Furar Danko 82

 




𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣2️⃣



.......Dada tayi tunanin Lulu zata sake dawowa gidan, amma bayan duk ƴan rakkiyar Baba sun dawo sai gashi babu ita, sai ma sanar mata da akai ta wuce gidan ta. Hakan ya sake girgiza Dada ta kuma tabbatar da eh lallai da alamar ƙamshin gaskiya a zancen mutanen nan asiri yaron nan yay ma jikarta. A take ta dannama Fulera mai ƙunshi kira, batare dako amsa gaisuwar ta ba tace ta sameta yanzun. Fulera ido a kuɗi tuni tai tsalle tayo waje da ga gidan su, dan dama dai zawarci take kusan shekara tara kenan. Cikin ƙanƙanin lokaci sai gata a Garko house. Ta sami Hajiya Dada tare da mai aikinta dake mata irin waɗan nan ayyukan na sirri, dan Dada tunda jajayen sawu ƴan hannun bin malamai ne kam. Cikin gurfana Fulera ta miƙa gaisuwa, Dada ta amsa cike da isa. Babu wani jan lokaci ta sanar musu abinda take son a mata. Zasuje wajen mutumin da tace mata a Zuru ita da mai aikinta. Ba haka Fulera taso ba, amma dai babu damar musu dan haka ta amsa da to. Mota Dada ta bada akaisu tare da kuɗin amma sai ta damƙawa mai aikin nata. Nan ma Fulera taji zafi, ta dai danne, damar fara fita data samu kafin mai aikin Dada ta kimtso ta samu ta dannama Hajiya Naqiba kira ta sanar mata komai. Dariya Hajiya Naqiba tai da faɗin, “Kai tsohuwar nan mayyace akwai shegen wayo. Barta ai inta san wata bata san wata ba. Kwantar da hankalinki bari na kirashi kafin ku isa.”

   Haka kuwa akai hajiya Naqiba tai kiran malam na-zuru, duk yanda suke so haka ta tsara masa, shima da yake shegen kansa ne yace karta damu. Abinka da lafiyayyar mota basu sha wahala ba, dan bayan azhar kaɗan suka isa zuru saboda gudu na masifa da drivern yayi. Malam na-zuru da yake yasan da zuwansu kafin ma su faɗi abinda ya kawosu ya shiga zayyane musu wai ai ya gani ne a cikin aikinsa. Tuni mai aikin Dada ta ruɗe ta danna mata kira, nan ma fa sukai magana da malam Na-zuru ya sake fanfa Dada da kalolin sharri wa Smart dangane da auren Lulu, harda cewa ai asiri Smart ɗin yay musu dan yaga kuɗi. A yanzu haka ma yana Niger yaje anyo masa wani babban ƙulli, zaita kwantar musu da kai ya nuna shi na ALLAH ne sai anan gaba kaɗan zai bayyana halayyarsa da mugun nufinsa. Tsaf Dada tahau ta zauna saboda tayi imani da malaman tsubbu matuƙa gaya. Malam na-zuru ya haɗa musu kayayyaki suka sake ɗakko hanya....

   WASHE GARIN Lahadi Lulu da ƴan kwananta ta zubasu a mota ta kaisu sabon Saloon da ta fara zuwa yanzu ana mata gyaran jiki. Tsaf aka gyara ƴammatan nan suka fito tas da su kamar basu ba. Daga Saloon sun shiga wani joint suka ɗan sha ice-cream da abinda baza'a rasa ba. Daga nan suka koma gida. Kasancewar duk sun gaji kuma basa tare da yunwa suka shige ɗakin dake matsayin masaukinsu masu kwanciya nayi masu fira nayi. Itama anan falo ta ɗan kwanta dan ta haɗiyi kayan nata duk da kaɗan take sha dan kar yaran su fahimta. Wayarta ce ta shiga ruri, takai hannu ta ɗauka tana jan ƙaramin tsaki. Ganin Dada ya sata waro idanu waje, sai kuma ta ɗaga da sauri. Kafin tace komai Dada ta ce, “Ina mai gadin naku anata horn kamar ya mutu”. Da mamaki Lulu tace, “Mai gadi kuma Dada? A ina wai?”.

    “Gidan da aka kawoki mai kama da bukkar fulani”. 

  Dariya Lulu tai tana miƙewa. Ta ce, “Uhm Dada baƙya gajiya dama mutane sharri idan baki son su. Wannan gidan ko makaho ya shafa ai yasan badaga nan ba. Ina zuwa”. Ta yanke wayar tare da zura slippers ta fita. Da kanta ta buɗe musu gate ɗin. Dada na hakimce a bayan danƙarereiyar motar da sukazo baƙa wulik, sai drivern ta. Koda ya samu waje yay parking sai da ya buɗe mata ta fito tana wani yamutse fuskartar ta tsufa da bin gidan da kallon banza. Yi Lulu tai kamar bata fahimceta ba ta rungumeta tana murnar ganinta. Dada ta tureta da faɗin, “Ni karki kadani fitinanniya”. 

   “Ni na isa kadaki Hajiyar Baba Garko. Yanzu yana asibiti yana fama da kansa ke kina nan kina yawo”.

   “Oh kijimin yarinya da ƙulli, yanzu zuwa na dubakin kuma bammayi miki gwaninta ba kenan”.

      “A'a kimun yi haƙuri muje ciki”.

   A falon ma dai Dada sai yamutse-yamutse take duk da ya mata ƙyau matuƙa. Nan ma Lulu tai kamar bata lura ba taje ta kawo mata ruwa da lemo. Tana zama ta jeho mata tambayar “Ina yaran dana ganki da su ɗazun?”. Cikin rashin damuwa Lulu ta nuna ɗakin da su Maryam suke. Ɗan jimm Dadan tai sai kuma ta miƙe, “Kinga muje ɗakin ki magana nazo muyi”. Babu musu Lulu ta miƙe suka nufi bedroom ɗinta da Asma'u ta gyara ƙal sai tashin uban ƙamshi yake yi. Nan ma dai sai da Dada ta gama ƙare masa kallo sannan ta ja numfashi. “Kaya har kaya anzo an zubesu a wannan takurarren gidan.” ƙin cewa komai Lulu tayi, dan haka Dadan ta cigaba da faɗin, “Game da zuwa duba Alhaji ne. Shin zakije ne?”. Ɗan jimm Lulu tayi, sai kuma ta nisa da faɗin, “Ina son naje kam Dada, sai dai yanzu Aliyu yayi tafiya maybe ya dawo gobe. Idan ya dawo mukai magana sai kiji”. Sosai zantukan lulun ke sukar Dada da sake gaskata fa amma jikarta asiri, yo Mawaddat ɗin ta data sani mai zafin nan da ƙyamar abu ga murɗaɗɗen hali wai namiji ke juyawa haka. Namijin ma talaka ɗan talakawa fitik mai amsa sunan drivern ta. Kai wannan al'amari akwai ayar tambaya. A zahiri kam murmushi tai da cewa, “To ba laifi hakan ma yayi. Af kinga zan manta ga wannan kisha maganin ciwon maran nan ne dake damunki dama nace zan amso miki, inata shiririta sai kwanaki aka amso kinata zuwa gidan kuma ina mantawa. Shiru Lulu tayi tana kallon goran ruwan kamar tace a'a sai kuma dai ta amsa, dan ranta bazai taɓa bata Dada acikin jerin wanda zasu iya mata wani abu daban ba, sannan tana saran ganin period ɗinta nan da kwana uku, tasan kuma azabar da take sha na ciwon maran. Amsa tai ta ajiye gefe, amma sai Dadan tace tasha mana. Ai ba'a wasa da magani. Badan Lulu taso ba ta buɗe tasha kusan rabi ta ajiye. Daga haka suka cigaba da hirarsu da Dada wadda duk bugun cikine akan auren nan da son sanin wanene Smart. Ita dai Lulu tana bata amsar abinda ta sani ne kawai, har cikin ranta kuma bata kawo komai ba. Sai da Dada take cemata tafa kula, karta yarda yaron nan ya mata wayo ya kwanta da ita, dan yanda kwanakin nan suka kusa cika zai iya shirya mata muguntar maza. Lulu tai murmushi da faɗin, “Dada kenan nace miki ki kwantar da hankalinki, Shifa Aliyu ba irin waɗan nan da kike tunani bane. Na tabbata tunda har ya amince da auren nan na wata ɗaya ne kuma zai sake ni bazai taɓa saɓawa ba zai sake nin, yanzu haka ma jiran dawowarsa nake mu fara maganar dan shiyyasa nace ki dakata da batun tafiyar nan, cases ɗin dake gabana zanyi ƙoƙarin kammalasu na ɗan ɗauki hutu daga duba Grandpa zan ɗan huta kafin na dawo Nigeria gaskiya”.

   Sosai Dada taji daɗi dan haka ta shiga sanya mata albarka. Daga haka ma sai ta miƙe tana faɗin, “To bara na wuce tunda na kammala abinda ya kawo ni. Sai na jiki ɗin”.

   Da sauri yabar jikin ƙofar ya shige bedroom ɗinsa. Wani irin harbawa zuciyarsa keyi da sauri-sauri. Dan shigarsu ɗakin babu jimawa ya shigo gidan. Duk da yay mamakin ganin mota baƙuwa a waje yay zaton kota Lulu ce aka kawo saboda bai ga driver ba, ashe ya ɗan fita miƙe ƙafa. Ya shigo gidan yaji shiru, ya wuce ɗakinsa kai tsaye ya ajiye kayan hannunsa shine ya nufo ɗakin Lulu da tunanin ko barci take. Kawai yaji Dada na magana a hanakali cikin salon makirci na tsoffin mata tana bugar cikin Lulu, shine fa ya nutsu. Jin komai ya sake tada masa da hankali, dan yanzu ne ya fahimci ainahin abinda take nufi da wata ɗaya wata ɗaya da take ta ambata masa zata koma free. Zuciyarsa ta sosu da tunanin shima Uncle Yousuf yaudararsa yake kenan? Sai kuma wata ke kwaɓarsa akan kada yay zargi cikin fushi, ya bincika dai sannan. Sunayen ALLAH ya shiga ambata har ya samu nutsuwar ajiye tunanin a ransa gefe, sai kawai ya faɗa wanka. Lokacin da yake fitowa yaji fitar motar data kawo Dada, sai kawai ya ƙarasa kimtsawa da yin shirin fita sallar magrib ya fito.

     Lulu da ke kwance a falo ta wani ɗan zabura alamar tsorata da ganinsa. Murmushi ya sakar mata da lumshe idanu yana kaiwa zaune kusa da ƙafafunta. “Matsoraciya relax ba aljani bane ni ne?”.

   “Taya zan yarda da haka bayan kace sai gobe ne zaka dawo, kuma ina wajen banga sanda ka shigo ba”.

  Murmushin ya sake sakar mata, a nutsensa da deep voice ɗin nan tasa dake fita da sanyin damuwar abinda yaji na tattaunawar ta da Dada duk da yana ƙoƙarin dannewa ya ce, “Mun gama abinda ya kaimu ne shine kawai muka yanke dawowa gida. Sanda na shigo kuma kina ɗaki ne da baƙuwa. Namayi zaton har zan kammala wanka nazo mu gaisa duk da bansan wacece ba”.

     Kaɗan ta sauke numfashi da ɗage kafaɗunta. “Dada ce kuma ta wuce. Tazo ne akan maganar zuwa duba Grandpa da aka wuce da shi London jiya”.

   “Ya salam jikin nasa ne dai?”.

  “Wlhy kuwa, fiye ma da yanda ake tsammani, dan a shekaran jiya doctors suka gano wai anyi poising ɗinsa ne da gubar da bata baiyana kanta sai tai kwanaki a jikin mutum”.

        “What! Sai kace wani a film?”.

    Lulu ta ce, “Hummm a tunaninka a Film kawai ake waɗan nan abubuwan? To a Nigeria ma a zahiri anayin fiye da haka. Kasan Grandpa ya Bama siyasar nan amanna matuƙa, shiyyasa muke tunanin ko'a cikinsu ne musamman daya kasance a hasashenmu a zuwa Legos ɗin nan da yay abun ya faru. Yanzu dai haka jami'an tsaro sun duƙufa bincike kan al'amarin ma”.

   Matuƙa Smart ya girgiza. Dan baiyi zato ko tsammanin wai da gaske irin wannan abubuwan da ake gani a Film na faruwa a zahirin rayuwar mutanen ƙasarsa ba. Kiran salla ta sashi miƙewa yana faɗin, “Ina ƴan hutun naki? Naji gidan shiru”. Bedroom ɗin da suke ta nuna masa. “Suna ciki fa, tunda muka dawo saloon suka kwanta wai sun gaji”. Kallonta ya tsayayi kamar zai yi magana sai kuma yay shiru dan shi dai bai san da wani fitarsu saloon ba. Zuciyarsa ta lallashesa akan a tari gaba. Yanzu zantukan ta da Dada ya kamata ya maidama hankali. Kafaɗa ya ɗan ɗage hannayensa duka a aljihu, ya ce, “Okay bari naje salla na dawo. A ɗan samamin wani abu mai ruwa-ruwa haka yunwa nake ji”.

   Harararsa tai da faɗin, “Kafa dawo zaka fara takurama mutane da mulkinka ko”.

   “Ni na isa. Karki damu cikin su Maryam wani yayi ki huta abinki. Ki dai tashi kiyi salla. Bara naje sai na dawo”. Daga haka ya fice kafin ma tace wani abu..........✍️

No comments