Furar Danko Book 2 Page 5

 𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲






  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗




           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻



      𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔

𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣




........Basuyi mata allurar zubda cikin ba kamar yanda Alh. Sulaiman da Dada suka bada umarni har Lulu ta farka, an gama dai duk wani shirye-shirye har Dada ta saka hannu. A hankali ta buɗe idanunta da sukai mata nauyi sosai tana bin ɗakin da kallo, sai da hankalinta ya gama dawowa jikinta sannan ta fahimci a asibiti take. Yunƙurawa tai da niyyar tashi sai hakan yay dai-dai da shigowar Dada ɗakin. “Sunahanallahi Mawaddat kin tashi?” cewar Dada tana nufota. Ita ta taimaka mata ta ƙarasa tashi, tare da kaiwa zaune a kusa da ita. Hakan ya bama Lulu damar kwantar da kanta a jikin Dadan tana hawaye. “Yaushe kika zo?”. Ta tambaya cikin raunin murya irin ta mara lafiya. Cike da kulawa Dada ta sake rungumeta a jikinta da faɗin, “Tun ɗazun dear. Ya kike jin jikin naki yanzu haka?”.

      “Dada ko ina namun ciwo, ga yunwa ina ji sosai”.

     “Ba dole kiji yunwa ba kina ɗauke da jinin yunwa. Shegen yaro da bai wuce saiti abu yi guda ya ɗiraka miki ƙunshi ya barki da jidali”.

    Da mamaki Lulu ta ɗago ta dubi Dada saboda rasa gane ina zantukanta suka nufa. Dada ta ƙyaɓe baki cikin hasala tana yin ƙwafa. “Dada wai mi kike faɗi ne?”.

           “Mtsoww ba komai tashi muje na kaiki ki wanke baki kizo kici abincin”. Duk da Lulu na son jin fassaran zantukan na Dada sai batai musu ba ta tashi a jikin nata, da taimakonta ta wanko bakinta da fuskarta suka dawo. Apple da tace tana so ta bata ta sha, takai kusan rabi ta ajiye ta ce ta bata yugut. Shi tasha sosai dan kaɗan ta rage a babbar robar da yake ciki. Sosai Dada ta saki baki tana kallon Lulun kamar wadda ke'a cikin yunwa. Ɗan gumin da ya tsatstsafo mata na ƙoshi ta kai hannu ta share tare da komawa jikin Dada ta lafe. Shigowar Dr Olivia ya sakata miƙewa zaune. Sannu Dr Olivia ke mata cikin fara'a da jin daɗin ganin ta tashi da daɗin rai, bayan ta ɗan tsokanarta ta ciro allurar da zatai mata. Lulu bata wani damu ba, dan ta ɗauka normal allura ce, dan haka babu musu ta yarda akai mata doctor na cigaba da tsokanarta.

          Minti talatin dai-dai dayin allurar nan wani irin ciwon mara na azaba ya tasoma Lulu. A take jikinta ya fara vibration, tai wani irin dunƙulewa waje guda tana kiran “Wayyo ALLAH na Dada marata”. Yanda ta saki siririyar ƙararar sai da zuciyar Dada ta harba, hankali tashe tai amfani da wayar landline dake a ɗakin tai kiran doctor Olivia. Tamkar dama a kusa take babu jimawa sai gata ta faɗo, zuwa sannan jini ya ɓalena Lulu abin babu daɗin gani....


      Iya wahala da azaba Lulu ta Shashi, inda da ƙyar aka samu jinin ya tsaya, akai mata allurar barci tare da gyarata, barcin wahala ne ya ɗauketa sai wata irin tagwayen ajiyar zuciya take saukewa a cikin barcin. Dada da duk ta shiga damuwa ta shiga tambayar doctor yanda ake ciki, Doctor ta tabbatar mata da aiki yayi ƙyau, dan yanzu haka dai ciki ya fita sai kuma ɗan jiyyar jiki da Lulun zatai na kwana biyu. Wata irin ajiyar zuciya mai nauyin gaske Dada ta sauke, a take tai kiran Alh. Sulaiman, a lokacin yana tare da su Hon. Misau suna tattauna batun Daddy. Kamar yaƙi ɗauka sai kuma dai ya ɗaga yana kaiwa kunne. A ɗan daƙile ya ce, “Dada nafa sanar miki inada uziri, mi kuma ya faru yanzun?”.

         A ɗan ɗokance da ture maganarsa ta farko Dada ta ce, “Ai an kammala aiki yanzu haka ciki yabi gottern turawa kuma”. Ajiyar zuciya Alh. Sulaiman yayi da faɗin, “To maddala, na san zasu sallameku yau ku koma gida, zuwa anjima idan na samu nutsuwa zan kiraki”. Daga haka ya yanke wayar batare da ya jira tace wani abu ba. Hakan ya bama Dada haushi dan bata gama maganarta ba, amma sai batace komai ba bayan jan tsoki. Kamar yanda ya faɗa zuwa dare da Lulu ta sake farkawa aka sallamesu. Duk da Lulu najin jikinta cikin rashin ƙarfi kwata-kwata ga jiri na ɗinarta bata kawo komai a ranta ba. An basu magunguna suka hau cab zuwa gida. Sun samu Ummita ta gama gyara ko'ina sai tashin fresheners masu ƙamshi da gidan keyi, cikin ƙarfin hali Lulu ta ce ma Dada tana son tai wanka first, amma ta taimaka mata. Dada da kanta ta cuccuɗa Lulu tare da taimaka mata suka fito, kaya ma da taimakonta ta saka, tana gama sawa tasha tea ɗin da mai aikinta Ummita ta haɗa mata bisa umarnin Dada. Sosai ta sha shayin har ma abin yaso bama Dada mamaki, ita dai cikin sauke numfashi ta koma ta kwanta dan barci takeji har yanzun.


       *_BAYAN KWANA UKU_*


  Yau kawani uku kenan da zubar da cikin jikin Lulu da batasan da shi ba ba kuma tasan an zubar ba. Ta ɗan ƙarasa jiyyarta ta kwanaki biyu yayinda Dada ke kula da ita a duk motsinta. Yanda ta miƙe da wuri zai baka tabbacin zuwan Dada yay mata daɗi, dan akoda yaushe tana nane da ita. Duk da tana jin kewar ƴan gidansu musamman Daddy, Uncle Yousuf, Da Ammah sai take ƙoƙarin dakewa da sakama ranta haushinsu akan basa sonta. Ga kuma Dada a kaikaice tana sake cusa mata laifinsu hadda sharri. A duk sanda kuma Dada ta ɗakko zancen Smart sai Lulu taja tsaki da yamutsa fuska cikin shagwaɓa tacema Dada bata son ji, ita a daina mata koda zancensa. Hakan nama Dada daɗi da sake zaburar da ita cusa ma Lulu ƙiyayyar Smart a zuciya har ma da su Uncle Yousuf. Tun ma abin baya tasiri a ran Lulu har ya fara a randa take cika kwanaki biyar da samun lafiya a bazata sai ga Alh. Sulaiman da Tajuddeen. Lokacin tana kwance a falo tana kallo. A zahiri ta warke ragal. Sai dai tana jin wani irin kasala da son shan fruits, dan rigima ma yau sai cewa tai a mata kunun gyaɗa. Da Dada tace ina za'a samo wata gyaɗa anan sai ta sanya musu kuka na gaske. Dole Dada tai kiran wani saurayi ɗan ƙawarta da suma suke nan Canada ɗin amma asalinsu ƴan Nigeria ne ya bazama nemawa Lulu gyaɗa. Sai ko gashi ya samo, Ummita ta amsa ta haɗa mata kunun data buƙata sannan aka samu lafiya. Wannan kunu shine a gabanta har zuwa yanzu lokaci-lokaci takan zuba tasha abinta har sai taji yakai mata sannan ta ajiye. Sororo tai da ganin Uncle ɗin nata da Tajuddeen, dan ita dai ganin nasu yazo mata a bazata. Yanayinta babu yabo babu fallasa ta tashi zaune tana musu sannu da zuwa. Sai kuma ta ɗan dubi Tajuddeen a yatsune tare da balla masa hararar kallon ƙurillar da taga yana mata. Sanye take da doguwar riga kalar ja da tabi jikinta ta lafe, sai rigar sanyi data ajiye gefenta kasancewar gidan akwai hitter dake ɗumama ko'ina. Rigar ta fisga ta sanya tare da komawa kwancenta kamar yanda take da. Sai dai ta danna wani ɗan maɓalli dake gefen kujerar ya bada ƙara sai ga Ummita da sauri ta fito da ga wani ɗaki tana faɗin, “Aunty kina buƙatar wani abu n...” ta kasa ƙarasawa saboda ganin baƙi. Batare da Lulu ta kalleta ba ta ce, “Ki sanarma Dada anyi baƙi”. Ummita data zube tana gaida su Tajuddeen ta amsa da to tana miƙewa ta nufi ɗakin da Dada da Lulun ke kwana. 

     Ta wutsiyar ido Alh. Sulaiman ke kallon Lulu da nazartar ta, ba yau ya fara fahimtar girman kai da izzar yarinyar ba irin ta uwarta da ma shegen ubanta ce. Dan duk da yake amsa sunan yayan mahaifiyarta bata wani sakewa da shi, hasalima a duk sanda suka haɗu takan dinga acting like tana jin haushinsa. Hakan yasa yake zargin ko mahaigunta ya sanar mata wani abu a kansa ne. Wata ƴar ƙaramar ƙwafa yayi ciki-ciki a ransa yana faɗin (Zan dawo dake cikin hankalinki ai yarinyabke da ubanki dama duk mai daure miki ƙugu). Tajuddeen kam kai tsaye ya kafe Lulu da kallo, itako duk da tana jin idanunsa a kanta tai biris da shi tamkar bama tasan ALLAH yay zamansa a falon ba da ga shi har ubansan. Laifin Tajuddeen ne ya shafi mahaifinsa Alh. Sulaiman a wajen Lulu, dan bama shi ba, duk wasu ƴan gidan su Tajuddeen Lulu ta tsanesu a dalilin Tajuddeen ɗin ba kamar yanda shi Alh. Sulaiman ke tunanin Daddy ya faɗama Lulun sirrinsa bane.

      Cikin nuna mamaki Dada dake fitowa ta ce, “A'a wai dama da gaske ne kuna tafen ashe dai?”.

          Murmushi Alh. Sulaiman yayi da amsa ma mahaifiyar tasa da “Wlhy kuwa Dada ai na tabbatar miki babu abinda zai hanamu zuwa. Idan muka gaisheki sai mu wuce mu duba Baba kuma duk da shi Tajuddeen zai dawo nan Canada ɗinne akwai aikin da zaiyi”. Dada bata samu damar bama ɗan nata amsa ba saboda miƙewar da jikanta yay Tajuddeen yaje ya rungumeta. Lulu da duk ke saurarensu gabanta ya faɗi jin wai Tajuddeen yazo aiki ne nan Canada. To lallai dolene kam tabar ƙasar nan kenan a wannan gaɓar. Dan bataga haɗin kifi da kaska ba tsakaninta da Tajuddeen bazasu taɓa kasancewa a inuwa guda ba. Tsam ta miƙe cike da izzar nan tata sai dai rashin ƙarfin jiki na ciwo duk ya cinyeta a tsaye ta ɗauki flaks ɗin kunun gyaɗarta ta bar falon. Su duka da kallo suka bita kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa. Dada ta katse shirun da faɗin, “Bara yarinyar nan ta shirya muku abinci ko. Sannunku da hanya”.

    Bakin Tajuddeen a washe yana sauke nannauyar ajiyar zuciya da ga dawowa hayyacin bin kallon Lulu da yay da ido ya kalli kakar tasu. Ido ya kashe mata tare da mata nuni da ɗakin da Lulu ta shiga da baki. Dada tai ƙaramar dariya da faɗin, “To Alhaji zumuɗinka kadai bi komai a hankali, dan bamu san wane kalar barbaɗe shegen yaron nan yay mata ba, maybe bata gama dawowa cikin hankalinta ba ta kuma butsare mana a karo na biyu kadai san halin taurin kai irin na Mawaddat da shegen fitina”.

        “Karki damu Grandma, komai zai tafi dai-dai kamar yanda aka tsarashi. Indai ni ne a wannan gaɓar babu garaje. Bamma san tasan komai har sai an ɗaura auren”.

     Ƙaramar dariya Dada tayi, yayinda Alh. Sulaiman ya kura musa ido kawai, sai dai baice dasu komai ba.......✍️



       _🤔To an taɓa aure akan aurene? Yau naga lukutar masifa Dada da Alh. Tsule fa babu man kai zasu iya ɗaurawa...🚴🚴🚴_




_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_


*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*


FURAR DANKO

Billyn Abdul


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay at👇


1487616276 

Access Bank

Bilkisa Ibrahim Musa

Sai katura shedar biyanka anan👇


09032345899


Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇

09033181070



*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*


*THANKS FOR CHOOSING US*🥰


Zafafa🫶🔥




*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

No comments