yakeso gani daji kamar ita

Yayi kewar tattausar fatanta

So yake ya kori tunanin

Amman ya kasa

A fili yake cewa yaufa kwana 

8 kenan da zuwanmu tsaki ya Dan ja

 cikin takaici

Yace toh wai me hadina da ita

Zuciyarshi ke cemai salon ta raina ka kake nema

Gaba daya kuma ya kasa samun nitsuba yasha magungu nansa har ya gaji Amman Sam ya kasa nitsuba

Tsaki yaja gamida miqewa

Jallabi ya zura a jikinshi

Cikin hada fuska ya nufi.

Cikin gida

Kai tsaye parlon

Nenne ya wuce tun daga baqin qofa yaji hayani yarsu sunata dry

Yana shiga ya samu hardasu Adam da Amira sun zo ga Anuty Sadiya ma tazo

Sai dai tana shirin komawa Dan dare ya farayi

Hannu Adam ya miqa mai cikin fara,a yace kai INA ka shigane haka 

Ga sakaliyarka ta buwa yemu da fitina wai ita yunwa takeji kuma bazata ci ko mai ba sai inabi da tufa ko dabino da kwakwa

A deren nan fisabilililahi a Ina za,a samo matashi

Abu sai kace mai ciki kodai da cikinne? bamu saniba!

Shi kan Yusuf baki ya tabe gamida bata fuska

Ita kuwa tana ganinshi

Ta gyara goyon da tayiwa Yusuf qarami

Ta matso kusa dashi cikin tura baki tace

Hamma Yusuf

Yunwa nakeji

Bai kulata ba bai kuma kalleta ba

Sai Adam da ya kwashe da dry yana tab lallai Aysha abin naki azimun ne

Sadiya ce tai dry tace wlh ko a can haka  take takura Yusuf gsky Aysha lamarinki da gyara

Ita dai qara matsoshi tayi tare da kamo hannu shi

Ta matse a qirjinta

Ta manna kanta kan damtsen hannushi

Cikin muryar maijin yunwar dan da  gske yunwar takeji

Tace Hamma Yusuf

Wlh yunwa nakeji.

Kai ya 

Dan sunkuyar cikin tsura mata ido

Yace toh ya kikeso nai miki?

Ko zaman ma bazaki barni nayi bane?

Ita dai cewa take ni yunwa nakeji

Juyawa yayi ya nufi kan dinning table 

ita kuma ta maqale dashi

Kulolin ya bubbude

Cikin Dan daga murya yace ba ga abinciba ki zauna kici

Mana

A a nidai ba tuwo Zan ciba


!Adam kam dasu Nenne dasu Usman

Mmk ne ya cikasu sosai

Yusuf ne ke ta faman sunqullah da Aysha fada da masifar nan duk ya qare


Adam kan sosai ya rinqa binsu da ido

Cikin mmk

Shi kuwa Yusuf parlorn

Ya dawo

 itama tana biye  dashi goye da Yusuf qarami da yake ta baccin sa

Maryam kan sai sake baki tayi tana kallon su

Amira CE ta Dan matso kusa da Adam a hankali tace ya Adam mu tafi gida bacci nakeji

Cikin kula

 ya shafa fuskarta yace toh

My mirah mu tafi ko

Hannu ya miqawa Yusuf cikin dry yace to babban Yaya mukam xamu wuce inda mukafi wayo.

Shi kuwa sai tabe baki yayi ya cilla mai harara cikin qasa qasa da murya yace wlh ka dai ji jikin ko kunya babu ka wani maqale a jikin mace yar qarama

Shi kam Adam dry sosai yayi cikin jinjina kai yace 

Toh wlh  ba wahalelle kamar ka kuma Allah ina gayama Kaine kake dab dajin kunyar 

Dan wlh ko yanzu kai abin tausayi ne ji yadda qanwata ke juya ka kamar masa a cikin kasko

Wlh tausayi kake bani

Ya rigada ka gama macewa a kan qanwata

Saura qiris girman kannan naka yaje qasa warwas


Sake hannushi yayi cikin kufala yace wlh kai banzane

Wlh ni ba wata mace da zata kai a  gareni bare Na wahala a kanta

Kaima ka sani sarai

Ina bata kulawa ne Dan ita amanar Ahmad ce kuma wlh ni tausayi ma take ban

Dry Adam ya kumayi tare da daga mai gira daya

Yace ai da Zara kaji wani Abu wai shi tausayi

To ka gama narkewa cikin wutan so yaro baka game bane


Duk mgnar da sukeyi ba Wanda yaji ko ita Aysha da take gefensu bata jiba.

Dan sai faman diri take cikin son yin kuka a ankali

Ta kuma cewa yunwa fa nakeji.

Da qarfi cikin fushi da tsawa

Yusuf ya juyo gunta

Kamar mai kwada mata Mari sai

Kuma ya bige da cewa

Kai naa shiga uku yanzu Dan Allah munxo gidan ma bazaki barni nasha iskaba

Dan Allah kar ki cinyeni

Aikin banxa sai shegen fitinar tsiya

Ki biyoni part dinmu kizo ki karbi

Inabin akwai guntun da Na ajiye Dan

 dama Na sanki kin iya naci mayya kawai

Yana kaiwa nan ya fita

Adam ne ya bishi a baya cikin

tsokana yace ai wlh ka hadu da raini kenan tunda ka kasa

Nuna mata cewar kaifa namiji ne

Yoh ba dole ta rainaka ba

Tunda zata ke zaton kai mata mazane

Tunda bazaka iya mata wani Abu ba ai ka ciyar da ita Don dole

A haka sukayi sllm suka tafi Sadiya ma ta fito ta tafi tare da mijinta


Yusuf kan yana shiga toilet ya fada wonka yaje yayi cikin jin zafin maganganun Adam a ranshi yake cewa mayya zatasa yara su rainani a banza

A hankali ya tabbayi kanshi

 wai shinma da gaske ne zata iya rainani

Wai tamin kallon mata maza kai INA 

A haka ya fito bai Sa komai ba ajikinshi

Sai wondo

 3qtr sai turare da ya feshe jikinshi dashi

A haka ya fito parlon ya fito keban ita kuma ta shigo

Cikin Dan murguda mai baki tace gani ka bani

Ni kam Zan tafi

Kallonta yayi a fakaice cikin jinjina kai lallei kuwa 

Yarinya kin rinqa

Bai kulata ba ya wuce ta gefenta bakin qofar yaje ya tura qofar garam ya murda key din ya zaroshi

Cikin mmk da tsiwa tace nifa ka bani in zaka bani ka wani rufe qofa

Danni bacci zanje inyi ehe😏


Kai ya jinjina cikin cije lips dinshi a ranshi yace zaki shiga taitayinki.


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI,WASMITI. page 9⃣6⃣ Na Ayasha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


A hankali ya tako yazo gabanta 

Ya tsaya cikin murtuqe 

Fuska


Itama kai ta dago

Sai kuma tayi saurin rumtse idanunta gam

Lkci daya jikin ta 

Ya fara rawa

Tsoro ya kamata

Dan tunda suke da 

Hamma Yusuf bata taba ganin shi ba rigaba

Qirjinshi da hannushi sun bata wani irin tsoro

Qirjin cike 

Yake da gashi baqiqqirin

Mai taushi da laushi yana konce lib a ajikinshi sai shewi yakeyi hannushi

Da sharaban qafafunshi

A ranta take cewa

Na shiga uku

Anya kuma 

Hamma Yusuf ne wannan 

Ido ta bude da sauri jin

Ya qara matsota

Ido ya tsura mata cikin

Yin piki piki da idan nashi

Hannushi yasa kan qirjinta

Ya kwance abin goyon

Da ta goya 

Yusuf qarami

Da sauri 

Ta buge hannun nashi Dan jin yana tabo albarkatunta

Cikin tsiwa tace 

Me haka ya za,ayi ka kwance mai zanin 

Goyonmu in ya fadifa

Me zaka cewa uwarsa 

Dan kai baka San wahalar yaro ba

Ni ka bani in zaka 

Zaka bani ehe😏

Duk mgnar da takeyi kanta a gefe Dan tsoron ganinshi take

Shi kuma shiru yayi ya tsura mata ido yadda take zuba mai tsiwa harda

Murguda mai baki

A ranshi yake cewa lallai yarinya kin gayamin mgn

Bansan wahalar daba!

Da kyau

Cikin ajiyar zuciya ya qara

Sa hannushi

Ya kunce abin goyon ya juya bayanta

Ya ciro yaron a bayanta 

Cikin bedroom ya nufa

Ita kuwa da sauri ta sake 

Qaton lufayan jikin ta!

Ta bishi a baya 

Tana ni kabani yarona wlh ni banson haka

Bai kulataba har sai da ya kontar dashi can gefen gaqon

Ya juyo

Cikin qatsaita

Gabanta 

Ya tsaya

Ita kam taki.kallonshi sai wani kauda kai takeyi tana ja da baya

Shi kuwa yana binta a baya

Har ta isa jikin gini

Hannushi yasa daga qasa ya jawo hijabin ya cire mata ya wurgar dashi can gefe

Ido ta zazzaro😳🙈🙊 da sauri ta kaleshi gamida Sa hannu bibbiyu ta tare qirjinta Dan dama zanin goyonne ya rufe mata qirjin 

Da garfi tace 

Me hakan

Cikin tsura mata ida 

Ya daga mata qirarsa daya😉

Murya a daqile yace

Fitsara

Ba kin iya yarashin kunyaba

Baki ta kuma murgudawa

Gami da kaucewa zata 

Wuce ta gefenshi 

Tare da cewa 😏ni baba son iskanci

Aikin banza kawai!

Da qarfi yasa hannushi ya kamo damtsen hanbayenta duk 

2 ya budesu daga kan qirjin nata

Ya turata zuwa jikin gini

Ya ware hannayen nata ya dannesu a jikin ginin

Qirjinta ya fito ras a gabanshi

Albarkatunta suka wani

Taso kamar zasu stone mai ido

A take bugun zuciyarsa ta tsananta

Numfashinsa ya fara carkewa

Ita kuwa

Sai kuka ta saki

Cikin mutsu mutsu kuma ta kasa qwatar kanta

Kai ya Dan sunkuyar 

Cikin rawar murya

Yace 

Ehh Na yarda ni Dan iskane

Kuma yanzu iskancin

Zan nuna miki

Ba daikince ke fitsa rerriya bace 

Zanyi mgnin wanban bakin da kike murgudamin

Gobe ko kudi aka baki kimin tsiwa bazakiyi ba.

Cikin kuka tace

Wlh bana so mugu kawai azzalumi

Da sauri yace qarya kikeyi kina so kam

In byake so me ya kawoki dakina ?

In bakya so meyasa zaki zomin ba ko Riga?

Ba dai so kike 

A miki ba shine kiketa maqalemin toh zaki samu

Baki ta kuma murgu dawa

Tace wlh Allah ya isa mugu azza lumi ba kai kace nazo zaka ban inabi 🍇

Ba 

Sai kuma tai shiru cikin zaro ido

Da firgici da bugawar zuciya

Jin yadda 

Hamma Yusuf ya

Hade bakinshi da NATA

Cikin wani irin salo

Ya cabko harsheta 

Tamkar mayunwacin zaki

Tsoronta ya qara tsananta gaba daya jikin ta sai rawa yakeyi

Ihu take sonyi Amman INA ya riqe harshen ta sai wani irin sarrafashi yakeyi yana tsotsa tamkar maye 

Sai numshi yaketa fixga

Jikinshi kuwa tuni ya fara rawan sanyin

Hannuta ya saki Dan ya tabbata yanzu kam ya gama mata illa Dan tsoro da firgici sun tafi da qarfinta

Kan qirjinta ya daura hannushi har rawa suke tamkar mazari

Bakinshi Na cikin nata 

Ya kuma rinqa 

Murza dukiyar fulaninta tamkar ba qobe

Ina gaba dayan su tsayuwa ta gagaresu

Dole suka zame kan carpet

Cikin azam ya qara matsota jikinshi

Gaba daya jikinshi sai rawa yakeyi

Ita kam Aysha

Hamma Yusuf yau ya zame mata dodo

Sai zazzare ido takiyi tana tsurawa fuskarsa ido

Shiki baima San tanayi ba

Da qarfi ta samu ta sabulo harshen ta daga kan nashi

Wayyo Yusuf qara matseta tayi tare da sakin wani marayan qara tamkar Dan da uwarsa ta qwace mai nono

Da sauri ya kuma cabko

Pink lips dinta


Allah sarki yau kam Yusuf ya samu ya hade da abin da yake ta bege🙈😝


Hannun ta tasa tana tureshi

Jin laushin tafin hannnta yasa jinin jikinshi tsinkewa

A take ya ji wani irin kuzari


Cikin azama ya cicci bota yayi kan gado da ita

Ita kam sai wutsul wutsuk takeyi

A hankali ya sake lips din NATA ya rinqa bin duk jikin ta da kissing har ya iso 

Kan qirjinta

Gaba daya ya fita hayyacinsa sai juyata yakeyi ta yadda yaga dama

Hannu 2 yasa ya runqumota gamida manna bakinshi kan mamanta 

Ya rinqa tsotsa

Sai gurnani yakeyi

Ita kuma ta samu an sake mata baki

Sai kuka takeyi tana qoqarin cire mamanta daga cikin bakinshi

Kuka take sosai

Tana wayyo Allah na wayyo ummina

Na shiga uku

Hamma Yusuf zai kasheni

Mugu kawai azzalumi

I Hert U 

Wlh Na tsaneka

Bana sonka ni kai ba Dan uwana bane

Mugu.

 dama kai ka mutuma ya Ahmad dina ya rayu!

A hankali kala manta suka rinqa ratsashi

Lkci daya

Jikinshi ya rinqa macewa

Yanayinshi ya sauwaya

Bakinshi ya zaro

Gamida komawa jikin pillows ya koma ya konta cikin fidda wani irin nishi

Ita kuwa da sauri ta yunqura zata miqe

Sai kuma taji

Yana riqe da hannuta

Gam

Cikin sanyin

Murya yace

Koma ki konta

_Amrita_ ba abinda zan miki,


Toh fa yau kuma Aysha ta koma

*Amrita* kenan😝😀


Hannuta

     ta rinqa qoqarin qwacewa Amman ta kasa

Shi kuwa da yaga haka da qarfi

Ya fizqota ta fada

Kan qirjinshi da yake bata tsoron

Matseta yayi da hannu bibbiyu

Cikin rawan murya

Yace 

*Amrita* 

Anan zaki kwana kiga time fa yanzu 2  Na dare zaki samu sun rufe qofar shiga

Ban son kije ki haduda wani abin cutarwa a gareki ke da Yusuf qarami nawa

Amrita kinsan

Cewa Ku 2 biyayena ya barmin amanarku

Ke kin kasance amanar tawace

Shisa kika zama amrita fatan kin game ma,anan *Amrita*

Dan kar kiyi tunanin

Wani Abu akan sunan


_Zadai ka gane_😝


Ita kam kuka takeyi cikin fushi da tsoro tace

Ka sakeni in tafi

Gwara Na hadu da komai ma ai Kaine babban abin cutawa ta

Bai kulata ba sai

Jawota kawai da yayi

Ya daura qafarsa daya kan mazaunenta

Hannushi kuma ya daura kan qirjinta

Kanta ya daura kan kafadarshi

Cikin tsawa yace maza kiyi bacci

Kar ki tayarmin da yarona da rikicinki.

 ta bude baki zata kuma mgn ya cabko

Harshen ta 

Zai fara tsotsa ta ture kanshi tace nabar kukan

Murmushin

Mugunta yayi yace aiko da kin kyautawa kanki


A haka cikin qirjinshi

Baccin tsoro da wahala da firgici ya kwasheta

Shi kam Yusuf yadda yaga rana haka yaga dare Daren wannan rana ya mishi duhu da tsawo

Yasha maganinshi har ya gaji

Amman bai samu nitsuwar da yeke buqataba

Tana baccinta Amman shi kwana yayi yana zirga zirga

Ya kuma yiwa kanshi alqawari bazai mata abinda bata soba sai da yardarta

Yaje parlo ya dawo kan gadon ya tsura mata ido

In ya gaji yasa hannu ya Dan shafi mamanta sai ya kuma rinqa sauqe ajiyar zuciya

A haka dai har aka kira sallah

 Da gyer ya samu yaje masallaci

Dan ma a cikin gidan yake

Dan gaba daya ciwon Mara ya addabi rayuwarsa


Yana shigiwa ya samu har yanzu bata farka ba shima Yusuf qarami Dan albarka ya bar Abbanshi ya Dan Shana

Sai yanzu yake qoqarin tashi

A hankali ya qarisa bakin

Gadon

Cikin sanyin murya da tsotsa lips dinshi

Ya rinqa kiran ta 

A hankali

Amman bata motsaba

Sai da ya Dan sunkuya cikin sanyin hannushi ya

Shafo qirjinta

Gami da cewa

*Amrita* ki tashi ki maida yaron nan gun mamsnshi a bashi nono

Cikin razana da firgita ta miqe

Sai kuma tayi saurin rufe qirjinta da hannu

Shima kai ya sunkuyar cikin murtuqe fuska waishi kar a rai nashi


_su Yusuf manya wai a dole kar a rainashi_


Ita kam sai hawaye a fuska share Dan tsabar takaici 

Shi kuma juyawa yayi

Hijabinta ya dauko

Ya wurga mata ya koma gefe ya dauko qur,aninshi ya fara karatu


Sa hijabin tayi gamida ruggumar Yusuf qarami

Ta fita tana sharar qollah da Jan Allah ya isa

Binta da ido yayi

Cikin ransa ya ji murmushi ya Dan kufce mai

Sosai yake tunata yadda ta tsorita a Daren jiya

A fili yace dama matsiwaci ya kan kasa CE matsoroci ai



Ita kam Aysha tana shiga taci karo da Nenne

Da sauri ta sunkuyar da kanta ido cike da qollah

Gani take kamar kowa yasan abinda Hamma Yusuf ya mata

Dakin Maryam ta nufa

Tana shiga ta samu ita kuma ta fito daga wonka

Kenan

Da sauri ta qarisa gunta

Cikin zubda qolka ta daura Yusuf qarami kan cinyar Maryam tace Maryam bashi nono ya Sha

Itako Maryam sai leqa idanta takeyi

Dry tayi cikin sanyin

Tace

Daga zuwa karbo

Inabi sai kuma aka tsaya karban pakala ko?

Ai ni wlh dama nasan wayone kawai Hamma Yusuf yake yi

Wai kibiyoni kixo ki karba shi dai yasan abinda yake so

Taci gaba da cewa

Su kuma haka Allah ya yisu

Haka ya Ahmad yake da 

Kuma kinga ya Adam ma ba sauqi

Ita kam Aysha  kuka ta saki gamida 

Kontar da kanta kan

Gado

Maryam tace toh lallai abin naki nayine

Cikin kuka tace

Maryam wlh ni bansan abinda Hamma Yusuf yake nufi da niba

Wlh so yake ya kashe ni

Yanzu gaba daya sai kinji yadda nakeji

Qirjina

Duk ya lallatsemin

Mamana sunyi jazawur

Mutum kamar maye

Cikin sanyin Maryam tace to Aysha ai Hamma Yusuf yama yi haquri yaufa kusan kwananku

18 Amman bai nemi haqinshiba

Aysha kam ta gano Maryam bata San wanne irin zama sukeyi da Hamman nasuba

Shisa cikin kuka 

Ta shige toilet tayi Alwala ta fito tayi

Sallah

Da Nenne ta shiga sai tai maza ta rufe ido

Wai ita maiyin bacci

Ita kuwa Nenne dadi takeji ganin yanzu komai ya daidaita tsakanin yaran nasu


Ita kam Aysha tun daga ranan take wasan buya da Yusuf

Shi kuwa Yusuf Allura ta tono mai garma

 

Ya gomce bai tsakalo jarabarsa ta tsiyar nan ba zuwa yanzu

Koyasha mgni basa mai aiki

Randa Adam yazo ya sameshi yana ta daura magunguna

Yasha tsiya kam

Har ya hatsala

Yanzu Sam bai iya bacci

Da ya rufe idanshi

Qirjinta zaike gani

Kullum sai yayi mafarkinta

Sosai yakejin nishadin in ya tuni yadda tsoron shi ya kamata ta rumtse ido sai

Zuba kuka takeyi

Mmki yake yadda lkci daya tsiwar tata ta gudu sai tsoro


Yau kwana 5 kenan da faruwar abin

Bayan sallan isha Yusuf ya nufi dakin umminshi

Dan yunwa yakeji ga bege da buqatuwa

Yana shiga 

Ya samu Aysha ita kadai

A dakin tana kan sallaya daga dukkan alamu

Ta Idar da sallah ne

Amman gani Hamma Yusuf ne yasa ta tashi

Cikin hikima ta rinqa jero nafilfili

Kai ya jinjina cikin ajiyar zuciya Dan ya ganota sarai

A hankali ya koma bayanta kan sallayar dai dai lkcin da tayi zaman tahiya......



*👀👀kai masu son ganin qoqof duk wannan idon leqen Hamma Yusuf toh Zan jamusu labule*😝😍😘


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

NAYI NADAMA

👇🏻👇🏻👇🏻

MI,WASMITI 9⃣7⃣,Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇

?🍇🍇🍇


```Ina qaunarki da alfahari dake 

Khaleesat Hydar```😍



Qara motsota ya kumayi 

Tare da manna faffadan qirjinshi kan bayanta

Hannushi ya zaqoyo ta gabanta

Ita kam Aysha 

Tun da taji

Motsinshi kusa da ita taji gaba daya tsoro ya rufeta tsikar jikinta ne yatashi yarr

A lkcin da taji

Yasa bakinshi ya kamo zip 

Din rigarta  ya zugeshi

Da sauri ta juyo cikin tsiwa tsiwa 

Tace 

Me hakan me nayin halin akuyanci

Ni gsky banson takura katsakeni

Ni ban iya rashin kunyaba.

Bai kula taba 

Sabida zuwa yanzu 

Ya fara daburcewa

a hankali ya cusa hannushi cikin rigar tata

Cikin sabon salo

Ya daura hannushi kan bres dinta 

Cabkesu yayi kamar a kidime ya fara shafasu da luguiguitasu

Gaba daya ya birkice sai wani irin numfashi yake ta

Fizga

Ita kuwa

Abin ya wuce saninta

Zuwa yanzu kokonto ya fara kamata

Anya kuwa 

Hamma Yusuf ne yake mata 

Wadan nan sabbabin darusan kodai

Aljanine

Cikin kidiman d qoqarin kwace kanta daga gareshi ta juyo

Dan taga shi din ne kam

Shi kuwa samun haka ya sashi samun damar daura kanshi kan cinyarta

Harshen shi ya zura cikin hudar cibiyarta

Da Dan qarfi ta saki

Qara gamida ci gaba da janye jijinta

Kuka ta saki

Tare da cewa

Na shiga uku

Kai mayene 

Cinyeni zakayi

Wayyo Allah Na.

A hakali

Cikin shan yaji 

Gamida tsura mata ido

Murya a daburce

Yace waye Dan akuya

Sannan waye mayen

Duk maganar da yakeyi hannushi Na kan abinda yafi komai fidda mai hankali a jikinshi

Ya dage sai cakudasu yakeyi 

Hannuta ta Sa

Tana jawo nashi

Ganin bazata iyaba

Yasa tasa kan yatsunta ta rinqa Jan

Gashin hannushi

Tana ka sakeni ni sallah zanyi

Ido ya kuma tsura mata cikin murtuqe fuska yace

Garya ne 

Ba sallan da zakiyi

Ai kin idar 

Ganina ne yasa 

Kika wani ci gaba da sallah

Toh wannan sallah da kikeyi INA da damar katseshi

Qara matsota yayi ya cire

Hijabin jijinta

Rigar ya ya tartare ya maidata kan wuyanta

Kanshi ya nufa kan bres din nata da sauri tace me hakan 

Cikin isa yace

Akuyancin

Zan goda miki

Tini ya manne bakinshi

Ya fara sarra fata

Cikin qorewa da karantar abin

Bakinta kuwa tuni

Ya mutu sai hawayen dake 

Zuba shi kuwa

Murzata yake iya son ransa

Wai ko zai samu sauqin

Abin

dake cinsa

Suna cikin haka

Kamar daqa

Sama yaji

Slmar

Usman

Da sauri cikin murtuqe fuska ya jawota ya kifata kan cinyarsa

Zip din rigar ya zuge ya hadamata shi miqewa yayi cikin taqqal tanqqal

Kamar bugegge ya koma kan kujera ya zauna gamida da

Zaro phone dinshi

Ya rinqa latsawa

Sannan ya amsa slmar

Ita kam tuni ta miqe cikin gyara daurin zaninta

Tare da ninke sallayar

Usman Na shi

Yace 

Hamma Yusuf barka da

Hutawa

Kanshi a qasa ya Dan geda mai kai alamar youwa

Ganin su biyu ne a dakin yasa Usman kuwa juyawa

Da sauri tabi bayanshi

Har taje bakin

Qofa

Taji shi

Cikin narkekkeyir

Voice

Yace

*Amrita*

Tsayuwa tayi bata fita kuma bata juyoba

Takowa yayi

Cikin qarfin hali

Ya Dan sunkuyo

Kanta gashin ya tattara ya tubke mata

A hankali yace

*Amrita*

Yunwa nakeji

Hannuta ya komo

Ya tura cikin rigarsa

Qasan cibiyarshi

Ya daura hannun nata cikin ajiyar zuciya yace

Kijifa cikina ba komai

Sai yunwa

Ita kuwa ido ta zazzaro

Jin inda yake qoqarin tura hannuta

Da sauri ta fizge hannun

Cikin azama tayi

Babban parlonsu inda nan suke taruwa suyita hira


Tana shiga ta samu su baba bello dasu Nenne da Ummi da ya Adam suna zaune

Daga dukkan alamu

Mgna CE mai girma da ma himmanci sukeyi

Shi yasa sai kuma ta juya a hankali

Ta nufi

Cikin

Kitchen

Tana zuwa sukaci karo

Da Lami mai aiki

Riqe da cup

Din tea

Hannu tasa ta karba cikin cewa youwa tawa nagode

Da sauri Lami tace 

Ke Aysha Na 

Yusufa ne fa

Karki Sha.

Cikin tsiwa tace

To sai me in nashi ne wlh shanyewa zanyi muga ta iko da mulki

Wai ke mama in dai Hamma Yusuf ya saki aiki 

Toh sai ki wani ajiye aikin kowa sai nashi

Shi kuma sai wani mulki yake shinfidawa

Fada take tana tafe

Kanta a kasa

Tana yau sai dai ya kwan da yunwar

Da sauri ta daqo

Kanta jin taci

Karo

Da mutum

Cikin zaro

Ido ta miqa mai

Cup din tare da cewa

Ni kam ga tea dinka ba ruwana.

Dry ta bashi sosai

Da ta zage tana mai iyayi

 Amman daga ganinshi ta daburce

Sosai dryar taso kubce mai

 Amman sai ya kuma murtuqe

Fuska yace

Wa zaisha sauranki

Duk kin zuba yawunki

A ciki qazama kawai

Ni zaki bawa jogolgolonki

Allah ya kiyaye

Ya tabe baki gamida yamutsa

 fuska ya kalli Lami yace a karo min wani kar a samun a wannan cup Din 

toh tace cikin mutun tawa

Shi kuwa juyawa

Yayi ya fita yana  ai sai ki shanye yawunki


*lol su Yusuf to wanne yawun kuma ya rege da bakashaba kai jin kai dai zai wahal da kai ka gama tsotse bakin year mutane sannan ka fito kace wai baka sha yawunta ba😂😝*


A parlor kuma

Cikin hikima da qirma baba bello da Abba ke yiwa su Ummi da Adam nasiha

Cikin sanyin Abba yace

Na tabbata kun sheida Allah shike rayawa kuma shi ke kashewa nakwo San kun yarda macecce bai dawowa sai dai idan dama suna yayi

Ko?

Nenne da zuciyarta ke ta bugawa tace 

Wannan haka ne mun yadda da haka 

Dan Allah a gaya maba meke faruwa

Cikin ajiyar zuciya

Abba yace 

Shekara 1  da ta gabanta

Munyi kuka munyi jimami mun shiga tashin hankali Na rashin Ahmad

Cikin rashin sanin Ahmad suna yayi ba mutuwa ba.

😳😳 cikin rashin fahimta Ummi da Nenne da Adam suka firfiti da ido woje cikin kidima d firgicin zancen da suke jin.

Kai Abba ya Jinjina musu

Cikin gsky da gsky 

Ya fara basu lbrin yadda abin ya kasance

  

       Randa Ahmad ya rasu

Mun dauko gawar da niyar zamuje muyi mata wonka da sutura

Ni da hydar da Dr Umar ardo

A wurin wonkanne 

Hydar ya kalli yatsar Ahmad Na harbawa cikin tsoro da firgici

Ya ke sheida mana da fari mun dauko gizone kawai Dan firgicin rashinshi ya samu hakan Amman daga baya sai mukaga

Jijiyar kanshi da ta dunduniyar qafanshi suna harbawa

A take Dr Umar ya goggo dashi anan take muka gano doguwar suma yayi kuma tabbas zai iya rasa ran nashi ko yaushi

Toh ganin haka yasa a Daren Dr Umar ya fita yaje ya shirya mana komawa India Amman sai ta Yola

Ganin bamu da tabbas din rayuwar Ahmad yasa mukaqi sheidawa kowa hydar ma muka hanashi fada 

  tun cikin Daren muka fita da Ahmad zuwa kamanni hospital

Sannan  muka dauko wota qawar da aka rasa yan uwanta mukazo ni da Hydar muka mata wonka muka mata sutura

Koda gari ya wayyi ita aka sallah ta

Kuma ita aka binne

In Baku mantaba a ranan

Ni da hydar muka tafi India

Tare da cemuku

Nine ban da lfy hawan jinjina ya yau

Shi kuwa Dr Umar zaku

Iya tunawa sai dare ya dawo gun gaisuwar makokin

Bayan yaga mu jirginmu ya tashi zuwa Abuja canma muna zuwa muka kuma miqewa India


            India

Qoqarrun likitocin zuciya

Suka dugufa sosai

Wurin cetoh

Rayuwar Ahmad

Babban matsalan a samu ya farfado sannan ai matsa aikin tiyatar zuciya

Mun zauna tsawon wata 7 Ahmad bai San inda yakeba sai numshin da yake fitarwa da taimakon Na ura

A haka wata tana ya farfado

Farin ciki a gunmu ba a mgn 

A take Na kira Dr Umar Na sheida mai toh ase lkcin Dana kira suna tare da yaya bello

Toh shima anan Dr Umar din ya mai bayanin komai

Dama kuma yana zuwa duvani a tunaninshi ni dinner ba lfyan da gske

A cikin week din akayiwa Ahmad aiki

Daga nan kuma ya sake komawa rayuwar bacci har tsawon wata 4

Sukuwa doctors sun bamu tabbacin insha Allah zai tashi cikin lfy

Toh yau kimanin wata daya kenan da farfadowar Ahmad kuma ya miqe garau sai dai an dorashi kan magunguna

Sannan 

Mun mishi bayanin komai

Tun daga ranar da Hydar ya dawo

Duk motsin da akayi a gida sai ya tura mai ko hira akeyi sai ya kira ya ajiye phone shima yayi ta jinku

Ahmad ya shiga rudani sosai

Shi ko yaushe Nenne Na biyaye Na Adam a wanne halin suke ya maryama take kullum sai ya sani a gaba da kuka kamar yaro shi dai

Biyayen shi

Ya matsa min sosai.


Cikin zumudi da tsantsar farin ciki su Nenne suka rinqa sharar qollah Adam miqewa yayi cikin kaduwa yana 


Yusuf INA kake

Da sauri Abba ya riqo hannushi

Cikin hada fuska yace ai matsalar Ku kenan Ku 3 nan muddin kaji Abu sai Yusuf da Ahmad sunji suma kuma haka suke shima kanshi Ahmad

Walahi sai da yamin alqawarin bazai kirakuma Amman za ake hadaku yanajin muryarku

Kai ya kada cikin sanyin jikin yace Abba wazai tayani farin cikin rayuwar Ahmad in ban gayawa Yusuf ba?

 Mu zamu tayaka

Ya bashi amsa gamida jawo shi ya zaunar

Cikin sanyin Abba yace

Mu har yanzu bamu gamsu da zaman Yusuf da Aysha bazamu bar Ahmad ya dawo ba har sai mun tabbatar duk sun ruggumi juna da tausayawa juna da kula da juna kuma ba abin da zai sasu hakan sai rashin Ahmad a kusa

Bazan bar Ahmad ya dawo ba har sai randa muka gamsu da zamansu

Har sai naga Yusuf ya yarda da ita amatsayin matar aurensa tukun


Dan shi kam Ahmad tuni ya dauki Maryam a matarsa sannan ya cire batun Aysha a ransa 

Cikin sanyi

Baba bello yace wannan shine yanzu abin da ya rege mu ga yanayin zaman Aysha da Yusuf

Din

Cikin zumidi

Nenne tace wlh yanzu Yusuf da Aysha sun daidaita Kansu

Kawai Ku barni naje Na Duba Ahmad

A hankali baba bello yace

Ba komai dama Ahmad mun dawo dashi yana cikin Abuja

Kuma dama nima a kawai wata sheriyar da zamuyi

A satinnan kuma a abujan ne za muyi dukda dai mutanen nan Taraba ne

Jukunawa ne sai Ku tayani da addu,a Dan zasu iya yin komai a kaina

In zanje xamu tafi tare

Toh Allah ya kaimu suka amsa baki dayansu rabbi kuma ya kareka daga sherrinsu

Amin ya amsa tare da rufe musu yaron da addu,a


Wata ranar Jumma,a

Da yamma liqis Yusuf ne tafe cikin qorewa yake dravin

Cikin nitsuba yayi parking a harabar gidan kaka

Cikin takun miskilanci

 ya nufi cikin gidan

A parlor ya sameta riqe da mayafinta

Tana ganinshi tace yauwa

Aysha kiyi sauri ki fito mu tafi ga Dudabe yazo zai regemana hannya mu huta tafiya da qafa

Ko Dudabe ? ta fada tana kallon idanshi


Fuska ya kara murtuqewa ya kalleta a yatsine yace da yake ni bawanku ne ko ?

Da banxo bafa

Kawai daga ganina sai ki wani CE ni zan kaiku

Ehh din sai ka kaimu

Kam sarkin baqin hali kawai.

Toh zan gani ai!

Yace cikin yatsine.


Daki ta shiga da sauri sai gata kuma ta fito

Tana mita 

Mutum ya shiga wonka kamar mai canza fata Dan jaraba har yanzu fa ko wonkan bata fitiba

Bai kulata taba 

Kuma baiyi mgn ba

Tsaki ya Dan ja

 cikin.

Ranshi kuwa wani sanyin yaji dama fitowan Na dolene Dan ya rasa yadda zaiyi ne

Da abinda ke damunsa

Cikin sauqe ajiyar zuciya ya miqe cikin dakin ya nufa

Da sauri kaka tace kai Dudabe INA zakaje? 

Ban sani ba ya bata amsa a kufule

Toh me zakayi a dakin?

 ta kuma tabbayarsa?

Gun mata ta zanje! ko zaki hanani ne?

Ya bata amsa

Cikin mmk tace toh su mata ta manya juyawa yayi lkcin da yake dab da shiga dakin ya harareta yace ko ban kaibane

In shiga gun Amanata

Kai ta jijjiga cikin sake baki tace a a banceba Allah ya kiyaye hanya a fito lfy nima nayi gaba.


Yauwa dako kinyiwa kanki adalci ya fadi tare da shigewa ciki

 

*Lol su Yusuf kace matarka kamu dawo kace amanarka toh wanne daya zamu dauka*😝😂


Ita dai kaka fita tayi cikin mmkin yusufa a yau din


Shikuwa

Yana shiga kai tsaye.ya nufuni.....


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 9⃣8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇



*Sisters ngd da kulawarku gareni Allah ya bar zumunci da qauna*


A hankali ya zauna a a bakin gado 

Cikin ajiyar zuciya

Ya Dan ture kayan da

Ta fitar. Da nufin sawa in ta fito

Pillows y jwo 

Ya konta cikinsu

A rigingine

Ido ya lumshe

Cikin wani irin sabon

Yanayi.

Ita kuma cikin sauri

Sauri ta kammala ta fito

Daure da towel 

A ququnta Dan idan ta kaishi kan qirjinta bazai rufe ququn nataba

Bakin gado ta matso

Gamida Dan jawo gefen towel

Din tana Dan goge damtsen hannuta

Tana Dan yarfa hannu

A hankali yaji feshin ruwa Na sauqa a fuskarsa

Ido ya Dan bude cikin

Bugaqar zuciya

Da sauri ya rumtse idan Dan ganin ta a haka zai dauke mai numfashi

Ita kuwa

Duk abin da take 

Batama San dashi a gunba

Shiyasa take 

Ta rausaya wa ko a jijinta

Mai ta Dan laqakato

Ta murza  a hannuta 

Ta rinqa shafe qirjinta dashi

Shi kuwa idanshi sunki

Yarda da hukuncisa Na rumtsesu ya hanasu

Ganin abincinsu

A hankali ya bude ido

Dai dai lkcin

Da ta sunkuyo

Ta kanshi da nufin

Lalubo

Kayanta

Qirjinshi ne ya rinqa bugawa da qarfi

Garfi a take hankalinshi

Ya fara barin jikinsa

Lkci guda yaji wani irin sanyi Na ratsashi

Tuni ya wore idanshi ras

Lips dinshi kuma tuni sun fara bari

Da sau cikin azama ya kamo gefen lips enshi Na qasa ya fara tsotsa kamar zai tsinkesu

Lkci guda ya daburce

Numfashi Sa ya fara carkewa.

Da qarfi cikin kidima yayi wani irin ajiyar hrt a dai dai lkcin

Da yaji 

Qirjinta Na gogar fuskarshi

Ido ya qara budewa

Ita kuwa pillows din ta dauke ta cillashi gefe

Ta qara sunku yowa

Kanshi

Bres dinta suka dire kan bakinshi da gemunshi

Cikin rashin sanin halin da yake ciki da kidima

Kawai ya manna bakinshi kan bres din nata ya Sa hannushi daya ya sanqalo

Bayanta

Ta konto

Kanshi luf

Ita kuwa

Tsoro da firgici

Sukasa ta saki qara da qarfi

Cikin kuka

Da kidima take kiran

Kaka 

Wayyo kaka 

Kaka INA kike kixo 

Na shiga uku

Duk ta kidime sai kaimai bugu take

Qara matseta yayi

Cikin qarfin hali ya zare harshensa daga kan bres 

Dinta murya Na rawa

Yace 

Ke ki dawo hankalinki

Me kike ta ihu nine fa Hamma Yusuf dinkine

Ita dai sai bugeshi take yaxu ta gane shi amman bata bar bugunba

Da qarfi ya hade hannayenta duk biyu ya riqe 

Da hannushi daya

Daya hannun kuma

Bakin bres

Dinta yasa yatsu biyu

Ya Dan matse da qarfi 

Cikin tsura mata

Ido 

Qara ta kuma saki cikin fiffixgewa

Qara matsewa yayi

Da qarfi 

Tace Hamma Yusuf

Kasheni 

Zakayine?

Kai ya jinjina cikin sanyi murya yace

Ke dai kike son kasheni

Cikin tsiwa tace

Ni banson mugunta

Da iskanci

Wlh ka fita hanyata

Ko

 in kira kaka ingaya mata

Mugu kawai azzalumi

Sake hannun nata yayi ya fizgota da qarfi ta fada qirjinshi

Matseta yayi da gsky

Ya rinqa goga qirjinta a nashi qirjin 

Hannu yasa ya kunce towel din

Da qarfi

Ya birki tota

Ta bude baki zatayi kuka

Ya cabke harshen ta

Ya rinqa tsotsa yana

Wasa da bres

Dinta tuni ya fita hayya cinshi

Sai gurnani yakeyi

Da fidda numfashi da gyer

Qara matsota yayi

Cikin jikin yasa hannushi biyu 

Kan bres dinta yana sarrafasu cikin qorewa

Da tsantsar buqatuwa

Gaba daya ya fita hayya cinsa

Ita kuma kuka takeyi

Sosai

Tana wayyo Allah wayyo Hamma Yusuf

Kayi haquri

Dan Allah kabari

Kuka takeyi sosai shi kuma zafin kukan nata yakeji

So yake yayi mgn Amman ya kasa 

Ya bude bakinsa da nufin

Yin mgn sai yaji numfashinsa

Na fita

Da qarfi ya qara manne bakinshi kan lips dinta ya rinqa

Tsotsa yana 

Ruggume da ita hannushi daya Na buga bayanta daya kuma Na kan bres

Dinta ture hannushi take tana

Qirjina ciwo

Da qarfi a kidime ya tashi ya tallabota

So yake yayi mgn Amman INA sai

Wani irin kuka da ya kece mai

Shi dinma

A zuciyarshi yake jin

Wani irin Abu mai naiyi ya danneshi

So yake ya lallasheta ya gayamata abinda zai mata dadi Amman ina sai gurnani yakeyi

Jin haka yasa itama ta qara rudewa

Cikin kuka ta riqe hannushi da suke rawa kar kar cikin rawar murya tace

Hamma Yusuf kayi haquri

Dan Allah ka barni

Hamma Yusuf zaka tsinkamin bres

Fa ko kasheni 

Kake sonyi ne?

Kai yarinqa kadawa cikin juya kai

Alamar a a 

Da gyer cikin fixgar numfashi

Yace

*Amrita*

Ni ne zan mutu wlh zan iya rasa raina ya zanyi Na Gaza haquri

Ki taimaki Dan uwanki

Cikin share qollah tace

Ni wlh banso

Wlh ni banson ka

Ka barni ni wlh tsoro kake  bani

jowata yayi cikin rawan jikin ya daura ta kan qirjinshi

Ya rinqa Dan buga bayanta

Yana shafa 

Kanta

Har zuwa Dan wani lkci

Sannan ya dawo hayya cinsa

Ita kam sai 

Kuka

Can dai

Yaji an fara kiraye kirayen sallan

Manqariba

Cikin qarfin hali

Y daqota daga jikinsa

A hankali ya sauqi

Yazo gaban mirror ya dauko towel

Dinta din

Hannu yasa ya 

Kamo nata

Ka fada ta maqale

Ido ya tsura mata 

Cikin rawar murya yace

So kike Na sake ko

Jarabebbiya kawai😡


Mmk ne ya kamata sosai wai ita Hamma Yusuf ke cewa jarabebbiya

Muryarshi ta qara katseta

Ki tashi ko Na hawo ne Na miki abinda kike son?

Da sauri ta miqe 

Tazo bakin gadon

Ta tsaya daga kan gadon shi kuma yana tsaye a qasan

A hankali

Ya wore towel din

Ya daura mata shi a qugunta

A hankali

Ya manna kanshi a tsakiyar qirjinta

Gami da sauqe ajiyar hrt

Can kuma ya do go

Cikin murtuqe

Fuska

Ya daura hannushi 

Biyu kan bres

Dinta yana cewa

Suma basu da kunya kamar ke

Sai suyi ta tsokale idan mutum

Shiyasa dole Na hukuntasu

Ita dai sai hawaye

Qara shafarsu

Yayi ya Dan kamo

Bakin daya bres din

Nata yasa a bakinshi

Ya fara tsotsa kuma

Lkci daya ya fara yin qasa qasa alamar zai durqushe

Ganin haka yasa ta share qollarta

Tasa hannu

Ta kamo

Bres

Cikin sanyi da tsura mai ido

Ta zaro shi

Daga bakinshi

 Cikin lumshe ido

Yace

Hmmm hashii

Hannu ya kuma kaiwa

Ya shafesu

A hankali cikin rashin sanin sanda zancen ya fito

Ya furta 

*I love you my

Amrita*

Yana fadin haka ya juya ya nufi

Parlon

Har yaje bakin qofa yace 

Ki shirya ki fito mu tafi

Ko Na dawo


Bayanshi tabi

Da ido

A fili ta kuma sakin kuka

Tare da cewa

Wanna wacce iriyar rayuwace

Anyya kuwa Hamma Yusuf yana da imani

Siket dinta ta dauko ta zura cikin share qollah

Tace Allah ya isanmin  mugu kawai

Duk ya cakudeni

Bayan ta fito

Ta sameshi a parlo

Ya zauna yana damqe da Mara

Yana ganin ta ya miqe

Hannu yasa y kamo nata

Cikin sanyi

Yace Amrita marana ciwo

Hannushi Na cikin NATA suka isa gun motar bayan ya rufe gidan

Suna shiga

Yaja

 tana gefenshi ta kauda kai

Ganin haka

Yasa ya

Jawota kadan

Ta Dan matsoshi

Ba kunya ya zura hannushi cikin

Rigarta

Ya cabke bres

Dinta ya rinqa shafewa

Har saida itama da kanta taji yana sauyata


A hankali ta juyo ta kalleshi

Bayan sun isa gida yayi parking Amman kuma hannushi Na jikinta

Shima ita ya tsurawa ido

Kai ta karyar cikin muryar kuka tace

Hamma Yusuf zan shiga cikin gida

Numfashi ya sauqe cikin sanyin

Yace toh

Na hanakine

Kalloshi tai cikin takaici

Ya maqale bres dinta sannan ya rufe qofa kuma wai ai Na hanakine

Shikuma ya kuma matseta cikin sanyi yace

Ki tafi mana 

Ido ta kura mai 

Shima tsura mata idon yayi

A ranta tace Amman lallai Hamma Yusuf Dan duniya ne bai da kunya

Kan hannushi da yaketa mutsu mutsu a cikin rigarta ta kuma kalla

Cikin sanyin tace ka sakeni ka kuma bude min mota

Na riqeki ne

? Ya tabbata yeta cikin isa

A hatsale tace ni Na gaji

Zaka sani ciwon nono

Kai ko a jikinka.

Cikin yamutsa fuska yace

Waya gaya miki ai so nake kema kiji irin azabar da kike jiyar dani inje inyi jinyar marata ke kuma keje kiyi Na bres

Dinki masu shegen Neman tsokananan

Da gyer dai ta samu ta zulle ta gudu cikin gida.



Aiko a Daren ranar daga shi har ita ba Wanda yayi bacci

Shi ba abinda yake mai yawo a idanshi sai surarta

Sha,warta sosai take cinsa

Ya kuma rasa dalili

Jinshi yake in bai malla ketaba zai iya resa ransa

Kwana yayi a zaune

Ita kam ta konta kam Amman da ta Dan motsa bres

 Dinta ke tuna mata Hamma Yusuf

Dan sunyi tsami

Mmk fal zuciyart ase dama maza basu da kunya

Ase haka Hamma Yusuf yake kamar maye

Lallai kuwa 

Zai gane itama tana da NATA salon muguntan


A haka dai suka kwana



Kaka kuwa ase gidan Adam taje Dan Amira Na naquda

Aiko washe gari da azahar ta haifi danta namiji


Bayan sun dawo gidane

Suka sheidawa su Nenne

Maryam da Aysha kam sunaji

Suka shirya

Suka tafi tare da ya Rabi,u

Basu Dade da isaba Hydar ma ya iso daga Yola

Murna kam ba,a mgn

Adam ya hada yan qanneshi

Ga Hydar ga Aysha ga Maryam ga matarsa kuma  yar uwarsa ga kuma danshi

Cike suke a parlon sai hira da nisha di suke Sha

A haka har akayi maggariba bayan sun dawo ne Aysha da Hydar suna

Zaune suna cin abinci a pilet daya

Haqiqa dama can shi Hydar yana jin Aysha fiye da ranshi a jikinshi

Ase qaunar ta dolece uwa daya uba

 daya



Suna cikin hakane Yusuf kuma ya iso

Tunda ya shiga ya ganta 

Yaji wani irin baqin ciki ya tokare mai maqoshi

Sosai

Yaji zafi ya za,ayi

Ta rinqa fita anquwa ba tare da ta nemi ixininshiba

Bayan ya karbi Dan ya mishi addu,oiCikin hikima ya tsura mata ido yako ci sa,a sukayi ido 2 cikin murtuqe fuska ya watsa mata harara

Ita kuwa baki ta murguda mai cikin tsiwa

Lips dinshi ya cije

Cikin isa yace

Ke Amrita taso mu tafi 

A tsiwace tace tare muka zone ni a gidan Dan uwana zan kwana ehe

Ganin zata jamai raini

 yasa ya fita

A cikin Mota yana son ya kira

Kuma bai da phone number finta

A karo Na forko a rayuwarsa da yaji baqin cikin rashin number wata a woyarshi

Can dai ya tuna ya kira Hydar

Cikin fada fada yace Hydar wai bakuji nace ta fito mu tafi bane 

Kun wani ajiyeni cikin mota sai kace yaron gidan Ku

Cikin girmamawa Hydar yace Hamma Yusuf wlh taqi tun dazu muke gama da ita harda kaka sai kuka tasa

Rai a bace ya fito

Ya dawo cikin gidan cikin fada yace

Ke ki fito mu tafi

Cikin tsiwa tace bazan koma bazan tafi da kaiba tafiyarka da ban tawa da ban 


Kaka ce tace 

Dan Allah Dudabe am ka barta ta kwana cikin yan uwanta

Cikin fushi yace ban amince ba bada yawuna ba

Adam ne ya kalleshi cikin mmk yace toh

Biyaye kaje zan dawo da ita anjima

A kufuli yace ke wato ban isa da ke bako yayi 

Kyu

Cikin Fushun ya juya ya fita

Sosai yakejin zafin fitan da take ba tare da izinishi ba

Kai tsaye gida ya koma

A babban parlon ya samesu a tare suna ta hira

Cikin halin miskilancin ya wuce kitchen

Goran FARO ya dauko mai sanyi wai ko zaiji sanyin a ransa


A can kuma yana fita ganin yadda ya fita a hatsala

Yasa Adam ya ingiza keyarsu

A bakin gate ya sauqe su ya juya ya koma su kuma suka nufi jikin gate din

Suna isa bakin gate din.....


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👇🏻👇🏻

_MI WASMITI_page9⃣9⃣

Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


```Amadadin sauran ma rubuta nake miqa saqon

Gaisuwarmu ga yar uwarmu

Anuty Ruky ma rubuciyar d'alibina da mariya

Muna miqa saqon taziyarmu gareki Na rashin yar 

Uwarki Rashida Allah ya jiqanta da Rahama ya kai haske makoncinta```



🍇Suna zuwa bakin gate 

Mati mai gadi ya kafa ya tsare ya hanasu shiga

Cikin mmk Maryam ta ke tabbaya yarshi akan wani dalili zakace ance kar mu shiga

Waya yasa ka hanamu shiga gidan?

Cikin bin doka da umurni yace 

Babana ne yace kar Na kuskura Na bar 

Aysha ta shigo 

Gidan

Cikin takaici da hatsala 

Aysha tace 

Hamma Yusuf ne yace kar kabarni Na shiga 

Gidan ? 

Ehh shine ya bata

Amsa

Cikin takaici tace aiko

Baimin hakaba nasan nan ba gidan ubana bane

Basai ya tozartani

Ba basai yamin koran

Kareba dadin

Abin muma muna da gidan uba

Hannun Maryam ta kamo cikin zubda qollah tace Maryam zomu koma gidan ya Adam ni gobe da sassafe zanyi sammako na koma Yola gidan ubana

A hankali Maryam ta bude baki cikin jin zafin abinda 

Hamma Yusuf ya musu

Tace 

Aysha ai shima Hamma Yusuf nan ba gidan shi bane

Kai kuma mati 

Wlh ka bude mana qofa ko kuwa Na kira ya Abubakar Na gaya mai kuma ka sanshi sarai wlh horon sojoji zaimaka

Cikin sanyin yace 

Toh ni ya zanyi 

Umurni

Babana ya bani kar Na barta tashiga inko Na barta a bakin aikina

Jin haka ya hatsala su

Cikin fushi suka tura shi suka shige


Suna shiga harabar gidan

Aysha ta fara kiran Hamma Yusuf

Da qarfi

Yana sama gun Abba ya jiyo kiran nata Tate suka sauqo da su Usman

Su Ummi da Nenne da suke parlon duk suka zubawa qofar shigan ido

Anuty Sadiya da ta iso ba jimawa itako sai kallon

Yusuf take cikin

Tuhuma

Shiko cikin

Isa da 

Qasaita da murtuqe

Fuska ya rinqa tako

Sitep din yana sauqowa

Suna shiga 

Hawaye shar 

A fuska ta isa

Gabanshi

Cikin muryar kuka 

Ido ta zuba mai 

Murya Na rawa

Tace

Na gaji wlh nagaji 

Hamma Yusuf nagaji da tozartani

Da takeyi

Dan wulaqanci dacin

Fuska shine zaka saka mai gadi ya hanani 

Shigowa gidan 

Ai ko bakamin

Hakaba ni nasan nan ba gidan ubana bane

Ai dama Na sani a tsawon shekarunnan Dan bakasan cewa ni ba yar gidan nan bace da kasani Na tabbata da ka Dade da korata

Amman Alhamdulillah

Muma muna da gidan

Uba 

Yanzu ka dates

Igiyoyin aurenka a kaina ka gani 

Ko awa daya bazan, garab!


Tunda ta fara

Mgn da kukan

Ya tsura mata ido

Cikin murtuqe fuska

Sai yanzu

Ya daga mata hannu

Cikin tsawa yace

Ya isa 

Haka 

Ehh ni nace ya hanaki

Shiga ko kina da abin yi akayi

Ki rufe min baki

Banson

Rashin tarbiya

Da kika fitan

Wa kika tabbaya?

Da izinin

Wa kika fita?

Waya baki daman fita?

Ko zaman kanki kikeyi?

Cikin Fushun ya qara matsota

Yadda baki tabbaya yeniba dole

Haka sai ki koma inda kika

Fito

Haka jiyama kika tafi gidan kaka ba tare da Neman izinina ba

Ko gani kike kinfi qarfi nane

Kamo hannuta yayi

Cikin Fushun sosai yace bacemin da gani

Ya tureta!


Jikin Ummi

Ta fada cikin

Kuka mai tsuma rai 

Cikin

 tafasan zuciya da baqin ciki

Ummi ta Dan tureta

Ta nufi gaban Yusuf

Tana zuwa 

Ta zuba mai mari

Mai bala,in

Zafi cikin

Fushi da zubda qollah

Tace 

Subahanallahi

Yusuf

Kasheni kake sonyi

So kake ka fasamin zuciya

Shi kam cikin mmk

Da rudu ya tallabe kuncisa

Yau Ummi harda 

mari Idanunsa suka kada sukayi jazazur

Gaba daya jijiyoyin kanshi suka tashi

Lips enshi sai rawa suke

Kai ya kawar cikin tsurawa qofar fita woje ido

Yana jin zantukan mahaifiyarshi Na ratsashi

Sautin Kukanta Na soya mai zuciya

Cikin ifirgicin jin kala manta ya zame 

Ya zauna kan sitep

Din

Kuka take tana

Kaitona da kai 

Yusuf Na haifeka nasha wahalarka

Amman a karo Na forko

Ka kasa yimana biyeyyah ka kasa son abin da muke so

Cikin zubda qollah

Tace 

Allah sarki duniya Allah bai barin wani Dan wani yaji

Dadi

Da ya bar rayuwar Ahmad kusa damu yaro mai biyeyya da sanin darajan

Iyaye Amman sai Allah ya nesantashi damu ya kusantoka damu

Wlh da kai muka rasa yafi da rashin Ahmad

Cikin sauri

Nenne tazo ta rufe bakin Ummi

Tana girgiza kai tace

Haba Ummi

Ya za,ayi bacin rai yasa kike furtawa danki

Irin kalamannan

Ita dai Ummi

Sai qollah

A hankali

Ta matso

Kusa da Aysha

Ta ruqqumota

Cikin NADAMA tace

Aysha kiyi

Haquri

Duk abinda Yusuf

Ya miki Nina Jamiki. ki gafatceni

Insha Allah tunda bakya sonsa dole ya sakeni

Kuma saidai shi ya bar gidannan

Cikin quna ta juyo ta kalleshi

Tace wlh kaji kunya ka kasa son yar matar da tasoka fiye dani Dana haifeka

Tasoka kamar ta mutu kai kuma kaqi jininta yarta da ta yi alqawarin baka tun kan ta haifeta

Maryam kam da Aysha sai kuka 


Shiko Yusuf ya rasa a duniyar da yake

Yau an  tono mai rashin Dan uwanshi

Ya tabbata da duk za,a taru a qishi toh Ahmad zai zame mai *Garkuwa*

Cikin fushi yaji Ummi nacemai tashi ka ficemin daga nan bana buqatar sake ganin ka

Har sai.ka rubuto min takaddar sakinta

ido ya bita  dashi Dan ya kasa tashi

Sai da ta kuma watsamai tsawa sannan ya miqe ya fita da gyer


Dakin

Ahmad ya bude ya shiga

Zama yake sonyi Amman zaman ya gagareshi

So yake yayi kuka kukan yaqi zuwa

Sai zirga zirga yake tayi

Sai yaje gabanta photo su su 3 ya rinqa mgn

Shi kadai

A wahalce yake cewa

Ahmad meyasa ka tafi ka barni bayan kasan ba mai sona sai kai kadai

Ba mai fahimtata sai kai

Ba maimin uxuri sai kai

Sai ya kuma dawowa bakin gado

Ya rinqa tura kanshi cikin pillows

Lkci daya ciwon kai mai tsanani ya rabkeshi

Ga zazzabi mai zafi

Sanyi ya rinqa ratsashi 

Dumi yake buqata Dumin jikin Aysha ya tabbata in yajita cikin jikinshi zaiji Dan dama dama

A haka ya kwana cikin azaba da tunani da tsoron Fushun iyayenshi

Gashi baba bello bayanan bare yaje gunsa ya samu sauqi


Ita kam Aysha ta gommace bata furta kalamanda da ta furtaba Dan

Ummi kwana tayi kuka

Sai tai taneman gafararta tana Aysha ban karbeki Dan nacutar dakeba Aysha Yusuf Na Haifa Amman ke nakeji fiye dashi

Sai da tarinqa kuka tana Ummi ni kam bakimin komaiba sannan tace toh karki sake cewa nan ba gidan Ku bane

Meyayi Yusuf me yayi ki

Karfa ki manta mahaifiyarki da mahaifin Yusuf uwa daya uba dayene

Cikin kuka tace bazan qaraba Ummi.


A haka ita kam Aysha ta Dan samu sakat da matsalan Yusuf

Ta sake sai shanawarta take yau tana nan gobe tana can 

Sam ta mance dashi sai dai wani lkci yakan fado mata a rai sai taji tsanarsa ta diranmata a rai


Yau kusan kwana biyar da faruwan abin 

Ba Wanda ya kuma ganin Yusuf

In banda sallah ba abinda yake fita yayi

Sai Adam da yake zuwa ya Dan je cikin gidan yazo mai da abinci dukda baicin ko mai sai Dan ruwan tea da yake Dan sha

Maryam tamai bayanin komai Amman shi Yusuf shiru yayi bai gaya maiba

 Sai yanxu da suke zaune

Sunata mgnar batun yadda suna zai kaya 

Sannan Adam ya Dan gyara zama yace

Biyaye 

Na,am ya amsa kanshi a qasa

Cikin sanyin yace

Yusuf meyasa kake barni so yake qoqarin yi maka illah a zuciyarka

Yusuf har sai yaushe zaka cire girman kai da miskilanci ka ruqqumi abin da kakeso

Kana son matarka meyasa ba zaka iya furtawa ba

Cikin yamutsa fuska da tabe baki yace

Ai sai kuma kai tayi banza kawai ka dauka kowa maye ne irinka

Cikin tsura mai ido

Yace ai wlh kai taka maitar tamafi ta kowa Yusuf

Zafa ka kashe kanka

Qwayoyin da kake Sha zasu maka illah 

Tsaki yaja cikin tashi zaune

Yace kai biyaye ni banda matsala komai

Da sauri yace qaryane duk Wanda ya ganka yaga mai matsala sai dai zurfin cikin ka kawai

Son Aysha ke dawayni da kai da begenta

Sai tunanin Fushun da Ummi keyi da kai,

Wadin?

 yace cikin tabe baki yace 

Wlh bata kai nasota ba bare sonta yayi dawayni da ni ba me zanso a jikinta kawai dai ni INA tausayinta ne kuma kasan ita Amrita amana tace kuma a gabanka Ahmad ya ban amanarta

Miqewa yayi cikin dry yace ehh lallai da da saura baka gasuba Yusuf Amman dai shawarata kaje kaba Ummi haquri zaifi

Sauran kuma basai Na baka shawaraba da kanka zaka nemi mafita


Yau suna yaro yaci sunan Ahmad

Anyi biki sosai yaro yasha gata


Yusuf kuwa zuwa yanzu ya gama gala baita

Shiyasa yau ana idar da sallan insha dakin ummin shi ya nufa

Zaune ya sameta a bakin gafo

Cikin sanyin ya qarisa gunta cikin sanyin sanyi ya zauna gefenta a hankali ya daura kanshi kan jinyarta

Cikin rawan murya yace

Dan Allah ummina ki gafarceni ki daina fushi dani

Na tuba kimin afuwa

Cikin fushi ta ture kansa ta miqe gamida cewa fitanmi a daki banson ganin ka!

Cikin mmk ya tsura mata ido

Ita kuwa a fusace ta buga mai tsawa ficemin a daki bana qaunar ganin ka

Miqewa yayi cikin qoqarin riqi hannuta

Yana mai Karya wuya yace

Ummi Fushunki masifa nefa a kaina ki gafar ceni

Da sauri tace fita nace ko

Haka ya fita jikin a sanyaye

Yazo dai dai qofar fita part din Ummi sukaci

Kari da  Aysha da take gudu da zare ido Dan ganin  hadarin da ya taso sai iska da walqiya da ake zubawa

Cikin tsoro ta fada jikinshi

Da  sauri ta kuma janye jikinta zata wuce ciki ya damqi hannuta 

Yana ja tana tirjewa ya nufi part dinsu da ita....


Bye garkuwan Fulani

[4/9, 2:25 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI WASMITI* page 1⃣0⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Janta yake tana tirjewa har suka isa Dan farfajiyar part din 

Nasu ganin yana qoqarin 

Janta ciki

Yasa ta sunkuyo da kanta ta kama damsen hannushi ta ciza

Zafin ya ratsashi

Cikin takaici

Ya yarfar da hannuta

Yace tafi

Nace ki tafi

Lkci daya kuma ruwa ya keto kamar da bakin qorya

Ga isaka mai sanyi dake busawa

Sai walqiya  sake ratsa garin taraba baki 

Daya

Tallabe hannushi yayi cikin

Kunan rai ya duqa a gun 

Ya rumtse idanshi ruwa Na sauqa kansu hasken fitulun wurin suka ratsasu

A hankali yace

*A,ish*

Ki tafi ki koma inda kike son zuwa ki barni

Ki tafi ki barni Allah zai zama ga tana

Kuma shi yasan taimakon da zaimin

Inma mutuwa tace hutu a gareni toh

Allah ya dauki raina da gaggawa nabi 

Biyayena Na huta da quncin rayuwa tunda Ahmad ya rasu ban sake farin cikiba

Na kasa samun madadinsa

*A,isha* ke baki da burin da ya wuce ki gasamin zuciya

Tafi ki barni ko nace 

Ki tafi

A dai dai lkcin kuma aka saki tsawa mai firgitarwa

Cikin tsoro da razani ta fada 

Jikinshi

Cikin rawar murya

Tace Hamma Yusuf tashi

Tashi ka rakani 

Ni tsoro

Nakeji

Da qarfi ya miqe cikin

Fizgar numfashi

Ya angizata

Ya juya ya hau kan baranda jikin windo yaje ya tsaya jikin fada yace

Duk inda kike zuwa yawon naki 

Nike rakaki ne?

Ko kina Neman izini nane

Gani walqiya yasa ta qara matsoshi

Cikin sanyin murya yace

*A,ish*

Kiji tsoron Allah fa kina sane da duk matar da ta fita ba tare da izin mijintaba har taje ta dawo Mala,iku Na tsine mata

Ido ya tsura mata cikin takaici yace

Kalli irin shigar da kike fita da ita

Ko wanne jakin da doki ya qaremiki kallo

Gaba daya ya fita hayya cinsa

Cikin sanyin yace 

Kinmin laifi

Sannan Dan nayi mgn kika hadani da Ummi

Sannan kika qaura cemin

A hankali ya matsota

Murya Na rawa 

Yace 

*A,ish*

Ke bakiyi kewar mijin ki bane?

Bakya jin kewata da rashina a kusa dake?

  Cikin tabe baki da jin qarfi quiwar ganin tsawan ya Dan lafa

Tace waye mijin nawa?

Wayeshi da zanji kewarsa?

Ni ban da miji sai Wanda zan aura kwananan 

Yanxu ma sakina nake jira gashi kuma Daba banda iddar mutum a kaina


Kalamanta sun kasance 

Tamkar wuta a zuciyarshi a take bugun zuciyarshi ta tsananta

Numfashi Sa ya fara daukewa

Da qarfi cikin dimuwa zai juya kenan hannushi ya bugi gilas din window

Aiko lkci daya taimar mugun yanka 

A tafin hannushi

Sai jini

Yake tsiyaya gashi dama rai ya baci jinin ya tsinke

Jinin ne yake zuba tsosai

Sai kuma ya maida hannu ya matse gilas 

Din jikinsa kab sai rawa

Yakeyi ya kasa mgn sai tsura mata idon da yayi

Cikin tsoro ta matsoshi

Ganin jinin Na zuba har 

Qasa hannun ta kamo

Cikin rawar murya tace

Hamma Yusuf

(Laru iyayam no  rufata ha judema fa)

Kaga yadda jini yake zuba a jikinka fa

Ka sake glass din

Kaji sai qara matsewa yayi

Cikin maida numfashi

Yace ki bacemin daga nan ki barni mana 

Badai ni ba mijinki

Babe INA saki kikazo nema 

Ki fita harkata

Qara matsoshi tayi ganin gaba daya baya cikin hayyacinsa

Yana fadin tunda ba mai sona da tausaya mi ai gwara Na mutu Ku huta da ganina

Dama haka kuke fata har kuna cewa da ni Na mutu Allah ya barmuku Ahmad

Toh zan bashi Ku huta

Dama nafi kowa buqatarshi sai Na bishi

Bakya sona 

Da sauri tace

Hamma Yusuf ka sake 

Muna sonka mana 

Da sauri 

yace qara kikeyi Aysha

Ba sona a qwayar idanki

Qara kamo hannushi tayi

Cikin kuka tace

Hamma Yusuf

Ya za,ayi kace ban sonka

Kaifa Dan uwanane Na jini

Jikin yarfe hannu

Yace Waya CE miki irin wannan  son nake so kiyi min

A a bashi nake keso ba

Aysha nifa mijinki ne ki dena ganina a matsayin  Hammanki Na wuce wannan matsayin

Cikin tsura mai ido tace 

Ni kai ba mijina bane!

Kai ya kada gamida qara matse glass din

Yana fadin toh ni mijinki ne ki yadda da cewa ni mijinki ne

Gaba daya ya rude ya rudata lkci guda kuma ruwa ya qara kecewa

Gashi duk sun jiqe

Cikin tsoro tace

Toh ka sake hannu ka

Na yarda!

Jin haka yasa shi janye hannushi da sauri

Ya tallabo

Fuskarta bakinshi

Ya hade da NATA cikin rawan jiki

Ya lalubo harshen ta

Ya rinqa tsotsa gaba daya fuskarta kuma ya shafeta da jininshi

Duk jikinsa sai rawa yakeyi

Da gyer ta zame bakinta daga nashi

Zata juya ya kamata

Bai tsaya ko INA da itaba sai dakin Ahmad

Suna shiga 

Ya matsota jikinshi

Cikin rawan jiki ya rinqa balle boturan 

Gaban rigar tata bayan ya zaremata After dress Dinta

Duk ya rude ita kam sai ido take binshi dasu

Haka kawai itama takejin wani Abu Na mata yawo 

shiyasa batayi yunqurin hanashiba

Yana cire rigar

Ya balle bel din ququnta

Cikin sanyin murya yace

Cire 

Wondon nan ya jiqe 

Yana fadin haka yana 

Zare riqar jikinsa da wondon

Da sauri ta rumtse idanta 

Gudun yin mummunan gani

Jinshi ya sunkuyo yana Jan Jens din  jikinta yasa ta bude ido

Daga shi sai towel a ququ girjinnan duk a woje

Tsoro ne ya rufe ta sosai lkcin da taji yana zare pant Dinta

Da qarfi tace

Hamma Yusuf

Me haka

Bai kulata ba saida ya zare 

Ya ciccibota

Ya haye kan gado da ita

Cikin blanket

Ya shige da ita

Wore towel din jikinshi yayi gamida matsota jikinshi cikin

Kidima ya dire hannushi kan bres

Dinta gamida furta

I miss you A,ish

Yamutsata yake kamar ba gobe

Ita kam Aysha in nace tsoroma Na rege 

Dan jin jikin Hamma ta a fili ya qona mata ruwan kai 

baki daya

Shiko zuwa yancu ya manta menene kunya bare nauyi bare wani gudun kar ta rainashi

Cikin wani irin kuka kamar yaro ya manna bakinshi kan bres Dinta ya rinqa sarrafa fatan kuma da hannu mai yankan Sam baijin zafin

Shafata yake daga kan lips Dinta yabi da yatsu 2 

Har zuwa kan bres 

Dinta a hankali yazo kan cibiyarta

Ita kam Aysha sai miqa takeyi

Duk gabban jikinta suna budewa suna karbar saqonnin 

Hamma Yusuf Dinta

A hankali ta daqo hannuta ta daura ka qirjinsa

Tana shafawa

Da sauqe ajiyar zuciya

 dan ta Dade tana Sha,a rawar taji ya kallan laushin gashin qirjinshi nashi yake

Sautin Ku kanshi ne ya dawo da ita hayya cinta

Kissing Dinta yake daga fuska har qirjinta har kan cikita har zuwa cibiyarta har ya gangara inda bazai faduba

Duk ya kidime ya rude ba abinda yake yi sai qurnani da nishi da wasu zantukan da baza,a gane ba

Bata gama tsinkewa ba sai da taji shi yana qoqarin yi mata rumfa da qirjinshi

Yana mai cewa

*Ihshat* 

Kin amince dani ?

kin yarda da baqoncina? kin amince 

Mu zama ma,aurata?

Cikin tsoro da rawar murya tace

Hamma Yusuf kayi haquri wlh inajin tsoro

Bazan iyaba zakajimin ciwo

Hamma Yusuf

Kafi qarfina !

Cikin

Gigita ya zame ya konta rubda ciki

Ba abinda yake 

Sai nishi

Yana

Wayyo Allah

Aysha marana zai balle

Zan mutu

Ki taima kamin

Cikin tsoron ta taso ta zauna

Cikin murya kuka

Tace

Hamma Yusuf karbar mgn kayi shiru zai bari

A hankali ya mirgino

Jikinta kanshi ya daura kan cinyarta

Gamida Dan jawota ta sunkuya ta yadda

Ya samu bakinshi ya iso bres

Dinta

Cabkewa yayi yayi luf a jikinta

Yana sarrafa ta cikin sauqi da jin dadin yanayin garin da iskar dake busowa 

ji yake ba wani mahaluqin da ya kaishi jin dadi a yanxu 

 itama shiru tayi

Gamida qara sunku yowa

Dan itama yana tsumata da salonshi

Qirjinshi take shafa,wa

Tana tura hannuta cikin sumar kanshi


A haka har suka Dan samu gamsuwa da juna

A hankali ya zare bres Dinta daga bakinshi

Cikin

Sanyin murya

Yace

*A,ish*

Shiru bata amsaba

Qara matsota yayi gamida kamo tafin hannuta yana wasa da yatsunta

Yace

*Habitti*

Ajiyar hrt ta sauqe.

Cikin shafo bres Dinta

Yace

 *A,ish*

Ummi Na fushi dani

Bansan ya zanyiba

Kowa haishina ke ji

Bana son bacin ran umina INA tsoron

Fushinta

Rayuwata zatayi duhu

In tana fushi dani

Ki tayani Neman gafararta

Cikin wani irin voice tace

Hamma Yusuf

Ba Wanda ya tsaneka

A hankali ya lalubo

Phone dinshi

Ya haska fuskarta

Cikin ajiyar hrt

Yace

Yarinya 

Kema a hannu kike

Tsoron ki ne zai cutar damu

Ji yadda idanki ya koma

Cikin kunya da takaici

Ta yunqura

Da sauri ya kamata

Ya matse a girjinshi

Cikin sanyi tace

Ummi cefa ta aikeni

Gidan kaka kuma tasan Na fito Dan ta kirani da ta ga hadari

Nasan yanxu tana can tana jirana

Cikin  isa

 yace

Da safe sai kice a gun mijinki kika kwana

Bataso a dole ya matseta ya hanata fita


Da asuba yana tashi ya hada musu rawan wonka ita ko duk tana bacci

A hankali yazo ya bude blanket din iya qirjinta

Sai yanxu yaga gaba daya ya shafeta da jininshi

A hankali ya tallabota bai direta ko inaba sai cikin ruwan

 dumin

Da sauri ta bude ido

Cikin sauri ta kuma rufewa ganinshi shima cikin ruwan

Ya miqo mata hannu

Jawota yayi ya rinqa shafesu da sabulu da ya dauko a dakinshi da kayan da zasu saka dan Na jiya a jiqe suke

Bayan sun fito dukkansu daure da towel

Ya matsota cikin  kauda kai

Ya zura mata wota yar rigarshi mara hannu sai hula

Cikin mmk da zare ido tace INA kayana

Sun jiqe kuma duk sun taba jini 

Ina tsoro kar umminki ta gani tace Na miki fyadeh ya fada cikin tausayawa kanshi

Ko in je in dauko miki? 

Cikin takaici tace

Yanzu ya zanyi

Matsota yayi ya zura mata rigar

Ya sunkuya ya xira mata Dan 3 qtr shi 

Inda yazo mata har qasan guywarta

jawota yayi gabanta mirror

Yace gashi kinsa kaya me ya rege

Cikin tura baki tace sai inje a haka

Ehh mana yace tare da fita ya nufi massalaci


Itako har ya dawo bata tafiba

Shima dama ya shi gone Dan ya kwashi kayan nasu

Gabanta yaje cikin

Sanyi da murtuqe fuska yace taho nan

Hannu yasa ya kamo nata

Ya jata suka fito

Kai tsaye dakin Ummi 

ya nufa da ita

Yana kiyi sauri muje yanzu nasan Ummi tana dakin Abba

Kina cire kayan ki kawomi abina kar  a gani

 a ranshi kuwa Allah Allah yake su hadu da Ummi Dan zata dauka ita Aysha ita ta bishi


Suna shiga 

Dakin

Ya matsota gamida

Sa hannu ya zuge

Zip din rigar 

Kenan 

Qofar toilet ta bude

Da sauri yasa hannu 

Ya.....



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👆🏻👆🏻

*MI WASMITI* page1⃣0⃣1⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Cikin lumshe ido

Ya shafa bres Dinta gamida Dan matsota 

Da sauri ta buge hannushi

Ta matsa gefe

Harara ya watsa mata gami da juyawa

Da sauri  ya sunkuyar da kai  fuska  a kunyace ganin 

Ummi da ta kafeshi da ido

Cikin tuhuma

A hankali ya bude 

Baki yace 

Ummi an tashi lfy

Batayi mgn ba sai hanyar fita da ta nuna mai da hannu

Cikin hada fuska

A hankali yace 

Ummi kiyi haquri

Fita dai nace

Toh yace gamida Dan Sosa qeya ya fice


Itako Aysha kunya ta hanata motsawa

Sai da Ummi

Tace 

Ki cire wannan kayan haukan

Cikin jin kunya ta shige toilet ta Sa doguwar rigarta sannan ta fito

Cikin tuhuma 

Ummi tace

Ina aikena?

Kai ta kuma sunkuyarwa cikin inda inda tace 

Hmm dama

Damanfa

Daman mefa?

 Kimin mgn 

Dama 

Hamma Yusuf ne ya

Karba.

 Toh meya kaiki gunshi

Rau rau tayi da ido

Ganin haka yasa umin ta fice tana zanyi mgnin shi

Badai rashin kunya yakeson koyaba


Shi kam Yusuf a wunin yau ya wuni

Cikin nishadi

Mai da wani tunani sai nata 

So yake yaji muryar ta Amman ya rasa ta ina 

Zai ganta

Gashi begenta ya mai mugun kamu

Konce yake a parlosu shi kadai

Yana ta tunani number ta yake son samu 

Cikin zaquwa ya miqe ya zauna

Adam ya kira

Yana dagawa 

Yace ya dai biyaye ?

Tsaki

Ya Dan ja cikin daqilewa yace

Number Yarinyar nan nakeso ka ban.

Sarai 

Adam ya gane Amman Dan ya cinnashi ya fada da bakinshi yace

Ai yaran suna da yawa wacce daya kasan yan matan da suke sonka basu da adadi

A hatsale

Yace can da shirmenka

Ni Na taba cema ka ban number watace bare ka tallatani

Cikin dryar mugunta yace 

Toh number wa kakeso?

Cikin yamutsa fuska yace 

Dan iska 

Number qanwarka zaka ban

Dry yayi sosai sannan yace 

Shege ai 

Taurinkai

Kashe maishi yakeyi

Shiko katse kiran yayi

Ba a jimaba yaga number

Da sauri 

Ya daga 

Cikin zumudi

Ya kirata

Har kiran ya katse bata dagaba

Kamar zai bari sai kuma yaji ya kasa

Haquri

Ita kuwa tana kitchen

Tana ta aiki Dan  baba bello Na hanya

Bayan ta gamane ta koma daki da niyar yin wonka

Har ta shiga toilet taji woyarta Na Neman agaji 

A hankali ta fito

Daure da towel

Cikin sanyin murya 

Tai slm

Ganin sabon number

Ne

Ajiyar hrt ya sauqe da qarfi jin voice dinta

Cikin sanyi yace

*A,ishhhhh*

Shiru tayidan tuno wannan sabon sunan

Wanda tasan

Mutum dayane ya rada mata shi Kuma ya shiga ranta

Muryarshi ta qara 

Katseta

Cikin mutuwar jiki

Yace *Habitti*

Me kikeyi INA kike nai ta kiranki byake daqawa

Shin bakisan zakisa zuciyar Yusuf ta fasheba

Cikin jin katsala ta qara narkewa jikin pillows

A hankali taji

Yana huramata iska 

A kunne ta cikin woyar

Ajiyar zuciya ta kuma sauqewa

Cikin narkekkiyar murya

Yace

Aysha 

 Bata Amsaba

Cikin shauqi ya qara matso pillows cikin qirjinshi

Yaci gaba da cewa

Dan Allah kiyiwa mijinki mgn kina sani firgici

A,ish ko byeke ji nane

Habitti

Cikin sanyin jikin tace

Hmm ahh INA jinka

Toh me kikeyi?

Wonka zanyi!

Cikin kasala yace ki zo nayi miki a nan

Shiru batayi mgn ba 

Cikin karya murya yace

*ishat* dina kizo hammanki ya miki

Ko inxo nandinne?

Cikin Shauqin da ta samu kanta a ciki da mmkin hali irin Na Hamma Yusuf

Tace 

Sai kazo din ai

A dakin Ummin?

Cikin furza iska

Yace cike inxo din mana ki gani

Fuska ta tabe tace toh

Kazo

Angama yace

Ita kuwa katse kiran tayi tana ai dai duk fitinarka ka nitsu

Cikin sanyi ta shiga toilet din

...

Shi kuwa yana miqewa cikin 

Miqar jaraba da begenta

Ya juyo kenan ya ga Adam tsaye a bakin qofa ya harder hannu a qirji ya zuba mai ido

Cikin tuhuma

Ganin haka yasa ya gano cewa ya jima a gun

Murtuqe fuska yayi cikin kauda kai

Yace kai 

Kauce

Cikin tsura mai ido yace anqi a kace din

Ina zakaje

Kollonshi yayi cikin isa yace

Gun matata zanje ko kana da mgn?

Dry Adam yayi yana lallai

Yusuf wlh baka da kunya

Ni kake gayawa haka ka manta zantu kanka Na bayako?

Tureshi ya danyi

Cikin cewa koma dai mene ai dai mata tace mallakina

Ni wlh matsala ta da kai Adam ka fiye Sa ido

Babban banza 

Kawai😡

Ya fadin haka yayi cikin gida

Da sauri Adam ya bishi a baya

Yana wlh kai kam Yusuf sai 

Allah ne kadai yasan sirrin ranka

Mutum sai muna furci kanaso kana kaiwa kasuwa

Shi dai tsaki yaja ya wuce part din Ummi

A hanyar shiga bedroom Dinta sukaci

Karo da ita

Cikin kauda kai

Yace 

Ummi yunwa nakeji

Wucewa tayi cikin parlon

Sai da taje har kan kujera tare da amsa SLM Adam da kaka da suke shigowa tare

Lkci gufa kuma ta juya gun da yake

Sai wayam baya gun

Cikin mmk tace

Toh 

INA yashiga kuma

 Hira sosai su kaka da Adam da Ummi keyi Amman ita hankalinta Na kan Yusuf din


A can kuwa

A hankali ya bude

Qofar toilet din

Cikin

Sanyi ya maida qofar ya rufe

Ita kuwa

Ta cika baf din da ruwa ta murza sabulu a jikinta ta kada ruwan kumfa ya cikashi

Tayi luf a ciki

Idanta a lumshe

Cikin ranta kuma gaba daya

Tunanin Daren jiyane a ciki

A hankali tasa hannuta ta shafa qirjinta

Dan tuno yadda Hamma Yusuf ke shafa qirjinta

A ranta tace

Banji abin da nakeji ba in Hamma Yusuf ya shafa qirjina ba

Baki ta Dan tura cikin

Qara rumtse ido

Tace hannun Hamma Yusuf da bane Dana kowa a duniya

A fili tace

Meyasa meyasa hakan ne

Hamma Yusuf

Cikin sabule  kayan jikinsa

Ya shiga cikin

Ruwan

Bakinshi ya kai kan kunneta

Yace

Mekuma NAYI ganifa nazo

Da sauri cikin tsoro da mmk ta bude ido

Sai kum taji kunya ta diran mata

Shi kuwa

Jawota

Jikinshi

Yayi cikin 

Sanyi 

Yace menene a nan din ya fada yana shafa qirjinta

A hankali ta sauqe ajiyar zuciya

Cikin Sa hannu ta sanqalo

Wuyanshi

Murmushi

Yadanyi cikin rada

Yace

I miss you

My dear 

Qara maqaleshi tayi

Cikin kidima ya hade bakinsu

Wuri daya

A hankali qabbansa suka rinqa sakewa cikin mutuwar zaune

Ya kamo harshen ta da ta rinqa lasar jajayen lips dinshi da suke bata dry in suna karkarwa

Lasar lips din take cikin salon da itama batasan tanayiba

Dan Hamma Yusuf cire mata hankali ta yake a jikinta

Maida ita yake irinsa 

Kama harshen yayi yana tsotsa yana kuma murza bres

Dinta ga sanstin ruwa ga Na sabulu gana fatarta

Tuni ya kidime ya kidima ta

Sai numfashi yakeyi sama sama

Ita 

Kuwa a hankali

Take 

Ki ranshi cikin mayen love

Tana Hamma Yusufff

A dakin Ummi fa


Ummin kuwa yanxu ta shigo

Dakin cikin 

Mmk take jin alamun mgn a toilet din batayi zaton yana cikiba 

Ta matsota bakin qofar da niyar cewa Aysha lfy take mgn a bayan gida

Dai dai lkci

Yusuf kuma ya tashi cikin kidima yana lalubo bres Dinta ya samu yasa a baki

Ganin yadda yakeyi yasa ta gano me yake muradi shisa cikin

 kidima itama

Ta tallabo kanshi kamar yaro ta Dan dago qirjinta

Cikin rumtse ido

Ta tura mai bres Dinta

A bakinshi

Cikin kidima da gigita ya cabke yana sarrafata

Ita kuwa cikin wani irin Abu da ya ratsata

Ta qara maqaleshi

Cikin sakin Dan qara 

Tare da cewa

Hamma _Yusuffffffffff_

Bai iya amsawa ba sai nishi Dan yakeyi

Jin haka yasa Ummi kuwa

Barin dakin da sauri

Kunya CE taji ta rufeta ba iyaka ji take kamar ta nitse

A fili tace

Na shiga 

3 yaushe Yusuf ya koma Mara kunya da dai nasanshi da kunya

Parlon takoma gunsu kaka

Shi kam Adam shima zaman jiran ganin ta INA Yusuf zai fito

Ne yakeyi


Su kuwa a toilet

Aysha ta haukata Yusuf shima ya haukata

Duk sun zama tabbabu

Ba abinda 

Take cewa

Sai qiranshi take cikin

Rada tna

Hamma ```Yusuffffffff```

Da gyer ya dago ya kalleta cikin tsura mata ido

Da shafa 

Abinda yake tafiya da imaninshi wato bres Dinta

Murya a daqile

Yace

Aysha

Haka zamuci gaba da rayuwa

Aysha bazaki tausaya manaba

Kiga halin da muke cikifa

A hankali ta matsoshi ta manna kanta kan faffadan qirjinshi

Tasa hannu daya tana wasa da tattausan gashin qirjin nashi

Ido ta lumshe

A ranta tace

Hamma Yusuf nima ka gama min illah bansan lkcin da ka karyamin zuciya ba 

A fili kuwa

Lumshe ido tayi

Cikin tura baki

Tace

Ni ka  tafi kar Ummi tazo 

Tallabo fuskarta yayi cikin rada

Yace

Aysha shekarunki

Nawa yanxu

Cikin kasala tace

20

Qara matsota yayi ya  manna qirjinshi a nata

Yace

In dai kina da lfy to wlh bazaki juri irin zamannan da mukeyuba

Wlh ni kam bazan iyaba

Ina cutuwa

Aysha nifa ba waliyi bane

Dole INA da buqarta matata a kusadani

Ina buqatar kulawarki

Wlh yau dinnan zan iya rada raina muddin 

Baki matso gareniba

Haquri Na ya Gaza

Kimin tallafi

In ba so kike Na mutuba

Duk ya qara rudata

Da sabon salonsa

Cikin shogoba tarinqa

Dan bugun qirjinshi

Tana 

Hamma Yusuf ka tashi ka fita

Ido ya tsura mata qaunarta Na ratsashi

Cikin sanyi ya kife guywarsa duk biyu

Murya Na rawa

Yace

Kimin alqawarin zakizo gareni yau

In dai kina son Na rayu

In kuwa da gsky ke kuke son Na mutu toh ba yadda Na iya

Itama 

ido ta tsura mai

Cikin sanyi ta miqa mai hannu

Tace bazan iya tashi ba

Daqo ta yayi cikin

Kada kai yace nima zan iya faduwa ko a hanya ne kema kinji

Bakida qarfi bareni

Yana dagota

Ya miqa mata towel

Zata daura a qirjinta yace a qasa zaki daura

Cikin tura baki tace sabida me?

Sabida ban tafiba tukun kuma ban gaji da kallon abina ba

Cikin jin tsikar jikinta Na tashi ta matsoshi

A hankali

Ta manna qirjinta

Kan nashi tana gogawa

Shiko ido ya tsura mata cikin mmki

A fili kuwa cewa yayi

Wlh kin kusa ki qarisani

Bata kalleshiba ta juya ta hada bayanta da qirjinshi

Cikin hikima ta kamo hannayenshi duk biyu ta daura

Kan bres Dinta

Da qarfi ya saki ajiyar zuciya gamida

Komawa jikin gini

Ita kuma cikin murmushi mugunta

Ta fita tana juya mai ququ


Tana fita ta zura rigarta tayi

Parlon

Cikin nishadi

Taje gun kaka

Dake cin

Fruits

Zama tayi itama tanaci

Tana ya Adam yanxu kam tunda Amira ta dawo gida kullum sai an ganka

Cikin dry yace wato da bana zuwa kenan ?

Dry sukayi

Gaba dayansu

Dai dai lkcin

Yusuf ya fito

Fuska a murtuqe

Har zai wuce

Kaka tace

Kai wannan d'a da baqin hali kake yanxu wato bamu kaima ka kellemu ba


Adam kuma miqewa yayi da sauri

Yana zuwa hannushi

Ya tura cikin gashin kan Yusuf

Shi kuwa tabe baki yayi yace

Ni banma gankiba

Sarkin mita

Ummi kuwa ita kunya kallon ida sukema takeyi


Suna fita Adam yace

Wlh Yusuf iskanci ka ya girmi shekaru na

Kasan Allah ka fara ban tsoro

Zaka cinyemin yar uwa ka toskeni

Ni INA bin taka yar uwar a hankali

Cikin 

Rawar murya kamar mai shirin kuka yace

Adam zadai ta kasheni ita 

Wlh Ummi bata saniba zata rasa danta a banza abin yamin yawa

Allah sarki Adam sai yaji tausayi yinshi

Cikin

Sanyi

Yace

Yusuf Aysha matar kace

Insha Allah bazata kashe ka ba

Yau zan samo ma mafita

Tunda kaga dama nima yanxu a gida zanke kwana tunda Amira ta dawo gidan itama


A haka ya Dan bashi qarfi guywa


Tun da akayi sallan insha Adam ya jashi suka koma parlon Ummi

Baba bello

Kuwa da yaje Abuja

A dole Ahmad ya biyoshi da yasan halin da Yusuf ke ciki Dan Adam Na gaya mai komai

Gashi tafi yar moto

Sukeyi dan Ahmad

Yace yana son ganin gari

Kuma zasu biya

Yola

So haka yasa zasuyi isan dare

Wata qil su isa irin qarfe 1 zuwa 2 haka.


Su kuwa su Yusuf

 Suna zaune Adam ya tasa Amira a gaba

Yana ta tura kan Ahmad qarami wai yasha nono

Ummi Na kallonsu cikin tsokana tace Adam wannan da nakafa kurane

Cinye mana diya zaiyi


Cikin tsokana Adam ya kalli Yusuf dake ta

Bin Aysha da ido

Yace Ummi ai wlh

Yusuf ya gado

Shi kuwa Yusuf bata fuska yayi ya miqe yabi bayan Aysha.....


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI*,Page 1⃣0⃣2⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Da sauri ya Sha gabanta cikin 

Karya murya da lumshe ido yace

A,ish 

Bata kulashiba ta kauce ta juya zata

Fita da sauri ya kamo

Hannuta

Cikin rada  tare da tsura mata ido yace Dan Allah ki saurareni

Plxx ki daina wahal dani haka

Wlh ina azabtuwa.qara matsota yayi cikin tausayawa kanshi yace wlh

Ji nake kamar zan mutu

Ki tausayawa Dan umanki

Da sauri ta Dan tureshi 

Cikin  murguda mai baki tace

Sai me ni me nawa a ciki

Ba abin da ya shafeni

Inma mutuwa CE ai ba kanka aka faraba kuma ba kanka za,a qarebe 

Hanyace kaje 

Muma muna zuwa

Ai in maye ya manta uwar da baici ta manta ba

Banza  Sokuwa kuma

Me zata iya maka wanne taimako zan maka

A hankali ya farajin ranshi Na tafasa 

Cikin murtuqe fuska ya kamota ya matse ta jikin gini ido a juye yace

Na mutu ko baki da matsala da mutuwa ta ko

Aysha ni kike gayawa haka

Kin kyau ta

A hankali ya kuma sakinta

Cikin sanyin yace

Ki sani 

Koda yau ko gobe ko next week ko next month ko next year 

Na rasa raina ko lfy ta 

Kece sila

Ke kika kasheni

Juyawa yayi cikin cize lips inshi ya fice

Kamar zay hadiyi zuciya

Yana fita

Sama ya haura 

Kai tsaye parlon baba bello

Yaje ya kwana kan 3 str dan

Bai son damuwa

Bayan azabar da yake Sha

Adam ne ya miqe yabi bayanshi

Cikin sanyi

Ya shiga ya sameshi

Konce ruf da ciki

Ya tura hannushi

Ta qasa ya damqi mararsa

Cikin kula yace

Biyaye meke faruwa? 

 baiyi mgn ba 

Sai qara matse mararsa da yayi 

Sunkuyo wa kanshi

Yayi cikin kula

Yace

Kasha mgnin ka kuwa?

Kai ya gyada mai alamar ehh

Sai zufa dake keto mai

Duk jikinshi ya fara bari

Zuciyarshi ta fara harbawa da sauri sauri

Cikin mmk 

Adam yace 

Toh Amman Yusuf

Wannan fa ba shine mafita

Ba dama Na tabbata a kawai randa mgnin zai Gaza sama maka nutsuwa

Ka tashi mu tafi 

Part namu 

Ni zan turo Aysha


Da qarfi ya samu ya yunqura ya zauna cikin

Rawan sanyi 

Yace

Banson

Ka barta

Adam ka barta

Meyasa?

Zan barta ya tabba yeshi cikin kulawa

Cikin tausa yawa kanshi

Yace

Aysha fa

Tace bata sona

Bata qaunar ganina

Tace ko Na mutuma

Ba ruwanta

Ita bai shafeta

Ba

Ga ummina itama

Bata qaunar ganina

Ko gaisuwata bata amsawa lkci daya

Ya rinqa karkarwa

Sai riqe Mara yakeyi

A tsorace Adam ya talla boshi

Lkcin da

Numfashinsa ya rinqa

Fita ba tare da ya komaba

Duk Sai damqe mararsa yake dafe da qirjinshi

Jijiyojin hannushi da qoshinsa duk sun taso 

Sama

Sosai

Adam  ya firgita da  tausaya mai cikin hatsala da tsoro 

 ya sauqo

Dakin Ummi ya nufa

A dakin ya sameta da Aysha 

Da Maryam

Harda Amira

Cikin fahimtarwa

Ummi ta musu

Bayanin dawowar Ahmad

Lkcin take sheida 

Musu Ahmad

Yana raye kuma yau zai dawo

Cikin tsoro da mmk da kaduwa

Duk suka daqo ido

Suka xuba mata

Baki Na rawa Maryam tace

Ummi ya Ahmad kuma

Ummi ko dai mafarki nakeyi

Kamo hannu 

Ummi Aysha tayi

Cikin

Zubda qollah

Tace

Ummi

Bakya mna irin wasannan

Ummi wannan wanne irin zance ne

Ummi macecce Na dawowa ne

Maryam ne ta qara ruqqume

Yusuf qarami

Cikin 

Zubda qollah

Tace

Ummi kina 

Nufin 

Yusuf ba maraya bane mahaifinshi Na raye Dan Allah  kimin bayani

Sauqowa tayi cikin

Gsky da gsky ta kamo

Hannusu

Su duka

Tace

Maryam Na taba miki

Qarya ko

Wasa?

Kai ta qirqiza

Alamar a a 

Cikin sanyi

Ummi tai

Musu bayani

Mai gamsarwa

Gaba daya ido

Suka rinqa

Bin juna dashi

Kowacce da tunanin ta

Maryam kam daqo Yusuf qarami tayi ta rinqa

Kissing dinshi

Da gudu ta ture Adam dake qoqarin shigowa ta nufi

Part din Nenne

A namma Nenne ta jadda mata hakan


Itako

Aysha da Amira Sai hamdala sukeyi

Cikin fada 

Yace ke

Aysha

Kixo

Da sauri ta

Isa gunshi

Cikin

Murna ta sanqalo hannushi

Baki Na rawa tace

Ya Adam

Ya Ahmad Na bai rasuba

Ya Adam wanne irin


Godiya zanyiwa

Allah Na

Ya Adam

Me zanyi

A yau NASA 

Ya Ahmad Na farin ciki

Cikin 

Fada yace

Farin cikin

Ahmad ya kan kasancene

Yayinda

Yusuf ke cikin Farin

Ciki

Gashi ke kuwa baki da buri Sai son baqan tawa 

Yusuf

Ko kin manta Ahmad kan sadaukar

Da duk wani Farin cikinsa da jindadinsa ga Yusuf ne

Ga Ahmad can ya kusa shigowa garin taraba

Kuma wlh bai begen ko uwar da ta haifeshi kamar yadda yake begen Yusuf

Gacan Yusuf

Kuma zuciyarsa na qoqarin

Fashewa

Cikin sanyi

Ta tsura mai ido

Shiko zame hannushi

Yayi ya nufi gun Ummi

Jikin a sanyaye yace

Ummi inajin tsoro

Kar randa Ahmad zai dawo garemu Yusuf kuma ya barmu

Wlh Ummi Yusuf bai da lfy

Ummi fushinki

Na cin ran Yusuf

Ummi kinsan biyaye Nada matsala zuciya kam ko?

Cikin Dan rashin damuwa

Ummi ta tabe baki tace

Adam ba yanxu ya bar nan ba

Ni banga me akayi maiba

Baqin halin shi ne kawai ya taso

Kai ya jinjina cikin

Jawo hannu Aysha

Yana zo nan

Da sauri

Ummi tace

Kai Adam sake min Y'a 

Ka fitanmin daga nan

Ba inda zataje

Cikin sanyi yace Dan Allah Ummi Dan Allah kiyi haquri

Cikin fada tace

Adam fitamin daga nan

Zaiyi mgn tace

Ya isa tafi kawai zamu rufe qofa

Juyawa yayi cikin 

Rashin mafita

Da sauri matarsa ta bishi a baya

Cikin kula take cewa ya Adam 

Meke damun Hamma Yusuf din

A INA yake

Hannuta ya kamo

Suka haura saman

Yana zomuje kiga halin da Yusuf ke cikifa

Suna shiga

Adam ya saki hannuta da gudu ya nufi

Kanshi ganin yadda yake juyi a tsakiyar carpet din parlon

Yana damqe da Mara Sai yunqurin amai yakeyi

Kuma ba abinda yake hararwa

Itama Amira isowa tai da gudu

Tana Hamma Yusuf

Shiko Adam jijjigashi yake yana Yusuf Yusuf shi kuwa Sai bishi da yakeyi da fizgar numfashi

Da gudu Amira ta sauqo

Qasa cikin kuka

Take kiran

Ummi da qarfi tana

Ummi Ummi kixo

Wayyo Ummi kizo

Hamma Yusuf

Sai kuma ta nufi

Sade din Abba tana

Abba kazo Hamma Yusuf fa bai

Da lfy

Allah sarki Abba cikin rawan jikin ya fito

Yana Amira INA Yusuf din meke damunshi 

Cikin kukan tace yana parlon baba

Ganin ya fito ta kuma yi bakin dakin Ummi tana 

Ummi wlh Hamma Yusuf baida lfy

Aysha dake

Konce

Gefen Ummi

Cikin sauri ta miqe ta zauna

Hannu Ummi ta riqo

Tana zare ido

Tace Ummi 

Ayyah Ummi kije ki Duba shi

Mana

Lkcin Amira kuma ta shigo

Duk ta rude hannu Aysha ta kamo

Tana ja tana kizofa kiga yadda yake

Ganin yadda amiran ta rude yasa ta bita Ummi ma ta miqe ta bita a baya

Suna fitowa

Parlon

Abba Na sauqowa da sauri yana Adam dauko shi mu tafi asibiti

Dai dai lkcin

Su Ahmad kuma sukayi SLM

Da qarfi Aysha ta fizge hannuta cikin Na Amira 

Cikin tsalle da karadi

Ta afka jikin Ahmad

Ruggumishe tai kamar zata mai dashi cikin jikinta


Ba abinda take furtawa Sai

Ya Ahmad Na

Ya dawo

Jin ihunta ya fiddo Maryam a guji

Jikin bugun zuciya

Tana zuwa kuma Sai tayi tura ta zuba mai ido

Sai kawai ta durgusa a gun Sai kuka ya kofce mata

Nenne ma Sai

Kuka

Shiko Ahmad

Sai murmushi yakeyi

Cikin yanayinshi mai sanyi

Yace

Ummi INA biyayena

Ya fada yana ture Aysha daga jikinshi

Gabanta Nenne yaje ya tsaya

Sai hawaye kawai  a fuskarsa

Durqusawa yayi a gabanta ita kuwa dafe kanshi tayi cikin

Sauqe ajiyar zuciya tace

Allah ya maka aibarka

Amin ya amsa cikin

Sunkuyar da kai ya isa

Gaban Maryam daketa ta rusa kuka ruqqume da dansu

Cikin murmushi

Ya bude hannushi

Murya a saqile

 yace

Ina kikene maryama

Na Duba gabas ban ganki ba Na Duba arewa ban gani

Jin haka yasa ta taso ta fada qirjinshi

Da qarfi ya sauqe ajiyar hrt

Yana mai cewa

Na godewa Allah daya manike

Maryama taho masoiya

Sake Maryam yayi ya juya gun Amira daketa sharar qollah

Yace Amira ba mgn ne 

A hankali ta matsoshi cikin 

Kuka tace 

Hamma

Hamma Yusuf fa 

Da sauri ya wore idanshi cikin

Kaduwa yace

Meyasa mu biyaye Na INA yake

Cikin kuka tace

Yana parlon Abba

Allah sarki Ahmad

Da gudu cikin

Kaduwa ya haura sama

Baba bello Na biye dashi a baya

Suma su Ummi duk suka bisu a baya

Suna shiga Ahmad

Yayi Kansu

Adam dake tallabe da Yusuf

Sai yunquri yakeyi

Ga rawan sanyi 

Hannushi kuwa duk biyu ya damqe mararsa

Idanshi A rumtse

Ganin

Haka ya ruda Aysha

Tsoro ya kamata da sauri

Jikin tsoro da kuka ta isa gabanshi

Da sauri ta kamo hannushi 

Tana

Hamma Yusuf

Ka tashi ka bude idonka

Duk da wahalar da yake ciki ya gane

Muryoyin nan biyu

Na Ahmad da Aysha

Cikin kaduwa da tsoro

Ya bude idanshi a wahala

Kan fuskar Aysha ya sauqe ganinshi

Baiga Ahmad dake ta gefenshi riqe da hannushi

Da iya qarfinshi ya fizge hannushi a NATA

Cikin rawar murya 

Yace sakeni

Karki qara tabani

Ki barni 

Bakince Na mutuba bai dameki ba

Kunce

Dani Na mutu Ahmad ya rayu

Bakwa sona

Shi kuwa Ahmad yana

Sona shine

Kadai

Mai bin bayana shine mai min uxuri

Gashi yanzu

Naji

Ahmad a kusa dani

Na tabbata

Kurwar Ahmad tazo

Bikon tawa

Zanbi Dan

Uwana

Zan mutu Ku huta da ganina

Cikin

Sauri Ahmad ya ruqqumoshi

Murya Na rawa yace

Biyaye Na bude idanka

Ba kurwatace ba nine

Dan uwanka Ahmad INA Raye ban mutuba

Itako Aysha sai

Kuka duk ta rude

A lkcin da taga

Ya sauqe wata iriyar nishi

Sai kuma yasake ko inanshi yayi

Luf

Da qarfi ta fada

Kanshi

Fuskarshi take jijjigawa

Tana ki ranshi da qarfi

Tana

Hamma Yusuf

Ka tashi

Wlh bance ka mutuba

Ka tashi

Ina sonka

Kife kanta tayi

Jikinshi

Cikin tsananin kuka

Ta rinqa sabbatu

Tana ya Ahmad ka gaya mishi

Nibance ya mutuba

Dan Allah Hamma Yusuf ka tashi

Ummi kixo kice kin yafe mai

Zai tashi bazai mutuba

Gaba daya

Suma tasasu kuka

Nenne CE

Taxo cikin sanyi ta kamo hannushi

Ta Dan matsa

Gun baba bello taje Wanda ya zama tamkar an dasashi

Tace

Suma yayi

Jin haka yasa

Adam dauko Goran ruwa mai sanyi ya Rina fesa mai a fuska

A hankali

Ya bude idanunshi

A hankali ya tsurawa.Ahmad ido

Sai kawai

Ya fada jikinshi

Ruggume juna sukayi

Cikin

Kuka tamkar yara

Ahmad ba abinda yake dafi Sai

Cewa yake

Yusuf

Insha Allah zamu rayu tare

Bazamu qara yin nesa da juna ba

Sai indai mutuwar gske ta riskeni 

Shiko Yusuf Sai hamdala yakeyi

Lkci daya kuma

Yunqurin aman ya sake

Taso mai da sauri

Aysha ta kuma fashewa da kuka

ta fada jikinshi

Tana 

Hamma Yusuf

Ka gafarceni

Wlh bansan hakan zai cutar da kaiba

Jinta a jikinshi ya angiza

Tunanin shi

Cikin rawan hannu ya matseta a qirjinshi

Murya Na rawa

Yace

A,ish

Ina sonki

Fiye da yadda nake son raina

Na rayu da sonki a zuciya ta tun bansan kainaba

Kefe farinciki Na

Kece haske rayuwata kin kasance bugun cuciyata

Dan Allah kar ki gujeni

Qara matsota yayi ya manta da kowa a gurin

Baijin kowa bai ganin kowa a wurin Sai ita

Duk ya rude

Gaba daya suka juya suka bar parlon ganin

Yana mammatse yar matarsa tuni ciwon maran ya fara tsikararsa

Suna fita

Ya tallabo fuskarta

Ya tsura mata ido

Cikin rawan murya yace

A,ish

Kin yadda dani ki yadda da baqoncina cikin rayuwarki

Ki taimaka min ki bani

Haqqina

Idanta ta rumtse cikin

Bugawar girji da tsoro ta manna bakin ta kan lips dinshi da suke ta rawa

Jin bakinta kan nashi yasa shi kidimewa da gigicewa cikin rawan hannu

Ya tura hanna yenshi cikin rigar

Baccin dake jikinta

A hankali ya sauqe ajiyar zuciya itako tsoro ne ya rufeta jin yadda a cabke.......




Ku biyoni page 103 kusha karatu

Da ganin salon koyarwar Hamma Yusuf😝


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👆🏻👆🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣0⃣3⃣Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 oh amrita shine abinda yusif yake fada yana juyata kamar waina a cikin tanda wani irin nishi yake futarwa kamar tsohon zakin daya shekara beci abinciba aysha kam ta tsorata da halin da hammanta yake ciki ga wani feelings da takeji na tsananin bukatarsa kawai saiji tayi ya sureta yai part dinsa da ita yana zuwa ya azata akan bed ya fara balle riggar jikinsa yai wulli da ita yai jifa da wandon aysha tana gani ta runtse ido kawai sai ji tayi anja rigarta ana shaffo nonuwanta abubuwan da sumafi daukan hankalinsa kenan yana cafkarsu ta saki wata kara data gara fidda hamma daga hankalinsa bakin nan ya kama rawa ba shiri ya cabki bakinta wani irin zazzafan rommans yake mata wanda betaba mata irinsaba tun tana jurewa harta fara maida martani kwata kwata hamma yusif ya fita daga duniyar ya tafi wata hakama aysha wani irin feelings take ji wanda sex kawai take bukata nonuwan nan kuwa sunsha tsotsa kamar za a guntule dan kan kawai asshhh isss washh dinsu kake ji a dakin  bakajin komai can ya cabji nononta yana gurnani yana mutsikasu can kuma saitaji dib ya dauke wuta kamar wanda ya suma ya kankameta some munite  letter san nan taji ya jata yana fadin amrita allah yai miki albarka kinshayar dani dadin da vantaba shaba a yau a zuciyarsa fada yake a hakama na kere dadina inahga na shiga wan nan korama uhmmm garin dadi na nesa kawai wani killer smile taga yanayi batason me yake tunaniba ita kanta yau ta bukatu da kasancewa da hammanta iya bukatuwa tana wan nan tunanin taji ya sunkuceta sunyi toilet a toilet dinma sunfi 1hour suna abu daya shine murza nono da shansu kamar sabon jariri lol😜 

A cikin gida kuwa suna shiga kowa yai bangarensa ahmat tunda  suka shiga yake kallon maryam kamar yamaidata ciki  su ummi kam da nenne kowa dakinsa yayi sabida sun fahimci abinda yake damun yusif ga kuma ahmat da sukaga yanabin maryam da wani kallo ko ba a cemusuba a matsayinsu na manya sunsan ma anar kallon adam kam yau yasamu damar shakiyanci sai dariya yake kasa kasa  yaiwa ahmat sallama wanda har yakai kusa da maryam ya dangi hannunta sunyi daki sai dagawa adam hannu yayi suna shiga ya rungumeta a tare suka saki wata ajiyar xuciya me karfi maryam ta saki kukan murna tana sauke yusif karami a bayanta yai wuf ya karbeshi yana hamdala da allah ya nunamasa kwansa a duniya san nan yaje ya kwantar dashi a gefan bed ya dawo gun maryam yanazuwa yaimata wata runguma yafara yamutsata abinka da gwaron shekara da watanni kisses dinta yake kamar ba gobe itama tana mayarmar ranar ahmat yayi kukan dadi ba a dadi assuba ta gari lovvers 

 Gari na wayyeww gida ya fara cika da yan taya farin cikin dawowar ahmat  rabi u  usman haidar iyayen kuka kenan har sun fara kukan murna abdull da sadig sai murna ake barinsu kaka innayi da innah da baffa ba magana ancika sai yanzu su hamma yusif suka fitk shida aysha shifa tunda yaji ahmat be mutuba yake jin dum wata matsalarsa ta kyau kana ganinsa kaga sabon ango sai yar ramar da yayi ta azabar ciwon mara daya sha yanazuwa sukai rungume juna shida ahmat da adam suna murna aysha kuwa hannun ahmat taja tana ya ahmad dina wai wacce irin murna ya kamata nayi ne su baki abin magana akai wuff akace party za a hada mana kawai hamma yusif yana zaune yana latse latse a waya kamr hankalinsa baya kansu nan ko komai ake hankalinsa yana kan amrita  kai innace muku xan rubuta iya murnar da familys din an sukai a ranar zan iya cika page din nan ban gamaba saidai na takaita ranar anyi walima da ciye ciye kowa yana farin ciki hala aka watse da alkawarin za a je a gyarawa su ahmat gidansu gobe saisu koma taro ya tashi kowa ya tafi yana murna 

Nima nayi murna da cikar familyn nan 



Kubiyoni kusha labari yanzu aka fara


By garkuwar fullani

Nagaisheki kawar arziki aysha s bayero 

(Maman shukrah)

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👆🏻👆🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣0⃣4⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Su Abba da su baba bello

Duk gidan suna cike 

Anata hira

Har kaka 

Da Anuty sadiya

 Suna cikin cikar 

Farin ciki

Ahmad ne

Da Yusuf

Suka shigo a tare riqe 

Da hannun 

Juna

Adam Na biye dasu

A baya

Suka shigo

Kan carpet suka zauna

Nenne tai murmushi cikin jin dadi tace

Yusuf sai yau naga

Yelwarka ta dawo

Kai ya sunkuyar

Cikin furta

Alhamdulillah.


Baba bello ya Dan kallesu cikin

Bada umurni

Yace

Ahmad Sai

Ka shirya

Gobe

Kuje Yola

Dan

Goggonku tace Sai dai

Tazo nace ta bari

Zakuje

Dan dama Maryam tunda ta aihu

Batajeba

Gashi

Adam ma zai

Kai takwaranka su ganshi

Dan haka Ku shirya gobe kuyi sammako

Kuyi Yola.

Cikin Farin ciki

Maryam ta miqe tana

Yauwa

Baba ni barima naje Na shirya

Amira ma miqewa tai

Gamida miqewa

Aysha.

 Ahmad

Qarami tana

Aysha karbeshi

Nima naje Na shirya mana

Ture

Dan pilet din gabanta tayi Wanda take cin

Inabi da tupa

A ciki

Ta kalli Amira cikin

Harara tace

Toh ai nima zanje

Nai shirin.

Ki bawa Ummi shi

Cikin,

 dry Amira tace

Toh fa ai banji

Ance dake  za ajeba da kike wani cewa zakije kiyi shirin,

Cikin harara 

tace toh ai Sai ki hanani

Sai kuma ta juya

Gun baba cikin

Sanyi tace

Baba INA nima zanje?

Naje Na shirya ko?

Ido ya Dan zuba mata Sai kuma ya juya ya kalli Yusuf da ya hade fuska

Cikin Dan murmushi yace

In mijinki ya barki zakije

Mana 

Ki tabbaya

 in ya barki Sai ki shirya.

Baki ta tura cikin

Takaici

Tace toh

Baba ai in kace naje dai shi kenan

Ko ?Hamma Yusuf, ta fada tana

Kallon fuskar Yusuf

Din,

Rai a hade ya qara yamutsa fuska yace

Bazaki jeba,

Ido ta zaro cikin

Hatsala

Tace 

Ni da gidanmu kace bazanje ba ?

Bai kulata ba

Sai ta kuma hararanshi tace

Wlh zanje

Haka kawai

Kowa zaije saini

Kace ba zanje ba

Ko kallonta bai kumayi ba.


Sadiya CE ta jawo hannuta

Tauzanar da ita cikin rada

Tace ke

Ki nitsufa a gabansu Abba kike

Kinga zai daureki da jijiyoyinki

Kimai rashin kunya a gabansu

Waya CE miki haka ake tabbayar miji Abu bare uwa uba

Namiji irin Yusuf

Basa son izzah

Ki kula

Kiyi lup ki nema a tsanake cikin faran ta mai Sai ya barki 

Tura baki ta kumayi

Cikin sanyi tace 

Ayyah Hamma Yusuf Dan Allah ka barni naje kaji ko

? Miqewa yayi cikin

Isa 

Yace

Bada yawuna ba.


Hannu Ahmad yaja suka fita 

Adam ko karbar Ahmad qarami yayi ya nufi gun matarsa

Itako Aysha

Gun Ummi ta matsota cikin

Shirin zubda qollah tace

Ayyah Ummi Dan Allah Ku barni muje da yan uwana

A hankali Ummi tace

Aysha

Bani da ja da abinda

Babanku yace

Ki nemi yardar

Hamman naku.

 Miqewa tayi

Cikin zubda qollah

Tace

Shi kenan kuma Sai ace Sai Hamma Yusuf ya yarda zanje wani wurin

Bayan kuma ansan

Dama kullum zagina yake Na fiye yawo Sadiya ce ta bita dakin Ummi

Kan gado ta sameta tana kuka tsaka ninta da Allah

Dan Aysha in taji

Tafiya gaba daya jikinta rawa yake

Bare wannan tafi yar da za ayita cikin farinciki


Cikin sanyi

Sadiya tace

Aysha tashi

Tashi kiji

Kinji ko?

A hankali ta tashi

Hannuta ta riqe cikin sanyi

Tace

Tashi ki ji INA kina son

Zuwa yolo?

Ehh ta bata amsa da sauri

Murmushi tayi cikin dabara tace 

Jekiyi wonka

Kizo

Insha Allah zakije.

Cikin murna tace

Dgske Anuty 

Ehh ke dai jekiyi wonka 

To tace cikin

Jin qarfi quiwa ta fada toilet

Wonka tayi mai rai da lfy

Tai buros 

Tana fita

Anuty Sadiya da kanta

Ta rinqa 

Murjeta da mayuka da turaruka

Cikin

Hikima ta gyara ta tsaf

Da kanta ta zabo

Mata kayan

Bacci

Ita kuwa Sai dry take tana ke dai

Anuty kina son gashin nan nawa kuma kema kina dashi

Dry ta danyi lkcin

Da ta miqa mata wasu riqan

Bacci

Farare masu ratsin ja ja 

Masu taushi da laushi

Sai qamshi suke fiddawa mai dadin shaqa

Rigar yar yelo yelo bata da kauri ko kadan 

Daga gefen Hanna yenta kuma ragane

Hannu kuma mai Dan guntune

Dan wondon kuma iya karsa cinyarta.

Karba tayi ta saka cikin

Lumshe ido

Tace Kai suna da kyau banma taba sasuba

Ya Hydar nane ya kawo minsu

Ga yadda suka min kyau

Anuty 

Dry tai cikin

Kada kai tace

Aysha ai dama ke kekkyawa ce

Qara dauko

Turaren 

lailatu sahra tai ta fesheta

Dashi

Cikin

Fahimtarwa

Ta

Miqa mata 

Hijabin da ta jiqeshi da qamshi

Tace sakashi

Kije

Gun 

Yusuf

Ki qasqantar da kanki

Karkiyi mgn cikin izza 

Ko fushi

Kiyi mai mgn

Cikin Neman

Alfarma

Ki tausasa laffuzanki

Na tabbata zai barki kije

Da sauri

Ta koma kan gado ta konta

Cikin tura baki

Tace wannan mugunne zai yarda cikin sauqi

Ni bazanjeba!

Cikin sauqe ajiyar hrt taja

Hannuta tace

Kije

Insha Allah zai barki

In kuwa bai barkiba Na miki alqawarin

Zan nace Sai ya barki Amman dai kije din.

Miqewa tai cikin

Cewa shi kenan tunda kince zaki tayani...

Tana fita 

itama Sadiya ta fita ta nufi part din nennenta

            🌹🌹🌹🌹

Tana fita

Ta nufi part dinsu

Cikin jin dadin iskar dake

Busawa

Da alamun hadari

Ga walqiya dake haskawa daga qasa alamun gagarumin hadarin


Sukuwa dama su Yusuf

Suna fita


Maryam ta biyosu

Cikin Dan sauri sauri

Tana ya Ahmad

Yana jin muryan ta

Ya tsaya cikin

Jaye hannushi daga cikin Na Yusuf

Din tana zuwa

Ta matsoshi cikin

Sanyi ta kamo hannushi

Tace ya Ahmad Na shirya kaya da yawa ko in munje zan dade ai?


Matsota yayi cikin

Shafa fuskarta yace

Bazan iyaba maryama INA buqatar ki

Ni wlh tafiyarba da za,a barta Sai

Next week

A barni da iyalaina naji duminku kuji dumina.

Shi kam Yusuf ganin

Sai shirin shafe juna suke ya sashi

Wucewa cikin

Cewa

Shi dai biyaye bazai canzaba


Yana shiga part

Dinsu 

Dakinshi ya wuce

Tartare dakin yayi

Ya gyareshi tsaf ya

Kuna A,C

Ya feshe dakin da

Turarukan daki.

Dakin yayi ras

Komai Na dakin

Farine da ratsin

Ja ja

Hatta bedsheet din da blanket

Din da carpet din tsakiyar dakin da labulayen

Ya bude widdunan da labulayen

Iskar daminan 

Mai qamshi Na ratsa dakin

Ga qamshin furannin

Cikin garden dinsu

Sai kukan tsuntsaye ke tashi,

Lkci

Daya yanayin

Ya canxa tunanin shi

Da gabban jikinsa

Gaba daya ba abin da yake muradi

Sai Ya jishi cikin jikin A,ish 

Dinshi

Surar jikinta kawai ke rudasa

Cikin tasowar

Wata muguwar Sha,awa

Ya rege kaya 

Jikinshi

Ya fada toilet

Wonka yakeyi

Yana tunanin

Ya zaiyi ya samu ganinta

Da gyer ya fito

Yana fita

Daure da towel a qugunshi

Ya rinqa 

Bin jikinshi

Da turaruka

Shi dama Yusuf ma abocin son qamshi ne

Gashin kanshi ya rinqa gyarawa

Yana zaune kan

Dressing stool

Ya Na shaqar qamshi

Sai lumshe ido

Yakeyi


A hankali ta tura qofar cikin yin slm

Idanshi a lumshe ya sauqe wata sassanyar ajiyar hrt

Qarasowa tayi

Cikin

Dan daure

Fuska

Shiko

Ta jikin madubi ya

Xuba mata ido

Farin cikene damqan cikin ransa

Ji yake tamkar ya rinqa buga tsalle ya ruqqumota

Amman bai son ta rainashi

Gwara ya tsare gudun kar ta ganoshi

Ya Dan harareta

Cikin isa

Ya miqe

Ya koma bakin gado

Ita kuma

Matsoshi tayi gunshi

Cikin jin haushin yadda ya wani

Share ta

Murya kamar zatayi

Kuka

Tace.

Ayyah Hamma Yusuf

Dan Allah kayi haquri ka barni inje

Yolannan

Baki ya tabe

Cikin mugunta yace

Ban aminceba.

Sai dai in satar hanyan zakiyi yadda kika saba

Sai kije keda mahaliccinmu

Qara kontar da murya tai cikin

Kauda kanta

Dan Sam bata son ganin qirjinshi

A hankali

Tace Ayyah Dan Allah fa Hamma am

Ido

Ya tsurawa bakinta

Da yake sheqi

Cikin fara canxawa

Yace

Nace bazaki jeba ko.

Ita kuwa Zuwa

Yanxu ta gama qulewa

Cikin

sanyi ta miqe

Baki a tuntsure

Tace

Kada ka barni din mana

Dan kaga amsa nazo Na tabbata yeka shine kake min wulaqanci

Ai ni dama Na sani bazaka barni ba

Juyawa tayi cikin

Takaici

Tace

Ni wlh in Dan tanine

Baka isa

Na nemi ixininka ba,

Ta juya zata fita

Ya miqe cikin zafin nama

Bakin qofa yaje ya rufe qofar ya

Juyo

Gunta

Rai a bace

Dan har cikin ransa yaji zafin furucinta

Fizgota

Yayi cikin

Zafi

Ya turata jikin

Gini

Cikin fada

Yace

Ni kike cewa ban isaba?

Ni dinne ban isanba?

Jin yadda ya matsota

Yasa ta rinqa

Juya kai cikin

Zare ido alamar a a

Zare hijabin

Jikinta

Yayi

Cikin

Hada fuska

Yace a yau dai zan isan zaki tabbata ni isheshene

Yana cire

Hijabin

Ya tsura mata ido

Cikin

Daukewar

Numfashi

Ya jawota

Cikin qirjinshi

Ya rinqa shaqar qamshi jikinta Dana iskar damina

Ita kuwa

Tureshi takeyi

Cikin

Cemai 

Ni ka sakeni

Baki a mace

Yace 

A,ish

Bata kulashiba

Sake Hanna yenta yayi

Cikin

Rawan jiki

Ya daura hannushi kan qirjinta

Boturan rigar

Ya fara ballewa

Da sauri

Cikin fushi

Ta huge hannushi

Tana me hakan

Ni banson

Jawota yayi

Cikin rawan murya

Yace

Ni kam INA so

Dan Allah Aysha

Kar ki cutar dani a wannan Daren jumma an

Ki barni Farin cikina ya cika

Jawota yayi

Bakin

Gado

Ita kuwa

Tirjewa tayi

Ganin

Haka

Yasa

Cikin

Garfi ya

Fizge rigar

Hannushi ya daura kan

Qirjinta

Bres Dinta

Ya cabe

Cikin wani irin yanayi

Ya rinqa matsarsu

Ita kuwa hannu tasa zata tureshi 

Ganin haka yasa cikin

Sanyi ya kamo hannuta

Cikin

Fita hayyacinsa

Ya konto towel din jikinsa

Hannuta ya jawo zai daura

Kan mararshi

Jin haka yasa ta tureshi da sauri

Taja da baya ta fada kan gadon

Ido a juye ya

Haye gadon Jawota jikinshi

Yayi cikin rawan

Murya yace

Dan Allah kiyi haquri ki tausaya min


Cikin halin  takaici tace

Ni ka barni


Tashi yayi ya zauna

Cikin sanyi ya komo hannayenta

Ya zaunar da ita

A hankali ya manna bakinshi kan NATA

Cikin

Wani salo

Ya zura mata harshensa cikin

Bakinta

Bata kamata sannan bata janye jijinta ba

Hannushi ya daura

Kan qirjinta

Ya cabke

Bres Dinta

A hankali ya rinqa

Shafarsu

Yana murza

Kansu

Lkci daya ya sauqe mata

Wata irin muguwar kasala

Da shauqi

Gaba daya taji gabbanta

Na buduwa suna karbar saqonin 

Hamma Yusuf

Din nata

A hankali ta daga hannayenta

Cikin macewar jiki

Tayi woni irin

Miqa gaba daya

Ta narke

Cikin jikinshi

Shi kuwa sai

Sarrafa dukiyar

Fulaninta yakeyi

A hankali ya gangaro hannushi

Kan mararta

Cikin wani tsoro

Jin hakan

Yasa Aysha

Ta saki wata maryaniyar ajiyar hrt

Cikin 

Kidima ta

Cabki harshen shi dake

Cikin bakinta

Ta fara tsotsa

Cikin sanyi da lumshe ido

Dan kuyarshi takeji

Gashi wuta a kunne

Gakuma suna saitin miro

Gaba daya ta qara birkita

Hamma Yusuf Dinta

Sai karkarwa yakeyi da nishi

A hankali taji

Lips dinshi suna motsawa alamar sun fara kadawarsun

Cikin sanyi ta zare harshensa ta laso lips din nashi


Shi kam ya gama kadewa

Qirjinta kawai yake kadawa

Ya tsurawa fuskarta

Ido

Jin ta Dan sake shine

Tare dasa hannu bibbiyu ta kare fuskarta

Yasashi

Kontowa

Kanta

Cikin kidima ya manne bakinshi

Kan bres Dinta ya 

Rinqa Sha tamkar yaro

Ya cabke dayan kuma da hannushi

Ita kam Aysha

A hankali

Take

Kiran shi

Cikin rawar murya tana

Shiiiihhh tana mimmiqewa

Ta hura mai iska a kunne

Cikin sanyi da sarqafewar murya

Tace

Ham Hamma Yusuffffffff

Sai ta kuma lumshe ido

Ta Dan qara tura mai qirjinta

Shi kuwa ya gama zaucewa

Ba abinda yake buqatar Sai

Kasantuwa tare da ita

So yake yaji jikinshi

Cikin nata

Cikin qurnani da nishi

Da shan yaji 

Ya rinqa

Mutsutsukata

Gaba daya ya gigice ya gigitata


Tasowa yayi cikin

Qarfin hali

Ya kashe wutar

Itako gaba daya take son tattaro qarfinta

Amman ta kasa

Sai jinshi

Tayi

Yayi mata rumfa da qirjinshi

Jin ko INA nashi a fili

Gashi itama duk ya rebata da suturanta

Yasa tsoro ya diran mata

Cikin firgici

Ta kamo hannushi

Tana karkarwa

Tace

Hamma Yusuf qirjina

Ciwo

Bayana ciwo

Ka sauqa kamin nayi

Cikin kidima

Yasa hannushi ya lalubo bres Dinta ya rinqa shafawa

Murya Na rawa

Yace .

Dan Allah A,ish 

Ki daure wlh

Bazan wahal dakeba

Plss matata ki agazamin

Walahi zan iya rasa raina.

Kuka ta saki cikin tsori ta

Tace

A a 

Hamma Yusuf wlh

Bazan iyaba

Ni ban tababa

Cikin 

Fizagar 

Numfashi

Yace

Na sani

A,ish nasan

Baki taba ba.

Wlh zan miki a hankali

Bazan wahal dakeba

Jawo hannuta

Yayi ya daura

Kan

Mararsa

Yana kinji

Halin da nake ciki

Janye hannuta tayi

Cikin

Tsoro

Jin abinda yake

Qoqarin aikata mata

Gadan gadan

Ya haye ruwan cikinta ya mata rumfa da qirjinshi

Jin zai rabata da budurcinta

Yasa ta dage ta tureshi

Cikin kuka

Tace

Bana sonka ni bazan iyaba


Kaima 

Bani kake soba

Yarintata kakeso


Da qarfi ya rufe mata

Baki

Cikin

Rawan jikin da murya

Yace

Wlh 

Ke nake so Aysha

Ba yarintarki nake Sha,awaba

Ke zatinki nakeso

Kuma sonne ya kawo Sha,rawar

Ki yarda dani

Kin sani da yarintarki nakeso wlh da Na Dade da cimma burina

Cikin 

Kuka tace

Wlh Hamma Yusuf yaudarata kakeyi

Baka taba sonaba

Koda a matsayin yar uwar ka bare a matsayin aurataiya

A duniya ba wacce ka sana kamar ni

Cikin

Kuka kamar yaro

Ya riqi hannuta

Ya kafa guiwarsa

A qasan gadon

Ya daura kanshi

Kan cinyar ta


Ya fara mgn cikin kukan sosai

Da rawan murya yace wlh

Shaquwa zata sanya

Yarda

Idan nace miki ke kadaice a zuciyata

Kuma ke Na zaba ki gaskatani ki bani dama

Qara kontar da kanshi yayi

Yaci gaba da 

cewa 

In na fada miki

To

Kiyarda mini

Duk tsanani da wuya

Zana sakarmi ki so😍

Kiyo riqo kar naga

Kin gajiyar

Indai kikai

Haka so

Ya habbaka

Zamuga ken tfy

Wlh A,ish

Da shaquwa

Aka samu yarda harso yasanyanmu kama da juna


Tureshi tayi

Cikin rawan jikin

Tace 

Hamma Yusuf fada kaiwa kakeyi

Cikin 

Qara matsota da rarrafe

Yace

Wlh

Shi bugatan da nake ciki in

Ya tsananta

Zai iya taba qoqolwata

Na qaqauta dakisan

Nufuna

Sirrikan cikina da zuciya ta

Nake sheida miki

Ki taimaka

Ki ka war min

Da buqatata

Dan duk kan alamar

Kin qullaceni

Kina fushi dani

Aysha

Bazan ga ken yanayi ba

Tunda byeka

Ra ayi 

Dole Na qarfafa

So nayo

Miki

Riqon da ba shayi

In kauda kurenan Na baya dan Na faranta miki

 Ni nace miki

Gwarai INA sonki

Karki qi yarda

Hannuta ya daura kan

Qirjinshi

Yaci gaba da cewa

Me kike so

Ya zamo alama Dan a  kawai sabon

Inko yarda kike buqata to ki sanya rebo 

Danke gudace

Daba kamarki

A zuciya ta da rayuwata


A hankali kalamanshi suka rinqa Ratsata jikinta

Yayi sanyi

Jin tayi shiru

Yasa

Ya matsota

Ya tura hannushi

Kan bres Dinta

Ya musu wani irin

Cabka tare da sauqe ajiyar hrt

Tureta yayi

Ta koma kan gadon cikin

Sheshsheqar kuka

Ya haye

Kan gadon 

Jawota...


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAWA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣0⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Jawota jikinshi

Yayi cikin

Rawan murya

Yake 

Bata haquri

Da furta 

Mata kalamai

Masu tsadar 

Samuwa 

Daga gareshi

Hannushi kuwa

Na kan 

Bres Dinta

Itako

Cikin tsoro 

Ta janye jikinta daga 

Gareshi

Cikin duhun

Ta lalubo

Hijabinta

Shi kuma

Miqewa yayi

Ya kunna wutan

Gunta ya nufa

Bayan ya daura

Towel a jikinshi

Matsota yake

Tana kaucewa

Har ya isa

Gareta

Hannushi

Yasa ya tallabe fuskarta

Cikin 

Sanyi

Yace

Dan Allah karki gujeni a wannan Daren

Plss

Ki kusan to gareni

Wlh zan cutu

Matuqar kika barni 

Cikin halinnan,

Zamewa tayi gefe

Da sauri

Ta bude

Qofar ta fice da sauri sauri cikin tsoro ta nufi cikin gidan

Dakin Ummi ta shige

Tana mai sauqe ajiyar hrt

A hankali ta fada kan gado

Ganin ba kowa a dakin yasa taji tsoro ya kamata

Cikin tunanin.

Tana zubda qollah

Dan tabbas Hamma Yusuf

Ya bata tausayi

Hamma Yusuf ne

Harda 

Kuka mutumin

Da kukansa ke 

Da tsada

Mutum mai

Dauriya 

Da jarumta

Gashi har 

Kuka yake 

Da hawaye tamkar

Yaro,


Shi kuma

Binta yayi

A baya 

Yana 

A,ish

Ki dawo

Dare yayifa

A parlon ya tsaya ganin

Gudunshi takeyi

Durqu shewa yayi

Kan carpet

Ya rinqa

Rawan sanyi

Lips inshi Sai

Bari suke

Har haqoranshi

Na bugar juna, Sai Hahhhhhh huuuum shiiihhh ahhyshihhh ykeyi

Duk tsikar 

Jikinsa ta mimmiqe

Kanshi Sai 

Sarawa yake

Gau gau

Lkci

Daya zazzabi

Mai zafi

Ya rufeshi

Mararsa ta rinqa tsikararsa

Ba abinda yake

Sai.

Surutai

Duk da iskar damina dake kadawa

Ga walqiya

Amman Sai zufa ke ketomai

A fili

Yake 

Cewa

Aysha 

Meyasa,

meyasa

Kika gujeni

A lkcin

Da nake da buqatarki

Ya zaki gujeni a lkcin

Da kika, zama 

Jinin jika

Cikin rawan murya yace

Bazan iya

Haquri ba,

Cikin wahala

Ya yunqura,

Ya gyara 

Daurin.

Towel din jikinshi

Fita yayi

Cikin sanyi yake 

Takawa har

Ya isa

Cikin parlon.

Ummi shiru ba kowa

Ga duhu 

Sai Dan haske,

A can cikin bedroom

Dinta

A ranshi

Yake tunanin

Ummi kam dai bata kwana dakinta

Sai dai Allah.

Yasa

Anuty Sadiya 

Bata dakin'


Cikin zulimi 

Ya tura 

Qofar a hankali ya shigo

Can ya hanqota kwance

Cikin blanket

Ta jawo pillows ta

Tura kanta a ciki

Wai duk" 

Kar taji tsawa kar taga walqiya.

Jikin window

Yaje ya bude. Window

Ya tartare labulayen

Iska ta rinqa

Busowa

Lkci daya.

Kuma Ruwa ya 

Fara sauqa

Cikin sanyi

Ruwane mai qarfi

Sai dai a hankali yake 

Sauqa.

Ba abin da ake yi Sai walqiya,

Da iska mai sanyi

Sai sauqan ruwa.shuuuuu shuuuuu"

 a hankali. Ya qarisa.

Kan gadon

Zama yayi.

Cikin rawan hannu

Ya janye blanket din

Ya ture 

Pillows din.

Lkci.

Daya kuma.

Aka saki wata walqiya.

Mai haske gske.

Sai tsawa kuma ta biyo.

Bayan walqiyar.

Tsoron ya hadun mata

Cikin,

Firgita ta bude.

Idan ganin.shine 

Yasa tai saurin.tashi tana jaa.da baya

Hannuta, ya jawo

Ya fizgota jikinshi "

Matseta yayi da qarfi,

Tare da sauqe ajiyar hrt.

Cikin.

Daqilewar 

Murya,

Yace INA zakije'

Meyasa kike gudana

Mesa bakya tausaya min'

Kinfi son Na cutune.

Kai ta rinqa kadawa'

Tana ni banson

Ka sakeni,

Qara matseta yayi

Ya tallabo kanta

Lips Dinta

Ya laluba ya rinqa

Tsotsa cikin nauyin zuciya'

Hannushi kuma.yasa ya zare hijabin

Tureta yayi

Kan pillows ya kontar da ita

Cikin rawan jiki'

Ya haura kanta,

Hannushi yasa ya ware

Nata ya dannesu

Kanshi ya, daura kan

Qirjinta.bres Dinta ya cabke ya rinqa tsotsa kamar cikin 

Gigita" ita kam tuni ta nemi idanta, da bakinta kuka takeyi

Sosai tana

Wayyo Allah Na 

Wlh bana so ka barni mugu kawai "

Bai 

Kulata ba Dan hankalinshi bai jikinshi

Da qarfi ta yunquro jin ya taqwara qafafunta ya waresu ya shige tsakiyar cinyarta yana cishirin shigarta  riqe hannushi tayi duka biyu'

Cikin kidima da tsoro da zare ido

Tace,

Wayyo Allah

Wayyo Hamma Yusuf Dan Allah da 

Manxonsa ka barni

Kayi haquri plxxx,

Na tuba

Hamma Yusuf ka tausaya min


Cikin kidima da rawan jiki da carkewar murya.

Yakai bakinshi dai dai kunneta

Cikin sarkeqar murya.

Yace 

Bazan iyaba ki tausaya min

Kiyi haquri ki nitsuba karkiyi naji miki ciwo

Plxxx A,ish

Ki nitsuba bazan wahal dakeba

Kiyimin agaji 

Hannuta tasa tana ture qirjinshi

Tana ,a,a. Dan Allah

Hamma ka tausaya min 

Qara sake nauyin qirjinshi yayi kan nata.

 cikin 

Karkarwa ya  ya matso da bakinshi kan kunneta a kideme yake

Furta mata Addu,arga.

(بسم الله الله‍م خنبنا الشيطاب وجنب الشيطان مارزقتنا)

Cikin 

Kuka sosai take cewa a,a 

,a,a Hamma Yusuf.


Yusuf kam ya rikece ya fita haytacinsa baiji bai gani

Shiyasa bai 

Jinta bare ya tausaya mata,


Allah sarki

Aysha azabar da take ratsata tasa ta

Cillah qara mai qarfi 

Cikin damqe damtsen hannushi

Cikin kuka sosai

Tana 

Wayyohhhh 

Hamma Yusuffffffffff

Zan mutu

Hamma Yusuffffffffff ka kasheniiihhh

Zafi zan mutu

Shima 

Yusuf

Kuka yakeyi tamkar yaro

Kuka yake cikin 

Fitar hayyaci

A haka ya rinqa 

Haqarta har saida 

Ya maidata cikekkiyar 

Mace,

Qara ta saki 

Cikin qaqameshi

Ta tura kanta cikin qirjinshi

Hannayenshi ta qaqqame

Shi kuwa 

Yusuf

Cikin

Shiga wota sabuwar

Rayuwa da duniya

Jinshi yake a sama

Ya kasa gane wanne hali yake ciki

Cikin kuka

Ya zurma cikin duniyar ma,aurata 

Ya kamo  tamkar zaucecce

Ya rinqa zuba mata 

Kirari yana

Aysha kece mace daya tamkar da dubu

Kece Farin cikina kece rayuwata

Kin kasance bugun zuciya ta

In bakya tare dani cutuwa nakeyi kece kadai mai iya sani nishadi kin canzamin rayuwa kin jiyar dani dadin da ban taba jiba kece mai iya kawarmin da qishinahh"

Ita kuma 

Aysha 

Tuni ta fara

Dauke wuta

Wasa wasa 

Yusuf

Ya kasa control

Din kanshi

Ita kam kuka take har muryar ta ta dashi.

Cikin lkci

Daya 

Numfashi ta ya fara 

Carkewa


Shiko bai bartaba har saida ya samu.

Cikekkiyar gamsuwa

Lkcin daya

Ta sauqi wani nannauyan numfashi

Shi kuwa 

Da garfi ya cakumota ya ruqqumota

Cikin kuka sosai

Ya zame 

Jikinshi

Ya tallabota ya daura ta

Kan qirjinshi

Cikin

Kukan 

Yake 

Fadin

Aysha 

Ngd 

Aysha kin gama min

Komai Aysha kinmi

Kyautar abinda yafi komai tsada a gareki

A,ish 

Me zan miki a duniya Na biyaki

A,ish 

Kin gama da zuciya ta

Yau kinsani cikin

Farin ciki

Kin gama min komai a rayuwa

Hannushi daya ya daura kan bres Dinta yana shafawa yana sauqe ajiyar hrt gamida cewa 

Allah ya miki albarka

Ita ko Aysha sai

Wani irin kuka take mai tsuma zuciyar mai sauraro

Gaba daya jikinta ya sake ko yatsarta bata 

iya motsawa

Dan muryar ta ma kab ya bace

Dan ta gama 

Wahala

Lkci

Daya zazzabi mai zafi

Ya rufeta

Sai rawan sanyi

Takeyi

Shima Yusuf tuni

Zazzabin ya rufeshi

Sai rawan sanyi yakeyi

Cikin 

Rawan sanyin 

Ya yunquro ya Dan qyara mata konciya

Tashi yayi cikin

Rufewan ido

Ya daura towel

Din a jikinshi

A hankali ya rinqa dafe 

Gini ya fta ya nufi part dinsu

Dan jin

Ana kiran sallah

Gashi dagashi Sai towel

Gashi duk jikinshi ya baci

Kunya yakeji kar 

Ummi tazo ta sameshi a dakin shiyasa ya fice da shirin

Yaje yayi wonka

Ya Sa kaya ya dawo

Ya gyara yar matarsa

Amman INA yana zuwa dakin

Jiri ya fara dibarsa 

Da gyer yayi wonka yana fita

Ya kasa tsayuwa

Gaba daya Sai rawan sanyi yakeyi,

Dole ko sallah

A dakin yayi yana idarwa

Ya zame kan carpet din ya konta

Zazzabi ko yace 

Bismillah

Sai 

 Jiri

Yanaji yana gani

Ya kasa tashi

So yake ya ganshi gashi ga 

Habittin shi ya bata kulawa

Ya ruqqumeta taji dumin jikinshi

Amman ya kasa"


Ita 

Kuwa

Tana jin matsishi

Yabar dakin

Ta sake wani sabon

Kuka

So take ta tashi

Amman ta kasa

Shiyasa ta koma ta yi lub

Tana mai kukan azaba da wahala.


Ummi kuwa

Tana tashi

Ta sauqi qasa

Dakinta ta shiga

Cikin

Sanyi ta matsota

Kan Aysha.

A hankali tace

Aysha, 

Ke Aysha

Tashi kiyi sallah

Yau kuma kin makara ko,?

Rufe idanta tayi

Cikin azaba da kunya

Taci gaba da 

Kuka

Ummi bata jin kukan samida muryar ta ta dashe

Har ta juya zata tafi

Ta kuma dawowa tana

Aysha ki tashi fa kar nasake  zuwa baki tashiba

Zata juya

Aysha ta daqo hannuta cikin wahala ta riqo

Hannuta

Sai kuma kawai ta fashe da kuka

Da sauri ta sunkuyo kanta

Cikin mmk da tsoro

Tace Aysha meke faruwa

Meke miki ciwo

Ita dai Sai kuka

Jan hannu nata tayi cikin cewa tashi ki shirya mu tafi asbiti

Da qarfi ta saki qara 

Tana wayyo Ummi bazan 

Iyaba

Cakin mmk ta kalli inda ta Dan janye tan jinine gaba daya a wurin

Lkci daya

Ta gano halin da yartata ke ciki,

Cikin

Bacin rai

Tace

Yanxu 

Fisabilillahi

Wannan wanne irin rashin

Imanine da tausayi

Komawa tai ta kamata ta jingibar da ita jikin gadon

Towel ta dauko mata 

Cikin tausaya mata

Allah sarki Ummi harda

Qolloarta Dan ta tausaya mata sosai

Miqa mata tayi ta shige toilet

Ta hada mata ruwan zafi

Ta fito 

Ta tallabeta suka shiga

Ita ta taimaka mata

Ta gasamata jikinta

Sannan tai wonka

Suna fita ta taimaka mata ta ziramata dogon riga.

Tea ta hada mata 

Ta kawo mata bayan tayi sallah

Kuma duk abinda take idanta a rufe yake

Sai qollah dake bin gefen idon

Sai tai

Dan qara tace

Ummi bazan iyaba komai ba

Ummi qafafuna

Cikin rarrashi

Tace kisha tea Aysha

Zamu tafi asbiti

Kinji ko


Da gyer tasha tea din kurba 3

Tace amai takeji

Ummi kam duk ta ji tsoron yadda take rawan sanyin

Usman ta qira yazo ya kaisu 

Asbiti

Bayan sun ga shiryawa wa

Sadiya takuma kira suzo su tafi tare

Su biyu suka tallabeta suka fito da ita

A parlon

Sukaci karo

Da Usman cikin

Tsoro da tausayi ya matsota yana

Sister me ya sameki Ummi mene ya sameta

Cikin

Dan badda abin Sadiya tace

Ba komai jirine ke damunta


Shiko Yusuf sai yanxu

Jirin ya Dan sauqa Sai dai zazzabi kam nanan daram

Ga ciwon kai

Miqewa yayi da gyer ya shirya cikin

Riga da wondo farare tas 

Turare kawai ya Dan pesa ya nufi part din umminshi cikin dauriya Dan kanshi kamar zai dare,


         A dai dai lkcin

Da ya shiga a lkcin

Aysha dake hannu Ummi 

Tai luuu da jiki  ta sake a jikin ummin gaba daya suka nemi faduwa 

A tsorice 

Ummi ta riqota tana jijjiga

Ganta tana Aysha 

Aysha bude idan ki

Shiko

 da sauri


Ya qarisa gunsu cikin 

Sunkuyar da kai gwayar ido a boye

Ya tallabota jikinshi

A hankali Ummi ta zame ta matsa gefe.


Shiko, cikin sanyi yake

Kiranta A,ish 

Amman INA 

Sai qara sakewa tayi a jikinshi lkci

Daya tai luu da ido

A tsorice

Usman yace

Hamma Yusuf ta sumafa sumatayi

Ummi ma matsota tayi cikin tsoro tana Aysha 

Bude idanki

Duk sun rude

Shiko 

Yusuf

Cikin far gaba ya qara tallabota

Ya ronqofo ya zauna

Gami da jingina da jikin

Kujera

Hannushi yasa tallabo kanta 

Cikin kula ya rinqa Dan juya kanta 

Yana Aish

Ki bude idanki

Ki tashi 

Karkiyi min haka

Am so sorry my Habitti

Sadiyace ta debo ruwa da sauri tazo tana gashi Yusuf ka yayyafa mata

Ummi 

Kuwa hatsala tayi tana

Ai 

Rashin imani  ne wannan da qarfi hali

Ka bamu yarinya mu tafi asbiti ka tsaya sakarci


Sarai yasan Ummi haushinsa takeji

Shiyasa cikin

Boye idanshi ya sunkuyo

Bakinshi ya manna 

Kan hancinta ya rinqa

Bata numfashi Sa har zuwa Dan wani lkci

A hankali 

Ta Dan yunquro cikin

Dan tari da kuka

Tana

Wayyo Hamma Yusuf

Dan Allah kayi haquri

Na tuba 

Ita kam Ummi juyawa tayi ta fita

Shiko 

Usman ganin kallon da Yusuf yamai 

Ya sashi 

fita yana

Ni ba ruwana bare a harareni

Cikin 

Sanyi

Ya qara mannata jikinshi

Gami da qara jingina da kujera

Cikin sanyi

Yace 

Anuty Sadiya

A Dan hada min ruwan zafi

Toh tace gamida 

Juyawa tayi 

Kitchen

Itako. Aysha 

Kai ta dago 

Murya Na rawa tace

Dan Allah Hamma Yusuf kayi haquri

Hannushi yasa cikin taushi ya share mata qollah

Cikin ajiyar hrt ya 

Manna bakinshi.............



By garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI WASMITI* page 1⃣0⃣7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


```Kuyi haquri masu karatu

Kunji ni shiru Na tsawon 

4 days

Wlh biki mukeyi Amman yanxu insha Allah zamu miqe har qarshe

Dan Allah masu Nina ta prvt Kuyi haquri wlh abinne yamin yawa bazan iya binku daya daya ba in tura muku ta prvt dinba Ku rinqa binmu ta group

Wlh baa wulaqanci bane```



Cikin riqarta ya rinqa shafa 

Cikinta

Yana sauqe ajiyar hrt 

Tuqi yake Amman gaba daya hankali shi bai kan titin.

Ido ya tsura mata cikin

Raunin murya

Yace ' Aysha 

Menayi miki haka mai tsanani

Da kika kasa yafemin

Hannuta ya kuma kamowa ya matse 

Cikin taushi ya jawota jikinshi

Yaci gaba

Da cewa ' Dan Allah 

Ki tausaya min 

Wlh bazan iya jumre rashinki a kusa daniba

Plxxx ki kijiqaina.


"Ita kuwa tureshi takeyi tana janye

Jikinta daga gareshi

Tana ' Ni ka sakarmin hannu kuma ka maidani 

Gida.


Sake hannun nata yayi 

Yaci gaba da tuqi

Ba tare da yace

Mata komai ba

Tafiya suke cikin

Dajin 

Gembu Wanda duk Wanda yasan

Gun yasan hanyace

Mai cike da tsaunuka da tsirrei

Da qoramai masu 

Gudana 

Qa sanyi dake ratsa illahirin

Wurin sanyi ne sosai ta yedda daga nesa zaka hanqo tamkar 

Hayaqi ke tashi

Sanyin ya hadu da sanyin 

A,C 

Ga qamshi dake ratsa su Na furrai

Da turaren jikinsu

Lkci 

Daya nishad'i

Ya rinqa ratsa zuciyar Yusuf

Tuqi yake Amman idanshi a lumshe Sai sauqe ajiyar hrt

Yake 

Yana murza siteri

Tuqin yake cikin qworewa da haddace hanyar


Ita kuwa Aysha ido

Ta tsura mai ganin yadda yake tuqi ido a rufe

Sosai Hamma Yusuf yacika duk inda 

Namiji yake kaiwa 

Tabbas Hamma Yusuf da banne a cikin maza

Haka take ta rayawa a ranta 

Tsajenshi ta kuma tsurawa ido

Yayi luf gwanin Sha,awa

Lkci 

Daya kuma ta saki

Qara gamida

Bubbuga cinyarsa ganin

Motar tayi

Cikin

Tsaunuka

Tana

'Hamma Yusuf

Kana tuqi kana baci

Dan Allah ka bude idanka

So kake ka kasheni ne


" bai kulata ba bai kuma bude idon ba

Shiyasa ta qara qwagumo shi

Tana

'Wayyo Hamma Yusuf

Ni ka sauqe ni

Dama ka d'auko ni ne Dan ka karni.


A hankali ya bude idanshi

Ya Sa hannu ya qara jawota jikinshi

Yasa hannu daya kuma yana tuqi

Kanta ya daura kan kafadarshi

Hannuta kuwa

Ya danna tsakiyar cinyarsa

A tare suka sauqe ajiyar hrt

Ita Na tsoro ne Dan har ga Allah

Yanxu tsoron sa takeji

Bare data ji

Inda ya tura hannunta

Shi kuwa

Wani irin sanyi yaji

Da 

Shauqi 

Shi yasa shi

Ajiyar hrt

Hannushi

Ya tura cikin

Qirjinta

Yana son

Lalubo

Bres Dinta

Amman yar rigarta ta hanashi sakewa

Lumshe idansa  yayi cikin

Isa yace

'Ki cire rigar nan

Ido ta zare cikin

Tsoro tace

Hamma Yusuf

A cikin

Motofa

Tuqifa kakeyi.


' Ehh

Na sani ya bata amsa cikin

Rawar murya

Yaci gaba da cewa

' So nake Na samu

Nitsuwa

Hankalina

Bazai dawo jikina ba har Sai

Na samu abinda ke damuna

Ya zanyi

Aysha

Dole fa ki zama jaruma

Ki cire tsoron nan

Dan in ba hakaba

Wlh zan iya fadawa wani hali


"Janye jikinta take

Sonyi

Tana mai zubda qollah

Tace

' Dan Allah

Kayi haquri

Hamma na

Wlh

Tsoro nakeji

Gashi

Mun fara shiga gari ma

Yanxu kam.


Ido ya Dan daqo

Ya tsurawa garin. 

Cikin

Sanyi

Yace 

Har mun isa

*Mai Samari*

Ita kam samun ya Dan saketa yasa ta janye ta gyara zaman ta

Ta tsurawa titin

Ido.


Ana kiraye kirayen

Maqqariba 

Suka 

Isa cikin

Birnin

 *Mambila*

Kai tsaye ya wuce

Family house dinsu

Bappi mai gadi ya bude musu

gate cikin

Zumu d'in ganin

Yusuf 

Dan

Yusuf tamkar

Hadari yake

Daya iso

Zasu samu

Kyautar sanyi


Yana parking

Ya fito

Cikin

Bude hanna yenshi

Yana mai shaqar iskar garin dayafi so fiye da ko ina

A ransa

Yanayin qarin Na tunzura

Yanayin halittar da rabbi yayi mai

Kye

Ya miqawa bappi

Cikin sanyi yace

Bude but

Ka shigar da kayayyakin

Karba yayi cikin Dan Fara,a 

Yace

' can part dinki

Zan kai ko?

Ba tare daya kalleshi ba yace 

'a a dakin 

Innayi zaka kai.

An gama yace cikin

Sauri ya fara kwasa


" itako Aysha tin tuni

Take on

Fita yaqi bude mata

Qofar Sai yanxu ya Dan zagayo

Ya bude

Qofar

Cikin

Yin piki piki da ido

Ya Dan nuna mata hannu alamar ta fito

Daya hannu kuma ya nuna mata qofar.

Cikin

Mmk

Irin wasu lamura Na Hamma Yusuf din nata ta zuro qafarta

Tana mai kallon shi

Har ta miqe

Shi ma idon

Ya tsura mata

Gami da qara matsota cikin

Rada

Yace

'Yadai

Kike ta kallona?

Na canxa ne?

Ko dai

Kema kewata ke damunku?

Da sauri tai qasa

Da Idon'ta

Shiko

Kamata yayi

Ya manna ta a qirjinshi

Cikin Shauqi

Yace

Kewarki ta kusa zautar dani

Na kusa macewa

Kin firgitani wlh

Banson

Kiyi nesa dani

Shiyasa Na kawoki nan

Dagani sake

Masu gidan sunyi tfya.

Janye jikinta tayi cikin

Mmk da tsoro

Ta nufi cikin

Gidan.


"Shiko Yusuf

Phone dinshi ya zaro ya kira ta

Baba bello ya sheida mai sunxo

Amman su Bappa Yaya ba sannan Dan haka karsuce zasu zo

Yana katse kiran ya kuma kira

Ahmad

Cikin

Dan fara,a

Yace '

B'iyaye

Mun isa lfy

Lau

 Dry shima Ahmad din yayi cikin

Tsokana yace

Ka sacemin

Qanwata ka bar Ummi nata fada

Sannan ka hana

Usman zuwa Dan qarfin

Hali

Fuska ya Dan yamutsa yaci

Gaba da cewa

' Ahmad

Wlh Ummi bata San halin da nake cikiba

Shi kuwa Usman

Shi yawone kawai ke cinsa

Yafi son yazo

Ya tare cikin

Labbun nan

Yayi ta tsinke fruits

Kamar wani biri.


Adam ne dake gefe ya karbe woyar cikin

Tsiya yace

' wlh andaiji

Kunya

Abu ya koma harda sace yar mutane

Ni dai fatana kar ka cinyemin qanwata

Yar marainiya.


Tsaki yaja cikin

Hada fuska

Yace kai

Ka cinyemin tawa qanwar

Da Allah can da Sa idonka

Ni banson masi

Katse kiran yayi

Ya nufi masallaci

Bayan yayi Alwala

Su kuwa Ahmad

Dryar Yusuf

Suka rinqa yi.


" ita kuwa Aysha

Tana shiga gidan ta rinqa mmk

Ganin da gske

Ba kowa a part din kakannin

Nasu

Sosai

Take jin tsoron

Hamma Yusuf din

Parlon ta zubawa ido

Komai nan tsaf gwanin

Sha,awa

Labulayen duk a sassake

Ga komai a shirye hatta kan dinning table

Komai tsaf

Ba wani haske sosai

Sai hasken

Cikin show glass

Sai sanyin A,C da Na yanayin garin daketa kadawa

Parlon Sai qamshi yake

Dan shi Bappa Yaya ko

Qiftawa yayi ta wurin Sai ya Dade yana qamshi bare inda yake rayuwa

A hankali ta zame gyelenta

Ta ja 

Trolley ta.

 tashigar

Cikin dakin innayi

Toilet

Ta shige 

Shawa ta sakarwa kanta

Har Na tsawon wani lkci

Sanyin garin

Da sanyin ruwan suka sauqe mata da nishadi

Cikin rausayawa ta rinqa murza sabulu mai qamshi 

A jikinta

Bayan tayi brush

Ta yi alwala

Ta fito daure a Towel

Zani ta zare ta daura

Gamida Sa hijabin

Ta tada kabbara

Tayi magga riba

Bayan ta idar ta dauko

Qur,ani

Tai ta karatu

Har aka kira ishah

Ta kuma miqewa tayi ishahn

Tanaidarwa tai shafa,I

Da witiri

Sannan ta ninke abin sallar

Gaban 

Mirror ta zauna

Ta jawo Jakarta

Ta rinqa murza mai a tattausar fararta

Sannan

Ta fidda humranta 

Ta bi jikinta dashi

Ta kuma dauko

Lovilia ta shafeshi a jikinta

Miqewa tayi ta zabo

Wasu tattausan

Kayan bacci

Rigace da Dan wondo

Farare tas Sai Dan ratsin

Yellow yellow a jikinsu

Wondon guntu ne iya karsa guiwarta

Sai yar rigar wacce iya karta

Ququnta

Daga samanta kadan 

Kadan kuma

Ta danyi shara shara hannuta kuma ragace

Gaban mirror ta koma dasu ta dauko

Turaren

Lailatu sahara

Ta feshesu tsaf

Sannan ta sakasu

Ta dauko

Hula 

Yellow ta murxa a kanta sannan

Ta dauko phone Dinta

Ta nufi 

Kitchen tana

Zuwa

Fridge

Ta bude

Tako yi Sa,a akwai

Abinda take mararin

Nono ta dauko mai sanyi

Ta burgeshi

Ta sanya sugar

Sannan

Ta Debi

Fruits

A pilet

Parlon ta dawo

Ta zauna kan 3 str

TV ta kunna

Ta koma ta zauna

Cikin sanyi da Dan jin

Tsoro

Ganin yadda labulayen ke kadawa alamar hadari

Na tasowa

Can dai taji

Iskar ta qaru sosai

Tashi tay cikin

Sauri

Ta rufe

Windows din

Lkci

Daya.kuma

Walqiya ta fara haskawa

Cikin

Tsoro ta koma

Jikin kujera ta da

Zauna


" Shi kuwa 

Yusuf

Ganin hadarin

Yasa shi

Fitowa

Gidan

Baba Ahamdu

Da sauri

Ya shige mota

Kai tsaye

```Jam baddu

Restaurant```

Ya wuce

Gudu gudu

Ya seyomusi abinda zasu

Dan ci da juices masu sanyi


Bai zame ko inaba Sai

Gida

Hadarin kuwa kamar

Jiransa yake

Yana parking

Ruwa ya kece kamar da bakin

Qorya

Fita yayi

Cikin tattara ledodin

Ya nufi

Bakin qofar

Cikin ruwan

Tuni ya jiqe carkab


Yana zuwa ya tura

Qofar ya shige

Cikin

Sauri

Yana

'Amrita

Ina kike

Ita kuwa Dan ganinshi da tayi Sai ta danji

Sauqin tsoron


Shi kuwa ganin ta share shi yasa shi

Wucewa gefen ta ya ajiye

Kayan hannushi

A ranshi kuwa yana

Oh kinji ba tsawa kenan

Toh Allah ya Sa ai tsawan


Tsayuwa yayi a gabanta

Cikin

Isa

Yana

'Ke baki iya cewa mutum barka da dawowa ba ko?

Bata kulashi ba Sai hararanshi da ta danyi qasa qasa


"Shi kuwa rigar jikinsa da ta jiqe ya cire ya cillata gefe

Ya kuma zame dogon wondon jikinsa

Sannan ya cire yar bes

Dinshi ya cillar gefe

Ya rege daga shi Sai

Bkss

Cikin sanyi

Yace ke 


" daqo idanta tayi

Ta kalleshi

Sai ta kuma

Saurin kife

Kanta jiki

Kujera

Jikinta har rawa yake

Ganinshi haka ya bata tsoro sosai

Shi kuwa

Zama yayi a gefen ta

Cikin

Qara matsota........


*By garkuwan Fulani*

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣0⃣6⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

Bakinshi 

Ya manna kan 

Kunneta cikin 

Sanyin murya yace

A,ish kiyi shiru

Kinji Na barki

Bazan kuma abin da zai cutarda keba kinji

Kiyi haquri kinji

My dear sis.

Shiru tayi cikin jin kun yarshi

Ta manna. Kanta kan qirjinshi

Hannu yasa ya ruqumota da kyau

Ya jingina jikin kujera 

Ajiyar zuciya ya rinqa sauqewa

Ido ya lumshe

Cikin manna mata kiss

A goshinta

Can kuma

Idon ya Dan bude cikin yamutsa fuska

Jin Shigowar su Adam

Da Ahmad

Dan Sam baison abinda zai takura Mashi Amritanshi.


Adam ne ya Dan kalleshi a fakaice

Ya kuma juyawa ya kalli Ahmad da ido ya nunawa Ahmad Aysha dake lafe cikin qirjin Yusuf din

Ya tabe baki

Ya miqawa Ahmad hannu suka tapa

Suka Dan kwashe da dry

Adam yace

Yusuf meke damunku?

Cikin harara yace ciwon so ke mana dadi

Ahmad ne yace 

Toh fa 

Wato ciwon so ke muku dadi

Sai suka kuma.dry 

Kai ya juyo cikin kallon

Ahmad a nitse 

Yana 

Biyaye harda kai

Wato wannan Yaya Na zauren ya koyama 

Sa ido

Dry Ahmad yayi cikin salonsa Na sanyin rayuwa da yanayi

Yace a a biyaye bance komaiba 

Fatana asha ciwon so lfy 

Haka dai sukayi tayiwa juna tsiya

Can.

Maryam da Usman dasu Rabi,u

Suka shigo a tare

Gaba daya kallon mmk suka tsaya yiwa Yusuf

Rabi,u ya kalleshi a fakaice gudun masifa

Ya kuma yafito Usman ya daga mai gira 

Aiko suka kasa tsare mmkinsu

Rabi,u

Ne Dan Neman mgn

Ya kalli inda suke cikin

Daga murya

Yace 

Ke Aysha tashi ki ban phone

Dina

Usman ko dry CE ta kofce mai

Shiko oga Yusuf kai ya dago fuska a murtuqe ya watsa musu mugun kallo 

Tuni Usman kam ya fice

Shiko Rabi,u matsawa ya danyi cikin hada fuska yace

Ni phone na

zata bani

Zan tafi school

Ne .

Bazata bayarba ya bashi amsa a kufule

Juyawa yayi  ya fita cikin kunquni


Haka ya maqaleta a parlon ko a jikinshi 

In Ummi tazo wucewa Sai ya kauda kanshi

Har dai zuwa Dan wani lkci 

Bacci ya debeshi

Ganin haka su Ahmad suka fice 

Suna dry.


Suna baccin Nenne ta shigo ta samesu ruqqume da juna

Klsu tayi cikin dry ta wuce kitchen gun Ummi.

Cikin fara,a 

Tace Ummi yau kuma baccin a parlon ki za,ayishi kenan

Tabe fuska tayi cikin takaici 

Tace yaro Sam 

Bayajin kunyar mutane yazo ya tare min a parlon

Bayan ya yiwa yarinya mugunta sannan ya tsare kar a kaita Asbiti

Dry Nenne tayi cikin sanyin tace ki bawa yaro matarsa sunyi komawarsu

Can su gama magale juna baki gansuba bare kice rashin kunya ce

Itama dry ta danyi sukaci gaba da aikin,


Basu farkaba sai da sukayi baccin 2 hours

Sannan Aysha ta Dan

Juya cikin sauri shima ya bude ido

Da sauri ya tallabeta 

Ya tallabo fuskarta ya tsura mata ido cikin ido

Murya a narke yace

I love you Amrita 

Kiyi haquri banson wahal dakeba Na kasa control din kai nane 

Baki ta Dan tura cikin kauda kai

Qara manneta yayi ya daura bakinshi kan kunneta cikin shauqi

Yace 

Kiyi haquri

Ki yafewa Hamma Yusuf dinki.

Kafada ta maqale alamar a,a 

Qara manna qirjinshi yayi kan nata

Cikin rada

Yace bafa laifina bane

Laifinki ne

Kai ta dago cikin alamun tabbata

Ta kalleshi

Gira ya daga mata

Gamida cewa

Ehh laifinki ne 

Dan ke kika gigitani

Kika haukatani

Ke kika jiyar dani abinda ban taba jiba

Kedin ta dabance

Ke dole en kasa sarrafa kaina Dan kedin ta dabance

Qara goga qirjinta yayi a nashi cikin sanyin yace

Aysha  kina da dadin da bazan iya zama da qishinkiba plss karkiyi nesa dani

Hannushi ya Dan kuma turawa cikin qirjinta

Ya shafo bres

Dinta cikin ajiyar hrt da lumshe ido

Yace 

Wlh a duniya bayan qur,ani

Ba abinda nake begen rigewa kamar wannan

Ba abinda zan taba naji dadi da sanyi a raina da rayuwata da ruhina Aysha sai bres dinki

Wlh hannuna qaiqayi yake min in ban shafesuba

Bakina nauyi yake min, in ban tsotsesuba.

Ya qarishe mgnar yana qoqarin

Tura kanshi cikin qirjinta

Da sauri.ta tallabo kanshi

Ido cike da qollah 

Tace 

Plss Hamma Yusuf Na tuba Dan Allah kayi haquri

Wlh bazan iyaba

Ciwo jikina.

Kai ya karya kamar marigayin zakara

Cikin sakewar jiki yace

Sai anjima 

Nazo ko?

Kai ta sunkuyar cikin yuqqurin miqewa

Sai kuma ta saki Dan

Qara

Da sauri ya miqe kamata yayi

Cikin rawan jiki

Yana

Ohh sorry Amrita

Hamma Yusuf dinnan bai kyau ta ba 

Sunkuceta yayi

Sai dakin 

Ummi

Kan gado

Ya direta 

Kiss ya manna mata a goshi

Cikin juya ido

Yace wlh zanyi miss

Dinki

Dan Allah kixo

Ki kwana da mijinki

Kinji dumina inji duminki.

Toh kawai tacema

Dan ta rabu dashi

Cikin salon Sha,awa yace

Ki rinqa shiga ruwan zafi a kai akai

Bari yanxu Na kawo miki mgnin

Toh ta kuma cemai duk idanta a rufe Dan kunyar shi da tsoron shi takeji.

Har ya juya zai fita ya kuma dawo

Hannushi ya tura cikin

Bres Dinta ya cabkosu

Da Dan qarfi

Yace

Wayyohhhh

Shehhhhhhhshh

Ham

Ya sauqe ajiyar zuciya ya fita

Yana ki matso da moyarki kinji

Noor hayat dina

Kai kawai ta gyeda mai

Dan gsky salon Hamma Yusuf salone mai tsadar gske


Yana fita ya hado mata magunguna da tek awy

Ga wasu kaji gasassu Sai qamshi suke

Sai madara mai sanyi

Da lodin inibi da su Apple mai sanyin gske.

Sai wasu qattin boruna sukuwa ya cikasu tab da English wes da sleeping dress masu taushi da santsi da tsulbi

Sai sweets lace da at ampopi masu kyawun gske

Sai yan kunne da sarqa da abin hannu da zobe 

Na zinari Sai sheqi da gyelli sukeyi ga kye din dalleliyar motarta mai tsadar gske

Turaruka kuwa ba,a mgn

Duk ya hadesu.


A parlon ya samu Anuty Sadiya

 Cikin Dan fara,a ta karbe kayayyakin ta shishigar

Tana Yusuf wannan kaya haka Na mene? 

Fuska

A sunkuye yace

Anuty Na Aysha ne

Tayi baccinne ?

Ehh tace mai 

Tana mai zubawa kayyakin ido

Shi kuwa dakin ya shige ya Dan shafo fuskarta cikin

Sanyi ya tallabota

Magunguna

Ya Dan tura mata a baki ya balli Goran 

FARO

Ya bata 

Duk abinda yakeyi tanaji

Sai ta qara lumshe ido

Yana gamawa ya gyara mata 

Blanket din 

Ya fice cikin kewarta


A dakinshi. Wonka yayi ya zo ya kwanta Sai murmushi yake yana.

 Alhamdulillah

Sam bacci ya kasa daukarsa ba abinda yake tunawa Sai Daren jiya

Haka yayi ta juyi

Sam ya kasa samun nitsuwa

Dole yajawo phone dinshi

Ya rinqa kira bata dagawa

Gashi baison yaje kar aga zalamarsa

Wurin text ya shiga

A rayuwarsa shi bai taba dadara kanshi baifa bata lkci yayi wasu kalaman wai so ya turawa kowaba

Amman gashi yau ya zauce Sai Zan tuka yake zubawa.

Da gyer dai ya samu barawo bacci ya saceshi.



Su kuwa a parlon Ummi

Gaba daya sun cika da mmk

Irin yadda. Hamma Yusuf dai

Ya tsaya da kanshi ya tarkatowa Aysha irin wadannan abubuwan da yake fadin shi yafi qarfin ya solance a gun mace

Rabi,u kuwa tsakaninshi da Allah yake fada yana

Wlh nima dolene fa dolema kawai a Samar min moto

Inba hakaba ayi bala,i haka kawai.ace Aysha ma najan motarta ni INA zare ido

Ga Usman dai ya Ahmad ya bashi

Abdul kuwa baba ya saya mai wato ni kam soko ko.

Dry sosai suka rinqa yiwa Rabi,u

Usman ko cewa yayi sunyi canjin moto

Itako Aysha sai binsu da ido takeyi

Saida  Ummi tazo ta koresu tukun

Ta Sam tayi baccinta Anuty Sadiya kuwa ta dage Sai hade mata kayan gyara takeyi.


Kashe gari da sassafe Yusuf yxo

A parlon ya samu Ummi

Bayan ya gaidata ya miqe ya nufi cikin

Dakin.

Da sauri

Cikin hada fuska

Ummi ta dakatar dashi

Cikin cewa

Kai dawo nan

Ina zakaje

Wai shin kai bakada tausayi ne

Nacema tana bacci

 tada ita zakayi kenan?

Kai ya jinjina a Lamar a,a 

Fuska a hade tace

Toh wlh ka kiyayeni

Kar Na qara ganin qafarka a nan

Kabarta taji dacutarta.

Kana jiko?

A Dan tsorice

Yace humm

Ummi dama mgnin

Zan bata

Kuma wai zan dubatane.

Tabe baki tayi cikin yatsine tace gashi

Ni ban iya bada mgnin ba ko?

A a yace 

Cikin sanyi yace ayyah

Ummi Dan Allah bari Na Duba jikin nata.

Bazaka Duba ba wlh ka fice kawai

Ta bashi amsa a fusashe

Shiko gaba daya ya gama cika

Haka ya juya a dole

Ya fita

Yana fita

Ya kirata har 

Kusan sau 8

Bata daga ba

A parlon su

Ya zauna

Cikin damuwa ya rubuta mata text

Kamar haka.


``` Assalamu alaiki

Ya sahibul qalbi

Fatan kin tashi

Lfy ya jikin

Yayi sauqi ko ?

Ko har yanxu yana ciwo?

Dan Allah Amrita ki kulanmin da kanki

Dan mu samu ki wore 

Dan wlh Na gaji da zaman

Takura Amrita

Daga yau zan fara mana shirin komawa

Dan in muna qasarnan

Za,a kasheni

Yanxu nazo

Ummi ta hanani 

Shiga

Amrita ya za,ayi nida matata a hanani ganinta

Dan Allah kixo gareni

Wlh ke kadai nake son ji a kusa dani

Plss ki tausayawa zuciyar Hamma Yusuf dinki

Dan Allah kixo gareni

Dan zuciya ta Na gasuwa da begenki

Kijin Aysha Dan Allah ki taho.```


Dry sosai Anuty Sadiya takeyi da taga text din

Cikin tsokana ta miqawa Ayshan

Karba tayi tana Duba ajiye woyar tayi

Cikin tabe baki

Itako Sadiya

Hadin

Wani gari ta dama da madara

Mai sanyi ta miqawa

Aysha

Tana gashi shanyeshi yanxu

Kina shan wannan gaba 

Yusuf sai yayi kuka cur da hawaye,

Ita bata daqo zanceba ta karba tana Sha tana lumshe ido

Dan dadinshi

Ummi da ta shigo yanzu cikin

Fada 

Tace 

Sadiya

Ban hanaki bawa Aysha irin wadannan abubuwan ba

 Ke kuma ba son zaqiba Sai dirka kikeyi

Wlh zaki gane kurenki Gun wannan

Fitinenne

Wlh zai jinyatar dake shi ko a jikinsa

Bakisha komai bama ya kika qare 

Kekuma Sadiya

So kike ya kashe miki qanwa ko?

Dry Sadiya tayi tace

Insha Allah ba mutuwa Sai

Ta zuciyarsa

Ita Sam Aysha har yanxu bata ganeba

Sai Sha take cikin nishadi.



Haka Sadiya da Nenne suka rinqa

Tsuma Aysha da Amira

Itama Maryam har gida ake kaimata bayan Wanda aka mata kafin su koma

Tafiya Yola kuwa dole aka dage Dan Ahmad yace bazai jeba Sai da Yusuf shiko yana jinya.


Yau kusan 8 days kenan

Ummi ta kasa ta tsare

Fir ta hasasu

Haduwa

Ko woyarshi ta hanata dagawa

Sai dai dubbban texis nashi

Mgnaganu kuwa Yusuf

Yayi magiya har ya gaji Yayi ta roqo ko muryarta a barshi yaji

An hana.

 Ita kuwa Ummi

Har yanxu gwada son da Yusuf kewa Ayshan take in bata gamsuba bazata bashi itaba bare su koma tare.


Yau juna,a bayan an sauqo daga sallan

Yusuf ya shigo gidan

Ranshi a bace yau kwana 9  kenan hanashi matarsa

 Can gefen garden yaje ya zauna qarqashin

Bishiyar maqqoro mai inuwa da

 sanyi 

 

Phone dinshi keta suwa Amman yaqi dagawa har sai da ta katse 

Kiran ya kuma shigowa a karo Na  3

Cikin hatsala ya zaro phone din

Sunan

Bappa Yaya y gani

Tsaki ya Dan ja

Tare da amsa kiran


Bayan sun gaisa ne 

Bappa Yaya yake

Cewa 'Dudabe

Ka gayawa bello kace   karku zo

Gobe Dan munyi tfy

Dasu innayi duka.


Fuska ya tabe gamida cewa toh. Sainjima ya katse kira

Yana toh ni menawa da tfyarku


Yana wurin ya haqqo

Usman

Na Jan Trolley

Ya bude matarsa ya saka

Ya kuma komawa

Ya qara fitowa da yar qaramar jaka

 Ido ya qurawa jakar sarai ya gano ta Aysha CE

Shiyasa ya miqe cikin Dan sauri

Ya isa gunshi

Ido ya zuba mai cikin ayar tabbata

Yace 

Kai INA zakaje

Kuma kai dawaye


Cikin Dan

Tsoro

Yace

Gembu mambila zamu tafi

Ni da Aysha kafin gobe INA kuma zakuxo ko hamma Yusuf?


Hara ya watsa mai

Cikin isa

Yace

Bazaka jeba.

D sauri yace 

Bazan jeba ko bazata jeba?

Fuska ya kuma hadewa

Yace kai din bazaka jeba ko kanada mgn?

Cikin maraicewa yace

 Ga kayanta Na cire ni ka barni nayi tfya ta

Cikin

Tsawa

Yace

Nace bazaka jeba

Maza

Kwashi kayan nata ka maidasu cikin motata

Sannan kaje.

 cikin gida kace mata da motata ma zaku tafi

Toh yace cikin

Fushi ya kwashi kayan

Ya mayar cikin motar Yusuf din

Ya shiga cikin gidan.


Shi kuwa Yusuf da sauri ya shirya kayan shi yazo ya shiga

Cikin motar ya zauna

Cikin Farin ciki

Yana haggosu

Suka isa

Gefenshi

Cikin sanyi

Usman yace

Zagaya can ki shiga

Bari Na dauko igiyar 

Charge Na

Toh tace cikin

Murna,

 shi kuma Usman ya koma cikin gida rai a bace.


Cikin

Rausa yawa ta bude

Gaba ta shige

Hankalinta nata woje

Dan haka bata ganshiba

Shi kuma

Jin qamshinta ya sashi sauqen ajiyar zuciya

Tare

Da lumshe ido ya Dan konto kanta kadan

Hannushi yasa ya 

Jawo murfin motar ya garqame

Ita kuwa

Tsoro ya bata cikin

Mmk tasa hannu zata bude

Ya ficgota ta fada jikinshi

Da sauri yayiwa

Motar figan

Nishadi

Ya fice daga gidan.

Hanyar Gembun ya miqa 

Ita kam sai

Qoqarin janye jikinta take shi kuwa ya maqaleta

Cikin rawa hannu ya tura hannushi cikin.....


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣0⃣8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Qara shige mata yayi

Cikin fuskantar juna

Ya Dan jawota jikinshi

Yasa hannu ya dauko ledar gasassun kajin

Ya ajiye gefenshi

Hannu yasa ya Dan yaga

Ya miqa mata

Cikin

Dan rawan sanyi

Yace 'bude baki kici.

Kai ta dago ta tura baki

Gami da cewa

'Na qoshi,

Me kikaci?

Ya tabba yeta cikin tura mata a baki

Kai ta kuma kawar wa

Ganin haka yasashi

Matsota da kyau

Ya Dan daga yar 

Rigarta ya tura hannushi

A hankali ya rinqa shafa cikin nata  ido ya tsura mata

Gamida cewa

'Kici abinci

Kar ki cutarmin

Da kanki ki cutar dani

Kinji ko Amrita.

Janye  jikinta ta yi cikin

Ture hannushi tace ' toh ni ka barni, 

Miqa mata yayi a baki tare da cewa zan barki in kinci 

In kuwa baki Ciba 

Wlh bazan barki ba

Ya qarishe mgnar yana tura hannushi 

Saman bres dinta.


" jin haka yasa da sauri ta bude baki ya samata 

Ita kuma ta kamo hannushi zata fitar.

Yai maza

Yace 

Sai kin gamaci zan barki.

Haka ta haquri a dole ya rinqa yagar naman yana tura mata 

Ya kuma dauko juice ya bata 

Har Sai da taji 

Kamar cikinta zai fashe

Cikin qoshi tace

' Hamma Yusuf ka barni haka ji nake kamar zanyi amai

A jiye cup din yayi gami da 

' cewa 

' D'aga rigar inga cikin 

Juya fuska tayi 

Tana 

Tura baki

Shi kuwa fuska ya murtuqe cikin fada fada yace ' bude in gani

Ko in matseki

Kin sanni sarai,

Jin haka yasa ta daga yar rigar

Qara matsota yayi yace ki daga ko in iso

Dagawa tayi har zuwa kan qirjinta

Ido ya tsurawa fatar cikin

A ranshi yake fatan 

Allah yasa a yau dinnan ya dasa qonsa a jikinta

A fili kuma

Shafa cikin yayi ya juya ya nufi 

Bedroom din innayi

Yana shiga wonka yayi

Ya fito ya shirya tsaf

Ya fito parlon daure da towel.

Can ya hanqota rakube jikin kujera

A hankali 

Ya qarisa gunta cikin sanyi

Yace Aeeeshar tashi kije ki kwanta

Miqewa tayi da sauri ganin zai zauna gefen ta

Fuska ya Dan tsare tare da cewa

Me hakan cinyeki zanyi ne?


" kai ta girgiza tare da cewa zanje in kwanta ne,

Kai ya gyada alamar

Jeki


"Tana shiga

Ta haye kan

Gado mai rumfar

Ta sassake labulayen

Ta konta luf abinta

Sanyi Na ratsata

A hankali ta rinqa sauqe ajiyar hrt

Ganin har zuwa Dan wani lkci

Bai shigoba yasa tandan nitsu

Har bacci ya fara dibarta.


" Shiko

Tana tfya yabi bayanta da kallo

Ququnta ta tsurawa ido

Sosai ta tafi da nitsuwarsa

Gaba daya ya daburce lkci daya lips dinshi suka fara sana,arsu

A hankali ya lashi lips din tare da kamo gefen lips ya fara tsotsa kamar yaro

Jikinshi duk ya fara rawa

Har zuwa wani lkci

Ganin bazai yiwuba ya jumre waba

Yasashi

Miqewa 

Ya kashe su TV

Sannan ya rufe ko ina ya shige dakin.


"A hankali ya dage labulayen

Cikin hikima ya kwanta gefen ta

Tare da sauqe labulayen,

Ajiyar hrt ya sauqe

Lkci daya kuma ya mirgina ya isa

Gareta

Hannushi yasa

Ya jawota jikinshi

Hularta

Ta sabule

Sannan ya Sa hannu a hankali ya rinqa zare rigarta daga jikinta

Har saida ya cireta ya cillah gefe

Hannushi ya kuma turawa cikin mararta

Ya sabule zip din Dan gajeren wondon

Dai dai lkcin

Ita kuma ta bude idanta 

Jin yana ta yamutsa ta da rebata da kayan jikinta,

Hannushi ta riqe

Cikin Dan tsoro tace

'Hamma Yusuffffffffff

Bai amsaba Sai

Hannushi daya ya qarisa sabuleta

Ya wore towel din jikinshi

Ya qara manneta jikinshi

Lkci daya ta zazzare ido tare da sauqe wani nannauyan numshi.


" shi kuwa a kidime ya Sa hannushi ya lalubo bres Dinta

Ya rinqa shafawa yana sarra fasu

Bakinshi ya manna kan bres din ya rinqa sarra fata

Hannushi daya kuma mararta yake ta shafawa yana Dan murzawa,


Itako Aysha tsoro yasa ta qamqame hannushi

Tana 

Dan Allah Hamma Yusuf

Ka bari

Wlh tsoro nakeji

Zafi,


Nishi ya rinqa sauqewa yana

Rawan jiki

Ya tashi ya zauna ya jawota jikinshi

Bakinshi ya kai saitin kunneta

Cikin

Voice xex yace

' uhmmmm 

Hisshhihh

Plxxx

Aysha kitai maka

Wlh bazan iya jumrewa ba

Ki taimaka min

Wlh Na kasa haqura

Ki tausaya min

Kiga tsawon kwanaki da Na zauna da kewarki


" Hannushi ta riqe Wanda yaketa

Latsar qirjinta

Wanda gaba daya itama ta kidima ta

Cikin

Rawar murya tace

' ni dai bana so.

Yunqura yayi cikin rawan jiki

Ya kwantar da ita

Cikin sanyi

Yayi mata rumfa da faffadan qirjinshi

Yana rada mata

Am so sorry

My dear

Zan kula dake 

Ki kula dani

Zan biki cikin

Sauqi

Insha Allah yau

Bazakiji

Zafiba

Kinji

Matata,

Ta bude baki

Zatayi mgn kenan

Tai sauri

Ta rumtse idanta

Gami da 

Damqe hanna yenshi

Tare da cije lips

Dinta jin

Yana ratsata

Jikinta duk ya dauko

Rawa

Zafin takeji yana ratsata Amman bai kai

Yadda ta zata ba irin Na wannan ranar ba

Cikin

Rawar murya

Tace '

Shiihhht 

Hamma Yusuf

Zafi

Dan Allah ka barni,


Ina shi kam Yusuf baima San tanayi ba

Yau ya jishi cikin wata sabuwar rayuwa

Ji yake da zai tabbata a haka da bazai gajiya ba

Gaba daya ya fita hayya cinsa

Sai wasu zantuka yake masu wuyar

Fada

Gaba daya jikinta

Binta yake da lasa da subbata

Ita kam Aysha tun tana Dan

Daurewa.kar tai kuka

Dan yadda yake Sa mata albarka

Yana '

ki jiqaina 

Aysha ki taimaka ki barni Na gamsu

Da nimar da Allah ya miki

Ki taimaka min

Ki ruqqume ni

A matsa yin mijinki

Na har abada

Aysha ki daure

Ki jiyar dani

Dadin da ban taba jiba

Gaba daya haka ya zauce ya zautar da ita

Juyata kawai yake yana haqarta ta inda yaga dama

Har zuwa

3:30Am

Ita kam Aysha

Gaba daya ta sake Sai

Qollah take tana

Qamqameshi

Tana

Hamma Yusuf

Na gaji

Bazan iyaba

Zan mutu

Numfashi Na zai dauke

Haka tai ta magiya

Sai 4 dai dai

Hamma Yusuf ya sarara mata

Ya koma jikin

Pillows ya kwanta

Ya jawota jikinshi

Ya ruqqume ta tamkar zai maidata cikinsa

Ita kuwa duk ta saki ta narke kanshi

Tana kukan

Gajiya da rashin bacci

Ta maqale jikinsa

Tana shaqar qamshinsa

Shiko bayanta

Ya rinqa shafawa yana

Ohh Amrita

Allah ya miki albarka

Rabbi ya saki farin ciki kamar yadda kika sani

Kin

Daukemin duk wata buqatata 

A,ish

Me kikeso

Na miki

A duniyar nan?

Cikin

Qara maqaleshi

Ta shafi sajenshi

A hankali

Tace

Ka barni

Ka dena takura min,

Ka tausaya min

Hamma Yusuf kafi

Qarfina

Bazan

Iya daukar

Yawan buqatar ka ba,

Numfashi ya furzar gamida

Kamo lips Dinta ya Dan tsotsa

Sannan yace

Ai zan mutu in Na barki

Aysha waya CE miki bazaki iya daukar nauyin buqatuna ba

Ai ke ta dabance 

Ko ganin ki nai nakanji gam suwa,


" A haka dai ta dan lafe a jikinsa har, akayi assalatu

Cikin Dan baccin da ta farayi ne taji ta cikin

Ruwa

Da sauri ta bude ido

Sai kuma ta rumtse ganin

Tare suke da Hamma Yusuf din nata

Ya caxge kamar bashi ba

Jawota jikinshi yayi

Tare da shafa qirjinta

Idan ta kuma budewa

Ido ta tsura mai shima itan yake kallo

Girarsa daya ya daga mata cikin

Rada yace

Sunefa suke tsoka nata

Ya fada yana nuna bres Dinta

Baki ta Dan tura tace

Me sukayi 

Kanshi ya manna kan qirjintan yana

Cewa sunce Na matsosu,

Itama miqa ta danyi

Dan ya fara sauqe mata wani salon

Fitina

Qirjinta ta Dan dago ta tura mai

Da sauri ya cabke har jikinshi

Na rawa kamar wani

Yaro ya rinqa tsotsarsu

Ita kuwa ido

Ta lumshe tana shafa kanshi da qirjinshi


"A haka dai da gyar sukayi wonka

Suka fito

Suna fita tea ya hada mata mai kuari ya bata tasha

Sannan ya tafi masallaci

Itama tayi sallahn


"Yana dawowa

Ya cire rigarsa

Ya raba gefen ta ya kwanta

Yana lalubota

Cikin

Baccin ta tashi

A Dan gajiye tace

Wlh Na gaji bazan iya ba plxx 

Hamma Yusuf bacci

Kai ya gyada cikin

Sanyi

Yace kiyi

Baccin

Ni ki barni da qirjinki ya isheni

Haka ya rinqa yamutsa ta

Sai 11 suka tashi 

Gidan baba Hamisu sukaje bayan sun kimtsa

Acan sukaci abinci

Bayan axahar suka fita shida baba hamisu

Ita kuma tai ta bacci

Sai 9 Na dare sannan suka koma gida


" yau kam Aysha kuka tai tayi taqi

Amincewa Dan gajiyar jiyama bata barta ba

Shiko Yusuf haka ya haquri ba Don ya soba Sai Don tausayinta yakeji

Dan shi da kansa yasan 

Ya murzata da yawa


" itako Aysha tun daga ran nan

Ta samu damar

Kaucemai bare da ta gane bai son

Takurata

Haka kullum yake kwana cikin buqatuwa itako tai ta baccinta


" Yau ma kamar kullum

Kwance suke

Cikin

Blanket

A hankali ya matsota

Murya Na rawa

Yace

Aysha

Da ixinin

Wa kika juyamin baya

Bana gaya miki

Banson hakan da kikeyi ba?


Cikin tura baki tace ngji

Bacci zanyi

Cikin Dan rauni yace

Aysha ki tausaya min mana

Wlh bazan iyaba

Yau kwana  4 muna tare Amman kin hanani haqqina


Tashi tai ta zauna

Cikin

Dan yamutsa fuska tace

Wlh kai Hamma Yusuf ka fiye jaraba

Na lura so kake ka tsotsemin ruwan jiki

Ido ya tsura mata cikin

Kufula yace

Bani NAYI kaina hakaba Allah ne yayini

Haka

Kuma kinsan haqqinane kam ko?


Konciya tai ta juya mai baya

Tace 

Ai jarabar tafi qarfina ne,

Ka takurani ka hanani sakewa wlh

Tai qasa qasa da murya tace jarabebbe kawai

Shiko ya jita sarai ranshi ya baci matuqa

Miqewa yayi ya sauqo qasa

Kan carpet ya wurga pillow ya kwanta

A ranshi

Yake jin zafin

Abinda tai mai watoh shi ya zamar mata kamar dole ko


Ita kuwa tana jin ya sauqa ta gyara kwanciya tai luf

Abinda


Shiko ya kasa bacci

Sai juyi yakeyi

Yana cikin haka phone dinshi ya kama ruri a hankali ya daga

Cikin sanyi yace

Abubakar

Na,am ya amsa cikin

Sanyi yace

Hamma Yusuf

Bacci zanyi Sai kuma duk naji hankalina ya dawo gida

Cikin gyara zama

Yace

Dan uwana 

Kazo mana muma munyi kewarka

Abubakar katashi hsnkalin

Ummi ma wlh duk ta damu da rashin zuwanka

Ajiyar zuciya ya sauqe

Tare da cewa

Hamma Yusuf

Zan zo Amman inaji

Kamar zuwan qarshe zanyi

Jikina Na bani mun kusa rabuwa,

Da sauri 

Yusuf ya dakatar dashi cikin

Tsoro yace

Haba Abubakar

Meyasa zaka gayamin haka Dan uwana

Dan Allah kar ka gayawa mahaifiyarmu haka Dan uwana

Dry Abubakar yayi cikin

Raha yace toh ba komai Hamma Yusuf kayi baccin ka Sai da safe

A haka suka katse kiran


Kashe gari

Yusuf

Bai nunawa Aysha komai

Ba da dere ko 

A kasa ya kwanta

Abin takaici kuma bata kulashi ba

A Daren ya samowa kanshi mafita

Shi da kanshi ya rinqa murmushi

Mugunta

Kashe gari da yamma

Ya shigo

Parlon ya samu ta ajiye nono

A kan stool 

Ta koma kitchen zata dauko spoon

Wasu tabs

Ya fitar daga aljihunsa

Ya murza guda

2 cikin

Nonon har ya juya Ya kuma

Juyawa

Ya qara murza 2 a cikin

Nono

Ya koma can gefe kan  1str ya zauna

Yana kada 

Qafa

Tana 

Fitowa ta dau cup din

Ta jujjuya nonon

Sannan ta rinqa Sha a hankali

Tana Dan lallatsa phone Dinta har ta shanye,


Shiko miqewa yayi

Cikin tsare gida

Yace

Ki shirya

In anyi sallah

Mu tafi

Restaurant

Toh tace cikin

Murna tace dama

Inabina ya qare


" bayan sun 

Kammalah cin abinci

Yalodo mata fruits

Qarfe 9 dai dai

Suka shigo

Mota 

Yaja suka

Nufi

Gida


Itako Aysha tun a cikin

Motan

Takejin

Wani irin

Yanayi Na ratsata

A hankali ta fara miqa

Duk gabanta

Suka rinqa budewa

Ta kasa gane meke faruwa da ita


" a haka dai ta daure 

Har suka isa gida

Suna isa

Wonka tayi

Ta shirya cikin rigar baccinta

Yar yeloluwa

Mai budedden qirji

Sai Dan igiya ta saman ta Dan daure


Tana tufa ta shima ya shiga

Ya watsa ruwan

Towel ya daura a ququnshi

Ya murza turare kawai a jikinshi ya koma parlon

Ya kwanta kan

 3str


Ita kuwa

Ido kawai

Take binshi dashi

Zuwa yanxu

Ta gano

Sha,rawar Hamma Yusuf dinne ke tsumarta

Kwanciya tai

Amman ta kasa nitsuwa

Cikin

Miqar ta miqe ta nufi

Parlon ido ta tsura mai

Cikin

Piki piki da ido

Sai wani miqa takeyi

Shiko dago kai yayi ya kalleta ya yamutsa fuska,

Yaci gaba da kallon shi

A hankali ta isa

Gefenshi ta......


By Garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👆🏻👆🏻

*MI,WASMITI* page1⃣0⃣9⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Wannan page din nakune matan


*® PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*

             P.M.L


"Gefenshi ta ratsa ta wuce

Kan 1 str ta zauna

Ta Dan jigina da jikin kujerar

A hankali tayi wani irin dogon miqa.

Ta Dan tura baki

Ta juya ta kalli 

TV

Wani Nigeria film yake gani

Gaba daya ya maida hankali shi

Kan tv su 

Kuwa arna Sai

Zuba Roman's

Suke,

 

" tsaki ta Dan ja

Tare da zamewa qasa

Tana daddamqe jikinta


" Shiko Yusuf sarai

Ita yake kallo

Mmk yake taurin kai irin

Na Amrita

A ranshi yace ko dama su mata haka suke sukan iya danne buqatarsa ba kamar mu maza ba

Ko kunyace

Murmushi

Mugunta ya danyi

Tare da tunanin

Koma dai menene yau zaki gane kurenki


Ita kuwa Aysha

Qirjinshi ta tsurawa ido

Ba abin da take so irin ta jita maqale a jikinshi

Amman kuma ta rasa ta inda zata 

Fara 

Yau dama ace da hadari da zata fake da haka ta maqaleshi


Tashi tayi ta zauna

Cikin wani irin

Voice

Tace

' Hamma Yusuffffffffff


Ya jita Amman bai kulata ba 

A karo Na 

2 tace

Shhhhhhhhhum 

Hamma Yusuf

Gaba daya gashin jikinshi ya mimmiqe jin irin sautin da ta kirashi

Dole ya juyo gareta

Cikin sanyi yace

'Menene ?


Kai  ta kwantar cikin salon yin 

Kuka 

Ta kum cewa

Hammaaa

Ido ya tsura mata 

Cikin jin tausa yinta

Dan a fili

Yake hanqo 

Buqatarsa da take a jikinta da qwayar idanta Amman kuma gashi ta kasa

Fada ko ta kawo kanta


Kai ya jinjina

Yace

Amrita

Baki da lfy ne?

 Kai ta gyada mai cikin

Zubda qollah

Cikin

Son yin dry

Yace

Meke 

Damunki?

Miqa ta kumayi

Tare da danna qirjinta jikin guiwarta

Murya Na rawa tace

'Nima ban saniba

 

Bakisan meke damunku ba ?

Ehh ta fada cikin

Kuka daya kufce mata


Shi kuwa kauda kai yayi cikin

Murmushi mugunta

Yace toh

Jeki kwanta


Miqewa tayi

Taje jikin

Tv ta kashe

Shiko ido ya tsura mata cikin

Hada fuska yace


'Meyasa zaki kashe bayan kinga 

Ina kallo,


 Juyawa tayi ta shige daki

Tana 

Mutum baida lfy ma baza,a barshi

Ya huta da hayanin

Tv ba


Tana fita ya 

Jawo 

Phone dinshi

Yako yi Sa,a Ahmad da Adam suna

Online suna ta hira

Sai ga Abubakar ma dasu Hydar,


"A dakin

Ta kasa

Zama 

Sai juyi take

A fili

Take cewa Na shiga

Uku meke faruwa dani

Can kuma ta koma

Parlon

Gabanshi 

Taje ta 

Durqusa

Ji take kamar ta fada jikinshi

Amman kunya takeji

Shi kuwa yana ganinta

Ya kauda kai

Ya rigada ya gano

Ta 

Kamu

Ya kuma San

Abinda yafi

Burgeta a jikinshi

Qirjinshi da damtsen hannushi 

Shiyasa yasa hannu

Yana shafa 

Sajenshi


Cikin sanyi

Ta saki Dan

Kuka tana

' Hamma Yusuf

Sai ya amsa yace mene?

Sai tai shiru

Ganin haka

Yace

Tashi 

Muje ki

Kwanta,


Miqewa yayi 

Ya nufi dakin

Tana biye dashi a baya


"Suna shiga ya gyara mata blanket din yace xoki kwanta

Ki bar kukan,


" cikin tsura mai ido

Ta hau ta kwanta

Ya Dan ronqofo

Ya gyara mata gashin

Kanta

Ya jawo blanket

Din ya rufeta iya 

Qirjinta

Ya juya 

Zai fice

Sai 

Kuma ya juyo da sauri jin

Ta riqe hannushi!

A Dan mmk 

Ya kalleta ido cikin

Ido

Ita kuwa

Sauri tai ta sada kanta qasa

Jan hannushi zai ta kuma qara riqewa

Juyawa yayi da kyau

Ya tsura mata ido

Cikin sanyi

Yace 

' Amrita

Meke faruwa?

Tsoro kike jine

Kai ta girgiza alamar a,a 

Sai qara jowoshi

Take

Murya can qasa qasa

Tace

Hamma Yusufhhs

Na,am ya amsa mata Sai kuma tai shiru

Ganin haka

Yasa ya janye hannushi

Ya juya yana

Tunda bazaki fadi meke damunki ba ya Na iya miki


Cikin sanyi ta diro daga kan gadon

Ta bayanshi

Ta tsaya

A hankali

Ta ja igiyar 

Rigar baccinta

Ta budata daga

Saman

Qirjinta ya fito

Fili

Qarisawa tayi

Gunshi

A hankali

Ta manna qirjinta a gadon

Bayanshi

Cikin

Wani irin salo

Ta sauqe nannauyar ajiyar hrt

Tasa hannuta ta zagayoshi

Ta gaba

Kan qirjinshi ta dire hannuta

Cikin

Rashin sanin ta iya salon

Ta rinqa murza qirjinta a bayanshi

Hannuta daya Na 

Murza nashi qirjin

Daya kuma

Tayi qasa dashi

Ta kamo

Towel din jikinshi

Zata kunce,

 

"Da sauri

Ya juyo kanshi

Yana kallon

Ikon Allah

Ita kuwa 

Luf ta rumtse idanta Dan kunya

Cikin

Dauriya Dan Aysha ta birkitashi

Ta qona mai jinin jiki

Murya Na rawa

Yace

Me hakan

Kije kiyi bacci

Ni kallo zanje inyi


Qara Jan towel din take

Da sauri ya riqe

Hannuta

Ya jata zuwa kan

Gadon

Cikin

Daurewa Dan shima so yake ya rama

Ajiyeta yayi

Ya Dan ja baya

Cikin

Sigar ki kula

Ya Dan sunkuyo

Ya ja igiyar rigar ya hada 

Saitin qirjinta

Mmk yake

Yadda hatta qirjinta cikowa bres Dinta sukayi

Kansu

Yayi jawur

Dan bakin

Ya hade 

Da ka gani

Kasan

A hannu take

Ita kuwa mmk

Take Hamma Yusuf

Dai

Mutumin

Da ko cikin

Bacci

Yaji qirjinta Sai

Ya shafa wai Amman

Yanxu shike rufe mata qirjin

Shi ko zuwa yancu

Makanta ta diran mai

Bai ganin

Komai Sai

Ita

Pillows yaja

Ya wurga 

Tsakiyar daki

Kan carpet

Ya taka

Yaje jikin

Gini

Ya kashe wuta

Yana 'ki kwota kiyi

Baccin ki

Gani

A dakin,


"Juyowar da zai

Yaji ta

Ta fada 

Kan qirjinshi

Ta narke

Tasa hannu 

2 ta sanqalo

Wuyanshi

Qirjinta ta rinqa 

Tura mai

Cikin

Goga mai ququnta

Ta zame towel din jikinshi

Tasa hannu daya ta

Sabule rigar jikinta

Cikin wani irin

Rawan jiki

Ta manna jikinta da nashi

Hannushi ta jawo ta daura kan qirjinta


" wayyo

Hamma Yusuf shi kam

Mutuwar tsaye yayi

Ba abinda yakeji

Da tunawa 

Sai

Randa ya fara 

Ganin qirjin Amritanshi

Randa shi

Ya mammatseta tana kuka tana kaucewa, 

Da gyara ya samu

Suka 

Isa kan carpet din


" zama yayi cikin

Sauqe numfashi

Ya jingin jikin

Gado

Ya bubbude Hanna yenshi

Tabbas a yau

Aysha ta bashi mmk

Ase dama cutar dashi takeyi

Sarrafashi take da juya shi

Kan cinyarsa

Ta dare ta zauna

Ta tallabo

Fuskarsa

Bakinta tasa cikin

Nashi

Ta lalumo 

Harshensa ta rinqa tsotsa

Shi kam

Sai

Numfashi yake

Sauqewa

Can

Kawai yaji

Kuka ya kufce

Mai

Cikin

Kukan

Ya tureta gefe

Ya matsa ya qamqame jikinsa

Murya Na rawa

Yace

'Amrita

Ki barni

Ki rebu dani

In so kike ki kashe niba

Meyasa

Kike son

Zalumtata?

Matsoshi tayi  ta narke jikinsa

Tana 

Hamma Yusuf

Kar kayi nesa Dani


Cikin

Wahala yace

Nike nesa dake ko kece keyin nesa dani

Sannan yanxu kinxo

Kin birki tani

Danace ki ban haqqina kuma

Ki fara min kuka da mita

Harda cemin

Jarabebbe

Toh kije ni Na haquri

Zan daure koda zan

Mutu

Kije bazan

Kusance kiba


Matsoshi

Ta kumayi

Cikin

Rawan jiki

Tace

Wlh bansan ya zanyiba Hamma Yusuf


Tureta yayi yana kinsan

Ya zakiyi

Nine dai bansan

Ya zanyiba


Adan kun yace tace

Hamma Yusuf

Idan ban rabeka ba wazan raba

Kaine 

Mijina

Haqqina

Yana kanka

Ba gun Wanda zanje Sai gareka


A hankali

Yace

Yau

Kin nemi haqqinki

A guna?

Kin yarda bani kadai

Bane jara bebben

Harda ke?

Matsoshi tayi

Cikin

Kunya ta fada jikinsa

Cikin

Salon salo

Ta dago qirjinta sama

Kadan

Kanshi

Ta tallabe

Ta rufe mai baki

Da bres Dinta

Kanshi Na qirjinta ya yunqura

Ya sunkuceta

Sai kan

Gadon

Yana direta ya Dan juya zai dauko

Pillows

Ta jawo shi

Jikinta da qarfi

Maqaleshi

Tayi

Cikin

Rada 

Yace

Amrita ai zaki

Karyani

Ki huta


Hannu tasa ta zagayoshi

Cikin

Kaiwa maqurar bu qatuwa


Tace

'Bana son

Duk wani Abu

Da zai nesantani

Da mijina

Ba abinda nake shauqi Sai

Hamma Yusuf Na

Plxx Hamma Na

Kar kayi nesa dani


Cikin sauqe numfashi yace

Ni nakine ke kadai

Amrita

Baki da kama a gareni

Yusuf nakine

Ke daya

Dama danke rabbi ya bani

Cikar haiba

Aysha banji

Komai a duniya Sai sautinki

Ban ganin komai

Sai fuskarki

Aysha sonki

A jinina yake

Amrita ki ankilta min jikinki

Dan shine nitsuwata

Qara matseta ya kuma yi

Cikin

Isar da dubban saqonnishi zuwa gareta

Ita kam

Gaba daya ta maqale

Hammanta

Tamkar zata hadi yeshi

Ba abinda take Sai

Shi take

Kira cikin

Sautin

Sarkewa

Tana 

Hamma Yusuffffffffff

Shiko ji yake

Ba Wanda yake kiran sunan shi dai dai Sai ita

Sai ta maqaleshi

Tace

Ohh

Hamma Na i miss  you so much

Shi kuwa

Yau 

Yusuf

Larabci

Yake ta bugawa

Yana  ya habbiti

Noor hayatina

Noor qalbina

Ya A ish,

 Ahaka suka zauce

Suka kidime

Juya abarsa yake son ransa

Yana murzata itama

Gwayar da ya dirka mata bai sakiba Sai

Maqaleshi take tana

Hamma Yusuffffffffff

Sune basu sararawa junaba har

4:20Am

Sannan

Ya sahirta cikin samun cikekkiyar gamsuwa

Jinshi yake a saman gyajimare

Cikin jarumta ya ciccibeta Sai

Cikin baf ya direta


Shima ya shige

Luf sukayi

Cikin

Ruwan

Bres dinta

Ya shafa cikin

Rada 

Yace

Basu gaji bafa

Idonta a rufe

Tace

Ai nakane Hamma Yusuffffffffff

 Tsura mata ido

Yayi

Cikin

Shauqi ya maqaleta

Yace

Wlh da Na cuci kaina Dana kashe rayuwata da Na rebu dake

Na tabbata bazan samu kamar ki ba

Sai yanxu Na gano

Tun da canma sonki

Ke d'awayniya

Dani

Kanta ta kontar

Kan kafadarsa

Cikin

Tura mai bres Dinta

Tace

 ' Hamma Yusuf

Ka manta dai

Da ai baka da abin qi Sai ni


Da sauri ya rufe bakinta

Cikin

Gskya da gskya

Yace


" ,ban taba tsanarki ba

Sai dai tsoron ki

Da nakeji

Amrita

Sabida a wancan 

Lkcin

Ina miki

Klon

Qanwata uwa  1uba  1

Sai

Kuma

Ko yaushe

Kece mai

Tayarmin

Da Sha,awata

Dana ganki

Nitsuwata ke tafiya

Shiyasa banson

Ganin ki

Danaji

Muryar ki

Sai Na daburce

Da zaran kin Dan tabani

Wlh Aysha Sai nayi wonka

Kin tuna randa

Kika fada jikina a rafi

Wai kije gun Ahmad

Shiyasa ko yaushe nake mmk inaga su Ahmad Na maqaleku kuma basa jin komai

Ase Dan ba Aure a tsakanin ku ne


A lkcin kuma 

Badon INA kauce miki ba zaki

Iya gane halin da nake ciki

Shisa kike min kallon mugu

Aysha 

Wlh Na cuci kaina da muka yi tsawon 2 year ban amshi a manataba

Tsofinnan sun min gata

Da suka aura min ke

Sun kuwa yi miki

Gata da basu bari Na sani ke matata bace

Dan da Na Sani da

Bazan iya haquri har ki girmaba

 

Yawan fadan da nake miki ase kishine ban saniba

Matseta yayi

Itama lafewa tayi jikinshi

Cikin

Tsune kanta a qirjinshi


A hankali yace

Amrita I

Love you so much

Zan dauwama in mai begenki

Qanwata a manata matata

 Da gyara sukayi wonkan suka fito

Bayan sun gama komai

Suka kwanta rama baccin deren da basuyiba


12 dai dai

Aysha ta sauqo

Kan gadon

Cikin mmk ganin

Hamma Yusuf

Baya dakin

Toilet ta shige cikin

Tsoro da mmk jin qafafunta Na rawa karkar

A daddafe ta shirya ta fito

Parlon

 tsaye tayi a tsakiyar parlon

Tana miqa

Batayi auneba taji

Yayi hogging Dinta ta baya

Cikin

Sanyi

Yace

Har yanxu

Miqa kike

Alamun baki

Gamsu ba kenan Dan ba yunwa kike jiba ba bacci ba kawai

Hammanki kike son raba kinji dumina

Qara matseta yayi,

Itako cikin

Tsoro

Tace 'a a 

Hamma Yusuf nagaji

Qafata ciwo

Sai rawa suke 


Dry ya danyi cikin

Salon shauqi yace

Qafafun basu gama karbar saqonnina bane

Shiyasa

Baki sababa 

So yanxu baqunta suke

Sai Na gama koyar dasu

Nima a farst  night dinmu nayi fama da hakan

Qafafuna suka rinqa rawa idan Na zauna da gyara zan tashi

In an taba cinyata kamar nayi ihu sabida sunyi abinda basu taba yiba,


*Inda mace zata iya gane namijin da bai taba kusantar mace ba kenan alamun suna da yawa wannan kadan ne daga ciki*


Yaci gaba da cewa

Gashi ke din ta dabance bana gajiya da ke

A shogobance tace

Ni wlh ban da qarfi

Cocci beta yayi cikin

Rada yace muje in baki Na qarin qarfi baby nah

Kan gadon ya direta

Tana 'ayyah Hamma Yusuf

Shima karya wuya yayi cikin

Koikoyarta

Yace

'Ayyah

Ki bar Hamma Yusuf dinki ya rege zafi.........


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👆🏻👆🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


~®PURE MOMENT OF LIFE WRITERS~

                 P.M.L


Ido ta lumshe cikin

Kunya ta shafi sajenshi da ya kwanta lub.

Shiko samun haka ya sashi

Lafewa jikinta cikin Isar da saqonnishi

Masu wuyar

Man cewa,

Cikin

Rad'a yace 

'Amrita ngd Allah ya miki albarka

Rabbi ya cika miki

Rayuwar ki da Farin ciki kamar yadda kika cika rayuwata da Farin ciki.


"Lafewa ta qara yi a jikinshi

Tana jin

Bugun zuciyarshi Na harbawa kan nata

A haka har zuwa Dan wani lkci

Sannan 

 Suka samu suka 

Yi wonka suka shirya

Suka fito parlo 

Kan carpet suka

Yi masauqi

Yusuf tallabe

Da amritarshi

Yana ta riritata 

Itama Sam har yanxu ta kasa

Jin ta gaji dashi

Shiyasa bata tsiri halin

Wahal da shiba..


"Suna  cikin 

Hirarsu 

Tana lafe cikin

Qirjinshi

Sukaji! 

SLM su Bappa

Yaya

Da sauri ta yunqura zata tashi

Shiko Sai qara matsota yayi.


" Suna shiga 

Innayi da inna 

Suka bisu da klon

Mmk

Shiko Bappa Yaya

Cikin

Jin dadin ganin su

Yayi

Murmushi

Dai dai lkcin

Da ya zauna kan kujera da suke qasanshi.

 Cikin happy

Yace 

'D'ud'a'be

Yaushe  kuka 

zo?

" Fuska ya Dan yamutsa cikin

Daqile murya 

Yace ' ba nacema ban son sunan nan ba?

' ehh ka fada kuma bazan bariba,

Kai dai wlh bakaji dadiba 

Mu muna sonka kamar mu mutu

Kaiko kana kinmu kamar ka mutu!


"Ajiyar zuciya ya sauqe cikin

Dan raha ya shafa suman kanshi

Yace 

' ai gwara da Baku 

Mutuba 

Bappa Yaya da ka mutu da wa zai ban Farin cikina?


" cikin mmki innayi tace ' menene Farin cikin naka?


"Murmushi yayi da iya gskyarsa yace

'Aysha

Mana.


"Aiko su inna suka rinqa dry, 

Shi ko ko a jikinsa

Bappa Yaya ne 

Ya Dan gyara zama ciki

Girma 

Yace 'Yusufa 

Kaga ribar bin mgnar iyaye ko?

Kaga illan bijire musu

Kai da kanka kasan yanzu ka samu cikekkiyar rayuwa

Sabanin baya da kake ganin

Mun qwareka mu samman ma ni.


Kai ya jinjina cikin

Sanyi

Yace ' Bappa Yaya

*MI,WASMITI* ko mi wadi ha wakkati to do,

*NAYI,NADAMAN* abinda Na aikata a wancan lkcin

Bana son tunawa sauqina ma daya da rabbi

Ya bar min

Dan uwana Ahmad da biyaye Na ya mutu da bazan yafewa kai naba.

Innayi tace ' komai ya wuce yanxu kam

Fatan rabbi ya Baku zuriya d'aiyiba,

Amin ya amsa cikin

Zumudi da jin dadin addu,ar.


"Haka sukayi ta Dan Hie ransu

 Biyar dai dai

Yusuf ya

Miqe cikin

Kammala shirinsa

Da Na Aysha 

Ya kalli su innayi

Cikin

Qaunar kakannin nasu

Yace 

' mukam zamu tafi

Sai

Next week

In munzo,

Bappa Yaya

Yayi ta nacin ya bari Sai gobe yaqi fir Dan shi a ganinsa

Zasu takuru

A dole ya barshi

Ya dauke yar matarsa

Suka tafi.


" cikin

Mota

Yusuf

Tuqi yake

Da hannu daya daya kuma ya jawo amritanshi

Yana Dan 

Shafa bayanta

Yana 

'Amrita

Bacci kike 

Jiko?

Kai ta Dan gyada mai a Lamar eh 

Cikin

Sanyin ya qara jawota jikinshi

Yace

Kwanta kiyi bacci

Kan cinyar 

Mijinki

Kinji ko

Matata?

 Itako

Ido ta tsura mai cikin

Mmk hali irin Na Hamma Yusuf

Wato

Shi Hamma Yusuf ya yarda da love

Ya Baiwa so

Amanna

Shi jin Kalmar so yake tamkar ruwan zinari

Shi Yusuf irin mazannan ne da so ke mai dasu

Bayi

Ya maidasu tamkar basu San komaiba


" A haka suka isa 

Gida 

Tana lafe a jikinshi

Tana baccinta.

Yana parking

Rabi,u da Usman suka iso

Cikin

Qaunar yayan nasu duk da zafibirin Na Yusuf yan uwanshi Na matuqar qaunarsa

Kye ya basu suka tattara kayansu

Suka shigar cikin gida.

Ummi Na ganin jakar Aysha

Tace

'Usman sun dawo ko?

Kai ya gyada Cikin

Leqa hanyar shiga

Yace ' wlh

Ummi Sai.kinga yadda

Autanki tayi kyau

Sai kace wata balarabiya

Sai dai ta Dan rame gsky.

Ajiyar zuciya ummi ta sauqe cikin jin dadi

Tace 'Toh ina take ne?

Rabi,u ne ya Dan Sosa qeya yana

Duba qofar shima yace

' kin Santa ai da shegen son jiki

Bacci fa takeyi a cikin

Motar ta wani

Maqale jikin Hamma Yusuf

Shiko

Ya wani rashe wai baya son ta tashi

Harda wani cewa

Mu bamu da nitsuwa bamuga tana bacciba.

Dry Ummi tayi

Cikin

Tsokana tace '

gashi a bayanku ai!

Aiko a tare suka juyo

Sai kuma sukayi dry.


" a motar kuwa

Cikin sanyi

Ya sunkuyo

Kanta hankali ya rinqa busa mata iska a kunneta

Itako jin iskar ta qara sakewa tayi

Luf ta juyo

Qirjinta sama,

Murmushi ya danyi

Cikin

Jin dadin

Yadda take

Murza shi

Kiranta yakeyi Amman shiru Sai sauqe numfashi takeyi,

Ganin haka yasa shi

Cikin

Qworewa

Ya qara manna ta jikinshi

A hankali ya tura hannushi

Bayanta

Zip Dinta ya zuge cikin

Hikima ya maidata kan cinyarsa 

Hannushi

Ya Dan tura cikin

Rigarta

Lkci daya ya dire hannushi kan bres Dinta

A take kuma ya lumshe ido ya sauqe ajiyar hrt,

A hankali yasa Dan yatsanshi ya rinqa zagaye bakin bres din

Cikin

Sauyawar voice

Ya rinqa kiranta

A,ishhhh

A hankali ta bude ido

Tare da Dan tsura mai idon

Sai kuma ta Dan tura baki

Cikin

Muryar bacci tace ' Hammaaa Yusuffffffffff

Ido ya tsura mata cikin

D'aga mata

Gira 

Hannushi ta Dan kama

A hankali ta jawo hannu

Shi kuwa

Kai ya karya

Yayi fuskarta tausayi

Cikin

Sanyi yace

'Aish

In Neman alfarma ki zo gareni mu kwana tare

Wlh bazan iya kwana banji duminki ba

Plxx karki manta ni

Baki ta Dan tura tana

'Hamma ni a gun Ummi Na zan kwana,

Cikin 

Tausayawa kanshi

Yace

Mijinki kuma ya kwana

Da waye

Kamata yayi ya ruqqume cikin

Tsokana yace

Yarinya ki Adana mijinki

Ummi ma ba dakinta zata kwana ba.


"Tureshi ta danyi

Ta bude qofa ta fito

Shima fita yayi

Ya zagayo yazo gabanta

Cikin

Gyara net dinshi

Ya juyata

Ya tura hannushi

Ta gabanta ya lalubo

Bres Dinta ya shafa cikin

Rada yace

Zanyi miss dinki

Tabas itama  taji Hamma a jikinta

Shiyasa Sai ta lumshe ido

Kawai.


Tana bude idon

Ta haqqo su ya Abubakar da Ahmad da Adam

Da sauri ta janye jikinta

Cikin

Happy ta isa garesu

Da Dan gudunta

Tana zuwa kamar zata fada jikin ya Abubakar Sai kuma ta tsaya cikin

Farin ciki

Tana '

Oyoyo ya Abubakar Na nayi missing dinka sosai

Shima Abubakar dry yake cikin

Jin dadin ganinta da yanayinshi Na tsantsar qaunar yan uwanshi

Yace Allah sarki

Aysha wato yanxu kin girma 

Kin dena 

Son jiki,

Dry tayi ta kamo hannushi tana

Bazan girmanwa Dan uwana ba ai,

Su Ahmad kam dry suka rinqa yi

Har suka qarisa gun

Yusuf

Cikin

Qaunar juna suka ruqqume juna

Suna dry

A hankali Yusuf ya qarisa gun Abubakar ya ruqqume shi

Cikin

Qaunar qanin nashi

Yace

*Babiker* dan

Haka yake kiran Abubakar din yana don tsokanarsa tun suna yara bare kuma da ya zama dole akwai Dan reni a tsakaninsu Na irin shi Abubakar shi yake bin Yusuf a aihuwa.


Dry Abubakar ya danyi Sai kuma ya matse Yusuf a jikinshi

Cikin

Sanyi da qaunar Dan uwana nashi yace

Hamma Yucut

Haka yake kiransa lkcin yarinta

Shima Yusuf dry yayi

Sai kuma yayi shiru

Jin Abubakar bai sakeshi ba

Kuma Sai

Zuciyrsa da yaji tana bugawa da qarfi-qarfi.

Cikin sanyi yaji

Abubakar Na rada mai

Hamma Yucut

NAYI kewarku

Ji nake kamar Na bar aikin

Sojannan Na dawo

Mu zauna nima in rayu cikin yan uwana kafin mutuwa ta rabamu,

Da sauri Ahmad yace

Haba Abubakar meyasa zaka Sa mana tsoro a zuqatanmu.


Adam yace 

Gsky Abubakar banson irin zantu kan nan naka,

Dry ya danyi

Fuskarsa tai

Ra's a zahiri

Dama da yawa kance kab yaran gidan

Abubakar ya fisu

Kyau danshi

Tamkar balarabe yake

Ga qira ga cikar zati ga haiba sannan shi mai yawan fara,ane da son Al,ummah

Dan shine qarami a Kansu Amman kab ya fusu tsawo da qiba,

Cikin fara ar yace

Toh ai rebuwa ya xama dole

Brothers Na,

Aysha kam

Tuni

Ta fara hawaye Dan ita tun kan ya Ahmad bata son jin irin zantu kan,

Dry shi kam Abubakar yake tare da jansu suka tafi cikin gida.


A babban parlon suka

Zauna akayi ta hira

Aysha ko da ta ga Ummi Sai tayi qasa d kai

Itako data gane Sai ta shereta sannan ta saki jikinta..


"Bayan 2 week, Rayuwa ta musu dadi kamanni 

Family ya cika da Farin ciki

Abubakar ma har yanxu yananan

 Gaba daya ya qara shigewa jikin yan uwanshi

Tuni hutunsa ya qare Amman yaqi komawa yace yana son shima ya rayu da yan uwanshi

Kuma yana son ya jejje xiyara gun yan uwansu

Haka ya rinqa Jan su Yusuf da Ahmad suna kutsawa cikin yan uwa da abokan arziqi

Har qauyuka saida sukaje.


" shiko Yusuf yakan Dan lallaba ya dauke matarsa su arece

 hotel ya dirka mata qwoya suje sui ta macewa juna,

Gaba daya yanxu

Ya maidata

Fulawarsa abin qawanyarsa.


"Yau da dere

Suna parlon suna cike suna hira

Abubakar ya Dan gyara zama

Cikin

Kallon yan uwanna shi

Yace

'Ya Adam

Gobe nefa zamu je yolan

Dan

Inaga Na kusa komawa wurin aiki

Gashi Hamma Yucut kuma saura

2 weeks

Ku koma Saudia ko?

Kai ya gyada mai cikin

Tsurawa Dan uwana nashi ido

Yace

'Ko Sai yaushe zamu kuma haduwa ne Babiker kam?


"Cikin dry yace

'Wata qil har Abadan!

!Gaba daya suka zuba mai ido

Cikin

Fada baba bello yace

Kai Abubakar wannan wanne irin furucine

Ummi kuma

Kai ta rinqa juyawa

Tana

Allah ya rufamin asiri

Nenne CE tace

Amin

Rabbi ya hanemu qara ganin wani gibin,


" shiko dry yayi cikin cewa Yoh ai mutuwa ta zama dole dama rayuwa wata ran Farin ciki wata ran bakinci,

A haka suka watse 

Sai Yusuf da duk jikinsa

Ya mace

Ya kalli Aysha da ke shirin

Fita cikin

Muryar tausayi

Yace

Amrita zoo,

Kamar ta fita Sai kuma ta juyo

Cikin

Sanyi

Tazo

Gabanshi

Hannushi ya miqa mata

Cikin

Mutuwar jiki

Yace

' tai maka min in tashi

Kamo hannu tayi ta ja

Shiko ya yunquro da gyer

Ya miqe,

 Sai kuma 

Ya fiz gota jikinsa

Cikin

Rada yace

Muje ki taimaka kamin

Ko kuzarina zai dawo

Wala Allah d'umin jikin ki ya farfad'o dani

Haka ya jata har zuwa

Dakinshi....


By Garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣1⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*PURE  MOMENT OF LIFE WRITERS*

                 P.M.L.W


Kan gado suka zauna 

Cikin sanyin jiki

Ya zame ya kwanta kan cinyarta

Yasa hannu ya zagayo bayanta ya tura kanshi tsakiyar qirjinta yayi luf kamar mai bacci Sai numfashi yake sauk'ewa a hankali

Gaba daya jikinshi yayi nuk'ui


Ita kuwa  jikin gadon ta Dan jingina Dan har cikin ranta take jin tausayi Hamma Yusuf din nata

Hannu tasa ta tallabe kanshi

Kamar K'aramin yaro

Ya k'ara 

Nanuk'arta

 

A haka har zuwa wani d'an lkci

sannan ya d'an  d'ago cikin

tsura mata ido

yace 

"Amrita ki kwanta ko" 

Ido ta lumshe cikin

Sanyi ta zame tayi luf

Jikin pillows

Shima k'ara matsota yayi

A hankali ya manna ta jikinshi

Jikin a sanyaye ya sabule 

Rigar jikinta

Ya barta daga ita sai

d'an gajeren wondo

Shima hakan yake

Jawota jikinshi yayi

tare da da daura hannushi kan cikinta ya rink'a shafawa da d'an latsa cikin,

cikin rada yace

"A,ish 

Kina mana addu,a kuwa?

 A sanyaye tace

"Addu,ar me fa?" 

K'ara matsota yayi cikin d'an

Rawan jiki

yace " addu,ar samun ciki mana 

Wlh inason baby inson inga jinina gashi har yanxu shiru"

 

Baki ta d'an tab'e cikin

yanayin ba damuna tace " ciki kuma aihuwa  kuma yanzu gsky ni kam ban isaba"

 

!Cikin mmk da jin tsoro da zafin mgnar ya tashi zaune ya tallabota 

Murya Na rawa 

Yace 

"Ayshaaa Sai yaushe kenan?

Me kike nufi da baki isaba

Plss ki taimaka kar ki datsemin hanyar 

Samun cikar burina da zuriya ta

Yanxu ke ko 

Yusuf k'arami da Ahmad basa baki Sha,awa?

 

Juyawa tayi cikin

Yatsuna fuska tana " ni bacci nakeji"


Abin ya bashi haushi shiyasa cikin 

Hatsala ya juyota gareshi

A fad'ance yace

"Sau nawa nake sheida miki ba,a juya min baya

Meyasa bakya jin mgna ta 

Nace miki

Muddin muna kwance tare ki dena juya min baya ba tare da izinina ba wlh

  Aysha kina cutar da zuciya ta da jikina duk sanda kika juya min baya 

Ki gaya min mana inma kin gajine Sai mu canza gefen kwanciya mu duka ba tare da kin juya min baya ba" 

 Shiru tayi a ranta tana

Na shiga 3 da hali irin rin Na Hamma Yusuf

Yanxu ko kwanciya Sai ya tsara min,

Shiko

Juyata yayi shima ya juya

A hankali ya dire hannushi kan bres d'inta 

murya na rawa 

Yace

"A,ish dan Allah ki dena juya min baya 

Ki tausaya min wlh ni kadai nasan zafin da nakeji in kika bani baya.


Shiru tayi Sai 

Jikinta da ya fara sakewa da mimmik'ewa sabida sak'onnin Hamma ta da take karba

A hankali ta 

Narke cikin jikinsa

murya a sanyaye 

Tace 

" Hamma Yusuf bacci nakeji

Plxx kayi haquri

Yau ka barni Na huta"

Kai ya gyada mata 

Cikin

K'ara ruggumota 

Tare da rada mata

" ba abinda zan miki

Kiyi baccin ki"


 a haka suka kwana cikin jikin juna

Har zuwa safiya

 Bayan ya dawo masallaci

Cikin gida ya wuce

A parlon ya samu Abubakar da su 

Usman

Duk suna riqe da carbi

Abubakar ne ya kalli Yusuf cikin

Murmushi yace

"Hamma Yusuf

Gwara aje a fara shiri.fa 

Dan su Usman kam har sun shirya"

  

Fuska ya yamutsa tare da cewa

" Sara kunan yawo ai su da sunji tfya jikinsu har bari yake,

Dry Abubakar din yayi gami da cewa toh nima dai kaga tfyata bari inje in shirya,


Yana fita shima Yusuf ya fita bayan ya gaida iyayenshi.


Tsayuwa yayi yana k'arewa gadon kallo bata nan

Har ya juya Sai kuma ya  jita a toilet alamar wonka takeyi

 Zare jallabiyar jikinshi yayi gamida tura k'ofar

ya shiga

Itako jin motsin shigowarsa yasa ta bude ido

Lkci daya kuma Sai taji kunya ta rufeta ganin yadda ya tsura mata ido

Shiko matsota yayi ya tsuguna gefen ta

Yasa hannushi cikin ruwan

ya d'an d'ibo ya zuba mata kan kirjinta 

Yasa hannu ya dauko sabulu

cikin sulbi

Ya rinqa murza sabulu kan k'irjinta

yana shafawa,


A take yanayinshi ya canza ya fara piki piki da ido

Lips dinshi suka fara rawa lkci daya sukayi jaa

Tuni ya kamo gefen lips d'in ya fara tsotsa

Duk ya cika ruwan da kumfa

ita ko ido ta tsura mai a ranta tana jinjina halitta irin ta Hamma Yusuf

Mutum kamar maye.


Cikin sanyi taji

yana mgn


"Ohhh shmmmhhhht Amrita Sai kuma ta jishi

Tsulum cikin ruwan

Lkci gida kuma ya fara yamutsa ta

Tuni ya birki tata itama Sai

Lafewa take a jikinshi

K'ok'arinshi

ya samu kanta ya rege zafi

Ita kuwa tak'i

Sai nok'ewa take

 Suna cikin haka yaji ana buga musu k'ofa.

 aiko ta yamutsa ya cukuikuyeta son ranshi

Itama ta taimaka mai Don ta samu ya barta 

Sai da ya d'anji gamsuwa sannan

Ya fesa mata wonka Ragusa kanshi

Ya mik'e ruggume da a barsa

Sai hada fuska fa yayi

Shi a dole an takura shi

Ba a barshi ya shanaba.

Ta gane sarai

Shiyasa suna fita ta zura rigarta har taje bakin k'ofa

ya kirata

Cikin isa.

  

Gabanshi ta Dan tsaya

Shi kuwa mai ya mik'a mata

Fuska a hade

Yace

" kina k'o'karin tafiya

Wazai 

Shafa min mai? Karba tayi ciki 

 tura baki a ranta kuwa 

Cewa take 

Wlh Hamma Yusuf ya fiye kalen fitina,


Shiko zama yayi Ra's yana tsura mata ido

Dole ta rink'a shafamai

Har ta gama 

Y klta cikin

Sigar k'auna da Sha,awa

yace

" jeki shirya

Habitti yau zamuje

Yola"


Sosai taji dad'i  Dan batayi zaton dasu za,a jeba

Cikin happy

Ta tallabo

Kanshi

Ta hade bakinsu

Ta laso lips dinshi

Sannan

Ta sauk'o zuwa k'irjinshi

Ta rink'a shafa sumar k'irjin

Tana sakemai kiss tako ina

Sai kuma ta juya da gudu tayi cikin

Gida.


Shiko murmushi ya rink'ayi yana shafa sajenshi da k'irjinshi

Dan yasan guraren Na burge Ayshansa.


Haka dai suka kammalah

Shirin su.


K'arfe 9 dai dai

Sukayi SLM da iayensu

Sannan suka yi musu addu,a

Suka shiga

Mota suka tafi

Mota 2 ne

 1 Abubakar ke tuk'i

Ahmad Na gefenshi

Aysha da Maryam Na baya

Yusuf Na baya shima gefen Ayshan Sa

Sai dayan kuma

Adam ke tuk'i Amira Na gefenshi

Sai Usman da Rabi,u dake

Baya


Tafiya suke cikin nishadi

Motar su

Na biye da juna.


Sunyi tafiya mai d'an nisa har zuwa

 Wuraren *zim*

 Sun fara hank'o

*Mayo balwa*


Aysha da tun sanda sukayi nisa a tafiya jikinta

Ya mace tayi nuk'ui jikin

Mijinta

Sai nuk'urkusarsa take

Tana ita murd'a takeji

Aman kuwa yak'i zuwa Sai yanzu.


Ta samu ya tokarota

Cikin

Wahala.

Ta kamo hannushi ta rik'e 

Jikinta har rawa yake

Cikin

Kuka tace

"Hamma Yusuf

Amai zanyi

Amai"

Shiko Yusuf da gaba daya

Ya rude dukkan tausayinta ya cikashi

Cikin

Kula ya tallabota

Ahmad dake gaba rik'e da Yusuf k'arami

Ya zaro 

Blanket din yaron

Ya mik'a mata yana

"Hingo biyaye bata tayi aman a ciki"


Karba yayi ya shinfida kan cinyarsa.

 aiko ta rink'a zuba amai


Kafin kace kobo

Duk tayi laushi

Sai numfashi take sama sama

Maryam kam sai sannu

Take tayi mata

Shiko

Abubakar gudu ya k'ara yana

"Sorry sis

Bari nayi sauri mu isa

Asbiti ma zamu wuce


Cikin

Aman tace

A a ya Abubakar ni Ku kaini gida inma mutuwa zanyi Na mutu a gida.


Da sauri Yusuf ya ruqqumota cikin

Rawan murya yace

" a a insha Allah ba abinda zai sameki.


Haka dai suka isa

Itako gaba daya ta gala baita.

Dama tuni marya ta gayawa 

Baba Umar

Tuni

Shiko

Dr Umar ardo

Ya tanadi Norse

Guda biyu


Allah sarki Yusuf gaba daya ya rud'e 

Duk jikinshi

Amai 

Suna isa

Ya ciccibota

A parlon ya direta kan 3str

Ayyah. Hydar shima gaba daya ya rude

Fifita yake mata rik'e da hannuta

Yana sister

Ki bude idanki

Ga ya Hydar dinki

Goggo Aysha ma duk Sai

Jikinta ya mutu

Tana Farin cikin ganinsu gashi wannan Abu ya kassarasu.


Shi kam Yusuf

Tallabeta yayihar zuwa sanda

Baba Umar ya iso

Gida

Suna zuwa

Suka fara yiwa  Aysha

 gwoje-gwoje


Lkci daya

Suka gano

Ciwon dake haddasa mata aman

Cikin tsantsar Farin ciki

Baba Umar

Ya kalli

Yusuf

Da yayi kalan tausayi

Yace

"Congrats

Yusuf

Sai kuma yai

Murmushi ya fice

Yana 

An mata allurar bacci

Yancu tayi wonka

Tana tashi komai zai

Normal.

Abubakar ne 

Ya mik'e cikin Farin cikin ya ruggume Dan uwanshi

Yana dry

Yace " Alhamdulillah

Hamma Yusuf

Allah ya amsa addu,a ata

Ase ba zanyi

Kukan rashin aihuwa ba

Hamma Yusuf wannan cikin

Ko macece ko namiji ne 

Ni za,a bawashi

Shima Yusuf murna da tsantsar farinciki

Kawai Sai ya ruggume k'aninshi

Yana mai zubda qollan Farin ciki

Yana 

" Babiker

Na bakashi

Insha Allah kome aka samu.nakane

Babiker ba zakayi

Kukan rashin Aihuwa ba Dan uwana.


Allah sarki

Gaba daya Sai

Suka cika da Farin ciki da tausayi

Rashin aihuwar Abubakar

Hydar ma Sai

K'ollah yake sharewa

Yana

Allah ya raba su

Lfy

Shi mahaifi yarsu ya tuno.


Shiko Yusuf so yake ya ganshi dagashi

Sai Matarsa ya ruggume abarsa ya kula da ita

Ya riritata

Amman INA tuni

Goggo Aysha ta jata sunyi

Cikin

D'aki

Maryam da Amira ma suka bi bayan su


Itako Aysha

Sam batayi Farin ciki da cikinba

Kuka ta rink'ayi

Da k'er tayi

Wonka suka dawo

Parlon inda suke

Cike

Gaba daya Sai ya zama duk tattalinta suke

Amman a hakan shi oga gani yake an takurasu ne

Kukan da takeyi har cikin ransa yakejin

Kukan

Ita ko lkci daya bacci yayi gaba da ita bayan ta konta kan  3str

Haka dai

Sukuma sukayi ta hiransu da nishadi

Da Farin ciki

Tuni Goggo Aysha ta sheidawa su Nenne 

Ummi ko dad'i kamar bazata mutuba.


Kai sunyi

Farin ciki kam.

Shiko Yusuf a takure yake Sam

An hanashi

Matarsa

Yau kwanansu  2da zuwa

Bayan sun gama cin

Abinci

Sun waste

Yusuf ya koma bakin gate

Ya zauna kamar wani maraya

Tsaki yaja yafi a k'irga

A fili

Yace su wadannan basu da matsala.

Yana zaune Sai ga

Hydar da maryam

Sun shigo

Cikin

Hade fuska

Ya "cekai dady

Dayake haka yake kiran Hydar tunda shi tokwaran Abbanshi ne.


Da sauri ya iso gareshi

Cikin girmamawa yace

"Na,am Hamma Yusuf

Shiko fuska ya murtuk'e

Tare da cewa

In ka shiga kace

Aysha tazo

Ga lamido

Yazo dubata yana 

Part dinka.

Toh ya amsa cikin

Sauri ya juya

Ya tafi.

Shiko

Ya tafi part din Hydar din,


Cikin gida kuwa

Aysha tayi wonkanta ta gama shirin

Baccin Sai k'amshi

Take

Hydar ya shigo

Cikin

Xoleyarta yace

'Mai ciki

Kije

Ga Dan uwan Hamma Yusuf dinnan

Lamido on top yazo dubaki suna can part dina.

Aiko su Amira Sai dry

Itako

Jin haushin dry yasa ta xura k'aton

Hijabi

Tayi

Part din ya Hydar din.

SLM tayi ta shiga Sai kuma ta tsaya tana

Kallon

Komai Na parlon tsaf

Kamar dakin mace

A fili tace kai

Ya Hydar ba dai tsaf taba,

Shiko

Yusuf jin motsinta ya fito dashi

Itako tana shirin lek'a cikin

Bedroom din

Da sauri ta tsaya

Gani

Zasuci karo

Shiko

Cikin rawan jiki

Da hannu da wata iriyar muguwar Sha,awa

Ya fizgota jikinshi

Ya ruggume tare da lalubo....


By Garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👆🏻👆🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣2⃣Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Cikinta ya rink'a shafawa yana d'an murzawa lkci

d'aya kuma ya tallabo konta

ya zira harshensa cikin

Bakinta

ya llbo

nata 

 ya rink'a sarrafata da juyata cikin salon k'auna da begenta.


Tuni itama ta mace da salonsa ta biye mai  sai sauk'e numfashi yake yana binta da kissi tako ina  har zuwa wuyanta ya ganggaro cikinta

hannu yasa cikin rawan jiki ya d'aga y'ar rigar jikinta

kanshi ya manna kan cikin

yana shafawa 

gaba d'aya ya rud'e ya rudata Sai nishi yake,

Sam ya kasa mgn,


Ganin haka yasa ta kamo hannushi cikin hikima ta jashi zuwa kan gado

ta zaunar dashi,

Itama ta zauna gefenshi 

Sannan ta tallabo kanshi

Cikin rad'a tace

"Hamma Yusuf jikina ba k'arfi,

 duk kasala nakeji

bansan ya zanyi ba gaba daya banjin dadin rayuwa ta"..


Matsota jikinsa yayi

cikin rawan jiki

Ya ruggume ta jikinshi,

ya rink'a shafa jikinta'

Yana murza fatan cikinta

Cikin rad'a yace

" Ayyah Amrita Na sannu zai bari insha Allah

Babynmu ke saki kasala 

Zan mishi fada 

ya daina wahal min da noor hayat dina".

  

Baki ta d'an tura tace

"Gsky ni bazan iyaba

Wlh kasan yadda zakayi dani".


Jawota jikinshi yayi ya sabule y'ar rigar jijintan gaba d'aya sannan ya janye nashi

ya jawota suka kwanta,

Murya Na rawa

yace 

" Zo zonan kinji

Ya habitti 

zan miki Allurar kuzari

zaki daina jin kasala,

Ta nan kuma zan isar da saqona zuwa ga d'iyarmu ta dena wahal da Amminta".

 yana mgnar ne yana shafe 

Ababenshi da yayi kewarsu tsawon 5 days.

Itako hannushi ta riqe cikin

shogoba tana

"Hamma Yusuffffffffff

Bazan iyaba plx  ka barni Na huta jikina ba k'arfi".


Cikin rawar murya da kid'ima ya matsota 

Jiki a hargitse 

yace


" Dan Allah 

Na tuba plxx ki taimaka min wlh Na Gaza hak'ura jina nake kamar Na shekara ban rab'eki ba ke nake bege ke nake muradi".


Zuwa yanxu itama da kanta tasan tayi kewar mijinta

Na mijinki duniya dole ta yi cip

Tuni ta shiga maida mai martani tana mai mak'al k'alemai

Tana zuba mai shogoba shiko ya shiririce ya xauce kanta ya biye mata 

Ya zama tamkar sauna,

Haka dai a birkice suka mak'alewa 

Juna

Itama Aysha da kanta tasan tayi kewarsa Dan zuwa yanxu ta fara sabawa da nacin Hamma Yusuf

Dolenta take jajircewa Dan dauke mai buk'atunsa

gudunkar ya fada wata rayuwar,


Haka suka rink'a farantawa juna har zuwa wani lkci sannan suka sahirtawa juna,

Cikin gamsuwa ya mak'alota kan faffadan qirjinshi

ya daura hannushi daya kan cikinta d'ayan kuma 

ya daura kan bres dinta yana shafarsu da latsarsu

Cikin gamsuwa

Jiki a sake da d'an rada

yace 

"Amrita 

Kin San cewa cikinnan tun 

Fats night dinmu

Kika cabesa 

Kika ajiye min

Gsky Amrita 

Kin iya karbar sak'onnin 

Hamma Yusuf dinki",😍😎


Kanta ta tsune cikin

k'irjinshi tana 'kai Hamma Yusuf

ai kaine abin naka ba sauk'i

Ba dole ciki

ya shige ba 

Ka mammak'ale min

Ka hanani sakat".


Dry yayi ya shafa bres Dinta

Cikin

Nishadi

Yace


" ke dince

Tamkar xuma kike ba,a miki lasa kadan a gaji

Dole kike birki tani kike hanani sanin koniwaye kece kike dauke

Control dina

Muddin najiki cikin jikina

Macewa nakeyi".


Kanta ta kuma tsunewa tace


"Gsky Hamma Yusuf jarumtarka tayi yawa"


k'ara rufeta da k'irjinshi yayi


Yana "yanxu ma k'ari nakeso wlh A,ish"


Tallabe kanshi tayi

Cikin rada tace

" A,ish takace 

Keutar da rabbi ya maka ne Hamma Na ba wani hijabin a tsaka ninmu"


Wayyo Yusuf gaba d'aya 

ya haukace ya kid'ime da kala manta da salon da take mai tuni suka macewa juna,

Juyata yake iya son rensa.

Itako Sai zautar dashi take da salonta.


A haka suka kwana cikin nishadi,

Kashe gari da asuban fari ta koma cikin gida

a daki

Ta samu su Amira 

Maryam Na ganinta ta danyi dry

Cikin tsokana tace

" ni kam Aysha yaushe kunyarku ta bace ke da Hamma Yusuf?

Da gani ake duk kun fimu kunya haka shima Hamma Yusuf ake ganin yafi su ya Adam kunya

Amman yanxu duk kun fitsre idonku"


Kai ta Dan sunkuyar cikin

Sanyi tace "wlh

Tausayi ya bani

Maryam saifa kinga yadda ya zama

gaba daya tunda muka zo a takure yake

Nima kaina INA tunashi

Shifa Hamma Yusuf

Ko bacci

Bai yin mai dad'i in baya tare dani"

 

Dry Amira tayi cikin shewa tace

Yarinya kin zama yar hannu

Hamma Na ya gama cika aiki"

 

Hararanta tayi cikin

Kwanciya da shirin Dan yin bacci

Tana 

"Hmmm 

Hamma Yusuf

Da banne 

Nima bansan San da ya maidani haka ba"


 Maryam CE tace "gskyanki

Ki kula da mijinki

Dan wlh ni da kaina jiya Na tausayawa Hamma Yusuf saifa kinga

Yadda idanunshi suka koma kamar bugegge ase duk

Jarabar tsiya ke cinsa"

 Mari ta Dan d'aka mata cikin

Kunya tace "kin dai ji jiki

Namma yayanki ne"


haka dai sukayi ta dry.


Kwanansu 4 a Yola duk sun zaga dengi sunje har gidansu Ummi, sun yawata cikin Yola son ransa Yusuf ko ba ruwanshi kiran matarsa zai su Shana a d'akin

Haydar.


Sannan yau suka koma Taraba

Cikin kewar juna

Hydar

Kamar kar ya rabu dasu,


Sun dawo cikin Farin ciki

Gida akayi ta murna.


Aysha ko tunda ta dawo

Laulayi yace bas millah

Komai taci Sai ta Harar

Ga jiri

Ga yawan bacci

Gaba d'aya

Kowa ya maida kulanshi gareta

Ita kam 

 ji take kamar tayi hauka Dan wahala duk Sai taji ta tsani cikin

Da zaran ta keb'e da Hamma Yusuf Dinta tai ta kuka

Shiko Sai dai yayi ta lallabata da bata hak'uri

Dole tasa ya rink'a danne buk'atarsa,


Ya Abubakar ma kula yake bata sosai.


Yau saura kwana biyu

Abubakar ya koma duk ya gama shirinsa


Suma su Aysha saura 6 days su koma.


Yau tun da safe

Aysha keta fama da amai da jiri

Komai taci Sai yayi woje cikin kuwa har ya fara d'an tasawa

Dan yanxu ya kai 3 month.

 Zaune take Gaban

Hamma Yusuf din a parlon

Ummi ta d'aura kanta kan cinyarsa

Ummi dasu Abubakar da Usman da Ahmad duk suna

Zaune,


Kuka take tana matse cikin

Tana lumshe ido

Cikin

gala baita take cewa


"Wayyo jikina cikina

Ni kam naga ta kaina

Wlh Na gaji da cikin nan Hamma Yusuf wlh kasan yadda zaka min".


Kai ya sunkuyar cikin jin juya

Wato tun dashi ya mata cikin

Shi zaisan yadda zai mata gashi

Duk shi a matse yake dan ya fara carkewa kwana ba adadi taren suke kwana Amman dole yake barinta Dan tausayinta da yakeji

Itako Sai ta kwana nuk'urk'usansa

Ummi har tsoro takeji Aysha tace a d'akin ta zata kwana Dan hanata bacci takeyi

Shiyasa ita da kanta take cewa tashi kibi

Mijinki

Ni bazan iya sakalcin kunnan ba.


K'ara matsoshi tayi cikin

Jirin tace

"Wlh Na gaji ni zan San yadda zanyi"


Shiko ido ya tsura mata gami da 

Tashi yana cewa Ahmad

"B'iyaye mu tafi",

 Mik'ewa Ahmad yayi cikin

Dry yace "sannu ko

Auta zai bari kinji

In anyi Sa,a yana cika 4 month zai bari"


Baki ta tura tana 


"Inadai ya Ahmad harda kai kuke min dry"

Shiko Yusuf hannushi yaja suka fice 

d'akinsu sukaje suka Dan Sha hira sannan Ahmad ya tafi

Shiko yayi shirin kwanciyarsa ya d'an kwanta a cewarsa kafin

Sakaliyarsa ta zo.


Itako tana shiga

Ta zauna cikin

gajiya da wahalan cikin,

Tashi tayi ta d'auko 

Pose Dinta

Cikin tsoro da k'arfin guiwa

Ta balli mgnin da ta seya tun a Yola tsoro ya hanata Sha

Ido ta rumtse

Ta d'aga 

Harshenta tasa k'wayar

a kasan harshen ta

tana Haba wlh gwara Na huta Na gaji.


Wonka ta shiga cikin

K'arfin guiwar zata rebu da bone

Ta fito ta kimts tsaf

A fili

tace

"Yau bazanma je gun Hamma Yusuf ba".


Ta kwanta cikin

Sanyi lkci

Daya taji sanyi ya fara rufeta

a hankali ta lashi k'wayar taji

Ya fara narkewa

Ajiyar hrt ta sauk'e a take kuma taji

Jikinta ya fara rawa

Sai zufa ta fara ketowa a jikinta

A take kuma taji

Mararta ta carke

Sai wani irin suka takeyi

Tuni ai ta tashi ta zauna

Wasa wasa Sai k'aruwa abin yakeyi

Ban daki ta shiga Dan wani irin fitsari takeji tana tsuguna wa kuwa taji ta kasa yin fitsarin

ta tashi ma ta kasa

Sai 

dafe gini tayi ta samu ta mik'e,

 Shiko Yusuf gaba daya

Kewarta dakewar babynshi sun hanashi

Bacci

So yake yaji

d'umi cikin da nata d'umin

ga begenta dake cinsa,

Ya kirata yafi a k'irga bata d'agaba

So Sai yake zaton ko ta samu tayi

Baccin

Kar ya tada ita


A haka ya kwana cikin

Takura

A ranshi kuma yana ya gaji da hak'uri.


Ita kuwa

Aysha kafin zuwa

k'arfe 4 ta gama fita hayya cinta

duk ta birkice

Kuka takeyi cur cur

duk ta hargitse

dole taimako take nema

da tsoro ne ya hanata zuwa

d'akin Hamma Yusuf

Amman zuwa yanxu

ta manta menene tsoron

Dan azabar da takeji

Cikin wahala ta fice ta nufi part dinsu.


Shi kuwa 4 dai dai ya tafi masallaci d'an rege matsalarsa da nafilfili.


Tana shiga

tana ki ranshi

"Hamma Yusuf cikina marata zan mutu"

ganin baya nan yasa

ta zame kan gado ta rink'a murk'ususu.


Shi kuwa saida akayi sallah sannan ya wuce

Cikin

gida 

a parlon ya samu Ummi

Suna gaisawa ya d'an

Kalli Ummi a Dan kunyace cikin

d'an fara,a

yace

"Ummi yau dai Auta tayi bacci kenan?

Kallon shi tayi cikin

fahimta tace

"ba gunka take bane"?


Kai ya gyada cikin

Sanyi yace 


"a a bata jeba"


kitchen ta shiga tana "a a kake dai ka Duba!"


Toh yace gamida ficewa 

ya nufi 

d'akinshi kai tsaye


Yana shiga ya hanqota kan gado a hargitse

Sai murk'ususu take

Duk ta hargitse

Tana ganinshi

ta mik'e cikin

Wahala ta fada jikinshi

Shiko a buk'ace ya ruggume ta

yana "


"ohh Amrita I missi u plx ki tai maka"


Itako cikin

Kuka ta k'amk'ameshi

Ta manna hannushi kan mararta

tana 


"Wayyo Hamma Yusuf

Cikina marata zan mutu"


Cikin tsoro da firgicin

yedda yaji mararta tayi tauri ga wani irin zafi da marar tayi


ya tallabo kanta cikin tsura mata ido 

yace 

"Amrita

yaushe ya fara miki?

Kin gayawa Ummi kuwa?

ya akayi haka ?

Duk ya rude 

dai dai lkcin

taji wani irin

axaba da suka daya sok'i mararta

K'amk'ameshi

Tayi gami da sakin wani irin

k'ara

ta kuma bude

Baki zatayi

k'arar.


Shiko cikin kidima

ya zura harshensa cikin

Bakinta

nata harshen ya lalubo

har zai kamo harshen ta da nufin hanata kukan

Sai kuma ya tura harshensa k'asan nata

Dan jin wani irin d'and'ano

da ya bashi tsoro


Ido ya zaro cikin

Firgici ya tallabo kanta

Murya Na rawa

yace


" Aysha me kika Sha?

Me a k'asan harshen ki"?

waya baki mgninan?


ido ta tsura mai ciki tsoron

ganin yadda ya hargitse.

 Fixgota yayi cikin

rawan jiki yace

"Wanne Dan iskanne ya baki

wannan mgnin"?


 Kai ta rink'a juyawa cikin tsoro lkci

d'aya kuma ta sunkuyo

ta kalli cinyarta jin

damshi Na bin k'afarta.


Shima ido ya Sada k'asa ganin jininne

ya fidda  hankalinshi

Jikinsa


wata iriyar tsawa ya buga mata cikin

fizgo hannuta

yana 

" Aysha

Xubar min da cikina zakiyi

Cikina kika zubarmin?


Sai kuma ya jata da k'arfi ya nufi part din Ummi


A part din Ummin kuwa su Abubakar da Usman har dasu Ahmad da Adam suna 

Cike a parlon 

Cikin firgita da kidima

yana shiga da itaya angi.......


By Garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*®PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*

             P.M.L.W


Gaban Ummi ya jata suka tsaya 

murya Na rawa cikin

kidima yace

"Ummi kalli,

 kalli abinda Aysha ta aikata min"

Itako Aysha 

Sosai tsoron shi ya rufeta ganin yadda ya daburce

Shiyasa sai k'ok'arin k'wace hannuta take

tana ciccije lips dinta Dan azabar da mararta ke mata,

Ita ko Ummi ido ta zuba mai cikin rashin fahimta

Su Ahmad ma duk ido suka zuba musu cikin alamun tabbaya.


Ummi ce 

Tayi Dan ajiyar hrt cikin dan mmk tace


 "mene ta aika kuma? kai da baka rebo da fitina".


cikin takaici da zafin abin ya zame k'asa a hankali

murya Na rawa da alaman kuka

ya rik'o hannu Ummi

Cikin 

Cikar bakin ciki

Yace 

" Ummi

Ki kalli jikin Aysha fa Ummi cikina ta zubarmin

Ummi meyasa meyasa haka

Me laifin yarinyar da bata zo duniya ba me tayi da za,a kasheta 

Ko ni laifin me nayiwa Aysha da bazata ita yace min ba

Ummi inma laifi nane ai ba kan 'yata ya kamata Aysha ta rama ba"


Lkci daya kuma Sai hawaye shur shur a fuskarsa

Gaba d'aya

Su Ummi suka cika da Al,ajabi

Su Ahmad kuwa ganin hawaye a fuskar b'iyayenshi ya tabbatar abin ya girmama.

ya Abubakar ne ya mik'e cikin 

Zullumi

ya tsaya gaban Aysha fuska a tsorace 

yace "Auta 

dgske zubar da cikin kikayi gaya min gsky

dan Allah meyasa kika zubar da cikin da muka dade muna tsumayi 

Auta da gske kin kauda Farin cikin mu"?

Kai ta rink'a juyawa

tana matse ciki ga zufa dake keto mata tako ina ga jinin da takeji yana bulbulowa 

cikin wahalan tace


" a a ni ban zubar ba ba abinda nasha"


Cikin kad'uwa 

Ummi tace

"Dama ya za,ayi ta zubar da ciki

Inama zata San salon zubda ciki

yarinyar da ba abinda ta sani

Shi dai

fitina yakeji"


Shiko Yusuf cikin

Kuka kamar yaro

yace


 "wlh Ummi zubarwa tayi ai naga abinda tasha kuma Na jishi

Wlh zubarmin da jikina tayi

Ummi wlh kashe min 'ya tayi"


Ahmad ne ya dafeshi cikin

tausarsa yace


"B'iyaye ka nitsu

Mu tabbaya yeta

Dan ni inaga zaiyi wuya tasan yedda zata iya wannan abin"


cikin kad'uwa da jin ta kaicin 

yau Ahmad ma ya kasa gsktashi

ya kallesu

Cikin

Rawan murya 


"Yace 

Wlh xubarwa tayi

Ummi 

Gata Ku abinci keta"!

 

A hatsale Ummi tace "ni dai banga komaiba

Sai dai in Kaine zaka bin cike ta sannan mu kuma mu abinci keka"


Jin haka yasa shi mik'ewa jiki Na rawa

ya fixgota jikinshi

Ya tallabo kanta 

Cikin bakinta ya tura yatsarsa

Dan dauko guntuwar k'wayar Sai kuma yaji ta narke Sai dank'onta


A harzuk'e Ummi tace "kai tafibcan sake yarinya mu tafi asbiti ba abinda tasha zaka bita da mita bayan tana fama da azabarta"


rai a cushe ya k'ara jawota ya matsota jikinshi da k'arfi

bakinshi ya manna kan nata cikin

Rawan jiki ya dannan harshensa dai dai inda ta manna k'wayar ya rink'a goga harshensa

Sannan ya zaro harshen nasa cikin

carkewar murya ya zare harshen ya nunawa Ummi 

tare da cewa


"Ummi kinga ni ko kinga abin da ta manna a bakinta 

Biyaye ka duba,

 

Jiki a sanyaye Ummi ta tsura mai ido

ganin harshensa

yayi wani yellow

Abubakar kuma

Juyawa yayi cikin

Zubda qollah

ya zauna kan 1 str murya Na rawa 

Yace 


" Auta meyasa ya za,ayi ki zubda ciki

Kinsan illar hakan kuwa

Auta kisan kaifa me cikin ya miki"


Ahmad ko

Cikin takaici yace


"Aysha kinji kunya

Kin cutar da mutane da suka yerda dake wlh kin dasa mana takaici

a rayu kanmu 

Ke wacce iriyar zuciya gareki"


Shiko Yusuf k'ara matsota yayi

cikin

Rawan 

Murya yace


"Aysha kin cuceni kin cucu abinda zaki aifa

Har Gaban ubangiji Sai munyi hisabi

Kin kashe min y'a

 A,ish duk tsanar da kike min bai kyautu ya shafi jinina ba

Nasan dai nine byake so shiyasa har kika zubar min da ciki

Kin cutar da zuciya ta

Allah Sai ya saka min

Kin yaudari Ummi da ta dauko duk yerda ta baki"


Matseta yayi da k'arfi saida tayi

K'ara cikin zare ido

Yace 

"Wanne d'an iskanne ya saida miki mgnin? a ina yake? ki gayamin ko shi waye ne wlh Sai Na d'aureshi"


Ido ta zazzaro cikin

gala baita tace

Wayyo cikina zan mutu

Ummu cikina "


Kicin zafin nama Ummi tamik'e 

tazo gabansu 

Hannu ta d'aga cikin

Kid'ima ta yarfawa

Yusuf d'in

Wani wawan mari

ta tureshi gefe

tana fada cikin

Fushi

Tana


"Haba wannan wanne irin rashin imanine

yarinya Na fama da wahalar zuban ciki sannan kun tsare ta da bak'ak'en mgn ganu sannan kai harda matseta

Zubar cikifa yafi aihuwa wuya kashe min ita zakayi"?


Shi kam Yusuf dafe kunci yayi

cikin rawan jiki da tashin jijiyoyin jiki

Yana mai

zubda k'ollah,


Adam da tun dam'azu ya shigo yana jin duk abinda suke fada

Ganin marinnda aka kifawa Yusuf

Yasa shi shigowa cikin hatsala

yana shiga

Kan Aysha yayi

cikin harzuk'a

ya jawota ya rink'a yarfa mata maruka.

Ita kam yanzu tsoro da hawala sun dauke ta shiyasa ta fada jikin Ummi

tana mai kuka

Da cewa

Wayyo.ya Adam Na tuba 

Wlh bazan k'ara ba


Cikin Fushun

Ya k'ara yin kanta.


Shiko Yusuf cikin

Muryar kuka

yace "

Adam barta 

Ba komai Allah Na sane dani.


Allah sarki 

Gaba daya Sai jikinsu ya mutu

cikin kasala

Ahmad ya jasu suka tafi part dinsu

Adam da Ahmad suka rink'a tausarsa da bashi baki

Shi dai Yusuf sai k'ollah yake sharewa

Ya rik'o hannu 

Adam yana 

"Adam ba laifinta bane

'Kiyeyya CE ta sata haka Aysha bata sona ta tsaneni shiyasa bata son aihuwa dani

ni Na nawa kaina

tun da Na kasa sawa Aysha ta soni a ranta gashi k'iyeyyar ta shafi y'ayana"


  Ahmad ne ya rink'a juya kai yana 

"a a Yusuf Na tabbata Aysha Na sonka ka dena fadar haka"


Shiko kai ya jinjina tare da sauk'e ajiyar hrt.

A haka dai sukata bashi baki

Sannan suka samu ya Dan nitsu,


Itako Aysha Abu wasa wasa

Jinin ya balle ga ciwon mara kamar k'ara shi ake

kafin zuwa 9 Na dere duk ta fita hayya cinta

Dole Ummi ta kira Abubakar ya kaisu asbiti

dama tun safen Ummi tace suje ita tak'i tana tsoro kar mgnar taje kunnen Abba


Aiko suna zuwa asbiti akace Sai an mata wonkin ciki

Sannan Sai mijinta yazo

yasa hannu

Kuma gashin sun gano zunda cikin akayi ba zubar kanshi bane,

Abubakar yace 

Ayi komai

Amman Ummi tace a,a a dai je a gayawa mijinta

Dole Abubakar ya koma

Gida

yana zuwa

ya sameshi a harabar gidan yana zaune shi d'aya idanshi a rumtse

 A hankali ya zauna gefenshi

cikin sanyi

Yace


"Hamma Yusuf"

A hankali ya bude idon ya zubawa Dan uwanshi

Shiko Abubakar kai ya d'an gyada mai alamun kayi haquri

Cikin sanyin yace


"Hamma Yusuf dama Aysha ne muna asbiti so ance Sai kaje

Dan Sai an mata wonkin ciki"


Da sauri ya mik'e cikin zare ido

yace 

"a a ban yerda ba wanne k'atonne zai mata aikin ba wani aikin da za,ayi mata"


hannu ya mik'ewa Abubakar yace 

"Mu tafi"


Suna zuwa asbiti

da kanshi ya shiga d'akin da take Sai murk'usuwa take.

yana zuwa

Ya kamo hannuta

cikin sanyi ya Dan matse

Rigarta ya d'an d'aga

cikin ya tsurawa ido

Gamida shafa cikin

Lkci d'aya kuma

Idansa ya cika da k'ollah"

ya zauna gefen ta Abubakar ya kira cikin

Sauri yace yaje gidaya kamo mai 

Zam zam da Zuma da garin habba.


Toh yace tare da juyawa ya fita

Shiko cikin 

Ya rink'a

Shafawa

yana kauda kai

Ita kuwa

Duk da wahalar tana ganinshi

Sai kife kanta take

A haka har Abubakar ya dawo

Shi da kanshi ya

Hada cikin

Sanyi yace

Amrita

Ido ta bude a hankali ta tsura mai ido

LLkc d'aya taji tausayinsa Na ratsata

Duk ya fige a wuni d'aya

Kai ta sunkuyar ido Na zubda k'ollah

Matsota ya kuma yi

ya mik'a mata 

Karba tayi tasha.

            ****

Lkci d'aya ta fara jin sanyin ciwon

Shiko tana Sha ya fita a wojen yacewa Ummi

Ku dawo gida kawai ba komai Dr yace ya rigada cikin ya fadi

Haka kuwa suka dawo gida


Ummi ta rink'a bata kula ta mu samman

 Shi ko Yusuf tun daga ranar ya dena shiga d'akin Ummi

Adam fushi yayi da ita Ahmad ma bai ko amsa gaisuwarta


Ummi ko tun tana jin kunyar ta har ta saki Dan ko a fuska bata taba nuna mata ba

Amman tana jin kunyar abin kam.


Yau kwananta 3 kuma jikinta ya d'an worwore

da safe .

Tana zaune

A dakin Ummi

Tana goge kayan Yusuf k'arami

Taji slmar 

Hamma Yusuf din nata


A hankali ta d'ago kai

ta tsura mai ido ya d'an rame Amman kuwa yayi wani irin kyau Sai kuma yanayin shi Na da  suka dawo Sam ba wolwola a fuskarsa ko fara,a mishkilanci tab fuskarsa kallon shi take ba ko kifta ido.


Shiko a hankali ya zauna can gefe

Gamida zaro phone dinshi

ya kara a kunne

A hankali yace

Ummi gani nazo ina jiranki

Sai kuma ya katse

 kiran ya zauna yana latsa phone dinshi din.


 cikin sanyi

tace ("Jam bandu na Hamma Yusuf ")

Ina kwana Hamma Yusuf.

Bai kulata ba sai kallonta da yayi ta gefen ido

Dai dai lkcin kuma Adam da Ahmad suka shigo

Kai ta sunkuyar tana mai gaidasu Amman duk ba Wanda ya kulata

Sai juyawa da Ahmad yayi yana

Biyaye bari inje gun Abba kafin ya fita don tare zamu fita

Mik'ewa tayi da sauri tabi bayanshi  cikin

Sanyi tace

Ya Ahmad ga kayan Lamd'o a kaimai

da yake bata kiranshi Yusuf sai Lamd'o take cemai  shi ko Ahmad yamutsa fuska yayi cikin

Gyatsine yace

"  ni Na kawo kyyane bare in meyar"

Da sauri tace Ayyah ya Ahmad kayi haquri ka kai musu

Tsawa yayi mata cikin fita yana 

In sun dame ki Ki jefar dasu Dan nasan ba son harkar yara kike ba.


Jiki a mace ta juya kenan

Sukaci karo kicibis

Ta fada jikinshi

Cikin sanyin ta tura kanta a faffadan qirjinshi tare da lumshe idan ta shima jiki a mace...


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*®PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*

             P.M.L.W


Gaban Ummi ya jata suka tsaya 

murya Na rawa cikin

kidima yace

"Ummi kalli,

 kalli abinda Aysha ta aikata min"

Itako Aysha 

Sosai tsoron shi ya rufeta ganin yadda ya daburce

Shiyasa sai k'ok'arin k'wace hannuta take

tana ciccije lips dinta Dan azabar da mararta ke mata,

Ita ko Ummi ido ta zuba mai cikin rashin fahimta

Su Ahmad ma duk ido suka zuba musu cikin alamun tabbaya.


Ummi ce 

Tayi Dan ajiyar hrt cikin dan mmk tace


 "mene ta aika kuma? kai da baka rebo da fitina".


cikin takaici da zafin abin ya zame k'asa a hankali

murya Na rawa da alaman kuka

ya rik'o hannu Ummi

Cikin 

Cikar bakin ciki

Yace 

" Ummi

Ki kalli jikin Aysha fa Ummi cikina ta zubarmin

Ummi meyasa meyasa haka

Me laifin yarinyar da bata zo duniya ba me tayi da za,a kasheta 

Ko ni laifin me nayiwa Aysha da bazata ita yace min ba

Ummi inma laifi nane ai ba kan 'yata ya kamata Aysha ta rama ba"


Lkci daya kuma Sai hawaye shur shur a fuskarsa

Gaba d'aya

Su Ummi suka cika da Al,ajabi

Su Ahmad kuwa ganin hawaye a fuskar b'iyayenshi ya tabbatar abin ya girmama.

ya Abubakar ne ya mik'e cikin 

Zullumi

ya tsaya gaban Aysha fuska a tsorace 

yace "Auta 

dgske zubar da cikin kikayi gaya min gsky

dan Allah meyasa kika zubar da cikin da muka dade muna tsumayi 

Auta da gske kin kauda Farin cikin mu"?

Kai ta rink'a juyawa

tana matse ciki ga zufa dake keto mata tako ina ga jinin da takeji yana bulbulowa 

cikin wahalan tace


" a a ni ban zubar ba ba abinda nasha"


Cikin kad'uwa 

Ummi tace

"Dama ya za,ayi ta zubar da ciki

Inama zata San salon zubda ciki

yarinyar da ba abinda ta sani

Shi dai

fitina yakeji"


Shiko Yusuf cikin

Kuka kamar yaro

yace


 "wlh Ummi zubarwa tayi ai naga abinda tasha kuma Na jishi

Wlh zubarmin da jikina tayi

Ummi wlh kashe min 'ya tayi"


Ahmad ne ya dafeshi cikin

tausarsa yace


"B'iyaye ka nitsu

Mu tabbaya yeta

Dan ni inaga zaiyi wuya tasan yedda zata iya wannan abin"


cikin kad'uwa da jin ta kaicin 

yau Ahmad ma ya kasa gsktashi

ya kallesu

Cikin

Rawan murya 


"Yace 

Wlh zubarwa tayi

Ummi, 

Gatanan  a bincike ta"

 

A hatsale Ummi tace "ni dai banga komaiba

Sai dai in Kaine zaka bin cike ta sannan mu kuma mu abinci keka"


Jin haka yasa shi mik'ewa jiki Na rawa

ya fizgota jikinshi

Ya tallabo kanta 

Cikin bakinta ya tura yatsarsa

Dan dauko guntuwar k'wayar Sai kuma yaji ta narke Sai dank'onta


A harzuk'e Ummi tace "kai tafibcan sake yarinya mu tafi asbiti ba abinda tasha zaka bita da mita bayan tana fama da azabarta"


rai a cushe ya k'ara jawota ya matsota jikinshi da k'arfi

bakinshi ya manna kan nata cikin

rawan jiki ya dannan harshensa dai dai inda ta manna k'wayar ya rink'a goga harshensa

Sannan ya zaro harshen nasa cikin

carkewar murya ya zare harshen ya nunawa Ummi 

tare da cewa


"Ummi kinga ni ko kinga abin da ta manna a bakinta 

Biyaye ka duba,

 

Jiki a sanyaye Ummi ta tsura mai ido

ganin harshensa

yayi wani yellow

Abubakar kuma

Juyawa yayi cikin

Zubda qollah

ya zauna kan 1 str murya Na rawa 

Yace 


" Auta meyasa ya za,ayi ki zubda ciki

Kinsan illar hakan kuwa

Auta kisan kaifa me cikin ya miki"


Ahmad ko

Cikin takaici yace


"Aysha kinji kunya

Kin cutar da mutane da suka yerda dake wlh kin dasa mana takaici

a rayu kanmu 

Ke wacce iriyar zuciya gareki"


Shiko Yusuf k'ara matsota yayi

cikin

rawan 

Murya yace


"Aysha kin cuceni kin cucu abinda zaki haifa

Har Gaban ubangiji Sai munyi hisabi

Kin kashe min y'a

 A,ish duk tsanar da kike min bai kyautu ya shafi jinina ba

Nasan dai nine byake so shiyasa har kika zubar min da ciki

Kin cutar da zuciya ta

Allah Sai ya saka min

Kin yaudari Ummi da ta dauko duk yarda ta baki"


Matseta yayi da k'arfi saida tayi

K'ara cikin zare ido

Yace 

"Wanne d'an iskanne ya saida miki mgnin? a ina yake? ki gayamin ko shi waye ne wlh Sai Na d'aureshi"


Ido ta zazzaro cikin

gala baita tace

Wayyo cikina zan mutu

Ummu cikina "


Kicin zafin nama Ummi tamik'e 

tazo gabansu 

Hannu ta d'aga cikin

Kid'ima ta yarfawa

Yusuf d'in

Wani wawan mari

ta tureshi gefe

tana fada cikin

Fushi

Tana


"Haba wannan wanne irin rashin imanine

yarinya Na fama da wahalar zuban ciki sannan kun tsare ta da bak'ak'en mgn ganu sannan kai harda matseta

Zubar cikifa yafi Haihuwa wuya kashe min ita zakayi"?


Shi kam Yusuf dafe kunci yayi

cikin rawan jiki da tashin jijiyoyin jiki

Yana mai

zubda k'ollah,


Adam da tun dam'azu ya shigo yana jin duk abinda suke fada

Ganin marinnda aka kifawa Yusuf

Yasa shi shigowa cikin hatsala

yana shiga

Kan Aysha yayi

cikin harzuk'a

ya jawota ya rink'a yarfa mata maruka.

Ita kam yanzu tsoro da hawala sun dauke ta shiyasa ta fada jikin Ummi

tana mai kuka

Da cewa

Wayyo.ya Adam Na tuba 

Wlh bazan k'ara ba


Cikin Fushun

Ya k'ara yin kanta.


Shiko Yusuf cikin

Muryar kuka

yace "

Adam barta 

Ba komai Allah Na sane dani.


Allah sarki 

Gaba daya Sai jikinsu ya mutu

cikin kasala

Ahmad ya jasu suka tafi part dinsu

Adam da Ahmad suka rink'a tausarsa da bashi baki

Shi dai Yusuf sai k'ollah yake sharewa

Ya rik'o hannu 

Adam yana 

"Adam ba laifinta bane

'Kiyeyya CE ta sata haka Aysha bata sona ta tsaneni shiyasa bata son Haihuwa dani

ni Na nawa kaina

tun da Na kasa sawa Aysha ta soni a ranta gashi k'iyeyyar ta shafi y'ayana"


  Ahmad ne ya rink'a juya kai yana 

"a a Yusuf Na tabbata Aysha Na sonka ka dena fadar haka"


Shiko kai ya jinjina tare da sauk'e ajiyar hrt.

A haka dai sukata bashi baki

Sannan suka samu ya Dan nitsu,


Itako Aysha Abu wasa wasa

Jinin ya balle ga ciwon mara kamar k'ara shi ake

kafin zuwa 9 Na dere duk ta fita hayya cinta

Dole Ummi ta kira Abubakar ya kaisu asbiti

dama tun safen Ummi tace suje ita tak'i tana tsoro kar mgnar taje kunnen Abba


Aiko suna zuwa asbiti akace Sai an mata wonkin ciki

Sannan Sai mijinta yazo

yasa hannu

Kuma gashin sun gano zunda cikin akayi ba zubar kanshi bane,

Abubakar yace 

Ayi komai

Amman Ummi tace a,a a dai je a gayawa mijinta

Dole Abubakar ya koma

Gida

yana zuwa

ya sameshi a harabar gidan yana zaune shi d'aya idanshi a rumtse

 A hankali ya zauna gefenshi

cikin sanyi

Yace


"Hamma Yusuf"

A hankali ya bude idon ya zubawa Dan uwanshi

Shiko Abubakar kai ya d'an gyada mai alamun kayi haquri

Cikin sanyin yace


"Hamma Yusuf dama Aysha ne muna asbiti so ance Sai kaje

Dan Sai an mata wonkin ciki"


Da sauri ya mik'e cikin zare ido

yace 

"a a ban yerda ba wanne k'atonne zai mata aikin ba wani aikin da za,ayi mata"


hannu ya mik'ewa Abubakar yace 

"Mu tafi"


Suna zuwa asbiti

da kanshi ya shiga d'akin da take Sai murk'usuwa take.

yana zuwa

Ya kamo hannuta

cikin sanyi ya Dan matse

Rigarta ya d'an d'aga

cikin ya tsurawa ido

Gamida shafa cikin

Lkci d'aya kuma

Idansa ya cika da k'ollah"

ya zauna gefen ta Abubakar ya kira cikin

Sauri yace yaje gidaya kamo mai 

Zam zam da Zuma da garin habba.


Toh yace tare da juyawa ya fita

Shiko cikin 

Ya rink'a

Shafawa

yana kauda kai

Ita kuwa

Duk da wahalar tana ganinshi

Sai kife kanta take

A haka har Abubakar ya dawo

Shi da kanshi ya

Hada cikin

Sanyi yace

Amrita

Ido ta bude a hankali ta tsura mai ido

LLkc d'aya taji tausayinsa Na ratsata

Duk ya fige a wuni d'aya

Kai ta sunkuyar ido Na zubda k'ollah

Matsota ya kuma yi

ya mik'a mata 

Karba tayi tasha.

            ****

Lkci d'aya ta fara jin sanyin ciwon

Shiko tana Sha ya fita a wojen yacewa Ummi

Ku dawo gida kawai ba komai Dr yace ya rigada cikin ya fadi

Haka kuwa suka dawo gida


Ummi ta rink'a bata kula ta mu samman

 Shi ko Yusuf tun daga ranar ya dena shiga d'akin Ummi

Adam fushi yayi da ita Ahmad ma bai ko amsa gaisuwarta


Ummi ko tun tana jin kunyar ta har ta saki Dan ko a fuska bata taba nuna mata ba

Amman tana jin kunyar abin kam.


Yau kwananta 3 kuma jikinta ya d'an worwore

da safe .

Tana zaune

A dakin Ummi

Tana goge kayan Yusuf k'arami

Taji slmar 

Hamma Yusuf din nata


A hankali ta d'ago kai

ta tsura mai ido ya d'an rame Amman kuwa yayi wani irin kyau Sai kuma yanayin shi Na da  suka dawo Sam ba wolwola a fuskarsa ko fara,a mishkilanci tab fuskarsa kallon shi take ba ko kifta ido.


Shiko a hankali ya zauna can gefe

Gamida zaro phone dinshi

ya kara a kunne

A hankali yace

Ummi gani nazo ina jiranki

Sai kuma ya katse

 kiran ya zauna yana latsa phone dinshi din.


 cikin sanyi

tace ("Jam bandu na Hamma Yusuf ")

Ina kwana Hamma Yusuf.

Bai kulata ba sai kallonta da yayi ta gefen ido

Dai dai lkcin kuma Adam da Ahmad suka shigo

Kai ta sunkuyar tana mai gaidasu Amman duk ba Wanda ya kulata

Sai juyawa da Ahmad yayi yana

Biyaye bari inje gun Abba kafin ya fita don tare zamu fita

Mik'ewa tayi da sauri tabi bayanshi  cikin

Sanyi tace

Ya Ahmad ga kayan Lamd'o a kaimai

da yake bata kiranshi Yusuf sai Lamd'o take cemai  shi ko Ahmad yamutsa fuska yayi cikin

Gyatsine yace

"  ni Na kawo kyyane bare in meyar"

Da sauri tace Ayyah ya Ahmad kayi haquri ka kai musu

Tsawa yayi mata cikin fita yana 

In sun dame ki Ki jefar dasu Dan nasan ba son harkar yara kike ba.


Jiki a mace ta juya kenan

Sukaci karo kicibis

Ta fada jikinshi

Cikin sanyin ta tura kanta a faffadan qirjinshi tare da lumshe idan ta shima jiki a mace...


By garkuwan Fulani

[4/9, 2:26 PM] ‪+234 909 785 3276‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👆🏻👆🏻

*MI,WASMITI* page1⃣1⃣4⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*®PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*

        P.M.L.W


Yasa hannu ya d'an tureta cikin murtuqe fuska

ya rab'a gefen ta ya wuce.

Jikin gini ta jingina rik'e da kayan

Yusuf k'arami 

gaba d'aya 

Salon rayuwar ta canza mata

bata jin dad'in 

Rayuwar Sam.

Adam dake gefen can kan kujera a zaune

ya tsura mata ido

cikin hada fuska yakirata

Jiki ba kuzari tazo ta zauna gefenshi

ta sad'a kai 

k'asa

Shima shirun yayi Na d'an wani lkci

sannan cikin

ta kaici.

yace 

"Aysha 

yanzu kinyiwa kanki adalci?

Kinyiwa mijinki adalci?

Kin yiwa Ummi adalci?

Aysha butulcin ki ya sani jin kunya wlh

Aysha kituna fa tsawon shekara 19 ni da kaina ban San cewa ba Ummi bace ta Haifeki bare Hydar bare ke 

bamu taba ganin maraicin rashin mahaifiyarmu a kanmuba bare a kanki

Ummi ta rik'eki ta soki fiye da yadda taso 'yayanta Na cikinta

A kullum ta kansa Yusuf cikin fushi sabida ke 

Yusuf da girmanshi bai wuce mari a gun Ummi ba saboda ke 

Haba Aysha yanxu kinyiwa 

Yusuf adalci kinyiwa 

Ummi kawaici"?

 

Kai ta jinjina cikin zubda qollah

tana girgiza kai

a lamar a,a.


cikin rawan murya yaci gaba da cewa


" a zaton ki Ummi bata son

D'an tane ?

Shine fa d'anta Na fari a duniya 

a tunanki bata son taga jininshi ne 

Aysha yanxu duk kawaicin da bayin Allahnan suka miki da abinda zaki saka musu

Ki tunafa irin son dasu Abba suke gwada miki 

kab family dinmu ba Wanda akewa son da ake miki

Duk son da akewa mahaifiyar mu Sai da aka ninkashi a kanki

Aysha ko sonne da gata yasa kike shirin tozarta mu

Wato baki da mai miki fada ko"?


kuka ta kama sosai tana 

"a,a 

ya Adam"


Cikin cije lips d'inshi

yace 

"Haka ne mana Aysha

Kuma tunda hakane 

Ni Na kira 

Babanmu Na gaya mai abinda kikayi

Na kuma fad'awa Hydar yanxu haka sun taso daga Yola

So Sai ki tanadi abinda zaki gaya musu

dan Na lura mu duk kin raina mu"


Zuwa yanxu kukan take sosai

a hankali ta matsoshi cikin kuka ta d'aura kanta 

kan guiwarsa

Murya na rawa

Tace


"Ayyah ya Adam dan Allah kuyi haquri

wlh bazan k'ara ba

Ka kira baba kace mai wlh bazan sakeba kuyi haquri dan Allah" 


 Ture kanta yayi cikin had'a fuska

Ya mik'e tare da cewa


"gafarar Allah da mijinki ya kamata ki nema ba ni ba 

Wlh ki gyara ala qarki da Yusuf in ba hakaba wlh ba ruwana da ke"


Yana kaiwa nan ya fice abinsa.


A parlon

ya samesu Suna

zaune Ummi ta kawo musu breakfast

ya zauna gefen Abubakar

Ummi dake ajiye musu pilet tana


"a Adam dama kana cikine?

"cikin girmamawa yace Ehh Ummi ai tare muke da Ahmad"


Aiko naji dad'i yau yarana duk a guna zasuyi kari"


  Abubakar

"Yace gsky kam Ummi yau kin hada yaranki"


Dry tayi cikin nufan d'akin tana bari Aysha tazo

Ta hada muku tea.


Ita kuwa Aysha a d'akin tasha kukanta ita bama abin da yafi cinta kamar Fushun Hamma Yusuf d'in nata 

Gaba d'aya ta resa sukuni

Kukan tayi mai isarta sannan ta kifa kanta kan kujerar 

A hakan Ummi ta sameta

Cikin kula tace

"Autan Ummi tashi kije ki hadawa yayunkin tea

Ko bacci kikeyi"?


cikin kauda kai ta goge fuska tace a,a Ummi bari inje

Cikin boye fuska ta fita

Dan kar Ummin taga halin da take ciki.


A parlon

Cikin sanyi ta zauna gefen Hamma Yusuf din ta jawo

Cups d'in

da pilets d'in 

Abubakar ta fara sawa ta Dan tura mai gabanshi cikin sanyi tace

" ya Abubakar ina kwana"

 Fuska a d'an sake yace lfy ya jikin dai?


"da sauk'i"

 tace cikin Sada kai k'asa


Sannan ta hadawa Ahmad da Adam ta mik'a 

Musu ba tare da kallonta ba suka d'an fara cin abincin,


A hankali taja d'aya cup d'in

da pilet din ta hada mai tea d'in 

ta zuba mai cibs

da d'an k'oi

Ta d'an sunkuyo ta gefenshi cikin jin wani irin tsoro ne ko kunyace ko Nadama ce ta kasa ganewa

A hankali tace


"Hamma Yusuf

Ur breakfast is ready"


kanshi a k'asa tamkar bai jita ba

 

Jiki a mace ta Dan juya gareshi

cikin sanyi tace


"Hamma Yusuf

zaiyi sanyifa"

 

Bai kulata ba sai phone dinshi da ya d'auka ya fara  latsawa

Ganin haka yasa

ta d'an tura hannuta ta k'asan

darning d'in ta d'aura hannuta kan cinyarsa cikin

sanyi ta rink'a 

murza cinyar tashi 

tare da d'an kauda kanta tana 


"Hamma Yusuf ko wani Abu kakeso in defema"


kai ya d'ago cikin 

Murtuqe fuska ya d'ago ya watsa mata harara 

Har saida taji ta kware da yawun bakinta da sauri ta janye hannuta daga jikinshi

Shiko mik'ewa yayi cikin

Jan tsaki 

da k'ara mata wani irin kallo

Itako cikin sauri tayi k'asa da kanta.


Kan kujera yaje ya zauna yana

B'iyaye 


"Lkci Na tfy fa Abba Na jiranka"


Adam ne ya mik'e cikin

d'an sakin fuska yace


"Yusuf Ko zamuje kaci 

girkin 

Miraa?


baki ya d'an tabe cikin sanyi yace,


"Azumi  nakeyi fa"

 

Ido Ahmad ya tsura mai Dan yasan abin da ya sashi cikin halinga 

Lkci d'aya ya k'ara jin haushin Aysha

A haka shima ya mik'e tare da cewa

B'iyaye bari in wuce gun abban.


A haka sukayi part dinshi shi da Abubakar da Adam 

A haka suka d'anyi ta hira

Har zuwa

2 dai suka fito

Bayan sunyi sallah

 A farfajiyar gidan suka samu baba Umar da Hydar sun iso tare da Abba 

Suna ganin su sukaje suka tarbesu cikin jin dadin ganin juna

 Parlon baba bello suka wuce.


Bayan sun gaggaisa

 Baba Umar ya kalli Yusuf dake gefenshi cikin

Sanyi da ta kaici

yace 


"Yusuf kayi haquri insha Allah ubangiji Na bayanka

Kuma bazaka tabeba insha Allah zan d'auki mata ki kan 

Wannan mugun abin da Aysha ta aikata ma"


Baba bello ne yayi gyaran murya cikin

Kallon Dr Umar

yace

" mu bazamu iya gyarawa ba kenan Umar?

Kana nufin mu Aysha tafi k'arfinmu ne?


kai ya d'aga cikin sauri

yace 

'A a wlh ba haka bane Yaya bello

Wlh rai nane ya b'aci matuk' gaya

Amman ni ban tunanin kun kasa a kanta

Amman a gsky gatar tayi yawa har ta fara sata kauce hanya Dan ganin ba mai tsananta mata"


Ajiyar hrt baba bello ya sauqe cikin sanyi yace toh ko in haka ne ka barni da ita.

zamu d'auki mataki

kar kayi mata mgn Dan yanzu bata worwore sosaima tukun"


Adam ne 

ya hada fuska tare da cewa

Wlh baba ni da zaku barni da nasan yedda zanyi da ita"


Hydar kuma cewa yayi ni wlh 

banyi zaton haka daga gareta ba

Naji zafin abin a raina

yarinya ai ba hakane a kantaba"


Shi dai Yusuf

Ido kawai yake binsu dashi 

A ranshi kuwa cewa yake


Koma dai me akayi ai ta rigada ta cutar dani ta gama kuntata min cikin kuma ba dawowa zaiyi ba gwara a barta kar a k'ara min zafi  2.


Baba bello kuma dole ya hana baba Umar mgn


Koda aka kirata tazo su gaisa zasu juya Yola yau din.


Gaba d'aya cikinta ya d'uri ruwa

tana shiga ta zauna gefen ya Hydar din nata

Tana 

"ya Hydar barka da zuwa"

Ko kallonta baiyi ba

Baba Umar d'inma  

da gyer yamsa gaisuwarta

Ya bud'i baki zai fad'a kenan

Baba bello yace 

"A a bamuyi haka da kaiba

Ke Aysha tashi ki tafi

aiko cikin murna ta fita Dan ta tsorita

gashi duk kunyar kowa takeji.


A haka suma suka juya suka tafi.


Biyar dai dai Na yamma

Yusuf ya shiga kitchen din Ummi yana

Kiranta cikin

yanayinshi Na  rashin wolwola

yana

" Ummee 

Ummi dake tare da Aysha a kitchen d'in

ta amsa mai tare da cewa mene Na kiran nan"?

K'ara hada fuska yayi ganin Ayshan Na gun

cikin juyawa yace

"Ummi dama abin buda baki nake son ki had'a min Dan naga lkci kar ya k'ure'


Toh tace tare da


 "cewa Aysha tashi

ki fara hada mai Dan INA da aiki da yawa ki daura mai kunun nono nasan yana so gashi dama Hydar ya kawo mana sabon nono

Maza mik'e"


Cikin sanyi ta mik'e 

Shiko da sauri

ya CE 

"Ban so a bari zanje gidan Anuty Sadiya ni wlh Ummi kin sani banson jogolgole da kwabe"

Yana fadin haka ya juya

Ita kuwa ido ta tsurawa k'eyarsa da gashin kanshi yayi luf a kwance

Ummi ko cewa tayi

Kiyi Aysha ki kaimai in yaga dama ya zubar,

Ita a nata tsarin

In ba haduwa sukeba bazamu dai dai taba

ta kuma ga alama Yusuf fushi mai tsanani yake,


Haka kuwa akayi ta hada mai komai


Ana fara kiran sallah

ta hada ta kaimai

d'akin ba kowa shiru

cikin kewar d'akin da mai d'akin ta 

har renta take jin kewar Hamma Yusuf d'in nata

Tayi kewar komai nashi.

ajiyewa tayi can gefe sannan

ta tsurawa d'akin ido

Komai nan tsaf Sai

Kan mirror da ya hargitse da kolaben turaruka

Ganin haka yasa ta tattara ta goge ta jerasu sannan ta canxa mai bedsheet da blanket ta shinfid'eshi ta share d'akin

ta koma cikin gida ta dauko d'an kasko ta samai turaren wuta mai d'an Karen k'amshi da sanyi

Ta sassake labulayen sannan ta kunna A.C

Ta kashe wuta ta kunna Na jikin wani fulawa

Wutan read Sai ya haska kalan komai Na d'akin

Sannan ta juya ta tafi

A cikin gida ta dama mai fura da nono mai sanyi ta Sa mai k'ank'ara a ciki.


Sannan ta zauna ta d'an gyara gashinta

Ummi dai Sai binta da ido takeyi

Tana gamawa wonka ta shiga ta shirya cikin

Rigar baccinta yar k'arama mai laushi da sulbi

ta fesa turaruka sannan ta konta

tare da cewa Ummi


"saida safe"

 Itako Ummi dry tayi cikin gano logonta tace


"Allah bamu Alkhairi"

Ta fita


Shiko Yusuf gidan Anuty Sadiya yaje 

Sukayi ta hira da Baban Yumin bayan sunyi buda bakin.


8 dai dai ya biya gidan kaka

Dan dama ya kirata ta dama mai tura

Yana karba a gora ya juya ya fita gidan ya nufa

Da sauri d'an hadarin daya taso

Sai iskar dake kad'awa

Yana isa ya rink'a sauk'e numfashi da shak'ar k'amshin dakin sosai yaji Dan sanyi a ranshi

Wonka yayi cikin jin iska Na ratsashi ya shirya ya kwanta

duk bai lura da gyaran da akayi maiba  bare yaga kulas din abincin

Gajiyar azumi tasa lkci d'aya bacci ya d'ebeshi

Gashi albarka cin azumin ya samu raunin abinda ke hanashi bacci.


Itako Aysha Ummi Na fita ta nufi dakin nasu

Cikin Sa,a ko ta samu bai rufe k'ofarba shiga tayi cikin hamdala sannan ta rufe k'ofar.


Kai tsaye  cikin d'akin ta shige

hangoshi tayi kwance cikin blanket yayi luf yana baccinsa

Samun haka

yasa ta sauk'e ajiyar hrt

gamida zare hijabin jikinta

A hankali ta haura kan gadon

cikin sanyi da kewar Hamma Yusuf d'in nata da kewar salon shi da tsarinshi da 

Begenshi

ta raba jikinshi

ta manna k'irjinta kan k'irjinshi

ta tura hannuta cikin gashin kanshi

Cikin hikima ta murza cinyarta cikin nasa cinyar tare da manna ......


By garkuwan Fulani[4/18, 9:33 PM] 

 [4/18, 10:14 PM] Aisha Aliyu Garkuwa: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*PURE MOMENT OF LIFE  WRITERS*

          P.M.L.W


```My lovely sis Khadeeja Ali Garkuwa Ina Farin ciki da haihuwarki lfy Allah ya raya mana kekkyawar babynmu cikin imani```😍😘



Lips d'inshi ta rink'a 

d'an lasa da harshenta mai sanyi tare da goga mai bres d'inta a k'irjinshi

gami da murza mai gashin kanshi.


Shi kuwa cikin bacci ya rink'a jin wani bak'on yanayi Na ratsashi duk gabb'an jikinshi suka fara karb'ar sak'on nata lkci d'aya tsikar jikinshi ya fara tashi sanyi ya fara ka dashi tuni lips d'inshi suka fara Dan motsawa.


Itako jin haka yasa 

ta cabke lips d'in cikin shauk'i da begen mijinta.


Jin haka yasa shi bude idanshi a hankali tare da tsurawa fuskarta ido

Lkci d'aya ya dan kuma kame jikinshi tare da d'an juyawa gami da Sa hannushi ya mirginata gefe

shima ya matsa tare da juya mata baya.

ba tare da yayi mgn ba.


Ita ko ido ta tsura mai cikin tsoro da mmk Hamma Yusuf ne yau ya juya mata baya

sannan Hamma Yusuf ne da k'aurace mata haka.


 kauda tunanin tayi ta kuma matsoshi ta manna k'irjinta a gadon bayanshi

tasa hannunta ta zagayoshi ta rink'a wasa da gashin k'irjinshi.

Hannu daya kuma kan mararshi ta d'aura cikin salon lallashi da ban hak'uri

ta k'ara matsoshi cikin

Muryar rad'a

Tace


"Hamma Yusuf"

 Bai kulata ba sai rumtse idanshi da yayi


K'ara narkewa tayi a jikinshi cikin taushi da lallashi.


Tace 

"Hamma Yusuf dan Allah ka gafarceni

Plsss 

Kamin mgn

Wlh reshin mgnar ka Na damuna,

kayi mgn Dan Allah Hamma Yusuf

ka yanke min duk hukuncin da yayi dai dai da laifina"


tureta ya kumayi ya mik'e 

tare da pillow a hannushi ya jefar kan carpet

ya kwanta rufda ciki.


Aysha kam zuwa yanxu kuka takeyi da hawaye cur cur kukan mara sauti

Cikin kukan

ta sauk'a 

gefenshi ta zauna ta kamo hannushi.


Cikin rawan murya tace


" Hamma Yusuf fushinka masifa ne a gareni ka gafar ceni

Ka min mgn dan Allah ka tausaya min Na kasa samun nitsuwa nasan nayi ma laifi Amman kamin afuwa"


Janye hannushi yayi cikin Jan tsaki ya kuma juya mata baya.


Cikin kukan ta fada jikinshi ta ruk'umoshi tare da had'e bakinsu 

wuri d'aya ta jawo hannushi ta d'aura kan bres d'inta

ta rink'a kissing nashi tako ina tana shafa fuskarsa

gaba d'aya ta narke jikinsa.


tana 

"Hamma Yusuf nifa matar kace meyasa kake juya min baya wlh bazan iyaba kamin duk hukuncin da za kamin Amman plss ka dena fushi dani"


 Sai kuma ta k'ara narke mai a jikinshi tare da k'ok'arin kunce igiyar rigar baccin Sa.


Da sauri cikin fushi yasa hannu ya tureta daga jikinshi

ya mik'e ya koma bakin gado,

Murya Na rawa yace


" Sai yanxu kika San ni mijinki ne sai da kika gama cutar dani wato gani jarabebbe zakimin duk abinda kike so kizo ki yaudareni me zakice min ai baki da bakin mgn a gareni Haba Aysha meyasa zakizo gareni ki fame min cutar da kika min"?.


Kai ta rink'a juyawa tana matsoshi jikinsa ta fada tare da ruk'k'umoshi

Murya Na rawa

tace


"Hamma Na kayi haquri ka gafarceni kar ka k'aura cemin Hamma Yusuffffffffff Kaine farin cikin Kaine cikar burina 

Wlh bansan da hakan ba saida ka k'aura cemin".


Cikin d'an d'aga murya yace 


" k'aryane bakya sona

k'iyeyya tace tasa kika zubar min da cikina da kina sona dole kiso jinina dole kiso haihuwa dani

Amman tunda hakane ni Na barki da mahaliccinmu

Amman kuma ya zama dole

*NAYI Aure* Dan Na samu mai haifamin yara dole Na nemi 

Cikar jin dadin Aure Dan bansan ribar auren da ba haihuwa ba"


😳kalaman Hamma Yusuf d'in nata jinsu tayi kamar ruwan wuta lkci d'aya ta kid'ime

 Fadawa jikinsa tayi da k'arfi ta mak'aleshi jikinta har rawa yake ta rink'a girgizashi da juya kai murya na

rawan 


"Tace a a ,a a Hamma Yusuf wlh zan haihu wlh ina sonka 

Wlh Hamma Yusuf banson ka k'ara Aure wlh zuciyata zata buga"


 Kukafa ta saki tsaka ninta da Allah tana jijjigashi da shafeshi

tare da sakemai kissi tako ina tana shinshinar duk wani sak'o Na jikinshi

Hannu biyu tasa ta tallabe kanshi cikin tsura mai ido da

 zubda qollah tace


"Hamma Yusuf"

Bai kulataba shi tun randa ta zubar mai cikinsa bai kuma d'an jin sauk'iba Sai yanzu da ta mace a kansa take ta furta mai Kalmar so Kalmar da bai tab'aji daga gareta ba gashi duk ta kashe mai jiki da jikinta da take ta goga mai

Har ranshi yaji dadin yadda ta rud'e da jin Kalmar zai k'ara Aure Dan shi dama gaba d'aya ya rud'e da tsoron ko sonshi ne batayi yana jin tsoro kar duk cikin da ta samu ta zubar mai. dry ke son kubce mai 

Amman Sai ya k'ara 

murtuk'e  fuska 

Cikin fushi yace


"K'arya kike gaya min da kina sona da baki zubbada min gudan jinina ba, dan ba yedda za,ayi nai wahala Na baki ciki ke kuma ki fidda min ajiyata, Don haka ba takura.

 zan Auri wacce zata iya rainon cikina ta Haifa min yara"


K'ara tallabe fuskarsa tayi cikin

Gsky da gsky ta tsura mai ido

Murya a raunane tace.


" Hamma Yusuf ina sonka ka yarda dani ina k'aunarka Hamma Yusuffffffffff Kaine cikon Farin cikina Hamma Yusuf da kai kad'ai zan iya rayuwar Aure kai kad'ai idona ke gani kai kasan salon zama dani wlh

NAYI NADAMA zubar da cikin nan wlh nima ina son inga gudan ji ninmu wlh wahalan laulayine, ya sani haka kuma bansan haka kake son haihuwar ba Dan Allah ka gafarceni naji Na yarda zan mana rainon duk abinda Allah ya bamu"


Tureta ya d'anyi gami da shafa bres Dinta cikin tabe fuska yace 


"Buk'atar ki dai ta ciyoki shine zaki zo ki yaudaren, 

Ni kuma yasu bazan iya aikin banza ba in miki ciki ki b'arar min da abina,

 Aure ne dai ya zama dole nayi shi


Janye hannuta yayi ya mik'e ya shiga toilet jin an fara kiran sallah.


Ita kuwa kai ta kife jikin gadon tai ta rusa kuka.


yana jinta kukan na k'ona mai rai Amman kuma ya zama dole ya janyewa Aysha Dan ta k'ona mai zuciya.


Yana fita ya zura jallabiya ya fesa turare ya nufi masallaci.


Ita kam da gyar tayi sallah a d'akin nashi ta Dan lafe jikin kujera tana jiran dawo warshi.


Shi ko ana fitowa massalacin  ya nufi cikin gida

A parlon ya tadda su Ummi harda su Ahmad da Adam duk sun zo yin SLM da Abubakar Dan zai koma yau d'in


Suna ta d'an hira

Shiko Abubakar Sai yai shiru ya rink'a binsu da ido in anyi abin dry ya d'an murmusa,

Yusuf ne ya zauna gefenshi cikin kula yace


" Babiker ban son tfyar ka yau d'inna ko zaka bari Sai gobe? "


Kai ya d'an jinjina cikin sanyi

Yace 


"Ai tfyar ta yau ta zama dole a gareni Sai dai kuyi hak'uri da reshina,

nima zan tafi cikin kewarku da k'aunarku 

Y'an uwana

rabuwa ta zame mana dole"


da sauri Yusuf ya rufe mai baki cikin

Jin tsoron kalaman d'an uwan nashi da mutuwar jiki da wani sanyi da yaji har cikin hanjinshi.

 Baki Na rawa yace



"Ummi ki gayawa babiker Dan Allah ya dena gaya min irin zantu kannan bana so"

ya k'arisa mgnar da k'arfi tare da fizgishi ya fada jikinshi suka ruggume juna, Sai kuma 

ya sakeshi ya juya ya fita

Ahmad ne ya kalli

Abubakar cikin sanyi

yace


"Abubakar meyasa Sa kake abinda ke bamu tsoro"?


Shiko dry ya danyi tare da dafa Adam yace


" kallesu fa ya Adam duk sun wani firgice yoh me a ciki Ku dama kunada masu muku Addu,a ko kun mace nifa ban dashi"


 Yusuf da yanzu ya fito d'akin Ummi yace


 "kaima kana dashi"

Ahmad yace "sosaima Dan gasu Yusuf k'arami da k'anneshi masu zuwa daga baya duk nakane Sai ka zaba"


Sosai yai dryar Farin ciki 

yace toh daga yau nine Abbinsu da sun fara mgn Ku koya musu sunana Abbi kuma su rink'a min Addu,a Allah ya kareni"


Insha Allah sukaci gaba dayansu dan jin dad'in ya sake


Shiko Yusuf A d'akin ya sameta zaune fuska a kumbure ido yayi jazir,

tana ganinshi ta mik'e da sauri zata fad'a jikinsa ya dakatar da ita cikin hada fuska yace.


"Dakata yanzu lkcin Rashida ne Dan zan kirata inji lfyarta"


Kamar wasa aiko taji Yusuf ya dage Sai hira yake da wacce yake kira Rashida dan Sai wani lumshe ido

yake.


Lkci d'aya taji wani irin malolon bak'in ciki ya tokari zuciyar ta cikin rufewar ido ta fice kai tsaye d'akin Ummi ta wuce.


Gaban Ummi da ya Abubakar ta zauna cikin zubda qollah

 cikin mmk ganin yadda fuskarta ta yi jazir

Ummi tace.


"Auta lfy? me ya same ki?


Kukan da take dannewa ya kufce mata cikin rawan

baki tace


" Ummi wai Hamma Yusuf zai k'ara Aure

Ummi har kiranta fa yakeyi a gaba na"


Dry sosai ta kama Ummi da Abubakar Amman Sai suka danne cikin hada fuska

Ummin tace


"Ehh Auta"


Cikin zare ido da dafe k'irji tace

 

"Ummi ehh fa kikace toh sabo da me Aure fa Ummi yanzu kishiya Hamma Yusuf zai min"


 Saiko ta k'ara sakin kuka.


Cikin Dan murmushi

Abubakar

yace


"Sabi da haihuwa yake so ke kuma bakya son haihuwar"


Cikin sauri ta juya gun ya Abubakar d'in nata jiki Na rawa

Tace.


"Wlh in so kuma zan Haifa mar ko 12 ne in zai ya bar batun Auren wlh zan haihu in Allah ya yarda"


Gaba d'aya Ummi da Abubakar sun cika da Farin ciki Dan ganin 

K'aunar Yusuf d'in da kishinsa a k'wayar idanuta da jikinta.

Shiyasa cikin sanyi Abubakar yace 

ke da mijinki ai ke zaki lallab'ashi Autan Ummi ni dai in an samu Na miji 

Amin mai suna"

 

Baki ta d'an tura tace


 "wlh bazai yarda ba ya Abubakar ka tayani bashi hak'uri"

 

Dry yayi sannan ya mik'e

ya ja jakarsa

Sannan yace


"Toh ba matsala

Muje parlon kinga lkci Na k'ure min"


Toh tace gami da bin bayanshi

Ummi ma bayanshi tabi suka fito.


A parlon gaba d'aya zuriyar suna cike.

Abubakar ya k'arisa Gaban baba bello

Cikin duk'awa

yace


"Ba yau zan tafi Ku gafar ceni hak'ik'a zan tafi cikin kewarku"


Kanshi ya dafa cikin sanya mai albarka

Sannan ya wuce gun Nenne itama  sanya mai albarka,

Yana tashi yaje

Gaban 

Umminsu da Abbansu

 Hannu su ya kamo duka

ya d'aura a kanshi

Cikin sanyi ya manna kanshi jikin Ummi tare da sauk'e ajiyar hrt

Sannan ya maida kanshi jikin Abban.


Murya na rawa

yace


"Ummi Abba Ku gafar ceni

Ku yafe min duk wani laifi da na muku a rayuwata

Ummi ki gafarceni wahal dake da nayi tun ina cikinki"


Ummi kam tuni jikinta ya saki

Ba abinda take Sai cewa take.


"Baka  min komai ba Allah ya ma albarka ya keutata rayuwarka Allah ya sanya sanyi a rayuwarka"


Amin suka amsa gaba d'aya parlon.


Cikin sanyi

Abba yace


"Abubakar ina alfahari da kai kuma ina mai ma fatan alkhairi a rayuwar ka

Allah ya ma albarka"


Amin ya amsa cikin sanyi ya saki Hanna yensu ya mik'e ya  ruggume k'annesa su Usman

sannan ya dawo gunsu Ahmad hada Ahmad da Adam yayi ya ruggume su cikin

Sanyi yace "zan tafi da kewarku"

Suma ruggume meshi sukayi suna muma zamuyi kewarku d'an uwa.


yana sakin su ya kamo hannun Aysha

yace 

"kinyi alk'awari ko? zaki min tokwara"?


A hankali tace ehh,

Dry ya danyi sannan yace


 "Da kyau"


Hannun Yusuf ya damk'o ya jashi suka fito harabar gidan sauran ma suka biyosu a baya cikin tsokona a hankali

yace 


"Hamma Yucut  kaji ko Auta tamin alk'awarin mai suna,

Kuma ni har ga Allah Na yarda naku gamsu da Nadamarta,

Plss Hamma Yusuf a rink'a nunawa yaran pictures d'ina Dan su sanni"


Kai ya gyada mai cikin sanyi yace


"Insha Allah 

Babiker ai dama dole zasu sanka

Abbinsu guda fa"


Juyawa yayi cikin Happy ya ruggume d'an uwansan.


Ciki sauk'e ajiyar hrt yace

"Ina sonka Hamma Yusuf ina sonka ina sonka"

 har baki 3 


Shi ko Yusuf ido ya tsura mai ya bude baki zai mgn kema.

 

Yai sauri ya shige mota

Fuska na zubda qollah

yace Na sani kaima kana sona d'an uwana 

ya juya gun sauran 

Cikin share 

K'ollah yace

"Kuma na San kuna sona nima ina sonku

Amman Sai wota rana".


Yana kaiwa nan yaja mota ya fice yana d'aga musu hannu.


Gaba d'ayansu binshi da ido sukayi jiki a mace,

har zuwa d'an wani lkci sannan suka koma cikin gida.


Shiko Yusuf d'akin shi ya koma haka kawai yaji jikinshi Na rawa

Sai dai ya zauna kusan awa 2 sannan ya mik'e cikin kasala

yaje Gaban mirror ya cire agogon hannushi zai ajiye kenan

idanshi ya k'ellah kan agogon Babiker d'inshi.


Ki ranshi yayi a woya yana d'agawa yace 


"Ya akayi ne Hamma Yusuf"?

cikin sanyi yace 


"ka manta agogon kafa"


Cikin dry yace 

"Na baka"

Da mmk yace "Na Daimon d'innanne fa da kake so sosai"


"Ehh Na sani toh inada Wanda zan bawa ne da ya wuceka"


Dry yayi yace "toh ngd k'anina"


Cikin dry suka sallami juna,


Shiko ya fada toilet yayi wonka

zuwa lkcin

An kira azabar ya wuce massalaci

Bayan an idar ya 

ya bi bayan su Ahmad suka shiga cikin gida.


Su Ahmad d'in sun isa tsakiyar parlon

Shiko yana bakin k'ofan parlon yaji kira ya shiga woyarsa

Sai da ya shiga cikin parlon sannan ya amsa kiran ganin Abubakar ne da mmk 

"yace har ka isa ko"?

Yana mgnan yana hararan Aysha dake

Tsaye a k'ofar kitchen.


Gaba d'aya ido suka zuba mai jin ya saki woyarshi da k'arfi,ta tarwatse a kan tais d'in


Ahmad ne yace lfy cikin mik'ewa ya nufi gunshi

Ina kafin ya k'arisa gunshi

Sai haggoshi sukayi yayi 

Luuu cikin sakin wani irin numfashi ya zube k'asa a.............


By garkuwan Fulani

[4/18, 10:14 PM] Aisha Aliyu Garkuwa: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣6⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_

            P.M.L.W



Cinkin firgici  da rud'ani da bugawar zuciya Ahmad,

ya tallabo shi 

ya d'aura shi kan cinyarsa,

jikinshi na rawa ya tallabo fuskarsa 

cikin kasa mgn ya rink'a girgiza kai kawai,

 zufa Na keto mai tako ina bugun zuciyar sa💓💔 Na harbawa da k'arfi.


Aysha ko cikin tsoro da zare ido da bugawar hrt da jin wani irin suka a k'akon zuciyarta 💘💔 ta iso garesu

Murya Na rawa ta 

tallabo fuskarsa

tana juyawa 

cikin d'imuwa ta rink'a 

ki ranshi da d'an k'arfi tana. 


"Hamma Yusuf, ka bud'e idonka  menene ya sameka? me aka gaya ma"?


K'ara shigewa jikinshi tayi cikin tsonanin tsorita,

tace,


"Wayyo Allah Na wayyo Hamma Yusuf na ka tashi ka gaya min meke faruwa? me ya sameka"?

 

Juyawa tayi cikin kid'ina ta kamo hannun

Ummu wace 

ta ke kamar an dasata ne Sai sanyi da ya rufe mata jikinta sanyin har cikin hanjinta a fili kuma Sai zufa ke keto mata.


Jijjiga Ummin tayi cikin kuka tace.


"Wayyo Ummi Hamma Yusuf dina 

Ummi in ya mutu nima nasan bazan rayuba, wayyo Allah na  Ummi kiga baya numfashi baya motsi".


Adam ne ya Dan juyo gareta cikin k'arfin hali yace,


" Aysha ki nitsu kibar kukannan".


Suna cikin haka phone d'in Ahmad

ya d'au suwa kamar bazai duba ba sai kuma ya d'aga ganin

Sunan Babiker ne a fuskar woyar

Jiki Na rawa ya d'aga ya d'an kara a kunne.

 

Lkci d'aya kuma ya saki woyar a k'asa cikin kid'ima ya rink'a juya kanshi

Sai yanzu ya samu bajinshi ya bud'e

kai ya rink'a juyawa yana.


"Kai kai  kai Sai kuma ya ruk'k'ume Yusuf a jikinshi da k'arfi ya saki wani irin kuka mai cin zuciyar mai sauraro.

Kuka yake yana rawan sanyi yana k'ara k'amk'ame Yusuf d'in.

Adam ne 

cikin tsoro da firgici

Yace 

"Innalillahiwainnailaihi raji un

yace haba Ahmad ka sanar damu meke faruwa"?


Nenne da ta shigo yanxu jin kukan Ahmad yasa ta k'aroso da sauri 

Jiki na rawa tace.


" meya faru me ya samemu a zuciyar nan? me ubangiji ya hukunta a kammu?

Ahmad

Ka gaya mana"?


Ummi kam hannu tasa duka biyu ta tallabe cikinta da k'irjinta 

tare da cewa

Wayyo Allah Na cikina sanyi kamar hanjina zasu tsinke"

 

Da sauri Nenne ta k'arisa gunta cikin cewa

 "meke faruwa damu ne"?


Aysha ce ta kamo hannun Ahmad cikin sakin wani irin kuka mai siririn sauri tace


 "ya Ahmad meya faru"?


Cikin kukan da kifa kai jikin Yusuf a hankali 

Yace,

 

"Aysha Babiker"

Sai kuma kife kanshi.


Ita ko Aysha cikin tsoro ta juya ta zubawa Ummi ido

Sai ta kuma sakin kuka.


Cikin rawan murya Ummi tace 

"Aysha me woyar ta kamo min? yau kuma gaya min ya zanyi da mu k'addari"


cikin kuka da carkewar mgn  tace

"Ummi ya ..

Ummi ya.. 

Ummi ya Abubakar"


Allahu Akbar uwa da d'a Sai Allah  Sai mutuwa,

 Ummi da fari murmushi tayi tana 

Kullum nafsin za,ikatil maut.

Allah sarki

Abubakar Na ase ban kwana kamin da gsk

Ya Allah Na ka jik'an wanna bawa naka Abubakar".


Ina Sai kuma zuciyar ta ta d'an yace 

Cikin sanyin sauti

ta saki wani irin kuka tare da rik'e cikinta tana 

Wayyo cikina 

Allah Na Na godema da wannan jarrabawa rabbi ka fini son Abubakar Allah kasa can yafi mai nan Abubakar Na yafema duniya da lahira".


Nenne kam itama kukan take sosai. tana Abubakar d'in ?"


Adam ko Komawa yayi ya zauna dirsham ayyah Usman

Dasu Abba da baba bello yanzu suka shigo gidan.


Suna shiga cikin tsoro baba bello Yace

 "meya faru"?


Ba Wanda ya samu da mar mgn Sai kuka

Cikin firgici da hatsala yace,


"Ku gaya min meya faru? kunyi shiru"


Adam ne cikin kuka da wani irin voice Yace

"Baba Abubakar Abubakar ne ya".


 Sai kuma ya kasa k'arisawa.


Allahu Akbar cikin mutuwar jiki da tsoro Abba da Baba ballo suka zame kan kujera

Usman ko da Rabi,u da Abdul,

Hade kai sukayi wurin d'aya suna wani irin kuka mai sanyin sauti.


Cikin k'arfin hali baba bello ya rink'a musu fad'a shi dinma kamar a gigice yake

yana.


" Haba Ahmad yanzu wannan shine matan da zakuyi wa d'an uwanku 

Adam har kai dinma kuka shine abinda zaku aikawa Abubakar

Usman ase ba Addu,a zakiyi mai ba"?


Ina shi ma Abba kanshi ya jingina jikin kujera yana ta nanata Addu,a Amman INA hawaye Sai zuba suke 

Ganin kukan Abba yasa Aysha sakin wani irin kuka sosai ta rink'a jin tausayi Abban.


Cikin yin Hamdala Ummi tace 


"Ahmad accident ne 

Abubakar yayi"?


Kai ya jinjina alamun a,a"

Cikin mmk tace


" toh me ya sameshi"?


Murya Na rawa yace


"Ummi kashe Abubakar akayi"!


Gaba d'aya parlon suka juyo gareshi cikin rud'u da alamun tabbaya

Abba ne yace waya kashe min Abubakar "?.


Cikin sanyi yace


 "wani yaronsa ne Adamu "


Baki Na rawa har suna had'a baki sukace Adamu,

Adamu Dan y'iware nan"?

Cikin gyada kai Yace shi ne.


    

Adamu wani Yaron Abubakar ne shike wakiltan sojojin kan hanya Na yankin Taraba zuwa binuye state kuma yaron ya dad'e da farautan rayuwar Abubakar Dan yana hank'k'o kanshi a matsa yin Abubakar kuma yana jin takaicin yedda Abubakar ke ta kai mai birki kan halinshi Na zalumci.


Toh da suka taso  

suna tfy har suka isa   cek point  na kan hanyar  Y'iwaren

ya samesu a lkcin azabar tayi sai 

ya tsaya  sunyi sallah da driver shi 

cikin sanyi yace.


"Sani muyi salla anan gunsu Adamu Sai mu wuce ko"?


cikin tab'e fuska Sani Yace 'ni wlh oga ban son Adamunnan mugune"


Dry ya danyi cikin sanyi yace 


"kake kyautatawa dan Adam zato kaji ko Sani? ba abin da zai faru face da sanin Allah"


Shi dai Sani ba Don ya soba 

suka tsaya sauran sojojin suna ta murna da ganin ogansu

Gashi da halin kyauta

Sunyi sallansu 

Sani ya fito musu da Abinci da Ummi ta had'a musu sukaci tare da sud'in.


Sun gama komai zasu tafi

Wani daga cikin su yabi bayan Abubakar cikin sanyi yace


 "oga Dan Allah kake kula da kanka a Gaban oga Adamu"


Dry yayi Yace ba komai Allah Na tare dani.


Har ya shiga mota

Adumun ya bishi rik'e da sanda irin ta kiwon shanu.


Cikin dry Yace 'kai 

Oga tsaya ba kai kace Fullo bane Sanda bata cinka

bari mu gani"


Cikin dry ya d'an juyo yana

 "ai fulanin da nacema bana yenxub..

Kafin ya k'arisa Sai sand'ar yaji

 kauuu a k'eyarsa zai juyo ya kuma sake mai d'aya a gadon bayanshi ya yunk'ura zai taso ya k'ara mai d'aya a tsakiyar kanshi,


Ganin abin ba Na wasa bane yasa sauran suka rarumoshi suka danne.


Shiko Abubakar cikin azaba ya fad'a jikin Sani.

  

yana numfashi da k'er yace

"Adamu yanxu nizakayiwa haka Amman ka sani Sai Na rama"

A take Sai ko ya fara aman jini.


Ihu bayan hari ganin haka Sai

Jikin Adamu ya d'au b'ari cikin tsoro da kuka

Yace.


"Na shiga uku

Abbakar aman jinin kakeyi 

Dan Allah ka gafarceni"


Cikin aman Yace 


"Sai Na rama fa"

 

Cikin kukan Yace ka rama indai zaka yafe min Dan Allah Abubakar ka gafarceni".


Sai ya kuma sakin kuka


Shi kuma aman yak'i tsayawa cikin galabaita Yace

Na yafema Dan Allah tunda 

Allah ma da kanshi yana son masu hak'uri da yafiya"


Cikin nishi Yace


 "Sani kira min

d'an uwana kira min Hamma Yusuf

 d'ina".


Shine fa a lkcin ya kira Yusuf.


Shiko yana jin muryar d'an uwanshi


Cikin fizgar numfashi yace


" SLM Hamma Yusuf

Adamu yamin dukan kisa ni nasan zan mutu Amman Na yafe mai 

Hamma Yusuf ko Na mutu Ku barshi Na yafe maiii,

Sai ya d'aura da Kalmar shahada...


ganin haka yasa 

Sani zare woyar cikin firgita Yace..


"Hamma Yusuf

Oga Abubakar ya rasu ya tafi ya barmu".


Furucin kenan da ya buga zuciyar Yusuf 

ya sashi sumewa.



Cikin Sauri Abba ya mik'e

tare da cewa baba bello Yaya mu tafi mu d'auko 

gawarsa muyi mai su tura".


har sun mik'e 

Cikin kuka 

Aysha tace 

Abba " kalli Hamma Yusuf shima a sune yake tun dazu bai numfashi "


Su gaba d'aya Sai yanzu suka Ankara kan Yusuf dake ruk'ume jikin Ahmad.


Kai Abba ya jinjina ya zo suka d'aga shi shi da Ahmad

Sama suka haura dashi har kan gadon Abban suka direshi

Abban ya duk'ufa kanshi cikin zubda qollah.

A Ranshi yake cewa Rashin d'an uwa bai da misali".


A hankali ya samu ya farfad'o sannan Abban ya mai Alluran bacci.


 Su kuma suka wuce.y'iwaren 

Kafin su iska  sarkin garin yasa akayi mai sutura akayi mai sallah Aka kaishi gidan shi Na gsky da yake abokin bappa yaya ne 

su Abbanma Sai k'abarinshi aka kaisu suka gani washe gari da safen sukayi sammako suka dawo

Adamu kuma da kanshi ya kai kanshi hukama dasu Abba sukazo

aka kawoshi garesu

Abba kam Na ganinshi Sai hawaye

Shiko baba bello cikin kuka 

Yace


 "Adamu kaci amanar abota a duniya"



Haka suka dawo gida aka zauna karb'ar gaisuwa


Shi ko Yusuf tunda ya farfad'o akayi mai Allurar bacci bai tashiba Sai washe garin da safe bayan su Abba sun dawo.



A hankali ya bud'e idanshi cikin wani irin tsinkewar zuciya da tuni abinda Sani Yace mai ya mik'e jiki Na rawa

Toilet ya shiga Alwala yayi cikin firgici kar acemai gsky ne abin da yaji

Sallolinshi ya rama sannan ya fara jera nafilfili.


Yana cikin sallanne Ahmad ya shigo ganin yana sallah yasa ya juya.


Parlon Ummi yaje cikin dashewar murya yacewa Aysha


"Auta kije d'akin Abba B'iyaye ya tashi ki tafin mai da abinci"


Aysha dake kwance jikin kakarsu innayi

Fuska a kub'b'ure fuskar tayi jazir ga wani zazzabi mai zafin gske cikin jin jirin ta mik'e tana goge k'ollah.


Kakace ta d'an rik'o hannuta cikin sanyi tace

"Kar kije mai da kuka"


Kai ta gyada cikin share k'ollah

A hankali ta haura saman

cikin sanyi ta bud'e k'ofar d'akin Abba ta shiga kanta a sunku ye

Shiko jin motsin bud'e k'ofar ya juyo a firgice.


ganin Aysha ya sashi tsura mata ido cikin son  ganin fuskarta 

Itako jin jirin yasa ta zame gabanshi

ta rik'o hannushi.


Ido ya zaro cikin rawan lips d'inshi

ganin hawaye a  idon ta

cikin tsoro 

Hamma Yusuf ya fad'a jikinta

kanshi ya manna a tsakiyar k'irjinta ya Sa hannushi ya ruk'k'ume ta cikin tsoro ya rink'a juya kanshi yana murzawa a k'irjinta kamar yaro cikin alamar kar ta gaya mai baya sonji

K'ara tura kanshi yake a k'irjinta

Itama Sa hannu tayi cikin kuka ta manna shi da jikinta ta k'ara matsoshi shi kuma k'ara narkewa yayi a jikinta.....



```WANNAN NOVEL D'IN NA SADAUKAR DASHI GA Y'AN UWANA YAYUNA 

YA ABUBAKAR DA AHMAD ALLAH YA GAFAR TA MUKU Y'AN  UWANA RABBI YA SANYAYA MUKU MAKON CINKU 

Yasa Aljannace makomarku".```



By garkuwan Fulani

[4/18, 10:14 PM] Aisha Aliyu Garkuwa: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👆🏻👆🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Pure moment of life writer's 

               P.m.l.w


www.aishaaligarkuwa.blogspot.com 



Lkci d'aya jikinshi ya rink'a bari yana tsuma hatta jijiyoyin kanshi saida suka taso sama fuskarsa tai jazir sai k'am-k'ameta yake,

ita kuwa kuka ta saki cikin dashewar murya ta sa hannuta ta tallabo fuskarsa ta rink'a juya mai kanta  alamar yayi shiru,

Shiko bai ma san halin da yake cikiba gaba d'aya ya resa me ke mai dad'i a duniya.


A parlon kuwa Abba ne da Baba bello suka shigo Dan gaisawa da su innayi da suka iso bada jimawa ba 

har sun juya zasu fita, Baba bello ya kalli Ahmad dake zaune gefen kaka cikin sanyi yace.


"Ahmad har yanzu Yusuf bai tashi bane "?

Kai ya d'an jingina a hankali yace.


" a a ya tashi".

   

yana fad'a mai haka Sai suka fasa fitan suka juya suka haura gun Yusuf d'in.


Cikin d'akin kuwa Yusuf duk ya rikice Aysha sai kuka take shima cikin azabar zuciya ya samu kukan ya kufce mai  da samun kukan sai ya daina rawan jiki  sai zamewa yayi kan cinyarta ya kife kanshi ya rink'a wani irin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro kukan da ka jishi kasan akwai k'una mai tsananin yawa a zuciyar mai yinshi.

  

Itama Aysha kukan take tana k'ok'arin tallabo shi.


Dai dai lkcin su Abba da Ummi da Baba bello da Ahmad suka shigo,

Su Na shiga 

Kukan Yusuf da Aysha da yedda suka ruk'ume juna suna kukan.

 ya tona musu zuciya lkci d'aya Ummi ta zame gefen su Cikin kauda kai 

Baba bello ne yayi k'arfin halin mgn

Bayan duk sun zauna sun sasu a gaba

Cikin dauri yace.


"Haba Yusuf wannan kuka ya isa haka meyasa bazamu d'au dangana ba shin ase ina yebonka ase kai d'in kafi kowa sakewar zuciya ji yedda kasa matarka a gaba kana kuka yanzu kasan tsawon wani lkci da Aysha ta d'auka tana kuka kalli fuskarta fa ka tausaya mata mana itafa abu 2 ne ya had'e mata kukan rashin d'an uwanta da kukan tausaya wa halin da kai mijinta zaka shiga na tabbata da ta ga ka daure da matsalarta  zata regu 

 kuyi haquri Yusuf am".

 

Kai ya d'an d'ago Cikin kallon iyayen nashi lkci d'aya kuma ya fad'a jikin Abban su ya saki wani irin sautin kuka yana.


" Abba shi ke nan Babiker Na ya tafi bazai dawoba ya tafi har abada"


Allah sarki Abba shima kukan d'an nashi sai ya sashi kuka cikin kukan yace.


"Yusuf Abubakar baiyi gaggawa ba kuma muma bamu makara ba hanyace wace dole ko wanne mai rai sai ya bita Yusuf ba Abubakar zamu yiwa kuka ba kanmu mukewa kuka, sabo mukewa kuka duk yedda muke sonshi Allahn da ya bamu shi ya fimu sonshi ka dena yiwa d'an uwana kuka,

insha Allah muna zata masa Rahama ka tunafa kashesa akayi".


Kuka ya k'ara saki Cikin k'uncin zuciya yace.


" Wlh ba dan Babiker da bakinshi yace min ko ya mutu shi ya yafewa Adamu  kuma yace min koya mutu kar muyiwa Adamu komai,

 badan hakaba wlh da Adamu Sai yaga k'ask'anci da sai ya d'an d'ani hukunci Amman Babiker yace kar amai komai".


Jin haka yasa Ummi ma sakin kuka.


Aysha ce cikin kuka tace.


"Hamma Yusuf ka gani fa kasa Abba da Ummi kuka Hamma Yusuf kayi haquri ka bar kukannan".


Ahmad ne ya matsoshi Cikin sanyi yace.


"Biyaye Abubakar yafi buk'atar Addu,armu da kukannan dan Allah ka daure ko iyayenmu Sa samu sauk'in abin".


kai ya rink'a jinji nawa Cikin sanyi Ahmad d'in ya rink'a goge mai k'ollan.


A hakan suka samu ya d'an dawo hayya cinsa sannan suka jashi suka fita wurin amsar gaisuwa.

 Suna fita gefen kakansu suka zauna shi da k'anneshi dasu Adam Allah sarki bappa Yaya Sai hawaye ke wonke mai fuska ganin yau Allah ya zare mai d'aya daga cikin jikokin nashi.

Cikin zubda k'ollah ya rink'a yi musu nasiha.


Da deddere Abba da kanshi ya kira Yusuf Yace yazo d'akin shi su kwana tare su Adam kuwa baba bello Yace su d'auki matansu su koma gida jensu da safe Sa kuma zuwa kafin ai safakar uku.


Shi ko Yusuf tun da suka shiga shi da Abba ba abinda yake Sai bawa Abba lbrin irin hirarrakin da Babiker d'in shi ya rink'a yima mai da yazo.

da k'er Abba ya lallabashi jin kukan da yake har numfashin Sa Na fita,

shiko 

Kasa baccin yayi Sai tashi yayi ya d'auro Alwala ya rink'a karatun k'ur,ani mai girma karatun yake da Farin Yana kuka daga baya kuma Sai kushi,i ya halarto mai  Amman haka ya kwana ba bacci kam Sai rawan sanyi da yake.


Itama Aysha a d'akin Ummi kukan da tasha ya k'ara ingiza zazzabi jikinta ga rashin cin abincin da takeyi lkci d'aya jiri ya sark'a feta ga amai da take Na wahala tayi kakari har ta banu amman ba  abinda za harar kafin zuwa safiya duk ta galabaita.


Kashe gari da sake ta kama ranarce za,ayi sadakan uku Dan da wuni akayi lissafin.

Tun asuba su Abba da baba bello da su Ahmad da Yusuf dasu Hydar gaba d'aya dai zuciyar tasu  suka hallara a masallaci gidan nasu da maqota da abokan arzik'i .

Akayi Sada kan uku  ana watsewa su Ahmad kuma da k'annesu suka suka d'auki k'ura,anai suka rink'a karatu da Addu,a da nemawa mamacin gafara.har zuwa Tara da rabi sannan suka koma Cikin gida,  a safiyar Dr Umar ardo da Goggo Aysha ma suka koma Yola Cikin jimamin rashin da sukayi, Hydar kam Yace bazai komaba tukun,

 su Bappa Yaya ma sun koma 

Anuty Sadiya ma Abba ya sata tfya dole tana kuka.


11 da kadan Na safe  su gaba d'aya suna zaune a parlon Ummi harda Nenne duk Dan su d'ebewa juna kewa.


Ummi dake ta zirga zirga ta fito jiki a mace ta kalli kaka a hankali  tace.


"Kaka jikin Ayshan Na fa yak'i duk ta gala baita gashi ko ruwa tasha Sai ta harar ni Na tsorita da abin" .


Hydar ne Cikin sauri yace.

 

"Toh Ummi mu tafi asibiti mana"


Kakan ma Asibitin tace suje,

Shiko Yusuf ido ya zuba musu cikin rashin abin cewa,

Sai Nenne ce tace


 "toh Ummi ta fito mu tsfin yafi ai ko"?.

 

Kai ta jinjina cikin sanyi tace.


" ko tsayuwa fa bata iyawa jiri da rawan sanyi, Amman dai bari Na tallabota".


Ummi Na shiga ta sameta ta fito wonkan da ta tayata ta shiga da Dan matsa ruwan kuma Sai ta d'an ji k'arfi kadan duk da tana jin jirin,

mai ta d'an shafa mata sannan ta taimaka mata ta zura doguwar riga sai d'an gyelenshi ta yafa, sannan ta Dan kamata suka fitoh parlon sunan

 isa,

 parlon sai jirin da wani irin duhu ya rufe nata ido,

Cikin sanyi da rashin k'arfin tace 

"Wayyo Ummi zan fad'i duhu nake gani".


Dai dai lkcin suka isa gun Yusuf aiko tai luu zata fad'i,

cikin hamzari ya tallabo ta ta fad'a jikinshi lkci d'aya yaji d'umin jikinta Na ratsashi kara tallabota yay Cikin shafa fuskarta ita kuma Sai lafewa tayi jikinshi tana shak'ar k'amshin turaren shi sai ta lumshe ido ta kuma bud'ewa.


Cikin sanyi ya d'an sunkuyo kamar Cikin rad'a yace.


" Amrita meke damunku meke miki ciwo"?


K'ara lumshe ido tayi kamar mai shirin suma.

 

Ganin haka yasa Cikin sauri ya tallabota ya mik'e jiki na rawa 

Hydar ne ya mik'e da sauri rik'e da key din mota yayi gaba Yana mu tafi hospital sauri sauri gudu gudu ya shige motar da Hydar ya bud'e musu Nenne dake binsu a baya ta zauna gaba kusa da Hydar d'in sannan shi kuma yaja mota suka tafi.


Suna zuwa Asbitin 

Doctor Suhana ta tarbesu su cikin kula da karamcin ta, lkci d'aya ta fara bin ciken lfyarta da abinda ke damunta da taimako abokiyar aikinta Anuty khady

Cikin k'orewarsu da iya warsu suka gano Cikin dake jikinta da kuma rashin nasarar da maganin da tasha ya kasa yiwa Cikin.


Cikin fara,a da happy Dr Suhana ta fito tana fita ta kalli Yusuf cikin fara,a tace.


"Congrat Dr Yusuf Aliyu Muhammad matar ka Na dauke da ciki har Na tsawon wata 4".


Ido suka zare   Cikin mmk da kaduwa Hydar harda k'warewa, 

Shiko Yusuf fuska ya murtuk'e Cikin kauda kai Yace.


"Dr Suhana mgnar gsky mukefa ba wasaba Abinda kika gaya min gske ne "?


Cikin gsky da gsky "tace wlh da gske ne Cikin  4 mornt gareta wlh  Dan mgnin da aka shawa Cikin baiyi tasiri ba sai dai kawai yaja mata koda ciki zatake yin period"


Hamdalah Yusuf ya rink'ayi lkci d'aya kuma ya tuna mgnar Babiker d'inshi inda yake ce mai 


"Hamma Yusuf Dan Allah idan abin Farin ciki ya sameke kake bayyana Farin cikina kan fuskarka  ban son jin ana cewa ba,a gane Farin Cikin ka da bakin cikinka,

Koda bana raye idan kai Farin ciki har kai murmushi zanji dad'i".


Tuno hakan ya sashi sujjada ga Allah Cikin farin ciki da fara,a  ya rink'a hamdala, su Nenne da Hydar kuwa tuni su isa gunta suka rink'a fara,a suna hamdalah.


Shiko Yusuf har zai wuce Dr Suhana tace Amman da d'an matsalah fa


Cikin tsoro yake tabbata yarta.


" matsala kuma? Matsala mece"?


Dan murmushi tayi cikin sanyi tace,


"Matsalar k'aramace wannan sanyin da take yawan ji har yake sata rawan sanyi gsky ba abinda zai cireshi sai d'umin jikinka".


Kai ya sunkuyar Cikin wucewa yana,


" wannan matsala ta k'are".


Yana shiga kanta ya tsaya yasa hannu ya tallabota Cikin sanyi yayi murmushi Yace 


"burin Babiker Na zai cika da izinin rabbi Sai dai ban saniba ko zai kuma yunk'urin zubar min da cikina"?


Kuka ta d'an saki Cikin sa hannu biyu ta zagaye k'ugunshi ta manna kanta kan jikinshi cikin sanyin murya tace.


A a, a a Hamma Yusuf bazan sakeba wlh Na baya ma kuskurene nayima alk'awarin ko zan resa raina zan reni Cikin nan".


Ajiyar hrt ya sauk'e tare da k'ara ruk'umeta suna shak'ar k'amshin juna da d'umin juna  ganin haka su Nenne kam suka fice,

 Suna fita  Dr Suhana ta shigo ta basu SLM da magungunansu sannan suka koma gida Cikin Farin ciki.



A gida kuwa gaba d'aya tasowan wannan ciki ya ciki zuk'atan zuciyar da Farin ciki  Ummi  saida tayi kukan Farin ciki.



Da Daren kuwa Yusuf ne zaune gefen Ayshan tana ta rawan sanyi Ummi dake gefe Cikin tausaya mata tace.


" shin wai su basu bata mgnin sanyin nan ne".?

 

Kai ya d'an sunkuyar Cikin Dan happy Yace 


"an bata mgnin Yana d'akina".

 Sai kuma ya d'an mik'e cikin sanyi ya kamo hannuta Yace.


" zo Muje in baki mgnin".


 Itako jin d'umin jinshi yasa ta mik'e cikin kasala tabi bayanshi.


Ita ko Ummi murmushi ta d'an yi da hamdala itama ta nufi d'akin mijinta.



Suko suna shiga bedroom d'inshi

ya jawota jikinshi cikin rawan jiki ya sabule rigar jikin.....



```Dubun k'aunata zuwa gareku matan group d'in Fasaha Writers INA yebawa gareku INA kuma alfahari daku  ba abinda zance daku sai Allah ya barmu tare```





By garkuwan Fulani

[4/18, 10:14 PM] Aisha Aliyu Garkuwa: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Pure moment of life writers 

              P.m.l.w



www.aishaaligarkuwa.blogspot.com



*Wannan shafi nakune Ummyn Yusrah & Asy Khaleel*


Jikinsa ya zare ya jawota jikinshi cikin rawan jiki ya haura da ita kan gado tare da zare y'ar rigar jikinta ya cillah gafe,

cikin fesa numfashi ya manna kanshi kan cikinta yasa hannushi daya yana shafa d'an  cikinda sai yanzu ya lura da girmansa kad'an,

itama mak'aleshi tai cikin kewar mijin nata da jin dumin jikinshi

ta k'ara yin kasa ta had'a k'irjinshi da nata tasa hannu ta tallabo fuskarsa ta d'aura tsakiyar k'irjinta,

tasa hannu tana wasa da gashin k'irjinshin.


Cikin rawan jiki da buk'atuwa ya fara manta halin da yake cikin bai son jin komai sai matarsa ita yake gani ita yakeji.


Shi da kan shi yasan yayi kewar bres d'innan  dole cikin begensu ya sa hannu yana  musu wani irin shafa da latsasu tamkar yau ya fara ganinsu da jinsu sai nishi yake sama sama,

itama lunshe ido kawai take tana mimmik'ewa  dan

gaba daya gab'b'anta tuni sun amshi sak'on da Hamma Yusuf d'in nata ke aika masu ,

sosai ta fara maida mai martani duk ta susutashi ta birkita mai k'wanya ta tsinka mai jinin jikinsa,

gaba d'aya jikinsa sai rawan sanyi yake tuni lips d'inshi sunka fara kad'awa sunyi jazir sun wani tsuke,


Cikin sha,awarsu ta yunk'ura ta had'e bakinshi da nata lips d'in ta cab'e cikin salon k'orewa da shauk'i da bege ta fara kissing nashi,

Shiko Yusuf mutuwar bori ya fara ba abinda yake sai lallatsata da shafeta cikin sanyi ya zare harshensa ya manna bakinshi kan bres d'inta ya musu wani irin kamu da tsotsa,


Cikin yankewar numfashi  Aysha kam ta saki wani gauron k'ara,

gamida  k'ara tura mai bres d'in ta tallabe kanshi kamar yaro, shiko tuk'uru yake sarrafata dan su da Kansu sun San sunyi kewar juna baranma shi Yusuf da yakeji kamar zai mutu in bata bashiba.


Itako sai mik'a take.

 tana.


"Ohhhh shiihhhhh 

Hamma Yusuffffffff".


Shiko zuwa yanxu baida bakin mgna.

 

Sai nuk'urk'usanta da ya keyi juyata yake tako ina yana sakar mata kiss yana shafe ababen marmarinshi.


A hankali yai mata rumfa da k'irjinsa,

cikin rawan murya kamar mai cutar bebanta yace.


" Amrita Ina sonki ki soni koda rabin yadda nake sonki ki rik'e min cikina ki rainar min jinina,

Kar ki,

 k'ini dan kokin k'ini ni bazan iya fushi dakeba bazan iya rayuwa ba keba ki jik'an mijinki wlh Aysha kece farin cikina kece jin dad'in rayuwata, kece nutsuwata kece ke iya gamsar da ni da sama min natsuwa".


Hannu ta sa ta sank'alo k'ugunshi ta had'e su wuri.


Da k'arfi ya saki numfashi dan jin jikinsu ya had'e sai kawai ya saki wani irin kukan jin dad'i da farin ciki, sai kuma ya kai bakinshi kan kunneta cikin kukan yace.


"Amrita bazan cutar dake da baby Na ba ko?

kar Na wahal daku  dan kune farin cikina".


Cikin rad'a ta k'ara shigewa jikinshi murya a daburce tace.


" uhhhhhh hammmmm

Shiihhhh

Hamma Yusuf ba komai gaba d'aya ni da babynka d'umin jikinka muke son ji,

bugun zuciyarka mukeson ta ratsa tamu baby ma yana kewar Abbanshi dan Abbanshi yayi fushi da Amminshi tsawon wata 1 baiji d'umin mahaifin shi ba".


Allah saki dama dole masoya basa fushi da juna,


Shiyasa Yusuf harda rakwafuwa yana.


 "Amrita kar kisake yin abin da zai had'amu har ta kai munyi nisa da juna".


Itama kukanne ya kwafce mata dan Hamma Yusuf ya kusa kaita mak'ura saura ta sume dan duniyar da ya cillata a yau ta tabbata a cikin mata 1000 da wuya a samu 20 da suka taba isa wanna duniyar masoya da ma aurata bata taba jin yadda takeji yau dinba 

 Hamma Yusuf d'in ya isarmata har abada 

Dole ta mak'aleshi tana kuka tana.


" Hamma Yusuf bazan sakeba zamu rayu tare zamu rayu cikin farin ciki  Kaine jigon rayuwata Kaine ka sanardani soyeyyar gsky kai da banne cikin maza mace bazata iya fushi da namiji kamar kaba".


 

Haka suka mace cikin so da k'aunar juna sunyi kukan dadinsu sun more sun mak'alewa juna son ransu  sun kashe kewar juna da ya cisu tsawon wata d'aya"...........


    ********************


Bayan wata Biyar 

  Baba bello ya kammala gidaje 3 da ya Gina komai iri d'aya kattin gidaje ne naji da fad'a 

Komai ya tafi da tsarin zamani ya malla kawa Adam da Ahmad da Yusuf gidanjen a Jere suke Na Yusuf ne a tsakiya sai Na Ahmad a gaban nashi sai na Adam a bayan nashi.



Yau jumma,a

kuma  yau ne suka tare a gida jen nasu duk da shi Yusuf yana Madina yaje karbo sakamakon kammala karatunshi inda ya zama cikken likitan musulunci,.

ya tafi da k'yar dan ya nace shi sai dai ya tafi da marsa a cewarsa har sati 2 bai jitaba bata jishi ba,

dole dai ya hak'ura ya tafin dan su Abba sunk'i ganin yadda cikin Ayshan ya girma,.

 

Ran da suka tare sai aka had'a Aysha da Kaka dan kula da ita.,

Suna tare jumma,a ana zaton Hamma Yusuf sai next Friday sai akwai kashe gari asabar ya diro kamar saukar yeso.


Yana isa gidan.

  Ummi tai tamai dry tana Auta ta komai haihuwa Yola dan babanta yace ta koma can sai ta gama 40 in ta haihunma.


Abu kamar wasa sai ga Yusuf a zaune dirsham gaban Ummin shi 

Yana rikici kamar yaro yana.


"Haba dai Ummi wlh ni bazan iyaba kawai adawo min da matata dan ni ban yadda ba da matata sai Na zama kamar banda mata dan Allah Ku tausaya min yanxu kwana 12 fa ban ganta ba den kice Wai ta komai Yola ni bazan iyaba Ummi kema kinsan ina buk'atar matata dan bazan iya rashinta a kusa daniba".


Ummi kan kunyace ta rufeta jin zantu kan Yusuf shi ko a jikinshi ganin zai mata barin zance yasa tamai bayanin gsky,

aiko

 ko minti 10 bai k'araba ya wuce gidansa dan dama yasan gidan dan tun kan ya tafi Baba bello ya basu takardun gidajen.



Yana shiga kai tsaye  parlon da ya hank'o da hasken wuta ya wuce yana shiga ya tsurawa Amritanshi ido ganinta tsaye kusa da TV tana wlh ke kaka sai kiyi ta cewa sai Arawa zaki kallah duk ki takurani.


Juyo wan da zatayi ta ga Hamma Yusuf d'in nata cikin mmk !da zare ido ta juya da d'an gudunta, tayi gunshi,

Shiko cillah jakarsa yayi ya ware mata Hannayenshi yana Came baby i miss you so much Noor hayatina,


Itako 

Kaka dake gefenta mik'ewa tayi tana 


"lfy Aysha baki da wayoko yanxu da wannan k'aton cikin kike tik'a gudun nan"?


Ita dai bata kulaba,

da gudunta ta fada jikinshi Hamma Yusuf d'inta ya Sa hannu ya ruk'k'ume matarsa sai kuma ya had'e bakinsu yai ta tsotsa sannan ya zira mata harshensa yana mata alamar yayi missing ta kama kar yayi kula aiko ta cafe lkci daya suka fara sauya numfashi cikin sanyi ya zame da ita kan carpet ya tallabota da kyau ya samu ya d'an zare harshensa,

Jin  gyaran muryan da Kaka ta musu,

Cikin borin kunya ya kauda kai yana

" ohh Amrita ai zaki cinye min harshe,

Ke kuma kaka me ya kawoki nan gidan? ni wlh kinsan banson sa ido ehe".



Cikin mmk Kaka tace 

"oho ba matsala ai zan tafi da ka samu ma Na yima gadin mata ko "?


Ta fada cikin fushi

Shiko mik'ewa yayi cikin dry sosai yace kai Kaka wasafa nake ai ke tamuce bazama Ki komai gidanki ba tare zamu zauna.


Dry itama tayi cikin jin dad'in sauyawar Yusuf ya komai mutun mai sauk'i  da fara,a da raha  da son yan uwa ya dena tsok'k'omar kowa a kanneshi ko don suma yanxu kan sun girma 

Hatta su Rabi,u da Usman sunyi Aure Hydar ma yayi da Abdul sai Sadip ne kadai ya rage bai yiba.



Cikin fara,a tace 


"inji ba yau zaka dawoba sai sati mai zuwa "?


Tab'e fuska yayi yace .


" Na kasa wlh bazan iyaba kewar mata ta nakeji ai nama yi k'ok'ari  ko Kaka? kwana 12 ba mata saura kad'anfa Na mutu Kaka".


Kai ta jinjina tana. 


"ban saniba kai baka da kunya sam yanzuba kamar daba wlh".


Kai ya d'an shafa ya kamo hannun Aysha ya shafa k'aton cikin ta yace.


"Wlh Kaka son Y'ar yarinyar nanne ya canzani gaba d'aya"


Duk sukayi dry

haka sukayi ta hira Yusuf ko a jikinsa sai lallatsata yake yana.


 "Amrita  nonon nan basu k'aru sosai ba anyako zasu isa babyn nan"?


Ganin zasu zarce Kaka tace sai da safe ta shige dakinta sannan tace 


"Aysha kizo ki karbi mgninki fa"

 

Tana fita ya mik'e da ita.


" yana jeki karbo kizo Dan zan gyarawa baby Na hanyan fita".


Tana shiga gun kakan ta k'ura mata ido cikin fad'a tace.


"Wlh ki kula da wannan jarabebben mijin naji in kinyi garaje zai takalo miki nak'uda shi ko a jikinsa".


Baki ta d'an tura cikin yatsune tace.


" Toh Na barshi da wahala kenan kwana nawa baya nan duk da haka bazan,aga hak'urinsa ba ko so kike Na tauye mai hak'k'insa 

ni baccima nakeji".


Tana kaiwa nan ta juya tana 

"ji tsohuwa da sa ido"


A d'akin kuma dry 

Yusuf ya rink'a yi yana.


"kai Kaka wato zan tsokalo miki nak'uda"


Itama dryan tayi tana shafa sajenshi

Lkci d'aya kuma suka mak'alewa juna cire rigarta yayi yana shafa bres d'inta yana.


"Amrita zaki iya ko? in  bazaki iyaba wlh zan hak'ura".


Kai ta tura a k'irjinshi cikin sanyi tace.


Toh in bazan iyaba wazai biyama buk'atarka? ko so kake Na barka cikin wahala? al halin kuma lfyta lau 

Ni cikina ba zai hanani kyautatawa mijina ba".


aiko cikin Happy ya fara murzanta yana sauk'e gajiyarsa da kewar ta da buk'an tana, sai muntashi yake yana sabbatu da sanya mata albarka.

gaba d'aya ya kasa control d'in kanshi itama yau jinshi take kamar wani dere da sukayi a Gembu ran da ya d'irka mata mgni.


Dama kunsan ance mai ciki da ban take bare kuma dama Aysha matar ni,imace.



Can dai Yusuf ya d'an sahirta mata jin gaba d'aya cikin ya takure gefe ya dunk'ule,


yakomata yayi cikin maida numfashi ya rink'a shafa kanta da cikin.


yana 

" ohhh Amrita Allah ya miki Albarka matar kirki y'ar aljannah".


Itako shiru tayi tana shafa sajensa ,

dan wani iron fitsari takeji mai azabar zafi ga wani irin Sara da k'ugunta keyi sai zufa ke keto mata tako INA,

cikin wahalan tace.


"Hamma Na ka gamsuko"?  


Shafa bres d'inta yayi da cikin ta yace.


 "sosaima" 


 Kai ta jinjina gamida yunk'uri ta mik'e ta nufi toilet.


Cikin kula yace 

"Amrita Na wahal da keko"?


"Ba komai Hamma Yusuf na"

 tace cikin k'arfin hali ta shige.



Tana tsugu nawa sai fitsarin yak'i fita sai saran da bayanta keyi ya k'aru.


Cikin Azaban ta fito tana zuwa ta kwana gefenshi ta d'aura kanta kan cinyarsa tana.


"Hamma Yusuf bayana,

bayana zai b'alle"


Cikin firgici ya taso ya tallabo kanta gamida shafa cikin cikin tsoro yace.


"Amrita karfa mgnar Kaka ta tabbata"? 



Jin sabon saran bayan ba sassauci ta mik'e da sauri ta shige toilet 

shima binta yayi da sauri tana shiga ta durk'usa a k'asa dan jin k'afafunta Na rawa duk sun mace


Shima durk'usawa yayi gabanta

Itako kusa jin wani irin azaba da nishi ta cakumo hannayeshi ta rik'e GAM ta rink'a wani irin nishi mai k'arfi,

Shi kuma sauri yayi ya gyara mata durk'uson ya janye towel d'in jikinta saman k'irjinta yakuma  jata ya mannata jikinshi.

Cikin soro yace 


" kiyi nishi Amrita haihuwace ga kan baby ki rik'eni da kyau"

 Aiko ta rarumoshi ta matseshi da iya k'arfinta ta saki nishi cikin, abbaton sunan Allah.


Shima k'ara rik'eta yayi

Sai ta kuma sakin nishi mai k'arf aiko sai ga,

Yaro k'ato fari tas ya fad'o cikin tafin hannun Hamma Yusuf d'in.

Wayyo dad,I Hamma Yusuf

Ruk'k'umesu yayi da baby da maman babyn yana hawayen farin ciki da hamdala ga Allah.


 shiko yaro sai kuka yake tsalawa alamar lafiya yake.


Kai Yusuf ya sunkuyar Dan lek'a fuskar Amritanshi

Cikin tsoro da firgita da kad'uwa ya zazzaro ido ganin halin da Ayshan ke ciki duk ta k'ak'and'are ta matseshi shi da yaron cikin azaba ta ......


By Garkuwan Fulani

[4/18, 10:14 PM] Aisha Aliyu Garkuwa: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👇🏻👆🏻👆🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣1⃣9⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Pure moment of life writer's

        P.m.l.w


www.aishaaligarkuwa.blogspot.com


Ta kuma yunk'uri da nishi mai k'arfi sai ga yarinya ta sumb'ulo,

tana cillah kuka, Yusuf kam gaba d'aya ya cika da farin ciki sai hamdalah yake yana ruk'k'ume da family d'inshi,

Ita kuwa Aysha komawa jikinshi tai ta lafe tana mai maida numfashi da sauk'e ajiyar hrt tana mai hamdala.


Lkci d'aya Hamma Yusuf ya kimtsa yaranshi da matarshi shi da kanshi ya musu komai ita ya fara tallafawa tayi wonka tare da Dan gasa jikinta sannan ya fito da ita ya taima ka mata ta kimtsa tsap abinsu yara kuwa, goge su yayi tsap ya murjesu da mayuka sannan ya shiryasu tsap ya nad'esu cikin blanket nasu masu laushi da taushi farare tas.


Har zuwa 5 ya kammala komai shima yai wonka ya fito ya nufi masallaci bayan sun idar da sallah ne Ahmad da Adam suka tsareshi a gaba suna mmk Wai yaushe ya dawo shine bai fad'a masu ba,

Shi kuwa dariya kawai yake yana ruk'k'ume su,

Cikin kewar juna da k'aunar juna, ya kallesu cikin farin ciki yace.


"Na dawo jiya da dare dama nace sai kawai Ku gani da safe".

 

Ahmad yace.


"Aysha ta murd'a kabbunta ko"?


Dariya yayi tare da cewa.


"A a baby's sun kira Abbansu dai".


Ido Adam da Ahmad d'in suka zuba mai cikin mmk da son gane zancensa.


Kai ya jinjina musu alamar

 "ehh hakane"


Adam yace.


"Me kake nufi"?


Gyara tsayuwa yayi tare da Dan sunku yawa yace.


" ina nufin Aysha ta Haihu ta haihu jiya da dare bayan Na dawo ta haifa mana tagwaye".


Lkci d'aya zuk'atan su suka cika da farin ciki 

Cikin zumud'in suka wuce gidan Yusuf d'in.


A gidan kuwa Kaka na idar da sallah ta d'an fito parlon,

ido ta tsurawa corridor d'in d'akin su shiru ba motsinsu cikin d'an tunani ta komai d'akinta tana shiga kuma taji muryar Ahmad na kiranta da sauri ta fito 

a parlon ta samesu ido ta tsura musu cikin tsoro

sai kuma tayi ajiyar zuciya ganin fuskokin su cike da annuri.


Adam ne ya kalleta da kyau yana.


"Kaka sai kawai muka samu yan tagwaye kai Alhamdulillah".


"Harara tasaki musu cikin tab'e fuska tace


 "ai koda bansan wahalar haihuwa ba haihuwar ba shan ruwa bane".


Dariya Ahmad yayi cikin sanyinshi yace.


" toh ni dai nasan biyaye na ba mak'aryaci bane kuma Na yard a da zancensa".


Shiko Yusuf kawai d'akin ya wuce yana shiga ya samu Aysha na rik'e da woya daga duk kan alama da Ummi take mgn dariya take tana.


"Wlh Ummi da gske Na Haihu kizo ki gani mana".


Karb'e woyar yayi yana dariya yace.


"Ummi ke dai kizo kigani"

Cikin gsky da gsky tace.

"Ni banson shirme fa"


shima cikin gskyar yace.


"Allah Ummi kizo ki gani"


Toh kawai tace.


A parlon kuwa tare suka fito shi yana rik'e da macen ita kuma tana rik'e da Na mijin.


Kaka kam tana ganin Aysha ba ciki sai yara a hannu ta bushe a tsaye tana zare ido da tafa hannu, 

suko su Ahmad karb'ar yaran sukayi suna ta ruk'k'umarsu da sanya musu albarka,

Ita kuma Aysha jikin kaka ta rab'a cikin tsokana tace.


"Kinga Hamma Yusuf d'ina ko yazo ya takalo nak'uda ya kuma karb'i haihuwar bamu ma baki tsoroba".


D'an tureta tayi tana.


"Can tafi daga nan Ku dai wlh Allah ya shiryeku".


Shiko Hamma Yusuf dariya yayi ya tallabo matarsa cikin so da k'auna yana.


" kin biyani ban mancewa da ranaku biyar masu haske a rayuwata".


Ahmad da Adam da kaka kam farin ciki kamar su had'iye hak'oransu.


Kafin ace kobo gida ya cika da yan uwa yadda matansu Usman dasu Rabi,u 

Su Ummi harda kukan farin ciki Hydar ma yana ji ya kawo Goggo Aysha da matarsa Nafeesat Aysha kam tana shan gata da kula 

Yusuf ko duk nacin kaka da Goggo Aysha dole suke hak'ura da Yusuf da ya nace shifa tare zaike kwana da matarsa da yaransa dole suka yarda dan in sun hana ma a gunsu yake tarewa 

Ummi zatayi fad'a yace.

ai yasan abinda yake shima kawai zai kula dasune.


Ran suna yara sunga gata da so gun kakannisu da iyayensu 

Ahmad da Adam sun taka rawar gani inda suka hana Yusuf kashe ko sisi 

Yaron

Yaci sunan Abubakar Abbanshi yace a kirashi da Abubakar d'inshi shi kuwa Babiker yake kiranshi ita kuwa mace sunan Ummi Aysha tace asa mata ana kiranta Mami,

Anyi suna lfy an waste lfy


Yara sun samun kula da gata tako wanna bank'aren.

Yusuf kuwa duk lkcinsa Na matarsa ce da yaransa ba ruwanshi ko gaban kaka lallatsata yake yana shi fa wlh ya gaji ai jego kam ya k'are.

Kaka ko tace jeki ya d'irka miki wani cikin tun yanzu shi ko a jikinsa.shi kuma sai yaita dry kawai.



Yau asabar ta kama kuma yau satinsu 4 da haihuwa,  

Tara dai dai Na dare suka waste hiran da suke a parlon,


Yusuf ya d'auki Mami dake bacci,

Cikin murmushi ya manna mata kiss a goshi sannan ya kalli Kaka yana dan dry yace.


"Kaka kalli yadda yarannan suke ta k'iba gashi basa rikici sai suita bacci abinsu shi babiker yamafi Mami Na girmi".


Cikin tuna baya tace.


 Aishi Abubakar komai Na mai sunan shi ya d'auko in mutun ya ganshi zaice d'an shine Na cikinsa".


Lkci d'aya fuskar Yusuf ta sauya, ya Sa hannu ya karbi yaron daga hannu Aysha ya had'a da Mamin ya ruk'k'ume su,

A take kuma ya juya ya tsurawa TV ido  cikin bugawar zuciya

Tashan 

MBC Bollywood ne suka sako tallan film d'in

*Kal ho laa Ho* 

wak'ar ya rink'a ratsashi yana tuna mai d'an uwanshi yana tuna yadda babiker ke son film d'in

Lkci d'aya jikinshi ya fara tsuma cikin sanyi ya mik'e rik'e da yaran ya wuce d'akinshi,

kan gado ya dire yaran yaje yai alwalah yazo yai ta nafilfili yana mai yiwa d'an uwanshi addu,a.


Ita kuwa Aysha a parlon jikin Kaka ta rab'e cikin sanyi tace.


"Kaka yau kuma Hamma Yusuf ba zaiyi bacci ba

Kaka me zan mishi in sama mai nitsuwa Na tabbata yau kwana kuka zaiyi".


Cikin share k'ollah Kaka tace.


"Aysha nima bansan ya akayi nayi mgnar Abubakar ba da nayi shiru".


Cikin sanyi tace.


 "Kaka ko bakiyi mgnan ba TV ya tuna mai ya Abubakar"


A hankali tace.


"Aysha tashi kije ki taushi zuciyarsa"


 Haka ta mik'e cikin sanyi taje gareshi 

tana shiga ta zauna gefen yaran ta zuba mai ido yana karatu k'ur,ani yana zubda k'ollah.

Lkci d'aya shima yaro ya fara kuka,

Itama Aysha sai ta tsurawa Hamma Yusuf d'in ido tana zunda hawaye.


Jin kukan yaron yasa ya rufe karatun yazo ya d'auki yaron ya mik'a mata ganin tana kuka yasa ya had'a su da babiker din ya ruk'k'ume.


Cikin sanyi yace.


"Na  bari kema kibar kukan

Nasan ganin halin da nake ciki ya saki kuka toh Na bari Amrita bazan sake ba".


Cikin kukan tace 


" kayi alk'awari"?


A hankali yace.


"Zanyi alk'awari bazan sake kukaba sai dai nai ta mai Addu,a,

Amman kuma kema yau ki tausaya ki motso gareni Dan begenki ya kusan karni".


Cikin sanyi tace.


"Hamma Yusuf ban gama workewa bafa"


Dariya ya d'an yi sannan ya d'age yaron daga cinyarta dan ya koma bacci ya kontar da yaron cikin sanyi yace.


"Waya ce miki baki workeba aike bazaki San kin workeba sai ni zan gano mana hakan ke dai bani Na d'an d'ana wlh zan miki a hankali ".


Ita dariya ma ya bata shisa cikin dryar ya lallaba ya hard'e abarsa, cikin sanyi da kewar juna suka haukacewa juna ya rink'a juyata da sarra fata. 


Cikin gamsuwa da Amritarshi ya kalleta cikin iya gskyarsa yace.


"Amrita d'aya tawa tamkar da dubu bakya canzawa sai k'ara d'an d'ano da kike kullum jinki name kamar Daren forkonmu".


Ita kam sai sumbatarsa take tana shafa sajensa.


 Haka rayuwa ta  mik'e musu cikin jin dad'i.




            *********


  *Bayan shekara 8*


Wani yammaci mai dad'i iskar damina Na kadawa gari yayi shiru sai sanyi mai k'amshi dan ruwan da akayi aka d'auk'e sai duhu da duniyar tayi 

a hankali Hamma Yusuf ya shigo parlon Ayshan dayasha gyara sai k'amshin da yake fiddawa ta kashe wutan parlon ta kunna wutan cikin shoo glass sai ya bawa parlon wani kala mai kyau.


Yaran dake zaune a parlon su 6 suna ta wasa suna ganibshi suka ruga gunshi

Mai dan girman cikin Wanda suke kira Yusuf yace.


'Abba kaga Ahmad ko tun dazu yanata zagin Nana Wai tayi sallah bata yiwa Abbinmu Addu,a ba ita kuma tace tayi" kanwar Ahmad k'aramine Yar Adam shiko Yusuf baison ana tab'a k'anneshi matan ko kad'an.


dariya Hamma Yusuf yayi cikin d'agawa Amritanshi gira yace.


"Kuna jina ko duk Wanda Baiwa Abbi Addu,a zanyi fad'a dashi kuma bazan sake zuwa dashi saudiba".


Cikin son Wanda sukewa Addu,an suka rink'a cewa.


 "Abba wlh kullum muna mushi, Abubakar k'ara mi yace "ni kullum sai namishi kuma incemai ina sonshi"

Mamice tace Abbah Nina ina mishi".


dariya yayi cikin jin dad'i yace.


"Allah ya muku albarka"

 Cikin far in ciki suka amsa tare da ficewa suna Abba zamu tafi gidan Baba Adam yace gobe zai kaimu Yola "


Cikin jin dad'i yace.


 "Allah kiyaye hanya"

har zasu fita Aysha ta kalleshi da kyau dan tasan inda yadosa

Sai tace.


"Hamma Yusuf cikin sanyin nan,? maza ku dawo"


Da sauri yace.


"Kai maza  Ku tafi Ku gaida su".


Aiko suka fice suna murna shiko suna fita.


Ya matsota cikin hararan love yace.


ai kin San abinda ke tare dani shine zaki taramin yara su tafi can Adam yaji dasu kinga kaka nacan zata tare musu yaran suma su hole".


Hannu tasa ta d'an tureshi tana.


"Kai girman ma kamar k'arama abin yake mutun kamar inji".


Cikin rawan lips yace.

 

"Allah a hannu nake"


 yana fad'a yana binta a baya

 Ganin zata mai nisa ya cabkota ya wuce da ita bedroom d'inshi suna shiga suka fad'a kan gado cikin rawan sanyi da rawan lips ya jawota jikinshi yana shafa bres d'inta da suke cike tib kamar bata tana sharyawa ba sai shek'i suke itama tuni tafara juyashi tana latsar lips d'inshi da suke ta bari dan fitina cikin kid'ima suka mak'a lewa juna murya na rawa yace.


*"Amrita jamana blanket kar Aysha Ali Garkuwa ta gammu ta samu abin rubutawa masu karatu".*


```Alhamdulillah ala kulli halin.  

 Na godewa Allah daya bani ikon kammalah labarinan lfy ina godiya gareku my lovely fans Allah ya barmu tare 

Har kullum kuna raina 

Masoyana```


```Afwan Afwan Afwan ina Neman yafiyarku 

Mace ko namiji baba ko yaro Wanda Na sani da Wanda ban saniba Wanda Na tab'a mgn dashi ko ita da Wanda ban tab'a mgn ba ni na yafewa kowa```


Jinjina gareku groups.


By Garkuwan Fulani

[4/18, 10:14 PM] Aisha Aliyu Garkuwa: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAYI NADAMA*

👆🏻👇🏻👇🏻

*MI,WASMITI* page 1⃣2⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


Pure moment of life writer's  

                 P.m.l.w


www.aishaaligarkuwa.blogspot.com



```Dedication gareku Ango 

Nura m inuwa da Amarya  Amina Tijjani wado Allah ya sanya Alkhairi a aurenku ya Baku zuriya d'aiyiba Allah yasa ayi a Sa,a 

Rabbi ya haskaka rayuwarku```


*🎷🎺🎤Yehhh Na jinjina muku yan social media ba mai rabani daku jama,ar social media kui haquri ga baitinku na biya*.


``` Mun jinjina muku Readers damu daku d'aya ne masu karatu kui haquri ga baitinku na biya```


*Tabba yarku ta isoni kamar haka?.*


Garkuwa a baya kinyi wani kuskure novel din *Mi,WASMITI* da kikayi a duniya dad'inshi yayi ta kewaya groups ya shiga sak'ok'in Nigeria shin meyasa kika ware 'yan wasu groups d'in?.


Su sukace ayi miki tabbaya nikum can zanmiki tabbayar sheidar suna k'aunarki gaba d'aya.


~Na jinjina muku y'an social media ba mai rabani daku Jama,ar social media kui haquri ga baitinku Na biya~


*Yehh dole naje duk inda rebo yake Na dena so babu gurin zuwa,

ban raina ranar da novels tai mini ta sanadi an sanni garuruwa,


😍😘Ina fahar da, group din 

Garkuwa family agida nake tun fari su sukayi mini Garkuwa😍


Tinda nazo a cikin y'ay'an Adam duk ajizi ansanshi da mantuwa. 

Kui haquri ga baitinku zan biya.


Garin masoyi nisa bai mini dana fad'a kuma yanxu ina tini,

Allah ya k'addara in zamto zuma dana fito ai taimini sansani.


Yau haquri zan baiwa zan baiwa fans na da sunfiso Na tsaya tamkar gini Rabbi nufeni silar novel da zanyi a gaba mutan k'asarmu su zauna lfy.


```Forko mutan PURE MOMENT OF LIFE  WRITERS zanai kira Wanda fagen Rubutu basa jira manya da yara a gsky na sansu da hattara sunce nazo naga yadda batin sannan na tabbata ni sukayin jira na mori so k'aunar da suke mini sunce na dage tannin k'irk'ira 

Kui haquri ga baitinku na biya``` 😘😍



Y'an JANNART LAMID'O novel  group duk Nisan da nayi musu amman dani sai alfahari suke novel na in sun gani ko a fushi suke   farin ciki gurbi nasa zai shige da zanaje ni  mu zauna so suke basu da niyar tsigen fiffige da gsky nunan k'auna suke Dan sun kirani sunai mini magiya, 

Kui haquri ga baitinku na biya.


Na am b'ato mutanen ANEELURV ONLINE WRITERS group su y'an k'waraine basu da Tsok'k'oma idan kaje kafad'a musu zasu rikeka da kyau harda lallama.



K'orai k'arai Na gane duniya mai sonka shikeyi maka iddima 

 Masoya na MELODY NOVEL  WRITERS gaisheku nai kuke reba gardama 

Kui haquri ga baitinku na biya.


A FASAHA ONLINE GROUP

 Sunana ya shahara In an kirani jama,a basa gudu. Dan haka nai kiransu da azzama zasu rik'e ni muje mu haye tudu albarkacin k'aunar da suke mini Na dad'i suke Jan ragamar social media toh Ku sanyi bazan manta suba.

 

WRITERS mu zamto tsintsiyaaa.


Mutan MUSAN KANMU MARUBUTA group gurinsu Na yana basu shiri da mai mini hassada farin halinsu yasa suka kauda kai harma suke nema suyimin gata.


Inda tarin masoya a ASY KHALEEL  NOVEL WORLD group kunji yanxu Garkuwa ina fad'a

Kui haquri ga baitinku na biya.


Mutan DAN GYARANKANMU group sunai mini Addu,a fatansu ko yaushe Na wuce Sa,a 

k'auna suma ba,a barsu a bayaba basa zama da mutum mai min ba,a.


NOVELS ARENA group Yadda suke mini cikin su suna akwai ni da jamma, a. 


UMMEE GARKUWA NOVEL GROUP zafi Kansu yayi musu da sunji nai jinjina a novel ban sasuba suna fad'a mini son da suke mini koda idanuna bai gansuba

kuji dalilana Y'an 

Ummee Garkuwa novel group jinjina gida biyune kuma narraba muna kamar k'aunar da kuke mini idan Na raina nayi k'uriciya.


Yehh y'an SMARTES ONLINE WRITERS

Kullum tunan suke nai musu baiti laifin ya wuce. 


NOVEL GROUP kafin nai musu baitinsu sai kuma duniya ta d'auki Wai bazan k'arisa novel din mi,WASMITI ba.

Kui haquri ga baitinku Na biya


Kai kuji sabon al,ajab UMMYN YUSRAH NOVEL group suna nema forgive sun fadan Na Dave da Addu,a mai hassada shi zai zsmma sankace.

Kui haquri ga baitinku na biya,


Rufaida NOVEL group Sabon zance suke Wai ya akwai nace bazan sasuba toh ga baitinku Na biya.


Can TABITAL FULAKU Suna tausa yamin sabida matsala  ciwon idon da nake fama shi barin infad'a muku kar Ku damu rabbi yana tare dani zan rayu k'alau kan gsky .


NOVEL MAKEUP & KITCHEN na yeba domin a fuska kunai mini farra,a

Kui haquri ga baitinku na biya.


Group d'in

 UWAR

GIDA & Hauwa novels  group dana zagaya

Cikin su Aysha Ali Garkuwa kamar a  group MAI,ADASHE,S FAMILY  nake.


MU GIRKA DA KANMU group da ZANGON LABARAI group Na Gaza rerrebe irin k'aunar da mukewa juna yadda kuke mini ga baitinku Na gino.



GROUP d'in ZAUREN GUZURIN GOBE ALK'IYAMA da 

Group d'in 

RAYUWAR MATA A MUSULUNCI kamar da zan wuce akwai masoya Na ciki Na tuno 


(HUMM Addu,a bata fad'uwa k'asa 

Wata ran sai Na zamo tauraruwar duniyaaaa)



Dubun jinjina da k'auna zuwa gareku masoyana wadanda ban abbaci sunan groups dinkuba  ban banta dakuba fans Na aduk inda kuke INA k'aunarku😘😍😘😍😘😍




Fatan Alkhairi a garemu baki d'aya sai min had'a a novel Na gaba



By Garkuwan Fulani

No comments