Abban Sojoji Takun Karshe

 [3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*

Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1







قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*



Zagayeta su kayi gaba ɗayansu,su jahad na ambatar sunanta,fawan ne ya ɗauko masu ruwa a fridge ya dawo ya miƙa ma uncle ɗinsu,kar6a yayi tare da buɗe murfin ya ɗebo ruwan hannunshi nata kerma ya watsa mata shi a fuskarta,nan take ta farka tana faman yin atishawa,Alhamdulillah suka shiga faɗi suna kallonta,yunkurawa tayi ta tashi daga zaune tana bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya kafin ta mayar da idanunta akan Su hosana da jahad da suka zuba mata ido,

   Muryarta na rawa tace"jaj..jahad hos...sana...ku ne?ko dae idona ne ke nuna mun ba dai dai ba?

  Ba ƙaramin farin ciki ne ya lullu6esu ba sehrish ta dawo cikin hayyacinta ta gane su,atare suka faɗa jikinta suka rungume juna suna kuka,

  Murmushi kawai Abusufyan ke saki bashi kaɗae ba ma fuskar kowannansu na ɗauke da murmushi,musamman Abbansu junaid farin ciki kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha,haka hajiya azeemarsu har cewa take yi"yanzu nan waɗannan ƴan ukun duka namu ne?ƴa'ƴan mu ne?Allah abun godiya,yau dole in yi nafilar dare don miƙa godiyata ga Allah S.W.A daya nuna mun ƴa'ƴan abusufyan ɗinmu da ranmu kuma da lafiyarmu,Ashe dae da rabon yara suga danginsu,bayin Allah sun sha wahalar rayuwa,amma bakomai har yanzu lokaci bai ƙure mana ba,zamu nuna maku soyayyar da baku samu ba arayuwarku,Zamu baku duk wani jin daɗi na duniya da kuka rasa,zamu gatanta ku,sai mun cika ku da farin cikin da zaisa ku manta duk wani ƙunci da kuka ta6a fuskanta arayuwarku,waɗanda kuma sukayi silar jefa rayuwarku cikin hatsari tabbas sai sun ɗanɗani kuɗarsu sai sunji dama ba'a halicce su cikin duniyar nan ba,


Abbansu junaid ya kar6e da cewa"Ae daga rana irin ta yau su fara ƙirgen kwanakin mutuwarsu,saboda ƙarshen su yazo,sun tabka babban kuskuren ta6a jinin SALAHUDDEEEN HUSSEIN!Wallahi thumma tallahi ɗaya daga cikinsu bazai sha ba!' ranshi amatuƙar 6ace yayi maganar,

   Abbas yace"Abba ina ganin yakamata yaran nan suje su kwanta dare yayi sosai,suna buƙatar hutu,in yaso koma menene gobe zamu ida tattauna akai,'

   Jinjina kai Abbansu yayi tare da mayar da idanunshi kansu sehrish dake manne da juna suna kuka,

   Gyaran murya ya ɗan yi masu,atare suka ɗago suna kallonshi da idanunsu dake zubar da hawaye,

  "Kuyi kuka yara bazan hanaku ba,dole kuyi kuka domin kuwa an cuci rayuwarku,an zalunce ku,an ƙuntata maku,an rabaku da mahaifinku na asali kuma an rabaku da danginku,duk akan laifin da baku kuka aikata ba,saboda son zuciya irin na mutanan nan su rasa akan wa zasu ɗauki fansar su sae akan waɗannan bayin Allahn....  'Shiru ya ɗanyi yana faman sauke ajiyar zuciya,

  abusufyan na zuƙunne akusa dasu ya sunnar da kanshi ƙasa,hakanan ya dinga jin kunyar yaran yana ji aranshi tamkar duk shi ne silar jefa su cikin halin da suka shiga,

  Su fawan kuwa dasu twins irfan jabeer da sauransu duk suna atsaye kowannansu jikinshi asanyaye kamar waɗanda aka zare ma lakka,lokaci guda sukaji tsananin Son yaran ya kamasu,

  duk wannan abun dake faruwa gwaggon katsina,na zaune saman kujera tana ta faman matsar kwalla,har lokacin bata daina tsinar dangin Sayyadi ba,haris sai faman lallashinta yake yi tana buge mashi hannu tana faɗin"ka rabu dani Harisu!abun da ciwo wlh,Zuciyata tafarfasa takeyi,ƴa'ƴan abusufyan ɗina aka wulaƙanta kamar dabbobi?wlh bazan ta6a daina tsinewa Sayyadi ba,munafuki algungumi ɗan wuta,Ya Allah ka tsine ma sayyadi da duk zuriyarshi harda unguwar zomar da ta yanke mashi cibinshi, Ya Allah kayi mana maganinsu,Sayyadi ko ɗan iska,uwarshi ta haifa mana masifa....munafuki lokacin da yake zuwa wurin abu har ƙasa yake zukunnawa ya gaishe Ni,da wata guntuwar jallabiyarshi ta gado,ƙafafun nan nashi kaman shebur sanye cikin silifar ɗan ta shegiya...Muna yi mashi kallon Biri yana yi mana kallon ayaba.....'

  sai faman sambatu takeyi abun ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,can kuma tace"Allah sarki abu,nasan yanzu ta gane cewa Allah ɗaya ne,yarinyar nan akwai taurin kai kamar kwallon goruba ga kafiya,kunnuwan nan nata kamar na Zoman daji falo falo dasu,ba irin jan kunnan da banyi mata ba,amma taƙi ji na,Ae ga irinta nan yanzu majnun ya koya mata hankali yanzu tana can Saman bola tana sambatu baiwar Allah,wama yasan uwa duniyar data shiga.......'

  "Sehrish ku tashi ku tafi ɗaki ku kwanta,gobe zamu ƙarasa magana daku," Abbansu ne yayi maganar,

  Miƙewa sukayi tsaye tare da yi masu sallama sannan suka wuce ɗakin nata,gaba ɗaya sehrish ta ɗan shiga ruɗu,batasan meya faru ba,amma bakomai yafi ɗaure mata kai ba face ganinsu hosana da jahad,taya akai suka San inda take har suka zo wurinta?abun kamar a mafarki take ganinshi,

  Atare suka shiga cikin ɗakin,anan fa suka tsaya suna kallon juna fuskar kowaccen su ɗauke da tsantsar farin ciki mara misaltuwa,

"Sehrish Ashe da rabon zamu sake ganinki a duniyar nan"?jahad ce tayi maganar yayin da hawaye ke sauka a fuskarta,

ta ɗaura da cewa "Sehrish munyi kewarki sosai,munyi kukan rashinki atare damu,munsha wahala sosai,abubuwa marasa daɗi sun faru damu bayan rabuwar mu dake,amma duk wani hali da muka shiga hakan baisa mun manta dake ba sehrish kullum kina aranmu,koda yaushe muna cikin zullumin a wane hali kike?kina raye kuwa?kina jin daɗin rayuwarki?kina da ƙoshin lpy ko akasin hakan ....'

  jin wannan maganar ta Jahad yasa ta fashe da kuka mai cin rai,janyota jahad tayi jikinta sosai ta rungumeta,itama hosana ta matsa tare da sanya hannayenta ta bayansu,suka haɗe su ukun,sun jima a wannan yanayin kafin daga bisani suka haye saman gadon su duka ukun suka zagaye junansu suna fuskantar juna a zaune

  Sai lokacin sehrish ta buɗe bakinta tare da cewa"inaso ku faɗamun meya faru na daina samun wayar tsohuwa,sannan kuma inason jin yadda akai har ku ka san inda nake,nayi mamakin yadda na manta daku gaba ɗaya acikin rayuwata,nasan ban kyauta maku ba,Amma kuyi haƙuri ku yafe mun........'

  ta ƙarasa maganar tare da kai hannunta ta shafo gefen fuskar hosana tana kallonta da idanunta waɗanda suka canza launi sosai,sai lokacin ta gane cewa ashe sune yaran da Marshal Omar ke ruƙo a wurinshi,rashin sani yafi dare duhu,har waya suka yi dasu jahad amma bata ganesu ba,saboda bata acikin hayyacinta,

  Jahad ce ta kwashe dukkan abunda ya faru tun daga kan Jefa wayar tsohuwa da hosana tayi acikin Masai da kuma mutuwar tsohuwa,da kuma zamansu acikin cell,haɗuwarsu da Marshal Omar,zamansu a wurin gwaggon katsina da kuma rayuwarsu agidan Aunty babba,komai ta sanar mata,

Sosai sehrish tayi kuka tamkar ranta zai fita,har zazza6i saida ya lullu6eta nan take,bakomai yafi girgiza ta ba face mutuwar tsohuwa,da kuma zamansu hosana a gidan Aunty babba,abun ba ƙaramin ta6a zuciyarta yayi ba,wani irin ciwon kai ne ya rufar mata mai raɗaɗin gaske,rarrafawa tayi ta koma gefe guda saman bed mattress ɗin ta kwanta tare da janyo pillow ta rufe fuskarta dashi,Wurinta su jahad suka koma tare da kwantawa kusa da ita,kowanannsu na acikin yanayi,tabbas sunga rayuwa......


Daƙyar bacci 6arawo ya sace su,amma fa dukkansu babu wanda babu zazza6i ajikinshi,


Kowa fa ya manta da cikinshi saboda lamarin su hosana,a gidan babu wanda yaci abincin daren shi,saboda ƙunci da takaicin yadda rayuwar ƴa'ƴan uncle ɗinsu ta kasance,


Lokacin da Azmee ta turo ƙopar ɗakin nasu samun su tayi kwance suna bacci kowacce fuskarta ɗauke da hawaye,bacci sukeyi amma hawayen basu daina zuba daga idanunsu ba,ba ƙaramin tausayinsu taji ba,ta jima tana kallonsu kafin ta rufe masu ƙopar ta koma bedroom ɗinta,


Kwance yake asaman katafaren gadonshi,tunda ya dawo bedroom ɗinshi,ya shiga toilet yayi wanka,ya dawo ya kwanta yana tunanin duniya,juyi kawai yake yi asaman gadon bacci yaƙi ɗaukarshi,har lokacin zuciyarshi bata sauka ba,abun ya dame shi sosae,ya tsani zalunci arayuwarshi,ya tsani mugun mutun mai hali irin na dabbobi,tabbas idan har sayyadi ya bari ya shigo hannunshi sai ya ɗanɗani kuɗarshi,daga baya kuma ya dawo yana tunanin wai yanzu ƴar yarinyar nan da take yi mashi aiki,ashe ƴar uwarshi ce?jinin shi?ɗiyar Uncle ɗinsu?hakan na nufin cewa ita ƙanwarshi ce...?

"Wonders shall neva end'ya furta hakan tare da lumshe idanunshi,nan take kuma ya tuna da hoton da Uncle abusufyan ya basu lokacin da suke a U.s,hakan na nufin cewa Hoton yaran ne ya basu lokacin da suke ƙanana,zan tambayi uncle hoton wacece nai selecting acikinsu,as I promised then  zan taimaketa da kuɗi ta sayi duk abunda takeso bazan fasa ba...... '


Wasu dae sunyi bacci a wannan daren yayin da wasu kuma Baccin ya ƙaurace ma idanunsu,a tsaye Abusufyan ya kwana idanunshi sun ƙanƙance saboda raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi,bawan Allah,wlh abunda ciwo,taya ma zai iya bacci?yasha kuka dae,ga wani irin Matsanancin ciwon kai da yake fama dashi,yawo yake ta yi acikin dakin yama rasa tunanin da zai yi yayin da tafin hannunshi na dama ke dafe da saitin zuciyarshi,wani irin bugawa takeyi mashi mara daɗi,


Yana cikin tsayuwar ne har aka kira sallar asuba bai ankare ba,sae da Yaji ana mashi knocking ƙopa,muryarshi ashaƙe yace"Wanene,"

"Ni ne"muryar Abban su junaid ce,

Hakan yasa shi cewa"ƙopar abuɗe take yaya ka shigo daga ciki,".  

Tura ƙopar Abba yayi ya shiga ciki yana ganin Abusufyan atsaye yace"dama saida rai na ya bani cewar baka yi bacci ba abusufyan,'

  Yayi maganar tare da ƙarasawa ya dafa kafaɗarshi yana kallon fuskarshi da hawaye suka wanke ta sharkaf,

Cikin sanyin murya yace"duk wanda yace maka kayi haƙuri tamkar ya cuce kane!amma ya zakayi abusufyan?dole haƙurin nan shi zakayi,nasan abun da ciwo,raɗaɗinshi na iya zarce na ƙunar wuta,abusufyan bazan ce kayi laifi ba,amma kasan cewa dole ne dama kaga badai dai ba!kayi aure batare da sanin mahaifiyarka ba,baka sanar mata ba balle tasanya albarka acikin auren naku,kunyi komai a6oye kai da gwaggon katsina,sai gashi yau Allah ya bayyana mana komai,nasan kai kanka kayi mamakin ganin Ƴa'ƴanka su duka ukun a ƙarƙashin kulawar gidan mu,kaɗan daga cikin Ikon Allah kenan!kwata kwata yaran basu san suna da dangi ba,garari kawai sukeyi a wulaƙance cikin gari,mu ma haka bamu son cewa akwai wasu ƴa'ƴa waɗanda suka kasance jinin mu ne su ba,babu wanda yasan haka,amma cikin ikon Allah da yake shi hakimun ne,sai gashi silar aikatau ɗaya ta faɗo hannunmu,yayin da silar ciwon ɗaya daga cikinsu da aka kai asibiti Allah ya ƙaddara haɗuwarsu da Omar yayin da shi kuma yaje wurin ɗan uwanshi Dr haris,lamarin ubangiji girma gare shi!gaba ɗaya Allah ya haɗa yaran a wurinmu ta hanyar da bamu ta6a tsammani ba,kamar yadda kai da gwaggon katsina baku yi tsammanin abunda kuka aikata asirrance zai tonu ba,tunda baku sanar mana ba sae gashi Allah ya sanar damu,su kansu yaran basu yi tsammanin zasu haɗu da dangin ubansu na asali ba,su dama basu da masaniya akan wanine ubansu......'

Dakatawa abba yayi da maganar yana kallon abusufyan dake ta faman shessheƙar kuka muryarshi na kerma ya shiga cewa"Ya Allah ka yafe mun kuskuren dana aikata na auren abu batare da sanin mahaifiyata ba da kuma dangina ba......tun farko nine silar jefa rayuwarsu Cikin halin da suka tsinci kansu,da ace ban 6oye ma kowa ba,duk da ammi bazata barni in auri abu ba amma ina da tabbacin cewar Abbanmu salahuddeen zai aura mun ita inna nasanar mashi,iyakaci dae Ammi zata zangwameta ne daga baya kuma nasan zata fara sonta,wlh ni sam tunanin hakan baizo mani ba a wannan lokacin,idona ya makance,kuma ba laifin gwaggon katsina bane,Son da takeyi mun ne yasa ta aikata hakan don ta faranta mun ganin halin da na shiga a lokacin jin cewar Mommynmu ba zata bari in auri abu ba,gashi na mutu akan sonta

kaicona.......'fashewa yayi da wani sabon kukan,dana sani kenan irin wadda ba'ason yinta,abun yayi ta maka ciwo azuciyarka,shiyasa kullum muke cewa Allah ya tsare mu daga aikata aikin danasani,saboda bai da daɗi,ɗaci gare shi,

    Ba ƙaramin tausayi yaba Abba ba,tuni shima hawaye suka fara sauka akan fuskarshi,janyo abusufyan yayi ajikinshi sosai ya rungume shi yana lallashinshi,

  A ƙarshe yace"Abusufyan ka manta da duk wani abu daya faru dazun,yanzu lokacin farin cikine,yakamata ka nuna godiyarka ga Allah subhanahu wata ala daya nuna maka wannan ranar da ya haɗaka da triplet ɗinka dukkansu da ransu kuma da lafiyarsu!wlh abusufyan dana ga yaran nan amatsayin ƴa'ƴanka kaɗan ya hana in buga tsalle saboda murna.....'yayi maganar yayin da suka raba jikinsu dana juna,

  tallabo fuskarshi abba yayi cike da zolaya yace"Kasan me?

  Abusufyan ya girgiza mashi kai alamar a'a,

  Abba yace"nifa ɗazu dana ga ka firgita da ganin yarinyar nan nayi tunanin cewa ko ka ƙyasa ne,har ina cewa shikenan lokacin barin gwaurantakar abusufyan yayi aduniya ashe ashe uban ne gaba ɗaya........'

  Ya ƙarasa maganar yana dariya,murmushi abusufyan ya ɗanyi,

  Abba ya kuma cewa"Wai yanzu nan duk aikinka ne waɗannan abusufyan?ashe dae ƙanin nawa bana wasa bane...'

  fashewa da dariya abusufyan yayi tare da sunnar da kanshi ƙasa,

  Hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Abba ba,dama so yake ya sanyashi farin ciki don ya gusar mashi da damuwar da yake ciki,

  dafa kaɗarshi abba ya kuma yi tare da cewa"duk haihuwata ya'ya goma sha takwas akan su jahan ne kawai na samu ƴan biyu,amma kai da yake mai sa'a ne,na ku ba irin namu bane sai gashi ka haifa mana ƴan uku reras!ko Ya ammi zata ji in taga ƴa'ƴan mara jin maganar nan nata abusufyan....nasan zata ce shegen bisa zai aika ae,

  Wannan karan atare suka fashe da dariya,

Daga bisani Abusufyan yace"yaya hussein inaso naga yaran nan sosai,na damu dasu wlh....'

  Wani irin kallon rainin wayau Abba yayi mashi kafin yace"yau naga ikon Allah!ni kake fadama kana son ganin ƴa'ƴanka?Yaran nan fa naka ne halak malak,ae ni nama yi tunanin a wurinsu zaka kwana,saboda suna buƙatarka sosai atare dasu,yanzu basu da burin daya wuce suga mahaifinsu atare dasu,"

  Wani irin daɗi ne ya lullu6e abusufyan yace

  "Zan iya zuwa wurinsu yanzu"?

Abba yace"Ka bari mu dawo daga masallaci inyaso kai tsaye kawai sai ka wuce wurinsu,"

  Fuskar shi ɗauke da farin ciki yace"okey,bari naje nayi alwala,"

  Abba yace"muna jiranka a main palour in ka kammala,ka same mu acan,"

  Yana ƙarasa maganar tashi ya juya tare da nufar ƙopar ɗakin nashi ya fuce tare da tura masa ƙopar,

  Toilet abusufyan ya shiga batare da 6ata lokaci ba,ya ɗauro alwalar,

Lokacin daya fito babban falon anan ya same su kowannansu ka kalla zakaga alamun damuwa a fuskokinsu,wasu ma da alama basuyi bacci ba,musamman Marshal Omar babu alamar yayi bacci adaren jiya,hatta Sgr ma akwai alamun rashin isasshen bacci atattare dashi,taya zaiyi bacci sayyadi na yawo acikin gari,shi fa in ya ƙullaci mutun irin haka har sai yaga bayanshi sannan yake samun kwanciyar hankali,su twins kuwa fuskokinsu sunyi jawur su da fawan,kowa dae da damuwa aranshi,


Bayan sun kammala haɗuwa suka wuce masallaci atare,


Tura ƙopar ɗakin nasu azmee tayi don ta tashe su sallar asuba,ba ƙaramin mamaki tayi ba,ganinsu ajere suna sallah,kowaccensu na sanye da dogon hijabi a jikinta hijjaban sehrish ne hosana da jahad suka sanya,abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,dama indae suna tare su ukun,musamman in akace maka akwai jahad atare dasu tofa basa wasa da ibada,duk da itama Sehrish ɗin ba daga baya ba,amma jahad ɗin itace kan gaba,saboda ita ba'a tashinta sallar asuba da zarar anfara kiran sallar asuba duk nisan baccin da tayi zata farka ne da kanta,abun sama rai ne da kuma sabo da yi,da kuma imanin mutun,


*Murmushi kawai azmee ke saki tana kallonsu gwanin ban sha'awa,ƴa'ƴan abusufyan,jikokin Ammi da salahuddeeen,ƴa'ƴan ƙanin Abban sojoji Abusufyan,ƙanne ga Marshal Da Sgr duk su kaɗae,abun farin ciki abun murna!yanzu su sun zama abunso wlh,yayyansu gaba ɗaya sojoji har goma sha takwas,ko sauro ne yayi gigin Cixon fatar jikinsu sae yaji saukar alburushin bindiga asaman goshin shi* 🤣


Azmee na tsaye tana kallonsu taji alamun motsin mutun a bayanta,jin an dafa ta yasa tayi firgit ta ɗan juya,Hajiya azeema ce jikinta sanye da hijabi blue,hannunta ruƙe da carbi,fuskar nan ɗauke da murmushi tace"Nazo ganin ƴa'ƴanmu ne,idan ba damuwa ki bani hanya in wuce ciki,"

  Murmushi azmee tayi tare da matsa mata hanya ta wuce ciki,sai da ta shiga ciki sannan azmee tabi bayanta tana cewa"sallah nazo in tashe su suyi,shi ne na same su ashe har sun tashi ma,abun ba ƙaramin burgeni yayi ba dana gansu ajere su ukun suna sallah,'

  Murmushi hajiya azeema tayi ayayin da take zama daga gefen gadon su tace"Albishirinki,"tayi maganar tana kallon azmee,

  Azmee tace"Goro,"

"Fari ko ja,"cike da zolaya tayi maganar,

  "Fari dae,shi ne ke tare da alkhairi,wannan launin jan alamace ta hatsari,"

Dariya hajiya azeema tayi kafin tace"Tab jiya anyi babu ke!Labari da ɗumi ɗuminsa!zazzafan gaske....'

  A ƙagare azmee tace"Meya faru"!

A lokacin su jahad sun sallame sallah,suna zaune saman dardumar suna sauraransu,

Nuna su hajiya azeema tayi tare da cewa"Ke wai ashe yaran nan ƴa'ƴan abusufyan ne!!!"

  Gaban azmee ne ya faɗi Rasss!saboda yadda maganar ta dirar mata kai tsaye acikin kunnuwanta,

  "Wai dagaske"?tayi tambayar cike da mamaki,

  Hajiya azeema tace"hmmmm ke dae bari,wani iko sai ubangiji,dagaske fa nake,babu wanda baiyi mamakin wannan abun al'ajabin ba,yara dae ƴa'ƴan ƙaninmu ne sufyan,'

  Juyawa azmee tayi tana kallonsu sehrish da sukayi zuru suna kallonsu musamman Sehrish da batasan kan zancen ba,saboda bata a hayyacinta lokacin da akayi maganar,amma lokacin da jahad ke bada labarin rayuwarsu taji komai a kunnanta kuma daga nan ne Sihirin jikinta ya lalace saboda tunaninta daya rinjayi kwalwarta harta tariyo dukkan abunda ya faru arayuwarsu ga kuma addu'ar da Sgr keta yi mata acikin kunne,


Cike da mamaki azmee tace"taya akai hakan ya faru?dama abusufyan ya ta6a aure ne kenan?

   Ataƙaice azeema ta bata labarin yadda abusufyan ya auri abu batare da saninsu ba,har suka samu ƙaruwar ƴan uku,'

  Wani irin farin cikine ya lullu6e azmee saboda tsabar farin ciki bakinta yaƙi rufuwa,

   "Jahad!dagaske ne abunda kunne na ke jiyo mun"?sehrish ce tayi maganar tana kallon jahad da tsananin mamaki,

  Murmushi jahad tayi ta jinjina mata kai alamar eh,ta ƙara da cewar"jiya duk baki a hayyacinki,abun farin cikin nan ya faru,Mun jima muna wahalar rayuwa ashe muna da dangi mai girma irin wannan bamu sani ba,cikin ikon Allah kuma sai gashi Allah ya haɗa mu dasu ta hanyar da bamuyi tsammani ba,ina tunanin addu'ar da muka jima munayi ne Allah ya kar6a mana,Ashe oumman mu sai da ta fara auren uncle ɗin su abusufyan sannan ta auri wannan fasiƙin mutumin sayyadi,da cikinmu ta shiga gidan shi........'

  Aruɗe sehrish tace"taya hakan zai yiwu?

  Hajiya azeema ce ta katse ta da cewar tabbas zancenta gaskiya ne sehrish!ku ƴa'ƴan ƙaninmu ne Abusufyan,sai da ya fara auren mahaifiyarku sannan Mugun mutumin nan daya ƙuntata rayuwarku ya aureta.......'gaba ɗaya hajiya azeema ta kwashe labarin rayuwar mahaifiyarsu agidan gwaggon katsina da kuma haɗuwarsu da abusufyan har izuwa rabuwar aurensu ta auri sayyadi ta sanar ma Sehrish,'

  tun kan takai ƙarshen labarin nata,Sehrish tayi sujjada,tana shessheƙar kuka,saboda tsabar farin ciki,Ashe ita ɗiyar uncle ɗinsu ce abusufyan?hakan na nufin su Babban yaya ƴan uwanta ne na jini!haba no wonder ae shaƙuwar dake tsakaninta da junaid tayi yawa,kai kana ganin abun zakasan cewar akwai alaƙa ta jini ajikinsu,ta damu da mutanen gidan sosai,ashe danginta ne su ɗin,

  Jikin azmee ba ƙaramin sanyi yayi ba bayan hajiya azeema ta sanar mata irin zaluncin da sayyadi yayi ma su Sehrish,har idanunta sai da suka cicciko da kwalla saboda tausayinsu da taji,ta jima tana tsinar sayyadi acikin zuciyarta,

Muryarta tamkar zatayi kuka tace"dama ina ta son mu samu lokaci Sehrish ta bani tarihinta wllh,ashe haka suka sha ukubar rayuwa bayin Allah,kai koma wanene wannan mugun mutumin ya cika babban azzalumi,saboda tsabar zalunci ya raba yara da mahaifinsu ya kuma ƙuntata rayuwarsu,duniya ina zaki damu.......'azmee na cikin magana,Abusufyan ya turo ƙopar ɗakin bakinshi ɗauke da sallama,gaba ɗaya hankalin su sehrish ya dawo kanshi,shi ma kuma yana ɗago idanunshi suka sauka akan ƴan ukun nashi,kwata kwata ma bai lura da hajiya azeema da kuma azmee dake a ɗakin ba,Su sehrish kawai yake kallo cike da so da ƙauna,ko kyaftawa baiyi,kamar ya haɗiye su haka yake ji,kamar yadda yake jinsu haka suma suke jinsu,sae ƙare mashi kallo suke yi kamar su watsa a guje su rungumo shi haka suka dinga ji,ta wani 6angaren kuwa abun ba ƙaramin yawo yake yi masu akai ba,Wai nan mahaifinsu ne halak malak,ubansu wanda yayi silar zuwansu duniwa,dama suna da uba da dangi a duniya?tambayoyi iri iri suke shiga yiwa kansu,

  Ganin sun zubama juna ido tsakanin Abusufyan da kuma su sehrish dake zaune saman darduma suna kallon shi,hakan yasa hajiya azeema tayi masu gyaran murya hankalinsu ya dawo kanta sannan tace"Zaman me kuke yi ne?baku ga mahaifin naku bane?ba zaku zo ku rungume shi ba,kuji ɗumin mahaifinku a jikinku?

  jin wannan maganar ta hajiya azeema yasa su miƙewa gaba dayansu jiki na rawa suka ƙarasa wurin shi,

Tunkan su ƙaraso ya buɗe masu hannayenshi alamar su shiga ciki,haɗasu yayi dukansu ya rungume su sosai ajikinshi kamar zai maidasu cikin cikinshi,hawaye ne suka shiga gangarowa a idanuwanshi da kuma idanuwansu sehrish,bai ta6a tunanin zaiga wannan ranar ba,yau gashi ga ƴa'ƴanshi sun dawo wurinshi,tabbas Allah ne ya kar6i addu'ar daya jima yana yi,atare suka ɗago idonsu cike tab da hawaye suka haɗa baki wurin cewa"Abba,"

Har cikin zuciyarshi yaji wani irin sanyi ya ratsa shi,muryarshi akasalance yace"Ku sake maimaitawa banji ba,"

"Abba,"suka maimaita mashi kamar yadda ya umarta,

"Wlh kunyarku nake ji!duk wani abu daya faru arayuwarku ni ne sila,Na cuci rayuwarku,Naji na tsani kaina ƴa'ƴana suna a wani hali na rayuwa amma nagaza taimakonsu,zan iya zuƙunnawa saman guiwaowina agabanku domin in nemi gafararku.....,'tunkan ya ƙara maganar gaba ɗaya ya tafi zai zuƙunna saman guiwowins,cikin sauri suka rurruƙe shi suna cewa"Abba dan Allah kada kayi mana haka bamu so,ka daina ɗaura laifin akanka,dama Allah ya riga da ya ƙaddara faruwar hakan,dan Allah kada ka zuƙunna agabanmu,mu fa ƴa'ƴanka ne,

Ganin dagaske kneel down zaiyi agabansu yasa suka riga shi zube wa saman guiwowinsu,tsayawa daga tsaye yayi yana kallonsu,Azmee da hajiya azeema duk suna kallon abunda ke faruwa,ba ƙaramin tausayi suka basu ba,

  "Abusufyan"! Hajiya azeema ce ta ambaci sunanshi,amsawa yayi yayin da ya mayar da idanunshi akanta,

  Anatse ta soma magana"yanzu ba lokacin baƙin ciki bane ko lokacin tuna baya,Lokacin farin ciki ne wannan,dariya yakamata in dinga gani a fuskar kowannanku ba hawaye ba,ko ba haka ba azmee?tayi tambayar tare da mayar da idanunta kan azmee,

Murmushi azmee tayi kafin tace"Wannan haka yake,Abusufyan ina tayaka Murna sosai,nayi farin ciki mara misaltuwa,naji daɗi da sehrish ta kasance ƴarka ce,ko ince suka kasance ƴa'ƴanka ne,lamarin ubangiji da girma yake,babu wanda ya ta6a tsammanin haka,naji ma ina ganin kamannin fuskarka a fuskar sehrish ashe ƴar kace.....'magana take hawayen farin ciki na gangarowa daga fuskarta,

   Murmushi kawai abusufyan ke saki,a lokacin harsu Sehrish sun miƙe tsaye suna tsaye akusa dashi,hosana ta rurruƙe hanunshi kamar wani zai kwace mata shi,

Hajiya azeema ce tace"Azmee yakamata mu basu wuri su gana da juna,don na lura da yadda Uban ƴan ukun nan ke zumuɗi akan ƴa'ƴanshi,"cike da zolaya ta ƙarasa maganar tare da miƙewa taja hannun azmee suka fuce suna dariya,

  Ajiyar zuciya ya sauke tare da mayar da idanunshi kansu jahad yace"kun samu bacci kuwa jiya?ya tambayesu ne saboda fuskokinsu daya gani duk a yamutse,musamman idanunsu sun ƙanƙance,

Haɗa baki sukayi wurin cewa"Eh,"

  Hosana tace"abba,dagaske kaine Abban mu ko?

  "Ga zahiri kin gani,"yayi maganar yana yi mata nuni da fuskarshi,murmushi suka saki gaba ɗayansu,

  Sun jima atsaye tare dashi suna magana jefi jefi saboda basu saba da juna ba,duk jin abun suke wani iri haka,kamar mafarki ne suke yi ba gaske ba,

   "Ku koma ku kwanta,kuyi bacci ku huta,idan har akwai inda keyi maku ciwo ku sanar mun zansa aduba ku yanzun nan....'wannan maganar tashi ba ƙaramin sanyaya masu jiki tayi ba,

  "Abba,lafiyarmu qalau,babu abunda ke damun mu,'suka faɗi hakan atare,

  Gyaɗa kanshi yayi tare da kama hanya zai juya da nufi yabar ɗakin nasu,

 Cikin sauri jahad ta ruƙo hannunshi tare da cewa"Abba,dan Alla kada ka tafi kabarmu,muna buƙatarka a kusa damu,muna so mu kasance tare da mahaifinmu,'

  Sehrish ta kar6e da cewa"hakane Abba,ka dawo mu zauna atare dakai,muna buƙatar kyakkyawar kulawa daga wurinka,'

  tana kai ƙarshen maganar hosana tace"Abba pls,ko don saboda Ni,"

Wani irin murmushin farin ciki abusufyan ya saki yana kallonta,batare da 6ata lokaci ba,suka wuce saman gadon nasu,a tsakiya suka sanya abusufyan,yayin da suka kwanta gefe da gefenshi,sosai ya rungume hosana ajikinshi,duk in ya tuna labarin yada ta samu ta6in hankalinta nan take sai yaji idonshi sun ciko da kwalla,

 "Idan Allah ya kaimu gobe,da kaina zan gyara maku gashin kanku inyi maku kalaba guda biyu,kamar yadda na ta6ayi maku Lokacin da kuna yara,nasan ba zaku iya tunawa ba,'


Jikinsu ne yayi wani irin sanyi, wani irin yanayi suka shiga gaba ɗayansu,

  

  

 

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



_Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata  zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari sannan a kula wannan itace numbar wayata,Wasu suna ɗaukar numbar Wanda suka bani tallarsu kayansu suna kiransu a matsayin ni,bayan ni ga numbar dana bada nan itace numberta_


*Nagode sosai da addu'o'inku agare ni,da kuma uzurin da kukayimun,har zuwa wannan lokacin,Allah yabar zumunci a tsakaninmu daga nan har gidan aljanna💃*



*nace ba Masu satar littafi suna fitarwa ta bayan fage,mai yasa baku ƙarasa masu labarin ba?kuma kenan saida kuka jira ni?ae nayi tunanin cewa zaku ƙarasa masu labarin ne ashe dai sai anjira Boss*😂🤣😅



Bismillah



Kai tsaye sautin ringing ɗin wayar ya daki dodon kunnan Aunty babba dake baje saman gadonsu tana Bacci,a lokacin ko yatsanta bata jin xata iya motsawa saboda baccin dake a idanunta,yatsina fuska tayi alamar an takura mata,

   Ishaq dake tsaye agaban mirror yana gyara jikinshi ya ɗan gyara murya tare da cewa"Madam ki daure ki tashi ki ɗaga kiran nan!da alama kira ne mai muhimmanci tun ɗazu wayar ke ta ringing,"

  Uban tsoki Aunty babba ta buga tare da yunƙurawa daƙyar ta tashi daga zaune,jikinta na sanye da sleeping dress,riga da wando purple colour,

  Fuskar nan tayi suntum kamar wadda aka nausa,hannu takai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman bedside drawer,duba screen ɗin wayar tayi ganin sunan Hayaam ya bayyana yasa ta ƙara tamke fuska kamar ta shanu,ɗaga kiran tayi tare da kara wayar a kunnanta,rai a6ace tace"Meyasa kika kirani fitsararra!ko kin kira ne don ki ƙarasa yimun rashin kunyar taki don ubanki,"

  on the other hand hayam tace"haba aunty laila,ni harna manta da abunda ya faru atsakanin mu.....'tunkan hayaam ta ƙarasa maganar Aunty babba ta katse mata hanzarinta da cewa"Idan kin manta ae ni ban manta ba,Ki faɗamun uban miyasa kika kira ni,idan ba haka ba ni zan kashe wayar,

  Zuba mata ido Ishaq yayi yana kallonta aransa yace"Zagi kamar ƴar maguzawa,ko kunyata bata ji,sae faman ɗura ashar take yi,ni dae Allah ya haɗani da Guyaba,'

     cike da damuwa hayaam ta sassauta muryarta,tare da cewa"Aunty laila,na shiga uku,ko ince mun shiga uku,Akwai gagarumar matsala,Gaba daya duk wani plan ɗinmu ya tashi aiki,'

  Tunda Aunty babba taji hakan,gabanta ya faɗi rasss,ƙasa ƙasa da murya tayi tace"Hayaam meya faru?wata irin matsala kike magana akai?

  "Aunty laila,Ashe yarinyar nan mai aikin gidansu,ɗiyar uncle ɗinsu ce Abusufyan!!!!!" tamkar saukar aradu haka aunty babba taji maganar Hayaam aikuwa a matuƙar gigice ta miƙe tsaye tana cewa

  "kutumar uba!inji ubanwa!yaushe Abusufyan ya ta6a aure,Wlh ƙaryane koma wani ɗan ƙaniyar ne ya faɗi maki hakan babban maƙaryaci ne....'

  Gaba daya hankalin ishaq ya dawo kanta,maganar dayaji tana fadi ta tsaya mashi aranshi,

   "Wani abusufyan din kuke magana akai,"

  Firgit Aunty babba tayi tare da ware ido tana kallonshi sam ta manta da cewar yana acikin ɗakin,

  Hankali a matuƙar tashe ta miƙe tsaye da nufin ta fuce daga cikin ɗakin,Saboda tsabar ruɗu ta nufi hanyar shiga toilet,

  gyaran murya ishaq yayi mata tare da cewa"kada fa ki shiga toilet da waya a kunnanki,'

  A zabure ta juya ta kuma nufi wardrobe da alama ruɗu yasa ta manta hanyar fita daga ɗakin,zuba mata ido yayi yana mai mamakin irin kiɗimar da tayi,to ko lafiya?ya tambayi kansa,

   Bata ankara ba sae da goshinta ya bugi jikin wardrobe din kayan nasu,sannan ta gane inda ta dosa,Rai a6ace ta kama hanya ta fuce daga dakin,saukowa downstairs tayi ta miƙi hanyar wannan tsohon store ɗin data ta6a garƙame su hosana aciki,anan corridor ɗin ta tsaya tana sauraran Hayaam,

  "Wlh Aunty laila da gaske ne,Ni shaidace,Naji komai lokacin da Uncle ɗin nasu yake korama junaid bayani,bama haka ba Aunty azmee da kanta ta gasgata mun hakan,Babban abunda yafi rikitar dani Yaran fa triplet ne ashe,kuma dukkansu Mata ne kyawawan gaske,kamannin su sak iri ɗaya,Kuma kina kallonsu zaki gane cewa ƴa'ƴanshi ne......'

  Hannu ɗaya Aunty babba tasa ta dafe tsakiyar kanta,yayin da dayan hannun ke ruƙe da wayarta data kara a kunnanta,

  "Hayaam bazan ta6a yarda da zancenki ba,Taya hakan ma zata faru!mutumin da bai ta6a yin aure ba,Shi za'ace yana da ƴa'ƴa har ƴan uku!Cikin shege kenan ya ta6a yima wata harya same su!Ni ban yarda da kalamanki ba,Hayaam kinsan cewa babu kyau tsoratar da musulmi,Idan wasa kike mun ki daina!!!!!

6acin raine yasa hayaam ta kashe wayar 

  Fashewa da kuka tayi saboda ƙululun baƙin cikin daya tokare mata maƙoshinta,ga zuciyarta dake ta faman tafarfasa,Gaba daya bata jin daɗin jikinta,

  Zubama wayar ido Aunty babba tayi tana kallonta,

  Tsoki taja tana jinjina kai tace"dama saida raina ya bani cewa ƙarya take yi mun,tayi mun hakan ne saboda ta tsoratar dani don in saukko,Shashasha kawai,

    "Mommy kin farka kenan"

Muryar hafsat ce ta katse mata zancen zucin nata,

  Juyowa tayi tana kallonta,atsaye take fuskar nan ɗauke da murmushi jikinta na sanye da riga da wando na jeans,ta ɗaure sumar kanta da ribbom,yayin da hannunta ke ruƙe da Cup mai ɗauke da Tea mai zafi sai faman tiriri yake yi,

  Tunda Aunty babba taga hafsat na murmushi tasan cewa akwai matsala,hakanan dae ba zakaga fuskar hafsat da murmushi ba tunda farar safiya,

  ƙaƙalo murmushin yaƙe Aunty babba tayi tare da cewa"Lafiya naga kina murmushi"?

  "Lafiya lou mommy,kawai wani abun farin ciki ne ya faru,nasan cewa muddin kema kika ji,zaki yi farin ciki sosai,'

  Murya asanyaye aunty babba tace"Faɗamun daughter har na ƙosa naji wannan abun farin cikin?halan an ƙara maku albashi ne?ko matsayi aka ƙara maki wurin aiki"?

  Dariya hafsat tayi tana girgiza kai tace"Mommy baki canka dai dai ba,wannan albishir ɗin da nakeso inyi maki yafi ƙarfin duk waɗannan abubuwan da kika lissafo,kar6i tea ɗin nan ki fara korawa kafin na faɗa maki,"

  Hannunta na kerma ta kar6i kofin da hafsat take miƙa mata,a hankali takai cup din  bakinta ta kur6i Tea ɗin,kusan sau uku tana kur6arsa,kafin ta ɗan jinkirta bayan ta janye kofin daga bakinta tace"daughter dan Allah ki faɗamun wannan wani abun farin ciki ne!wlh duk na ƙosa naji,'

  "Zan faɗa maki mommy amma mu shiga daga cikin palour mu zauna,'

  "Ba inda zanje,idan zaki faɗamun ki faɗamun kawai,Sae ja mun rai kikeyi," tayi maganar tana faman tamke fuska,

  Hafsat tace"bada jimawa ba,Na kira Aunty azeema,don in gaishe da ita,Anan take sanar dani cewa ƴa'ƴan uncle abusufyan Sun bayyana...!

  Tunkan ta ƙarasa maganar a gigice Aunty babba ta saki kofin dake hannunta,Ya tarwatse ƙasa,Ruwan tean dake ciki ya fallatsar masu a ƙafa,

  ja da baya hafsat ta ɗanyi tana kallonta tace"haba mommy,so kike ki ƙonamin ƙafa ta,daga faɗin abun farin ciki?

  Rai amatuƙar 6ace tace"Ki 6ace mun da gani sakarya kawai,Maƙaryatan banza,bazan ta6a yadda da kalamanku ba,duk bakinku ɗaya da Hayaam,'

Ta faɗi hakan tare da kama hanya fuuuuu kamar zata tashi sama,ranta duk a jagule,bin bayanta hafsat tayi da kallo harta haye upstairs,ta6e baki tayi tare da watsa hannayenta tace"I don't care, Ni dae farin ciki nakeyi,Daddy ma nake jira in tambayeshi yaushe zamu je gidan saboda a qagare nake dana ga ƴa'ƴan uncle ɗinmu Abusufyan,tunkan na gansu har naji ina sonsu sosai,in ma na tashi tafiya hada tsaraba zan tafin masu dashi,'

  Cike da farin ciki hafsat take maganar,zuƙunnawa tayi tana tattare kofin da aunty babba ta fasa,


Lokacin da Aunty babba ta ƙarasa bedroom ɗin nasu,har ta ɗaga ƙafarta zata zura acikin ɗakin taji muryar ishaq yana cewa"Alhamdulillah!Alhamdulillah!Alhamdulillah!Abba nayi farin ciki sosai,Meyasa tun jiya ba'a sanar dani ba,ae da tunda sanyin safiya zanyi maku dirarr mikiya,Amma ina taya uncle murnar ganin ƴa'ƴanshi,kuma ina tayamu murnar samuwar ƴan uku acikin zuri'ar mu,gaskiya bazan ma iya jurewa ba,Zan shirya nazo ne kawai,saboda na qosa naga ƴan ukun mu bayin Allah....   

    Abba yace"wani abun ma sai kayi tozali da yaran,kyawawan ƴan mata dasu,Yadda kasan photo copy ɗin abusufyan haka suke,kamanninsu sak iri ɗaya da nashi,'

  Murmushi Ishaq yayi tamkar yana agabanshi yace"Abba kafin na ƙaraso,dan Allah a isar musu da saƙon gaisuwata,Ace yayansu General ishaq yana gaishe su sosai da sosai,kuma saboda suma zaiyi zuwa na musamman,'

  "Insha Allah zan sanar masu yanzun nan,Allah ya kawoka lfy,"

  "Ameen Abbana,"

Sun jima suna waya kafin sukayi sallama ishaq ya ajiye wayar,

  tashin hankalin da ba'a sama shi date!!!!!!!

  Magana dae ta tabbata da gaske ne zancen da hayaam da hafsat suka faɗa mata,Tabɗijancan,

  Dakyar ta iya shiga cikin ɗakin,lokaci guda ta rasa kuzarin jikinta kamar wadda tayi Zazza6i na sati ɗaya,

  Jin takun tafiyarta yasa ishaq juyawa yana kallonta fuskarshi a washe har ya kammala shiryawa cikin haɗaɗɗiyar shadda,

  Ganin yana ƙoƙarin buɗe baki yayi mata magana yasa tayi saurin katse shi da cewa"Naji abunda ya faru,Hafsat ta sanar dani komai,ina tayaku murna,'ko amsar shi bata tsaya ji ba,ta faɗa cikin toilet,

  Tana juyo muryarshi daga cikin bedroom ɗin yana cewa"Ni yanzu zan wuce Abuja ne,inyaso kun biyo ni daga baya ko zuwa gobe ko jibi haka,duk dae yanda kuka yanke shawara keda hafsat,

  daga cikin toilet tace"Allah ya sauke ka lpy,in anje agaishe mana da mutanen gidan,"

   "zasuji insha Allah," ya amsa mata tare da kama hanyar fita daga ɗakin.


❤🤍❤


Acan 6angaren kuwa har lokacin suna a falon kan junaid da Uncle abusufyan ya gama fahimtar dashi game da Su Hosana da jahad,

jiki asanyaye yace"Amma meyasa su ba suyi rayuwa atare damu ba?meyasa Abba?uncle why?cike da tuhuma yake maganar yana kallonsu,yayin da fuskarshi ke ɗauke da damuwa,

abban su ne yace"Junaid,mu kanmu bamu san dasu ba,da ace munsan da zamansu da bamu bari hakan ya faru ba,ƙaddara ce kawai ta riga fata,"

  Shiru junaid ya ɗanyi yana ƙare ma su Jahad kallo,yaso ace tun fil azal tare da yaran ya taso,da ba ƙaramin kulawa zasu samu a wurin ƴan uwansu ba,Allah sarki rayuwa kenan,Rashin sani yafi dare duhu,su kansu su Sehrish sae dama dama suke da sun san cewa suna da wannan family ɗin daba abunda zai hana su nemi danginsu,Tabbas an cuci rayuwarsu ƙiri ƙiri an rabasu da Ubansu kuma an hanasu danginsu,wata shari'ar dae sae a lahira,


"Nasan yanzu kowa yana jin yunwa,saboda halin da muka shiga jiya babu wanda ya samu damar cin abinci acikin mu,Yakamata yanzu komai ya wuce,Lokacin farin ciki ne,Za'a shirya gagarumar walima saboda ƴan ukun mu,munaso su manta da duk wani abu da ya faru a rayuwarsu kuma su ƙaddara cewa tamkar yau ne suka faɗo duniya,ko ba haka ba"? Ya yi maganar yana kallon matasan gidan dake atsaye,Kowannansu fuskarshi asake,su fawan ne suka haɗa baki wurin cewa"Wannan haka yake Abba,In sha Allah zamu nuna masu soyayyar ƴan uwantaka,har sai sun manta da dukkan wani ƙunci da suka fuskanta na rayuwarsu,' murmushi kawai Abusufyan ke saki don ba ƙaramin daɗi yaji ba,

Marshal Omar yace "Sannan kuma muna ƙara baku haƙuri game da halin da kuka tsinci kanku,duk da ba laifin mu bane,amma mun ɗaura ma kanmu laifin,Muna neman afwarku,Hosana Sehrish and Jahad,forgive us pls,'

  gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi,lokaci guda kuma sukaji wata irin soyayyar ƴan uwansu ta kamasu,

Jahad ce tayi ƙoƙarin cewa"duk wani abu daya faru damu dama can rubutaccen ne!Allah ya riga da ya ƙaddara faruwan hakan,mun gode ma Allah da muka cinye wannan jarabawar,da juriya kuma da haƙuri,yanzu gashi gaba ɗayanmu muna farin cikin wannan rana da Allah ya haɗamu da danginmu,Babban abun farin cikin ma da ya kasance Uncle abusufyan shine mahaifinmu ba waccen fasiƙin mutumin ba.......'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya zo mata,Janyota Abusufyan yayi tare da rungumeta ajikinshi,yana ɗan bubbuga bayanta,

  "Ya Omar," hosana ce ta ambaci sunan shi,tana faman kumshe dariya abakinta,gaba ɗaya suka mayar da hankalinsu akanta,nuna shi tayi da yatsanta sannan ta nuna kanta,kafin ta haɗe yatsun wuri guda ta ƙullasu,Alamar ita dashi sun zama  ƴan uwan juna, ƙayataccen murmushi Marshal ya saki yana kallonta,

Duk wannan abun dake wakana akan idon Sgr dake atsaye,ya goya hannayenshi asaman wide chest ɗinsa,Har lokacin bai sauko ba,hankalinsa fa bazai kwanta ba har sai yayi tozali da YA SAYYADI,


Suna cikin magana muryar azmee ta katse su da cewa"Abba an kammala shirya breakfast ɗin,yakamata ku hallara a dining ɗin," tana magana idonta na akan su jahad fuskar nan ɗauke da murmushi,

   Batare da 6ata lokaci ba,gaba ɗayansu suka hallara asaman zungureran dining table ɗin wanda ke shake cike tab maƙil da kayan makwalashe naci dana sha,mutun goma shabiyu yake ɗauka,akwai kuma wanda Abban su junaid yasa aka ƙara cikin wanda aka shirya walimar jiya dasu,Ansanya shi a gefen nasu mai mazaunin mutun shida,Aunty azmee ta jera wasu kayan kalacin asaman shi,anan Abusufyan ya zauna tare da su sehrish jahad da hosana,


Tun daga kan yadda kowa ke zuba abinci acikinshi zai tabbatar maka da cewar ba ƙaramar yunwa suke ji ba,ko azmee basu jiya tayi serving ɗinsu ba suka shiga zuba abincin da kansu,Sgr ne kawai tayi serving ɗinsa sae kuma Abbansu,amma sauran ba wanda ya tsaya jira,wurin yayi tsit bakajin hayaniyar komai,sai sautin Cokulla,kwas kwas kwakwasss,


ɗagowa Marshal omar yayi karaf idonshi yaci karo dana hosana,ta zuba mashi ido ko kyaftawa batayi,kasancewar table ɗinsu na kusa dana juna,tazarar kadan ce,

  Da cokalin hannunshi yayi mata nuni da plate din gabanta,alamar ta mayar da hankalinta kan abunda take ci,

  murmushi tayi tare da kai hannu ta dauki lemu tana korawa,

  Junaid kuwa duk ya rasa samun natsuwa sam ya gaza cin abincin dake a gabanshi sae faman juya cokalin yake yi acikin plate,duk in ya tuna abunda yayi ma Jahad acikin mota amatsayin Sehrish sai yaji gabanshi ya faɗi rass,fargabar shi kada jahad tayi tunanin ko ɗan iska ne shi,tunda ba sanin shi tayi ba,kar kuma tace zata sanar ma wani abunda yayi mata,tunawa yayi da lokacin daya tsoma harshenshi acikin bakinta ya ƙanƙameta yana kissing lips ɗinta,ba iya nan ba ya tsaya har hannunshi saida ya zura ackin hijabinta

  Hankali tashe junaid ya miƙe yana ƙoƙarin barin dining ɗin,hankalin kowa ya koma kanshi,

  Har suna haɗa baki wurin tambayar shi ina zashi,

  fuskarshi ɗauke da damuwa yace"Abba,bana jin yunwa,dama munyi breakfast tare da Mommy,zanje wurinta yanzu" Abbansu yake ma magana amma hankalinshi na akan Jahad dake shan farfesun da azmee ta zuba mata a plate,da alama ba ƙaramin daɗi farfesun yayi mata ba,duba da yadda ta mayar da hankali akanshi,

  "Okey,zaka iya tafiya," ya bashi amsa,cikin sauri junaid ya kama hanyar zuwa bedroom ɗin Abbansu don acan ta sauka,yana tafiya yana waiwayen su jahad aranshi yana cewa"wayyo Allah na,bansan me zai biyo baya ba,nasan cewa dole ta sanar ma Uncle abunda nayi mata,idan ta faɗa mashi shi kuma zai faɗa ma Abban mu ne,Abban mu kuma zai faɗa ma Babban yayanmu ne,shi kuma zaice wuyana ya isa yanka tunda har na iya Sumbatar mace daga nan zaiyi tunanin turani aikin Soja abunda banso,shikenan tawa ta ƙare'

  ranta ne ya bata cewar ana kallonta,hakan yasa ta tsagaita daga shan farfesun da takeyi,ta ɗan ɗago idanunta,kai tsaye suka sauka akan junaid dake can nesa dasu yana kallonsu,

Mamaki ne ya kamata ganin yadda ya ƙura mata ido yana kallonta,aranta tace"bansan meyasa yake kallona ba,tsorana kar ace baisan ganina ne,'

  "Allah yasa halinta irin na Sehrish ne,idan takasance mai sauƙin kai irin na rishi ɗina nasan cewa zata rufa mun asiri,amma anya zatayi sauƙin kai?Nasan me zanyi daga yanzu zan dinga ɗaure mata fuska,in nuna kamar na tsane ta,nasan hakan ne kawai zaisa taji tsorona taƙi faɗa masu abunda ya faru atsakaninmu!good idea",

  Yana kai ƙarshen zancen zucin nashi ya watsa mata harara tare da murguɗa mata baki,ya juya ya nufi bedroom ɗin abbansu,

   Jiki asanyaye jahad ta ɗauke idanunta daga kallon bayanshi da take yi,lokaci guda taji komai ya fita ranta ba don komai ba sai don kallon da taga junaid yayi mata,maganarta ta tabbata,Junaid baison ganinta,tunda gashi ya harare ta kuma hada murguɗa mata baki,

  Muryar daddynsu ce ta katse ta da cewa"Jahad,meya faru ne?naga kin daina shan farfesun ina fata lafiya?

  firgit ta ɗanyi tare da wurga eye balls ɗinta akanshi tace"Am ok daddy,'

  jinjina kansa yayi kafin yace"Ku saki jikinku,kuci abinci sosai,kada kuji komai,nasan baku saba ba,don na lura akwai rashin sabo atattare daku,amma a hankali zaku saba da ƴan uwanku,'

  hosana tace"Abba ae ni,nama saba da kowa,baka ga yadda nake ta cika cikina da abinci ba,jahad ce ke jin kunya,ni bana jin kunyar kowa,'

  Dariya sukayi gaba ɗayansu,Sehrish na cikin sakin dariyar nan,Karaf idanunta suka haɗu dana Sgr,ɗagowar shi kenan yayi arba da ita,gabanta ne taji ya faɗi rass saboda fuskarshi a murtuke take ba annuri,nan take dariyar da takeyi ta koma ciki,ganin ta zuba mashi ido,yasa shi jefa mata harara,a hanzarce ta kawar da idanunta daga kallon fuskarshi da take yi,jikinta kuma yayi sanyi,ta shiga tambayar kanta dalilin hararar da taga big bro yayi mata,kodai baya farin ciki ne da kasancewarta JININ SA!?tabbas hakan zai iya faruwa,Wataƙil kodan ya saba ganinta a matsayin ƴar aikinsa,baiwarsa,ƙasƙantacciya shiyasa yanzu Yake nuna 6acin ranshi don yana ganinta tamkar a matsayi ɗaya suke dashi,Ƴa'ƴan Wa da ƙani,da alama hakan baiyi masa ba,

"Idan har dagaske ne abunda nake hasashe,insha Allah zan tattara na bar masu gidan,saboda bana son 6acin ranshi,zan iya yin komai don farin cikin shi," ta ƙarasa zancen zucin nata tare da sake ɗagowa a hankali don ta saci kallonshi,adai dai lokacin shima ya ƙara ɗagowa da kyawawan idanuwanshi kai tsaye suka shiga cikin nata,nan take taji gabanta ya kuma faɗuwa rass,kasa janye idanuwanshi yayi daga kallonta da yake yi,a yayin da yake jujjuya spoon ɗin dake hannunsa acikin plate ɗin abincin gabansa,har Yanzu bai daina mamakin kasantuwarta ƴar uwarshi ba,ta jininsa,tamkar a mafarki haka yake ganin abun,ganin ta zuba mashi ido batare da ta janyesu ba yasa shi ɗaure fuskarshi yasha murrr,saboda kada ma yarinya taga fuska har tayi tunanin raina sa don tasamu matsayi,

   "U will still remain who u are,wadda take aiki a ƙarƙashina,Matsayin dana baki kenan,"ya fada a ransa

  Murmushi Abusufyan yayi tare da cewa"bazasu kara wahala ba,bazan ta6a bari hakan ya faru ba,tunda dae har yaran nan suka bayyana a matsayin ƴa'ƴana,In sha Allah bazan ƙara bari suyi aikin wahala ba,ko cokali bazan ƙara bari ɗaya daga cikinsu ta ɗauko ba acikin gidan nan,rayuwar hutu kawai nake so suyi rayuwar ƴanci," ya ƙarasa zancen zucin nashi a yayin da yake bin kowaccen su da kallo cike da so da ƙaunar ƴa'ƴan nashi,'

  Janye idanunshi yayi daga kan nata,kafin ya miƙa hannu tare da ɗaukar Glass cup mai ɗauke da abun sha me sanyi ya kai shi saitin mouth dinsa yana sipping ɗinshi anatse,yayin da sanyin lemun ke ratsa throat ɗinsa,a hankali ya lumshe idanunsa tare da ɗan ware su kaɗan,again suka ƙara sauka akan na sehrish a karo na uku kenan,agaggauce tayi hanzarin janye idanunta daga kan fuskarshi ta mayar dasu akan plate ɗin abincin dake a gabanta,



Hannu Sgr ya sanya tare da yago tissue ya goge bakinsa,kafin ya miƙe tare da juyawa ya nufi upstairs,Miƙewa Marshal yayi da alama shima ya kammala breakfast Ɗin nasa,shima upstairs ya nufa,


Fitowar Hajiya azeema keda wuya daga cikin bedroon ɗinta,ta jiyo muryar gwaggon katsina tana ta faman sambatu tana cewa"Tsiyarta kenan mutun yazo gidan ƴan gayu,Ni bazan iya rayuwar turawan nan ba,taya za akai ma mutun salalar biredi tare da tea rabin kofi kamar wata ƴar iska ace in sha"?

  Tafiya take tana sambatu  zaninta a hannu sai ɗan undi ajikinta,kanta kuwa ta kifa wannan ɗaurin ɗan kwalin nata mai kama da helmert,

  har zata gifta hajiya azeema tayi gyaran murya tare da ambaton sunanta"Goggo," fuska a yamutse ta juyo tana kallonta,dawowa tayi daga gefenta suna fuskantar juna tace"Yawwa azeema,wai nikam inaso in tambayeki,'

Natsuwa hajiya azeema tayi tare da cewa"ina sauraronki gwaggo,"

  "Jiya nayi wani mafarki,ƴa'ƴan abusufyan sun bayyana,wasu ƴan uku kyawawan gaske,da nayi tunanin koda gaske ne abun ya faru amma daga baya na gane ba gaskiya bane,in ba haka ba,yaushe abusufyan ya ta6a yin aure"? Tayi tambayar tana kallon hajiya azeema,wadda ta saki baki tana kallon gwaggon,

  Ganin azeema tayi sototo tana kallonta yasa tayi tunanin cewa ko abunda ta faɗa ya bata mata rai ne,

  "Nasan dole kiyi mamaki kema,Mafarkin fa kamar dagaske,ɗaya daga cikinsu har tana sharara mana labarin ƙarya waisu ƴa'ƴan wata zainabu ne,kuma ma acikin labarin hada wata hajiya Ameena,in banda shaiɗan ina abusufyan ina ƴa'ƴa"?

  Ƙiris ya rage Azeema ta fashe da dariya agaban gwaggon katsina,ganin yadda ta haƙiƙance tana kora mata bayani,kuma babu alamun wasa a fuskarta,

Ƙunshe dariyar bakinta tayi tare da basar da ita tace"Gwaggo Anya kina shan maganinki kuwa?ina Dr harris yake?gaskiya inason ganinshi,'

  Tsoki gwaggon katsina taja tare da cewa"Harrisun daya zama ɗan iska,"

Waro ido waje azeema tayi tace"gwaggo harris ne ɗan iska"?

  ta6e baki tayi tare da cewa"Zan masa ƙarya ne?ba ɗan cikina bane"?nasha wahalar yima yarona tarbiya amma waccen sauden.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya ciyota,zanin hannunta takai saitin idonta tana ƙoƙarin goge hawayenta,

  Zuru harris yayi wanda fitowarshi kenan kuma atare da saude suka fito,jin maganar gwaggone ma yasa yayi hanzarin cire hannunshi daga cikin na sauden,

  Hajiya azeema tace"gwaggo faɗamun me harris ɗin ya akaita,?

  Hankali tashe Saude tace"ya harris pls kada ka bari gwaggo ta faɗa mata abunda muka aikata,kasan gwaggo yadda take ɗaukaka abu,inta tashi faɗi saita ƙara ma miya gishiri,'

  Dr harris yace"just don't worry ur self,insha Allah bazata faɗa mata ba,"

Faɗin hakan keda wuya gwaggon Katsina tace"Azeema abun da ciwo,yanzu yunwa nake ji,shiyasa ma kika ga nafito ina sambatu,Wurin waccen matar zani,wlh ba azmee ba Allah yasa ramadan ce ita yau saina zazzaga mata rashin mutunci!Ni zata raina ma hankali tunda safe,takawo mun tea rabin kofi da salalar biredi wai in fara da wannan,don ta raina mun hankali,nayi mata kama da kusu ne?

  Rai a6ace tayi maganar,aikuwa atare haris da saude suka fashe da dariya,a hanzarce ta juyo sakamakon jin sautin dariyar tasu,nan take ta tsuke fuska ganin shi tare da saude,

  Murmushi Hajiya azeema tayi tare da cewa"haba gwaggo baki fahimce ta bane,cewa fa tayi ki fara da wannan tana nufin kafin ki tashi fitowa zuwa yin breakfast ɗin,yanzu haka yana can an shirya mana mu kawai ake jira muje muci namu kalacin,"

  Hajiya azeema ta ƙarasa maganar tare da ruƙo zanin hannun gwaggon tace"Bari na taimaka maki ki ɗaura shi,"

  Girgiza kai tayi tare da cewa"Barmin shi a hannuna,nafison inji iska na shiga ta ko'ina,"murmushi hajiya azeema tayi kafin tace"hakan ma yayi gwaggo,ae under skirt din ma bamai sharashara bane,yana da kauri,amma duk da haka dae ki ɗaura zanin yadda zaki fito da kyau tunda ga rigarshi kin sanya ajikinki,Kuma kinga Abusufyan na nan,Ga kuma ƴa'ƴansa,bazasu so suga gwaggonsu a haka ba,"

  wani irin ƙayataccen murmushi gwaggon katsina tasaki tare da cewa"Kenan dagaske ne Mafarkin da nayi jiya"?

  Jinjina kai Azeema tayi tace"Ae suna nan,duk abunda ya faru jiya dagaske ne,ba mafarki kikayi ba,agabanki akayi komai kin dai shafa'a ne,'

  Jin haka yasa tayi saurin mayar da zanin ajikinta tana ɗaure shi tana cewa"Allah sarki ƴa'ƴan abusufyan ɗina,bayin Allah,sunsha wahala a hannun wannan fasiƙin mutumin baƙin shaiɗani,Allah mutumin nan ƙaho ne kawai bai fito masa aka ba,amma ina tantama anya ba Irin shaiɗan bane"? 

   "gwaggo kidaina maganarsa ma,Ni wlh ko zancen shi ma bana so anayi,Na tsani mutumin nan kamar yadda natsani mutuwa ta,"acewar hajiya azeema,tayi maganar ne a yayin da take kama hanyar Zuwa Dining area ɗin nasu,bin bayanta Gwaggon tayi tana cewa"Ae ko sai dai ki toshe kunnanki,don zancen sayyadi ya zama dole,in har ba'a kawo min kansa ba,bazan daina faɗan sunan shi ba,'

  Murmushi kawai hajiya azeema tayi,atare suka ƙarasa dining area din,

   Gaggaisawa suka fara yi da junansu,su jahad na ganin saude suka tashi atare suka nufe ta,dama Jiya basu samu damar gaisawa da ita ba,saboda yanayin da suka shiga gaba ɗayansu,haɗasu tayi ta rungume ajikinta,cike da farin ciki tace"Ina tayaku murna sosai,nayi farin ciki sosai,Ya harris ya sanar dani komai agame daku,ashe ku jininsu ne,'ta ƙarasa maganar ayayin da take raba jikinta daga nasu,kowannansu fuskarshi ɗauke da murmushi,Jahad tace"Aunty saude kinga ikon Allah ko?munsha wahala sosai,mu kanmu bamu ta6a tunanin cewa muna da dangi ba,amma sai gashi ƙaddara ta haɗamu da ya Omar,Ita kuma ƴar uwarmu Sehrish ƙaddarar aikine ya kawota gidan nan,Muna tare da ƴan uwanmu ba tare da mun sani ba,sae gashi rana ɗaya Allah ya bayyana mana komai,'

  Saude tace"Congratulations Once again,ina ƙara tayaku murna sosai da kuka fito daga tsatson wannan Family ɗin,abun alfahari ne wannan"kafin ta mayar da idanunta kan Hosana,Cike da zolaya taja kumatunta tare da cewa"Hosana Kinga yadda kika canza?kamar ba wannan Sha takwas sha taran ba,mai ɗan kai,kinyi kumatu kamar Balon balon,Ga haske gaskiya ya Omar ya Iya raino,"

  Fashewa da dariya hosana tayi tana faman sunnar dakai,

 "Kiyi ma sister ɗinku mana,Ita bazata taso mu gaisa ba"?tayi maganar tana kallon sehrish dake zaune,tana faman kallonsu ɗaya bayan ɗaya,

  Murmushi jahad tayi tare da juyawa tayi mata alamar ta taso da hannunta,

  Miƙewa sehrish tayi tare da nufar inda suke,koda ta ƙaraso saude ta sanya hannu tare da janyota ta rungumeta,kafin ta raba jikinta dana sehrish tace"Masha Allah,gaskiya ban ta6a ganin triplet,masu kama iri ɗaya sak kamar taku ba,ina taya ki murna sosai da Allah ya haɗaki da ƴan uwanki,da kuma mahaifinku,da kuma danginku,'

  Fuskar sehrish ɗauke da murmushi tace"Ngde sosai,"

 "Allah ya tsare mana ku,Ya Albarkaci rayuwarku ya kuma kare ku daga sharrin maƙiya,'

  Atare suka amsa mata da Ameen,bama su kadae ba,hadasu Abba dake sauraron maganganun nasu,


Kamar yadda Abba yayi alƙawarin shirya gagarumar walima na bayyanar ƴa'ƴan ƙaninsa Abusufyan,Da kanshi ya fidda date ɗin da za'a gabatar da ita,Kuma tun aranar ya fara kiran Ƴan uwa da abokanan arziƙi yana sanar dasu game da ƴa'ƴan abusufyan da suka bayyana,Babu wanda bai bari ba,kowa kira yake tun daga kan danginsu na Zaria,na damaturu dana sauran states ɗin da kuma waɗanda ke zaune Ƙasashen waje,kowa saidaya sanar mawa,Bayan Abbas ya koma gidane da safe Amani ke tambayarshi meya faru ne jiya ya hanasu zuwa gidansu,Anan ya kwashe duka abunda ya faru game da su Sehrish ya sanar mata,wani irin farin ciki ne ya cika ta,Ba don komai ba sai don sanin cewa plan ɗin Aunty babba ya gama Tarwatsewa,ae tunda taji cewar ƴan mata ne kuma sun kai shekara goma sha bakwai zuwa sha takwas kyawawan gaske,Nan fa ta kwashe da dariyar mugunta aranta tana cewa Naga yadda za'ae Aunty laila ta cimma burinta,Gida bai ƙoshi ba taya za'a ba na waje,Ae tuwona maina za'ayi,Haba ae xance ya ƙare,

   ita kanta Amani ta ƙosa ranar walimar tazo saboda suje gidan,saboda taji cewar Aranar Aunty babba da hafsat zasu zo Abuja,babban burinta taga tashin hankalin da aunty babba zata fuskanta inta gansu,


Ranar walimar kuma yayi dai dai da ranar da Ammi zata zo,tare da wasu daga cikin danginsu,haka zalika captain Najeeb da kuma Talal suma duk a ranar zasu dawo gida,ba don komai ba sai don su sanya ƴa'ƴan uncle ɗinsu abusufyan acikin idanunsu,Kowa ɗokin ganinsu yake yi kamar kamar me,musamman da sukaji irin rayuwar da yaran sukayi a wulaƙance sai suji wani irin tausayinsu da kuma ƙaunarsu ya shiga cikin ransu,kuma duk aranar MG Osman da kuma Captain Adam suma zasu dawo gida,wanda tun dawowarsu daga U.s suka tafi sada zumunci,Gaskiya wannan Babbar rana ce,Hakan yasa ma Zamuyi shiri na musamman ni da makaranta littafina don mu halarci gidan amatsayin gayyar soɗi tunda ba'a gayyace mu ba,Sa kaine kawai,


Cikin ƴan kwanakin nan wata irin rayuwar farin ciki suke gudanarwa tare da Daddynsu,kullum yana manne dasu,Da kanshi ya zauna yayi masu kitson kalaba guda bibbiyu akansu kamar yadda ya ta6a yi masu suna yara,koda yazo kan Sehrish,Cike da mamaki yace"Ya akai naga gashin kanki guntu?ko kinyi wani ciwo ne dayasa aka datse maki gashin,"girgixa kai tayi tare da cewa"a'a Laifi nayi ma Babba yaya shine ya yanke mun gashin da almakashi,"

 da buɗar bakin Abusufyan sai cewa yayi"Yayiwa kanshi ai," murmushi sehrish tayi duk da batasan me daddyn nasu yake nufi da hakan ba,duk a wannan kwanakin basu je school ba,Abusufyan da kanshi yace kada su damu shi da kanshi zai kaisu makarantar don karma a tuhume su,


A 6angaren Sir Commander haroon kuwa,tamkar munafuki haka ya koma acikin gidan,ba kowa ma ke sanin lokacin da yake shigowa gidan ba,da kuma lokacin da yake fita,Da alama dae akwai wani abu da yake shiryawa a 6oye,


*AMRISH*


Zaune take acikin class ɗin gaba daya ta shiga damuwar rashin ganin Sehrish kwana biyu ko layinta ta kira bata samu,hatta wayar junaid ta jaraba kira shima ba'a ɗagawa,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,tagumi tayi idonta cike tab da hawaye saboda damuwar da take ciki,taso ace sehrish na nan atlease zata ɗebe mata kewa,tana cikin wannan tunanin har malam ya shigo cikin class ɗin nasu bata sani ba,bayan ya kammala amsar gaisuwa daga wurin student din,kai tsaye ya ƙarasa seat ɗin da Amrish take,hannun shi yakai wanda ke ruƙe da maker ya ɗan bubbugi desk ɗinta,a firgice takai idanunta akanshi,Yunƙurawa tayi tare da miƙewa ganin Ya mu'allim,wanda tun ranar daya ba sehrish Ruwan addu'ar nan bai ƙara zuwa makarantar ba,duk da sun samu labarin cewar Ya tafi Umra ne,shiyasa aka musanya masu shi,

  Murmushi ya ɗan saki afuskarshi yana kallonta yace"tunanin me kike yi ne?har na shigo cikin class ɗin baki sani ba?

  Muryarta na rawa tace"Ayimun afwa ya mu'allim,Bana jin daɗi ne bansan ka shigo ba,

  Jinjina kanshi yayi tare da ɗan kai idanunshi kan Seat ɗin sehrish yace"Ina yarinyar nan take?ƴar family ɗin Salahuddeeen hussein naga kamar bata a class ɗin"?

  fuskarta ɗauke da damuwa tace"Batazo ba,yau kusan kwana huɗu kenan bata zo school ba,kuma nayi trying kiran layinta amma bana samu,har brother ɗinta na kira,shima layinsa ba'a samu,'

    Jin hakan yasa shi fargabar to kodai wani abu ya faru da yarinyar?Yaso yaji ya tayi da ruwan addu'ar daya bata,shin tasha ko bata sha ba?

  Jinjina kanshi yayi tare da juyawa yace"Allah yasa dae lafiya,in har batazo ba,zuwa sati mai zuwa zan je gidansu don na binciki dalilin rashin zuwan nata,'

  Jiki asanyaye Amrish ta koma ta zauna,saman seat ɗin nata,jikinta har ya fara kerma saboda tsoran kar ace wani abune ya faru da Sehrish,

  A ƙarshe dae ta yanke shawarar neman gidansu don taje ta ganta da kanta.



  *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃



*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI.  MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*



*LOCATION KANO*


08062073990

Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku



Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku


It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.

Snack

Awarah 

Farah

Zobo

Samosa

Cup cake etc 

Contact me 09063302182or 09012179727.


   



  

  

  

  



    

 

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*



"Allah ya kaimu lpy,Abba,'jahad da sehrish ne suka haɗa baki wurin bashi amsa,

Abusufyan yace"ba abba zaku dinga kirana ba,saboda ana kiran Yaya hossein da Abba,abun zai dinga ruɗa mutane ne arasa gane wani abban kuke nufi,amma ku dinga kirana Daddy,saboda a bambanta sunan,ina fata haka yayi maku?

"Eh daddy,"suka haɗa baki wurin bashi amsa,hakan ba ƙaramin daɗi yayi mashi ba,

  "Abba ita Oumman mu fa?dagaske ne ta haukace kuma tana saman bola tana hauka kamar yadda gwaggon katsina tace?kuma wanene majnun ɗin da naji gwaggo tace shi ya koya ma oummanmu hankali,'hosana ce tayi maganar,jahad tace"Ke fa matsalarki kenan baki da kan gado,tunda kika ji ance Majnun ae kinsan wa ake nufi,'Murmushi Abusufyan yayi yana sauraronsu,

  Sehrish tace"dan Allah ku daina magana,kuna takurama daddynmu bacci fa yake ji,baku ga idanunshi ba,

   Mayar da idanunshi yayi kan sehrish data aza kanta asaman kafaɗarshi,kafin ya mayar da idanunshi kan jahad itama tana manne dashi,ga hosana kuma data manne mashi asaman chest ɗinshi,kamar zata koma ciki,Allah kaɗai yasan irin farin cikin da yake ji acikin ranshi,daɗi kamar ya kashe shi,babban burinshi Ammi tazo taga yaran daga zarar ta amince dasu,bai da wata sauran damu,zancen sayyadi kuma ya gama sama ranshi lokacin mutuwarshi yazo,Saboda Case ɗinshi na hannun Zaki da damusa,tabbas sai ya ɗandani kuɗarsa,

  "Daddy,bakace komai ba!oumman mu fa muna so mu sake ganinta atare,"muryar hosana ce ta dawo dashi daga zurfin tunanin daya shiga,firgit ya danyi tare da sanya hannunshi ya shafa kanta yace"Kada ku damu,insha Allah komai yazo ƙarshe,Oumman ku duk inda take bi'iznillahi za'a ganota ne,inason komai ya lafa ne,daga ni har ku mu samu kwanciyar hankali sosai,sannan zan fara sanyawa a binciko mun makwabtan nan naku,ina da tabbacin cewa za'a samu wasu bayanai masu muhimmanci a wurinsu,"

  Ba ƙaramin daɗi suka ji ba,burinsu oummansu itama tashigo cikin wannan daular suci gaba da rayuwa acikin family ɗin Abbansu,

  "Daddy Allah ya taimaka,kuma ya baku sa'a akan duk wani yunƙuri da zakuyi na ganin kun kawo ƙarshen Mugun mutumin nan dashi da duk wani wanda yake da hannu akan cutar da zuri'armu,Allah ya tonu asirinsu,kuma Allah ya bayyanar da Oumman mu da ranta,Insha Allah daga rana irin ta yau zamu kasance kullum muna taya ku addu'a saboda asamu nasarar kama ya sayyadi,'murmushi abusufyan yayi yana sauraran maganar jahad,bayan ta kammala maganar Sehrish tace"insha Allah daddy zamu tayaku da addu'a kuma zamu jajirce wurin ganin mun bada gudummawa wurin binciken gano waɗanda ke da hannu akan cutar da zuri'armu,duk da mu mata ne muna da rauni,amma hakan bazai hanamu miƙewa tsaye ba wurin kawo ƙarshen Ya sayyadi da kuma ire irensa,shaiɗanun dake take masa baya,'

  tana kai ƙarshen maganarta hosana tace"Abba don Allah Idan kun gano ya sayyadi,inaso abani damar da zan fasa mashi tsakiyar goshin shi da bindiga,ko in harbi saitin zuciyarshi ta daina bugawa,"

  Dariya sosai abusufyan yayi yana sauraron kalaman hosana,

  "Hosana,ae idan ya mutu ta hanyar harsashin bindiga sai inga kamar yayi mutuwar sauƙi ne,nafi so ya rayu tamkar matacce,gashi da rai amma baida wani sauran amfani,shi kanshi sai ya dinga roƙon Allah ya ɗauki ranshi ya mutu ya huta,a tunanina ba,amma abunda nake gani yakamata mu shirya mashi mummunan ƙarshe,wacece acikinku zata bamu idea?yayi tambayar yana jiran amsoshinsu,

  Kowacce da irin shawarar da take bayarwa akan yadda za'a shiryama ya sayyadi mummunan ƙarshe,bad ending kenan,ba kamar hosana tafi kowa bada mummunar shawara,daga bisani kuma suka fara tsara ma kansu Happy life bayan an kashe ya sayyadi da tawagarsa,zasu fita ƙasashe daban daban yawon shaƙatawa tare da daddynsu,oummansu da kuma ƴan uwansu,araina nace hada mazajanku ko abun kamar zaifi bada citta harda kanunfari.......'


Bacci ne ya ɗaukesu atare manne da juna saman gadon,abun gwanin burgewa uba da ƴa'ƴanshi masu kama guda.


Har wuraren ƙarfe goma na safe basu farka ba,dama sun tara bacci sosai a idanunsu,har Abbansu junaid sai da ya leƙo ɗakin ya same su a baje suna sharar bacci murmushi ya saki,tare da curo wayar shi daga Aljihun rigar jikinshi,hoto ya ɗaukesu kusan guda uku,bayan ya kammala ya maida masu ƙopar ɗakin ya rufe,


Bayan ya fita daga sashen su  kitchen ya nufa a lokacin Azmee harta kusa kammala aikin breakfast,yayi mamakin ganinta ita kadae tana ta faman aiki,

  Tana ganinshi ta ajiye aikin da takeyi ta ƙaraso gaban shi tare da gaishe shi cikin girmamawa tace"barka da safiya Abba,antashi lpy?jiya sai muka ji abun farin ciki,Hajiya azeema ke sanar dani wai ashe su sehrish ƴa'ƴan Abusufyan ne,Wlh nayi farin ciki sosai,dama na jima ina ganin kamanninta da Shi,'.

Fukarshi asake yace"wllh Alhmdllh,mun Samu ƙaruwar ƴan uku,ni dai ince jiya banganki ba,ae naso ace agabanki akayi komai,kema kiji wannan abun al'ajabin da kuma tashin hankalin,labarin dae babu daɗin ji,Amma ta wani 6angaren kuma mun gode ma Allah da ya bayyana mana yaran nan amatsayin jinin mu,munyi farin ciki sosai,har Walima ma nake so asake shirya mana saboda yaran nan,'

Murmushi azmee tayi tare da cewa"Yaushe kenan?ko yau zamu fara shiryawa ne"?

  Girgiza kai Abba yayi alamar a'a sannan yace"Wannan walimar ta musammance,gagarumin shagali za'ayi,akwai buƙatar kwanciyar hankali kafin lokacin,amma zanyi shawara da Abusufyan,idan har muka tsara komai,zan sanar maki,don ku shirya tarbar baƙi,zamu sa aƙaro wadanda  zasu tayaki aiki.....'

  Tunkan yakai ƙarshen maganar azmee tace"a'a Abba,zan iya ni kaɗai,basai an ƙaro masu aiki ba'

  "Okey,ba damuwa naga kina ta wahala ke kadae,wai nikam ina yarinyar nan take ne?wata ƴar fara kanwarsu laila?naga kamar atare kuke aikin girki da ita ko ta koma gida ne"?

  Azmee tace"a'a bata koma ba,bata jin daɗin jikinta ne,shine nace mata ta huta kawai,in taji sauƙi taci gaba da tayani,saboda yarinyar akwai son aiki,'

Jinjina kai Abba yayi tare da cewa"Allah ya bata lpy,bari zanyi ma Kanal yousouf magana ya dubata...'

  Cikin sauri azmee tace"A'a....ae na bata magani dama ciwon ciki ne,insha Allah zata warke,'

   "Okey,' ya ambaci hakan tare da fucewa ya wuce cikin main palour dinsu,

  Zama yayi saman sofa yana murmushi,bakomai yake tunawa ba face yadda yaga abusufyan tare da ƴan ukunsa,aranshi yace"Allah sarki,rayuwa kenan komai mai wucewa ne in bawa yasa haƙuri aransa,junaid tun yana jinjiri rabonshi da mahaifiyarshi,sai gashi jiya rungume da ita yana bacci,ƴan ukun abusufyan tun suna ciki rabonsu da ubansu, tun kafin cikinsu ya bayyana ma,sun sha wahalar rayuwa amma sai gashi komai na rayuwarsu ya canza yanzu tamkar basu ta6a shiga wani ƙuncin rayuwa ba,sannu a hankali zasu manta da duk wata uƙuba da suka sha arayuwarsu,Yau dae gasu can rungume da mahaifinsu suna bacci,Allah sarki,

A ƙarshe kuma yace"Oh,ni kuma gani nan babu mai rungumata,abusufyan nacen rungume da ƴa'ƴan shi,junaid ma na can manne da mommynsu,gaskiya nayi kewarsu sosai......'


"Abba!" karaf kiran ya sauka a kunnanshi a ɗan firgice ya juya don yaga wanene,bakowa bane face Junaid yana tsaye hannunshi ruƙe da waist ɗinshi,har yanzu shaddar jiya ce ajikinshi,fuskar nan tashi cike da annuri sai faman zabga murmushi yake yi yadda kasan wanda akayi mashi albishir da gidan Aljana,

  Wani irin farin ciki ne ya lullu6e abbansu,yunkurawa yayi zai miƙe tunkan ya ƙarasa miƙewar junaid ya watsa da gudu kai tsaye ya faɗa jikinshi sosai ya rungume shi yana faɗin"I really miss u Abba,'

  "Nima junaid nayi kewarka sosai,jiya da tunaninka na kwana araina,'yayi maganar yana ɗan bubbuga bayanshi,

   raba jikinsu sukayi dana juna,ganin abbansu na kallon bayanshi yasa shi cewa"Abba mommy ko?

  murmushi yayi tare da cewa"Ashe ka gane,ta ina ne?ko ba tare kuka zo ba?

  ɗan ta6e baki junaid yayi nan fa hankalin abbansu ya tashi,.

Jiki asanyaye yace"Junaid bazata zo ba ko?Allah yasa dae ba Australlia ta koma ba,dama tunda na ganka kai kadae gabana ya fadi,don nasan halinta,'

  Fashewa da dariya junaid yayi ganin yadda Abban nasu ya tashi hankalinshi don baiga mommynsu ba,

  ɗaure fuskarshi yayi"oh ka ɗauki abun wasa ko?ba zaka faɗamun ina take ba,'

Yana cikin maganar ya jiyo takun takalminta,baisan lokacin daya janye junaid gefe ɗaya ba,Zuba mata ido yayi yana kallonta fuskarshi ɗauke da murmushi,tsayawa tayi tana ƙare mashi kallo,ba ƙaramin kyau tayi ba saboda kwalliyar da junaid yayi mata,da kanshi ya shafa mata janbaki ya gyara mata jagirar idonta,duk da haskenta sai da yashafa mata hoda,wai don Abbansu ya ganta da kyau,kuma shi da kanshi ya za6a mata rigar da zata sanya,jallabiya ce brown colour mai kyan gaske tayi rolling mayafi akanta,kamar wata balarabiya,tayi haske sosai kamar wata fatalwa,ga tsayi dake gareta kamar Sgr,

   Komawa junaid yayi saman sofa yana kallonsu,jira yake yaga mai zasu yi,sun wani ƙura ma juna ido,sae murmushi yake saki,


Cigaba da tafiya tayi harta ƙaraso kusa dashi suna fuskantar juna,

  Waro ido waje junaid yayi tare da cewa"Anshiga uku,Abba kaga yadda ka koma agaban mommy,wai dama ahaka kukayi aure Wayyo Allahna'

  maganar junaid tasa suka fashe da dariya gaba ɗayansu,shi abunda ya bashi mamaki tsawonta agaban abban nasu,sae yaga abban nasu ya koma mashi guntu,

  Sun jima suna sakar ma juna murmushi kafin daga bisani suka rungume juna sosai,kamar zasu zama daya,ba ƙaramin kewar juna sukayi ba,duk da akwanakin can baya yana kai mata ziyara Australlia,daga bayane ya daina zuwa saboda abubuwa da sukayi mashi yawa,

  Kasa rabuwa sukayi da junansu,junaid kuwa ya tasa su gaba yana kallonsu kamar wanda ya samu television,

  Adai dai lokacin twins suka shigo cikin falon,sakamakon Yunwa data ciwo su,karaf idanunsu suka sauka akan Mommynsu dake rungume da Abbansu,har suna haɗa baki wurin Cewa"Mommy!"

Cikin sauri suka raba jikinsu dana juna,wurga idanunta tayi akansu jahan da ayaan dake tsaye suna kallonta fuskar kowannansu ɗauke da farin ciki,

  Da gudun gaske suka ƙarasa inda take gaba ɗaya suka faɗa jikinta,haɗasu tayi duka ta rungume ajikinta,tuni taji hawaye sun cicciko a idanunta,tayi kewar ƴa'ƴanta sosai,muryoyinsu tamkar zasu yi kuka suka haɗa baki wurin cewa"we really missed u mom!ashe zamu sake ganinki acikin gidanmu,'suka ƙarasa maganar ayayin da suke raba jikinsu da nata,

  Hawaye tagani a idanunsu,cikin sauri ta sanya hannunta tana share masu hawayen muryarta na rawa saboda kukan daya zo mata daƙyar ta iya cewa"i missed u too my twins,nasan ban kyauta maku..... '

  Jahan ya katseta"Mommy abubuwa da yawa sun faru,wanda da ace kina tare  damu na tabbatar cewar bazasu faru ba,mun yi rashinki akusa damu mommy,munyi kewarki......'

  "Mommy..amma dae ba zaki sake komawa ba ko"?acewar ayaan

Jinjina mashi kai tayi alamar eh sannan tace"nadawo kenan bazan sake komawa ba,I will be with u,for the rest of my life....."

  Murmushi kawai Abbansu ke saki yana kallon uwa da ƴa'ƴanta,abubuwan farin ciki dae sai faruwa sukeyi acikin gidan,

  "Mommy,kinga junaid ko ya girma sosai,yayi kukan rashinki sosai lokacin da baki nan,amma yanzu nasan cewar zaki bashi kulawa,dan Allah mommy ki bashi kyakkyawar kulawa saboda yafi kowa buƙatarki,'ayaan ne yayi maganar yana kallon junaid dake zaune yana ta faman murmushi,

Itama kallon nashi tayi tare da cewa"Insha Allah ayaan,daga yanzu junaid zai canza gaba ɗaya,zan bashi kyakkyawar kulawa,bama shi kadae ba hada ku gaba dayanku,Amma banga fawan ba dasu Irfan,and kanal yousouf ko duk suna ciki ne"? 

  Jahan yace"basu tashi daga bacci ba,bari naje na kira maki fawan ɗin,'

Dakatar dashi tayi da cewa"A'a kada ka tashe shi daga bacci,nasan daga ya farka yaji labarin zuwa na zaizo ne,but where is Alexander?

  Atare suka haɗa baki wurin cewa"Mommy wanene Alexander kuma"?

  Dariya Abbansu yayi tare da cewa"tana nufin Babban yayanku,ae sunan data raɗa mashi kenan ko kun manta,'

  "Ae mun saba da kiranshi da babban yaya,mun manta da wannan sunan,shima yana a bedroom ɗinshi,duk bacci sukeyi saboda jiya bamu samu isasshen bacci ba,

  Abba ne yayi mata nuni da 3 seater din dake gefensu yace"bismillahi,ki zauna mana ko baki gaji da tsayuwa bane,ko da yake na tuna fa Soja ce matar tawa,'yayi maganar cikin zolaya,

  Murmushi kawai tayi tare da samun wuri ta zauna,shima abban nasu ya zauna daga gefenta,wuri su ayaan suka samu saman 2 seater suka zauna,

Cike da kulawa tace"Amma meya hanaku samun bacci da wuri ne?naji kunce baku samu isasshen bacci ba ko wani abu ya faru ne'?

   Ayaan yace"abun farin cikine ya faru jiya agidan nan mommy,nasan kin kwaso gajiyar tafiya,idan kika huta nasan cewa Abba zai baki labari anjima,"

  Da sauri junaid yace"meya faru ne?dan Allah ayaan ka faɗa mana yanzu kawai,Mommy fa tun jiya tazo ƙasar nan,muna acan tare da ita agidanta ma muka kwana,bata sanar ma kowa ba,sae abban mu,'

  Baki sake jahan yace"Wai dagaske?mommy abun ƴar haka ce,wato shine mu ba'a sanar mana da zuwan naki ba,junaid kawai kika sanar mawa,no wonder shiyasa jiya ban ganka ba,abun ya tsayamun araina,ba don abunda ya faru ba na bayyanar ƴa'ƴan uncle ɗinmu daba abunda zai hana mu nemeka a wannan lokacin,duk wannan abun shiya ɗauke mana hankalinmu....."tunkan ya ƙarasa maganar Junaid yace"Ƴa'ƴan uncle?wani uncle ɗin kenan"?aɗan rude yayi maganar,

  Miƙewa Ayaan yayi tare da ruƙo hannun junaid yabar wurin tare dashi,sai da suka samu wurin da bakowa sannan yace"kai kasan meya faru jiya"?

  Cike da zumuɗi junaid yace"taya za'ae in sani,ni da bana agida,don Allah ka sanar dani har naƙosa naji,'

Ayaan yace"hmmmmm,labari da ɗumi ɗuminsa,ko kasan cewa yarinyar nan Sehrish ɗiyar uncle ɗinmu ce Abusufyan?

  Gaban junaid ne ya faɗi rasss!saboda yadda maganar ta dira a kunnanshi,can kuma ya ɗan ɗaure fuskarshi yace"pls Ya ayaan dan Allah ka daina jamun rai,ni dae ka faɗimun gaskiyar abunda ya faru,'

  Ayaan yace"kai nifa bada wasa nake maka ba,na ta6a maka wasa irin wannan ne!Sehrish ɗiyar uncle ɗinmu ce abusufyan,

  Tur6une fuska junaid yayi tare da ɗan bubbuga ƙafarshi rai a6ace yace"yaushe uncle ya ta6a aure da har zai haifi ƴa'ƴa,kuma ma ƴar tashi ka rasa wadda zaka ce sae sehrish,kaji tsoran Allah ya Ayaan,babu kyau ƙarya,'

  Rai a6ace Ayaan ya dunguri goshin junaid tare da cewa"Shashasha,ana ƙoƙarin a fahimtar dakai amma kaƙi yadda,don ubanka kaje ɗakin nasu ka leƙa,zaka ga abun mamaki,'

  Turo baki junaid yayi tare da juyawa ya nufi hanyar xuwa ɗakin sehrish yana cewa"mai ƙarya dae ɗan wuta,'

  Murmushi ayaan yayi yana kallon bayanshi,yasan cewa muddin junaid yaga Sehrish da ƴan uwanta sai ya haukace masu,farat ɗaya bazaiyi tunanin ƴan uku bane,sae ranshi ya fara bashi cewar Aljanune,


aikuwa,junaid na ƙarasawa kopar dakin,a hankali ya sanya hannunshi tare da tura ƙopar dama a buɗe take,zura ƙafarshi ya fara yi kafin ya ƙarasa shiga bedroom  ɗin,koda baby junaid ya shiga ciki bai kai idanunshi kansu ba,sae da ya fara rufe ƙopar ɗakin sannan ya juyo fuskarshi a washe,Karaf idanunshi suka sauka akan abusufyan dake rungume da hosana suna bacci,gabanshi ne ya faɗi rass cike da mamaki yace"Kai uncle tare da rishi ɗina,kwance saman gado suna bacci,Anya kuwa bansamu matsalar idanu ba......'

  "Junaid!" Jin an ambaci sunanshi yasa shi juyawa a firgice yaci karo da Sehrish dake zaune gaban mirror tana shafa powder a fuskarta,sae faman sakar mashi murmushi take yi,waro ido waje junaid yayi a tsananin tsorace ya mayar da idanunshi kan hosana dake rungume da abusufyan ya kalleta ya sake juyowa ya kalli wadda ke zaune agaban mirror,

  Muryarshi na rawa yace"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Nashiga ukuna!wai meyake damuna ne!meyake shirin faruwa dani ne!kodai nafara gamo da aljanu ne......'bai kai ƙarshen maganar tashi ba yaji an buɗe ƙopar toilet ɗin dakin,da sauri ya wurga idanunshi wurin,

  Jahad ce ta fito,jikinta sanye da bathrobe,alamar wanka tayi,

  Tashin hankalin da ba'a sa mashi date,

  Hankali amatuƙar tashe junaid ya dinga kallonsu ɗaya bayan daya,idan ya kalli jahad sai ya kalli sehrish dake zaune gaban mirror,sae ya kuma juya ya kalli Hosana dake manne da uncle ɗinsu,

Tunkarar shi jahad tayi fuskarta ɗauke da murmushi,sehrish kuma na cewa"Junaid nice fa,baka gane ni ba,"

  Ae ina,a gigice junaid ya fasa wata uwar ƙara wadda tayi sanadiyar tashin Abusufyan da hosana daga dogon baccin daya ɗaukesu,

Da gudun gaske junaid ya damƙi handle din ƙopar ɗakin tamkar zai balle ta,buɗewa yayi tare da watsa wa da gudu har yanayin tuntube,tun kan ya fito daga corridor din dakin,Abbansu da mommynsu dasu twins suka nufo wurin saboda jin sautin razananniyar ƙarar da junaid ya saki,

  A sukwane ya faɗo wurinsu,hankalin Abbansu ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin yadda junaid ke gudu duk tsigar jikinshi ta tashi,

  Daƙyar suka samu suka damƙoshi saboda ƙokarin guduwa yake yi daga cikin gidan,

Hatta Marshal Omar da Sgr sai da suka jiyo ƙarar junaid,duk wani mai bacci acikin gidan sai da ya farka,ɗaya bayan ɗaya suka shiga fitowa suna tambayar ko lafiya,

  Jikinshi sae kerma yake yi duk yabi ya firgice,tambayarshi suka shiga yi ko lafiya,

  Muryarshi na kerma yace"Abba rishi uku acikin ɗakinta,Abba na mutu wlh aljanune ke bibiyata......'yana faɗin hakan ya sume ajikin Abban nasu,

  Tunda sukaji haka ransu ya basu Cewar yaje ɗakin Sehrish ne,Abbansu baiso hakan ba,dama yasan shi firgitacce ne,yaso ace tun farko saida ya fara yi mashi bayani anatse sannan yaje ɗakin nasu,

  Ayaan kuwa tun lokacin da yaji junaid ya fasa ƙara,ya ƙumshe dariya abakinsa,saboda yasan tsiyar daya tsula mashi,zaiyi wuya junaid ya yarda cewar Sehrish ƴan uku ne,ba kasafai yake fahimtar irin waɗannan abubuwan ba,sai an zaunar dashi cikin lalama anyi mashi bayani dalla dalla,sannan ake samu ya yadda,


"Junaid ne ko"?abusufyan ne yayi tambayar,yayin da yake daga zaune saman gadon,

  Sehrish tace"Shine daddy,ya ruɗe ne saboda ya ganmu mu uku,ya tsorata sosai naso na fahimtar dashi amma sai naga ya watsa aguje,'jin haka yasa abusufyan yin hanzarin saukowa daga saman gadon ya fuce daga ɗakin,

  Jikin jahad ba ƙaramin sanyi yayi ba,ganin halin da junaid ya shiga saboda ya gansu su uku,tsoronta kar wani abu ya same shi,ganin yadda ya watsa waje aguje,

   "Inaso naje naga halin da yake ciki,bansan meyasa ya firgita ba har haka,"sehrish ce tayi maganar a yayin da take miƙewa daga saman stool,jikinta na sanye da farar riga da dogon wando fari,kanta kuma na sanye da hula fara ta roba,buɗe ƙopar dakin tayi ta fuce tare da nufar inda suke,

  Komawa jahad tayi ta zauna saman kujerar gaban mirror,hannu tasa tare da ɗaukar man shafawar sehrish ta buɗe shi tana lakuto shi a hannunta tana shafa ma jikinta,

  "Jahad wai meya faru ne?naji sautin ƙara a kunne na," hosana ce tayi maganar,tana zaune tsakiyar gadon sae faman hamma takeyi saboda yunwar da take ji,

  "Ƙanin Ya Omar ne,junaid ya shigo ɗakin nan,ina tunanin ya tsorata ne da ganinmu shiyasa ya firgita,saboda yaga fuskokinmu iri ɗaya dana sehrish,"

  sauko da ƙafafunta tayi ƙasa tana cewa"bari naje naga meke faruwa a wajen,"

 Da sauri jahad tace"Kada ki fita hosana!sehrish ta fita muddin ya ƙara yin arba dake zai zauce ne,ki bari sehrish tadawo sai muji daga bakinta,idan an fahimtar dashi ya fahimta,sai mu fita atare,

  Hosana tace"amma fa Yunwa nake ji sosai aciki na,'

  "Bari daddy ya dawo zanyi mashi magana,nasan zai sa ashirya mana breakfast ɗinmu,'acewar jahad,

  Murmushi hosana tayi tare da cewa"jahad bakiji irin farin cikin da nayi ba jiyan nan!,wlh inason Daddynmu sosai,tun lokacin da gwaggon katsina tace mu ƴa'ƴan abusufyan ɗinta ne,ta kuma kirashi awaya tabamu mu gaisa dashi,tun daga lokacin nake jinshi araina,na dinga addu'ar Allah yasa ya zama mahaifinmun duk da alokacin nasan wanene mahaifin namu......'

  "Nikaina hosana a lokacin,da muka fara waya dashi sai da naji jikina yayi sanyi,naji wani irin yanayi atattare dani ashe dae dagaske mahaifin namu ne,gaskiya munyi dacen uba,yana da kirki sosai duk da ban zauna dashi na wani lokaci ba,amma tun daga kan Fuskarshi zakasan cewar mutumin kirki ne,ashe lokacin da muna yara har zuwa ya ta6ayi ya ɗauke mu yakaimu gidansu yayi mana wanka sannan yayi mana kitson kalaba,bawan Allah,Allah kaɗai yasan yadda yaji acikin zuciyarshi lokacin da wannan baƙin mugun ya rabashi damu,' 

  Hosana ta ƙara da cewa"Mummuna kawai,fuskarshi kamar ɗuwawu saboda rashin kyau,har naqosa naga yadda Ya omar ɗina zai karairaya ƙasusuwan jikinshi,"ta ƙarasa maganar tana yin nuni da hannayenta,yadda takeso Omar yayi ma Ya sayyadi,

  Ta cikin mirror jahad ke kallonta tana dariya tace"ae ba ƴa'ƴa Omar kaɗae ba,baki lura da yadda wannan mai blue eyes ɗin nan yayi ba,wani fari kyakkyawa mai ƙirar nan,har ni sai da na tsorata dashi ganin yadda ya zabura yabar wurin yana huci......'

  Hosana tace"ae nagane shi,Ni wlh tsoran idanunshi nake ji, kaman aljani,wai shima yanzu ɗan uwanmu ne ko?duk ƴan gidansu ya Omar ne ko?

  "Yayanmu zaki ce,ae yanzu duk wanda kika gani acikin gidan nan,to yayan mu ne,jiya baki lura da wani matashi acikinsu ba wani fari,mai mutunci wanda yazo ya kira mu,lokacin da alAbbansu ke neman mu"?

  Murmushi hosana tayi alamar tagane shi tace"daga gani zaiyi sauƙin kai sosai,kuma da alama ba ƙaramin farin ciki yake damu ba,mun gode ma Allah jahad daya haɗamu da dangin mu,'



 Lokacin da sehrish ta shiga main palour din nasu,anan ta samu matasan gidan duk tsaitsaye akan junaid,dake kwance saman doguwar sofa ɗin da Abbansu ya kwantar dashi,a lokacin har sun yayyafa mashi ruwa ya farfaɗo,bakinsa sai faman kerma yake yi kuma har lokacin bai daina faɗin "Rishi guda uku"ba,

  Abusufyan yace"bawan Allah,nidai naji an saki ƙara ashe wai junaid ne,bansan time ɗin daya shigo ba,lokacin ina bacci ne,ae da ban bari hakan ya faru ba,da tun lokacin na fahimtar dashi,ashe har yanzu junaid na nan da wannan firgitar tashi,ae nayi tunanin ya daina,'

  Shafa gefen fuskarshi abba yayi a yayin da yake zaune daga gefen daman kujerar yace"Ya tsorata ne sosai,ae ni kaina banyi tsammanin zaije ɗakin nata bane,naso ace saida na fara yi mashi albishir sannan yaje wurinsu,'

  Jahan dake tsaye yace"Aikin ayaan ne,shine ya tura shi ɗakin nata,'ya ƙarasa maganar yana hararar ayaan dake tsaye yana dariya,

  Duk Alexandra na tsaye tana sauraronsu,sam batasan inda zancen nasu ya dosa ba,

  Koda sehrish ta ƙaraso,zuba mata ido Alexandra tayi tana kallonta,gaban sehrish ne ya faɗi lokacin da tayi arba da ita,har sai da ta ambaci Innalillahi acikin zuciyarta,ba komae ya firgitar da ita ba face ganin fuskar sgr a fuskar matar,kuma batasan da ita acikin gidan ba, sai dai lokaci guda taji aranta kaman ta ta6a ganin hoton matar,

  Cike da mamaki Alexandra tace"wacece wannan kuma"?tayi maganar tare da yin nuni da sehrish wadda tuni ta koma bayan abusufyan ta tsaya,

  Jahan ne ya bata amsa da cewa"Ƴan ukun uncle abusufyan ne,'. 

  "Abusufyan kuma?dama ya ta6a aure ne?

  "Eh,ya ta6a aure batare da sanin kowa ba,sai daga baya abun ya bayyana cewar ƴa'ƴansa ne,kuma ƴan ukune kamanninsu iri ɗaya sak,abunda yasa kika ga junaid ya ruɗe kenan,baisan cewa su uku bane,ɗaya ya sani acikinsu,muma sai jiya Allah yasa mukasan da zamansu muka san cewa ƴa'ƴanshi ne,Nasan abba zai sanar dake komai,'

  Jinjina kai Alexandra tayi tare da ɗan ta6e bakinta,yayin da ta janye idanunta daga kan sehrish ta mayar dasu kan junaid dake ta faman sambatu,

  "Abba pls ku fahimtar dani mana!meyasa nake ganin Sehrish guda uku?ko na samu ta6in hankali ne,'

  "Junaid u should calm down ur mind,in baka natsu ba taya zamu fahimtar dakai,"acewar abbansu,

  Jin hannun mutun acikin nata yasata yin saurin juyawa,sai lokacin ta lura dashi sam bata ga fitowarshi ba,

  "Mommy,"ya ambaci sunanta cikin sanyin murya,cike da farin ciki tace"Fawan!ka farka daga baccin kenan"?tayi maganar ayayin da take janyo shi jikinta,sosai ta rungume shi,

  "Mommy tun yaushe kika zo ba'a sanar mun ba?sae dai na fito na ganki unexpected"

  "Tun jiya nazo fawan,muna tare da junaid acan gidana muka kwana tare dashi sai yau da safe muka dawo atare,da fatan na sameka cikin ƙoshin lapiya,'

  "Alhamdulillah mommy munyi missing ɗinki sosai da sosai,'

  "Nima nayi missing ɗinku fawan,'magana suka cigaba dayi atsakaninsu,

  Duk wannan abun dake faruwa alexandra bata tanka ma abusufyan ba,shima kuma bai tanka mata ba,tun lokacin daya shigo falon yayi arba da ita,yaga ta kawar da kanta gefe tun daga lokacin shima ya share ta,dama bata shiri dashi,tun lokacin da Abba ya aurota,ya ta6a zama agidan,yanayin yadda take wahalar da yayanshi ne yasa yayi mata rashin kunyar da ta haddasa gaba atsakaninsu,saboda shi bakinshi bai rufuwa muddin yaga tana gaya ma Yayanshi hossein magana saiya mayar mata da martani mai zafi,wannan dalilin ne yasa Abba yace ya tattara ya koma wurin ammi don bazai iya jurar zama dashi ba,kullum haɗa mashi Bomb yakeyi acikin gida,shiyasa abusufyan bai zauna agidan yayan nashi ba,kuma ammi bata kawo shi gidan ba lokacin daya addabeta da rashin jin maganarshi,kawai ta yanke shawarar kai shi gidan hajiya Ameenatu,

   Kowa daya fito tun daga kan su irfan jabeer,khaleed da kanal yousouf babu wanda baiyi farin cikin zuwan mommynsu junaid ba,daya bayan ɗaya saida tayi hugging ɗinsu ajikinta,kanal yousouf ne kawai ta manna ma kiss a gefen fuskarshi,ji suke tamkar mahaifiyarsu ce Maryam ta dawo gidan,Allah sarki Allah ya jiƙan rai,tun daga yanayin yadda alexandra ta kar6esu hannu bibbiyu tana rungumarsu ransu ya basu cewar ta shiryu yanzu,da alama babu wannan girman kan nata da kuma Zafin ran nan,

   Sehrish dae duk jikinta yayi sanyi tun daga kan irin kallon da taga Mommynsu junaid nayi mata,ranta ya bata cewar akwai matsala,sam fuskarta babu yabo babu fallasa lokacin da Jahan ke sanar da ita cewar ɗiyar uncle ɗinsu ce,

  Abbansu na ƙoƙarin fahimtar da junaid,suka jiyo muryar sgr yana tambayar"Meya faru ne!"yayi maganar ne ayayin da yake saukowa daga saman stairs ɗin,jikinshi na sanye da shirt fara ta ɗame jikinshi sai kuma dogon wando jeans,ba ƙaramin kyau yayi ba,

Gaba daya suka juyo suna kallonshi,Marshal Omar na biye dashi abayanshi,atare suka sauko,

  Wani irin farin ciki ne ya lullu6e alexandra lokacin da tayi arba da first born dinta wato Surgeon General Rafayet,gaba ɗaya tagaza rufe bakinta saboda ba ƙaramin so take mashi ba,tana matuƙar alfahari dashi,

  Sehrish kuwa tunda taji muryarshi taji gabanta ya faɗi rass,tabbas tayi kewarshi sosai,jiya abubuwan da suka faru ne suka hana takai mashi dinner ɗinshi,tasan cewa daƙyar ne idan yaci wani abu ajiyan nan,

  Aranta tace"bansani ba ko yana farin ciki da kasancewata ƴar uwarshi,ɗiyar ƙanin Mahaifinshi,ko yaya yaji aranshi"?

   Jahan ne ya sanar dasu abunda ya faru da junaid,

  ƙarasawa Sgr yayi wurin Mommyn tasu,ita tafara manna mashi kiss a gefe da gefen fuskarshi sannan shima yayi mata kamar yadda tayi mashi,daga bisani kuma suka rungume junansu,

Abun ba ƙaramin burge sehrish yayi ba,har sai da ta ɗan saki murmushi kaɗan a fuskarta,

  "Am really glad to see u mom,"ya furta hakan ayayin da suka raba jikinsu daga na juna,

  Shafa gefen fuskarshi tayi tare da cewa"Yanzu ka kyauta mun?tun yaushe rabon dana sanya ka a idanuna Alex?ka daina zuwa wurina,kusan 1 year kenan baka tako ƙafarka kazo ba,'

  Ganin hawaye sun cicciko a idanunta yasashi yin saurin ruko hannayenta tare da cewa"pls mom just forget about the past,nasan ban kyauta ba,amma kullum kina araina,kuma ina kiranki awaya muna gaisawa....'

  Abbansu ne ya katse firar tasu da cewa"Ashe ba daɗi,Rama mun yayi Nima,ƙiri ƙiri kin rabani da aurena kinsa anata yi mun kallon Tazuru,'

  Dariya sukayi gaba ɗayansu,banda sehrish dake tsaye jugum tana sauraronsu,

  Matsawa Omar yayi cike da zolaya yace"Oh Mommy abun ƴar wariyar launin fata ce ko?atare da bro ɗina muka fito,amma ko kulani bakiyi ba...'yayi maganar yana ɗan ɗaure fuskarshi,

  murmushi alexandra tayi tare da komawa wurin marshal,ta manna mashi kiss agefen fuskarshi sannan ta dafa shoulders ɗinshi tare da cewa"Omar ni bazan iya cewa komai ba,so nake nafara huce haushina akanshi kafin nadawo kanka,dama kaine mai ɗan son zumuncin,duk lokacin da kuka samu hutun aiki kana janyo shi kuzo wurina,amma yanzu duk kun juya mun baya,ni nasan duk shirin Abbanku ne yasan cewa dole nayi kewarku....'

  Omar yace"no ba haka bane mommy,rayuwarce sai a slow,bamu manta dake ba,kuma kamar yadda rafayet ya fadi,muna kiran ki fa awaya kullum mu tambayi lpyrki,da ace kin ƙara 1 week baki zo nigeria ba,da kin ganmu munzo,ba don ma aiyuka da sukayi mana yawa ba,ae da mun rigaki zuwa....'

  Ba ƙaramin daɗin kalaman Omar taji ba,yasan duk wata hanya da zaibi don ya kare kansu a wurinta,ba kamar SGR ba,shi kai tsaye kawai yake maganarshi ba wata kwana kwana,'

  Sai da suka samu natsuwa sosai,sannan suka tattara hankalinsu kan junaid,

   "Ina sehrish take ne"?Abbansu ne ya ambaci sunanta,saboda yaga gifcinta a wurin,

  Da sauri ta amsa mashi da cewa"Gani nan Abba,"tayi maganar tare da fitowa daga tsayen da take abayan daddynsu,

   Haɗa ido sukayi da Sgr,da sauri ta kawar da idonta,zuciyarta na harbawa da ƙarfi da ƙarfi,daƙyar ta iya ƙarasawa wurin abban nasu ta gaishe shi,

  Bayan ya amsa mata yace"ki fahimtar da junaid,ina tunanin in yaji daga bakinki zaifi yadda cewa ku ƴan uku ne,'

   Murmushi sehrish ta ɗan yi tana kallon fuskar junaid wanda ke kwance saman kujerar duk yabi ya rikita kanshi,tunda tayi magana yasan cewa itace saboda yaji muryarta,

   Cikin sanyin murya ta soma magana,

  "Junaid ka manta kwanaki na ta6a sanar dakai cewa Ina da ƴan uwa?waɗanda nake kira da wayarka?

"Amma ai kince mun baki da wasu ƴan uwa lokacin da muka yi maki magana akansu ni da aunty azmee,"yayi maganar yana faman hura hanci,

  "Junaid a lokacin bana cikin hayyacina bansan ya akai na manta dasu ba,amma yanzu nadawo hayyacina kuma Zan iya tuna komai a game dasu,idan baka yadda dani ba,bari na tuna maka,ko ka tuna Yarinyar daka ɗauko a school cikin motarka?tun lokacin saida nayi ƙoƙarin fahimtar dakai cewar bani bace,ni ina a makaranta ka barni,shine dalilin da yasa nasha wahala aranar,'

  Jin wannan maganar ta sehrish yasa junaid miƙewa daga zaune,bakomai ne ya faɗo mashi aranshi ba face,yadda jahad ta kasa sakewa dashi,kuma launin gashin kanta baƙi ne ba irin na sehrish ba,hatta muryarsu ma akwai ɗan bambanci,haba no wonder shi dae ya jima yana tunanin cewa al'jana ya ɗauko a motarshi ashe ashe mutunce,indae dagaske ne xancen sehrish hakan na nufin cewa ƴar uwartace ya ɗauko a motarshi?to kodai sune yaran da Ya Omar ɗinsu yasa su gyarama gidan uncle ɗinsu zai kawosu suyi rayuwa aciki......'bai ƙarasa zancen zucin nashi ba,Muryar Omar ta katse Hanzarin shi"Junaid!maganar da take faɗa maka dagaske ne!they're triplet,kuma ƴa'ƴan uncle abusufyan ne,dukanmu bamu son da haka ba sai jiya Allah ya bayyana mana komai,'

  Yana kai ƙarshen maganar tashi ya juya tare da kallon fawan yace"Kaje ka kira mun su hosana da jahad suzo ya gansu da idanunshi don ya shaida cewar mutane ne ba aljanu ba,'

  Cike da zumuɗi fawan ya wuce bedroom ɗin sehrish a lokacin har jahad ta kammala shirya kanta cikin riga da skirt na sehrish,ba ƙaramin kyau tayi ba,

  Kwankwasa ƙopar fawan yayi kafin ya turo tare da cewa"Ya omar nason ganinku yanzu,'jin haka yasa sukayi saurin kimtsawa,duk suka yafa gyala a kansu,

  Atare da fawan suka shigo cikin main palour ɗin,

   Jerawa sukayi kusa da sehrish duk sun sha jinin jikinsu tsoransu kar ace wani abun ne kuma ya taso,

  zuba masu ido junaid yayi yana kallonsu,idan ya kalli jahad sai ya kalli hosana,

  A ƙarshe ya tsaida idanunshi kan jahad,ta hanyar gashin girarta ya gane cewa itace ya ɗauko a motarshi,har suka sha Love,

  Dafe kanshi yayi tare da cewa"OMG!Abba kenan reesh ƴar uwata ce,jini na,ɗiyar uncle ɗinmu abusufyan!taya hakan ya faru?kuma dama rishi ƴan uku ne su ba ita kaɗae bace!idan har dagaske ne meyasa basu taso atare damu ba!!!!!!!_

Karaf maganganun da junaid ke faɗi suka dira a kunnan Hayaam,wadda fitowarta kenan,yunwa ta korota daga bedroom ɗinta ta gaza jurewa shine ta lalla6a ta fito don ta shiga kitchen,

  Gabanta ne yayi wani irin bugu ji kake rasss!rarasss!hankali amatuƙar tashe ta ɗago da idanunta ta sauke su akan Mutanen dake tsaitsaye acikin falon,waro ido waje tayi ganin Sehrish dasu jahad,anan ta tuna abunda azmee ta faɗa mata jiya na cewa ƴan uku ne su,kuma kamanninsu iri ɗaya sak,a fili ta ambaci"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!Ya Allah ka rabani da mugun Ji da kuma mugun gani!nashiga uku Ni yau Hayaam,bari dae na ƙara kasa kunne naji uban da suke tattaunawa,ya Allah kasa korar shaggun za'ayi daga gidan,


"Junaid sehrish ɗin daka sani da kuma waɗannan biyun masu kama da ita sak,ƴa'ƴana ne,ni ne mahaifinsu,Na auri mahaifiyarsu ne ba tare da sanin kowa ba........'ataƙaice Abusufyan ya fayyace ma Junaid komai,

  Saboda tsabar kiɗima hayaam ƙiris ya rage ta fasa ƙara a wurin,ta matukar firgita da jin abunda abusufyan ya sanar ma jahad,tashin hankalin da ba'a sama shi date,gudu gudu,sauri sauri hada tuntube wurin komawarta cikin bedroom ɗinta,jikinta sae faman kerma yake yi kamar wadda sanyi ya kama,hannu ta aza asaman kanta tana faɗin"nashiga uku!na bani na lalace!ƙarshe na yazo acikin gidan nan!taya akai haka ya faru duk ina nan sake da baki bansani ba,wai yanzu dagaske yarinyar nan mai aikin gidan dana raina,nake ganinta ƙaskantacciya yar wurin uncle ɗinsu ce Abusufyan,Tabɗijancan,Kallo ya koma sama!kai anya kuwa banyi kuskure wurin sauraran maganar shi ba?

  Turo ƙopar da akayi ne yasa ta yin firgit ta juya,

 Tana ganin azmee hannunta ɗauke da plate na breakfast ɗin da ta kawo mata,

  Jiki na rawa hayaam ta ƙarasa wurinta tare da cewa"Aunty Azmee wai dagaske ne Seh...seh..rish ɗiyar uncle ɗinsu ce abusufyan!"

  Ƙayataccen murmushi azmee ta saki tare da cewa"Dagaske ne mana!Nima sai da asuba nakejin wannan labarin a wurin Hajiya azeemarsu....'tunda azmee ta soma magana hayaam ta fita hayyacinta,

  Har sai da azmee ta ambaci sunanta"Hayaam!naga kamar kin tafi duniyar tunani ne?lafiyarki kuwa?

  Murmushin yaƙe ta saki tana ƙoƙarin danne damuwarta tace"Azmee bana jin daɗi ne,zuciyata tafarfasa takeyi ne,"

.azmee tace"Allah sarki,dama saida raina ya bani cewa baki lafiya,To Allah ya sawake,yanzu dae ga wannan ki fara karyawa nasan kina jin yunwa.....'

  Wani irin bugu Hayaam takai ma plate ɗin dake hannun azmee nan take yayi gefe guda ya tarwatse ƙasa,snacks ɗin dake aciki suka 6are,

  Ita kanta hayaam sai da ta firgita saboda ba'a cikin hayyacinta tayi hakan ba,tsananin 6acin rai ne da ƙiɗimar da tayi,

  Hankali tashe azmee tace"Hayaam!!'

 Tunkan ta karasa maganar hayamm ta zukunna  jiki na rawa tashiga kwashe snacks ɗin dake zube aƙasa tana mayarwa cikin plate din,

  Muryarta na rawa tace"dan Allah aunty azmee ki tafi kawai,nagode sosai zanci....'

 Ƙiris ya rage azmee ta fashe da dariya,ganin yadda la66an hayaam ke kerma kamar gandar nama,tasan cewa duk akansu sehrish ne,

  "Allah ya baki lafiya,"ta ambaci hakan tare da juyawa tabar mata ɗakin,

  Azmee na fita hayaam ta jefar da plate ɗin,

. miƙewa tsaye tayi nan fa tashiga safa da marwa tana zagaye ɗakin,bakowa ne ya faɗo mata aranta ba face Aunty laila,tabbas ya kamata tayi gaggawar sanar da ita halin da ake ciki,

   Jiki na rawa ta ɗauko wayarta dake ajiye saman mirror,tana danna wayar yatsun hannunta na kakarwa,daƙyar ta tsaida hankalinta wuri guda ta danna ma Aunty Babba kira.

   

  

  



  

 

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



_Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata  zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari sannan a kula wannan itace numbar wayata,Wasu suna ɗaukar numbar Wanda suka bani tallarsu kayansu suna kiransu a matsayin ni,bayan ni ga numbar dana bada nan itace numberta_


*Nagode sosai da addu'o'inku agare ni,da kuma uzurin da kukayimun,har zuwa wannan lokacin,Allah yabar zumunci a tsakaninmu daga nan har gidan aljanna💃*



*nace ba Masu satar littafi suna fitarwa ta bayan fage,mai yasa baku ƙarasa masu labarin ba?kuma kenan saida kuka jira ni?ae nayi tunanin cewa zaku ƙarasa masu labarin ne ashe dai sai anjira Boss*😂🤣😅



Bismillah



Kai tsaye sautin ringing ɗin wayar ya daki dodon kunnan Aunty babba dake baje saman gadonsu tana Bacci,a lokacin ko yatsanta bata jin xata iya motsawa saboda baccin dake a idanunta,yatsina fuska tayi alamar an takura mata,

   Ishaq dake tsaye agaban mirror yana gyara jikinshi ya ɗan gyara murya tare da cewa"Madam ki daure ki tashi ki ɗaga kiran nan!da alama kira ne mai muhimmanci tun ɗazu wayar ke ta ringing,"

  Uban tsoki Aunty babba ta buga tare da yunƙurawa daƙyar ta tashi daga zaune,jikinta na sanye da sleeping dress,riga da wando purple colour,

  Fuskar nan tayi suntum kamar wadda aka nausa,hannu takai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman bedside drawer,duba screen ɗin wayar tayi ganin sunan Hayaam ya bayyana yasa ta ƙara tamke fuska kamar ta shanu,ɗaga kiran tayi tare da kara wayar a kunnanta,rai a6ace tace"Meyasa kika kirani fitsararra!ko kin kira ne don ki ƙarasa yimun rashin kunyar taki don ubanki,"

  on the other hand hayam tace"haba aunty laila,ni harna manta da abunda ya faru atsakanin mu.....'tunkan hayaam ta ƙarasa maganar Aunty babba ta katse mata hanzarinta da cewa"Idan kin manta ae ni ban manta ba,Ki faɗamun uban miyasa kika kira ni,idan ba haka ba ni zan kashe wayar,

  Zuba mata ido Ishaq yayi yana kallonta aransa yace"Zagi kamar ƴar maguzawa,ko kunyata bata ji,sae faman ɗura ashar take yi,ni dae Allah ya haɗani da Guyaba,'

     cike da damuwa hayaam ta sassauta muryarta,tare da cewa"Aunty laila,na shiga uku,ko ince mun shiga uku,Akwai gagarumar matsala,Gaba daya duk wani plan ɗinmu ya tashi aiki,'

  Tunda Aunty babba taji hakan,gabanta ya faɗi rasss,ƙasa ƙasa da murya tayi tace"Hayaam meya faru?wata irin matsala kike magana akai?

  "Aunty laila,Ashe yarinyar nan mai aikin gidansu,ɗiyar uncle ɗinsu ce Abusufyan!!!!!" tamkar saukar aradu haka aunty babba taji maganar Hayaam aikuwa a matuƙar gigice ta miƙe tsaye tana cewa

  "kutumar uba!inji ubanwa!yaushe Abusufyan ya ta6a aure,Wlh ƙaryane koma wani ɗan ƙaniyar ne ya faɗi maki hakan babban maƙaryaci ne....'

  Gaba daya hankalin ishaq ya dawo kanta,maganar dayaji tana fadi ta tsaya mashi aranshi,

   "Wani abusufyan din kuke magana akai,"

  Firgit Aunty babba tayi tare da ware ido tana kallonshi sam ta manta da cewar yana acikin ɗakin,

  Hankali a matuƙar tashe ta miƙe tsaye da nufin ta fuce daga cikin ɗakin,Saboda tsabar ruɗu ta nufi hanyar shiga toilet,

  gyaran murya ishaq yayi mata tare da cewa"kada fa ki shiga toilet da waya a kunnanki,'

  A zabure ta juya ta kuma nufi wardrobe da alama ruɗu yasa ta manta hanyar fita daga ɗakin,zuba mata ido yayi yana mai mamakin irin kiɗimar da tayi,to ko lafiya?ya tambayi kansa,

   Bata ankara ba sae da goshinta ya bugi jikin wardrobe din kayan nasu,sannan ta gane inda ta dosa,Rai a6ace ta kama hanya ta fuce daga dakin,saukowa downstairs tayi ta miƙi hanyar wannan tsohon store ɗin data ta6a garƙame su hosana aciki,anan corridor ɗin ta tsaya tana sauraran Hayaam,

  "Wlh Aunty laila da gaske ne,Ni shaidace,Naji komai lokacin da Uncle ɗin nasu yake korama junaid bayani,bama haka ba Aunty azmee da kanta ta gasgata mun hakan,Babban abunda yafi rikitar dani Yaran fa triplet ne ashe,kuma dukkansu Mata ne kyawawan gaske,kamannin su sak iri ɗaya,Kuma kina kallonsu zaki gane cewa ƴa'ƴanshi ne......'

  Hannu ɗaya Aunty babba tasa ta dafe tsakiyar kanta,yayin da dayan hannun ke ruƙe da wayarta data kara a kunnanta,

  "Hayaam bazan ta6a yarda da zancenki ba,Taya hakan ma zata faru!mutumin da bai ta6a yin aure ba,Shi za'ace yana da ƴa'ƴa har ƴan uku!Cikin shege kenan ya ta6a yima wata harya same su!Ni ban yarda da kalamanki ba,Hayaam kinsan cewa babu kyau tsoratar da musulmi,Idan wasa kike mun ki daina!!!!!

6acin raine yasa hayaam ta kashe wayar 

  Fashewa da kuka tayi saboda ƙululun baƙin cikin daya tokare mata maƙoshinta,ga zuciyarta dake ta faman tafarfasa,Gaba daya bata jin daɗin jikinta,

  Zubama wayar ido Aunty babba tayi tana kallonta,

  Tsoki taja tana jinjina kai tace"dama saida raina ya bani cewa ƙarya take yi mun,tayi mun hakan ne saboda ta tsoratar dani don in saukko,Shashasha kawai,

    "Mommy kin farka kenan"

Muryar hafsat ce ta katse mata zancen zucin nata,

  Juyowa tayi tana kallonta,atsaye take fuskar nan ɗauke da murmushi jikinta na sanye da riga da wando na jeans,ta ɗaure sumar kanta da ribbom,yayin da hannunta ke ruƙe da Cup mai ɗauke da Tea mai zafi sai faman tiriri yake yi,

  Tunda Aunty babba taga hafsat na murmushi tasan cewa akwai matsala,hakanan dae ba zakaga fuskar hafsat da murmushi ba tunda farar safiya,

  ƙaƙalo murmushin yaƙe Aunty babba tayi tare da cewa"Lafiya naga kina murmushi"?

  "Lafiya lou mommy,kawai wani abun farin ciki ne ya faru,nasan cewa muddin kema kika ji,zaki yi farin ciki sosai,'

  Murya asanyaye aunty babba tace"Faɗamun daughter har na ƙosa naji wannan abun farin cikin?halan an ƙara maku albashi ne?ko matsayi aka ƙara maki wurin aiki"?

  Dariya hafsat tayi tana girgiza kai tace"Mommy baki canka dai dai ba,wannan albishir ɗin da nakeso inyi maki yafi ƙarfin duk waɗannan abubuwan da kika lissafo,kar6i tea ɗin nan ki fara korawa kafin na faɗa maki,"

  Hannunta na kerma ta kar6i kofin da hafsat take miƙa mata,a hankali takai cup din  bakinta ta kur6i Tea ɗin,kusan sau uku tana kur6arsa,kafin ta ɗan jinkirta bayan ta janye kofin daga bakinta tace"daughter dan Allah ki faɗamun wannan wani abun farin ciki ne!wlh duk na ƙosa naji,'

  "Zan faɗa maki mommy amma mu shiga daga cikin palour mu zauna,'

  "Ba inda zanje,idan zaki faɗamun ki faɗamun kawai,Sae ja mun rai kikeyi," tayi maganar tana faman tamke fuska,

  Hafsat tace"bada jimawa ba,Na kira Aunty azeema,don in gaishe da ita,Anan take sanar dani cewa ƴa'ƴan uncle abusufyan Sun bayyana...!

  Tunkan ta ƙarasa maganar a gigice Aunty babba ta saki kofin dake hannunta,Ya tarwatse ƙasa,Ruwan tean dake ciki ya fallatsar masu a ƙafa,

  ja da baya hafsat ta ɗanyi tana kallonta tace"haba mommy,so kike ki ƙonamin ƙafa ta,daga faɗin abun farin ciki?

  Rai amatuƙar 6ace tace"Ki 6ace mun da gani sakarya kawai,Maƙaryatan banza,bazan ta6a yadda da kalamanku ba,duk bakinku ɗaya da Hayaam,'

Ta faɗi hakan tare da kama hanya fuuuuu kamar zata tashi sama,ranta duk a jagule,bin bayanta hafsat tayi da kallo harta haye upstairs,ta6e baki tayi tare da watsa hannayenta tace"I don't care, Ni dae farin ciki nakeyi,Daddy ma nake jira in tambayeshi yaushe zamu je gidan saboda a qagare nake dana ga ƴa'ƴan uncle ɗinmu Abusufyan,tunkan na gansu har naji ina sonsu sosai,in ma na tashi tafiya hada tsaraba zan tafin masu dashi,'

  Cike da farin ciki hafsat take maganar,zuƙunnawa tayi tana tattare kofin da aunty babba ta fasa,


Lokacin da Aunty babba ta ƙarasa bedroom ɗin nasu,har ta ɗaga ƙafarta zata zura acikin ɗakin taji muryar ishaq yana cewa"Alhamdulillah!Alhamdulillah!Alhamdulillah!Abba nayi farin ciki sosai,Meyasa tun jiya ba'a sanar dani ba,ae da tunda sanyin safiya zanyi maku dirarr mikiya,Amma ina taya uncle murnar ganin ƴa'ƴanshi,kuma ina tayamu murnar samuwar ƴan uku acikin zuri'ar mu,gaskiya bazan ma iya jurewa ba,Zan shirya nazo ne kawai,saboda na qosa naga ƴan ukun mu bayin Allah....   

    Abba yace"wani abun ma sai kayi tozali da yaran,kyawawan ƴan mata dasu,Yadda kasan photo copy ɗin abusufyan haka suke,kamanninsu sak iri ɗaya da nashi,'

  Murmushi Ishaq yayi tamkar yana agabanshi yace"Abba kafin na ƙaraso,dan Allah a isar musu da saƙon gaisuwata,Ace yayansu General ishaq yana gaishe su sosai da sosai,kuma saboda suma zaiyi zuwa na musamman,'

  "Insha Allah zan sanar masu yanzun nan,Allah ya kawoka lfy,"

  "Ameen Abbana,"

Sun jima suna waya kafin sukayi sallama ishaq ya ajiye wayar,

  tashin hankalin da ba'a sama shi date!!!!!!!

  Magana dae ta tabbata da gaske ne zancen da hayaam da hafsat suka faɗa mata,Tabɗijancan,

  Dakyar ta iya shiga cikin ɗakin,lokaci guda ta rasa kuzarin jikinta kamar wadda tayi Zazza6i na sati ɗaya,

  Jin takun tafiyarta yasa ishaq juyawa yana kallonta fuskarshi a washe har ya kammala shiryawa cikin haɗaɗɗiyar shadda,

  Ganin yana ƙoƙarin buɗe baki yayi mata magana yasa tayi saurin katse shi da cewa"Naji abunda ya faru,Hafsat ta sanar dani komai,ina tayaku murna,'ko amsar shi bata tsaya ji ba,ta faɗa cikin toilet,

  Tana juyo muryarshi daga cikin bedroom ɗin yana cewa"Ni yanzu zan wuce Abuja ne,inyaso kun biyo ni daga baya ko zuwa gobe ko jibi haka,duk dae yanda kuka yanke shawara keda hafsat,

  daga cikin toilet tace"Allah ya sauke ka lpy,in anje agaishe mana da mutanen gidan,"

   "zasuji insha Allah," ya amsa mata tare da kama hanyar fita daga ɗakin.


❤🤍❤


Acan 6angaren kuwa har lokacin suna a falon kan junaid da Uncle abusufyan ya gama fahimtar dashi game da Su Hosana da jahad,

jiki asanyaye yace"Amma meyasa su ba suyi rayuwa atare damu ba?meyasa Abba?uncle why?cike da tuhuma yake maganar yana kallonsu,yayin da fuskarshi ke ɗauke da damuwa,

abban su ne yace"Junaid,mu kanmu bamu san dasu ba,da ace munsan da zamansu da bamu bari hakan ya faru ba,ƙaddara ce kawai ta riga fata,"

  Shiru junaid ya ɗanyi yana ƙare ma su Jahad kallo,yaso ace tun fil azal tare da yaran ya taso,da ba ƙaramin kulawa zasu samu a wurin ƴan uwansu ba,Allah sarki rayuwa kenan,Rashin sani yafi dare duhu,su kansu su Sehrish sae dama dama suke da sun san cewa suna da wannan family ɗin daba abunda zai hana su nemi danginsu,Tabbas an cuci rayuwarsu ƙiri ƙiri an rabasu da Ubansu kuma an hanasu danginsu,wata shari'ar dae sae a lahira,


"Nasan yanzu kowa yana jin yunwa,saboda halin da muka shiga jiya babu wanda ya samu damar cin abinci acikin mu,Yakamata yanzu komai ya wuce,Lokacin farin ciki ne,Za'a shirya gagarumar walima saboda ƴan ukun mu,munaso su manta da duk wani abu da ya faru a rayuwarsu kuma su ƙaddara cewa tamkar yau ne suka faɗo duniya,ko ba haka ba"? Ya yi maganar yana kallon matasan gidan dake atsaye,Kowannansu fuskarshi asake,su fawan ne suka haɗa baki wurin cewa"Wannan haka yake Abba,In sha Allah zamu nuna masu soyayyar ƴan uwantaka,har sai sun manta da dukkan wani ƙunci da suka fuskanta na rayuwarsu,' murmushi kawai Abusufyan ke saki don ba ƙaramin daɗi yaji ba,

Marshal Omar yace "Sannan kuma muna ƙara baku haƙuri game da halin da kuka tsinci kanku,duk da ba laifin mu bane,amma mun ɗaura ma kanmu laifin,Muna neman afwarku,Hosana Sehrish and Jahad,forgive us pls,'

  gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi,lokaci guda kuma sukaji wata irin soyayyar ƴan uwansu ta kamasu,

Jahad ce tayi ƙoƙarin cewa"duk wani abu daya faru damu dama can rubutaccen ne!Allah ya riga da ya ƙaddara faruwan hakan,mun gode ma Allah da muka cinye wannan jarabawar,da juriya kuma da haƙuri,yanzu gashi gaba ɗayanmu muna farin cikin wannan rana da Allah ya haɗamu da danginmu,Babban abun farin cikin ma da ya kasance Uncle abusufyan shine mahaifinmu ba waccen fasiƙin mutumin ba.......'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya zo mata,Janyota Abusufyan yayi tare da rungumeta ajikinshi,yana ɗan bubbuga bayanta,

  "Ya Omar," hosana ce ta ambaci sunan shi,tana faman kumshe dariya abakinta,gaba ɗaya suka mayar da hankalinsu akanta,nuna shi tayi da yatsanta sannan ta nuna kanta,kafin ta haɗe yatsun wuri guda ta ƙullasu,Alamar ita dashi sun zama  ƴan uwan juna, ƙayataccen murmushi Marshal ya saki yana kallonta,

Duk wannan abun dake wakana akan idon Sgr dake atsaye,ya goya hannayenshi asaman wide chest ɗinsa,Har lokacin bai sauko ba,hankalinsa fa bazai kwanta ba har sai yayi tozali da YA SAYYADI,


Suna cikin magana muryar azmee ta katse su da cewa"Abba an kammala shirya breakfast ɗin,yakamata ku hallara a dining ɗin," tana magana idonta na akan su jahad fuskar nan ɗauke da murmushi,

   Batare da 6ata lokaci ba,gaba ɗayansu suka hallara asaman zungureran dining table ɗin wanda ke shake cike tab maƙil da kayan makwalashe naci dana sha,mutun goma shabiyu yake ɗauka,akwai kuma wanda Abban su junaid yasa aka ƙara cikin wanda aka shirya walimar jiya dasu,Ansanya shi a gefen nasu mai mazaunin mutun shida,Aunty azmee ta jera wasu kayan kalacin asaman shi,anan Abusufyan ya zauna tare da su sehrish jahad da hosana,


Tun daga kan yadda kowa ke zuba abinci acikinshi zai tabbatar maka da cewar ba ƙaramar yunwa suke ji ba,ko azmee basu jiya tayi serving ɗinsu ba suka shiga zuba abincin da kansu,Sgr ne kawai tayi serving ɗinsa sae kuma Abbansu,amma sauran ba wanda ya tsaya jira,wurin yayi tsit bakajin hayaniyar komai,sai sautin Cokulla,kwas kwas kwakwasss,


ɗagowa Marshal omar yayi karaf idonshi yaci karo dana hosana,ta zuba mashi ido ko kyaftawa batayi,kasancewar table ɗinsu na kusa dana juna,tazarar kadan ce,

  Da cokalin hannunshi yayi mata nuni da plate din gabanta,alamar ta mayar da hankalinta kan abunda take ci,

  murmushi tayi tare da kai hannu ta dauki lemu tana korawa,

  Junaid kuwa duk ya rasa samun natsuwa sam ya gaza cin abincin dake a gabanshi sae faman juya cokalin yake yi acikin plate,duk in ya tuna abunda yayi ma Jahad acikin mota amatsayin Sehrish sai yaji gabanshi ya faɗi rass,fargabar shi kada jahad tayi tunanin ko ɗan iska ne shi,tunda ba sanin shi tayi ba,kar kuma tace zata sanar ma wani abunda yayi mata,tunawa yayi da lokacin daya tsoma harshenshi acikin bakinta ya ƙanƙameta yana kissing lips ɗinta,ba iya nan ba ya tsaya har hannunshi saida ya zura ackin hijabinta

  Hankali tashe junaid ya miƙe yana ƙoƙarin barin dining ɗin,hankalin kowa ya koma kanshi,

  Har suna haɗa baki wurin tambayar shi ina zashi,

  fuskarshi ɗauke da damuwa yace"Abba,bana jin yunwa,dama munyi breakfast tare da Mommy,zanje wurinta yanzu" Abbansu yake ma magana amma hankalinshi na akan Jahad dake shan farfesun da azmee ta zuba mata a plate,da alama ba ƙaramin daɗi farfesun yayi mata ba,duba da yadda ta mayar da hankali akanshi,

  "Okey,zaka iya tafiya," ya bashi amsa,cikin sauri junaid ya kama hanyar zuwa bedroom ɗin Abbansu don acan ta sauka,yana tafiya yana waiwayen su jahad aranshi yana cewa"wayyo Allah na,bansan me zai biyo baya ba,nasan cewa dole ta sanar ma Uncle abunda nayi mata,idan ta faɗa mashi shi kuma zai faɗa ma Abban mu ne,Abban mu kuma zai faɗa ma Babban yayanmu ne,shi kuma zaice wuyana ya isa yanka tunda har na iya Sumbatar mace daga nan zaiyi tunanin turani aikin Soja abunda banso,shikenan tawa ta ƙare'

  ranta ne ya bata cewar ana kallonta,hakan yasa ta tsagaita daga shan farfesun da takeyi,ta ɗan ɗago idanunta,kai tsaye suka sauka akan junaid dake can nesa dasu yana kallonsu,

Mamaki ne ya kamata ganin yadda ya ƙura mata ido yana kallonta,aranta tace"bansan meyasa yake kallona ba,tsorana kar ace baisan ganina ne,'

  "Allah yasa halinta irin na Sehrish ne,idan takasance mai sauƙin kai irin na rishi ɗina nasan cewa zata rufa mun asiri,amma anya zatayi sauƙin kai?Nasan me zanyi daga yanzu zan dinga ɗaure mata fuska,in nuna kamar na tsane ta,nasan hakan ne kawai zaisa taji tsorona taƙi faɗa masu abunda ya faru atsakaninmu!good idea",

  Yana kai ƙarshen zancen zucin nashi ya watsa mata harara tare da murguɗa mata baki,ya juya ya nufi bedroom ɗin abbansu,

   Jiki asanyaye jahad ta ɗauke idanunta daga kallon bayanshi da take yi,lokaci guda taji komai ya fita ranta ba don komai ba sai don kallon da taga junaid yayi mata,maganarta ta tabbata,Junaid baison ganinta,tunda gashi ya harare ta kuma hada murguɗa mata baki,

  Muryar daddynsu ce ta katse ta da cewa"Jahad,meya faru ne?naga kin daina shan farfesun ina fata lafiya?

  firgit ta ɗanyi tare da wurga eye balls ɗinta akanshi tace"Am ok daddy,'

  jinjina kansa yayi kafin yace"Ku saki jikinku,kuci abinci sosai,kada kuji komai,nasan baku saba ba,don na lura akwai rashin sabo atattare daku,amma a hankali zaku saba da ƴan uwanku,'

  hosana tace"Abba ae ni,nama saba da kowa,baka ga yadda nake ta cika cikina da abinci ba,jahad ce ke jin kunya,ni bana jin kunyar kowa,'

  Dariya sukayi gaba ɗayansu,Sehrish na cikin sakin dariyar nan,Karaf idanunta suka haɗu dana Sgr,ɗagowar shi kenan yayi arba da ita,gabanta ne taji ya faɗi rass saboda fuskarshi a murtuke take ba annuri,nan take dariyar da takeyi ta koma ciki,ganin ta zuba mashi ido,yasa shi jefa mata harara,a hanzarce ta kawar da idanunta daga kallon fuskarshi da take yi,jikinta kuma yayi sanyi,ta shiga tambayar kanta dalilin hararar da taga big bro yayi mata,kodai baya farin ciki ne da kasancewarta JININ SA!?tabbas hakan zai iya faruwa,Wataƙil kodan ya saba ganinta a matsayin ƴar aikinsa,baiwarsa,ƙasƙantacciya shiyasa yanzu Yake nuna 6acin ranshi don yana ganinta tamkar a matsayi ɗaya suke dashi,Ƴa'ƴan Wa da ƙani,da alama hakan baiyi masa ba,

"Idan har dagaske ne abunda nake hasashe,insha Allah zan tattara na bar masu gidan,saboda bana son 6acin ranshi,zan iya yin komai don farin cikin shi," ta ƙarasa zancen zucin nata tare da sake ɗagowa a hankali don ta saci kallonshi,adai dai lokacin shima ya ƙara ɗagowa da kyawawan idanuwanshi kai tsaye suka shiga cikin nata,nan take taji gabanta ya kuma faɗuwa rass,kasa janye idanuwanshi yayi daga kallonta da yake yi,a yayin da yake jujjuya spoon ɗin dake hannunsa acikin plate ɗin abincin gabansa,har Yanzu bai daina mamakin kasantuwarta ƴar uwarshi ba,ta jininsa,tamkar a mafarki haka yake ganin abun,ganin ta zuba mashi ido batare da ta janyesu ba yasa shi ɗaure fuskarshi yasha murrr,saboda kada ma yarinya taga fuska har tayi tunanin raina sa don tasamu matsayi,

   "U will still remain who u are,wadda take aiki a ƙarƙashina,Matsayin dana baki kenan,"ya fada a ransa

  Murmushi Abusufyan yayi tare da cewa"bazasu kara wahala ba,bazan ta6a bari hakan ya faru ba,tunda dae har yaran nan suka bayyana a matsayin ƴa'ƴana,In sha Allah bazan ƙara bari suyi aikin wahala ba,ko cokali bazan ƙara bari ɗaya daga cikinsu ta ɗauko ba acikin gidan nan,rayuwar hutu kawai nake so suyi rayuwar ƴanci," ya ƙarasa zancen zucin nashi a yayin da yake bin kowaccen su da kallo cike da so da ƙaunar ƴa'ƴan nashi,'

  Janye idanunshi yayi daga kan nata,kafin ya miƙa hannu tare da ɗaukar Glass cup mai ɗauke da abun sha me sanyi ya kai shi saitin mouth dinsa yana sipping ɗinshi anatse,yayin da sanyin lemun ke ratsa throat ɗinsa,a hankali ya lumshe idanunsa tare da ɗan ware su kaɗan,again suka ƙara sauka akan na sehrish a karo na uku kenan,agaggauce tayi hanzarin janye idanunta daga kan fuskarshi ta mayar dasu akan plate ɗin abincin dake a gabanta,



Hannu Sgr ya sanya tare da yago tissue ya goge bakinsa,kafin ya miƙe tare da juyawa ya nufi upstairs,Miƙewa Marshal yayi da alama shima ya kammala breakfast Ɗin nasa,shima upstairs ya nufa,


Fitowar Hajiya azeema keda wuya daga cikin bedroon ɗinta,ta jiyo muryar gwaggon katsina tana ta faman sambatu tana cewa"Tsiyarta kenan mutun yazo gidan ƴan gayu,Ni bazan iya rayuwar turawan nan ba,taya za akai ma mutun salalar biredi tare da tea rabin kofi kamar wata ƴar iska ace in sha"?

  Tafiya take tana sambatu  zaninta a hannu sai ɗan undi ajikinta,kanta kuwa ta kifa wannan ɗaurin ɗan kwalin nata mai kama da helmert,

  har zata gifta hajiya azeema tayi gyaran murya tare da ambaton sunanta"Goggo," fuska a yamutse ta juyo tana kallonta,dawowa tayi daga gefenta suna fuskantar juna tace"Yawwa azeema,wai nikam inaso in tambayeki,'

Natsuwa hajiya azeema tayi tare da cewa"ina sauraronki gwaggo,"

  "Jiya nayi wani mafarki,ƴa'ƴan abusufyan sun bayyana,wasu ƴan uku kyawawan gaske,da nayi tunanin koda gaske ne abun ya faru amma daga baya na gane ba gaskiya bane,in ba haka ba,yaushe abusufyan ya ta6a yin aure"? Tayi tambayar tana kallon hajiya azeema,wadda ta saki baki tana kallon gwaggon,

  Ganin azeema tayi sototo tana kallonta yasa tayi tunanin cewa ko abunda ta faɗa ya bata mata rai ne,

  "Nasan dole kiyi mamaki kema,Mafarkin fa kamar dagaske,ɗaya daga cikinsu har tana sharara mana labarin ƙarya waisu ƴa'ƴan wata zainabu ne,kuma ma acikin labarin hada wata hajiya Ameena,in banda shaiɗan ina abusufyan ina ƴa'ƴa"?

  Ƙiris ya rage Azeema ta fashe da dariya agaban gwaggon katsina,ganin yadda ta haƙiƙance tana kora mata bayani,kuma babu alamun wasa a fuskarta,

Ƙunshe dariyar bakinta tayi tare da basar da ita tace"Gwaggo Anya kina shan maganinki kuwa?ina Dr harris yake?gaskiya inason ganinshi,'

  Tsoki gwaggon katsina taja tare da cewa"Harrisun daya zama ɗan iska,"

Waro ido waje azeema tayi tace"gwaggo harris ne ɗan iska"?

  ta6e baki tayi tare da cewa"Zan masa ƙarya ne?ba ɗan cikina bane"?nasha wahalar yima yarona tarbiya amma waccen sauden.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya ciyota,zanin hannunta takai saitin idonta tana ƙoƙarin goge hawayenta,

  Zuru harris yayi wanda fitowarshi kenan kuma atare da saude suka fito,jin maganar gwaggone ma yasa yayi hanzarin cire hannunshi daga cikin na sauden,

  Hajiya azeema tace"gwaggo faɗamun me harris ɗin ya akaita,?

  Hankali tashe Saude tace"ya harris pls kada ka bari gwaggo ta faɗa mata abunda muka aikata,kasan gwaggo yadda take ɗaukaka abu,inta tashi faɗi saita ƙara ma miya gishiri,'

  Dr harris yace"just don't worry ur self,insha Allah bazata faɗa mata ba,"

Faɗin hakan keda wuya gwaggon Katsina tace"Azeema abun da ciwo,yanzu yunwa nake ji,shiyasa ma kika ga nafito ina sambatu,Wurin waccen matar zani,wlh ba azmee ba Allah yasa ramadan ce ita yau saina zazzaga mata rashin mutunci!Ni zata raina ma hankali tunda safe,takawo mun tea rabin kofi da salalar biredi wai in fara da wannan,don ta raina mun hankali,nayi mata kama da kusu ne?

  Rai a6ace tayi maganar,aikuwa atare haris da saude suka fashe da dariya,a hanzarce ta juyo sakamakon jin sautin dariyar tasu,nan take ta tsuke fuska ganin shi tare da saude,

  Murmushi Hajiya azeema tayi tare da cewa"haba gwaggo baki fahimce ta bane,cewa fa tayi ki fara da wannan tana nufin kafin ki tashi fitowa zuwa yin breakfast ɗin,yanzu haka yana can an shirya mana mu kawai ake jira muje muci namu kalacin,"

  Hajiya azeema ta ƙarasa maganar tare da ruƙo zanin hannun gwaggon tace"Bari na taimaka maki ki ɗaura shi,"

  Girgiza kai tayi tare da cewa"Barmin shi a hannuna,nafison inji iska na shiga ta ko'ina,"murmushi hajiya azeema tayi kafin tace"hakan ma yayi gwaggo,ae under skirt din ma bamai sharashara bane,yana da kauri,amma duk da haka dae ki ɗaura zanin yadda zaki fito da kyau tunda ga rigarshi kin sanya ajikinki,Kuma kinga Abusufyan na nan,Ga kuma ƴa'ƴansa,bazasu so suga gwaggonsu a haka ba,"

  wani irin ƙayataccen murmushi gwaggon katsina tasaki tare da cewa"Kenan dagaske ne Mafarkin da nayi jiya"?

  Jinjina kai Azeema tayi tace"Ae suna nan,duk abunda ya faru jiya dagaske ne,ba mafarki kikayi ba,agabanki akayi komai kin dai shafa'a ne,'

  Jin haka yasa tayi saurin mayar da zanin ajikinta tana ɗaure shi tana cewa"Allah sarki ƴa'ƴan abusufyan ɗina,bayin Allah,sunsha wahala a hannun wannan fasiƙin mutumin baƙin shaiɗani,Allah mutumin nan ƙaho ne kawai bai fito masa aka ba,amma ina tantama anya ba Irin shaiɗan bane"? 

   "gwaggo kidaina maganarsa ma,Ni wlh ko zancen shi ma bana so anayi,Na tsani mutumin nan kamar yadda natsani mutuwa ta,"acewar hajiya azeema,tayi maganar ne a yayin da take kama hanyar Zuwa Dining area ɗin nasu,bin bayanta Gwaggon tayi tana cewa"Ae ko sai dai ki toshe kunnanki,don zancen sayyadi ya zama dole,in har ba'a kawo min kansa ba,bazan daina faɗan sunan shi ba,'

  Murmushi kawai hajiya azeema tayi,atare suka ƙarasa dining area din,

   Gaggaisawa suka fara yi da junansu,su jahad na ganin saude suka tashi atare suka nufe ta,dama Jiya basu samu damar gaisawa da ita ba,saboda yanayin da suka shiga gaba ɗayansu,haɗasu tayi ta rungume ajikinta,cike da farin ciki tace"Ina tayaku murna sosai,nayi farin ciki sosai,Ya harris ya sanar dani komai agame daku,ashe ku jininsu ne,'ta ƙarasa maganar ayayin da take raba jikinta daga nasu,kowannansu fuskarshi ɗauke da murmushi,Jahad tace"Aunty saude kinga ikon Allah ko?munsha wahala sosai,mu kanmu bamu ta6a tunanin cewa muna da dangi ba,amma sai gashi ƙaddara ta haɗamu da ya Omar,Ita kuma ƴar uwarmu Sehrish ƙaddarar aikine ya kawota gidan nan,Muna tare da ƴan uwanmu ba tare da mun sani ba,sae gashi rana ɗaya Allah ya bayyana mana komai,'

  Saude tace"Congratulations Once again,ina ƙara tayaku murna sosai da kuka fito daga tsatson wannan Family ɗin,abun alfahari ne wannan"kafin ta mayar da idanunta kan Hosana,Cike da zolaya taja kumatunta tare da cewa"Hosana Kinga yadda kika canza?kamar ba wannan Sha takwas sha taran ba,mai ɗan kai,kinyi kumatu kamar Balon balon,Ga haske gaskiya ya Omar ya Iya raino,"

  Fashewa da dariya hosana tayi tana faman sunnar dakai,

 "Kiyi ma sister ɗinku mana,Ita bazata taso mu gaisa ba"?tayi maganar tana kallon sehrish dake zaune,tana faman kallonsu ɗaya bayan ɗaya,

  Murmushi jahad tayi tare da juyawa tayi mata alamar ta taso da hannunta,

  Miƙewa sehrish tayi tare da nufar inda suke,koda ta ƙaraso saude ta sanya hannu tare da janyota ta rungumeta,kafin ta raba jikinta dana sehrish tace"Masha Allah,gaskiya ban ta6a ganin triplet,masu kama iri ɗaya sak kamar taku ba,ina taya ki murna sosai da Allah ya haɗaki da ƴan uwanki,da kuma mahaifinku,da kuma danginku,'

  Fuskar sehrish ɗauke da murmushi tace"Ngde sosai,"

 "Allah ya tsare mana ku,Ya Albarkaci rayuwarku ya kuma kare ku daga sharrin maƙiya,'

  Atare suka amsa mata da Ameen,bama su kadae ba,hadasu Abba dake sauraron maganganun nasu,


Kamar yadda Abba yayi alƙawarin shirya gagarumar walima na bayyanar ƴa'ƴan ƙaninsa Abusufyan,Da kanshi ya fidda date ɗin da za'a gabatar da ita,Kuma tun aranar ya fara kiran Ƴan uwa da abokanan arziƙi yana sanar dasu game da ƴa'ƴan abusufyan da suka bayyana,Babu wanda bai bari ba,kowa kira yake tun daga kan danginsu na Zaria,na damaturu dana sauran states ɗin da kuma waɗanda ke zaune Ƙasashen waje,kowa saidaya sanar mawa,Bayan Abbas ya koma gidane da safe Amani ke tambayarshi meya faru ne jiya ya hanasu zuwa gidansu,Anan ya kwashe duka abunda ya faru game da su Sehrish ya sanar mata,wani irin farin ciki ne ya cika ta,Ba don komai ba sai don sanin cewa plan ɗin Aunty babba ya gama Tarwatsewa,ae tunda taji cewar ƴan mata ne kuma sun kai shekara goma sha bakwai zuwa sha takwas kyawawan gaske,Nan fa ta kwashe da dariyar mugunta aranta tana cewa Naga yadda za'ae Aunty laila ta cimma burinta,Gida bai ƙoshi ba taya za'a ba na waje,Ae tuwona maina za'ayi,Haba ae xance ya ƙare,

   ita kanta Amani ta ƙosa ranar walimar tazo saboda suje gidan,saboda taji cewar Aranar Aunty babba da hafsat zasu zo Abuja,babban burinta taga tashin hankalin da aunty babba zata fuskanta inta gansu,


Ranar walimar kuma yayi dai dai da ranar da Ammi zata zo,tare da wasu daga cikin danginsu,haka zalika captain Najeeb da kuma Talal suma duk a ranar zasu dawo gida,ba don komai ba sai don su sanya ƴa'ƴan uncle ɗinsu abusufyan acikin idanunsu,Kowa ɗokin ganinsu yake yi kamar kamar me,musamman da sukaji irin rayuwar da yaran sukayi a wulaƙance sai suji wani irin tausayinsu da kuma ƙaunarsu ya shiga cikin ransu,kuma duk aranar MG Osman da kuma Captain Adam suma zasu dawo gida,wanda tun dawowarsu daga U.s suka tafi sada zumunci,Gaskiya wannan Babbar rana ce,Hakan yasa ma Zamuyi shiri na musamman ni da makaranta littafina don mu halarci gidan amatsayin gayyar soɗi tunda ba'a gayyace mu ba,Sa kaine kawai,


Cikin ƴan kwanakin nan wata irin rayuwar farin ciki suke gudanarwa tare da Daddynsu,kullum yana manne dasu,Da kanshi ya zauna yayi masu kitson kalaba guda bibbiyu akansu kamar yadda ya ta6a yi masu suna yara,koda yazo kan Sehrish,Cike da mamaki yace"Ya akai naga gashin kanki guntu?ko kinyi wani ciwo ne dayasa aka datse maki gashin,"girgixa kai tayi tare da cewa"a'a Laifi nayi ma Babba yaya shine ya yanke mun gashin da almakashi,"

 da buɗar bakin Abusufyan sai cewa yayi"Yayiwa kanshi ai," murmushi sehrish tayi duk da batasan me daddyn nasu yake nufi da hakan ba,duk a wannan kwanakin basu je school ba,Abusufyan da kanshi yace kada su damu shi da kanshi zai kaisu makarantar don karma a tuhume su,


A 6angaren Sir Commander haroon kuwa,tamkar munafuki haka ya koma acikin gidan,ba kowa ma ke sanin lokacin da yake shigowa gidan ba,da kuma lokacin da yake fita,Da alama dae akwai wani abu da yake shiryawa a 6oye,


*AMRISH*


Zaune take acikin class ɗin gaba daya ta shiga damuwar rashin ganin Sehrish kwana biyu ko layinta ta kira bata samu,hatta wayar junaid ta jaraba kira shima ba'a ɗagawa,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,tagumi tayi idonta cike tab da hawaye saboda damuwar da take ciki,taso ace sehrish na nan atlease zata ɗebe mata kewa,tana cikin wannan tunanin har malam ya shigo cikin class ɗin nasu bata sani ba,bayan ya kammala amsar gaisuwa daga wurin student din,kai tsaye ya ƙarasa seat ɗin da Amrish take,hannun shi yakai wanda ke ruƙe da maker ya ɗan bubbugi desk ɗinta,a firgice takai idanunta akanshi,Yunƙurawa tayi tare da miƙewa ganin Ya mu'allim,wanda tun ranar daya ba sehrish Ruwan addu'ar nan bai ƙara zuwa makarantar ba,duk da sun samu labarin cewar Ya tafi Umra ne,shiyasa aka musanya masu shi,

  Murmushi ya ɗan saki afuskarshi yana kallonta yace"tunanin me kike yi ne?har na shigo cikin class ɗin baki sani ba?

  Muryarta na rawa tace"Ayimun afwa ya mu'allim,Bana jin daɗi ne bansan ka shigo ba,

  Jinjina kanshi yayi tare da ɗan kai idanunshi kan Seat ɗin sehrish yace"Ina yarinyar nan take?ƴar family ɗin Salahuddeeen hussein naga kamar bata a class ɗin"?

  fuskarta ɗauke da damuwa tace"Batazo ba,yau kusan kwana huɗu kenan bata zo school ba,kuma nayi trying kiran layinta amma bana samu,har brother ɗinta na kira,shima layinsa ba'a samu,'

    Jin hakan yasa shi fargabar to kodai wani abu ya faru da yarinyar?Yaso yaji ya tayi da ruwan addu'ar daya bata,shin tasha ko bata sha ba?

  Jinjina kanshi yayi tare da juyawa yace"Allah yasa dae lafiya,in har batazo ba,zuwa sati mai zuwa zan je gidansu don na binciki dalilin rashin zuwan nata,'

  Jiki asanyaye Amrish ta koma ta zauna,saman seat ɗin nata,jikinta har ya fara kerma saboda tsoran kar ace wani abune ya faru da Sehrish,

  A ƙarshe dae ta yanke shawarar neman gidansu don taje ta ganta da kanta.



  *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃



*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI.  MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*



*LOCATION KANO*


08062073990

Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku



Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku


It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.

Snack

Awarah 

Farah

Zobo

Samosa

Cup cake etc 

Contact me 09063302182or 09012179727.


   



  

  

  

  



    

 

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



_Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata  zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari sannan a kula wannan itace numbar wayata,Wasu suna ɗaukar numbar Wanda suka bani tallarsu kayansu suna kiransu a matsayin ni,bayan ni ga numbar dana bada nan itace numberta_


*Nagode sosai da addu'o'inku agare ni,da kuma uzurin da kukayimun,har zuwa wannan lokacin,Allah yabar zumunci a tsakaninmu daga nan har gidan aljanna💃*



*nace ba Masu satar littafi suna fitarwa ta bayan fage,mai yasa baku ƙarasa masu labarin ba?kuma kenan saida kuka jira ni?ae nayi tunanin cewa zaku ƙarasa masu labarin ne ashe dai sai anjira Boss*😂🤣😅



Bismillah





❤🤍❤



A hankali ya tura ƙopar bedroom ɗinsa tare da shigewa ciki,turus yayi ya tsaya yana kallon junaid dake manne da Mommynsu suna bacci yadda kasan wani jinjiri ya ƙanƙame ta sae faman sharar bacci suke yi atare,murmushi ya ɗan saki tare da wuce wa cikin bedroom ɗin,Rage kayan jikinshi yayi bayan ya kammala ya shige cikin toilet,Within 15mins yayi wanka,sae gashi ya fito ɗaure da towel,tsaf ya kammala gyara jikinshi agaban dressing mirror,kafin ya koma wurin Closet ɗinshi,ya ɗauko wasu lallausan kayan bacci riga da wando farare ya zura ajikinshi,bayan ya kammala shirin kwanciya,ya zagaya ta baya dai dai saitin da junaid yake manne da mommyntasu ya lalla6a tare da hayewa saman gadon,zuba mata ido yayi yana kallonta,kullum koma mashi takeyi tamkar sabuwar amarya,ji yake kamar ma ba'ajima da yin aurensu ba,saboda tsabar son da yake yi mata,ba ƙaramin kewar matar shi yayi ba,har yanzu bai kammala hucewa ba,tunda tadawo kullum da daddare suna manne da juna,a kwanakin nan ba ƙaramin kwanciyar hankali ya samu ba,ya zama cikakken mutun don rashin Alexandra ba ƙaramin gibi yayi mashi ba,kasa janye idanunshi yayi daga kallonta da yake yi,tayi wani irin haske mai kyan gaske,fatarta kamar ta jinjiri saboda tsabar sheƙin da takeyi da daukar ido,bin dogon gashin kanta yayi da kallo wanda ya baje agadon bayanta,a hankali ya mayar da idanunshi akan farar half vest ɗin dake ajikinta,nan take ya fara shiga yanayi na buƙatarta,ga kuma junaid ya riga shi,to ya kenan?

  ƙasa ƙasa yayi da muryarshi dai dai saitin kunnan Junaid ya ambaci sunan shi a hankali"Junaid!junaid!tashi ka koma bedroom ɗinka,"yayi hakan ne saboda baison ya tashe ta,yasan inta farka ba lallai tabari ya rabata da junaid ba,jin shiru junaid bai motsa ba yasa shi ƙara ɗan ɗaga muryarshi yace"junaid!junaid!pls get up and go back to ur bedroom,inaso in kwanta ne!"

  Shiru junaid ba alamun ma zai farka,hannu yasa tare da ɗan bubbuga kafaɗarshi yace"Junaid!junaid!Ka tashi mana!!"

  Duk wannan suratan da Abbansu keyi kaf a kunnan junaid,sarai yana jinshi yayi banza dashi,tun kiran farko da yayi mashi ya farka,koda yaji Abbansu na cewa ya tashi ya koma bedroom ɗinshi zai kwanta,sai ya ƙara ƙanƙame mommyn tasu,don yaci alwashin cewa yau fa abbansu bazai kwana tare da mommynsu ba,ba don komai ba sae don shi aganinshi Abbansu baiyi mashi adalci ba,don me zai dinga kwana tare da Mommynsu bayan shi ne ya dace su dinga kwana tare da ita,Saboda tafiyar da tayi ta barshi tun yana jinjiri,yanzu lokacin shi ne bana abbansu ba,dole ya haƙura yabar mashi,Tashin hankalin da ba'a sama shi date!

  "Junaid!nafa son cewa kana ji na,kayi banza ka ƙyale ni!zaka tashi ko saina yi wurgi dakai,"a faɗace Abban nasu yayi maganar yana kallonshi,

  turo baki junaid yayi cikin ƙunƙuni yace"Abba,wlh ba inda zani!yau kwana na ne,"

  Har saida gaban Abbansu ya faɗi rass saboda yadda maganar ta junaid ta dirar mashi a kunnanshi,Cike da mamaki ya maimaita maganar "yau kwanana ne!"!

  Junaid dake maƙale da Mommynsu yace"eh,abba kadaina ma wahalar da kanka,Allah yau ba inda zani,kullum sai kayimun wayau,kana kwana tare da mommy,fisabilillahi Ni da kai waye ya dace ace yana kwana tare da Mommy!!!?

  Saboda tsabar takaici sam abbansu ya rasa me zaiyi ma junaid,gashi babu mabugi a kusa balle ya kwaɗe shi,ko ya samu sanyi aranshi,

  Ganin junaid ya turje bilhaƙƙi dagaske yake bazai tashi ba,gashi kuma Alexandra tafara mutsu mutsu alamun suna takura mata,kuma baiso ta farka daga baccin saboda gudun karta hanashi kora junaid izuwa bedroom ɗinshi,hakan yasa ya yanke shawarar binshi ta lalama,

  Sassauta muryarshi yayi tare da cewa"Pls babyn abbansa,abeg dan Allah ka tashi ka koma bedroom ɗinka,help ur dad pls,bakasan halin da nake ciki ba,pls junaid ɗin Abbansa,"

  Ƙara ƙanƙame Mommynsu yayi tare da cewa"wlh Abba dama kadaina yi mun magiyar nan,ni yau tare da mommyna zan kwana,"

  Muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"to ni a ina kakeso na kwana?junaid baka tausayin Abbanka ko?meyasa zakayi mun haka?yau kuma rigimar akaina zata ƙare"?

  ashagwa6e junaid yace"Abba,gaskiya kayi haƙuri nidai babu inda zani,kaje bedroom ɗina ka kwana mana,'yayi maganar tare da ƙara shigewa jikin Mommyn tasu,

  Rai a6ace Abba yace"Don ubanka zaka tashi ko bazaka tashi ba!!"?

  shiru yayi bai tanka mashi ba,sae ma minsharin ƙaryar da ya dinga ja,don abban nasu yasan cewa bacci ya ɗauke shi,

  A daddafe Abbansu ya miƙe daga zaunen da yake gefen gadon,ranshi duk a jagule kamar ya aza hannu aka ya fasa ihu haka yake ji,shi kaɗae yasan halin da yake ciki,bai ta6a sanin cewa junaid bai da wayau ba sae yau,duk yasa ya zama abun ban tausayi,hawaye ne kawai bai zubar ba,amma ba ƙaramin 6ata mashi rai yayi ba,ya jima yana zagaye a cikin bedroom ɗin,yana kallonshi,a ƙarshe ya nufi ƙopar bedroom ɗin tare da buɗewa ya fuce waje,

   "Gobe ma anan zan kwana,"junaid ne yayi maganar bayan jin fitar abban nasu daga ɗakin,


"Daughter"! ƙiris ya rage ta saki tray ɗin dake hannunta,don bata tsammaci jin muryar mutun a bayanta ba,bakowa bace wannan face Sehrish wadda ke tsaye a cikin kitchen tana shiryama Sgr fresh fruits tare da coffee,jikinta na sanye da doguwar riga ta bacci mara nauyi milk colour tayi rolling mayafi akanta launin baƙi,

Ganin daddynsu yasa ta sakin murmushi tare da cewa"daddy,dama idonka biyu bakayi bacci ba har wannan lokacin"?

  ƙarasa shiga kitchen ɗin yayi yana cewa"taya zan iya baccin?bayan ɗaya daga cikin ƴa'ƴana idonta biyu bata runtsa ba,raina ne ya bani cewar akwai wadda batayi bacci ba acikinku shiyasa na fito don inga wacece ashe kece...."

fashewa da dariya sehrish tayi jin abunda yace,shima dariyar ce ɗauke a fuskarshi,

..tsayawa yayi dab da ita yana kallon kayan marmarin da ta kammala Jera ma sgr,ta gyare tsaf ta yayyanka mashi su,

  "Yanzu wannan kayan daɗin duk na wanene?ko ke zaki sha"?yayi tambayar a yayin da yakai hannunshi cikin ƙayataccen tray din wanda ke ɗauke da plate na kayan marmarin ya ɗauki yankin abarba ɗaya tare da turata abakinsa yana sha,

  "Bani zan sha ba,na babban yaya ne,"tunkan ta ƙarasa maganar taga ya dakata da taunar abarbar da yake yi yana kallonta fuskar shi ɗauke da mamaki yace"Kina nufin Rafayet kika shiryama wannan?shiya sanyaki ne"?

  Jinjina kai tayi tare da cewa"eh daddy,shine ya buƙaci na dinga kai mashi fruit tare da coffee adai dai irin wannan lokacin ƙarfe sha biyu na dare in sun dawo daga aiki....'daƙyar ta ƙarasa maganar ganin yadda fuskarshi ta canza,alamar wani abu baiyi mashi daɗi ba,

  "Daddy wani abu"?ta furta hakan tana kallonshi,

  shiru yayi jimmm kamar mai nazarin wani abu,kafin daga bisani yace"da sanin Abbanku"?

  girgiza kai tayi alamar a'a sannan ta ƙara da cewa"yasan cewa inayi mashi aiki daddy,amma banda tabbacin cewar ko yana da masaniya akan hakan,bansani ba ko babban yayanmu ya sanar dashi,'

  ta6e baki Uncle abusufyan yayi kafin yace"Abba bazai ta6a bari ba,bana tunanin cewar ya sani,taya mace kamarki zata dinga zuwa ɗakin namiji a irin wannan lokacin!!?

  Gabanta ne taji ya faɗi rass,sunnar da kanta tayi tana wasa da yatsun hannnunta,

  "That's imposssible!!!Banaso gaskiya hakan bai kwantamin araina ba,duk da ɗan uwanki ne shi a yanzu,amma hakan bai dace ace kina zuwa ɗakinshi ba a irin wannan lokacin,in fact ba'a son mace da namiji suna ke6ewa,nasan kinsan da wannan!"

  Muryarta na kerma tace"Hakane daddy,

  Jinjina kanshi yayi tare da cewa"Yawwa,ɗauki kayan marmarin ki kai masa,kada ki makara,"

  Hannunta na kerma ta ɗauki tray din da sauri da sauri ta nufi hanyar fita daga kitchen ɗin,har ta kusa fita daga cikinsa,muryarshi ta dakatar da ita,

  "Sehrish,"

"Na'am daddy,"ta amsa mashi tare da ɗan juyawa ta baya tana kallonshi,

  "daga yau!banaso ki ƙara zuwa don kiyi mashi aiki,koda da safe ne ko da rana,Azmee itace mai aikin gidan nan,idan ma da buƙatar masu aikin zansa a ƙaro wasu,amma ba zakuyi aiki wa kowa ba,ina fata kin fahimce ni,'

  Tunda abusufyan ya fara maganar gabanta ya shiga faɗuwa,hankalinta yayi mugun tashi,tuni idanunta sun fara canza launi,

  Fuskarta ɗauke da damuwa tace"daddy,inajin tsoran shi sosai,bansan taya zan sanar dashi hakan ba,'

  Murmushi Abusufyan yayi tare da takawa kusa da ita suna fuskantar juna yace"Bance ki sanar mashi ba,kawai inaso daga yau ki ɗan ɗaga ƙafa daga zuwa part ɗinsa don kai mashi abinci ko yi masa gyara,nasan cewa bazai damu da hakan ba,tunda ga azmee,in ma yayi magana akan hakan ki sanar dashi cewa"NI NA HANAKI!"

  wani irin wahalallen yawu Sehrish ta haɗiye a bakinta,sam bazata iya yima daddyn nasu gardama ba,tasan cewa yayi hakan ne saboda tausayinsu da yake ji,baison suna aikin wahala,amma wannan hukuncin da ya yanke mata ba ƙaramin horo bane agareta,Na farko hakan zai nisanta tsakaninta da SGR,ganinshi zaiyi mata ƙaranci,in har ba downstair ya sauko ba,Allah ya haɗasu to bafa zata samu damar ganinshi ba,Abu na biyu kuma hayaam zata samu damar shige masa,don tasan cewar daga ta daina yin aiki a ƙarƙashinsa,hayaam zata kunno kai,na uku kuma batasan me zai biyo baya ba,in har yasan cewar ta daina yi mashi aiki,Shin zai damu ko bazai damu ba.....'

  "Zaki iya tafiya,kada ki jima a bedroom ɗin nashi,dare yana ƙara yi,da zarar kin kai mashi,kiyi hanzarin komawa cikin ƴan uwanki ki kwanta kiyi bacci ki huta,

  "Toh Abba,zanyi duk yadda kace,"

Murmushi abusufyan ya saki tare da cewa"ki kulamin da kanki daughter,sai da safe,"

murmushin tayi itama bayan ta amsa mashi,batare da 6ata lokaci ba,ta wuce sashen Sgr,kamar wadda aka zare ma lakar jikinta haka take tafiya,ba don komai ba sai don Hukuncin da Daddy ɗinsu ya yanke,Taya zata iya rayuwa batare da tana sanya babban yaya acikin idanunta ba akai akai!anya kuwa zata iya jurewa?wa zai kula mata dashi kamar yadda take kula dashi?tashin hankalin da ba'a sama shi date,


Wani irin farin cikine ya lullu6e hayaam dake la6e wurin kitchen ɗin tana sauraron abunda Uncle abusufyan ya tattauna tare da sehrish,kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha don tsabar farin ciki,ashe munafukar tana la6e ta kasa kunne tana sauraronsu,bakomai ya fito da ita ba daga ɗakinta face yunwar da taciyota,hakan yasa ta lalla6a ta fito don ta sama ma kanta abunda zata ci,anan ne fa tajiyo muryoyinsu suna magana acikin kitchen ɗin,shine tayi masu la6e,ta kwashe duk abunda suka tattauna acikin kunnanta,Lokaci guda ta manta ma da yunwar da take ji acikin cikinta,gudu gudu sauri sauri ta koma bedroom ɗinta,faɗawa tayi saman gadonta tana faman tiƙar dariya,bayan ta tsagaita da yin dariyar tashiga tufka da warwara acikin zuciyarta,

  "Idan har inaso in samu nasarar cigaba da zama acikin gidan nan,dole saina haɗa kai da wani!wanda zai taimaka mun,wurin ganin na cimma burika na!tabbas ina bukatar shi,"ta ambaci hakan ayayin da take ƙoƙarin miƙewa daga zaune,

  *WANENE SHI*!? 


*Surgeon General Rafayet*


A ƙopar shiga bedroom ɗinshi ta tsaya,zuciyarta duk a ƙuntace take,don idanunta acike suke tab da hawaye ba don komai ba sai don hukuncin da daddynsu ya yanke agame da zuwanta part ɗin SGR,yanzu shikenan Yau zata kasance rana ta ƙarshe da zatayi aiki a sashen shi?shikenan bazata ƙara takowa ba da sunan ta kula dashi ba? 😥


Tamkar ta fashe da kuka haka ta dinga ji,dakyar ta daure ta cije tare da zuba sallama,shiru ba'a amsa mata ba hakan yasa ta ƙara daga muryarta,ta kuma zabga sallamar akaro na biyu,shima shiru bai amsa mata ba,hakan yasa ta fara tunanin cewa kodai yayi bacci ne ko kuma yana acikin toilet,don tasan shi akwai yin wankan dare duk in xai kwanta,


Tunani tayi ai shi muharraminta ne a yanzu hakan yasa ta kutsa kai tare da shigewa cikin bedroom ɗin nasa,wani irin daddaɗan kamshi ne ya daki hancinta,mai daɗin gaske,ga ratsa zuciya,lumshe idanunta tayi a hankali tare da sake buɗesu,tana ƙare ma shimfiɗeɗen gadon nashi kallo,kasa janye idanunta tayi daga kallon shi da takeyi,Yana a kwance saman gadon,yayi covering jikinshi da lallausan blanket ɗinsa,dai dai saitin stomach ɗinsa bargon ya tsaya,sumar kanshi ta rufe mashi fuskarshi da alama dae a gajiye suka dawo yau,baccin ma kamar bai shirya mashi ba ya ɗauke shi,duba da yadda yayi kwanciyar,right hand ɗinshi na asaman kanshi ya zagayo dashi ta dayan 6angaren,


A hankali sehrish ke nufar gadon nasa tana tafiya kamar wadda kwai ya fashe mawa akai,saboda rashin kwarin jikinta,ajiye mashi tray din tayi asaman side table ɗinsa,sannan tashiga tunanin,kodai ta tashe shi daga baccin kota ƙyale shi?ta jima tana nazari kafin zuciyarta ta bata shawarar cewa ta tashe shi kawai,ganin cewa ba kayan bacci ne ajikinsa ba,hakan na nufin baiyi night bath ɗin daya saba yi ba,tabbas bazaiji daɗin baccin shi ba,

  Zuba mashi ido tayi tana ƙare mashi kallo,anan taga zufa na tsattsafowa a saman dogon hancinsa,da kuma wuyansa,mamakine ya kamata,aranta tace"Zufa kuma?duk da sanyin A.c dake akwai?karfa ace babban yaya bashi da lafiya"?cike da damuwa tayi tambayar,can kuma tace"kodan baiyi wankan daren daya saba yi bane?zai iya yiyuwa hakane,amma fa ina tsoran tashin shi daga bacci,

  Bari dai kawai na haƙura kar in jama kaina,don na lura kwanan nan ɗaure mun fuska yake yi,kamar nayi masa wani laifi,'

Tana kai ƙarshen zancen zucin nata,tayi wani kwakkwaran juyi da nufin tabar wurin,cikin rashin sani tayi tuntu6e da doguwar ƙafarsa ɗaya data sauko ƙasan gadon,birkicewa tayi duk yadda taso ta ruƙe jikinta amma abun ya faskara,gaba ɗaya ta tafi ɗungurugum ta faɗa saman jikinshi,


Hankali a matuƙar tashe Sehrish ta zazzare idanunta tana kallon fuskarshi,gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,ganin ya fara motsa idanunshi yasa ta soma kiciniyar miƙewa daga saman jikinsa,sae dai kash bata samu wannan damar ba domin kuwa Sgr harya ware kyawawan idanuwanshi,biji-biji ya dinga ganinta acikin idanunshi,ita kuwa tuni jikinta ya shiga kerma,a hankali yakai hannunshi tare da ɗan Murza idanunshi,kafin ya ƙara ware su da kyau akanta,gaba ɗaya duk tabi ta rikice tuni zufa ta fara tsattsafo mata,ganin cewa dagaske dae ita yake kallo yasa ta ambaton nashiga uku,a hanzarce ta bar jikinshi ta sauka daga saman gadon,la66anta na rawa tace"dan Allah kayi haƙuri babban yaya,wlh ba yin kaina bane,na kawo maka fruits ne kuma banyi niyyar na tashe ka ba,tuntu6e nayi da ƙafarka na faɗo saman jikinka.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda wani irin kallo da taga yana jifarta da shi,sunnar da kai ƙasa tayi tana faman wasa da yatsun hannunta dake ta faman kerma,

  "Kneel down," ya furta da wata irin kasalalliyar murya ta wanda bacci bai ishe shi ba,

   cikin sauri Sehrish ta zube saman guiwowinta agaban gadon nashi,

"Ur Hands up and close ur eyes," yayi maganar yana yi mata nuni da hannunshi,

  Jiki na rawa ta ɗaga hannayenta sama tare da kulle idanunta,sosai ta rufe su,tana matsar kwalla, 

  "Kada kiyi attempting buɗe idanunki,ko sauke hannayenki if not kinsan mai zai biyo baya,'

  Muryarta na kerma tace"bazan buɗe ba,'

"Gud," ya furta hakan a yayin da yake cire blanket ɗin dake rufe da jikinsa,a hankali ya sauko daga saman gadon,tsayawa yayi yana rage kayan jikinsa,sae da ya rage daga shi sae short,sannan ya wuce cikin toilet ya rufe ƙopar,

   Saboda tsabar tsoro batama san cewa Sgr ya shiga toilet ba,sae faman shessheƙar kuka takeyi,after some minutes ya fito daga cikin toilet ɗin nasa,jikinshi sanye da bathrobe white colour,gaban dressing mirror ɗinshi ya zauna,ya shiga shafe jikinshi da mai,bayan ya kammala ya feshe ko'ina tass da tsadaddun tururrukan jikinshi,nan take ƙamshin ya gauraye ko'ina na cikin bedroom ɗin,ya jima agaban mirror ɗin kafin ya yunƙura tare da miƙewa ya nufi can cikin bedroom ɗin wurin Closet ɗinshi,

  Almost 30mins Sehrish tayi zuƙunne saman guiwowinta jikinta na kerma,

  dawowa yayi jikinshi sanye da nigh dress masu kyan gaske,

   Wuri ya samu ya zauna daga gefen gadon yana fuskantarta,a hankali ya miƙa hannunshi tare da buɗe side drawer ya ɗauko wannan hoton da Uncle ɗinsu Abusufyan ya ta6a basu lokacin da suna ƴan shekara sha a duniya,zuba ma hoton ido yayi yana ƙare mashi kallo,kafin ya ɗago da idanunshi ya azasu akan fuskar sehrish yana kallonta,da alama nazarin wani abu yake yi a fuskarta da kuma fuskar ƙaramar yarinyar dake acikin hoton hannunsa,so yake ya gano wacece yarinyar dake acikin hoton nan,ƴar ƙaramar yarinya wata zararriya da ita,gashin kanta duk ya tarwatse ya yamutse yayi datti babu gyara,kayan jikinta duk sun fita hayyacinsu sun yage,ga ƙafafunta ko takalma babu,fuskarta kuwa duk tayi jaga jaga da majina,hoton yayi confusing ɗinshi,kokwanto ya shiga yi anya itace a cikin hoton?kodai ɗaya daga cikin ƴan uwanta ne,

    "Open ur eyes,"

Jin muryarshi yasa tayi saurin buɗe idanunta wanda ke fitar da kwalla,muryarta na rawa tace"babban yaya dan Allah kayi haƙuri bazan ƙara ba,"tayi maganar tana faman shassheƙar kuka,

  Miƙa mata hoton hannunshi yayi tare da cewa"Who is she"?

  hannunta na kerma ta kar6i hoton daya miƙa mata,Ƙura ido tayi tana kallon hoton,nan take tashiga tambayar kanta ina Sgr ya samu hoton ɗaya daga cikinsu?ita kanta bazata iya tuna waya ɗauki hoton ba,kuma haka zalika bazata iya tantance wacece acikin hoton ba,saboda abun yayi confusing ɗinta,Kamar ita kamar kuma hossana,saboda gashin kan daya harmutse kamar na Mahaukaciya,tasan cewa hosana ce kawai keda irin wannan hargitsastsen gashin,

  "Ina sauraranki,"ya furta hakan a yayin da yakai hannunshi tare da ɗaukar cup of cofeen da takawo mashi,ya shiga kur6ar shi anatse,

  Cikin en ena tace"Wannan kamar hosana ce,bazan iya tantance wacece ba,'

  ɗaure fuskarshi yayi tare da cewa"Oh ba zaki iya tantance wacece acikin hoton ba?what does that mean"

  Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Inaji hosana ce,wannan itace gashin kanta yake a haka,"

  Hannu Sgr yasa tare da kar6e hoton ya ajiye shi a gefen shi,'

  Tsuru tsuru tayi da idanunta,cike da tsoran kar ace ta ƙara wani laifin,

  "I want u to tell me..,wannan bastard ɗin menene ma sunan shi?

  "Ya sayyadi," ta bashi amsa,

"akwai wasu mahimman bayanai da nakeso naji daga gare ki,hope zaki natsu kiban amsa," jinjina kai tayi tare da cewa"in sha Allah,"

  "Awani area kuka zauna a kano?"

"A hotoro ne" ta bashi amsa,

Jinjina kai yayi tare da ajiye cup ɗin dake hannunshi,then ya ɗauki banana yana 6areta a hankali yace"zaki iya tuna address ɗin gidanku kenan"?

  "Eh,"

"Okey,' ya ɗanyi shiru bayan yakai ayabar abakinsa ya ɗan gutsireta acikin bakinshi,kafin ya kuma cewa"a labarin da sister ɗinki ta bayar,ta faɗi cewa shi wannan mutumin ya ta6a nemanku,a cikinku akwai wadda ya ta6ayin raping"?

Daram!!!taji gabanta ya faɗi,girgiza kai tashiga yi muryarta har tana harɗewa wurin saurin cewa"babu...bai ta6a samun nasarar yin hakan ba,yadai ta6a yunkurin hakan,"


Shiru Sgr ya ɗanyi sae lokacin ya ɗan ɗago da idanunshi ya kalli fuskarta,gaba daya duk tabi ta rikice jikinta sae faman kerma yakeyi,yanayinta kuma kamar akwai wani abu data 6oye masa,

  "Tell me the truth!kinsan bana son ƙarya,even if u hide it to me i will find out soon,so its better ki sanar dani,before naji a wurin wani!!"

  Hawaye taji sun wanke mata fuskarta,ji take kamar ta tashi ta watsa da gudu,saboda ta tsani taji ana zancen Ya sayyadi,

  ɗagowa tayi da idanunta waɗanda suka rune suka canza launi,kai tsaye suka sauka acikin nashi,cikin shessheƙar kuka tace"bazan maka ƙarya ba,yaso yayi hakan amma Allah bai bashi dama ba,'

  "In har dagaske ne abunda kika faɗa,to meyasa kike kuka"?

  "Saboda banason ana mun maganar shi,hakan yana tunamin rayuwar da mukayi a baya,"

  kawar da idanunshi yayi daga kan fuskarta,sannan yace"Its okey,u can wipe ur tears,amma ba hakan yana nufin za'a daina maki maganar shi bane!dole ta hanyarku ne zamu samu dukkan bayanan da mukeso,before muci nasarar kama shi,'

  Hannu tasa tana share hawayenta tace"Allah ya bani ikon Amsawa,"

  "U can leave,"ya bata umarnin tafiya,

  Tashi tayi jikinta asanyaye ta juya tana nufar hanyar fita daga bedroom ɗin nashi,gaba ɗaya duk jikinta yayi mugun sanyi,wata irin kasala ta lullu6eta,har ta kusa fita daga bedroom ɗin nashi ta ɗan tsaya tare da juyowa a hankali don tayi ma ɗakinshi kallon karshe tunda daga yau bazata ƙara zuwa sashen shi ba,da sunan yi mashi aiki,


Juyowarta keda wuya,idanunta suka shiga acikin nashi,har saida gabanta ya faɗi,kasa tafiya tayi kallonshi kawai takeyi,a yayin da shima yake kallonta,

Kusan 8 mins sannan taji muryarshi acikin kunnanta yace"Lafiya"?

  girgiza kai tayi alamar ba komai,kafin tasa kai ta fuce daga bedroom ɗin nashi,


Saukowa downstair tayi,hawaye nata faman zarya a fuskarta,sai da ta goge tears ɗin sannan ta wuce  bedroom ɗinsu, a hankali ta tura door ɗin ɗakin ta shiga,Samun Jahad tayi zaune daga gefen gadon ta zabga tagumi,yayin da hosana ke ta faman sharar bacci,

  Bayan ta rufe masu ƙopar ɗakin ta koma daga gefen jahad ta zauna tare da ambaton sunanta"Jahad,"

  A razane ta ɗago tana kallon Sehrish,sam bataji shigowarta ba,

  "Mekike tunani ne"?

Murmushi jahad ta ɗanyi tare da cewa"Ashe kin fita,na farka ban ganki ba,acikin ɗakin,'

Sehrish tace"Naje part ɗin babban yayanmu ne,'

"Wannan mai blue eyes ɗin"? Jahad ta tambaya yayin da take kallonta,

"Eh,Sunan shi RAFAYET,amma suna kiranshi da BABBAN YAYA,"

  "Shine babbansu kenan"?acewar jahad,

  "A'a bashi bane babbansu gaba ɗaya ba,Akwai wanda suka girme shi sosai,Sunan ne ya dace dashi shiyasa suke kiranshi da haka,"

  Jahad tace"kamar bazaiyi sauƙin kai ba,na lura ko magana baisan yi,ni in inama kallonshi tsoro yake bani,araina har cewa nake yi wai shima nan ɗan uwanmu ne,ƙwayar idonshi daban koda yake ga Ayaan nan shima idanunshi ash ne,mommynsu ma nata kalar na babban yaya ne,amma Mommynsu fa kamar bata son ganinmu nake gani ko kin lura da haka"?

  Sehrish tace"eh hakane,amma kada kisa ma ranki wannan,idan kika lura abun kamar a jininsu yake ita da babban yaya,in ka biye ta yanayinsu toh bazakayi rayuwa asake ba,duk zaka takure kanka ne,kayi tunanin cewa kamar sun tsani mutane basa son ganinsu bayan ba haka bane,kawai basu cika son magana ba,ko kallon mutane basa son yi,'

  Cike da mamaki jahad tace"tofa su kuma haka suke?shiyasa junaid shima baison ganina,har yau fa junaid ko son haɗa ido baiyi dani,in kuwa muka haɗa ido dashi har hararata yake yi ya kuma murguɗa mun baki,Wlh bana jin daɗin abunda yake yi mun,sai inga kamar ya tsane ni ne,abun ba ƙaramin damuna yake yi ba,gashi inason nasamu kusanci sosai dashi,kamar yadda naga kuna shiri a tsakaninki dashi,bansan meyasa ni yake mun haka ba,'

  Tayi maganar fuskarta ɗauke da damuwa,

  Sehrish tace"kai junaid ɗin keyi maki hakan?to ae duk gidan nan babu kamar shi,indai wurin son mutane ne,yafi kowa faran faran da mutane kullum cikin fara'a yake,Junaid fa ko yau kuka fara haɗuwa dashi zai nuna tamkar kun ta6a haɗuwa a baya,kuma yadda zai saki jiki da mutun zaisa kayi tunanin kamar kun share shekaru kuna atare,"

  Sosai Sehrish ta shiga kora mata bayani agame da junaid,

  Abun ba ƙaramin ɗaure ma jahad kai yayi ba,cike da mamaki tace"To Amma meyasa ni yake mun haka"?

  Murmushi sehrish tayi tare da cewa"dole akwai dalili,amma ki barni dashi in sha Allah zan tambaye shi inji,"

  gyaɗa kai jahad tayi tare da cewa"Shikenan,dan Allah duk yadda kikayi dashi ki sanar mun,"

  sun jima suna fira atsakaninsu kafin bacci yayi awon gaba dasu,ƴan ukun Abusufyan,


Wuraren ƙarfe biyu daidai na dare,wata irin guguwar iska,ta shigo ta cikin windown ɗakin su Sehrish mai matuƙar tsoratarwa da kuma razanarwa baƙi wulik mai tafe da wani irin sauti,wanda ya ciccika kunnuwansu,a firgice hosana ta farka tare da fasa wata irin razananniyar ƙara,wanda yayi silar tashin Sehrish,ita kanta ta tsorata da ganin guguwar iskar nan,ta tattare wuri guda yadda kasan kwarangwal din mutun haka shape ɗinta ya koma bayan ta sauka a dakin nasu,ga yayi ajikinta,

  Ƙanƙame Sehrish hosana tayi sosai tana cewa"Wayyo Allahna,mun shigo uku,ina daddynmu yake,menene wannan abun,'

  Babu abunda Sehrish ke ambato face"innalillahi wa'inna ilaihirraji'una,yayin da ta ƙura idanunta akan guguwar nan data saukar masu acikin ɗakinsu,

  jikinsu sae faman kerma yake yi gaba ɗayansu,hakoransu sae faman rawar ɗari suke yi kaf kaf kaf,saboda wani irin sanyi daya ziyarce su,

  ganin guguwar ta tsaya agefen gadonsu,kamar su take kallo don harda ƴan idanu gare ta hakan yasa suka ƙara fashewa da kuka suna faɗin"Wayyo Allah mun shiga uku!"

A firgice jahad ta farka,jin ihun da su hosana keyi,adai dai lokacin hosana na cewa"wlh hada ƴan idanu ke gare ta,mun shiga uku,"

  Zuba masu ido jahad tayi tana kallonsu ganin yadda suka kware baki suna kuka,Ga bargo a hannunsu,sun rurruƙe,

  A hankali ta mayar da idanunta kan abunda suke kallo,guguwar nan ta gani tsaye da suffar kwarangwal tayi masu ƙuru da ido,

  "Jahad kina ganin abunda muke gani kuwa"?Sehrish ce tayi mata maganar,

  Jinjina kai jahad tayi tare da cewa"Nagani,mutun ne wannan ba guguwar gaske ba,koma waye yazo ne don ya tsoratar damu ne kawai babu abunda zai iyayi mana,"

  Hankali atashe hosana da sehrish suke kallon jahad,jin abunda tace,babu alamun jin tsoro atattare da ita,hankalinta kwance tayi maganar,ganin haka yasa suma suka dakatar da kukan da sukeyi,

   "Wama ya sani,ko ya sayyadi ne yazo da suffar guguwar nan don yazo yaga yadda muka koma," jahad ce tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya,


Baki asake suke kallonta,sehrish tace"Anya jahad ba macanzarki akayi mana ba?na fara kokwanto anya kece?taya zaki ga wannan tashin hankalin amma ki nuna baki damu ba?guguwa face tayi suffar kwarangwal kuma hada ƴan idanu kuru tana kallonmu ki kalla dakyau,"

  Tsoki jahad taja tare da cewa"Nice mana,nifa Allah kaɗai nake tsoro,dashi na dogara,wannan koma menene yazo wlh ni dariya ma halittar take bani,ji idon fa yadda yake jujjuyawa kamar an ɗorashi,' fashewa da dariya jahad ta kuma yi,Kafin ta kalli su hosana tace"abunda za'ae yanzu muja bargo mu lullu6e,mu rabu da ita,idan ta gaji da tsayuwa ta tafi,koda yake ba ƙafafu gareta ba,fiffike zatayi ta tashi,'

Ta ƙarasa maganar cike da nishaɗi,jan bargon nasu tayi,cikin sauri suka gyara kwanciyarsu ta lullu6esu da bargon,saboda tsabar tsoro Bargon da suka lullu6a dashi sae faman kerma yake yi,

  "Jahad dagaske,baki ji tsoron wannan abun ba"?kasa-kasa Sehrish ta tambaye ta,

  Murya na kerma jahad tace"yanzu haka ma kuka nake yi,wlh atsorace nake,ƙarfin hali kawai nayi,saboda na ta6a jin wani malami yace idan ka nuna kana jin tsoran Aljani shine yake cin nasara akan mutun,shi har faɗama yake yi da aljanu shine nima na jaraba yin irin nashi,'

  Duk da halin da Sehrish ke ciki sai da ta fashe da dariya tana kumshe baki,

  "Jahad kinja mana bala'e,koma meye yanzu kin ƙara fusata shi da kalamanki,bansan me zai biyo baya ba,"acewar sehrish,

  Jahad tace"Addu'a zamuyi kawai,insha Allah ba abunda zasu iya yi mana,'

  Muryar hosana suka jiyo abayansu tana cewa"Sehrish dan Allah kuyimun addu'a,ko fatiha bazan iya karantawa ba a halin da nake ciki a yanzu,ga fitsari ya matse ni,'muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,

  Jahad tace"ki tashi ki shiga toilet mana!kinsan Allah kada kiyi mana fitsarin kwance,'

  Fashewa da kuka hosana tayi tana cewa"taya zaki ce in shiga toilet bayan wannan halittar na nan ta ƙura mana ƴan idanunta,Allah ba inda zanje,sai dae ki tashi ki rakani ko kuma inyi shi a wando,'

  Har haɗa baki sukeyi wurin cewa"Wai wa zai raka ki"?

  "Ke ko sehrish daya daga cikinku ta rakani,"

  "Tab,wlh nidai ba inda zanje,sai dai ko Sehrish," jahad nakai ƙarshen maganarta sehrish tace"Ke baki je ba sai ni kike tunanin cewa zan rakata,Ae wlh sai dae tayi shi a wando,ba inda zanje,"

  Ganin basu ɗauki maganarta serious ba yasa ta ƙara fashewa da wani kukan mai sauti,

    "Dawo tsakiyarmu ki kwanta,zanyi maki addu'ar ɗaukewar fitsari,ae na iya,Oumma ta ta6a koya mana,"fashewa da dariya sehrish tayi tana cewa"kai jahad,ni ban ta6a jin wata addu'a ta ɗauke fitsari ba,'

  Tashi hosana tayi tare da komawa tsakiyarsu ta kwanta,tana jiran Jahad tayi mata addu'a kamar yadda tace'

  "Rufe idanunki"jahad ta fadi hakan fuskarta ƙumshe da dariya,runtse ido hosana tayi tare da cewa"Na rufe,"

  Tofa mata addu'a jahad ta shiga yi a fuskarta,ita kanta me addu'ar batasan me take fadi ba,sae faman motsi take da baki,intayi sosai saita tofa ma hosana a fuskarta,

  A ƙule hosana tace"waini sai tofa mun miyau kike a fuskata,kuma ni banji kina addu'ar ba,'

  "Ita addu'ar a sirrance akeyinta,ba a bayyanata,kiyi shiru kawai zanci gaba da karanta maki har a samu fitsarin ya ɗauke,

  Shiru hosana tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,yayin da jahad taci gaba da karanta mata addu'ar,duk sehrish na sauraronsu,

  Abu kamar wasa,bacci ya ɗauki hosana,

  "Kamar tayi bacci"?sehrish ta tambaya,

  Jahad tace"eh,tayi bacci yanzu saura mu ya rage muyi bacci,'

  Sehrish tace"taya zamu iya bacci da waccen halittar a ɗakinmu?inta cutar damu fa"?

  Jahad tace"Insha Allah ba abunda zata iya yi mana,muyi addu'a kawai mu kwanta,mu ɗauka kamar mafarki ma mukeyi,"

  Kamar yadda jahad tace haka suka haɗa baki suna karanta addu'oi,bayan sun kammala kuma suka shiga karanta ayoyin alkur'ani mai girma atare,cikin lokaci ƙankani bacci ya ɗaukesu,

  Yin baccinsu keda wuya wannan guguwar ta disashe daga wurin ta 6ace 6aat.


Tashin hankali,kowaye yazo masu da wannan suffar?


Abunda ya faru bayan fitar abbansu daga bedroom ɗinshi,kai tsaye ya wuce upstairs part ɗin Marshal Omar,jikinshi duk asanyaye haƙika junaid ba ƙaramin 6ata mashi rai yayi ba,da alama sakin fuskar da yake yi mashi ne yana wasa dashi kamar tsaranshi,hakanne yasa raini ya fara shiga tsakaninsu,


Da sallama abakinsa ya shiga bedroom ɗin Marshal,samunshi yayi a kwance yana sharar bacci,bedside lamps ɗinsa ne suka haskaka wurin bed ɗinsa,

Shiga ciki abbansu yayi tare da hayewa saman gadon,ya jingina bayanshi a jikin headboard ɗin gadan,Ranshi duk a jagule yama kasa kwanciyar saboda yasan cewa koya kwanta bazai iya runtsawa ba,ba ƙaramin ƙuntata yayi ba,junaid ya fusata shi sosai,

  Kwakkwaran juyi marshal yayi zai gyara kwanciyarshi,karaf idanunshi suka sauka akan Abban nasu,cike da mamaki ya ambaci sunanshi"Abba!"

  fuskarshi ɗauke da damuwa yakai idanunshi akan fuskar Marshal yace"Omar,dama ba bacci kakeyi ba ne?"yayi maganar ayayin da yake ƙoƙarin 6oye damuwarshi,

  Yunƙurawa Omar yayi tare da tashi daga zaune yana fuskantar abban nasu yace"Abba!meya faru naganka anan?kuma fuskarka da alamun damuwa attare dakai,"?

  shiru abbansu yayi na wani lokaci yana deciding akan ya faɗa ma Omar halin da yake ciki ko kuwa ya ƙyale zancem kawai,

  "Omar,ashe junaid bai da wayau har yanzu yaro ne shi"?

  aɗan ruɗe omar yace"me junaid ya aikata,"?

  "Hmmm,ya hanani sakat Omar,ƙiri ƙiri junaid ya shige mun ɗakina,yana can rungume da mommynsa,nayi nayi dashi ya tashi in kwanta amma ya ƙiya,wai har ni yake ce ma Yau kwanan sa ne!"?

Murmushi marshal Omar yayi jin shiriritar junaid,wato yau da Abbansu yake kishi,

   "Abba,just calm down ur mind,ka bani 5 minutes yanzu zan dawo,just wait," 

  Ya ƙarasa maganar tare da miƙewa ya kama hanyar fucewa daga bedroom ɗin,

  Zugudum abbansu yayi yana jiran dawowar Marshal,


Saukowa downstairs yayi kai tsaye ya wuce bedroom ɗin Abban nasu,a hankali ya tura door tare da shigewa ciki,koda junaid yaji an tura ƙofa sae ya ɗan ɗago da kanshi don yaga wanene,ashe baiyi bacci ba damuwar jahad ta hana shi sak har yanzu a tsorace yake,duk a tunaninsa abbansu ne,karaf idanunsa suka sauka akan Marshal Omar dake shigowa ciki,ae yana ganin Marshal Omar ya qara ƙanƙame mommynshi,don yasan cewa abbansu ne yakai shi qara shine akazo a ɗauke shi,

  Omar na ƙarasawa wurin gadon ya Shiga tattara hannun jallabiyar jikinshi,muryar junaid kamar zai kuka yace"Ya omar dan Allah kada ka ɗauke ni,wai ni mai yasa akeso a takuramin.....'bai ƙarasa maganar ba Omar ya ɗaukesa gaba ɗaya ya aza a kafaɗarshi,ya fuce tare dashi daga ɗakin,

  Suna tafiya yana kuka kamar ƙaramin yaro,Omar yace"rufe mun baki junaid,banason ƙara jin wani sounds daga bakinka stupid,wai har abba kake cema Yau kwananka ne!tsaran wasan ka ne!ko don kaga yana wasa dakai ne shiyasa ka raina shi?

  Ya ƙarasa maganar a lokacin da yake hawa upstairs,

Cikin shessheƙar kuka junaid yace"Ya omar,ni fa ban raina shi ba,saboda me zai dinga zuwa yana kwana tare da mommy,bayan ni ya dace ace ina kwana a wurinta,abba baiyi mun adalci....'

  Katse shi omar yayi da cewa"Shut up junaid,'

     Tsit junaid yayi yana faman hura hanci,

  "Tunda har ka fara kishi da mahaifinka,hakan na nufin cewar zaka Iya aikin Soja!yadda zaka ji daɗin kishin ƙasarka,"

  Hankali tashe junaid yace"Am sorry ya Omar,bazan ƙara ba,Zan daina hanashi kwana,'

   girgiza kai Omar yayi yana cewa"Ban amince ba,zuwa aikin Soja ba fashi junaid,U.S ma zamu turaka,zanyi ma sgr magana,dama abba kawai muke jira ya amince,kaga yanzu ka 6ata mashi rai nasan cewar a shirye yake daya miƙa ka wurinsu koya huta da shiriritarka,

   Turo kopar bedroom ɗinsu yayi ya shige da junaid ciki,Abba na ganin shi ɗauke da junaid,ya ɗaure fuska a cikin zuciyarshi kuwa ba ƙaramin daɗi yaji ba,

  Sauke shi saman gadon Omar yayi tare da cewa"Maza ka kwanta,"

   turo baki junaid yayi yana kallon Abbansu,zuba mashi ido abban yayi yana kallon ikon Allah,

   Kwantawa junaid yayi tare da Lullu6ewa da bargo,yayi ƙasa ƙasa da muryarshi yana cewa"abba hankalinka ya kwanta,ka rabani da mommyna,kuma gobe can zan kwana,in kuma aka hanani ɗakinsu sehrish zan dinga kwana,"

  Saukowa abba yayi daga saman gadon ya kalli Omar tare da cewa"ngde ssae Omar,Ni zan wuce,mu kwana lpy,"

  Fuskar Marshal ɗauke da Murmushi yace"Gud night abbana,"

  Har yakai bakin ƙopar fita daga ɗakin ya juyo yana kallon Omar ɗin dake tsaye yana kallon bayansa yace"Omar wai cikin triplet ɗin nan Wacece taka acikinsu"?

  Sunnar dakai ƙas Omar yayi yana faman sakin Murmushi,daƙyar ya iya furta sunanta"Hosana,"


Jinjina kai abbansu yayi fuskar nan ɗauke da murmushi yace"batare da 6ata lokaci ba,bayan an kammala walimar jibi zan nema maka auranta a wurin mahaifinta,saboda banason wani daga waje ya gansu yace yana so,nafison dukansu su auri na gida,saboda na yadda sosai da irin tarbiyar dana baku,zaku kula da rayuwarsu sosai,"

  "But....Abba Rafayet fa,?shima zaka nema mashi auren ɗaya daga cikinsu in yaso sai a haɗa auren atare!!!!?




  *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃



*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI.  MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*



*LOCATION KANO*


08062073990

Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku



Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku


It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.

Snack

Awarah 

Farah

Zobo

Samosa

Cup cake etc 

Contact me 09063302182or 09012179727.

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: Sai faman safa da marwa takeyi acikin bedroom ɗinta,gaba ɗaya ta rasa samun natsuwa,hakanan ta dinga jin fargabar zuwa abuja,ga zumuɗin zuwan da takeyi amma kuma tana zullumin abunda zai biyo baya,hakanan ta dinga jin kamar wani abu mara daɗi zai faru,ƙafafunta har sun fara ciwo saboda zaryar da take ta faman yi,tun bayan da ta kammala sallar asuba bata koma bacci ba,Jikinta na sanye da Zumbuleliyar riga doguwa brown,sae guntun hijabin da ta kammala sallah dashi,hannunta na ruƙe da wayarta,wani tunani ne ya fado mata aranta,cikin sauri ta shiga danna wayar dake hannunta,Hayaam ta buga ma waya,nan take kiran ya shiga,batare da 6ata lokaci ba hayaam ta ɗaga kiran,daƙyar take magana saboda ta katse mata baccinta,rai a6ace tace"Lafiya kika kira Ni?bayan kin gama kwashe mun albarka"!

  Cikin lallami Aunty babba tace"Dan Allah hayaam komai ya wuce kinji ƙanwata?nasan ban kyauta ba,amma kiyi haƙuri,"

  Tsoki hayaam taja tare da cewa"hmmm,halan yanzu kin gasgata maganata ne?shiyasa kika kira don jin ƙarin bayani?

  Aunty babba tace"EH,hakane,na yadda da abunda kika faɗamun,tuntuni shiyasa ma na kira ki,"

  Hayaam tace"Yanzu ya kenan?ya zamuyi?don gaskiya akwai matsala aunty laila,burin mu bazai ta6a cika ba,muddin yaran nan suna nan!"

  Jinjina kai Aunty babba tayi tana cewa"babban takaicina yaran da suka kasance mata ne!har ƴan uku,gaskiya abusufyan bai kyauta mana ba tsakani da Allah,haka ake?kawai sai yaje yayi aure a 6oye batare da sanin kowa ba?wai kuma da sanin ammi kuwa"?

  Hayamm tace"Anya,gaskiya ina tunanin Ammi bata sani ba,'

  Jin haka yasa Aunty babba cewa"Allah yasa in tazo tace bata amince da yaran ba,kinsanta Jarababbiyace,musamman ma da yayi auren bada saninta ba,Wai shin su yaran ina mahaifiyarsu take ne?tana da asali kuwa"?tayi tambayar cike da son jin ƙarin bayani,

  Hayamm tace"Ina fa,ae rannan na tambayi azmee game da mahaifiyarsu,shine take sanar dani cewa mahaifiyar yaran Ƴar fa mai gadin gidan gwaggon katsina ne!basu da wani asali,buzaye ne ƴan niger,"

  Aunty babba tace"tabɗijancan aikuwa Ammi bazata ta6a yarda dasu ba,kinsanta ta tsani mutun mara asali,gata ita kaifi ɗaya ce muddin tace bata yarda dasu ba amatsayin ƴa'ƴan Abusufyan to fa korasu zatayi daga gidan,yakamata muyi wani abu akai,tun kafin takai ga zuwa,"

  Hayaam tace"meke nan zamuyi?kinsan fa gobene walimar kuma gobe zata zo,"

  "Abunda zamuyi shine,Ae ina da numbar Ammin a wayata,zanyi amfani da sabon sim ɗina,wanda ban fara amfani dashi ba,zan kirata na sanar da ita game dasu tunkan taji a wurin wani,"acewar Aunty babba

  dariya hayaam tayi tare da cewa"Gaskiya aunty laila kin iya haɗa tuggu,ni sam banyi tunanin hakan ba,wannan ce hanyar da zamu bi wurin tarwatsasu,idan kika kirata awayar ki tunzurata sosai,ki ɗaurata akan network har sai ta amince da kalamanki,ki sanar da ita cewa yaran shaggu ne,abusufyan yayi ma mahaifiyarsu ciki a 6oye,shine suka so su 6oye mata,don karta sani,"

  Murmushi Aunty babba ta saki tana cewa"hakan yayi sosai,zan tsara komai yanzu........."tana cikin maganar taji alamar dirar motar ishaq,

  Cikin sauri tace"Hayaam inaso ki ɗauko min hoton yaran kafin muzo gobe,zan kashe wayar yanzu ishaq ya dawo,

  "Toh aunty laila,zanyi ƙoƙarin ɗauko maki hoton nasu,"


Daga haka sukayi sallama da juna,

Ajiyar zuciya aunty babba ta sauke,har taji wani sanyi a ranta saboda ta samu mafita,


Bayan sun kammala wayar hayaam ta buɗe ƙopar ɗakinta tare da fitowa,cikin sanɗa hayam take tafiya don kar wani ya ganta,a haka har ta ƙarasa bedroom ɗinsu sehrish,tura ƙopar tayi cikin sa'a ta samu ƙopar ɗakin a buɗe,leƙa kanta ta fara yi anan ta same su,suna ta sharar bacci wanda tun bayan sallar Asuba da suka tashi suka koma suna yin baccin,


Murmushi ta saki tare da sa kai ta shige ciki,adai dai bakin gadon nasu ta tsaya tare da ɗago da wayarta dama already a cikin camera take,Saita fuskarsu tayi dama kuma duk suna facing ɗin ceilling,kyakkyawan hoton fuskokinsu ta ɗauka,bayan ta kammala ɗaukar hoton,ta lalla6a batare da kowa ya ganta ba,ta koma bedroom ɗinta,cikin sauri ta tura ma Aunty babba hoton ta whatsapp ɗinta,


❤🤍❤


Wuraren karfe takwas,suka farka daga bacci,sehrish ce ta fara shiga toilet tayi wanka,bayan ta fito daga wankan jahad ta shiga ciki,gaban dressing mirror ta zauna ta gama shafe jikinta,ta feshe shi da turare,sannan ta koma ta ɗauko Jallabiya fara ta zura ajikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,musamman adon dake jikin rigar na stones,shiya ƙara ƙawata rigar,bayan tayi rolling kanta da mayafin rigar,ta fito daga cikin bedroom ɗin nasu ta wuce kitchen,cike da zumuɗin kaima babban yaya breakfast ɗinshi gaba ɗaya ta manta da abunda Uncle abusufyan ya faɗa mata,


A kitchen ta samu azmee,har ta kusa kammala girkin,ganin yadda take ta aiki ita kaɗae yasa sehrish taji duk ba daɗi,muryarta a sanyaye tace"Ina kwana Aunty azmee,"

Juyowa tayi daga tsayen da take gaban gas cooker,fuskar nan ɗauke da murmushi tace"Lafiya lou ƴan matan abusufyan,fatan kun tashi lafiya"

  "Lafiya lou,amma aunty azmee gaskiya banajin daɗi in naga kina aiki ke kaɗae,meyasa baki tashe mu ba,munzo mun tayaki aikin"?tayi maganar yayin da take ƙarasa shiga cikin kitchen ɗin,

  Azmee tace"kada ki damu,na riga na saba da aiki,wannan ba wani abu bane,Abba ma ya nemi daya ƙaro masu aiki amma nace mashi ya barshi kawai,saboda na saba da yin aiki ni kadae,"

Girgiza kai sehrish tayi tare da cewa"that's impossible,gaskiya in har ba zaki amince a ƙaro masu aiki ba,to daga yau Ni dasu jahad zamu dinga tayaki aiki,don bazaiyiwu ba kiyi ta wahala ke kaɗai,"

  murmushi kawai azmee tayi batare da tace Komai ba,

   "Aunty azmee idan akwai abunda kika kammala inaso zan fara kaiwa dining in jera,kinga na rage maki wani aikin,"

  "Ban kaiga shiryasu ba,amma sai dai idan zaki kaima Sgr nashi,sae na haɗa maki,ki kai mashi,"

  Murmushi ta saki tare da cewa"Toh,"


Shirya mata breakfast azmee tayi acikin ƙayataccen tray,bayan ta kammala,sehrish ta ɗauki tray ɗin tare da fucewa daga kitchen ɗin,


tana cikin tafiya harta kusa hayewa upstairs taji anyi mata gyaran murya abayanta,cikin sauri ta juya don taga Wanene,ganin Uncle abusufyan yasa gabanta faɗuwa,saboda tana kallonshi ta tunano da abunda ya faɗa mata a daren jiya,


Muryarta na rawa ta furta"Daddy,"ƙarasawa yayi wurinta tare da tsayawa dab da ita fuskarshi a ɗaure yace"Me na faɗa maki jiya?tun yanzu zaki fara sa6amun"?

Hankali tashe sehrish tace"a'a daddy,wlh mantawa nayi,bazan ƙara ba,dan Allah kayi haƙuri,"

   "Zo ki wuce ki mayar da kayan abincin kitchen,inyaso azmee taje takai masa,"

  Jiki asanyaye Sehrish ta juya tare da kama hanyar komawa kitchen,duk wannan abun daya faru akan idon,Mommynsu junaid alexandra,tana tsaye abakin part ɗinsu na downstairs tana kallonsu,


Haka ta koma kitchen da kayan abincin idonta cike tab da hawaye,taci burin ta ganshi yau,amma Uncle abusufyan yayi mata tsiya,

Tamkar wadda aka zarewa laka haka ta shiga kitchen ɗin,Azmee na ganinta dauke da tray a hannu tace"Lafiya naga kin dawo da kayan abincin"?tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,muryarta tamkar zatayi kuka tace"Uncle ne ya hanani zuwa part dinsa da sunan aiki,tun jiya da daddare ya gargaɗeni akan Karna kuskura na ƙara yin aiki a ƙarkashinsa,bansan meyasa ya hanani ba,"

Cike da mamaki azmee tace"to fa!ko meyasa yayi hakan?kuma kin tabbata bakiyi wani laifin ba wanda yajawo har ya hanaki aiki a part ɗinsa"?

  "Aunty azmee ni banyi laifin komai ba,"ta ƙarasa maganar a yayin da take ajiye tray ɗin hannunta,

  Shiru azmee tayi aranta tana mai mamakin hukuncin da Abusufyan ya yanke ma sehrish,to kodai don saboda basa shiri da Alexandra ne?tabbas zai iya yiyuwa hakane!tunda akwai gaba atsakaninsu,dole kuwa ya hana Sehrish tayi ma Sgr aiki,don bazai ta6a yarda ƴarsa tazama baiwarsa ba,

  "Aunty azmee ko zaki iya nema mun alfarma a wurinsa yabarni in cigaba da aiki acikin gidan nan kamar yadda na saba,"muryar Sehrish ce ta katse mata tunaninta,

  zaro ido azmee tayi tare da cewa"Ni ƴar ubanwa?na isa in shiga tsakaninki da mahaifinki?bazaiyiwu ba sehrish,shawarar da zan baki shine kawai ki bi Umarnin mahaifinki ki xauna lafiya,Shi kaɗae yasan dalilinshi na yin hakan,kuma in har kika yi mashi biyayya zakiga ribar yin hakan,"

  ɗakyar ta iya haɗiye yawun bakinta,ga hawaye sae faman zarya sukeyi a fuskarta,

    "Wannan hukuncin da mahaifinki ya yanke,yayi mun dai dai,don koda bai dakatar dake daga yi mashi aiki ba,to ni dakaina zan hanaki!"

  Gaban Sehrish ne ya faɗi rass jin muryar Mommynsu junaid abayanta,Azmee kuwa na ganinta tasha jinin jikinta don tasanta sarai bata da mutunci ta wani 6angaren,

  Juyawa sehrish tayi da sauri tana kallonta,

  A hankali take tunkararsu yayin da take ci gaba da magana"Banason kusancinki dashi ko kaɗan!just maintain a good distance between u and him,In ba haka ba,You will see the trouble!!"Jikin sehrish har kerma yake yi don ba ƙaramin tsoranta takeyi ba,koƙarin 6oyewa a bayan Azmee takeyi,don gani take tamkar Alexandra zata bugeta ne,

  Koda ta ƙaraso dab dasu,harara ta wurga ma azmee tare da cewa"Matsa daga gabana,da ita nakeson magana,"jiki na rawa azmee ta janye jikinta gefe guda,aranta tace"tashin hankali ashe har yanzu matar nan,bata canza ba,lallai akwai matsala,"

   goya hannayenta tayi asaman ƙirjinta,yayin da suke fuskantar juna ita da Sehrish,saboda tsabar tsoro ƙiris ya rage sehrish ta saki fitsari,ko idonta bata iya dagawa ta kalleta saboda yadda tayi mata tsaye aka,

  Wani irin kallo Alexandra ke bin Sehrish dashi,tun daga ƙasa har sama,yatsina fuska tayi tare da cewa"Ur name"?

  Murya na kerma tace"Sehrish,"

  Jinjina kai alexandra tayi tare da cewa"saboda daddynki ya hanaki aiki a part ɗin rafayet shine kike kuka?why?

..girgiza kai sehrish tashiga yi tana cewa"a'a..ba saboda haka nake kuka ba...."

  "Kukan menene toh"?ta sake jefa mata tambaya a karo na biyu,

  "Babu komai,"ta bata amsa tana faman zazzare idanu,

  Murmushin gefen fuska alexandra ta saki kafin ta kuma cewa"dama ana kuka ne just without any reason?ki faɗamun gaskiya mana,kodai kin faɗa tarkon shi ne"?

  Waro ido waje Sehrish tayi hankali tashe tace"a'a ba haka bane,kawai ina kuka ne saboda tsoron hukuncin da babban yaya zai yanke mun in ya gane cewa na daina yi masa aiki,"

  Ta6e baki alex tayi tare da cewa"Just calm down ur mind,Bama zai ta6a damuwa akan hakan ba,kiyi ma mahaifinki biyayya,kuma ki nisanta kanki dashi kamar yadda nace,hakan zaifi maki kwanciyar hankali,"tana kai ƙarshen maganarta,ta juya cike da isa tare da fucewa daga kitchen ɗin,


Fitarta keda wuya Azmee ta mayar da idonta kan sehrish saboda ta lallashe ta,amma ina,tuni sehrish ta watsa da gudu tabar kitchen ɗin,


A bakin ƙopar dakinsu ta tsaya tana faman shessheƙar kuka,zuciyarta har wani tafarfasa takeyi mata,dole tayi kuka saboda tasan cewa ta rasa Sgr na har abada,tunda mahaifiyarshi ta nuna bata sonta,zuƙunnawa tayi a ƙopar ɗakin tana cigaba da kukan nata,ta jima zuƙunne a wurin cikin wani irin yanayi mara daɗin ji,tana jiyo muryarsu jahad acikin bedroom ɗin,suna tattaunawa kan wankan da zasu ɗauka gobe ranar walima,hada zancen saloon ɗin da daddynsu yace zai kaisu ayau,

  gaba ɗaya taji komai ya fita ranta,don har wani zazza6i taji ya saukar mata ajikinta,ita kaɗae tasan raɗaɗin da takeji acikin zuciyarta,hannu tasa tare da share hawayenta sosai don karsu hosana su gane cewa tayi kuka,bayan ta kammala goge hawayen ta miƙe,tare da buɗe ƙopar ɗakin tashiga ciki,

  Jahad na zaune gaban mirror tana shafa powder a fuskarta,hosana kuma na tsaye gaban wardrobe tana cewa"Nama rasa wani kaya zansa yau,saboda inaso in na kammala shiryawa inje in tashi Ya Omar daga bacci don nasan cewa bai kaiga tashi daga bacci ba,"ta ƙarasa maganar tare da ɗan juyawa ta kalli jahad tace"daddy yace yau zai kaimu Saloon ko?to da yaushe zamu fita?donni hada ƙunshi za'ayimun a hannuna,yanzu ma in naje ɗakin ya Omar zan tambayeshi wani kalar ƙunshi yakeso ayimun baƙi ko ja," jahad tace"Soyayya daɗi,kunshin ma sai an tambayi ya omar wani kala yakeso kenan?to gyaran gashin fa?shi bazaki tambayeshi wani kala yakeso ba?

  murmushi hosana tasaki tare da cewa"dole ma in tambayeshi wani kalar gyaran gashi yakeso ayi mun,"_

  Suna cikin magana muryar Sehrish ta katse su da cewa"Ƴan uwana rabin raina,me kuke tattaunawa akai ne?naji kamar ana gulmar ƴa omar,ko kunnena ne,'tayi maganar tana ƙoƙarin danne damuwarta,gefen gadon ta samu ta zauna,tana faman sauke ajiyar zuciya,

.juyowa sukayi suna kallonta,hosana tace"Sehrish ina kika je,na tashi ban ganki ba,har naji tsoran kada ace wannan halittarce mai ƴan idanu ta ɗauke mana ke"

  Dariya sehrish tayi tare da cewa"ni harna manta da wannan abun,koda na tashi daga bacci ban iya tuna abunda ya faru jiya ba,sae naji kamar duk a mafarki ne,"

  Hosana tace"Ae taji tsoro ta gudu,yau da daddare in tadawo,zan aro bindigar yaya Omar in harba mata bullet acikin idanunta,"atare suka fashe da dariya jin abinda hosana tace,hada kwatantawa da hannunta yadda zatayi shooting din guguwar,

  Jahad tace"Cika baki kawai,kin manta kukan da ki kayi mana ajiya?kinfi kowa tsorata,ba don nayi maki addu'ar ɗaukewar fitsari ba,da ba'asan me zai biyo baya ba....'dakyar ta ƙarasa maganar saboda dariyar da tazo mata,

  cike da nishaɗi suke yin firar tasu,kafin lokacin yin breakfast yayi atare suka fita,Hosana ta wuce part ɗin Omar,yayin da su kuma suka wuce dining,Sehrish dae jurewa kawai takeyi,suk ta gaza sakewa saboda rashin sanya sgr a idanunta,gashi bai sauko downstairs ba,saboda Azmee takai mashi nashi a part ɗinsu,kuma sam bai tambayeta akan Sehrish ba,Hakan na nufin cewa Sgr bai damu da ita ba ko kaɗan,dama haroon yace Iskace ke wahalar da mai kayan kara,


Yana kwance yana sharar bacci,hosana ta shiga bedroom ɗin nashi,lalla6awa tayi ta haye saman gadon har wurinshi ta ƙarasa,saitin fuskarshi tana kallon zunzurutun kyawunsa,


Hura mashi iska tayi a fuskarshi,nan take ya ɗan motsa tare da yatsina fuskarshi,murmushi hosana ta saki tare da kai hannu ta toshe mashi hancin shi,aikuwa a gigice ya farka batare da ya sani ba ya tattara dukkanin ƙarfinshi ya cakumi hosana tare da yin wurgi da ita,gaba daya ta tafi yaraf ta kife ƙasan tiles ɗin daga gefen gadon,nan take ta fashe da kuka saboda hancinta daya daki ƙasa,shi duk atunaninshi wani ne ya kawo mashi hari shiyasa yayi mata haka,kuma yana yin wurgin da ita,yaci gaba da baccinsa,dama duk a cikin magagin bacci ne yayi mata hakan,


Cikin baccinshi ya jiyo sautin kukanta tana cewa"Wayyo Allah,hanci na ya fashe,ya Omar ka kashe ni,"


A firgice ya ware idanunshi tare da miƙewa daga zaune yakai idanunshi wurin da sautin kukan ke fita,anan ya samu hosana dafe da hancinta a zaune dirshan tana kuka,


Hankali atashe ya sauko daga saman gadon ya zukunna agabanta yana tambayarta lafiya?garin yaya taji ciwo a hancinta,


Cikin shessheƙar kuka tace"bakaine ka cakume ni ba,kayi wurgi dani daga saman gado na faɗo ƙasa har hancina ya bugu,"


Waro ido waje yayi tare da cewa"Ni kuma dakaina"?

Jinjina kanta tayi tare da cewa"Eh mana,saboda kawai na toshe maka hanci,

  



🙏🙏🙏



  

 

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


❤🤍❤




*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




Hannu yasa tare da tallabo fuskarta yace"Hosana bada sani na nayi maki hakan ba,laifin ki ne,meyasa zaki toshe mun hancina?so kike na mutu'?

Girgiza kai tayi"a'a,banso ka mutu,ae ni wasa nayi maka ko,"tayi maganar tana satar kallon fuskarshi,

  "Faɗa mun me ya kawoki bedroom ɗina har saman gadona"?

   A ƙule tace"nifa nazo ne na tashe ka don kaje ka ci abinci,naga kowa ya fito banda kai,kuma zasu iya cinye abincin duka,"

 fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Waya faɗa maki za'a cinye abincin,ae ko ban fita ba Azmee zata kawo mun ne har cikin part ɗina,"

    Shiru tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,ɗagowa ta ƙara yi zata saci kallonshi suka haɗa ido,ganin yadda yake kallonta ko ƙyaftawa baiyi hakan yasa ta ɗaure fuska cikin shagwa6a tace"Ya omar wannan kallon fa,ka wani tsare ni da ido,"

  yadda tayi maganar ba ƙaramin burgeshi tayi ba,ya jima yana kallonta batare da yace wani abu ba,har sai da ta hasala rai a6ace tace"shikenan tunda ba zaka mun magana ba,bari na tashi na tafi,dama ko abincina banci ba,saboda kawai inzo in tashe ka daga bacci,amma ko farin ciki ba kayi ba,'

  Ajiyar zuciya ya sauke tare da ruƙo hannunta cikin nashi"Hosana,so nake ki faɗa mun gaskiya,kina sona da gaske?kuma zaki aure ni? Waro ido waje hosana tayi tana kyakkyaftasu kamar na ƴar tsana jin abunda yace,a ruɗe tace"Ya Omar!aure fa!"_

Jinjina mata kai yayi tare da cewa"eh,aure hosana ko baki shirya ba,"

  Turo baki ta ɗanyi tana ƙunƙuni ƙasa ƙasa,hankalinsa kam harya ɗan tashi saboda ganin yadda ta tsorata don yayi mata zancen aure,dama fargabarsa kada sai anje wurin nema mashi auranta tace bata shirya ba,don yasan ba cikakken hankali gare ta ba,


Lalla6ata ya shiga yi"pls hosana,ki faɗamun gaskiya,zaki aure ni"?

  daƙyar ta iya buɗe baki tace"Ni yanzu tashi zanyi in tafi,dama zuwa nayi fa don in tambayeka,wani kalar ƙunshi kake so ayimun baƙi ko ja,"

   ya lura cewa batason zancen auren shiyasa ta kawo maganar ƙunshin,cikin sanyin murya yace"Nafison jan lalle zai fi yi maki kyau,kuma ba mai yawa ba ƙunshin,ƴar flower kawai za'a zana maki mai kyau,"

  Yana kai ƙarshen maganar,hosana ta miƙe tana faman shan ƙamshi,da sauri ta juya ta bar bedroom ɗin nashi,bin bayanta yayi da kallo har ta fuce,jiki asanyaye ya miƙe tare da nufar toilet ya shige,

   Hosana na fita daga cikin bedroom ɗin nashi,a falonsa ta tsaya tana faman zabga murmushi,tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,Yau ya Omar ya nuna yana sonta harma yanayi mata zancen aure,ta rasa ma wa zata fara faɗamawa,sai faman zagaye zagaye takeyi a cikin falon,


Wuraren ƙarfe biyu da rabi na rana,Abusufyan ya ɗaukesu acikin motarshi kamar yadda yayi masu alƙwarin kaisu wurin saloon da kanshi,hosana da jahad suna a bayan motar duk sun ɗau wankan jallabiya sun laga mayafi,Sehrish na agaban motar kusa da driver seat inda Uncle abusufyan ke zaune yana driving ɗinsu anatse,Su jahad da hosana sae fira sukeyi tare dashi,amma ita ko uffan bata tanka masu ba,dama tunda ta shigo cikin motar Abusufyan ya lura da yanayinta,


gyaran murya yayi mata hakan yasa ta ɗan dago da kanta ta kalle shi,

  "Meyake damunki ne Daughter?tunda kika shigo cikin motar nan baki tanka mana ba,ga ƴan uwanki suna ta fira a tsakaninsu amma ban dake". 

  Muryarta asanyaye tace"Babu komai,"

  "ko don saboda na hana ki kai ma Sgr abinci ne"? Yayi maganar batare daya kalleta,

  Cikin sauri tace"a'a ba haka bane,kawai bana jin daɗin jikina ne,"

  "Ban yarda ba daughter,saboda shi ne yasa kika shiga damuwa,"_

  Shiru tayi bata ce komai ba,murmushi abusufyan yayi kafin yace"banyi hakan don na takura maki ba,face don na ɗaukaka darajarki,nasan ba zaki fahimce ni ba a yanzu amma nan gaba da kanki zakiyi mun godiya akan hakan,idan kuma hakan ya 6ata maki rai,kiyi haƙuri,'ya ƙarasa maganar adai dai lokacin da suka ƙaraso wurin Saloon ɗin,parking ɗin motar yayi jahad da hosana suka fita waje,tana ƙoƙarin buɗe motar ta fita ya ambaci sunanta"Sehrish,"juyowa tayi tare da kallon fuskar daddyn nasu tace"Na'am daddy,"

  "Murmushi kawai nakeso kiyi mun kafin ki fita,"

fashewa tayi da dariya har fararen hakoranta suka bayyana,duk a tunaninta wani abu mai muhimmanci ne yasa ya kirata,ashe kawai don ya tambayi murmushinta ne,shima dariyar yakeyi,kafin su fita daga cikin motar atare,


**************

Fitowarshi kenan daga wanka,yana cikin shirya kanshi cikin riga da wandon jeans,yaji an kwankwasa ƙopar ɗakinshi,daga muryarshi yayi tare da cewa"ƙopar a buɗe take,"yayi maganar tare da juyawa yana kallon mai shigowar,

  Cike da mamaki yace"Ya HAROON!kaine!dama kana nan,"

Shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da ƙarasa shiga cikin bedroom ɗin nashi yana cewa"Ina nan mana junaid,kaine ka manta dani,kowa ma ya manta dani,"

  "Ya haroon ba haka bane,wlh ni ban manta dakai ba,kana araina,"

  ta6e baki haroon yayi alokacin da yake tsayawa agaban junaid suna fuskantar juna yace"Ka ƙara kyau da haske,hankalinka kwance baka da wata damuwa,ba kamar ni ba,kullum cikin damuwa nake,zuciyata har nauyi takeyi mun saboda halin da nake ciki amma babu wanda ya damu dani,yau ko mutuwa nayi babu wanda zai damu,sae ma farin ciki da za'ayi,"

  Jin wannan maganar ta haroon yasa jikin junaid yin sanyi,wani irin tausayin shi ya kamashi,muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"pls Ya haroon dan Allah kadaina faɗin wannan maganganun,wlh bana jin daɗi,"

  "Junaid ƙarya nayi ne?an damu dani acikin gidan nan ne?kowa yayi watsi dani,babu wanda ke damuwa dani,tamkar bare haka nakeyin rayuwata,hatta azmee da take ƴar aiki acikin gidan nan ta fi ni muhimmanci tunda ita ana damuwa da ita,ni kuwa fa?

  Hawaye ne suka cicciko a idanun junaid,dama shi akwai tausayi,gaba ɗaya tausayin haroon ya kamashi,saboda duk abunda ya faɗi gaskiya ne,ba'a damu dashi ba,ko zancen shi ma babu maiyi acikin gidan,idan zai share wata a waje babu mai tambayar ina yaje,

  "Tamkar maraya ni fa haka nake acikin gidan nan,kalli kaga yadda na koma duk na rame saboda damuwa,gaskiya ni bazan iya cigaba da rayuwa ba junaid,zan kashe kaina ne kowa ya huta," yana kai ƙarshen maganarshi ya juya da sauri zai bar ɗakin,

  Da gudun gaske junaid ya rungumoshi ta baya tare da fashewa da matsanancin kuka yana cewa"Meyasa ya Haroon!pls stop saying that,banason jin kana zancen mutuwa,ko kowa bai damu dakai ba,Ni nadamu dakai,ko don saboda ni ya haroon kada ka aikata hakan,idan ka kashe kanka,nima bazan rayuwa ba,zan bi ka mu tafi tare,"

  Wannan kalaman na junaid ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya su kayi ba,cire hannunshi yayi daga ruƙon da yayi ma waist dinshi,sannan ya juya suna fuskantar juna yace"Junaid dagaske ne ka damu dani?kuma bakaso in mutu"?

  cikin shessheƙar kuka junaid yace"Eh ya haroon bana so pls,"

  Hannu haroon yasa yana share mashi hawayenshi,kafin daga bisani ya janyo shi ajikinshi tare da rungume shi sosai ajikinshi,kamar zai mayar dashi cikin shi,saitin kunnanshi yakai bakinshi tare da cewa"I love u so much junaid,cos you're so special,in dai zan kasance tare dakai bazan ta6a shiga wani ƙunci na rayuwa ba,kallon ka kawai zai iya sanya farin ciki a cikin zuciyata,daga yanzu inason ka zama abokina junaid,saboda ka dinga ɗebe mun kewa,muna fita yawo atare,don bani da aboki,nifa kowa gudu na yake yi,bansan meyasa ba,'ya ƙarasa maganar tare da janye junaid daga jikinshi,

  "Junaid!ka amince zaka zama abokina"?

Jinjia kai junaid yayi tare da cewa"Eh,na amince,amma dan Allah ya haroon kadaina zancen zaka kashe kanka,banjin daɗi banso pls,"

  "Shikenan na daina,daga yau kome kakeso ma zanyi,am sorry na sanyaka zubar da hawayenka,"

  "Ya haroon ni zanje nayi ma Abba magana akanka,nasan abba zai fahimce ni,"

  cikin sauri haroon ya ruƙo hannun shi tare da cewa"A'a junaid,just leave it,banason kowa yasan meke tsakanina dakai,kada kayi ma kowa maganata don ba lalle su fahimce ni kaman yadda kai ka fahimce ni ba,"

  "Shikenan bazan faɗa ba,"

"Yawwa junaid ɗina,Yanzu zan barka ka ƙarasa shiryawa,"

  Yana faɗin hakan ya juya tare da fucewa daga ɗakin junaid,ya koma bedroom ɗinsa,agaban dressing mirror ɗinshi ya tsaya yana ƙarewa fuskarshi kallo,

  A hankali wannan mugun murmushin nashi ya soma bayyana akan fuskarshi,fashewa yayi da dariya kafin daga bisani ya ɗaure fuskarshi,kalaman junaid ya shiga tariyowa,tuni jikinshi yayi sanyi,ta wani 6angaren ji yake tamkar bazai iya ba,amma bai da wata mafita daya wuce wannan!

  "Junaid kada ka damu zamu mutu atare,"ya faɗi hakan tare da komawa ya zauna daga gefen gadonshi,


Bayan junaid ya kammala shiryawa,saukowa downstairs yayi har lokacin jikinshi ba kwari,haroon ba ƙaramin tausayi ya bashi ba,A main palor ya samu Abbansu tare da Momnynsu  dasu Twins suna fira atsakaninsu,tunkararsu yayi fuskarshi ɗauke da murmushi,suna haɗa ido da Abbansu ya watsa mashi harara,sunnar da kai ƙasa junaid yayi da wurin Abban yaso ya fara zuwa amma wannan hararar da yayi mashi ce tasa ya fasa zuwa ya wuce wurin mommynsu,dukawa yayi tare da manna mata kiss kafin ya rungumeta,fuskarta asake tace"My romeo,"Amsa mata yayi da mommy,a lokacin daya koma wurinsu twins suna gaisawa,Jahan yace"Ina zuwa naga key ɗin mota a hannunka,"

"Zanbi su uncle ne," ayaan yace"Kada ka bari Mommy taji to,in ba haka ba bazata bari kabi su ba,"

    "Saboda me"?ya tambaya yana kallonshi,Jahan ne ya bashi amsa da cewa"Saboda bazata barka ba,idan ta tambayeka ina zaka je,sae kace mata gidan abokinka zakaje,"duk wannan maganar da sukeyi a kunnan abbansu saboda yana kusa dasu,kallonsu kawai yakeyi,juyawa junaid ya ɗanyi tare da satar kallon mommyn,idonta na akanshi hakan ya tabbatar mashi da cewar so take taji me suke cewa,'

  "Ka tafi kawai,"acewar ayaan,

  harya juya zai tafi ya tuna da Abbansu,dawowa yayi tare da zuƙunnawa agabanshi yace"Abba,"ɗaure fuska abba yayi batare da ya tanka mashi ba,

  "dan Allah kayi haƙuri abba in na 6ata maka rai,bazan ƙara ba,"

  Ta6e baki abba yayi tare da cewa"Junaid kenan,ae ni yanzu babu ruwana dakai,kafi ƙarfi na,"_

  Ashagwa6e ya kuma cewa"pls abba,kayi hakuri,ka manta da abunda ya faru jiya,bazan ƙara ba,"

    "Naji,tashi ka tafi,ka kulamun da kanka,"

  Murmushi junaid ya saki tare da mikewa ya manna mashi kiss a fuskarshi,sannan cikin sauri ya kama hanyar fita,

  "Junaid ina zuwa"? Jin muryar Momnynsu yasa shi dakatawa da tafiyar da yake yi,

   tsayawa yayi tare da juyawo ya kalleta,

   "Mommy gidansu abokina zani je,"

  "Kai da wa?waye zai kai ka?

Nuna mata key ɗin motarshi yayi kafin yace"Ni zan kai kaina,"

Jinjina kai tayi tare da cewa"Okey,u can go," da sauri ya fuce daga cikin gidan,

  Mayar da idanunta tayi akan abbansu tace"Dama inaso inyi magana dakai,wai meyasa kuka bar romeo yana Driving da kanshi?Also babu wani security guard dake tsaronsa,Shi kadae yake yawonshi,"

  Abba yace"Allah xai tsare mana shi,"

Alexandra tace"Nasan da wannan,Amma wannan babban ganganci ne,koda ace kowanne daga cikinsu zaiyi yawonshi batare da security guards ba,amma bai kamata ace kamar junaid ƙaramin yaro yana yawo shi kaɗae ba,ba wani tsaro atare dashi,Especially yadda kowa ya sanya mashi ido,gaskiya ni hakan bai kwanta mun araina ba!!"

shiru abbansu yayi yana nazarin maganarta,

  Jahan yace"Gaskiya Abba,maganar mommy gaskiya ne,yakamata ace junaid akwai security guards dake tsaronsa duk inda zaije,musamman a wannan yanayin da muke ciki,bibiyar rayuwarmu akeyi don kawai acutar damu,junaid kuma yafi kowa ƙaranta acikinmu,yana buƙatar security,"

  "Abunda nake ƙoƙarin fahimtar dashi kenan,"acewar mommnynsu,

  jinjina kai Abba yayi tare da cewa"hakane,zanyi wani abu akai',

   daga nan suka cigaba da tattauna a tsakaninsu,


*Boss Bature*


Tun bayan da Hayaam ta tura ma Aunty babba hotonsu hosana,bata samu damar duba hoton nasu ba,ko whatsapp ɗinta bata shiga ba,wayarma tana ajiye cikin bedroom ɗinta,Shirye shiryen zuwa walima kawai sukeyi,atare da hafsat suka fita saloon daga nan za'ayi masu ƙunshi,bayan nan kuma zasu biya Shopping mall,saboda siyayyar da tace zatayi ma Ƴa'ƴan uncle ɗinsu,basu suka dawo gidan ba sai wuraren karfe shida na yamma agajiye suka dawo,kowa ya wuce bedroom ɗinshi,Aunty babba na shiga ɗakinta,kai tsaye ta faɗa saman gadonta ta shiga sharar bacci,Hafsa kuwa saida ta fara yin wanka,ta canza kayan jikinta izuwa riga da skirt marasa nauyi,sannan ta fito falo ta kwashe shopping bags ɗin da suka bari a falo,takaisu ɗakinta,tana cikin dudduba kayan wayarta dake ajiye gaban mirror ta shiga ringing,hannu takai tare da ɗaukar wayar tana kallon screen ɗinta,ganin Sunan Aunty Hayaam ya bayyana akan secreen ɗin wayar,yasa ta ɗaga kiran tare da karawa a kunnanta,

  "Assalamu Alaikum aunty hayaam,'

Ko amsa mata sallamar batayi ba tace"Hafsat ina Aunty laila take ne?tun da sassafe na tura mata hoton bata duba ba,har nagaji da jira,"

  Hafsat tace"yanzu muka dawo daga kasuwa agajiye,tana a bedroom ɗinta ina jin bacci ne ya dauketa,ko inyi mata magana ne"?

  Hayaam tace"A'a,kawai idan ta tashi ki sanar da ita cewa na tura mata hoton ƴa'ƴan abusufyan ɗin,ta duba ta whatsapp ɗinta,"

  Wani irin farin ciki ne ya lullu6e hafsat,muryarta na rawa tace"hoton ƴa'ƴan Abusufyan dinmu!zan sanar mata kuwa,"

  Rejecting call ɗin tayi,da gudu ta fito daga bedroom ɗinta,kai tsaye ta haye upstairs ɗakin aunty babba,tura kopar ɗakin tayi tare da shigewa ciki,a kwance ta samu aunty babba saman gadonta sai sharar bacci takeyi,ga wayarta ajiye agefenta,

  Cikin sanɗa takai hannu tare da ɗaukar wayar,ta danna power ɗinta ta kawo haske,ganin akwai password yasa ta ɗan bubbuga kafarta tana cewa"Kai mommy,yanzu dole sae kin tashi sannan zan samu damar ganin hoton babies ɗinmu!gaskiya ni a ƙagare nake,"

  Tana cikin maganar,ta tuna da finger print ɗin dake akwai ajikin wayar,nan take zuciyarta ta bata shawarar cewar me zai hana,ta lalla6a ta hau saman gadon,ta dangwalo yatsan aunty babba,kota samu wayar ta buɗe,Good idea,ta furta hakan tare da lalla6awa ta hau saman gadon,cikin sanɗa ta ƙarasa inda aunty babbar take,hannunta ta ruƙo tare da sanya yatsan hannunta a wurin,ya rubuta mata wrong,haka ta dinga bin yatsun hannun aunty babba tana jarabawa,har sai da taci nasarar buɗe wayar,saukowa tayi daga saman gadon,ta tsaya atsaye,hannunta har kerma sukeyi wurin daddana wayar,tsoranta kar Aunty babba tafarka saboda tasan halin Mommyn nata,ta tsani wani ya ɗaukar mata wayarta,kamar mara gaskiya,

   Tana shiga whatsapp ɗinta,sai ga wani security ɗin,rai a6ace tace"Mommy kamar mara gaskiya,duk tabi waya ta garƙame da security,"

  Allah yaso shima finger print ne,komawa tayi tare da dangwalo yatsan aunty babba,whatsapp ɗin ya buɗe,

  Kaitsaye ta shiga chat ɗinsu da Hayaam,anan taga hoton da Hayaam ta tura mata,bai buɗe ba hoton saboda data a kashe take,cikin sauri hafsat ta kunna data ɗin,nan take yashiga loading yana ƙoƙarin budewa,a hankali hoton ya soma bayyana,ƙura ido hafsat tayi tana jiran hoton ya kammala buɗewa,

  Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu ji kake Daram!!Dararam!!tamkar ana buga ganga,Waro ido waje hafsat tayi agigice a matukar razane,tamkar wadda taga Zombie,hankali a matuƙar tashe tace"Kai!!!"

  Hannunta har kerma yakeyi wurin yin zooming ɗin hoton nasu ta matso dashi kusa don tagani dakyau,gaba ɗaya tagama kiɗima,wata irin zufa ce  ta soma tsattsafo mata agefen fuskarta,daƙyar take iya haɗiye yawun bakinta saboda maƙoshinta daya bushe ƙamas,juyawa tayi ta kalli Aunty baba dake ta faman mutsu-mutsu alamar zata farka daga baccin da takeyi,aikuwa cikin sauri tayi deleting ɗin hoton gaba daya,sannan ta rufe wayar,tayi wurgi da ita asaman gadon,jikinta na kerma ta fuce daga dakin,gudu gudu sauri sauri haka take tattaka stairs ɗin ƙiris ya rage ma tayi tuntu6e saboda yadda jikinta ke rawa kafkaf kamar wadda sanyi ya kama,

  Bedroom ɗinta ta koma,tana shiga ta aza hannu akai tana faɗin"Tashin hankali!In har dagaske ne abunda idanuna suka gane mun acikin hoton nan kenan hakan na nufin cewa HOSANA DA JAHAD Suna araye kuma suna a gidansu daddy!taya hakan ya faru?Kenan Ya Omar shine ya ɗaukesu?Ina wannan tsohon mutumin da mommy tasa ya kwashe su da nufin ya zubar dasu?Taya akai hosana da jahad suka kasance ƴa'ƴan uncle ɗinmu!?wacece ita ɗayar yarinyar mai kama dasu sak!dama su ƴan uku ne?Tabɗijancan,akwai matsala,

  Komawa tayi gefen gadonta ta zauna tare da kifa hannunta asaman fuskarta,hosana da jahad suna raye,suna gidan abban mu,wayyo Allah na,ina farin ciki sosai,duk da ina tsoran abunda zai biyo baya,Ashe jinina ne su!shiyasa akace rashin sani yafi dare duhu,mun cutar dasu sosai,mun zalunce su bayin Allah,mutuwa ce kawai batazo ta daukesu ba acikin gidan nan amma sunsha wahala,sun ƙuntata,tabbas Mommy mun shiga uku,idan Abba yaji,daga ni harke ba wanda zai tsira,kwara ni hukuncina mai sauƙi ne tunda na nuna masu soyayya daga baya amma ita mommy itace silar fitar dasu daga gidan nan don azubar dasu,Wayyo Allah na!,

  Yatsun hannunta sae faman kerma sukeyi,jiki na rawa ta ɗauki wayarta tare da lalubar numbar junaid ta danna mashi kira,

  A lokacin junaid yana tare dasu Uncle abusufyan,dama sai daya fara kiranshi a waya ya tambayi address ɗin inda suke ya bashi,har an kammala yi masu saloon tuntuni,anyi masu ƙunshin jan lalle a hannuwansu,daga can suka wuce shoprite siyayya,bayan sun kammala siyayyar,suka biya gidan Uncle ɗin nasu wuraren 6,saboda su kwaso wasu daga cikin kayansu Jahad da hosana wanda zasuyi kwalliyar walima dasu,

  A bayan motar junaid aka sanya trolley ɗin kayan nasu,sannan Sehrish da hosana suka shige motar abusufyan,jahad kuma ta shiga motar junaid,atare motocinsu suka fita daga cikin gidan,

  Tunda jahad ta shiga motarshi,ya ɗaure fuskarshi,dama tun wurin siyayyar yake ta shan mur yana murtuke mata fuska,amma hakan bai hana tayi masa magana ba,duk in ta ɗauko abu sai ta gwada mashi ta tambayeshi zaiyi mata kyau,daƙyar yake amsa mata da eh,ko a'a,sai dae kawai tayi murmushi ta girgiza kai,

    Kiran Hafsat na shigowa a wayarshi,yace"ki ɗauki wayar,ki amsa wayar sai ki sanyata a handsfree,"

   hannu jahad tasa tare da ciro wayar daga aljihun gaban rigarshi,picking call ɗin tayi bayan ta sanyata handsfree sannan tayi Mata sallama,

   Muryar hafsat ce ta karaɗe kunnansu"Junaid!kana ina ne"? Gaban jahad ne ya faɗi rass saboda jin muryar hafsat,duk da bata tabbatar da cewar ita bace,amma muryar tayi mata kama da ta sister hafsat,

  "Ina akan hanyar komawa gida ne yanzu hakan,"

   Hafsat tace"junaid dan Allah so nake in tambayeka,waɗannan yaran ƴa'ƴan uncle abusufyan Ƴan uku ne"?

  "Of course they are triplet,"ya bata amsa a yayin da yake ƙoƙarin juya sitiyarin motar,ya karya kwana,

  Hafsat tace"Ya sunan su"!

Juyowa yayi ya ɗan kalli jahad da idanunta ke akan shi,kafin ya mayar da idanunshi kan driving din da yakeyi,a jere ya ambaci sunayensu"Hosana Sehrish Jahad"!hafsat na jin haka,a gigice ta kashe wayar,

  "kiran ya katse,"Jahad ta faɗi tana ƙare ma wayar kallo,

  "May be network ne,idan na koma gidan zan kirata,"

   "In mayar maka da wayar"? 

  "A'a ki ruƙe a wurinki,idan mun isa gida zan kar6a,"

  ta amsa mashi da toh,

Gallery ɗinshi ta shiga tana kallon kyawawan hotunanshi da yayi,tare da videos,yawanci duk na ban dariya ne,wasu yana a kwance,wasu ya zullo harshe waje,wasu hotunan ya kashe idanunshi,

  Dariya ta dinga yi a yayin da take kallon videos ɗinshi na tiktok,duk yana sauraron sautin dariyarta,wani lokacin har satar kallon fuskarta yakeyi,ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,musamman inta tuntsire da dariya,wani sa'in hada kifa kanta saman laps dinta saboda tsabar dariya,murmushi kawai yayi tare da mayar da hankalinshi akan driving ɗin da yake yi,a haka har suka ƙarasa gida,


Bayan hafsat ta katse kiran,ta Kifa kanta asaman pillow ɗinta,tare da fashewa da wani irin matsanancin kuka,dama ance dana sani ƙeya ce,


Farkawa Aunty babba tayi da wata irin matsiyaciyar yunwa,sae faman hamma takeyi,tashi tayi daga zaune tare da kai hannu ta ɗauki wayarta tana cewa"Ko hayam ta tura mun da hoton?bari na duba na gani,Allah yasa dai bata manta ba,"

  shiga cikin whatsapp ɗinta tayi tare da duba chat ɗinsu da hayaam,rai a6ace taja dogon tsoki tare da cewa"Wai dama bata turamun hoton ba!harfa ƙara nanata mata nayi akan ta tura mun hoton amma bata turo ba," ta ƙarasa maganar tare da yin wurgi da wayar saman gadon,

  Saukowa tayi daga saman gadon,fita tayi daga cikin bedroom din ta sauko ƙasa,kai tsaye ta nufi kitchen,

  Batare da 6ata lokaci ba,ta shiga harhaɗa kayan da zatayi amfani dasu,bayan ta ɗaura girkin,ta ɗebo snacks a plate ta haɗo da coke mai sanyi ta dawo falo,ta zauna,tana ci tana kallo a plasma hankalinta kwance,


jin motsin mutun a gefenta yasa tayi firgit tare da juyawa don taga wanene,ashe hafsat ce atsaye yanayinta kamar na wadda tayi amai da zawo,fuskar nan tayi gwanin ban tausayi,idanunta sun ƙankance saboda kukan da tasha,

  "Hafsat!lafiya naga fuskarki tayi jawur?kinyi kuka ne"?

  Girgiza kai hafsat tayi tare da cewa"Babu komai mommy,wani film nake kallo acikin wayata,shine ya sanya ni kuka,"

  Tsoki Aunty babba taja"shirmen banza,kawai daga kallon film saiki kama kuka kamar wata sakarya,"

  murmushin takaici hafsat tayi tare da samun wuri daga gefen aunty babba ta zauna,batare da tace komai ba,

   Aunty babba taci gaba da cewa"gaskiya kowane film ne wannan ya ciri tuta tunda har ya iya sanyaki zubar da hawayenki,yadda kike da shegen taurin kai,

    "Mommy ba zaki gane bane,"

"Taya za'ae in gane?tunda bakiyi mun bayanin meya faru ,acikin film ɗin ba,ki ɗan bani labari mana,"

  Gyara zama hafsat tayi kafin ta soma bata labarin kamar haka"wata matace fa,mijinta ya kawo mata wasu marayun yara donta rainesu a wurinta,tun ranar da mijin ya kawosu gidan shi kuma yayi tafiya,ae kuwa matar nan,ta shiga gana masu azaba,ta hanasu abinci yunwa kamar zata kashesu,har bugunsu takeyi,sannan kuma ta dinga sanyasu aikin wahala,har saida suka kusa rasa rayuwarsu,mommy kinsan meya faru"?

  Dakatawa Aunty babba tayi daga shan lemun hannunta da takeyi tace"a'a saikin faɗa,"

  "Hmmm,Mommy ƙarshe fa matar nan,tasa aka kwashe yaran nan,aka 6atar dasu saboda kawai kar asirinta ya tonu a wurin mijinta...'

  "Hakan da tayi yayi mun dai dai,"Acewar aunty babba,

Murmushi hafsa tayi kamin tace"Ae ban ƙarasa maki labarin film ɗin ba,bayan tasa an zubar da yaran nan,ita duk a tunaninta sun mutu ma,Ashe can wurin gararin rayuwar da sukeyi a daji Allah ya haɗasu da kanin mijinta har ya taimakesu ya kaisu gidansu mijin,da akayi bincike aka gano cewar yaran ƴa'ƴan kawunsu ne wato ƙanin mahaifinsu,"

  Aunty babba tace"tashin hankali!ita ko wannan ya zatayi da kanta?

  Dariya hafsat tayi tare da cewa"Nima abunda nake tunani kenan!amma Mommy idan kece ya zakiyi,"

  shiru Aunty babba tayi tana tunani kafin daga bisani tace"Ae kawai tunkan asirina ya tonu zan gudu ne,a neme ni arasa,amma nikam hafsat wai ya sunan Film ɗin nan ne?tayi tambayar tare da kallon hafsat ɗin wadda itama kallonta takeyi,mikewa hafsat tayi tsaye tare da cewa"An fara kiran sallar magriba,bari naje nayi salla,"

  "Amma baki faɗamun sunan film ɗin ba!"Aunty babba ce ta sake nanata mata tambayar da tayi mata,

    *AN YANKA TA TASHI* shine sunan film ɗin mommy,yanzu na kalleshi a tashar youtube,tana kai ƙarshen maganarta,ta juya da sauri ta wuce bedroom ɗinta,

  Zugudum Aunty babba tayi tana maimaita sunan film ɗin da hafsat ta faɗa mata,wato An yanka ta tashi,

  Aranta tace"gaskiya ya kamata in kalli film ɗin nan,Inaso inga yadda matar nan zata ƙare,ko ya mijinta zaiyi da ita?tabɗijancan,akwai badaƙala,"tayi maganar tare da mikewa ta wuce kitchen domin ta duba girkin da ta ɗaura,


Bayan ta kuma fitowa daga kitchen ɗin,upstairs ta wuce bedroom ɗinta,gefen gadon ta zauna tare da miƙa hannunta ajikin drawer chest ta janyo gidan farko,sabon sim ne ta ɗauko tare da daukar wayarta dake ajiye saman gadon,zura sim card ɗin tayi aciki,sannan ta lalubo lambar wayar Ammi wadda tayi copying kan phone,danna mata kira tayi,nan take kiran ya shiga,kusan sau uku kiran na katsewa batare da anyi picking ɗinsa ba,tana kira a karo na hutu Ammi ta ɗaga kiran 😳


ɗan zaro ido Aunty babba tayi kafin ta gyara natsuwarta tare da zabga sallama"Assalamu Alaikum Ammi barka da warhaka,"ta maƙe muryarta yadda ammi bazata iya gane muryar wacece ba,

  on the other hand Ammi ta amsa mata da cewa"Wa'alaikumus salam,barkanki dai,zan iya sanin dawa nake magana"a dake take magana,

Aunty babba tace"Nasan bakisan dawa kike magana ba,saboda baki sanni ba,Ni matar abokin Abusufyan ce,wadda ke zaune a ƙasar turkey,"

  Shiru ammi tayi tana sauraran me magana,

  Aunty babba taci gaba da cewa"akwai wani mummunan abu da abusufyan ya aikata a 6oye baison kowa ya sani,shiyasa na kira don in sanar dake,don banason abunda zai ta6a mutuncin family ɗinku,wannan abun kunya ne,muddin ya fita waje mutane sukaji to fa,zaku rasa duk wata ƙima da martaba da kuke da ita....'

  tana cikin magana Ammi ta dakatar da ita"Ya isa haka!banason wata kwanana,ki faɗamun abunda kikeson sanar dani!me Abusufyan ya aikata?wani laifi ne wannan da har kike ikirarin zai ta6a ƙimar family ɗinmu a idon jama'a,"?

  Wani irin wahalallen yawu aunty babba ta haɗiye kafin daƙyar ta soma kora mata jawabi kamar haka

   "Shekarun baya da dadewa,Abusufyan yayi ma wata fyaɗe,harta samu ciki....."

  Wata irin tsawa da Ammi ta daka mata har sae da takusa sakin fitsari a wando,a tsiwace tace"Dakata!ki iya bakinki!kinaso ki shiga tsakanina da ɗana ne!wacece ke,kada kiyi tunanin kin kirani da 6oyayyiyar number,zan iya sa agano munke duk inda kike,"

  Muryar Aunty babba na kerma tashiga faɗin"wlh dagaske nake ammi ba ƙarya nake ba,gobe idan kinzo abuja wurin walima,zaki ga yaran,ae suna nan gidan Abba,Sun jima suna 6oye maki gaskiya,saboda tsoron hukuncin da zaki yanke ma Abusufyan,yanzu haka maganar da nake maki,sun gama shirya yi maki ƙaryar cewar yaran ba shaggu bane ta hanyar aure aka haife su bayan ba haka bane,suna nan yaran ƴan uku ne mata,sun girma sosai,' tana kai ƙarshen maganar Ammi tace"Kin gama"?

  Shiru Aunty babba tayi tana faman mazurai aranta tace"Wannan tsohuwa badae taurin kai ba,bansan ya zanyi na fahimtar da ita ba,ta cika jaraba,"

  tana cikin wannan zancen zucin Ammi ta katse kiran,

  Wurgi Aunty babba tayi da wayarta,tare da mikewa tana cewa"Ae shikenan,nasan cewa gobe tana ganin yaran zata tuna da kalamai na,daga nan saita ɗauki hukuncin daya dace,"


❤🤍❤


*Boss Bature*


Zaune yake asaman Sofa mai mazaunin mutun uku,gaba ɗaya ya tattara hankalinshi akan Laptop ɗinshi da yake daddawana anatse,jikin shi na sanye da linen tank top,blue colour tabi shape din jikinsa,sick pack din nan nasa ya bayyana ajikin rigar,trouser ɗin jikinsa kuma white colour ne,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga kowani sashe na jikinsa,


Shigowa Azmee tayi part ɗin nasa da sallama a bakinta,yayin da hannunta ke ruke da tray,amsa mata sallamar yayi batare daya ɗago ya kalleta ba,ƙarasawa azmee tayi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman empty table din dake a gefenshi,hannu takai tare da ciro plate ta daukko serving spoon tana ƙokarin buɗe warmer,muryarshi ta katse mata hanzarinta da cewa"ɗazu da safe meyasa kika kawomin breakfast?kuma kika gyaramun bedroom ɗina,dama kece ke gyara mun part ɗina ne"?

  gabanta ne taji ya faɗi rass,muryarta na kerma tace"A'a bani bace,Sehrish ce,"

  "Meya hanata yi mun aiki,"?yana magana yana danna laptop dinsa har time ɗin bai ɗago da idonshi ba ya kalle ta,

  Azmee tace"Am...um...dama..."bata ƙarasa maganar ba,ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannunshi,cikin sauri ta shiga taitayinta,

  Cike da bada Umarni yace"Call her right now,"

  Jiki na rawa azmee ta juya tare da fucewa daga part dinsa,downstairs ta saukko,babu kowa a falon duk suna a bedroom ɗinsu,wasu ma sunyi bacci,

  Kai tsaye ɗakinsu Sehrish taje,tsayawa tayi abakin ƙopar ɗakin tana kwankwasawa,sai faman knocking takeyi amma ba'a buɗe mata kopar ba,da alama sun jima da yin bacci,

  Har sae da ta fidda rai da za'a buɗe mata kopar,tana kokarin juyawa tabar wurin,taji alamun za'a buɗe kopar,Jahad ce ta buɗe ɗakin tana tambayar wanene,

  Ganin azmee yasa tayi saurin gaishe da ita cikin girmamawa,

  Azmee da nan take ta gane ba sehrish bace tace"kiyi hakuri na tashe ki kina bacci,Sehrish nake nema,dan Allah ki sanar da ita cewa SGR yana nemanta a part ɗinsa,"

  Jahad tace"tayi bacci,bari na tashe ta,"tayi maganar tare da juyawa cikin sauri ta shiga cikin ɗakin,

Wucewa azmee tayi ta koma kitchen,cike da zullumin mai zai biyo ba idan Sehrish ta sanar ma Sgr cewa Uncle abusufyan ne ya hanata yin aiki a part ɗinsa,tabbas za'a kwashi ƴan kwallo,


"Sehrish!ki tashi babban yaya yana son ganinki a part ɗinsa,dan Allah ki tashi kije,"jahad ce keta kokarin tashinta daga bacci,sehrish kuwa sai faman mutsu mutsu takeyi,daƙyar ta iya cewa"Wanene ke nema ne'?

 Jahad tace"babban yaya,"

Jin sunanshi yasa Sehrish buɗe idanunta ta wurgasu kan jahad dake tsaye,yatsina fuska tayi tare da maimaita sunan nashi"babban yaya?shike nema na,waya faɗa maki"?

 "Aunty azmee,yanzun nan bata jima da tafiya ba,naga kamar ma bata acikin natsuwarta,"

  Jin hakan yasa gaban sehrish faɗuwa rass,yunkurawa tayi tare da mikewa zaune,ta saukko da ƙafafunta ƙasa,kafin ta miƙe tsaye,saboda tsabar saurin ta fita ko Mayafi bata ɗauka ba,gashi kanta ko kallabi babu,sumar kanta ce da tasha gyara,an mayar mata da gashin mai gazar gazar ya sauko har kafaɗarta,a hankali gashin kan nata ke toho yana fitowa,har ta launin gashin anyi mata dying dinsa ya koma 2 colour,Kayan bacci ne ajikinta riga da wando sharara suke,farare masu laushin gaske,irin waɗanda kana sanyasu ajikinka,Ko baka jin bacci nan take zai zo maka,

  Tunkan ta ƙarasa shiga falon nashi take jin ɗar ɗar acikin zuciyarta,tun jiya rabon da ta sanyashi acikin idanunta,daƙyar ta iya yi mashi sallama tare da kutsa kai cikin falon nashi,bai amsa sallamarta ba,har ta ƙarasa inda yake,atsaye muryarta na rawa tace"Gani,"bai dago ba kuma bai tanka mata ba,sae ma cigaba da danna system ɗinshi da yake yi,lokaci bayan lokaci yakan kai hannunshi ya dauki Coffee ya kur6a,zuba mashi ido tayi tana kallon kyakkyawar fuskarshi,ba ƙaramin kewarshi tayi ba,sam batayi tunanin ma zai nemeta ba,

  sai da ta ƙara cewa"babban yaya gani,Aunty azmee tace kana kira na,"sannan ya soma magana anatse"yau da safe,meya hanaki zuwa part ɗina"?

  Shiru tayi gabanta na faɗuwa,batasan amsar da zata bashi ba,saboda tsoran abunda zai biyo baya,

  "Kinsan bana maimaita magana,amsarki nake jira,"

  Runtse idanunta tayi aranta tana fadin"nashiga uku,!Allah ka kawomin ɗauki,bansan me zan faɗa masa ba,"shirun da tayi mashi ne ya fusata shi,aikuwa a zafafe ya daka mata tsawa,har sai da ta zura da gudu saboda yarda ta tsorata,kama hanyar fita tayi saboda ruɗewar da tayi,hakan yasa ya miƙe tsaye tare da bin bayanta,ruƙo hannunta yayi tare da fusgota ta dawo saitin shi,Waro ido waje tayi tare da ja da baya da baya,har suka ƙure ma bangon,runtse idonta tayi muryarta na kerma tashiga faɗin"Am so sorry babban yaya,I can explain,zan faɗa maka,"

  A hankali ya ware blue eyes ɗinshi akan fuskarta,sumar kanta yabi da kallo,yayi mamakin ganin yadda gashin yayi tsayi cikin ƙankanin lokaci har ya kamo kafaɗarta,gyaran gashin da akayi mata ya ƙara fiddo da kyawun fuskarta,mayar da idanunshi yayi akan La66anta dake ta faman kerma duk tabi ta gigice,lokaci guda ya tsinci kanshi cikin wani irin yanayi mara misaltuwa,moving ya ƙarayi gaba ɗaya yayi mata rumfa da faffaɗan ƙirjinshi,lokacin da taji tsinin hancinshi na gogar nata,nan take gabanta ya kuma bugawa daramm,jikinta ya shiga yin kerma ta ko'ina,gaba ɗaya duk tabi ta susuce har lokacin ta gaza buɗe idanunta saboda tsabar tsoro,jin saukar hannunshi asaman ƙirjinta yasa ta yin saurin ware idanunta arazane,kai tsaye suka sauka cikin nashi,face to face,Eyes to eyes,nose to nose,mouth to mouth!!,

   A firgice ta janye idanunta daga kan fuskarshi ta mayar dasu akan ƙirjinta,Ashe gaban rigarta ne ta bari a buɗe ta manta bata sanya links ɗin rigar ba,Shine ya sanya hannunshi a wurin yana manne mata su,jurewa kawai takeyi amma ba ƙaramin yanayi Sgr ya jefa mata ba,musamman yadda hannunshi ke nutsewa a cikin boobs ɗinta,ba ita kaɗae ba,hatta shi kanshi daya kai hannunshi wurin saida yayi regretting,saboda wani abu daya dinga jin yana fisgarshi yadda kasan magnet,mayen karfe ba,

  daƙyar ya iya zame hannunshi daga saman ƙirjin nata,bayan ya kammala sanya mata links ɗin,Sannan cikin sanyin murya yace"tell me the reason why baki zo yi mun aiki da safe ba!bakisan bana son sharing a aiki na ba!?

  Magana yakeyi amma idanunshi sae ƙokarin lumshewa sukeyi tamkar mai jin bacci,wanda kuma ba kowa ne yajawo hakan ba face Sehrish,

   Cikin en ena tace"Kayi haƙuri ba laifina bane,Daddy ne ya hanani zuwa"

  Cike da mamaki yace"Kina nufin Uncle ne ya hanaki zuwa,"

  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,yayin da take ta faman haɗiyar yawu,

. "just without any reason ya hanaki aiki a ƙarƙashi na"?

   daga mashi kai tayi alamar eh,

Cije pink lips ɗinsa yayi tare da tsoma hannunshi acikin sumar kanshi yana cakuɗata,ranshi a matuƙar 6ace yace"hakan bazai ta6a yiyuwa ba,dole kiyi aiki a ƙarƙashina!ban damu da matsayinshi a wurinki ba,dole ne ayimun biyayya!!!!!!!!*


   *Tashin hankalin da ba'a sama shi date!*


Gobe walima,suwa suka shirya zuwa💃💃💃💃


  *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃



*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI.  MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*



*LOCATION KANO*


08062073990


Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku



Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku


It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.

Snack

Awarah 

Farah

Zobo

Samosa

Cup cake etc 

Contact me 09063302182or 09012179727.

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




Ranshi a matuƙar 6ace yace"hakan bazai ta6a yiyuwa ba,dole kiyi aiki a ƙarƙashina!ban damu da matsayinshi a wurinki ba,dole ne ayimun biyayya!!!!!!!


Waro ido waje Sehrish tayi tana kallonshi,hankali atashe jikinta sai faman kerma yakeyi,ji take tamkar ta zura da gudu,saboda yadda taga Sgr ya fusata tsoranta kar ya ciro belt ɗin wandonsa ya rufe ta da bugu,tana cikin wannan zancen zucin muryar shi ta katseta da cewa"listen to me!"

Natsuwa tayi tana sauraronshi kamar yadda ya Umarta,

  "Banaso na ƙara ganin Azmee tazo part ɗina da sunan za tayi mun aiki,ke nakeso ki kawo mun breakfast sannan ki gyaramun part ɗina,hope u understand?"

  Muryarta har kerma takeyi wurin cewa"E zan..na..fahimta,'

  Jinjina kanshi yayi tare da cewa"Okey,yanzu kizo kiyi serving ɗina,then idan kin kammala ki gyara mun bedroom,"babu wasa a fuskarshi yake yin maganar,wato yadda ya tsare Sehrish yadda kasan ƴar cikinshi,ta yi tsuru tsuru,Ni dai bansan ya Sehrish zata ƙare ba,ga umarnin mahaifinta gana kuma yayanta mai matukar tsauri,shin wa zatayi ma biyayya?a sanin mu dai Umarnin Mahaifi shine sama da komai,bayan na mahaifiya,bari mu gyara zama muga yadda wannan Al'amarin zai kaya,


Ja da baya yayi tare da juyawa ya koma saman sofa ya zauna sannan yace"Am waiting for u,"

Jiki asanyaye Sehrish ta ƙaraso inda yake,yatsun hannunta sae kerma sukeyi,a haka ta shiga serving ɗinshi,a plate ta zuba mashi chicken pepper soup ta tura mashi agabanshi,yana ci tana satar kallon fuskarshi,ba ƙaramin mamaki Sgr yake bata ba,ta jinjina ma ƙarfin halinsa na yau,batasan me zai faru gobe ba amma tabbas akwai badaƙala,


Bayan ya kammala cin dinner ɗin nashi,sai da ta gyara mashi bedroom ɗinshi,sannan ta samu ta fito daga part ɗinsa da kayan abincin,a hankali take taka stairs ɗin,ranta a jagule ba don komai ba sai don karya umarnin mahaifinta da tayi,wanda kuma ba komai ne yaja hakan ba face shegen tsoron Sgr da takeyi,da ba don haka ba,da ba abunda zai hana tayi mashi gardama,don a yadda yake da bad temper ɗin nan ta kuskura tace zatayi mashi jayayya,bugu zai kai mata,zuƙunnawa tayi asaman steps ɗin benen tana faman cizon la66anta,a hankali ta furta"sae yaushe ne zan fita daga wannan KURKUKUN ƘADDARAR da nake ciki?yaushe ne abubuwa zasu fara tafiya dai dai arayuwata?daga wannan sai wannan"? Idonta cike tab da hawaye tayi maganar,kafin ta yunƙura tare da miƙewa ta nufi bedroom ɗinsu bayan ta kai kayan kitchen,a hankali ta tura ƙopar tare da shigewa ciki,bayan ta datse ƙopar ta juya,mamaki tayi ganin jahad ruƙe da wayarta a hannunta ta ƙura ma screen ɗin wayar ido,duk a tunaninta zata zo ta same ta tayi bacci,ashe bata koma bacci ba tun bayan da Azmee ta tashe ta,


Ƙarasawa tayi tare da hayewa saman gadon a gefenta ta zauna,cike da mamaki take kallon jahad,ganin ko motsi ba tayi,bama tasan ta shigo ɗakin ba,ko menene yaja hankalinta haka?

  "Jahad!"Sehrish ce ta ambaci sunanta,a firgice ta juyo tana kallonta,ganin sehrish yasa ta sakin murmushi tare da cewa"Har kin dawo,ae nayi tunanin acan zaki kwana,"

  dariya sehrish tayi tare da dungurin goshinta tace"Abun hada tsokana,Nima nayi tunanin zanzo na same ki,kina bacci ashe idonki biyu,me kike yi da wayar ne"?don naga gaba ɗaya yaja hankalinki,"

  Ƙayataccen murmushi jahad ta saki tare da cewa"Hmmmm ba zaki gane bane,wani zazzafan hausa novel ne nake karantawa acikin wayarki,dama jira nakeyi kizo in tambayeki a ina zan samu cigaban littafin"?

  Cike da mamaki Sehrish tace"Novel kuma?ae ni bana karatun littafin hausa,banma san ya akai kika samu littafin a wayata ba,don gaskiya bana ajiye su,"

  Wani kallon rainin wayau jahad tayi mata tare da cewa"Kina nufin duk haɗuwar littafin nan baki ta6a karanta shi ba!hakanan kike ajiyar shi acikin wayarki?

  Yatsina fuska Sehrish tayi tare da cewa"nifa bansan dashi ba,may be cikin friends ɗina na makaranta ne wata wurin tura ma wasu ta turamun shi batare da sani na ba,"

  jinjina kai jahad tayi tace"gaskiya an barki a baya,tunda uwata ta haife ni ban ta6a karanta littafin me shegen daɗi irin wannan ba,tunda na fara karantashi bakina ke awashe,kamar anyi mun albishir da gidan aljanna,"ta karasa tana daria,

  Ta6e baki sehrish tayi tare da cewa"Wai ya sunan Littafin ne?naji sai faman zuzuta shi kike yi,inaso inji sunanshi ne saboda tun daga kan sunan littafi ake tantance in mai daɗi ne ko mara daɗi,"

  Ƙayataccen Murmushi jahad ta saki tare da Furta sunan Littafin*A SANADIN MAKWABTAKA*!

  Maimaita sunan Sehrish tayi"A sanadin makwabtaka"

  Jahad tace"kwarai kuwa,sunanshi kenan,"

  Gyara zama sehrish tayi tare da cewa"kawo wayar mu gani,zan jaraba karanta one page naji ya daɗinsa shin yakai Abban sojoji da nake jin friends dina nata faman cewa ya hadu"?

  Jahad tace"Ae ya zarce nan,"tayi maganar tare da miƙa mata wayar tace"one page kika ce zaki karanta,zan jira ki kammala don inci gaba daga inda na tsaya,"

   Hannu sehrish tasa tare da kar6ar wayar,ta buɗe page ɗin littafin asanadin makwabtaka,a natse ta fara karantashi,"

  Zuba mata ido jahad tayi tana jira taga reaction ɗinta,

  a hankali murmushi ya fara bayyana akan fuskar Sehrish,daga ƙarshe ma ta fashe da dariya,tunda tafara karanta littafin sae faman zabga murmushi takeyi,ita da tace zata karanta one page sai gashi ta zarce page biyar,ganin abun ya wuce gona da iri yasa jahad sanya hannu ta kar6e wayar tana cewa"Ya isa haka,je ki kwanta,gobe akwai shirye shiryen waleema,"

  ɗaure fuska sehrish tayi tare da cewa"wlh baki isa ba,sai da kika fara ɗanɗana mun zuma abakina na lasa daga baya kuma kizo kice zaki hana ni"?

    itama jahad ɗin ta tamke fuskarta tace"ae ni na fara karantawa tun farko,ke da bakisan ma da zaman littafin acikin wayarki ba sai da na faɗa maki"

  wurga mata harara sehrish tayi tare da miƙa mata hannu tace"Bani wayata,"

  Jahad tace"wlh bazan bada ba,sai na kammala karanta littafin nan,"

  Abu kamar wasa suka shiga cece kuce,ran sehrish yayi mugun 6aci,aikuwa ta cakumi wuyan rigar jahad,nan fa suka shiga kokowa asaman gadon kamar ƴan wrestling,wani bugu da Sehrish takai ma jahad a kumatunta ne yasa ran jahad ya 6aci,a fusace tayi wurgi da wayar Sehrish,kai tsaye ta faɗi saman tiles,ta daku sosai ji kake taratssss!screen ɗin wayar ya tarwatse,

  Tashin hankali,

la66an sehrish har kerma sukeyi wurin cewa"kika fasa mun wayata"?

  Girgiza kai jahad tayi hankalinta a matuƙar tashe tace"dan Allah sehrish kiyi haƙuri,wlh bada sanina nayi hakan ba,raina ne ya 6aci saboda naji zafin bugun da kikai man"

  Hawaye ne suka cika idon Sehrish cikin murya kamar ta mai son yin kuka tace"Ni babban baƙin ciki na,ba wayar data fashe bane,nasan daddy zai iya canzamin wata,Amma littafin fa?a ina zan same shi,daga ji zai dauke ma mutum damuwa yasa shi nishadi"? 

   Jahad tace"Am so sorry sehrish,na maki alƙawarin cewa,zan nemo maki shi,nasan baza a rasa me shi ba,akwai wata class mate ɗina sunanta hafsat bature,ta kware wurin karanta littattafan hausa,insha Allah idan muka koma school zan tambayar maki ita,nasan bazata rasa littafin a wayarta ba,idan ma babu littafin to ina da tabbacin cewar tasan marubuciyar shi,sae ta bamu numbar wayarta,"

  Jin haka yasa sehrish sakin murmushin jin daɗi,matsawa tayi tare da rungume jahad tace"yawwa jahad,kinyi tunani mai kyau,nagode sosai,yakamata mu kwanta yanzu,dare yayi fa sosai,"

  tayi maganar ayayin da ta gyara kwanciyarta,itama jahad ta kwanta,atare su kayi addu'ar bacci cikin ƙanƙanin lokaci baccin ya ɗaukesu,


"Nagode sosai da shawarwarin daka bani,kuma insha Allah ina da tabbacin cewar in muka biyo mashi ta wannan hanyar zamuci nasara akanshi,abun zai zama tamkar wasan kwaiwayo," Acewar Abbansu junaid dake tsaye a bakin ƙopar fita daga ɗakin Uncle abusufyan,Uncle ɗin na a bayanshi fuskar kowannansu ɗauke da murmushi,da alama sun kammala tattaunawar da sukeyi,


"Nike da godiya yaya Hossain,idan har wannan abun ya tabbata,zanfi kowa farin ciki,"


Juyowa Abba yayi cike da zolaya yace"kada ka manta,gobe ne fa sunan ƴan ukun da aka haifa maka,me zaka yanka masu"?

..sunnar dakai ƙasa Abusufyan yayi yana dariya,yace"Sa za'a yanka masu guda uku,raguna uku,ɗawisu guda uku,ƴan shila guda ɗari uku,kaji guda ɗari uku suma,"

   Dariya Abba yayi yana bubbuga kafadarshi yace"Abun ya ƙayatar dani wato komai guda uku kenan za'a yanka masu,idan ma ba uku ba to ɗari uku,dole dae ukun ta fito kamar yadda suke ƴan uku,a ƙagare nake da goben nan tayi,bari na hanzarta zuwa na kwanta,"

  "Allah ya nuna mana ita lafiya,"acewar abusufyan daga haka Abba ya bude kopar tare da fucewa yana faɗin"mu kwana lfy,"

   Bayan fitarshi,Abusufyan ya koma tare da hayewa saman katafaren gadonshi,yayin da idanunshi ke fuskantar ceiling,bakomai ne ya faɗo mashi aranshi ba face ABU,a kullum cikin tunanin wani hali take ciki yake,haƙiƙa ya damu da ita sosai,kusan kullum ne sai yayi mafarkinta,dama da yawa idan ka sanya abu aranka,zaiyi wuya bakayi mafarki akansa ba,babban abunda yafi damunshi duk in zai ganta a mafarkin cikin wani irin mawuyacin hali,

  "Bakomai ne yasa na damu sosai akanta ba,face sanin cewa ita marainiya ce,bata da kowa a duniyar nan wanda zai damu da ita idan bani ba,da kuma ƴa'ƴan data haifa ba,Abu bata da kowa bata da wanda zai neme ta idan wani mummunan abu ya faru da ita,da ace ƙaddara bata haɗani da Abu ba harna aureta ba,a yau akace ta 6ace,nayi imanin cewa babu wanda zai damu akan hakan,mahaifinta ne kawai shi kuma Allah yayi mashi rasuwa,Allah yajiƙanka baba buzu,haka ya damƙa mun amanarta,duk da yasan halina bana jin magana ga ƙuruciya dake fusgata,yayi mun halaccin da bazan ta6a mantawa ba,kuma Insha Allah zan ruƙe mashi amanar daya bani,bazan ta6a mantawa dashi ba,saboda shine silar komai,gashi har nasamu ƙaruwar ƴan uku tare da ƴarsa,naso ace yana raye nasan zaifi kowa farin cikin ganin jikokinsa,'

  Hawaye ne suka soma gangarowa daga cikin idanuwansa masu ɗumin gaske,murmushin takaici ya saki tare da gyara kwanciyarshi,ya runtse idanunshi daƙyar bacci ya ɗauke shi,


A 6angaren Abba kuwa,bayan sun rabu da Uncle abusufyan,yana shiga bedroom ɗinshi,ya tsaya turus ganin junaid kwance yana sharar bacci,ga mommynshi agefe tana bacci itama,girgiza kai yayi tare da cewa"bansan meyasa junaid keyi mun haka ba,ya raina ni wlh,"juyawa kawai yayi tare da fucewa daga bedroom ɗin ya koma upstairs bedroom ɗin junaid ya nufa ya kwanta,ya ƙyale shi ne saboda yana cikin farin cikin gobe walima,baison abunda zai 6ata ranshi,


Wuraren ƙarfe 2 na dare junaid ya farka sakamakon zungurar shi dayaji anyi da sanda,a firgice ya tashi zaune yana faman zazzare manyan idanunshi masu ɗauke da bacci,ƙasa ƙasa yaji ana ambatar sunanshi Junaid!junaid!aikuwa a tsorace ya sanya hannunshi tare da toshe kunnanshi ya fasa uwar ƙara,kai tsaye sautin ƙarar daya saki ta daki dodon kunnan Alexandra,a firgice ta farka,ganin junaid da tayi a zaune jikinsa sai kerma yake yi hakan yasa ta miƙe tare da janyoshi jikinta tana faɗin"junaid!romeo ɗina what's wrong with u?baka lafiya ne,"duk tabi ta tsorata da halin da yake ciki,

..Muryarshi na kerma yace"Mommy,wani abu zai faru dani,dan Allah ki taimaka mun,banso in mutu yanzu,"

  Jin wannan maganar ta junaid ba ƙaramin tayar mata da hankali tayi ba,kankame shi ta ƙarayi muryarta na rawa tace"Junaid,kadaina faɗin haka banason ji,babu abunda zai faru dakai indai kana tare dani,nasan cewa mafarki kayi,pls calm down ur mind,mu koma mu kwanta,

  ɗagowa yayi daga jikinta,cikin shessheƙar kuka yace"Mommy dan Allah,ki tashi muyi sallah,sai kiyimun addu'a,"

   a ruɗe tace"Salla kuma junaid,am not a muslim bana sallah,zan daiyi maka addu'a,"

   "A'a mommy nidai ki tashi muyi sallah,kiyimun addu'a,"Ashagwa6e yayi maganar,

  "Junaid ka fahimce ni,bakasan cewa niba musulma bace!ko daddynku bai ta6a faɗa maka bane,Ni bana sallah,I don't even know how to do it,"

  Jin haka yasa junaid sake fashewa da wani sabon kukan mai sautin gaske yana cewa"Mommy ki tashi muyi sallah,ki tashi mommy!wlh idan baki tashi munyi sallah kinmun addu'a ba mutuwa zanyi,"

  Tashin hankali,gaba daya junaid yabi ya rikice mata ya hanata sakat,duk yadda taso ta fahimtar dashi akan cewa ita ba musulma bace,bata sallah amma abun ya faskara,junaid ya kurmance mata,

  Babu arziƙi ta amince zatayi sallar,tasata gaba yayi ta shiga toilet ta dauro alwala,ko alwalar bata wani iyaba,ruwa kawai ta watsa a fuskarta,ta wanko hannayenta da kafafuwanta tafito,shi ma ya shiga cikin toilet ɗin,wucewa tayi wurin wurin closet ɗinsu,ta buɗe kayan Abbansu ne a jere sai kayan sawar ta,wanda tazo dasu,gaba daya babu hijabin da zata sanya,dakyar ta samu wani mayafin doguwar rigarta mai ɗan tsayi,ta ɗauko shi tare da sanyashi ajikinta,sae yayi mata tamkar hijabi,

  tsayawa tayi tana jiran junaid ya fito suyi sallar,lamarin nashi ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,ƙiri ƙiri junaid yasata za tayi sallah,ya rufe idonshi ya nuna tamkar baisan cewa ita ba musulma bace,aranta tace"Anya junaid bai samu ta6in hankali ba?in ba haka ma meyasa zai yi forcing ɗina akan inyi salla bayan yasan cewa ni ba musulma bace,Omg!ni bansan ma ya akeyin sallar ba,ko time ɗin baya dana ta6a musulunta ba don Allah nayi ba,ko sallah banyi a lokacin,"

  tana cikin zancen zucin nata sai ga junaid ya fito daga cikin toilet yana faman yarfa hannunshi,ruwan alwalar da yayi yana ɗiɗɗigowa ƙasa,

   Carpet ɗin salla ya dauko masu na abbansu sannan ya dawo ya shimfiɗa masu shi,

  Juyawa yayi tare da kallon Mommyn tasu wanda tayi sototo tana binshi da kallo,

  "Ni zan shiga gaba saiki tsaya abaya,"

   Dawowa bayanshi tayi ta tsaya,shi kuma ya tsaya agaba,tare da daidaita natsuwarshi,ya kabbara sallar,anatse suka shiga yin sallar atare,tunda suka kai raka'a dayan farko,bacci ya kwashe Alexandra,junaid bai sani ba yaci gaba da yin sallarshi,sai da yayi kusan raka'a takwas sannan ya sallame,

  cikin bacci taji an ambaci sunanta da ƙarfi"Mommy"!!a firgice ta farka tare da buɗe idanunta tana kallonshi,muryarta adisashe irin ta mai bacci tace"junaid har mun kammala sallar,"zum6ura mata baki yayi rai a6ace yace"nadai kammala sallar mommy,kin barni ni kaɗae,kina ta bacci,"

  cikin lallashi tace"kayi haƙuri romeo ɗina,saida na faɗa maka cewa banyin sallah,nifa ban iya ba,nadai samu nayi ɗaya,dakyar itama na samu nayi ta,don bacci nake ji,"

  "Shikenan kiyimun addu'a yanxu,sai muje mu kwanta"

  Yadda yayi maganar ba ƙaramin tausayi ya bata ba,nan take taji kamar bata kyauta mashi ba,jiki asanyaye ta sanya hannunta tare da ruƙo hannunshi,ta shiga karanta mashi addu'oin,cikin harshen Faransanci,bai damu da yaren da takeyi mashi addu'ar ba,saboda yasan cewa Allah yana ji da kowani irin yare aka roƙesa,"

  Ta jima tanayi mashi addu'a tana tottofa masa asaman sumar kanshi,kafin daga bisani suka koma saman gadon suka kwanta,ba ƙaramin kwanciyar hankali junaid ya samu ba,tunda ta tofa mashi addu'ar nan take yaji wani sanyi aranshi,tamkar an bashi ƙwarin guiwa,kuma tunda ya kwanta bacci ya ɗaukeshi bai ƙara jin an zungure shi ba,


DARE YAYI GARI YA WAYE,


Tun bayan Kammala Sallar asuba,Azmee da Saude,Suka fara ɗaura girke girken da zasuyi anan cikin gida,Uban aiki ne a gabansu,saboda Abinci ne kala kala zasuyi,na kasashe daban daban,saukin su ma Naman da za'a yanka basu zasuyi aikinshi ba,An riga da an bada aikin naman already,sai dai kawai in an kammala akawo masu shi Hada snacks sukayi order wanda za'a ci,akwai kuma Naman da Azmee zatayi masu farfesu dashi,da kuma tsiren nama,don ta kware a wannan 6angaren,Sunyi nisa acikin aikin sai ga Hajiya azeema ta shigo,bayan sun gaisa da junansu,itama tace tazo ayi aikin da ita,hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba,nan suka haɗu su uku,suka tasar ma girkin nan,Cikin ƙanƙanin Lokaci,Wani irin daddaɗan ƙamshi ya gauraye ko'ina na kitchen ɗin,


Hatta main palour ɗin kamshi ya karaɗe cikinsa,gwaggon katsina dake kwance,saman gado,tun bayan sallar asuba ya ɗauketa,tana cikin bacci ta dinga jin ƙamshin abinci nashiga Hancinta,ba arziƙi ta farka tana faɗin"wannan wani irin ƙamshi ne mai tashin mutun daga bacci"?tana maganar tana shinshinar kamshin,saukowa tayi daga saman gadon,jikinta sanye da kayan baccin nan nata na gado,fitowa tayi daga cikin bedroom ɗin nata tana tunkarar inda kamshin ke fitowa,


Kamar daga sama suka ji muryar gwaggo tana cewa"Ikon Allah,ƙamshi ya tashe ni daga bacci,ya kawo ni cikin kitchen,don inci daɗi,"

  Murmushi suka saki gaba ɗayansu,kafin suka shiga gaishe da ita,

  ƙarasawa tayi cikin kitchen ɗin suna haɗa ido da saude ta watsa mata harara tare da cewa"ya akai kuka bar wannan tana girki?bafa ta iya girki ba,Rannan ta zuba mana Gishirin lalle amatsayin gishiri cikin farfesun nama,gaba ɗaya girkin nan bai ciyu ba,ƙarshe saboda tsoran kar asirinta ya tonu inyi mata faɗa,ta dauki farfesun ba tare da sanin kowa ba taje ta zuba ma karnukan layinmu,kunsan kare da nama nan fa suka lashe farfesun nan tasss suka cinyi shi,aikuwa cikinsu ya kumbura sumtum,sukayi mussai,gaba ɗaya suka mace aka zubdo su,mai karnukan nan yace bazai yarda ba,sai yayi shari'a da Saude,ranar saude har gudawa saida tayi don jin za'a kaita ƙara kotu,yarinya tabi ta burkice mana,daƙyar Harrisu ya biya diyarsu,daba don haka ba,da tuni saude an jima da yanke mata hukuncin kisa....'

  Tunkan gwaggo takai karshen Labarin da take basu gaba ɗaya suka fashe da dariya,banda saude wadda ta tur6une fuska,rai a6ace tace"Kai gwaggo,"

  gwaggo tace"ƙarya nayi?ko ba haka akayi ba,ki faɗi tsakaninki da Allah in ba ayi hakan ba,ranar fa har gudawa kikayi,kika dinga kuka kina cewa gwaggo ki maishe ni rugarmu,saboda kawai na kashe karnuka shine za'a kai ƙarata kotu,wlh ko shanun baffa na kashe ba za'ayi mani wannan hukuncin ba,sai ku ƴan gayu da kuka ɗauki ran kare da mahimmanci karen da ko hisabi baza'ayi dashi ba,"

  Sake fashewa da dariya sukayi,yadda gwaggo take kwaikwayon muryar Saude,ba ƙaramin dariya ta basu ba,saboda hausar irin ta fulanin da basu kware bace,"

fuskar saude tamkar zatayi kuka,batasan meyasa gwaggo keyi mata haka ba,duk in suka shiga cikin mutane saita kunyata ta,wannan labarin da take bayarwa ya jima da faruwa,tun lokacin da Dr harris ya ɗaukota daga rugarsu ya kawota gidansu,lokacin batasan komai ba,ita arayuwarta ba abunda ta bama mahimmanci inba Kiwon shanu ba shi kadae tafi sani,gwaggo kuma bata koyar da ita komai ba,kwana uku da zuwanta gidan ne,ta shiga kitchen ta ɗaura masu girki,tana cikin girkin ta fara neman gishiri zata zuba acikin,gafa gishirin acikin farar roba an zubashi,amma saboda ta saba ganin gishiri kulle acikin leda yasa tayi zaton koba gishiri bane,hakan yasa ta fito ta wuce ɗakin gwaggo don ta sanar da ita cewa babu gishiri a gidan,tana shiga ɗakin gwaggon katsina,ta same ta tana bacci,harta juya zata fita shine taga wasu kullun kaya da aka kawoma gwaggo acikin leda,nan fa ta shiga laluban kayan,ta zaƙulo ledar gishirin lalle ta fuce dashi,duk a tunaninta gishiri ne,dayake kanta a toshe yake,kwata kwata bata lura da lallen dake acikin ledar ba,ita dae kawai gishirin lallan ta ɗauko,taje ta zuba masu acikin girkin,ba don Allah yasa gwaggo ta tashi tana neman gishirin lallanta ba,har saude taji,daba ƙaramin illa zata yi masu ba,karshe dai abun kan karnukan layinsu ya ƙare,tun daga wannan lokacin ne harris ya sanyata a makaranta,da kuma makarantar koyon girki,har ta samu ta kammala secondary,daga nan ne akasamu kanta ya waye,

  "Gwaggo me kikeso a zuba maki ne?nasan yunwa ce ta koro ku,"azmee ce tayi maganar,

  Gwaggo tace"komi ma da kuka girka,a zuba mun in ɗanɗana inji yaya ɗanɗanon girkin naku yake,don tunda kuka sanya saude acikin girkin nan naku nasan cewa dole a samu matsalar rashin gishiri kodae ta zuqa shi,ko kuma yayi kaɗan,"

murguɗa mata baki saude tayi tare da juyawa ta shige cikin store,tana faɗin"nashiga uku da wannan matar,a haka Haris yakeso in zama surukarta,bansan ya zan ƙare da ita ba,lafiya lou nake yin girkina acan gida,har santi takeyi amma yanzu tazo sai sharri takeyi mun agaban mutane,Zamu koma gida ne,nasan me zanyi mata,ae mun saba dama,"

  Saude bata fito daga cikin store ɗin ba,sai da taji fitar gwaggo daga kitchen din,bayan sun zuzzuba mata abincin da suka girka,komai sai da tasa suka zuba mata,a ƙaton tray ta fuce dashi tana cewa"idan na cinye wannan zan dawo a ƙara mun,"

  dawowa tayi cikinsu suka cigaba da aiki,azeema tace"sai kin dinga haƙuri da ita,bayin kanta bane,ku tayata da addu'a,Allah ya yaye mata wannan haukan da aka ɗaura mata,"

  Saude tace"insha Allah,zamu cigaba da tayata da addu'a,ae yaya harris ya sanar dani komai,na tausaya mata sosai,Allah dai ya tonu asirin waɗanda ke shirya masu wannan maƙarƙashiyar,Allah ya kawo ƙarshensu,"

  Azmee tace"ae bazasu kai labari ba,a sannu asannu zasu gane kurensu,"

  Suna aiki suna tattaunawa game da irin rayuwar da su sehrish sukayi a baya,


Wuraren ƙarfe 10 sun kammala Komai,an gyara kitchen ɗin tamkar ba'a ta6a girki acikinsa ba,tun da wuri Abokanan Abba suka fara zuwa,Hada wasu daga cikin abokan Abusufyan wanda ke zaune a Nigeria,tuni gida ya fara ciki,tun da su sehrish suka tashi daga bacci ko arziƙin yin wanka basu samu damar yi ba,saboda kiransu da ake tayi,duk wanda yazo saiya buƙaci a kira mashi su ya gansu,daga sunje haka za'a dinga yabon kyawunsu ana sanya masu albarka,gashi duk wanda sukaje gaidawa cikin abokanan Abba,sai Yayi masu kyautar makudan kudi,babu wanda yayi masu kyautar ƙasa da naira dubu ɗari biyar,hosana duk tabi ta susuce,sae faman lissafin kuɗaɗen da suka samu takeyi,daga sun dawo cikin ɗaki zata fara fadin Abokin abba mai farin gemu ya bamu kyautar Dubu ɗari takwas,sae wannan abokin nasa mai sanye da kaki da yazo ya bamu kyautar gonaki guda uku,kuma ya haɗa mana da dawakai,Sai kuma wannan mai ƙaton tumbin shine ya bamu kyautar miliyan Uku,Ni miliyan ɗaya,Jahad miliyan ɗaya,sae sehrish itama miliyan daya,bayan shi kuma sae wannan abokin daddyn namu ɗan fari mai kumatu,wanda ya biya mana Umrah,Ashe da rabon zanje in ta6a ka'aba ɗakin Allah,harma in roƙe shi akan ya yaye mun haukan dake damuna,don banson jin anace mun Zararriya,haka ta dinga sambatu har sai da suka fara gajiya da surutun hosana,


Sehrish na cikin toilet tana wanka,amma hankalinta gaba ɗaya ya tafi akan Sgr,kalamanshi na jiya ne suka shiga dawo mata acikin kanta,dole tayi aiki a ƙarkashin shi batasan meyasa yake son ganinta a matsayin ƴar aikinsa ba,

Tana cikin wannan zancen zucin tajiyo muryar jahad,daga waje tana cewa"Sehrish dan Allah kiyi sauri ki fito,inaso nima nayi wankan,kafin asake kiran mu,"

  jin haka yasa tayi saurin kammala wankan ta fito,ɗaure da towel a waist ɗinta,shiga ciki jahad tayi,don tayi wankan itama,duk hosana na zaune gefen gadonsu hannunta ruƙe da biro da memo din Sehrish sae faman lissafin kyaututtukan da suka samu takeyi,"

  Girgiza kai sehrish tayi tare da cewa"Aiki ya same ki hosana,kowa na ɗokin zuwa yayi wanka amma ke hankalinki na akan kuɗin da muka samu,abunda baki sani ba,idan mukayi wanka mu kayi kwalliya,sae mun samu ninkin abunda muka samu a yanzu,"

  Juyowa hosana tayi tare da waro ido jin an ambaci kuɗi tace"dagaske kike sehrish idan mukayi wanka mukayi kwalliya zamu samu fiye da wannan kuɗin da muka samu"?

  Jinjina kai sehrish tayi tace"kwarai kuwa,ke dai kawai ki tashi ki fara yin wanka,jahad na fitowa,ki shige ciki,"

  Cike da zumuɗi ta miƙe ta koma ta tsaya a kopar shiga toilet ɗin tana kwankwasa ma jahad,

  "Ki fito nima in shiga,"

 Murmushi sehrish ta saki,dama wayau tayi mata,don taji ɗazu suna magana da jahad tana cewa ita ba yanzu zatayi wanka ba,sae da marece,bayan tun yanzu akeso su shirya,don agansu da kyau,

 Gaban dressing mirror ta zauna,tana shafa mai ajikinta,sae faman sauri takeyi saboda taje part ɗin Sgr,kamar yadda ya umarce ta akan taje da safe ta kai mashi breakfast ɗinshi,kuma ta gyara mashi bedroom ɗinsa,light makeup tayi a fuskarta,saboda wannan wankan safe ne zata ɗauka,da anjima Azmee tace za'ayi masu  makeover,tamkar brides haka zasu fito,


Bayan ta kammala yin kwalliyar,komawa tayi wurin wardrobe din kayansu ta buɗe tana ƙare masu kallo,dama kullum zata zura kaya ajikinta sai ta tsaya yin ruwan ido wurin za6en kayan da zata sanya,

"Da rana zan sanya shadda lace ɗita,da marece kuma zan ɗauki wankan Swiss lace,yanzu dae bari na sanya wannan Arab gown ɗin,naga sai faman ƙyalli takeyi,in na sanyata ajikina,ba ƙaramin kyau zanyi ba,"ta ƙarasa maganar tare da janyo rigar,golden colour ce,gaba ɗaya jikinta adon stones ne masu ƙyalli da ɗaukar ido,batare da 6ata lokaci ba ta shiga kiciniyar zura rigar ajikinta,daƙyar ta shigeta saboda ta matse ta,gaba ɗaya tabi shape ɗin jikinta,kirjinta ya fito sosai,ga wani uban hips daya bayyana ajikin kayan,dama akwaita da diri sosai,don dai bata cika sanya kayan da zasu bayyana surar jikinta bane,hannun rigar na net ne,dogo ne ya kawo har wrist ɗinta,kana hangen fatar hannunta ta ciki,

   siririn mayafin ta ɗauko,ta sanyashi asaman kafaɗarta,wa'iyazubillah,ba ƙaramin wankuwa sehrish tayi ba,juyowa tayi tare da kallon Hosana wadda ta saki baki tana kallonta,tace"Nayi kyau,"

  Yadda hosana ta saki baki,tana kallonta ko kyaftawa batayi ba ƙaramin dariya ya bata ba,har saida ta ambaci sunanta,sannan hosana ta iya buɗe baki tace"Wlh kinyi kyau Sehrish sosai,kamar ƴar matan aljanna,"

  Dariya Sehrish tayi yayin da ta koma gaban mirror tana kallon kanta,hannu tasa tare da daukar kwalbar turarenta,tabi jikinta ta feshe,sannan ta fuce daga ɗakin,tun da tafito idon kowa ya dawo kanta,abokanan matasan gidan da suka hallara a babban falon,duk saita tsargu,kitchen ta wuce anan ta samu Azmee tana zuzzuba ma saude abinci acikin warmers tana fitarwa waje,wurin baƙi tana kai masu,

  Ae tunda azmee tayi arba da ita tashiga zuzuta kyanta,

 "Aunty Azmee ni nasan ban kai haka ba,kawai kina hura mun kaine,". 


Azmee tace"ae kin zarce duk yadda nake faɗi maki,dama shi mai kyau bai gane yana da kyau,sai in ana faɗi,"

  murmushi kawai ta saki tare da cewa"Aunty azmee ina kayan breakfast ɗin babban yaya inaso nakai mashi,"

  "Oh kin manta cewa abusufyan ya hanaki"?

  "Nasani Aunty azmee,bansan ya zanyi bane,babban yaya jiya yace,baison ki ƙara aiki part ɗinsa,ni kawai yakeso in dinga zuwa inayi mashi aiki,kuma har faɗa mashi nayi akan cewa daddy ya hanani amma yace shi babu ruwanshi,kawai nayi mashi aiki,

  Jinjina Kai azmee tayi tare da cewa"Tabɗijancan,aikuwa akwai matsala!don wlh Abusufyan yaji wannan maganar bazai yadda ba,kuma ke in banda abunki kin manta wanene abusufyan a wurinki,mahaifinki fa ne,taya zaki tsallake umarninsa kibi na babban yayanku?hakan na nufin cewa yafi iko dake akan mahaifinki?kina ganin cewa abusufyan zaiji daɗi idan yaji cewa kin cigaba da yi mashi aiki"?

 Jin wannan maganar ta azmee yasa jikinta yin sanyi,sunnar da kanta ƙasa tayi,tuni idonta sun ciko da kwalla,

  Gyaɗa kai azmee tayi tare da cewa"Nasan don baki da yadda zakiyi ne sehrish,zan shirya maki breakfast ɗin ki kai mashi,amma karki kuskura ki bari Uncle abusufyan ya gani,kuma koda ya kamaki,kada ki sanya sunana aciki,"

  Amsa mata tayi da toh,

Batare da 6ata lokaci ba,Azmee ta shirya mata warmers da sauran tarkacen abincin acikin kayataccen tray ta bata takai mashi,'

 Tunda sehrish ta fito daga kitchen ɗin gabanta ke faduwa sai faman waige waige takeyi,tsoranta kar daddynsu ya ganta,cikin sa'a ta haye upstairs batare da taci karo dashi ba,

Ajiyar zuciya ta sauke lokacin data ƙarasa cikin falonshi,babu kowa aciki,hakan yasa ta tunanin ko bai tashi daga bacci bane,tana ƙoƙarin shiga bedroom ɗinshi,taji muryar namiji a bayanta,

  "Ji mana,"a firgice ta juyo don taga wanene,ɗan zaro ido tayi tana kallon matashin daya biyota,acan falo ta ganshi tare dasu kanal yousouf da alama abokinsu ne,

  Murmushi ya sakar mata tare da cewa"Am sorry na biyo bayanki batare da saninki ba,nagaza jurewa ne shiyasa na yanke shawarar yin hakan,'

 muryar sehrish na kerma tace"Am...um..dan Allah ka jira ni awaje,yanzu zan fito,

  "Okey,zan tsaya awaje,but pls don't stay long,"

  Ya faɗi hakan tare da juyawa zai fita,har ya sakai zai fita daga falon,ya kuma juyowa tare da kallonta har lokacin tana a tsaye yace"Kin tafi da imanina sosai,zan iyayin komai don na mallake ki,"ya ƙarasa maganar tare da fucewa,

  Ajiyar zuciya Sehrish ta sauke aranta tace"Kowanene wannan jarababben,baisan nan part ɗin wanene ba,so yake yaja mun masifa,ya wani kwaso kafafunshi ya biyo ni,'

  kamar ance ta juya,idanunta suka sauka kan Sgr dake tsaye ya goya hannayenshi asaman faffaɗan ƙirjinshi,fuskar nan kwata kwata babu annuri,daga shi sai short fari ajikinsa,

  

Gabanta ba ƙaramin faɗuwa yayi ba,ƙiris ya rage ta saki tray ɗin hannunta,tuni jikinta ya soma rawa,


  "Zoki wuce ciki,"yayi maganar babu alamun wasa a fuskarshi,jiki na rawa ta nufi bedroom ɗin nasa,matsa mata hanya yayi ta wuce,sannan ya kama hanya azafafe ya fito daga falonsa,anan waje ya samu saurayin nan,tsaye yana jiran fitowar sehrish bawan Allah,ya ɗauki wankan suits,sae faman zabga murmushi yake yi,

..jin an ta6a kafadarshi yasa shi juyowa don yaga wanene,gabansa ne ya faɗi Rasss lokacin da yayi arba da sgr tsaye agabanshi ya ruƙe qugu,tamkar zaki haka ya koma mashi,mugun tsoranshi suke ji,saboda ko magana bata ta6a haɗashi da abokanan ƙannenshi ba,labarinshi kawai suke ji a wurin su Irfan,babu wanda baisan Sgr ba,wato babban yaya,

  Fuskarshi a tamke yace"Wani ganganci ne yasa ka biyota har cikin part ɗina!"?

   Muryarshi na kerma yace"wlh ni ba ita na biyo ba,zuwa nayi kawai don in gaishe ka,dama Jabeer ne yace yakamata muzo mu miƙo gaisuwa wurin babban yayansu,kaji dalilin dayasa na kwaso ƙafata nazo,"

  Wani irin kallo sgr ya wurga mashi,jin ya sharara mashi ƙarya bayan yaji duk abunda yake faɗa ma sehrish,

  Sunnar dakai saurayin yayi yana faman mazurai,tsoranshi karya kai mashi naushi,

   Hannu Sgr yasa tare da ruƙo neck tie ɗinsa yace"menene sunanka"

   Cikin sauri yace"Jazz,"

Sgr yace"Jazz ko?let me warn u,ka tsaya a iya matsayinka,in ba so kake ka kwana a gadon asibiti ba,ka rufe idanunka daga kallon matan mutane,hakan zaisa ka zauna lafiya,'yana kai ƙarshen maganarshi yace"just u can leave....."ae tunkan sgr ya ƙarasa maganar,Sir Jazz ya watsa da gudu jiki na rawa ya sauka downstairs,

  Ajiyar zuciya sgr ya sauke tare da juyawa ya koma ciki,


a ƙopar shiga bedroom ɗin ya tsaya,yana kallon sehrish dake ƙoƙarin gyara mashi gadonshi,har ta ajiye mashi kayan breakfast dinsa,yadda ta rankwafa shape ɗin hips ɗinta ya fito sosai,ba ƙaramin kyau tayi masa ba,sai yanzu ya gane dalilin dayasa wannan saurayin ya biyota,tunda yaga babban kaya dole ya zauce,baisan cewa babban goro sai magogin ƙarfe,


gyaran muryar da yayi ne yasata yin saurin ɗagowa,tana ganinshi tasha jinin jikinta,ƴan kame kame tashiga yi kamar wata mara gaskiya,ƙarasa shiga ciki yayi tare da samu wuri daga gefen gadon ya zauna,sannan anatse yace"Am hungry,"

cikin sauri ta dawo gaban table ɗin tashiga ƙoƙarin yin saving ɗinshi,coffee mai zafi ta fara miƙa mashi acikin cup,hannu yasa tare da kar6a,yana cikin kur6ar coffeen kamar ance mashi ya ɗago,idanunshi suka sauka akan Boobs ɗinta da suka fito sosai,tamkar zasu fasa gaban rigar,zukunnawar da tayi ne yasa suka yi hakan,

  Nan take ya shaƙe,ba arziƙi ya ajiye cup ɗin dake hannunshi,gaba ɗaya duk yabi ya susuce ya shiga yin tari,tamkar maƙoshin shi zai 6allo,ganin haka yasa sehrish dakatawa daga yin saving ɗinshi da takeyi,tashiga yi mashi sannu,

daƙyar ya samu ya daidaita natsuwarshi,muryarshi ashake yace"Ke!ina scarf ɗinki yake"?

  Muryarta na kerma tace"gashi nan agefenka,da zanyi gyara ne,na ajiye shi anan don karya takuramin,

  Harara ya ɗan watsa mata tare da cewa"ɗaukarshi ki yafa,banason na ƙara ganinki haka kina yawo,"

  "Toh,"ta amsa mashi,sannan ya kai hannunshi a gefenshi ya ɗauko mata mayafin ya miƙa mata,tana kokarin kar6a ta aza hannunta asaman nashi,ɗagowa yayi da idanunshi kai tsaye suka shiga cikin nata,agigice tayi saurin kawar da nata idanun,

  Tunda yake arayuwarshi wata ƴa mace bata ta6a jan hankalinshi ba,da surar jikinta,harya shake irin haka ba,mata dayawa suna kawo mashi kansu,wasu har cire kayansu sukeyi don suja ra'ayinshi,amma basu ta6a cin nasara ba,donshi bashi da wannan Sha'awar ko kaɗan,akan sehrish ne kawai ya ta6a ganin wani sauyi,A ranar da suka faɗa saman gadon shi atare,har yau yana mamakin wannan abun,


*Aunty Babba*


Tuni sun kammala shirinsu na zuwa abuja,wankan shadda ta ɗauka,doguwar rigace ta kashe ɗaurin ɗan kwali abun sai wanda ya gani,Hafsat kuwa Code lace ta sanya ajikinta,riga da skirt milk colour,su aunty babba hada trolley na kayan sawa,ta sanya abayan boot ɗin motarsu,dama tace in taje sai tayi sati biyu,hafsat dae kallonta kawai takeyi,ita kadae tasan me zai biyo baya,hafsat ce take tuƙin motar yayin da aunty babba ke zaune agefenta,

  kafin su fita daga garin Kaduna,Hafsat tace"Mommy,yakamata mu tsaya a kasuwa ki saya mana niqabi,"

aunty babba tace"Niqab kuma?daughter me zamuyi da niqabi sai kace wasu munafukai,"

  murmushi hafsat ta saki tare da cewa"Mommy zaiyi mana amfani sosai,tunda nace maki mu sayi niqabi akwai dalilin dayasa nace maki haka,'

.....guntun tsoki aunty babba tasaki tana cewa"Ni ba wani niqabin da zan siya,kedai in kina buƙata ga hanya nan kije ki siya,"

  Parking ɗin motar tayi,adai dai bakin wani shopping mall,

  "Ni zanje in siya,kina bukatar wani abu"?

  "A'a adawo lafiya," 

Fita hafsat tayi daga motar,kusan 15 mins sai gata tadawo hannunta ruƙe da sabon niqab,ta siyo,komawa tayi cikin motar,sannan ta tashi motar,suka miƙi hanya,


A 6angaren Amani kuwa tuni ta kammala shirinta,sun ɗau wankan lafaya itada Amal,Abbas da kanshi ya ɗaukosu acikin Motarshi,


Wuraren ƙarfe biyu da rabi na rana,wasu matsiyatan motoci haɗaɗɗun gaske,suka shigo cikin layin gidan,irin motocin nan na jigunan masu kuɗi,masu rai da numfashi,su huɗu ne motocin tare da security guards suke,kowace mota soja ne ke driving ɗinta,har suka ƙetara gate ɗin gidan,

   A jere motocin suka tsaya,da gudu wani soja,jiki na rawa yazo ya buɗe mata ƙopa,

   Tunkafin ta fito daga cikin motar,hayaƙin tabar da take sha ya fara fesowa waje,tashin hankali da ba'a sama shi date !Ko wacece Wannan



  *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃



*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI.  MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*



*LOCATION KANO*


08062073990

Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku



Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku


It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.

Snack

Awarah 

Farah

Zobo

Samosa

Cup cake etc 

Contact me 09063302182or 09012179727.


   



  

  

  

  


   

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



Ƙarasa fitowa tayi daga cikin motar,jikinta na sanye da wani jigunannan lace,anyi mata riga da zani,rigar takai har guiwarta,ta coge ɗaurin ɗankwalin nan ture kaga tsiya,tun daga kan wuyanta zuwa hannayenta,duk zinari ne,tsohuwa mai ran ƙarfe,hajiya Ammi kenan Ummu Hossein,Ummu Azeema,Ummu Abusufyan,kaka ga su junaidu da kuma sehrish,fara ce tass bafullatanar asali doguwa kuma siririya,tsufanta bai hanata yin gayu ba,tsohuwar soja ce wadda tasha gwagwarmaya,kuma itace mace ta farko a lokacinsu data fara ruƙe muƙamin Major General,kaifi ɗaya ce ita,mace mai wuyar sha'ani,mutum mai tsananin haƙuri ne kawai zai iya jurar zama da ita,hannunta ɗaya na ruke da sandar karfe ta alfarma,yayin da ɗayan kuma yake ruƙe da sigari,tana tafiya tana busa ta,har ta hanci hayaƙin ke fitowa,


Babu wanda yayi tunanin cewar zatazo da wuri,bata sanarma kowa ƙarfe nawa zata zo ba,duk sunyi tunanin sae wuraren marece zata ƙaraso,Atare da MG Osman da Captain Adam suka zo,sae Hajiya Sarah ƴar wurin yayanta Modibbo,tare da ya'yanta mata su biyu Yasmeen da noor,dukkansu ba zasu wuce shekara ashirin da biyu ba,tunda matasan gidan sukaji zuwan ammi nan fa kowa yasha jinin jikinshi don sun san zuwanta bai cika zama alkhairi ba,duk in tazo sai wani abu ya faru,wannan karan basu san dame tazo ba,gaba ɗayansu sun hallara a main palour ɗin suna jiran ƙarasowarta ciki,mutun ɗaya ne bai fito wurin tarbarta ba,bakowa bane face Abusufyan,tun da yaji zuwanta ya kasa samun sukuni,sae faman safa da marwa yakeyi acikin bedroom ɗinshi,jikinshi nata kerma ba don komai ba sai don zullumin abunda zai biyo baya,idan tayi arba da triplet ɗinshi,duk da yayi ma kanshi alƙawarin cewar,koda ace ta koresu to tabbas ƙafarsu ƙafarshi,bazai ƙara barin rayuwarsu ta wulaƙanta ba,duk inda zasu je zai kasance atare dasu,


  hayamm kuwa tana la6e jikin window tana leƙen Ammi,tun fitowarta daga mota,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta saboda tana sa ran cewar tuggun da suka shirya,zaiyi aiki,


Lokacin da suka shiga falon,nan fa kowa ya shiga miƙa gaisuwa,abun da zai baka mamaki,ko amsawa wannan batayi kamar mai fama da ciwon baki,sai dae ta ɗaga masu hannu,Azmee ce ta kaisu ɗakunan da aka gyara masu,domin su sauke gajiyar da suka kwaso,kafin zuwa anjima,kowa sai da ya kara zuwa gaishe ta ɗaya bayan ɗaya har ɗakin data sauka,mutun uku ne kawai basuje gaishe ta ba,Sgr,Abusufyan sae junaid wanda bai kaiga fitowa ba daga bedroom ɗinshi,


Mg Osman kuwa a nan falon suka zauna tare da Marshal Omar,suna gaggaisawa,saboda anjima ba'a haɗu ba sunyi kewar junansu sosai,


Hayaam tana ƙoƙarin zuge glass ɗin windon da take leƙe sai ga Motar Abbas tayi parking cikin gidan,tsayawa tayi tana jiran ganin su wanene kuma suka ƙara zuwa,kodai Aunty laila ce ta ƙaraso ne,bata ƙarasa zancen zucin nata ba,Abbas ya fito daga cikin motar,daga bisani kuma Amani da Amal suka fito atare daga cikin motar,

Ƙura ido Hayaam tayi tana ƙare ma Amal kallo,cike da mamakin wacece wannan Kyakkyawar yarinyar da Amani tazo da ita,A iya saninta dae Amani bata ta6a haihuwa ba,balle harta haifi ƴa kamar wannan,duk yadda taso ta gane wacece yarinyar nan amma hakan ya gagara,kwakwalwarta a toshe take,saboda tsabar mugunta irin tasu tun Amal na ƙarama suka canza mata kamanni saboda uƙubar da take sha a hannunsa,dole hayamm ta kasa gane wacece ita,

"Hayam!"muryar Azmee ce ta karaɗe kunnanta,da sauri ta rufe glass ɗin windown tare da juyowa tana kallon Azmee,shigowarta kenan ɗakin jikinta na Sanye da jallabiya baƙa,anyi mata kwalliyar zanen flower blue,veil ɗin data yafa ma blue ne,ba ƙaramin kyau azmee tayi ba,ta wanku sosai,

  Ƙarasawa hayaam tayi wurinta tana faɗin"Aunty Azmee sae yanzu za'a tuna dani?yunwa kamar zata kashe ni,kowa yana rayuwarshi acikin gidan nan sai ni duk a ƙuntace,"

  "Ke kika so ki ƙuntata kanki hayam,Sgr yanzu haka ya manta da cewar ya koreki daga gidan nan,zai iya yiwuwa ma ya manta dake gaba ɗaya,kuma kinga yau ranar Walima ne mutane duk sunzo,ba dole bane ya ankara dake ba,bama haka ba mutumin da kafin ya ɗaga ido ya kalli wani aiki ne a wurinsa,don haka ina baki shawarar ki daina kullan kanki,"

   Tun kan azmee ta ƙarasa maganar hayaam ta soma washe baki,la66anta har rawa sukeyi wurin cewa"An..aunty Azmee kina nufin sgr ya manta da laifin da nayi mashi kuma zan iya fita inyi yawo na acikin gidan nan kamar kowa,'

  Jinjina kai azmee tayi tare da cewa"Of course,amma fa hayaam koda gigin wasa kada ki kuskura ki ƙara yunƙurin zuwa sashen shi!duk yawon da zakiyi ki tsaya a downstairs babu ruwanki da abunda ya shafi upstairs ina fata kin gane"?

    yatsina fuska tayi tana fadin"dama ni Aunty azmee me zai kai ni,waccen karan ma tsautsayi ne da ƙaddara,"

"Sannan kuma,kada ki kuskura ki ƙara shiga shirgin Sehrish!kinsan dai yanzu tafi ƙarfinki nesa ba kusa ba,ƴar masu gida ce ita,kuma shalelen daddynsu,ga kuma yayyanta maza muddin kikace zaki ta6ata wlh zaki ta6o ma kanki ne,akanta sae abaki Red card na barin gidan nan,"

  ta6e baki hayaam tayi,tana faman hura hanci,maganar ba ƙaramin ƙona mata rai tayi ba,don bata da yadda zatayi ne,

  Murmushi azmee tasaki tare da juyawa ta kama hanyar fita tana faɗin"Yakamata kiyi wanka,ki shirya saiki fito ayi shagalin dake,"

  Cikin sauri ta ruƙo rigar Azmee tace"Aunty Azmee don Allah ki taimakamun wlh yunwa nake ji,tun jiya da daddare rabona da Abinci,"

  "Its Okey,zan kawo maki yanzu,"

Komawa ciki hayaam tayi tana jiran azmee ta kawo mata abinci taci,kafin tayi wanka ta kimtsa,

bayan su Amani sun shigo cikin main palour ɗin,anan suka zauna suna gaisawa dasu kanal yousouf,kafin tabar wurin tare da Amal,wurin Azmee taje suka gaisa tayi masu kwatancen ɗakin Hajiya Azeema da kuma na gwaggo,duk saida tabisu ta gaishe su,hatta ɗakin Abusufyan saida suka je,sukayi mashi Allah sanya Alkhairi,daga nan suka dawo kitchen,lokacin Azmee tana haɗa ma Hayaam lunch ɗin da zata kai mata,

    Juyowa tayi jin sallamarsu tace"har kun dawo"?

Amani tace"Eh,duk naje nayi masu Allah sanya alkhairi,yanzu abunda ya rage mun inason zuwa wurin dasu yaran suke,bansan a wani ɗaki suke ba,'

Azmee tace"Ae suna nan ɗakin da Sehrish take,ae kinsan ɗakinta wanda ke a kusa da namu,yakamata kuje wurinsu,'

  Murmushi Amani ta saki aranta tace"ba dole inje ba,ni da nakeson na gyara tsakanina da Sehrish,"

  A fili kuma tace"okey,nagane ɗakin bari muje wurinsu,"

   Juyawa sukayi atare da Amal suka nufi ɗakinsu sehrish,abakin ƙopar ɗakin suka tsaya,Amani ta kwankwasa ƙopar,jahad ce ta buɗe kopar,ba ƙaramin kyau tayi ba,wankan swiss lace ne ajikinta wanda aka haɗa da bazin shadda,stones work ne ajikin kayan wanda ya ƙara fito da ɗinkin sosai,

  Murmushi Amani ta sakar mata tare da cewa"Sehrish ce ko"?ta tambaya ne saboda Abbas ya sanar da ita cewar kamanninsu ɗaya sak,

  Martanin murmushin jahad ta mayar mata kafin tace"A'a,ba ita bace,tana ciki in kira maki ita ne,"ta ƙarasa maganar tana kallon Amal wadda itama jahad ɗin take ta kallo,

   Amani tace"bari mu shiga daga ciki,sai mu gaisa,"

  Matsa mata hanya jahad tayi suka shiga cikin ɗakin,

   A lokacin Sehrish na kwance saman gadon ta ɗan kishingiɗa,tana hutawa,saboda ba ƙaramin gajiya tayi ba,sun sha zurga zurga,gashi Anjima za'a fara walimar bayan Sallar la'asar,shiyasa ta dawo ɗaki don ta huta,kafin lokaci yayi,ganin Amani yasa ta miƙewa daga zaune tana kallonsu,

  Wuri Amani ta samu daga gefen gadon ta zauna,Amal ma ta zauna,tun kafin ma Amanin tace wani abu sehrish tace"Sannunku da zuwa,"hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Amani ba,tayi tunanin zata ga akasin haka ne,

  "Yawwa,fatan mun same ku cikin koshin lafiya"?

Sehrish tace"Lafiya lou Alhmdllh,"

Amani tace"kin gane ni ko"?murmushi kawai sehrish ta saki,taya za'ae ta manta da matar da tace zata iya rasa ranta idan ta cigaba da shisshige ma matasan gidan,

  "Ina fata dai baki ruƙe ni aranki ba?dan Allah ki manta da komai dana ta6a faɗa maki,komai ya wuce,yanzu zumunci ya ƙullu atsakaninmu,ko wancen karon ma da nayi maki wannan maganar,wlh bada wata manufa na faɗa maki hakan ba,"

  Jinjina kai Sehrish tayi tare da cewa"babu komai,ae ya riga ya wuce,"

  Ba ƙaramin daɗi Amani taji ba,juyawa tayi tare da kallon jahad dake tsaye tace"zo ki zauna mana,inaso muyi fira tare daku,"zagayawa jahad tayi ta 6angaren hannun hagu ta zauna daga gefen gadon,

Amani tace"ina cikon ta ukun take ne?Abbas ya faɗamun cewa ku ƴan uku ne,"

  Jahad tace"hakane,hosana ce babu,taje wurin yaya Omar ne" shiru Amani ta ɗan yi tana maimaita sunan hosana a cikin zuciyarta,kamar ta ta6a jin sunan abakin wani,"ke ya sunanki"?

"Ni sunana jahad," jinjina kai amani tayi tare da cewa"Suna mai daɗi,amma nifa bansan komai ba,agame daku,sehrish kawai nasani tana aiki a gidan nan,"

  Jahad tace"ae mu muna a wurin ya Omar ne,shi ya taimake mu a lokacin da muke cikin mawuyacin hali,bayan ƙaddara ta rabamu da ƴar uwarmu,"

..A ruɗe Amani tace"Hannun Ya Omar"

Jahad tace"eh,"

  Cike da son jin ƙarin bayani Amani ta kuma cewa"Kun zauna a kaduna ne"?

  Ita kanta jahad sai da gabanta ya faɗi jin Amani ta ambaci kaduna kai tsaye,taya akai tasan cewa sun zauna a kaduna,

  Daƙyar ta iya bata amsa da cewa"Eh,mun zauna acan,daga baya ne Ya Omar ya dawo damu Abuja,gidan daddynmu,"

  Tashin hankali,miƙewa amani tayi da sauri jikinta na rawa tace"Ga Amal nan ƙanwata ce,in ba damuwa ta zauna a wurinku,"

  Amsa mata sukayi da toh,cikin sauri ta fuce daga ɗakin,kallon juna jahad da Sehrish suka yi atare,duk sun lura da yadda Amani ta ruɗe,

   "Wacece wannan Sehrish"?jahad ce tayi mata tambayar,sehrish tace"matar yaya Abbas ce,Aunty Amani,"

  Taso ta ƙara tambayarta,amma saboda Amal dake zaune a wurin yasa tayi shiru,tabbas ta so taga kamannin Aunty babba kaɗan a fuskar Amani,duk da Amani tafi kyau sosai,kuma ita bata da jiki irin na Aunty Babba,miƙewa jahad tayi tare da cewa"Zan fita yanzu zan dawo,"

Sehrish tace"adawo lafiya,"

Bayan jahad ta fita,Sehrish ta kalli Amal dake zaune,rashin sabo yasa ta kame kanta wuri guda,

  Murmushi tasakar mata tare da cewa"ki saki jikinki mana,naga duk kin gaza samun natsuwa,ko dan bamu ta6a haɗuwa bane?"

  Sunnar da kai Amal tayi tana murmushi,wata irin kunyace da ita,daƙyar ta iya cewa"banta6a zuwa nan ba,yau nafara zuwa,bazan iya sakin jikina ba,tunda bansan kowa anan ba,"

  Sehrish tace"Ae kuwa yanzun nan zansa ki saba dani,da farko dai ki dinga kirana da Aunty Sehrish,saboda ina kallon ƙaramar fuskar nan taki nasan cewa na girme ki,tsawo ne kawai gare ki,amma a shekaru ba zaki wuce sha huɗu ba,ko nayi ƙarya"?

 dariya Amal tayi tana girgixa kai tace"A'a bakiyi ƙarya ba,shekarata sha huɗu amma na kusa kai shekara goma sha biyar,nan bada jimawa ba,"

  "Kice zamu zo yanka cake ko"?acewar sehrish,

  Amal tace"Eh,zan gayyace ku idan lokacin yayi,"

  Sehrish tace"Nima na kusa cika shekara sha takwas,banma sani ba ko na kai shekara sha takwas ko ban kai ba,nifa banma son ranar da aka jefo ni duniya ba,ni dai kawai na ganni ina yawo na ne....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda dariyar da Amal ta kwashe da ita,abu kamar wasa sai gashi cikin lokaci ƙankani sun saba da juna,nan suka zauna suna ta fira atsakaninsu,


Amani kuwa tun bayan da ta fita daga ɗakinsu sehrish,tarasa inda zata tsoma kanta,abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,Aunty babba ta sanar da ita cewar tasa an zubar da yaran da Omar ya kawo mata,kuma tace mata ƴan biyu ne yaran,hakan na nufin cewar jahad ne da hosana a wurinshi?kamar yadda jahad ta sanar da ita cewa su A wurin yaya Omar suke,indae dagaske hakane to taya akai Yaran suka dawo wajen Marshal Omar bayan tasa an zubar dasu!?kodai Omar ya sanya ɗan leƙen asiri ne acikin gidan?tabbas hakan zai iya faruwa,indai kuwa hakane Watan cin uban Aunty laila ya tsaya,Zuwa maiduguri ba fashi,

  Acewar Amani wadda ke ta faman yin safa da Marwa a tsakanin corridor ɗin ɗakunansu sehrish,daga bisani tace"Allah yaso ni ban tsoma hannu na ba,a wurin cutar dasu ba,ashe da rabon aure na yayi lasting,Aunty babba kam ta shiga uku,taja ma kanta bala'e,kwara ma da hakan ya faru,da nayi niyyar ɗaukar ma Amal fansa,amma yanzu na fasa,zan zuba idone kawai inga yadda dramar nan zata kaya,"ta ƙarasa zancen zucin nata,fuskarta ɗauke da murmushi,ba komai take hangowa ba face yadda rayuwar Aunty babba zata ƙare,........'


Bayan fitar jahad,kitchen ta wuce ta shirya lunch acikin tray,kamar ita zata ci,upstairs ta wuce dashi,adai dai ƙopar ɗakin junaid ta tsaya tare da sanya hannunta ɗaya,ta ɗan bubbuga ƙopar ɗakin,wata murya taji daga cikin ɗakin ta amsa mata da cewa"Wanene"?muryar kuma bata junaid bace,

  "Ni ce," ta bashi amsa ataikace

"Kece wa"? 

"Jahad,"shiru taji anyi mata kafin,harta fidda rai da za'a buɗe mata,tana ƙoƙarin barin wurin taji alamun ana buɗe ƙopar,tsayawa tayi har ya kammala bude kopar,ganin fuskar wani daban bata junaid ba yasa tasha jinin jikinta,musamman yadda taga fuskar mutumin a murtuke babu fara'a ko misƙala zarratin,

   "Wa kike nema"?

Muryarta na rawa tace"Wurin junaid nazo,naga ban ganshi ba duk yau,"

  "Shine kika zo kawo mashi abinci?yace maki yana jin yunwa ne"?shiru jahad tayi masa batace komai ba,da alama dae wannan ba ƙaramin masifaffe bane,

  "Wuce ki shiga,"ya faɗi hakan tare da matsa mata hanya ta wuce ciki,shi kuma ya fuce daga ɗakin,

  jikinta sai kerma yakeyi saboda tsoran mutumin da tayi arba dashi,hakanan taji tsanarshi aranta,kuma sam baiyi mata kama da mutanen kirki ba,

  Lokacin da ta ƙarasa shiga ɗakin a kwance ta samu junaid,daga shi sai farar shirt da short fari a jikinshi,ya kwantar da kanshi asaman pillow,idanunshi na arufe,ajiye mashi tray ɗin tayi asaman front table ɗin gadon nasa,sannan ta samu wuri daga gefen gadon ta zauna tare da ambaton sunanshi"junaid,"

  A hankali ya buɗe idanunshi tare da azasu akan fuskar jahad,yanayin shi ya nuna tamkar baijin daɗin jikinshi,idanunshi kansu sun marairaice,

    Bai tanka mata ba sae da ya gama ƙare mata kallo sosai,saboda ya tantance wacece acikinsu,tashi yayi daga zaune sannan yace"Jahad ko"?

  ɗaga mashi kai tayi alamar eh,sannan ta ƙara da cewa"duk yau ban ganka ba,shiyasa nace bari nazo na duba ka,hada abinci ma nazo maka dashi,duk da bansan ko kana jin yunwa ba,"

   "Thanks for your caring,duk yau babu wanda ya damu dani,sai ke kawai,naji daɗi sosai,"yayi maganar tare da sauko da ƙafafunshi ƙasa,hannu yakai zai ɗauki jug,ta riga shi ɗaukar jug ɗin tare da cewa"bari na zuba maka,"dakatawa yayi ta tsiyaya mashi lemu mai sanyi acikin cup,sannan ta miƙa mashi,yasa hannu ya kar6a,tare da kai cup ɗin saitin bakinshi yana kur6a,

   binshi tayi da kallo,yayi wani irin haske fari fat,kamar mara  jini a jiki,hakanan ta dinga jin wani irin tausayinshi na shigarta,ga tsananin ƙaunarshi da takeyi kamar kamar me,

   Har ya kammala shan lemun bata sani ba,juyawar da zaiyi suka haɗa ido dashi,kawar da idonta tayi gefe guda tare da yin saurin cewa"Kamar baka lafiya ko"?

   "Me kika gani"?

"Kawai yanayinka na gani,kamar na wanda bashi da ƙoshin lafiya,"

  "Lafiyata ƙalou,don inajin yunwa ne shiyasa kika ganni haka,amma da zarar naci na ƙoshi,zan dawo dai dai,"

  "Kasan kana jin yunwa amma meyasa baka tashi ka nemi abinci ba"?tayi maganar a yayin da take janyo plate ta shiga zuba mashi fried rice aciki,

   "Tun safe fa naketa yin bacci,ni kaina bansan ya akai nayi bacci mai tsayi ba,kuma dana tashi jikina duk ba ƙwari,shiyasa bansamu na sauko downstairs ba,saboda kasalar data baibaye ni,

   "Kuma baka sha wani abu ba?kamar maganin bacci"? 

  Shiru junaid ya ɗanyi yana tunani kafin yace"a'a bansha komai ba,amma ya haroon ya kawo mun wani tea a cup wuraren ƙarfe takwas yace mun insha,kuma saida na tambayeshi maganin menene yace mun maganin ƙara kuzari ne,shine nasha,tun daga lokacin nidai ban ƙara sanin meke wakana ba,yanzu ma da kika ganni a kwance tashi na kenan,kuma shi ya tashe ni,yace mun in tashi inyi wanka in shirya,lokacin walima ya kusa,"

  ɗagowa jahad tayi tare da kallon fuskarshi tace"Wannan mutumin daya fita yanzu shine Ya haroon"!?

  ɗaga mata kai yayi alamar eh,

ta kuma cewa"Wanene shi?don ban ta6a ganinshi ba a gidan,"

    Junaid yace"Shima yayan mu ne,bai cika zama gida bane shiyasa baki ta6a ganinshi ba,"

   "Kada na cika ka da surutu,ka fara cin abincin,"

  Maƙe hannayensa yayi tare da cewa"Hannu na ciwo yakeyi mun,"murmushi ta saki tare da kai hannu ta ɗauki cokali tana faɗin"bari na baka abaki to,"

  ɗebowa ta dinga yi tana tura mashi abakinshi yana Ci suna fira,gwanin ban sha'awa,a haka harta samu yaci abincin sosai,sannan ya tashi ya shiga toilet wanka,zama tayi tana jiran fitowarshi saboda yace ta jira shi,su fita atare,hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,a sannu a sannu dai junaid ya fara sakewa da ita,Allah sarki


*Boss Bature*


Bayan Sallar la'asar,kowa ya ɗauki wani sabon wankan,Amani da kanta tayi masu Jahad makeup ita da Hosana da Sehrish,gaba ɗayansu suka sanya Swiss lace ajikinsu,wanda aka ɗinka masu shi domin su sanya a aranar walimar,riga da skirt ne ba ƙaramin kyau kayan sukayi masu ba,sun wanku iya wankuwa,yadda kasan dollar wurin kyau haka suka koma,Suna acikin ɗakin nasu Su huɗu hada Amal,in aka haɗa da Amani sun zama su biyar kenan,zama tayi tana ƙarasa gyara masu ɗaurin ɗan kwalin da tayi masu,


A Can ciki kuwa Matasan gidan duk sun hallara,Azmee da Saude ne suke ta ɗawainiyar bin kowani table dake a wurin suna Jejjera abinci kala kala,daga bayane hayaam ta samu damar fitowa daƙyar,tun tana ƴan kame kame kamar mara gaskiya har dae ta fara sakewa,tashiga tayasu Azmee kai ma baƙi lemu,


A hankali Motarsu Aunty Babba,ta shararo izuwa cikin gidan,a dai dai parking space,hafsat ta tsayar da motar,tare da juyawa ta kalli fuskar Mommyn nata dake ta faman jan minshari,tunda suka taho ta kama bacci acikin motar,hannu hafsat tasa tare da bubbuga kafadarta,a firgice Aunty babba ta farka tana fadin"Har mun ƙaraso ne,"

  Hafsat tace"eh mana,gamu acikin gidan ma,kin barni da driving kina ta sharar bacci,'

Yamutsa fuska Aunty babba tayi tare da buɗe motar tana faɗin,wlh agajiye nake,ga baccin ma bai isheni ba,kuma yunwa ma nake ji,'

   Bayan motar ta tsaya tare da buɗe Boot ɗin motar,ta curo trolley ɗin kayansu,tare da saukko dashi ƙasa,

   Sai da hafsat ta sanya niqabin da ta siya a hanya sannan ta buɗe motar ta fito,hannunta ruƙe da ƴar purse ɗinta,ganinta da niqabi yasa Aunty babba jan guntun tsoki tare da fadin"Yau naga ikon Allah,kamar wata Munafuka,kin nace dae yau sai kin sanya wannan baƙin abun a fuskarki,kamar wata ƴar shi'a"

   "Mommy ba zaki gane bane,"

Tayi maganar tare da kama hanyar shiga cikin gidan,bin bayanta aunty baba tayi tana fadin"ba zaki zo ki kar6i trolley ɗin ba"

  "Haba Mommy,Duk aikin driving ɗin da nayi,kuma sai na wani ɗauki trolley,ae ke yakamata ki janyoshi,tun fa da muka kamo hanya kike ta bacci,kika barni da aiki,nima agajiye nake bazan iya ɗaukar shi ba,"

   "Kar Allah yasa ki ɗauka toh,"suna tafe suna magana har suka shiga cikin Main palour ɗin,Hayaam najin sallamar Aunty babba,ta wani saki ihu har saida hankalin kowa ya dawo kanta,da gudu taje ta rungumota tana faɗin"Wayyo Allah aunty laila,tun dazu nake ta baza ido inga zuwanku amma shiru,har na fara fidda rai da zuwanku ashe kuna hanya,"tayi maganar tare da raba jikinta daga na aunty babba,fuskar nan awashe Aunty babba tace"Mezai hana mu zuwa,naso na sanar maki wlh mantawa nayi,koda yake bacci fa nayi a mota,hada ƙarin haka yasa ban samu na kira ki awaya ba,'

  "Gaskiya nayi kewar ku sosai,"acewar hayaam tayi maganar a yayin da take mayar da idanunta akan Hafsat dake sanye da niqabi,a ruɗe tace"Kai!wai hafsat ce sanye da niqabi,"

  Hannu hafsat ta sanya tare da ɗan ɗage niqabin tace"Nice mana,gaba ɗaya hankalinki na akan mommy dayake kinfi damuwa da ita,"

  Washe baki hayaam ta kuma yi tare da rungumo hafsat ajikinta tana faɗin"Sorry bangane ki bane wlh,kema ce kin sanya niqabi kamar wata mara gaskiya,"

  Suna cikin magana muryar Azmee ta katse su da cewa"maraba da manyan baƙi,Yau su hajiya laila ne a gidan namu,wata sabon gani,yau za'ayi ruwa da ƙanƙara,"

  Dariya sukayi gaba ɗayansu,kafin daga bisani Aunty babba tace"Ae wannan zuwan na musamman ne,Har sai kun gaji damu Allah,"tana magana hafsat na zungurinta alamar ta daina faɗin zasu jima,amma zafin ɗumi yasa ko lura batayi ba balle ta ankare,

  "Ae tunda na ganku da trolley ɗin kayan nan nasan cewa zaku jima mana anan,wataƙil ma har sai an aurar da ƴa'ƴan namu tukunna,kunga sai ayi agabanku,'

  Gaban aunty babba ne ya faɗi rass,a razane tace"Auren wasu ƴa'ƴa kenan"?

  dariya azmee tayi tare da cewa"Ƴa'ƴanku mana na wurin Abusufyan,"

  ɗaure fuska Aunty babba tayi tana fadin"haba dae,wani aure kuma ana zaman lafiya,daga ganin yaran kuma sai ki fara yi masu fatan yin aure,duka nawa suke,bana ji ance ƴan shekara sha bane,'

  kafin azmee ta kuma cewa wani abu hafsat tace"Dan Allah mu shiga ciki mu zauna,wlh agajiye nake,gashi ko salla ma ba muyi ba,"

 Atare suka ƙarasa shiga ciki,bayan sun kammala gaisawa da mutanen dake zaune a babban falon,daga bisani hayaam takaisu bedroom ɗinta,suna shiga ciki hafsat ta cire niqabin data sanya,tai wurgi dashi saman gadon,tashige toilet don ta ɗauro alwala,a ƙagare take da tayi arba dasu jahad,duk da tsoran karsu canza mata,musamman in suka tuna abubuwan da sukayi masu a gidansu,tana cikin toilet tajiyo muryar hayaam tana fadin"Tun jiya fa na tura maki hotunan nasu,baki gani bane,kuma har hafsat saida na kira a waya na sanar da ita don ta tunasar dake,'

  Aunty babba tace"Gaskiya ni banga wani hoto ba da kika turamun a whatsapp ɗina,mu barma zancen tunda dae gani acikin gidan zan gansu da ido,batare da nasha wata wahala ba,'

  Hayaam tace"Ae yanzu haka suna can cikin ɗakinsu tare da Amani...'

  Cike da mamaki Aunty babba tace"Amani kuma?Ubanme ya haɗata dasu da har take shiga ɗakinsu?Oh ni yau naji ikon Allah,wannan shisshigi da kutsu irin na Amani,"

  "Nima azmee ce ke sanar dani cewa tana a ɗakinsu wai tanayi masu kwalliya,ni duk bama wannan bane damuwata ba,Akwai wata kyakkyawar yarinya fara da Amani tazo da ita,na rasa gane wacece yarinyar nan,kuma fuskar yarinyar sak irinta amanin ce,"

  Aunty babba tace"To fa,ko ina tasamu yarinya,zai iya yuwuwa fa daga gidan marayu Abbas ya ɗaukko masu ita don su raina,kinfa son cewa basu ta6a haihuwa ba,'

   "Bari naje ciki,kada azmee taji ni shiru,ina ɗan tayata aiki ne,'acewar hayaam

  Harara Aunty babba ta watsa mata tare da cewa"dama aiki na turoki kiyi acikin gidan?shiyasa naga duk kin zabge,nida zanzo inga ko'ina na jikinki ya cicciko,amma sai uban ƙasusuwan wuya,kamar wadda tayi jinya,'

  Tsuke fuska hayaam tayi tana faɗin"Bakisan halin dana shiga bane,shiyasa zaki ce haka,tunfa da Sgr ya kore ni daga gidan nan,ban ƙara samun kwanciyar hankali ba,kullum ina ƙumshe acikin ɗaki saboda tsoran kar muyi arba dashi,ga ciwon yunwa dake damuna,ba don azmee ba ae da tuni na jima da sheƙawa,itafa ce take kawomun abinci har ɗakina,wani lokacin in ta manta bata kawo mun ba,sae dai fa in dare yayi kowa yayi bacci in saci hanya inje kitchen in ɗebo abinci,gaskiya nasha wahala sosai,

  "Laifinki ne hayaam,kina zaman zaman lafiyarki acikin gidan nan,Amma kika toƙano masifa,kirasa wa zaki kaima hari sai Sgr,ae wlh ki godema Allah dabai kakkaryaki ba,nikaina nayi mamaki da kikace iya korarki yayi kawai,'

  Tur6une fuska hayaam tayi tare da juyawa tana fadin"Ni dae mu bar maganar ae yariga da ya wuce,kuma ma ae ya yafe mun,bakiga yanzu ina yawo na hankali kwance acikin gidan ba,"

  Aunty babba tace"Allah yasa dagaske ne cewar ya yafe maki ɗin,sai kiyi taka tsantsan kafin mu samu Allah ya cika mana burin mu,don wannan karon da shirina nazo,Bazan bar gidan nan ba,har sai naga an shafa fatihar aurenki,keda Sgr,"

Cike da farin ciki hayaam ta sanya tafin hannunta tare da rufe fuskarta tana sakin dariyar farin ciki,

   "Aunty laila kina ganin hakan zai yiwu kuwa?ga Yaran nan ƴa'ƴan abusufyan,wlh ba ƙananu bane balle ace basu isa aure ba,Sun kaifa sha Takwas inaji,kuma wlh bakiga surar jikinsu ba,matane sosai,ni tunda nagansu ma duk sai naji na tsani kaina,kuma kinga su ƴan gidane za'a iya tunanin haɗasu auren Zumunci...'

  Tunkan ta ƙarasa maganar aunty babba tace"Impossible!wlh bazai ta6a yiwuwa ba!Muddin ina numfashi ɗaya daga cikinsu bazata ta6a auren Sgr ba,kwara ma Omar abra saita haƙura amma Allah sgr ya Haramta agaresu na haramta masu shi,da bala'e sai ya aureki,ko anaso ko ba'aso,babu wani shege daya isa ya hana wlh,babu shi,"yadda Aunty babba ke cika baki tana magana ba ƙaramin dariya ya so yaba hafsat ba dake acikin toilet tana sauraronsu,ita batasan halin da suke ciki ba,sae faman kuri take tana cika baki,

   Ita kuwa hayaam sae faman washe baki takeyi,gaba daya ta miƙa yardar ta ga Aunty babba,ae gani takeyi zata iya aikata komai don ta mallaka mata Sgr,

     Bayan fitar hayaam daga ɗakin Hafsat ta fito daga cikin toilet din,idonta na akan Aunty babba data ɗan kishingiɗa asaman gadon,

  "Mommy yakamata kije kiyi sallah,kinsan fa yanzu za'a hallara gaba ɗaya wurin waleemar yakamata ki hanzarta yin sallar,"

   yatsina fuska tayi tare da cewa"Anya zan iya yin sallar nan kuwa,nagaji sosai,zuwa anjima dai nayi sai in haɗa da magriba duka inyi,"

  girgiza kai kawai hafsat tayi batare da ta ƙara cewa komai ba,don ba yau ta saba yin haka ba,ita kanta hafsat ɗin zamanta dasu jahad ne ta fara yin sallah cikin lokacinta,

  

Zaune yake agefen gadonshi ya zabga uban tagumi,tun bayan da suka dawo daga sallar la'asar,yadawo ɗakinshi atakure,turo kopar ɗakin nashi Abba yayi tare da shigowa ciki,ba ƙaramin tausayi abusufyan ya bashi ba,wuri ya samu tare da zama daga gefenshi sannan yace"Bana faɗa maka cewa ka kwantar da hankalinka ba?jibi yadda duk kabi ka tukura kanka,"

  ɗagowa yayi tare da kai idanunshi kan abba,muryarshi asanyaye yace"bansan ya zanyi bane,hankalina yaƙi kwanciya wlh,bansan wane hukunci Ammi zata yanke mun ba,ni tsorona kada tace bata yarda cewar da aure na samu su jahad ba,kasan halinta yaya hossein,tana da wuyar sha'ani,"

Abba yace"hakane,amma insha Allah zanyi iyakar bakin ƙoƙarina wurin ganin na fahimtar da ita,kaima kasan cewa bazan ta6a bari yaran nan su tozarta ba akan idon kowa,Ammi tana buƙatar hujjoji masu ƙarfi kafin ta gasgata abu,zamuyi kokari wurin ganin cewa munyi amfani da hujjojin da muke dasu a hannu wurin fahimtar da ita,abunda nakeso dakai yanzu ka saki jikinka,nasan cewa da anjima kaɗan idan ta farka daga bacci zata fito nan babban falon,so nake kazo da ƙwarin guiwarka ka gaishe da ita,kasan kun jima baku haɗu ba,kuma dama can kai mai laifi ne a wurinta,'

  fuskar Abusufyan cike da damuwa yace"Hada ƙarin hakan yasa nake fargabar haɗuwa da ita,Ni kullum mai laifi ne a wurinta,ko kirana ma bata ɗagawa,tunda nabar nigeria shekara goma sha,amma mommy bata ta6a ɗaukar waya da sunan zata kira ni ba,kuma ko na kirata bata ɗagawa,ni ina ganin kamar bata so na ne,shiyasa takeyi mun haka,'

   ruƙe hannunshi abba yayi acikin nashi"abunda kake tunani ba haka bane,zanma iya cewa tafi sonka fiye da kowa,kuma ta damu da kai sosai,babban laifin da kayi mata shine naƙin sanar da ita dalilin da yasa kabar Nigeria,ammi batasan komai game da tafiyarka ba,tayi kewarka sosai,don akwai lokacin da ta kirani a waya,kuka ne kawai batayi ba a lokacin,saboda ka tafi batare da saninta ba,wannan dalilin ne yasa take fushi dakai,amma yanzu ina da tabbacin cewar in har muka sanar da ita dalilin tafiyarka,zata fahimce mu,kuma zata kar6i yaran nan hannu bibbiyu,kuma zata yafe maka"

  Jiki asanyaye abusufyan yace"Allah yasa,dana fi kowa farin ciki,"

  Murmushi abba yayi tare da miƙewa tsaye ruke da hannun abusufyan yana cewa"Tashi muje ciki,nasan yanzu haka triplet ɗinka suna nan,sun ɗau wanka suna jiran daddynsu don suyi hoto tare dashi,"

  Jin haka yasa Abusufyan sakin fara'a a fuskarshi nan take yaji damuwarshi ta ragu saboda an ambaci ƴan ukunshi,

   atare da abba suka fito daga cikin ɗakin,adai dai lokacin Hajiya Azeema da gwaggon katsina da saude suma duk sun fito,kowa yasha kwalliya a fuskarshi,ga harris shima tare da Marshal Omar duk sun hallara anan falon,A jere su Sehrish suka fito su uku Ita dasu jahad hosana,sae Amal dake abayansu tare da Amani,

  Ae tunda suka shigo cikin falon hankalin kowa ya dawo kansu,yadda kasan wasu taurari haka suka bayyana,kai tsaye wurin abusufyan suka nufa,haɗasu yayi su duka ya rungumesu sosai,bayan ya sakesu,suka gaishe da Abba tare dasu Marshal Omar dake tsaitsaye a wurin,Hannu abba yasa tare da jan kumatun hosana yace"Amaryar Omar,irin wannan kyau haka,"da sauri tasa hannu tare da rufe fuskarta,tana dariya,kawar da kai gefe Omar yayi yana ɗan sakin Murmushi,da zasu bashi dama da ba abunda zai hana ya rungumota don ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,matsowa kanal yousouf yayi kusa dasu yana fadin"Uncle ni wacce za'a bani acikinsu tunda ya Omar yayi kamun tashi,kada su ƙare ni in rasa,"dariya sukayi gaba dayan su,Uncle abusufyan yace"Layi zaka bi,don mutun ko da kuɗinshi saida rabonshi," Abba ya kar6e da cewa"kwarai kuwa,sae wanda ya dage da sallar dare zamu bamawa,"

  daga bayansu suka jiyo muryar junaid yana cewa"Kamar ni kenan,duk gidan nan babu wanda yakai ni tashi yin sallar dare,"ya ƙarasa maganar tare da ruƙe qugunshi,fuskar nan ɗauke da wannan kyakkyawan murmushin nashi,yayin da idanunshi ke akan jahad,

  fashewa suka kumayi da dariya,kanal yousouf yace"haba junaid,cewa zakayi duk gidan nan babu wanda yakai ka,sharar bacci idan dare yayi,mutumin da daƙyar ake tashin shi sallar asuba shine yake cika baki yana faɗin yafi kowa sallar dare,"

  bubbuga ƙafa junaid yayi cike da shagwa6a yace"Kai yaya yousouf dan Allah ka daina faɗin haka,kada kasa araina ni,"

  "Raini kuma na yaushe junaid!agabansu fa kake bubbuga ƙafa kamar ƙaramin yaro kana shagwa6a,a haka kake cewa kar araina ka,wace mace ce zata so ta auri shagwa6a66an namiji irinka?acewar kanal yousouf,

  Tur6une fuska junaid yayi yana faman zumbura baki,juyawa yayi tare da kai idanunshi kan abusufyan yace"Uncle,ae dai zaka bani kyautar ɗaya ko"?

  Abusufyan yace"mezai hana junaid?ko sisi bana buƙata,duk wacce kakeso acikinsu,zan baka ita kyauta,basai ka biya sadaki ba," gwalo yayi ma kanal yousouf yana fadin"ae dae Uncle yace zai bani,kuma a kyauta ma,"

  Hakan ba ƙaramin dariya ya basu ba,duk wannan rashin wayon da Junaid ke yi akan idon jahad,zubama sarautar Allah ido tayi,aranta tace wai dama haka yake?saboda ita bata ta6a ganin junaid na shagwa6a agabanta ba,hada su gwalo ɗabi'unsa kamar na yaron goye,kaɗan kika gani


Cike da nishaɗi sukeyin firar tasu,adai dai lokacin General ishaq da Abbas suka shigo cikin main palour ɗin,sae faman sakin fara'a suke yi,ƙarasa shigowa sukayi kai tsaye suka nufi inda su Abba ke tsaye,gaishe da abba sukayi,kafin su jahad suka haɗa baki wurin gaisar dasu,


Fuskar ishaq ɗauke da murmushi yace"Masha Allah,nama rasa abunda zance,yanzu wannan duk namu ne"?yayi maganar yana nuna su hosana,Abba ne ya bashi amsar cewa"Naku ne ishaq,halak malak Allah ya mallaka maku,gasu nan harsu uku,"

  Abbas yace"kamar yadda Allah ya nuna mana wannan ranar da ranmu kuma da lafiyarmu,ina fata Allah ya ƙara haɗamu a ranar auransu kamar haka dae........' haɗa baki su Abba suka yi wurin cewa"Ameen,"banda abusufyan wanda ya sunnar da kanshi ƙasa yana murmushi,Sehrish da jahad kuwa duk kunya ta gama rufesu,

 Abba yace"ko baku son auren ne"? Shiru su kayi suna faman ƙumshe dariya,


"Sun ma isa suce basa so?ga yayyansu nan duk tazurai,ae dole su bada hadin Kai asamu a rufa ma juna asiri," cike da zolaya ishaq yayi maganar,yayi matuƙar basu dariya, 


Adai dai lokacin Aunty babba ta shigo cikin falon ita da hafsat,😲




  *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃



*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI.  MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*



*LOCATION KANO*


08062073990

Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku



Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku


It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.

Snack

Awarah 

Farah

Zobo

Samosa

Cup cake etc 

Contact me 09063302182or 09012179727.


   

  

 

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





Tofah nan fa kowa ya shiga tunanin wata hujja ce Sgr ke da ita?kanga wayar yayi a kunnansa,then Calmly ya furta"Ku ƙaraso ciki,"jin haka yasa kowa kai idanunshi kan ƙopar shigowa falon,don ganin su wanene zasu shigo ciki,

Bada jimawa ba,wata haɗaɗɗiyar Wheel chair Golden Colour mai ɗauke da wani dattijo tsoho tukuf fari tass hatta sumar kanshi furfura ce fara tass babu zaren gashi ko ɗaya daya kasance launin baƙi,hatta gashin girarsa dana idonsa fari ne tass duk furfura ta mamaye ko'ina,wani matashi ne ke ruƙe da ita yana turashi a nutse,tashin hankali ae koda Ammi tayi Arba da mutumin dake a saman wheel chair ɗin nan,hankalinta gaba ɗaya ya tashi haikam,ba ita ba Hatta su Abba dasu Gwaggo da Azeema sunyi matuƙar mamakin ganinshi,saboda a iya saninsu baya qasar,a Saudi Arabia yake da zama,amma sai gashi yau Unexpected yazo,wannan wani irin zuwan bazata ne?


Lokacin da matashin ya ƙaraso dashi ciki Ammi ta tabbatar da cewar dagaske dae shine,a kiɗime ta miƙe tsaye muryarta na in,ina ta ambaci sunan shi"Mo...moddibo"

Wani irin kallo tsohon ya wurga mata,kallon zakiyi bayani,gwaggon katsina kuwa wani irin farin ciki ne ya lullu6e ta,saboda tasan cewa tunda Modibbo ya tako da ƙafafunsa yazo Nigeria to tabbas za'a samu maslaha,saboda duk duniyar nan babu wanda ke taka ma Ammi burki in ta burkice sai Shi!mugun shakkar shi take ji,saboda shi tamkar Ubane agareta,a hannunshi ta taso,shiyasa yasan hanyoyi da dama da zai iya tankwarata,kuma duk wasu halaye nata da ɗabi'unta nashi ne sak ta ɗaukko,amma shi da ya manyanta ya ajiye wannan jin kan,'



Bayan saurayin ya tsayar da wheel chair ɗin,Modibbo ya yunƙura tare da miƙewa da sandar hannunshi,cikin sauri suka bashi wuri,ya samu wuri ya zauna a hakimce saman sofa,nan kowa ya shiga gaishe dashi suna yi mashi sannu da zuwa,fuskar nan tashi asake yake amsa masu,ba ƙaramin daɗin zuwan modibbo suka ji ba,bayan ya kammala kar6ar gaisuwarsu ɗaya bayan ɗaya,

  Sannan Ammi tace"Yaya sannu da zuwa,ya gajiyar tafiya"

   Fuskarshi aɗaure yace"Gajiya tabi jiki,ae ba yau nazo ba,tun shekaran jiya ina ƙasar nan,zuwa ne kawai banyi ba,kuma ba don kowa nazo ba sai don saboda ke!"

  Jin haka yasa ta koma ta zauna,jiki asanyaye,

Cikin sauri Abba ya kalli su fawan tare dayi masu alamar su tashi su bar wurin,"mikewa su kayi dama Jahan a ƙagare yake daya bar wurin,duk ji yake kamar ya ɗosa mazannansa akan wuta,atare suka miƙe tare da barin wurin,Ya rage daga Gwaggon katsina,Abbansu,hajiya Azeema,General ishaq,da Cg Abbas,Uncle Abusufyan,marshal Omar da Sgr,bayan su kuma sae su Jahad dake zaune ƙasa,duk sunyi zuru rayuwarsu a hannun Allah,basu san su wanene waɗannan tsoffin ba,amma sun tsorata dasu,musamman Ammi data tayar masu da Hankali,har tana ƙoƙarin korarsu daga gidan,


Bayan su jahan sun shiga ciki,ya fashe da dariya hada dafe ciki yana faɗin"Dama ance GABA DA GABANTA ALJANI YA TAKA WUTA"💥


Junaid kuwa,bedroom ɗin Abbansu ya wuce,anan ya samu mommynsu tsaye agaban drawer,jikinta sanye da doguwar riga,tana ƙoƙarin sanya mayafi akanta,

  Sam bata lura dashi ba,har saida ya ƙarasa bayanta tare da rungumota,hannu tasa tare da janyoshi ta dawo dashi ta gabanta,a shagwa6e ya ambaci sunanta"Mommy dama kina a ɗaki,bakisan meke faruwa ba a babban falo,"

  Hannu tasa tare da shafa fuskarshi tace"Romeo,bani da alaƙa da abunda ke faruwa acan,yanzu faɗamun naga fuskarka kamar akwai damuwa,"

  "Mommy,ba Ammi bace take son korar su Jahad daga gidan nan ba,"

  "To menene damuwarka aciki don ta kore su"?

  Sakin baki junaid yayi yana kallonta kafin ya ɗaure fuskarshi yace"Haba Mommy,ƴa'ƴan uncle ɗinmu fa ne,taya ba zan damu ba,uncle fa yana sonmu sosai,muma dole mu so ya'yanshi,kuma su jinin mu ne,nidai wlh banso ta koresu,kuma Allah koda ace ta koresu,wlh saina bisu.....'ya ƙarasa maganar yana zum6ura baki,

  Hannu tasa taja kumatunsa"Ni kuma an gaya maka zan barka ne?zansa a ɗauke mun kaine,in kaika U.s mu cigaba da rayuwarmu acan,ko ba zaka bi mommynka bane,"

   Bubbuga ƙafarsa yayi tare da cewa"I wanna fallow u Mom,amma Allah sai dai mu tafi mu duka tare dasu sehrish,jahad da hosana,"

   "Dole dai saina je dasu"?

ɗaga mata kai yayi alamar eh,janyo shi tayi ta rungumeshi ajikinta,"don't worry dear kome kakeso zanyi,indae hakan zai faranta maka rai,yanzu mu zauna ka tayani fira,inaso mu tattauna wata magana dakai mai mahimmanci,"

  Komawa sukayi tare da zama daga saman gadon,suka ci gaba da tattaunawa a tsakaninsu,


*Aunty Babba*


Lokacin da suka faɗa cikin ɗakin suna murna ita da hayaam,tsayawa sukayi daga tsaye,suna tattaunawa,Aunty babba tace"Ae dama saida raina ya bani cewar Ammi bazata barsu su zauna a gidan nan ba!gaskiya matar nan ta burge ni wlh,yadda ta zagesu tass ta kirasu da shaggu hakan ba ƙaramin nishaɗi ya sani ba,in banda ma shashasha irin Abusufyan taya zaka kawo ƴa'ƴa daga sama kace ya'yanka ne,kuma kayi tunanin cewa kowa zai yarda dakai?Ae ni wlh tayi mun dai dai matar nan,"


Ta ƙarasa maganar tana faman sakin shu'umin murmushin nan nata,


Hayaam tace"Nima ba ƙaramin burgeni tayi ba,naci dariya lokacin data korasu suka watsa aguje suna kuka,ƴan jakar uban,yanzu sai muga ina zasu dosa,dama su kashe kansu kawai su huta muma kuma munsamu natsuwa," cike da nishaɗi take maganar tana watsa hannu alamar ita ko ajikinta,

  "Dama abunda yasa nake son Ammi ta koresu,kinga na farko zasu fita daga cikin zuri'arsu ne gaba ɗaya,babu su babu auren ɗaya daga cikin ƴa'ƴan Abba,saboda Ammi bazata bari su auri bare ba,balle kuma yaran da ta ambaci sunansu da shaggu,Secondly kuma wannan korar da tayi masu,zai hana Ishaq da Omar su tuhume ni akan tonan asirin da waccen Zararrar taso tayi mun a bainar jama'a,kinga riba biyu kenan," 

  Tana kai karshen maganarta,hayaam ta ɗaura da cewar"wannan haka yake Auntyna,mu ɗin jinin nasara ne,duk abunda muka sa agaba sai munga bayanshi koma uban menene shi,"

  Dariyar mugunta Aunty babba ta kuma saki kafin tace"Bazan ƙyalesu haka nan ba,saboda Omar zai iya bin bayansu don ya taimakesu,dole in samu wanda zaibi takansu da mota su mutu kawai,kowa ya huta,"

  Hayaam tace"faƙat!kinga babu su a duniyarma balle ayi dasu,"

.......duk wannan surutan da suke yi,Amani na la6e a ƙopar ɗakinsu wadda bata idasa rufewa ba,tana recording ɗin muryoyinsu a wayarta,don taci alwashin saita tarwatsa duk wani plan nasu,Ni boss nace kinyi mun dai dai,


*Boss Bature*

The genius


  ❤🤍❤


bari mu leƙa falo muga meke wakana,shin ansamu cigaba ko kuwa ana nan yadda ake?


Natsuwa su kayi gaba ɗayansu,wurin yayi tsit tamkar mutuwa ta gifta,kowa ya natsu ya nabba'a tamkar ɗalibai ne agaban ya sayyadi,bafa sayyadi mijin abu ba,ina nufin malami,kar ayimun wata fahimta,


"Waɗannan sune ƴan ukun Abusufyan ɗin"modibbo ne yayi maganar yayin da idanunshi ke akan Su jahad dake zaune sunyi zuru zuru,'

  Har suna haɗa baki wurin cewa"Sune,"

Jinjina kai yayi tare da mayar da idanunshi kan Ammi yace"Ki kace yaran shaggu ne ko?Wata hujja gare ki na cewar bada aure ya haifesu ba?

  Fuskarta aɗaure tace"Ina da hujja,saboda nice mahaifiyarshi,kuma ni bansan an ɗaura mashi aure da kowa ba,"

  Girgiza kai modibbo yayi,sannan yace"hannunki ya taso ne?ko kuwa wurin ki kaɗae  za'a iya ɗaura mashi aure ne"?

  Shiru tayi batace masa uffan ba,cigaba da magana yayi"don haka baki da wata hujja ta cewar abusufyan yayi aure ko baiyi aure ba,ya samu ƴa'ƴa,wlh Aisha kin ban mamaki!wai har yaushe ne zaki ajiye waɗannan makaman yaƙin naki ne?ke fa yanzu ba yarinya bace,kin tara ya'ya da jikoki amma har yau bazaki ajiye wannan zafin ran naki ba,sai yaushe ne ya'yanki da kuma jikokinki zasu ji daɗin zama dake ne?yanzu ni ba misali bane agareki?ko bakisan wanene modibbo ba?kinfi kowa sanina bani da wasa ko miskala zarratin,duk wani kangararre acikinku,keda ƴan uwanki nine nan nake tankwarashi,amma yanzu saboda na manyata,na tara ya'ya da jikoki,duk na ajiye waɗannan ɗabi'un,Na canza kaina ne ba don komai ba sai don saboda ya'yana da kuma jikokina suji daɗin zama dani,kuma suyi alfahari dani amatsayina na kakansu,bawai su dinga tsoro na ba,suna gudu na harma su dinga yi mun fatan mutuwa,kamar ke ɗin nan dai.....'yayi maganar yana nuna ta da sandar hannunshi,sunnar dakai Ammi tayi tana faman jinjina kai,


Canza harshe modibbo yayi izuwa harshen fulatanci,yayi hakan ne saboda kada faɗan da zaiyi mata ya zama tamkar tozarci ne agaban jikokinta,


  "Gaba ɗaya kin takurawa rayuwar ya'yanki,da ta jikokinki,kin hanasu sakat,ko irin wasan dake tsakanin kaka da jikan nan bakya yi masu,kullum burinki ki ƙuntata rayuwarsu,shin menene ribarki idan kinyi hakan? Ya ɗan dakata da maganar yana kallonta,kafin yaci gaba da cewa"Yanzu jibi yaran nan ƴan wurin fatima,hakanan kika ɗaura karan tsana kika ɗaura masu sai kace ba jininki ba!in ma saboda mahaifiyarsu ne,ke kin ta6a ganin inda laifin wani ke shafar wani ne?in kuwa haka ne ae da dukkanmu mun shiga uku,saboda wancan zaiyi sata ne a ɗaura maka laifin bayan bakai ne ka aikata ba,"

  Katse shi tayi cikin harshen fulatanci tace"Amma yaya modibbo ni meyasa ya'yana basu jin maganata ne?basu ɗaukeni mahaifiyarsu ba,suna yin abu gamon kansu batare da sun sanar mun ba,Hossein ya ƙetare ƙasar nan yaje yayi aure batare da sani na ba,sai dai kawai na ganshi da mata ya dawomin,matar kuma ma farar fata ba jinsun mu ba,sannan kuma Abusufyan shima yayi aure batare da sani na ba,saboda me zasuyi mun haka ne?

anzo dai dai wajen,acewar modibbo gyara zama yayi sannan yace"kin manta yadda akai kika auri salahuddeen ne?to idan kin manta bari na tuna maki,dama duk wanda ya bijire ma iyayensa ko ba daɗe ko ba jima sai shima yaga ba dai dai ba,na farko bada sa hannun iyayenmu ba,kika shiga aikin Soja,babu irin yadda ba'ayi dake ba don ana ganin bai dace dake ba,ba kaman daya kasance ke bafullatana ce,amma kika ƙeƙashe ƙasa kikace sai kinyi aikin soja,a ƙarshe da aka takura maki,shine kika tattara kayan ki kika dawo gidana da zama saboda kina tunanin cewar ni zan goya maki baya don ki samu abunda kikeso,da kika zo wurina a lokacin na nuna cewar nima bazansa hannu na ba acikin lamarin tunda har iyayenmu sun nuna basu so,a ƙarshe sai kika gudu batare da sanin kowa ba,kika shiga aikin Soja,sae dai kwatsam muka ganki da kakin Soja ajikinki,ko ba haka akayi ba"?


Wata irin zufa ce ta shiga wankowa a fuskar Ammi sam bata ta6a tsammanin cewa wannan ƙaramin kuskuren data aikata na bijirema iyayensu,zai dinga bibiyar rayuwarta bane,

"Akan wannan aikin sojan da kika shiga,babu wanda baiyi kuka dake ba,saboda kafiya,da taurin kai irin naki,ga jinkai dake gareki,iyayenmu basu isa su baki umarni kai tsaye kiyi abu ba,sai sun biyo ta wurina saboda shakkarki da suke ji,bayan wannan kuma,baki sanar ma kowa ba game da salahuddeen lokacin da kuka fara soyayya dashi ba,sai daga baya ne muka fahimci shi ya hure maki kunne har kika bijire mana kika shiga aikin sojan,hakan kuma yasa duk muka ki amincewa da farko ki aure shi,amman da yake Allah ya kaddaro aure tsakaninku ba yadda muka iya dole muka kyale ki ko don kafewar da kika yi da kuma rabon itama Ameena anan zata samu mijin, ko ba haka akayi ba"?

  Jinjina kai Ammi tashiga yi yayin da idanunta suka cicciko tab da kwalla amma bata bari sun zuba ba,

Gwaggon katsina kuwa,sae faman sakin murmushi takeyi,tana faɗin"kwarai kuwa,haka akayi,"Abban su junaid kuwa da hajiya azeema duk jikinsu yayi mugun sanyi,sae yanzu suka gane daga inda matsalar take,dama duk in mutun yaga rayuwarshi tana tafiya ba dai dai ba,kuma bai akaita wani zunubi,toWlh ya binciki kanshi!ya tuhumi kanshi ahankali zai gano dalili,


Su jahad dae suna nan tsugunne sun kasa kunne suna sauraronsu,sai dai subi bakin modibbo da kallo,daga bisani in Ammi na magana subi ta da kallo saboda basu iya fulatanci ba,haka Marshal Omar dasu ishaq duk basa jin fulatanci,haka zalika Sgr baya jin harshen nasu,dama shi ko hausa daƙyar ya koye ta,kuma har yau in yana magana da harshen hausa sai ka gane cewar ɗan koyo ne don sam hausarsa bata nuna ba shiyasa bai fiye yin magana da hausa zalla ba saiya haɗa da turanci ko spanish,amma kuma hausar tashi ba ƙaramin daɗi takeyi ma mutane ba,


  Murmushi Modibbo ya ɗan saki kafin yaci gaba da cewa"ina fata yanzu kin tuna komai"?

  Siraran hawayen da take 6oyewa ne suka gangaro a saman fuskarta,muryarta ƙasa ƙasa tace"Na tuna,"

  Modibbo yace"Tunda kin tuna bari na ƙara ɗaura ki akan hanya,irin abunda kika aikata ne yasa shima ɗan cikinki da kika haifa yaje yayi aure batare da saninki ba,saboda gudun kada ya fara sanar dake ki hana shi yin auren,hossein ya auri Alala..kunzandariya...."kasa ƙarasa maganar yayi saboda bai iya ambaton sunanta ba,abun yaso yaba Sgr dariya,amma ya basar da ita tare da gyara mashi sunan yace"Alexandra ne sunan,"

Modibbo yace"yawwa ɗan gari,bazan dai iya Ambaton sunan nata ba,a barshi a fatima,tunda ae ta ta6a musulunta,kuma muna sa ran zata ƙara musulunta insha Allah,"

  Suka ɗanyi dariya,kafin ya ɗaura da cewar"Hossein ya auri fatima batare da saninki ba,saboda yasan halinki sarai kin tsani jinsin da ba naki ba,gudun kar ya sanar dake kiƙi amince masa yasa shi yin hakan,sannan......"modibbo bai ƙarasa maganar ba,ammi ta kuma katse mashi hanzarinshi da cewa"Yaya modibbo amma ae ni harsu biyu sukayi mun haka!bayan ni,ni kaɗai ce na bijire ma iyayenmu haka,"

  wannan maganar ta Ammi yasa shi yin dariya,tare da girgiza kai yace"in kikayi wata maganar kina tunamin da ƙuruciyarki wlh,dama ita irin sakayyar nan tamkar ramuwar gayya haka take,kuma ita ramuwar gayya tafi ta gayyar zafi,sakamakon abunda kika shuka ne,yasa kika girbi kyakkyawan sakamakon da ya zarta nakin,kuma tunda har kika iya ƙyale hossein bayan laifin daya aikata maki na auren bare kuma farar fata ae yaci ace kin yafe ma Abusufyan tunda shi da ƙuruciyarshi ya auri yarinyar,kuma hada sa hannun gwaggonshi,kuma kinsan wacece ita a wurinki,da mahaifinmu da nata uwa daya uba daya,kuma saboda yardar da kikayi da itane yasa kika damƙa mata amanarshi,ita kuma ƙaunar da take yi maki ne ya shafi ɗanki da kika haifa,hakan yasa ba zataso wani abu ya cutar dashi ba,Yaro ya nuna yana son ƴar mai gadin gidansu,ke kuma kin tsani auren bare mara asali,gashi shi kuma yaron ya kwallafa rai akan yarinyar,don lokacin da ita Aminatu taso ta sanar dake game da yarinyar balbaleta kikayi da masifa,kina cewa karta kuskura ta bari alaƙarsu tayi nisa,ta raba tsakaninshi da yarinyar,a ranar saida Abusufyan ya suma jin za'a raba shi da abunda yakeso,wannan dalilin ne yasa hajiya ameenatu ta aura mashi yarinyar batare da ta sanarma kowa ba,sai ni ɗinnan da nake magana,"

  ɗagowa Ammi tayi tana kallonshi cike da mamaki,

  Jaddada mata maganar yayi"kwarai kuwa ta sanar dani,nasan da zancen auren,kuma aranar da aka ɗaura auren Abusufyan da zainabu abu,ina ɗaya daga cikin waɗanda suka halarci ɗaurin auren batare da sanin kowa ba,ita kanta hajiya ameenatu batasan na halarci ɗaurin auren nasu ba,a iya waya kawai ta sanar dani,sae kuma akaci sa'a ina da wani taron manyan malamai da zamu halarta anan jihar kano,wannan ne babban maƙasudin daya kaini garin harna shaida wannan ɗaurin auren....."

Ae tunkan modibbo yakai ƙarshen maganar wani irin murmushin farin ciki ya bayyana akan fuskar kowannansu,saboda yayi maganar ne cikin harshen da zasuji,wata irin nauyayyiyar ajiyar zuciya abusufyan ya shiga saukewa,nan take yaji wani irin sanyi ya ratsa zuciyarshi,duk da yayi mamakin zuwan modibbo wurin ɗaurin auran nashi saboda bai ganshi ba,amma tunawa da irin dubban al'ummar dake a masallacin kuma ya kasance ranar juma'a ne ana kammala salla aka ɗaura auren nasu,tabbas bazai iya tantance kowa dake a wurin ba,amma ko a lokacin bayan an ɗaura auren sun koma gida sai da baba buzu ya kirashi gefe guda yake sanar dashi cewa"Wani babban malami,yayi mashi alheri bayan sun fito daga masallaci,kuma yana tunanin cewar Kamar jininsu ne saboda yaga kamannin Hajiya ameena a fuskarshi,a lokacin Abusufyan bai gane wanene ba,sai yau da modibbo yayi maganar nan kwatsam ya zancen ya faɗo mashi aranshi bayan ya shiga zurfin tunani,tabbas kuwa modibbo ne,

  Murmushi modibbo yayi tare da kallon Abusufyan yace"nasan zakayi mamaki,saboda nazo ɗaurin auren ka batare da sanin kowa ba,uzuri ne ke gare ni a lokacin shiyasa ban nemeka ba,don nasan muddin ka ganni a lokacin saika nace akan in tsaya,"

  ya ƙarasa maganar tare da mayar da idanunshi kan Ammi,tun kafin ya kuma cewa wani abu,muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"Amma yaya kasan da maganar auren nashi shine ba'a sanar dani ba?saboda me?

  "Saboda halinki"! Kai tsaye ya bata amsa,

  "Tabbas naso in sanar dake ko alokacin,saboda kinsan cewa ni bana jin shakkarki,hajiya ameenace ta rokeni akan cewar karna sanar dake,saboda hakan zai iyasa ki fusata harma ki yanke ma Abusufyan hukunci mai tsanani,kuma a ƙarshe zumuncin dake tsakaninki da ita ya tarwatse,dana nace akan zan sanar dake har kuka saida tayi mun,wannan dalilin ne yasa ban sanar dake ba,kuma ana haka daga baya kwatsam naji labarin mutuwar auren Abusufyan ɗin,hada ƙarin haka yasa akabar zancen gaba ɗaya,ashe yarinya ta fita da cikinsa ta auri wani,to kinji dalilin dayasa mu kanmu bamu san da ya'yan nashi ba,har suka kai wannan girman a hannun mijin da ta aura daga baya,"

  Dakatawa yayi da maganar,falon yayi shiru na wani lokaci,kafin ya mayar da idanunshi kan Sgr dake zaune,yace mashi"ka kunna mata audio din nan daka kunna mun itama ta saurare shi,"

  "Okey,"ya amsa mashi tare da,daddana wayar hannunshi,ya shiga audio din tare da kunnashi,sannan ya miƙe tare da ƙarasawa kusa da kujerar da Ammi ke zaune ya miƙa mata wayar,yatsun hannunta na kerma tasa hannu ta kar6i wayar tashi,ta ajiye asaman hannun sofa ɗin tana sauraronshi,wannan audio din na labarin da abusufyan ya bayar ne da kuma Labarin dasu sehrish suka bayar na irin ukubar da suka sha a hannun ya sayyadi,ashe ranar da abun ya faru,Sgr ya ɗauki audio na maganganun da sukayi kaf acikin wayarshi,tabbas shi ba ƙaramin jami'in Soja bane!yana Aikinsa wani lokacin tamkar jami'in sirri,Na jinjina masa,da irin baiwar da Allah yayi mashi da kuma irin kwazon dake gare shi,ta ko ina Sgr ya haɗa,shiyasa nace maku shi ɗin komai nasa Extraodinary ne~~~ 


Miƙewa junaid yayi tare da ruƙo hannun Mommynsu yace"Shikenan mommy tunda mun kammala discussion din,ki taso muje falo pls,kada kice baki zuwa,in ba haka ba raina zai 6aci,wlh ko abincin dare bazanci ba,indai kika ƙi zuwa gaishe da modibbo,"

Cike da mamaki tace"Modibbo?kana nufin mahaifin maryam oummunsu Omar?

  daga mata kai yayi alamar eh,

Shiru tayi tana wani tunani,a iya saninta modibbo mutunne mai mutunci sosai,saboda shine ya taka ma Ammi burki a lokacin da taso Abba ya sake ta,tabbas bazata ta6a mantawa da halarcin da modibbo yayi mata ba,

Ganin ta miƙe yasa junaid sakin murmushi yace"mommy zaki ko"? Jinjina mashi kai tayi alamar eh,

Janyo hannunta yayi har suka ƙaraso falon,ganin hankalin mutanen dake acikin falon gaba daya yana akan Audio din da ammi ke saurare,hakan yasa itama ta samu wuri ta zauna,junaid ma ya zauna gefenta,yayin da idanunshi ke akan su sehrish,sam basu lura dashi ba saboda hankalinsu duk ya tashi,a sakamakon Audio din da aka kunna,saboda sun tsani jin labarin rayuwarsu,ko miskala zarratin,

  Kowa ya natsu yana sauraron audio ɗin,lokacin da Abusufyan ya kammala bada tarihin rayuwarshi da abu,sai next audio ɗin ya shiga wanda Jahad ke bada labarin rayuwarsu,nan take hankalin AMMI yayi mugun tashi,jikinta har tsuma yakeyi,tuni wasu siraran hawaye suka shiga zarya a kuncinta,ita kanta Alexandra jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,tunda take arayuwarta bata ta6a jin tausayin wani ɗan adam ba,daga ita har ammin kamar yadda sukaji tausayin waɗannan bayin Allahn ba,Very heart touching story,wanda duk wani mai imani In ya saurareshi dole ya zubda hawaye,in ma baiyi kuka ba,

   Ganin yadda hawaye ke sintiri akan fuskar AMMI yasa Omar ya cire hanky daga aljihunsa ya miƙa mata,dama kamar yasan cikin buƙatarshi take,a fuskarta ta kifa hankacif ɗin,ta fashe da matsanancin kuka mai cin rai,kowa yayi mamakin yadda Ammi ke kuka,cikin shessheƙar tace"ku kashe mun audio din nan ya isa haka,kunnuwa na bazasu iya jurar jin wannan tashin hankalin ba,'

  dama Audio ɗin yazo ƙarshe,junaid ne ya mike ya ɗauki wayar,tare da miƙa ma babban yayansu ita,ya kashe audio ɗin,

  "Shiyasa akeso ko da yaushe mutun ya kasance mai sauƙin kai,kada ya cika tsaurara al'amurransa,yanzu da ace banzo ba,da shikenan,haka zaki kora yaran nan,ke baki tsaya kinyi bincike ba,kuma baki saurari bayani daga gurin kowannansu ba kawai kin tashi kin yanke hukunci,sai daga baya kuma kizo kina danasani"

  daƙyar ammi ta iya furta"Astagfurullah Allah na tuba!ka yafe mun,rashin sani ne yasa na kirasu da shaggu,game da halin da yaran nan suka tsinci kansu,duk laifin mahaifinsu ne,shine silar komai,duk da daman Allah ya ƙaddara faruwar hakan babu wanda ya isa ya hana,amma Abusufyan bai kyauta ma rayuwarsu ba,meyasa bai sanar ma kowa ba don aɗauki mataki?saboda kawai yayi mashi barazana?Amma dai Allah ya tsine ma fasiƙin mutumin nan,Wlh bazan barsu ba,saboda me laifin kakansu zai shafe su?wannan wata irin mugunta ce mara kan gado,?bai tsaya a iya kan ya'yan salahudeen ba,hada jikokin duka yake ɗaukar fansa akansu,?kuma shima salahudeen ɗin daya kashe mahaifinsu ae don saboda mugayen laifukan da aka kamasu dashi ne,ɗaukar fansar ta mutun ukuce suke ɗauka,mahaifinsu da kuma mahaifiyarsu,da kuma wannan ɗan koran nasu,dukkansu Allah zai toni asirinsu,'

  Jinjina kai modibbo yayi yana sauraronta saida takai ƙarshen maganarta,tukunna yace"ba komai ne yasa na tako nazo ƙasar nan ba,face don abu uku,kuma ina fata zaki bani haɗin kai domin asamu maslaha atsakaninku gaba daya,saboda baza a ta6a cin nasarar gano waɗannan masu ɗaukar fansar ba,har sai ku na cikin gidan kun fara haɗa kanku,in ba haka ba,munafukan dake shirya maku zagwan ƙasa zasu samu nasarar cin galaba akanku,ta hanyar rarraba kawunanku,saboda ni inaji araina cewar masu shirya wannan maƙarƙashiyar suna ATARE DAKU!sun shiga cikinku,suna acikin rayuwarku!'


 Wannan maganar ba ƙaramin jijjigasu tayi ba,don sai da kowannansu ya ɗago yana kallon fuskar modibbon,

  "Nasan zakuyi mamaki amma nan gaba sannu a hankali zaku shaida maganata,yanzu dae bari inyi abunda ya kawoni,"

  "AISHA" Ya ambaci sunan Ammi,muryarta asanyaye ta amsa mashi da Na'am,

  "Banaso in ƙarajin wani ƙorafi akanki!wannan ne na farko kuma wannan ne na ƙarshe!idan har kinaso ki zauna lafiya,to ki gyara tsakaninki da ya'yanki!da kuma tsakaninki da Jikokinki,na uku kuma shine tsakaninki da surukarki fatima,"ya ƙarasa maganar yana nuna Alexandra da sandar hannunshi,ɗagowa ammi tayi tare da kai idonta kan Mommynsu junaid wadda itama kallon nata takeyi,kawar da kanta tayi gefe batare da tace komai ba,

  Cigaba da magana modibbo yayi,"Allah ma mukanyi masa laifi kuma ya yafe mana,balle mu ƴan adam,fatima bata yi maki laifin komai ba,tun farko koda kike mata magana take mayar maki saboda kin nemi cin zarafinta ne!wanda kuma ba kowa ne zai iya jurewa ba,balle ita da take jar fata,yanayin rayuwarsu ko ince tarbiyarsu ba irin tamu bace,don da a ƙasarsu ne kikayi mata haka zata kaiki ƙara kotu ne a yanke maki hukunci,babu ruwanta da Cewar ke surukarta ce,sannan kuma bai kamata ki nuna mata ƙiyayya ba,duk maison naka ae masoyinka ne!ɗanki fa takeso,kuma saboda son da take mashi tabar iyayenta da kowa nata tazo ƙasar nan,inda bata san kowa ba,ko tsoron acutar da ita batayi ba,bakowa ne ma zai iya wannan kasadar ba,don haka yakamata ki so fatima saboda masoyiyarki ce,ba maƙiyiyarki ba,idan don ta kasance farar fata ce,damu dasu shin ba Allah bane ya halicce mu ba?ya banbanta mu ne?ko wani yafi wani ne"? Ya ɗan jinkirta da maganar yana kallonta,

  Kafin ya ɗaura da cewar"Yakamata ki ajiye wannan gabar dake tsakaninki da ita,Yanzu fatima ta wuce suruka a wurinki,tamkar ƴ'a take a wurinki,tunda ta hayayyafa da ɗanki,yakamata kiyi alfahari da ita saboda itace ta haifa maki ɗaya daga cikin jikokinki wanda duniya take alfahari dasu,waɗanda suka ɗaukaka darajar mu a idon duniya,"

  Nauyayyiyar ajiyar zuciya Ammi tasaki tare da gyaɗa kai tace"Insha Allah komai ya wuce,"

  Murmushi Abba ya saki ranshi fari tass kamar an yi mashi albishir da gidan aljanna,

  "Sannan kema Fatima inaso ki ajiye dukkan wasu makaman yaƙin ki,kibi surukarki tamkar mahaifiyarki,kiyi mata biyayya amatsayinta na wadda ta tsugunna ta haifi uban ya'yanki,"

  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Nima a wurina komai ya wuce,dama saboda ƙiyayyar da take nunamin ni da ya'yana ne yasa nima nake ƙinta,amma daga yanzu insha Allah babu wanda zai ƙara jinkan mu,"

  Tana kai ƙarshen maganar junaid yace"Gaskiya,wannan sulhun bai cika yadda akeson shi ba,Mommy da Ammi basu ta6a yin koda musabaha ba,yakamata yau su tashi su rungume junansu ta hakan ne zamu gane cewar sun shirya da junansu,"

  Gaba ɗayansu suka saki murmushi,miƙewa Alexandra ta farayi kamin Ammi itama ta miƙe,suka ƙarasa tare da rungume juna,tafi su Abba suka shiga yi wanda hakan yaja hankalin sauran matasan gidan,har suka firfito cikin falon don suga me ke wakana,ae koda su kayi arba da Ammi da Alexandra rungume da juna,nan fa suka shiga sowa,abun ba ƙaramin farin ciki ya sanyasu ba,musamman su Fawan don sun jima suna jiran wannan ranar tazo,ashe da rabon zasu ganta da idanuwansu,

  "Ki yafe mun duk abubuwan da nayi maki,kuma inaso ki sani ba don bana sonki bane yasa nayi maki hakan ba,kawai haline irin nawa,da kuma sharrin shaiɗan" Ammi ce tayi maganar ayayin da take raba jikinta daga na alexandra,fuskar kowanansu ɗauke da siraran hawaye,

  Murmushi alex ta saki kafin tace"Allah ya yafe mana gaba ɗaya,inaji kamar nafi kowa farin cikin wannan ranar,"tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya,suna cikin rahar nan sukaji ana ɗaukarsu hoto ket ket!!

  Da sauri suka waiga don su ga wanene,ashe wai fawan ne ya ɗauko camera ɗinsu,yana ɗaukarsu hoto yana faɗin"yau a daily trust dole su buga wannan gagarumin labarin,zazzafan gaske,Ammin mu wato kakarmu a yau ta rungumi surukarta wadda ta kasance mahaifiyarmu bayan sun dade suna shan gwagwarmaya ,"

  Dariya sosai su kayi,ganin ya sanyasu raha,yasa shi cewa"Abba mu shigo ciki a ƙarasa tattaunawar tare damu?

  Fuskar Abbansu ɗauke da murmushi yace"why not,a yanzu an sasanta komai,an samu maslaha,zaku iya zuwa ku zauna," 

  Jin haka yasa suka ƙaraso ciki,gaba ɗayansu ne hada su twins jabeer,khaleed irfan dasu kanal,wuri suka samu suka zazzauna a ƙasa,

  Junaid yace"Yawwa Amminmu,yanzu saura Uncle ɗinmu bawan Allah,yayi missing ɗinki sosai yakamata shima ki rungumeshi,ko yaji sanyi aranshi,"ya karasa yana langa6ar da kai.

   Juyawa Ammi tayi tare da kallon abusufyan wanda ke a zaune,idonshi na kallon ƙasa,

  Gyaran murya ta ɗan yi mashi,ya ɗago da idonshi ya kalleta,cike da zolaya tace"So kake sai nace ka taso"?

  Fashewa yayi da dariya,kafin ya miƙe da sauri ya faɗa jikinta,sosai ta rungume shi ajikinta,tana ɗan bubbuga hannunta a bayanshi tace"nayi kewarka sosai,ka sani kuka Abusufyan,fiye da tunaninka,hakanan ka tafi ka barni shekara da shekaru...."tana maganar hawaye na fita a idanunta,

  ɗagowa yayi daga jikinta,idonshi na fitar da kwalla yace"Ki yafe mun Ammi,nasan ban kyauta maki ba,nayi maki abubuwa da dama wanda bakyaso,nasan cewa hada haƙƙinki ne ke bibiyar rayuwata shiyasa ma harya shafi ya'yana,...."

    Hannu tasa tana share mashi hawayenshi tace"Na yafe maka abusufyan,dama ni burina shine ka dawo kusa dani,kuma Alhamdulillah,gashinan ka dawo cikin yan uwanka,naji daɗin hakan sosai,Allah ya ƙara haɗamun kanku,"

  gaba ɗaya suka amsa da Ammin,

"AMMI saura su rishi,su baki rungumesu ba,kalli fa kiga yadda duk suka shiga damuwa,bayin Allah,"

junaid ne ya sake yin maganar yana raku6e fuska,alamar tausayi

   Kallonsu Ammi tayi,sun cunkushe wuri guda kamar kifin gwangwani,musamman Sehrish jikinta har lokacin sae kerma yake,a hankali Ammi ta taka izuwa inda suke,ta zuƙunna agabansu,sannan takai hannunta tare da shafa fuskokinsu,kafin tace"dole in nemi yafiyarku,saboda na jefebku da mummunan kalma,bisa rashin sani,ina mai matuƙar baku Haƙuri akan abunda ya faru a rayuwarku!ba laifinku bane laifin wasu ne akeso a ɗaura maku shiyasa aka biyo ta hanyarku duk don a ƙuntata mana,amma nayi maku alƙwarin cewa ɗaya daga cikin waɗanda sukayi sanadiyar wulaƙanta rayuwarku,Wlh bazai sha ba!daga rana irin ta yau zansa a fara bincike akansu har sai Allah ya tonu asirin kowannansu,kuma nayi maku alƙawarin cewa,zansa akawo maku wannan fasiƙin mutumin har inda kuke don ku wanke mun mummunar fuskarshi da tafukan hannayenku,"

  Jin wannan maganar ta Ammi yasa Hosana fashewa da dariya,har white teeth ɗinta suka bayyana,dimples ɗin fuskarta suka lotsa,Jahad ma murmushi ne ya bayyana a fuskarta,sehrish ce kawai batayi murmushi ba,da alama kamar akwai wani abu dake damunta,duba da yanayin jikinta dake ta kerma,

  Ruƙo hannayensu ammi tayi tare da miƙar dasu tsaye sannan ta haɗasu duka ta rungumesu sosai,ajikinta,

Wani irin matashin murmushi ne ya bayyana a fuskar kowannansu dake a falon,haƙika sunji daɗin wannan ranar,tsakaninsu da Allah sai godiya daya bar Modibbo a raye har zuwa wannan lokacin,saboda shine silar komai daya faru ayanzu,da bai zo ba da akasin hakan ne zai faru,

   Addu'oi' Ammi ta shiga karantowa tana tottofa masu akawunansu,a ƙarshe tace"Allah yayi maku ALBARKA,"suka amsa mata da Amin,

  Komawa su kayi kowa ya zauna,itama ammin ta zauna,bayan kowa ya natsu Modibbo yace"ko akwai mai magana acikinku"?

  Da sauri Abbansu junaid yace"Ina da magana,"

Modibbo yace"faɗi kai tsaye muna sauraronka,"

   "Yawwa kawuna,dama akan maganar fatima ne da Abusufyan!har yanzu basu shiri a tsakaninsu,tun wani sa6ani da suka ta6a samu a lokacin baya,to har yanzu basa jituwa,yakamata aduba lamarin,'

  Sunnar dakai ƙasa Abusufyan yayi,kamar yadda itama alexandran tayi,

  "Ae yanzu ko banyi masu magana ba,zasu shirya kansu ne ko don zumuncin dake a tsakaninsu,da kuma ƴa'ƴayensu,"

  Murmushi kowannansu,yayi abusufyan yace"Insha Allah komai ya wuce a wurina,dama can ni ban ta6a ruƙeta araina ba,nasan rashin kunyar da nakeyi mata ne a lokacin baya yasa take fushi dani har yanzu,amma ina neman afuwarta,"

  Yana kai ƙarshen maganarshi,Alexandra tace"Nima komai ya wuce a wurina,Allah ya yafe mana baki ɗaya,kuma ya ƙara haɗa kawunanmu,"

 Wani irin ihu junaid ya fasa,saboda tsabar farin ciki,hankalin kowa ya koma kanshi,ganin sun zuba mashi ido yasa shi sanya tafin hannunshi ya rufe fuskarshi,saboda kunyar data rufe shi,ƙasa ƙasa yake sakin dariya,bakomai ne yasa shi wannan farin cikin ba,face Shiryawar da Momnynsu tayi da Uncle ɗinsu,ko ba komai zai samu amincewarta wurin auren ɗaya daga cikinsu,💃


"Gobe da safe zan wuce damaturu,tunda naci nasarar haɗa kawunanku,ina fata zaku kasance a haka ko bayan tafiyata," atare suka amsa mashi da cewa"Insha Allah,"

 "Amma mun jima bamu haɗu ba,bazaka ƙara kwanaki ba"? Ammi ce tayi maganar,

  murmushi modibbo yayi kafin yace"kada ki damu,tun da dai na shigo ƙasar zaku dinga ganina ne akai akai,insha Allah,"



  Alhamdulillah,The end🥱🤣😂😅 nan bada jimawa ba,zan rubuta hakan insha Allah,nasan wasu har gabansu ya faɗi rass.........





  *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃



*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*


*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI.  MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*



*LOCATION KANO*


08062073990

Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku



Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka 

Wadrobe balls 

Madarar kulleccham 

Vaseline kulleccham 

Kajiji

Halut

Couscous 

Khumrah 

Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku


It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining.

Snack

Awarah 

Farah

Zobo

Samosa

Cup cake etc 

Contact me 09063302182or 09012179727.

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*


_Ga duk mai son karanta littafin Abban sojoji,kai tsaye ya tuntu6eni ta numbar wayata 08103884440_


Special thanks to hafsat Usman Abubakar🥰,



"Koda ace baka samu zuwa ba,xamu zo nan damaturun,dama mu ya dace ace mun je can gaba ɗayan mu bayan komai ya lafa,ko don saboda ƴan ukun abusufyan,zamu je dasu don suma suga danginsu dake acan da kuma na zariyya,dana sauran state,"acewar ammi,

Modibbo yace"hakan ma yayi,Allah yayi maku albarka gaba ɗayanku,"suka haɗa baki wurin amsa mashi da ameeeen,


Duk wannan abun dake faruwa Aunty babba da hayaam suna acikin ɗaki,kowannansu ya dafi waya sai danna yake yi,gaba ɗaya tunaninsu ya tafi akan cewa An kori su sehrish,hakan yasa hankalinsu ya kwanta luf,


miƙewa zaune aunty babba tayi daga kishingiɗen da take,fuskar nan a washe tace"Oh ni ƴasu,ko ina waɗannan ƴan ukun suka dosa yanzu?

Hayaam tace"Wama ya sanin masu,suna can suna gagari acikin gari,ƙarshenta ma a samu wata babbar mota zubin ɗan gotte tayi mana awon gaba da kawunansu,"

  Fashewa su kayi da dariya,sai da suka tsagaita dayin dariyar Aunty babba tace"duba mun ƙarfe nawa yanzu,agogon wayata ba saiti,"

   "kusan Ƙarfe tara fa yanzu,gashi ko abincin dare ma ba mu nema ba,"

  Tsoki taja"mtsww,wannan wani irin gidane!A tunani na Azmee ya kamata ace ta kawo mana dinner ɗin mu har cikin ɗaki,ni bansan menene amfanin matar nan ba a cikin gidan nan,bata wani aiki,sae dae ta dafa masu abinci,ta zauna taci ta ƙoshi ta tara tumbi,ta mayar da gidan kamar na ubanta,"

  Hayaam ta ɗaura da cewa"Ae kwanaki har magana taso ta gayamun,saboda waccen korarriyar yarinyar,Sehrish take da suna ko wa ma......."dakatawa tayi da yin maganar sakamakon turo ƙopar da taji anyi,atare suka kai idanunsu wurin,

  Azmee ce ta shigo hannunta ɗauke da tray,koda su kayi arba da ita,nan fa suka shiga yin ƴan kame kame na rashin gaskiya,

   Basu amsa mata sallamar da tayi masu ba,ƙarasawa tayi ta ajiye masu tray ɗin a ƙasa,sannan tace"abinci ne na kawo maku,bansan ko kuna buƙata ba,naga baku fito kun nema ba,shine nace bari na kawo maku a ɗaki,"

Washe baki suka shiga yi,hankalinsu harya kwanta,da alama bataji gossiping ɗinta da sukeyi ba,

  "Mun gode sosae Azmee,wlh kina ƙoƙari sosai acikin gidan nan,ke kaɗae kike duk wasu aikace aikace na gidan nan,shekara da shekaru,baki ta6a gajiyawa ba,kin mayar da dangin nan tamkar naki,bansan meyasa har yanzu kike tare dasu ba,wahalar tayi yawa,yaci ace yanzu kin nemi miji kinyi aure,amma in kika cigaba da zama a haka,rayuwarki zata ƙare ne a matsayin baiwa kuma bazawara,ba wani cigaba," 

  Tunda Aunty babba tafara magana azmee ta zuba mata ido tana kallonta,batare da ta ƙyafta idanunta ba,har sai da Aunty babba takai ƙarshen maganar,sannan tace"Bani da amsar da zan baki Laila,amma inaso ki sani dangin nan basu ɗaukeni kamar yadda kikayi tsammani ba,kuma ni bana gajiya da aiki a ƙarƙashinsu,saboda sunyi mun halarcin da bazan ta6a mantawa ba,"

  Juyawa azmee tayi da sauri ta kama hanyar fita daga ɗakin,harta ruƙe handle ɗin ƙopar zata buɗe muryar aunty babba ta katse mata hanzarinta da cewa"har yaushe ne zaki cigaba da danne abunda ke zuciyarki?

  "Mekenan"!azmee ta tambaya a yayin da ta juyo da kanta tana kallonta,

  "Azmee nafa son komai!na son cewa akwai wanda kikeso acikin gidan nan!saboda kin ta6a sanar dani a lokacin baya,ko kin manta"?

  Baza kunne hayaam tayi tana sauraronsu,

  "Hakane,na ta6a sanar dake,amma yanzu babu wannan a zuciyata,kuma ko a lokacin dana so shi,saboda irin kyautatawar da yake yi mun ne,kuma da tausayin shi da nakeji,na rashin matarshi a kusa dashi,Amma yanzu Alhamdulillah,uwar ƴa'yanshi tana a kusa dashi,babu wata sauran damuwa,


Murmushi aunty babba ta saki tare da miƙewa daga zaunen da take a gefen gadon,ta tunkari azmee tana cewa"Yanzu ke sai ki haƙura dashi?baki kwaɗayin ki aure shi,ki samu ƙaruwa dashi,ko don ki samu gado acikin gidan nan"? Da alama Aunty babba so take ta tunzura azmee,

  Girgiza kai azmee tayi"ni bani da buri akan tara dukiya,bana kwaɗayin abun duniya,saboda sanin cewa komai na tara ƙarshe a gidan duniyar nan zan barshi!albashin da nake samu acikin gidan nan ya isheni in ƙarashe rayuwata dashi,"

   Ta6e baki aunty babba tayi,fuskar nan ɗauke da shu'umin murmushin nan tace"Yanzu shikenan kin za6i ki ƙarashe rayuwarki a ƙarkashin wasu kenan?ke baki da ƴancin kanki?wlh azmee bakisan ciwon kanki ba,ban ta6a ganin ƴar wahala irin ki ba,kin ƙuntata rayuwarki,kin ƙasƙantar da kanki,duk don saboda ki faranta ma wasu!har yau babu wani cigaba a arayuwarki,yakamata ace yanxu kin mallaki katafaren gida naki na kanki,kin kuma mallaki mota,kinje hajji da umrah,kin kuma je yawon shaƙatawa dubai da sauran ƙasashe,haba azmee yakamata kiyima kanki adalci,wlh kina cutar kanki,Nidai shawara nake ba......"

  Tsawar da azmee ta daka mata ne yasa ta kasa ƙarasa maganar,ba ƙaramin razana tayi da tsawar ba,tamkar ba abakin azmee ta fito ba,

   "Ke baki isa ki tunzurani ba,laila!ki iya bakin ki,in ba so kike kija ma kanki ba,ki tsaya a iya matsayinki,nima in tsaya a nawa,idan ki kayi kuskuren shiga gonata wlh ranki zaiyi mugun 6aci," tana ƙarasa maganar,ta janyo ƙopar da sauri ta fuce,

  "Hmmmm Aunty laila,matar nan fa ba zaki ta6a iya canza mata ra'ayi ba,don na lura itama kaifi ɗaya ce,"

  Jinjina kai aunty babba tayi aranta tana mai mamakin irin yadda azmee ta daka mata tsawa,sai kace batasan matsayinta agidan Ba,!

   Komawa tayi cikin ɗakin ta zauna dirshan a gefen gadon,ranta ba ƙaramin 6aci yayi ba,taso ace taci nasara akan azmee ko don su sami haɗin kanta wurin Cimma burinsu,guntun tsoki taja tare da cewa"Ƴar wahala,sai kace tafi kowa tsoron Allah,kullum haka zaki ganta da cazbi a hannunta tana yawo,"

Ta ƙarasa maganar tare da mayar da idonta kan tray ɗin abincin da azmeen ta kawo masu,yatsina fuska tayi tare da kai hannu ta buɗe warmer ɗin,dambun shinkafa ne yaji kayan haɗi sai ƙamshi yake yi,a plate ta zuba masu nan suka zauna,suna ci ita da hayaam kamar wanda yunwa ta koro,


Azmee kuwa bayan fitarta daga ɗakin nasu,jiki a sanyaye ta wuce ɗakinta,kalaman aunty babba ba ƙaramin 6ata mata rai su kayi ba,zuciyarta ta sosu sosai,daure wa kawai takeyi,da ace bata kai zuciyarta nesa ba da ba abunda zai hana ta wanke fuskar laila da mari!


Sam ta manta da hafsat dake kwance a ɗakinta,baiwar Allah tun bayan fitarta daga ɗakin hayaam,ta wuce ɗakin azmee batare da sanin kowa ba azmee ce kaɗae tasan cewa tana a ɗakinta,anan tayi wanka,ta kuma ci abinci ta kwanta,saboda wani irin zazza6i daya saukar mata ajikinta,kwata kwata zuciyarta ba daɗi,tayi danasanin rayuwarta fiye da a ƙirga,idanunta na tsananin son ganin Su Jahad,amma tsoran tunkararsu takeyi,gashi har tsaraba tayi masu don ta basu hmmm,duk in ta tuna irin uƙubar da suka sha a hannunsu,sae ta fashe da matsanancin kuka,tun azmee na rarrashinta har ta gaji ta ƙyaleta,idanunta sun kumbura suntum haka la66anta ma,bakomai take yi ma fargaba ba,fa ce irin hukuncin da Mahaifinta zai yanke mata,don kuwa tasan muddin yaji abunda suka aikata masu jahad,Wlh ba zasu sha ba,su dukan su sae sun fuskanci mummunan hukunci a wurinsa,gaba ɗaya tayi nisa cikin zurfin tunani,taji shigowar azmee cikin ɗakin,buɗe idanunta tayi tana kallon azmee dake shigowa,yanayin yadda taga fuskar azmee ya tabbatar mata da cewar tana cikin damuwa,gefen gadon ta zauna zugudum yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,

  "AUNTY AZMEE" muryar hafsat ce ta dawo da ita cikin hayyacinta,juyawa tayi bayanta tare da kai idanunta kan fuskar hafsat dake kawance,ƙoƙarin 6oye damuwarta tayi kafin tace"har yanzu bakiyi bacci ba?

  Miƙewa hafsat tayi daga zaune,sannan tace"Bazan iyayin bacci ba aunty azmee,inajin tsoron abunda zai biyo baya,nasan cewa daddy bazai ƙyaleni ba,"ta ƙarasa maganar tana faman matse kwallon dake gangarowa akan fuskarta,

    "Kidaina sa damuwa aranki hafsat,a yadda kika bani labarin irin ruƙon da kuka yi masu jahad,da farko atare kuka azabtar da rayuwarsu ke da mahaifiyarki amma kuma daga baya kin nuna masu soyayya,ina mai tabbatar maki da cewar wannan soyayyar da kika nuna masu daga baya itace zata cece ki a hannun mahaifinki...."

  "Taya kike tunanin hakan zai zame mun mafita aunty azmee?bayan ni ce dakaina,na ɗauki su jahad acikin mota ta,na fitar dasu daga cikin gidan,na damƙa su a hannun wannan mugun mutumin wanda mommy tasa ya zubar mata dasu a daji!"tana magana hawaye na zuba a fuskarta,

  "Amma Ae kin sanar dani cewar,Mommynki yaudararki tayi akan cewar gidan marayu zaki kai su ashe zubar dasu take so ayi,"

  "Hakane aunty azmee,amma ae su hosana basu son da haka ba!nasan cewa sun tsaneni yanzu,kallon mayaudariya suke yi mun,kuma ba kowa ne ya jawo mun haka ba,fa ce Mommy,"

   Ta ƙarasa maganar tare da fashewa da wani sabon kukan,

   "Ga shawara"! Cikin shessheƙar kuka Hafsat tace"Ina...sauraronki,koma wata irin shawarace inaso,"

  "Gobe da safe tun kafin Abbanki ko Omar suyi yunƙurin tunkarar Su jahad akan maganar,ke ki fara yin hanzarin zuwa wurinsu ki nemi yafiyarsu sannan kiyi masu bayanin cewar bada saninki ba,wannan mutumin ya ɗauke su ya kaisu daji don ya zubar dasu ba,Mommynki ce ta yaudareki akan cewar gidan marayu zai kai su....."

  "Aunty azmee kina ganin in na faɗa masu hakan zasu yarda dani?hosana fa tana da ta6in hankali,daƙyar zata fahimce ni,"

.."kada ki damu,zasu fahimce ki,ki kwantar da hankalinki kawai,kamar kina acikin jirgi mai ya qare,"murmushi hafsat ta ɗan saki,har taji sanyi aranta,fatan ta Allah yasa gobe in taje wurin su Jahad,su fahimce ta,

Sun jima suna tattaunawa atsakaninsu kafin daga bisani,azmee tabar ɗakin hafsat kuwa bargo taja ta lullu6e kanta,sannu a hankali bacci ya ɗauke ta,

   

Acan falo kuwa bayan komi ya lafa,Ammi tace"Yakamata kowa yaje yayi sallah,ya kwanta ya huta,"amsa mata suka yi da toh,sannan kowannansu ya miƙe tare da nufar Bedrooms ɗinsu,atare Su jahad suka miƙe,saida suka fara yi ma su ammi sallama,ta amsa masu fuskarta asake tare da tunasar dasu akan in zasu kwanta kar su manta suyi addu'a,a ƙarshe dae falon ya rage babu kowa cikinsa,irfan shiya jagoranci Modibbo har zuwa ɗakin da zai zauna kafin gobe,Bayan ya kaishi ɗakin,Azmee ta shirya mashi kayan tea takai masa,kamar yadda ya buƙata,


*Boss Bature*


  🤍❤🤍


A 6angarensu sehrish kuwa,bayan sun koma bedroom ɗinsu,alwala kowannansu yayi sannan su kayi salla atare,bayan sun kammala suka haye saman gadonsu,cikin ƙanƙanin lokaci bacci ya ɗauki Jahad da Hosana,banda sehrish wadda bacci ya ƙaurace ma idanunta,tabbas ɗazu ta tsorata sosai da Ammi ta koresu,abun ya razanar da ita,ta kuma ji matuƙar tausayin Daddynsu,duk in tazo rufe ido,fuskarshi take gani a lokacin daya fashe da kuka yana faɗin cewa sai dai ta tsine mashi amma sai yabi ƴa'ƴan shi,bazai bari rayuwarsu ta wulaƙanta ba,tabbas ba ƙaramin so yake yi masu ba,yana tsananin ƙaunarsu fiye da tunaninsu,lokaci guda abunda ya faru a babban falo ya shiga dawo mata acikin kanta,mikewa tayi daga zaune,ta jingina bayanta a headboard din gadon,yayin da hannayenta ke rungume da pillow,a hankali tashiga tariyo abunda ammi tayi,na bijirema umarnin iyayenta,wanda hakan yasa ita ma ƴa'ƴanta suke bijire mata,Wannan abun ba ƙaramin tsoratar da sehrish yayi ba,saboda tunawa da Umarnin da mahaifinta ya bata na hana ta zuwa sashen sgr da sunan yi mashi aiki,amma taƙi bin umarninsa,hakanan ta dinga jin gabanta na faduwa,runtse idanunta tayi tare da buɗesu a hankali,wasu siraran hawaye ne suka shiga gangaro mata a fuskarta,a hankali la66anta suka soma motsi,ƙasa ƙasa take magana,matsar da kunne na nayi don inji me take cewa,

_Ya Allah ka yafemun!bani da hankali nayi kuskure,saboda kawai son wanda baisan inayi ba,saboda na faranta ma wanda nakeso,naƙi bin umarnin mahaifina,wlh bazan ƙara ba,inajin tsoron nima ƴa'ƴan da zan haifa suƙi bin umarni na,bana fatan hakan ya faru,zan daure nayi mashi biyayya_

  Tafin hannunta tasa ta goge hawayen dake zuba a idanunta,bakomai idanunta ke hango mata ba,fa ce kyakkyawar fuskar SGR,tabbas yau yayi masu abunda ba zasu ta6a mantawa ba arayuwarsu,yana da matuƙar kirki sosai,bakowa ne zai gane hakan ba farat ɗaya,shi na musamman ne,samun mutun mai irin kyakkyawar zuciyarshi a wannan zamanin da muke ciki,zaiyi matuƙar wuya,

  Zuro ƙafafunta tayi ƙasa daga saman gadon,ta miƙe tsaye,jikinta na sanye da riga da wando na bacci,milk colour,takawa tayi izuwa gaban door ɗin dakin,ta buɗe bayan ta fita ta janyo masu ƙopar ta rufe,

  A hankali take tafiya,ga wani irin sanyi dake ɗan ratsa sassan jikinta,amma sam bata jin sanyin,saboda daɗinshi take ji,zura hannayenta tayi acikin aljihun wandon jikinta,kai tsaye ta wuce main palour din,wayaam taga babu kowa kamar yadda tayi tsammani,da alama ma mutanen gidan duk sunyi bacci,hakanan taji tana marmarin tasha Cornflakes acikin wannan daren,juyawa tayi da sauri ta nufi kitchen,within minutes ta fito hannunta ɗauke da Cup,ta cika shi da cornflakes haɗi na musamman tayi mashi,ta zuba uwar madara da bornvita duka ta sanya,ta kuma Tsula sugar,'

  Dawowa tayi falon,ta zauna saman sofa tare da aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,nace sannu ƴar masu gidan,

  Motsa cornflakes ɗin ta shiga yi,da cokalin hannunta sae faman jujjuyashi takeyi aciki,kafin daga bisani ta shiga ɗebowa tana kaiwa abakinta tana sha,tana taunarsa kunnuwanta na motsi saboda daɗin da yayi,bakowa ne ya faɗo mata aranta ba fa ce junaid,abokin shiriritarta,murmushi tayi tare da cewa ɗan uwana rabin raina nasan yanzu haka yana can yana sharar baccinshi,da ace idonshi biyu da atare zamu sha wannan cornflakes din,i really missed u junaid,rashin kwanciyar hankali yasa,mun nisanta da juna,amma insha Allah tunda komai ya dai²ta,yanzu bamu da sauran wata damuwa,zamu dinga fita yawan shaƙatawa atare mu dukkan mu,


Ita kaɗae abunta sai faman sambatu takeyi,kamar wata zautacciya,tana cikin shan cornflakes ɗinnan,ta wutsiyar idonta ta hango mutun a tsaye ƙiƙam,aikuwa hankalinta yayi mugun tashi,kasa juyawa tayi saboda tsoron kar ace dodo ne,tuni jikinta ya fara kerma,dama gata da shegen tsoro,zuciyarta ta shiga bugawa da ƙarfi da ƙarfi,tunaninta wanene mutumin data hango tsaye a upstairs,tsabar tsoro ya hana ta juyawa ta kalleshi da kyau,wani irin wahalallan yawu ta haɗiye,ajiye cup ɗin dake hannunta tayi,sannan ta lalla6e tare da saukowa daga saman sofa ɗin,ta durƙushe ƙasa tayi sujjada,kamar maiyin sallah,duk don saboda kar dodon ya ganta,a hankali ta shiga rarrafawa a ƙoƙarinta na tabar falon,ta koma ɗakinsu,

  Shikuwa mutumin dake tsaye goye da hannayenshi asaman ƙirjinshi,zuba ma sarautar Allah ido yayi,abun ba ƙaramin mamaki ya bashi ba,tsoran yarinyar harya so yayi yawa,ko kallon inda ya ke bata yi ba,ta wutsiyar ido kawai taga inuwarsa amma ta sama ranta cewar wani mugun abunne,sam baiso ta tsorata ba,don bada niyar wannan yazo wurin ba,

  Wani abune ya faɗo mashi aransa,cikin sauri ya koma cikin part ɗinsa,jimmm kaɗan sai gashi ya dawo hannunshi ɗauke da wayarsa,tsayawa yayi tare da saita wurin da take yana ɗaukarta video kasancewar akwai haske sosai a main falo din,

  Ba ƙaramar wahala sehrish tasha ba,da wannan rarrafen ta ƙarasa har wurin da zata shiga corridor ɗin ɗakinsu,gaba ɗaya zufa ta wanke mata fuskarta,tana ƙokarin shiga,wani abu ya faɗo mata aranta,tsayawa tayi tana tunanin kodai ta juya taga wanene shi tunda dae ta iso wurin da zata shiga ɗakinsu,koma menene ai bai isa ya cutar da ita ba,da zarar ta juya taga dodo ne,sae ta watsa da gudu ta shige ɗakinsu,taja ƙopa ta rufe,fakat,

  Jikinta na kerma,amma ahaka ta daure ta ɗan juyo da kanta,takai idanunta saman upstairs din,ae batasan lokacin da taƙarasa juyowa gaba ɗaya ba,ta baza idanunta donta tabbatarma kanta abunda take gani,ƙura ido tayi tana son gano wanene saboda yayi mata nisa,wannan hasken fatar nashi ne ya fara sa ta tunanin kamar sgr ne,ƙara zuba ido tayi anan ta hango wannan doguwar sunar kan tashi,tabbas kuwa shine,ajiyar zuciya ta shiga saukewa a fili tace"Ashe babban yaya ne,nasha wahalar banxa,Allah yasa dai ban zubar da cornflakes ɗina ba,

  ganin tana kallonshi,yasa ya janye phone dinsa,ya kashe camera ɗin ya tura wayar a short pocket dinsa,da hannu yayi mata Alamar taxo,

  Waro ido tayi tare da nuna kanta,don ta tabbatar in ita yake kira,nuna ta ya kuma yi da hannunshi,

  Gabanta ba ƙaramin faɗuwa yayi ba rasss,tsoranta kar ya tuhumeta akan meya hanata zuwa part ɗinsa kai mashi Cofee don yau bata je ba,


  Miƙewa tayi kamar wata mara gaskiya,haka ta tunkaresa,kamar an zare mata lakar jikinta,a hankali take tattaka matattakalar stairs ɗin,harta ƙarasa ɗan nesa dashi tukunna ta tsaya,tunda ta saci kallonshi sau ɗaya,tayi arba da faffaɗan ƙirjin nan nashi,gashi babu shirt ajikinsa,Shorts ne kawai black colour ya sanya,kuma ma dai ba ƙaramin kyau yayi masa ba,

  Ganin ta tsoge wuri guda,yasa shi moving ya ƙarasa inda take dab da ita,don har saida ta ɗan ja da baya,saboda ƙure matan da yayi,

  Lokaci guda tarasa natsuwarta,sai ƴan kame kame take,a ƙarshe ma ta zura hannunta acikin sumar kanta,tana ɗan sosawa,ƙamshin turaren jikinshi ba ƙaramin illa yake yi mata ba,saboda wani yanayin da take tsintar kanta aciki,

     gaba ɗaya idanunshi na akan lips ɗinta,mutsu mutsun da takeyi da bakinta,ba ƙaramin tafiya yake yi dashi ba,

   Almost 5 mins suna a haka sannan ya buɗe baki da wannan Sexy voice ɗin tasa yace"Meyasa baki yi bacci ba"?

  Muryarta na kerma tace"bana jin bacci ne,"

  "Okey,that's y You came out to disturb those who are sleeping"?


sunnar dakai ƙasa tayi tana girgiza mashi kai,alamar a'a,ganin ta dage sai faman sosa gashin kanta takeyi,yasa shi kai hannunsa ya damƙo wrist ɗin hannunta da ta zura acikin sumar kanta yace"ƙaiƙayi kike ji ne"?

  A ruɗe tace"eh,"

Jinjina kanshi yayi tare da sakin hannun nata,

.."lemme help u.......'ɗagowa tayi a razane jin abunda yace,ko amsarta bai tsaya ji ba,ya sanya hannunshi tare da zagayo dashi ta gefen waist ɗinta ya tallabota sosai, ya janyota gaba ɗaya ta faɗa asaman wide chest ɗinsa,nan fa hankalinta yabi ya tashi,ta susuce ta zauce ta rasa uwar ubanta,a hankali ya ɗago da right hand dinsa,ya tsoma shi acikin lallausar sumar kanta,wani irin massage ya shiga yi mata,wanda ya haifar mata da wata irin matsananciyar kasala ajikinta,ita kanta batasan lokacin da ta zagaye waist ɗinshi ba da hannayenta duka,ta ƙankame shi sosai kamar zata koma cikin cikinshi,yana jin yadda numfashinta ke fita da zafi zafi,tausasan la66anta sai gogar masa fatarsa suke,sosai sehrish ke shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinshi,tana jin kanta a wata irin duniya,wadda ba kalar tamu ba,just like in the dream haka take kallon lamarin,ta rasa gane wai shin SGR sosa mata kanta yake yi ko kuwa,saboda daɗin dake ratsa jikinta yafi ƙarfin a kirashi da daɗin susa kawai,tamkar zata zauce haka take ji,ga wani irin abu dake yi mata yawo a jikinta tamkar zufa,'


Duƙar da kansa ya ɗanyi tare da kai hancinsa ya cusa sa shi acikin sumar kanta,ƙamshin man da take shafama kanta ne ya daki hancinsa sosai ya shaƙe sa,lumshe idanunsa yayi tare da ɗan ware su a hankali ya buɗe su,kafin ya mayar da la66ansa asaman fatar kunnanta,tamkar mai yin whispering haka ya shiga yi mata magana"tell me What did you do in the kitchen when you entered"? Yayi maganar tare da raba jikinshi daga nata,idanunshi tamkar na mai jin bacci,

  "Cornflakes na haɗa,saboda in sha,"ta bashi amsa a yayin da idanunta ke kallon yatsun hannunta data haɗesu wuri guda tana wasa dasu,.

  "Okey,ɗaukomin cornflakes ɗin,inaso nasha nima,"

  Batare da musu ba,ta juyawa da sauri da sauri ta sauka downstairs,a nan saman table,ta ɗauko cup ɗin da ta ajiye,sannan ta dawowa upstairs ɗin ta kawo mashi,miƙa mashi tayi,ya sanya hannu tare da kar6ar kofin,spoon ɗin ya ɗauka tare da ɗan jujjuya shi,kafin ya ciko cokalin yana ƙokarin kaiwa bakinsa yaji tace"Kamar yayi yawa,'ɗan ɗagowa yayi da idanunshi ya kalli fuskarta da sauri ta kawar da nata idanun gefe,saboda taga ya ɗebo da yawa ne kuma mouth ɗinsa is too small shiyasa tayi mashi magana,a ganinta cokalin bazai iya wuce wa ba,ta cikin bakinsa,amma sai gashi ya shanye abunsa,bayan ya tauna cornflakes din,ya ɗan dakata tare da cewa"Bana shan sugar sosai,sannan milk ɗin ma tayi yawa acikinsa,meyasa kika sanya da yawa har haka"?

. shiru tayi tana faman wurga ido,

Miƙa mata cup ɗin yayi tare da cewa"Kar6i kayan ki"hannu tasa ta kar6a,sannan tace"Zan iya tafiya,"?

  Hanya ya nuna mata tare da cewa"na ruƙe ki ne"?

  Ajiyar zuciya ta sauke,kafin ta juya da sauri da sauri ta sauka donwstairs,duk yana binta da kallo,kitchen ta shiga a tsaye ta ƙarasa shanye cornflakes din ta ajiye cup ɗin,sannan ta fito tare da kai idanunta Upstairs taga in yana nan,a tsaye ta same shi,idanunshi a lumshe,

  Juyawa tayi ta kama hanyar zuwa bedroom ɗinsu,adai² corridor din ta kuma tsayawa tare da ɗan waiwayawa don taga in yana nan koya tafi,Again ta ƙara ganinshi a tsaye kuma da alama ita yake kallo,ranta ne ya bata cewar kodai tayi masa bye bye da hannunta,may be ya mayar mata da martani,

  ɗaga hannunta tayi tare dayi mashi bye bye,abun mamaki sai gashi ya ɗaga mata hannu yana yi mata bye bye din shima,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,har batasan lokacin da ta fashe da dariya ba,da gudu ta juya tare da faɗawa bedroom dinsu,

   Ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa ya koma cikin part dinsa,bayan ya shiga bedroom ɗinsa,toilet ya fara shiga,bada jimawa ba,ya fito tare da hayewa saman shimfiɗeɗen gadonshi ya kwanta,tare da janyo pillow ya rungume shi asaman wide chest dinsa,yayin da blue eyes ɗinsa ke kallon haɗaɗɗen ceilling ɗin ɗakinsa,ya rasa gane meke damun shi,amma tabbas yana jin missing ɗin wani abu sosai atattare dashi,yana tsananin buƙatar wani abu,wanda baisan menene shi ba~~~~~~~

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*


_Ga duk mai son karanta littafin Abban sojoji,kai tsaye ya tuntu6eni ta numbar wayata 08103884440_


Special thanks to hafsat Usman Abubakar🥰,



"Koda ace baka samu zuwa ba,xamu zo nan damaturun,dama mu ya dace ace mun je can gaba ɗayan mu bayan komai ya lafa,ko don saboda ƴan ukun abusufyan,zamu je dasu don suma suga danginsu dake acan da kuma na zariyya,dana sauran state,"acewar ammi,

Modibbo yace"hakan ma yayi,Allah yayi maku albarka gaba ɗayanku,"suka haɗa baki wurin amsa mashi da ameeeen,


Duk wannan abun dake faruwa Aunty babba da hayaam suna acikin ɗaki,kowannansu ya dafi waya sai danna yake yi,gaba ɗaya tunaninsu ya tafi akan cewa An kori su sehrish,hakan yasa hankalinsu ya kwanta luf,


miƙewa zaune aunty babba tayi daga kishingiɗen da take,fuskar nan a washe tace"Oh ni ƴasu,ko ina waɗannan ƴan ukun suka dosa yanzu?

Hayaam tace"Wama ya sanin masu,suna can suna gagari acikin gari,ƙarshenta ma a samu wata babbar mota zubin ɗan gotte tayi mana awon gaba da kawunansu,"

  Fashewa su kayi da dariya,sai da suka tsagaita dayin dariyar Aunty babba tace"duba mun ƙarfe nawa yanzu,agogon wayata ba saiti,"

   "kusan Ƙarfe tara fa yanzu,gashi ko abincin dare ma ba mu nema ba,"

  Tsoki taja"mtsww,wannan wani irin gidane!A tunani na Azmee ya kamata ace ta kawo mana dinner ɗin mu har cikin ɗaki,ni bansan menene amfanin matar nan ba a cikin gidan nan,bata wani aiki,sae dae ta dafa masu abinci,ta zauna taci ta ƙoshi ta tara tumbi,ta mayar da gidan kamar na ubanta,"

  Hayaam ta ɗaura da cewa"Ae kwanaki har magana taso ta gayamun,saboda waccen korarriyar yarinyar,Sehrish take da suna ko wa ma......."dakatawa tayi da yin maganar sakamakon turo ƙopar da taji anyi,atare suka kai idanunsu wurin,

  Azmee ce ta shigo hannunta ɗauke da tray,koda su kayi arba da ita,nan fa suka shiga yin ƴan kame kame na rashin gaskiya,

   Basu amsa mata sallamar da tayi masu ba,ƙarasawa tayi ta ajiye masu tray ɗin a ƙasa,sannan tace"abinci ne na kawo maku,bansan ko kuna buƙata ba,naga baku fito kun nema ba,shine nace bari na kawo maku a ɗaki,"

Washe baki suka shiga yi,hankalinsu harya kwanta,da alama bataji gossiping ɗinta da sukeyi ba,

  "Mun gode sosae Azmee,wlh kina ƙoƙari sosai acikin gidan nan,ke kaɗae kike duk wasu aikace aikace na gidan nan,shekara da shekaru,baki ta6a gajiyawa ba,kin mayar da dangin nan tamkar naki,bansan meyasa har yanzu kike tare dasu ba,wahalar tayi yawa,yaci ace yanzu kin nemi miji kinyi aure,amma in kika cigaba da zama a haka,rayuwarki zata ƙare ne a matsayin baiwa kuma bazawara,ba wani cigaba," 

  Tunda Aunty babba tafara magana azmee ta zuba mata ido tana kallonta,batare da ta ƙyafta idanunta ba,har sai da Aunty babba takai ƙarshen maganar,sannan tace"Bani da amsar da zan baki Laila,amma inaso ki sani dangin nan basu ɗaukeni kamar yadda kikayi tsammani ba,kuma ni bana gajiya da aiki a ƙarƙashinsu,saboda sunyi mun halarcin da bazan ta6a mantawa ba,"

  Juyawa azmee tayi da sauri ta kama hanyar fita daga ɗakin,harta ruƙe handle ɗin ƙopar zata buɗe muryar aunty babba ta katse mata hanzarinta da cewa"har yaushe ne zaki cigaba da danne abunda ke zuciyarki?

  "Mekenan"!azmee ta tambaya a yayin da ta juyo da kanta tana kallonta,

  "Azmee nafa son komai!na son cewa akwai wanda kikeso acikin gidan nan!saboda kin ta6a sanar dani a lokacin baya,ko kin manta"?

  Baza kunne hayaam tayi tana sauraronsu,

  "Hakane,na ta6a sanar dake,amma yanzu babu wannan a zuciyata,kuma ko a lokacin dana so shi,saboda irin kyautatawar da yake yi mun ne,kuma da tausayin shi da nakeji,na rashin matarshi a kusa dashi,Amma yanzu Alhamdulillah,uwar ƴa'yanshi tana a kusa dashi,babu wata sauran damuwa,


Murmushi aunty babba ta saki tare da miƙewa daga zaunen da take a gefen gadon,ta tunkari azmee tana cewa"Yanzu ke sai ki haƙura dashi?baki kwaɗayin ki aure shi,ki samu ƙaruwa dashi,ko don ki samu gado acikin gidan nan"? Da alama Aunty babba so take ta tunzura azmee,

  Girgiza kai azmee tayi"ni bani da buri akan tara dukiya,bana kwaɗayin abun duniya,saboda sanin cewa komai na tara ƙarshe a gidan duniyar nan zan barshi!albashin da nake samu acikin gidan nan ya isheni in ƙarashe rayuwata dashi,"

   Ta6e baki aunty babba tayi,fuskar nan ɗauke da shu'umin murmushin nan tace"Yanzu shikenan kin za6i ki ƙarashe rayuwarki a ƙarkashin wasu kenan?ke baki da ƴancin kanki?wlh azmee bakisan ciwon kanki ba,ban ta6a ganin ƴar wahala irin ki ba,kin ƙuntata rayuwarki,kin ƙasƙantar da kanki,duk don saboda ki faranta ma wasu!har yau babu wani cigaba a arayuwarki,yakamata ace yanxu kin mallaki katafaren gida naki na kanki,kin kuma mallaki mota,kinje hajji da umrah,kin kuma je yawon shaƙatawa dubai da sauran ƙasashe,haba azmee yakamata kiyima kanki adalci,wlh kina cutar kanki,Nidai shawara nake ba......"

  Tsawar da azmee ta daka mata ne yasa ta kasa ƙarasa maganar,ba ƙaramin razana tayi da tsawar ba,tamkar ba abakin azmee ta fito ba,

   "Ke baki isa ki tunzurani ba,laila!ki iya bakin ki,in ba so kike kija ma kanki ba,ki tsaya a iya matsayinki,nima in tsaya a nawa,idan ki kayi kuskuren shiga gonata wlh ranki zaiyi mugun 6aci," tana ƙarasa maganar,ta janyo ƙopar da sauri ta fuce,

  "Hmmmm Aunty laila,matar nan fa ba zaki ta6a iya canza mata ra'ayi ba,don na lura itama kaifi ɗaya ce,"

  Jinjina kai aunty babba tayi aranta tana mai mamakin irin yadda azmee ta daka mata tsawa,sai kace batasan matsayinta agidan Ba,!

   Komawa tayi cikin ɗakin ta zauna dirshan a gefen gadon,ranta ba ƙaramin 6aci yayi ba,taso ace taci nasara akan azmee ko don su sami haɗin kanta wurin Cimma burinsu,guntun tsoki taja tare da cewa"Ƴar wahala,sai kace tafi kowa tsoron Allah,kullum haka zaki ganta da cazbi a hannunta tana yawo,"

Ta ƙarasa maganar tare da mayar da idonta kan tray ɗin abincin da azmeen ta kawo masu,yatsina fuska tayi tare da kai hannu ta buɗe warmer ɗin,dambun shinkafa ne yaji kayan haɗi sai ƙamshi yake yi,a plate ta zuba masu nan suka zauna,suna ci ita da hayaam kamar wanda yunwa ta koro,


Azmee kuwa bayan fitarta daga ɗakin nasu,jiki a sanyaye ta wuce ɗakinta,kalaman aunty babba ba ƙaramin 6ata mata rai su kayi ba,zuciyarta ta sosu sosai,daure wa kawai takeyi,da ace bata kai zuciyarta nesa ba da ba abunda zai hana ta wanke fuskar laila da mari!


Sam ta manta da hafsat dake kwance a ɗakinta,baiwar Allah tun bayan fitarta daga ɗakin hayaam,ta wuce ɗakin azmee batare da sanin kowa ba azmee ce kaɗae tasan cewa tana a ɗakinta,anan tayi wanka,ta kuma ci abinci ta kwanta,saboda wani irin zazza6i daya saukar mata ajikinta,kwata kwata zuciyarta ba daɗi,tayi danasanin rayuwarta fiye da a ƙirga,idanunta na tsananin son ganin Su Jahad,amma tsoran tunkararsu takeyi,gashi har tsaraba tayi masu don ta basu hmmm,duk in ta tuna irin uƙubar da suka sha a hannunsu,sae ta fashe da matsanancin kuka,tun azmee na rarrashinta har ta gaji ta ƙyaleta,idanunta sun kumbura suntum haka la66anta ma,bakomai take yi ma fargaba ba,fa ce irin hukuncin da Mahaifinta zai yanke mata,don kuwa tasan muddin yaji abunda suka aikata masu jahad,Wlh ba zasu sha ba,su dukan su sae sun fuskanci mummunan hukunci a wurinsa,gaba ɗaya tayi nisa cikin zurfin tunani,taji shigowar azmee cikin ɗakin,buɗe idanunta tayi tana kallon azmee dake shigowa,yanayin yadda taga fuskar azmee ya tabbatar mata da cewar tana cikin damuwa,gefen gadon ta zauna zugudum yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,

  "AUNTY AZMEE" muryar hafsat ce ta dawo da ita cikin hayyacinta,juyawa tayi bayanta tare da kai idanunta kan fuskar hafsat dake kawance,ƙoƙarin 6oye damuwarta tayi kafin tace"har yanzu bakiyi bacci ba?

  Miƙewa hafsat tayi daga zaune,sannan tace"Bazan iyayin bacci ba aunty azmee,inajin tsoron abunda zai biyo baya,nasan cewa daddy bazai ƙyaleni ba,"ta ƙarasa maganar tana faman matse kwallon dake gangarowa akan fuskarta,

    "Kidaina sa damuwa aranki hafsat,a yadda kika bani labarin irin ruƙon da kuka yi masu jahad,da farko atare kuka azabtar da rayuwarsu ke da mahaifiyarki amma kuma daga baya kin nuna masu soyayya,ina mai tabbatar maki da cewar wannan soyayyar da kika nuna masu daga baya itace zata cece ki a hannun mahaifinki...."

  "Taya kike tunanin hakan zai zame mun mafita aunty azmee?bayan ni ce dakaina,na ɗauki su jahad acikin mota ta,na fitar dasu daga cikin gidan,na damƙa su a hannun wannan mugun mutumin wanda mommy tasa ya zubar mata dasu a daji!"tana magana hawaye na zuba a fuskarta,

  "Amma Ae kin sanar dani cewar,Mommynki yaudararki tayi akan cewar gidan marayu zaki kai su ashe zubar dasu take so ayi,"

  "Hakane aunty azmee,amma ae su hosana basu son da haka ba!nasan cewa sun tsaneni yanzu,kallon mayaudariya suke yi mun,kuma ba kowa ne ya jawo mun haka ba,fa ce Mommy,"

   Ta ƙarasa maganar tare da fashewa da wani sabon kukan,

   "Ga shawara"! Cikin shessheƙar kuka Hafsat tace"Ina...sauraronki,koma wata irin shawarace inaso,"

  "Gobe da safe tun kafin Abbanki ko Omar suyi yunƙurin tunkarar Su jahad akan maganar,ke ki fara yin hanzarin zuwa wurinsu ki nemi yafiyarsu sannan kiyi masu bayanin cewar bada saninki ba,wannan mutumin ya ɗauke su ya kaisu daji don ya zubar dasu ba,Mommynki ce ta yaudareki akan cewar gidan marayu zai kai su....."

  "Aunty azmee kina ganin in na faɗa masu hakan zasu yarda dani?hosana fa tana da ta6in hankali,daƙyar zata fahimce ni,"

.."kada ki damu,zasu fahimce ki,ki kwantar da hankalinki kawai,kamar kina acikin jirgi mai ya qare,"murmushi hafsat ta ɗan saki,har taji sanyi aranta,fatan ta Allah yasa gobe in taje wurin su Jahad,su fahimce ta,

Sun jima suna tattaunawa atsakaninsu kafin daga bisani,azmee tabar ɗakin hafsat kuwa bargo taja ta lullu6e kanta,sannu a hankali bacci ya ɗauke ta,

   

Acan falo kuwa bayan komi ya lafa,Ammi tace"Yakamata kowa yaje yayi sallah,ya kwanta ya huta,"amsa mata suka yi da toh,sannan kowannansu ya miƙe tare da nufar Bedrooms ɗinsu,atare Su jahad suka miƙe,saida suka fara yi ma su ammi sallama,ta amsa masu fuskarta asake tare da tunasar dasu akan in zasu kwanta kar su manta suyi addu'a,a ƙarshe dae falon ya rage babu kowa cikinsa,irfan shiya jagoranci Modibbo har zuwa ɗakin da zai zauna kafin gobe,Bayan ya kaishi ɗakin,Azmee ta shirya mashi kayan tea takai masa,kamar yadda ya buƙata,


*Boss Bature*


  🤍❤🤍


A 6angarensu sehrish kuwa,bayan sun koma bedroom ɗinsu,alwala kowannansu yayi sannan su kayi salla atare,bayan sun kammala suka haye saman gadonsu,cikin ƙanƙanin lokaci bacci ya ɗauki Jahad da Hosana,banda sehrish wadda bacci ya ƙaurace ma idanunta,tabbas ɗazu ta tsorata sosai da Ammi ta koresu,abun ya razanar da ita,ta kuma ji matuƙar tausayin Daddynsu,duk in tazo rufe ido,fuskarshi take gani a lokacin daya fashe da kuka yana faɗin cewa sai dai ta tsine mashi amma sai yabi ƴa'ƴan shi,bazai bari rayuwarsu ta wulaƙanta ba,tabbas ba ƙaramin so yake yi masu ba,yana tsananin ƙaunarsu fiye da tunaninsu,lokaci guda abunda ya faru a babban falo ya shiga dawo mata acikin kanta,mikewa tayi daga zaune,ta jingina bayanta a headboard din gadon,yayin da hannayenta ke rungume da pillow,a hankali tashiga tariyo abunda ammi tayi,na bijirema umarnin iyayenta,wanda hakan yasa ita ma ƴa'ƴanta suke bijire mata,Wannan abun ba ƙaramin tsoratar da sehrish yayi ba,saboda tunawa da Umarnin da mahaifinta ya bata na hana ta zuwa sashen sgr da sunan yi mashi aiki,amma taƙi bin umarninsa,hakanan ta dinga jin gabanta na faduwa,runtse idanunta tayi tare da buɗesu a hankali,wasu siraran hawaye ne suka shiga gangaro mata a fuskarta,a hankali la66anta suka soma motsi,ƙasa ƙasa take magana,matsar da kunne na nayi don inji me take cewa,

_Ya Allah ka yafemun!bani da hankali nayi kuskure,saboda kawai son wanda baisan inayi ba,saboda na faranta ma wanda nakeso,naƙi bin umarnin mahaifina,wlh bazan ƙara ba,inajin tsoron nima ƴa'ƴan da zan haifa suƙi bin umarni na,bana fatan hakan ya faru,zan daure nayi mashi biyayya_

  Tafin hannunta tasa ta goge hawayen dake zuba a idanunta,bakomai idanunta ke hango mata ba,fa ce kyakkyawar fuskar SGR,tabbas yau yayi masu abunda ba zasu ta6a mantawa ba arayuwarsu,yana da matuƙar kirki sosai,bakowa ne zai gane hakan ba farat ɗaya,shi na musamman ne,samun mutun mai irin kyakkyawar zuciyarshi a wannan zamanin da muke ciki,zaiyi matuƙar wuya,

  Zuro ƙafafunta tayi ƙasa daga saman gadon,ta miƙe tsaye,jikinta na sanye da riga da wando na bacci,milk colour,takawa tayi izuwa gaban door ɗin dakin,ta buɗe bayan ta fita ta janyo masu ƙopar ta rufe,

  A hankali take tafiya,ga wani irin sanyi dake ɗan ratsa sassan jikinta,amma sam bata jin sanyin,saboda daɗinshi take ji,zura hannayenta tayi acikin aljihun wandon jikinta,kai tsaye ta wuce main palour din,wayaam taga babu kowa kamar yadda tayi tsammani,da alama ma mutanen gidan duk sunyi bacci,hakanan taji tana marmarin tasha Cornflakes acikin wannan daren,juyawa tayi da sauri ta nufi kitchen,within minutes ta fito hannunta ɗauke da Cup,ta cika shi da cornflakes haɗi na musamman tayi mashi,ta zuba uwar madara da bornvita duka ta sanya,ta kuma Tsula sugar,'

  Dawowa tayi falon,ta zauna saman sofa tare da aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,nace sannu ƴar masu gidan,

  Motsa cornflakes ɗin ta shiga yi,da cokalin hannunta sae faman jujjuyashi takeyi aciki,kafin daga bisani ta shiga ɗebowa tana kaiwa abakinta tana sha,tana taunarsa kunnuwanta na motsi saboda daɗin da yayi,bakowa ne ya faɗo mata aranta ba fa ce junaid,abokin shiriritarta,murmushi tayi tare da cewa ɗan uwana rabin raina nasan yanzu haka yana can yana sharar baccinshi,da ace idonshi biyu da atare zamu sha wannan cornflakes din,i really missed u junaid,rashin kwanciyar hankali yasa,mun nisanta da juna,amma insha Allah tunda komai ya dai²ta,yanzu bamu da sauran wata damuwa,zamu dinga fita yawan shaƙatawa atare mu dukkan mu,


Ita kaɗae abunta sai faman sambatu takeyi,kamar wata zautacciya,tana cikin shan cornflakes ɗinnan,ta wutsiyar idonta ta hango mutun a tsaye ƙiƙam,aikuwa hankalinta yayi mugun tashi,kasa juyawa tayi saboda tsoron kar ace dodo ne,tuni jikinta ya fara kerma,dama gata da shegen tsoro,zuciyarta ta shiga bugawa da ƙarfi da ƙarfi,tunaninta wanene mutumin data hango tsaye a upstairs,tsabar tsoro ya hana ta juyawa ta kalleshi da kyau,wani irin wahalallan yawu ta haɗiye,ajiye cup ɗin dake hannunta tayi,sannan ta lalla6e tare da saukowa daga saman sofa ɗin,ta durƙushe ƙasa tayi sujjada,kamar maiyin sallah,duk don saboda kar dodon ya ganta,a hankali ta shiga rarrafawa a ƙoƙarinta na tabar falon,ta koma ɗakinsu,

  Shikuwa mutumin dake tsaye goye da hannayenshi asaman ƙirjinshi,zuba ma sarautar Allah ido yayi,abun ba ƙaramin mamaki ya bashi ba,tsoran yarinyar harya so yayi yawa,ko kallon inda ya ke bata yi ba,ta wutsiyar ido kawai taga inuwarsa amma ta sama ranta cewar wani mugun abunne,sam baiso ta tsorata ba,don bada niyar wannan yazo wurin ba,

  Wani abune ya faɗo mashi aransa,cikin sauri ya koma cikin part ɗinsa,jimmm kaɗan sai gashi ya dawo hannunshi ɗauke da wayarsa,tsayawa yayi tare da saita wurin da take yana ɗaukarta video kasancewar akwai haske sosai a main falo din,

  Ba ƙaramar wahala sehrish tasha ba,da wannan rarrafen ta ƙarasa har wurin da zata shiga corridor ɗin ɗakinsu,gaba ɗaya zufa ta wanke mata fuskarta,tana ƙokarin shiga,wani abu ya faɗo mata aranta,tsayawa tayi tana tunanin kodai ta juya taga wanene shi tunda dae ta iso wurin da zata shiga ɗakinsu,koma menene ai bai isa ya cutar da ita ba,da zarar ta juya taga dodo ne,sae ta watsa da gudu ta shige ɗakinsu,taja ƙopa ta rufe,fakat,

  Jikinta na kerma,amma ahaka ta daure ta ɗan juyo da kanta,takai idanunta saman upstairs din,ae batasan lokacin da taƙarasa juyowa gaba ɗaya ba,ta baza idanunta donta tabbatarma kanta abunda take gani,ƙura ido tayi tana son gano wanene saboda yayi mata nisa,wannan hasken fatar nashi ne ya fara sa ta tunanin kamar sgr ne,ƙara zuba ido tayi anan ta hango wannan doguwar sunar kan tashi,tabbas kuwa shine,ajiyar zuciya ta shiga saukewa a fili tace"Ashe babban yaya ne,nasha wahalar banxa,Allah yasa dai ban zubar da cornflakes ɗina ba,

  ganin tana kallonshi,yasa ya janye phone dinsa,ya kashe camera ɗin ya tura wayar a short pocket dinsa,da hannu yayi mata Alamar taxo,

  Waro ido tayi tare da nuna kanta,don ta tabbatar in ita yake kira,nuna ta ya kuma yi da hannunshi,

  Gabanta ba ƙaramin faɗuwa yayi ba rasss,tsoranta kar ya tuhumeta akan meya hanata zuwa part ɗinsa kai mashi Cofee don yau bata je ba,


  Miƙewa tayi kamar wata mara gaskiya,haka ta tunkaresa,kamar an zare mata lakar jikinta,a hankali take tattaka matattakalar stairs ɗin,harta ƙarasa ɗan nesa dashi tukunna ta tsaya,tunda ta saci kallonshi sau ɗaya,tayi arba da faffaɗan ƙirjin nan nashi,gashi babu shirt ajikinsa,Shorts ne kawai black colour ya sanya,kuma ma dai ba ƙaramin kyau yayi masa ba,

  Ganin ta tsoge wuri guda,yasa shi moving ya ƙarasa inda take dab da ita,don har saida ta ɗan ja da baya,saboda ƙure matan da yayi,

  Lokaci guda tarasa natsuwarta,sai ƴan kame kame take,a ƙarshe ma ta zura hannunta acikin sumar kanta,tana ɗan sosawa,ƙamshin turaren jikinshi ba ƙaramin illa yake yi mata ba,saboda wani yanayin da take tsintar kanta aciki,

     gaba ɗaya idanunshi na akan lips ɗinta,mutsu mutsun da takeyi da bakinta,ba ƙaramin tafiya yake yi dashi ba,

   Almost 5 mins suna a haka sannan ya buɗe baki da wannan Sexy voice ɗin tasa yace"Meyasa baki yi bacci ba"?

  Muryarta na kerma tace"bana jin bacci ne,"

  "Okey,that's y You came out to disturb those who are sleeping"?


sunnar dakai ƙasa tayi tana girgiza mashi kai,alamar a'a,ganin ta dage sai faman sosa gashin kanta takeyi,yasa shi kai hannunsa ya damƙo wrist ɗin hannunta da ta zura acikin sumar kanta yace"ƙaiƙayi kike ji ne"?

  A ruɗe tace"eh,"

Jinjina kanshi yayi tare da sakin hannun nata,

.."lemme help u.......'ɗagowa tayi a razane jin abunda yace,ko amsarta bai tsaya ji ba,ya sanya hannunshi tare da zagayo dashi ta gefen waist ɗinta ya tallabota sosai, ya janyota gaba ɗaya ta faɗa asaman wide chest ɗinsa,nan fa hankalinta yabi ya tashi,ta susuce ta zauce ta rasa uwar ubanta,a hankali ya ɗago da right hand dinsa,ya tsoma shi acikin lallausar sumar kanta,wani irin massage ya shiga yi mata,wanda ya haifar mata da wata irin matsananciyar kasala ajikinta,ita kanta batasan lokacin da ta zagaye waist ɗinshi ba da hannayenta duka,ta ƙankame shi sosai kamar zata koma cikin cikinshi,yana jin yadda numfashinta ke fita da zafi zafi,tausasan la66anta sai gogar masa fatarsa suke,sosai sehrish ke shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinshi,tana jin kanta a wata irin duniya,wadda ba kalar tamu ba,just like in the dream haka take kallon lamarin,ta rasa gane wai shin SGR sosa mata kanta yake yi ko kuwa,saboda daɗin dake ratsa jikinta yafi ƙarfin a kirashi da daɗin susa kawai,tamkar zata zauce haka take ji,ga wani irin abu dake yi mata yawo a jikinta tamkar zufa,'


Duƙar da kansa ya ɗanyi tare da kai hancinsa ya cusa sa shi acikin sumar kanta,ƙamshin man da take shafama kanta ne ya daki hancinsa sosai ya shaƙe sa,lumshe idanunsa yayi tare da ɗan ware su a hankali ya buɗe su,kafin ya mayar da la66ansa asaman fatar kunnanta,tamkar mai yin whispering haka ya shiga yi mata magana"tell me What did you do in the kitchen when you entered"? Yayi maganar tare da raba jikinshi daga nata,idanunshi tamkar na mai jin bacci,

  "Cornflakes na haɗa,saboda in sha,"ta bashi amsa a yayin da idanunta ke kallon yatsun hannunta data haɗesu wuri guda tana wasa dasu,.

  "Okey,ɗaukomin cornflakes ɗin,inaso nasha nima,"

  Batare da musu ba,ta juyawa da sauri da sauri ta sauka downstairs,a nan saman table,ta ɗauko cup ɗin da ta ajiye,sannan ta dawowa upstairs ɗin ta kawo mashi,miƙa mashi tayi,ya sanya hannu tare da kar6ar kofin,spoon ɗin ya ɗauka tare da ɗan jujjuya shi,kafin ya ciko cokalin yana ƙokarin kaiwa bakinsa yaji tace"Kamar yayi yawa,'ɗan ɗagowa yayi da idanunshi ya kalli fuskarta da sauri ta kawar da nata idanun gefe,saboda taga ya ɗebo da yawa ne kuma mouth ɗinsa is too small shiyasa tayi mashi magana,a ganinta cokalin bazai iya wuce wa ba,ta cikin bakinsa,amma sai gashi ya shanye abunsa,bayan ya tauna cornflakes din,ya ɗan dakata tare da cewa"Bana shan sugar sosai,sannan milk ɗin ma tayi yawa acikinsa,meyasa kika sanya da yawa har haka"?

. shiru tayi tana faman wurga ido,

Miƙa mata cup ɗin yayi tare da cewa"Kar6i kayan ki"hannu tasa ta kar6a,sannan tace"Zan iya tafiya,"?

  Hanya ya nuna mata tare da cewa"na ruƙe ki ne"?

  Ajiyar zuciya ta sauke,kafin ta juya da sauri da sauri ta sauka donwstairs,duk yana binta da kallo,kitchen ta shiga a tsaye ta ƙarasa shanye cornflakes din ta ajiye cup ɗin,sannan ta fito tare da kai idanunta Upstairs taga in yana nan,a tsaye ta same shi,idanunshi a lumshe,

  Juyawa tayi ta kama hanyar zuwa bedroom ɗinsu,adai² corridor din ta kuma tsayawa tare da ɗan waiwayawa don taga in yana nan koya tafi,Again ta ƙara ganinshi a tsaye kuma da alama ita yake kallo,ranta ne ya bata cewar kodai tayi masa bye bye da hannunta,may be ya mayar mata da martani,

  ɗaga hannunta tayi tare dayi mashi bye bye,abun mamaki sai gashi ya ɗaga mata hannu yana yi mata bye bye din shima,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,har batasan lokacin da ta fashe da dariya ba,da gudu ta juya tare da faɗawa bedroom dinsu,

   Ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa ya koma cikin part dinsa,bayan ya shiga bedroom ɗinsa,toilet ya fara shiga,bada jimawa ba,ya fito tare da hayewa saman shimfiɗeɗen gadonshi ya kwanta,tare da janyo pillow ya rungume shi asaman wide chest dinsa,yayin da blue eyes ɗinsa ke kallon haɗaɗɗen ceilling ɗin ɗakinsa,ya rasa gane meke damun shi,amma tabbas yana jin missing ɗin wani abu sosai atattare dashi,yana tsananin buƙatar wani abu,wanda baisan menene shi ba~~~~~~~

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*






Gaba ɗaya Aunty babba idonta bai hango mata su hosana ba,kutsa kai kawai takeyi cikin falon,hafsat dai tana la6e a bayanta,cike da fargaba,

Ƙarasawa sukayi wurinsu,daga bayansu Sehrish suka tsaya,hakan yasa bata samu damar ganin fuskokinsu ba,sai faman washe baki take yi,gaishe dasu Abba suka farayi,fuskar kowannansu awashe,"Ishaq shine baka sanar dani zuwansu ba,"acewar Abba,General ishaq yace"Ni kaina bansan sun karaso ba,nadaisan munyi dasu kan cewa zasu taho,"

Abusufyan yace"masha Allah hafsat ta girma sosai,ba don ina ganin hoton ta ba,da bazan  iya gane ta ba,

  Sunnar da kai ƙasa hafsat tayi tana murmushi ƙasa ƙasa,yayin da zuciyarta ke a cunkushe,

  duk su hosana basu ɗauki muryarta ba,amma da zarar tayi magana sai sunji tamkar sun ta6a jin muryar matar dake magana,

    "Muna taya ka murna Abusufyan,ƴa'ƴa har ƴan uku Allah ya albarkaci rayuwarsu,Alla ya.........'bata ƙarasa maganar ba sakamakon juyowar da sehrish tayi,Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu ji kake daram!!!dararam!!!yadda kasan ana buga ganga,Saboda tsabar kiɗima bata san lokacin da ta furta"Kutumar Uba...."gaba ɗaya hankalin kowa ya dawo kanta,jin ashar ɗin data buga,Hakan yasa Jahad da Hosana juyowa atare,Waro ido waje tayi hankalinta a matuƙar tashe,lokaci guda duk tabi ta gigice ta ruɗe ta rikice ta fita hayyacinta abunda batayi tsammani ba,la66anta har kerma sukeyi wurin nuna su da hannu tana ƙoƙarin tayi magana amma kermar da bakinta keyi ya hanata cewa komai,

  Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin matar da ta azabtar da rayuwarsu,ta ƙuntata masu ta kusa halakasu,hosana kuwa a matuƙar tsorace ta faɗa bayan Marshal Omar ta ƙanƙame shi tana faɗin"Ya Omar,bansan ganinta,tsoranta nake ji,itace matar da ta azabtar da rayuwarmu,itace tasa aje a jefar damu cikin daji,har wannan tsohon mutumin ya kusa cutar dani,don Allah ya Omar ku kureta,azzaluma ce macuciya ce,bata tsoran Allah,bata da tausayi kuma bata da Imani,

Hankalin kowa dake a wurin ya dawo kansu,gaba daya Abba dasu Abusufyan da sauran mutanen dake a wurin duk sun ruɗe sun gaza gane inda zancen nata ya dosa,Ishaq kuwa tun da yaga jikin Aunty babba na kerma,zufa na keto mata,ranshi ya bashi cewar tabbas ta aikata wani abu ne,saboda yasan halinta,muguwace kuma bata da gaskiya,Bashi ba hatta Marshal jikinshi yayi mugun sanyi,musamman da yaji hosana na fadin ta cutar da rayuwarsu nan ya fara tunanin Wasu abubuwa da yake zargi a lokacin baya,da kuma maganar da major ya ta6a sanar dashi na cewar baya son ya shiga tsakaninshi da matar Yayan shi,

 hannu Aunty babba ta aza akanta tana faɗin"Shikenan An yanka ta tashi,amaimakon ta mutu,nashiga ukku ni laila,Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wani tsautsayi ne da ƙaddara suka kawo ni gidan nan,'

Tunda Abbansu junaid yaji hakan yasan cewa tabbas akwai wani abu daya ta6a faruwa a tsakaninsu,koma dae menene bai kamata,su tuhumeta ba agaban ƙannen mijinta,a bainar jama'a kuma,ko ba komai Matar babban yayansu ce,

  "Ya Omar dan Allah,tabar wurin nan wlh bansan ganinta,kashe mu take son yi,shiyasa ta biyo mu har nan,"gaba ɗaya kukan hosana ya cika kunnuwansu,'

  Wani irin wahalallan yawu Aunty babba tazo haɗiyewa,nan take ta yanke jiki a wurin ta faɗi asume,da sauri hafsat ta tsugunna tare da tallabo ta,tana jijjjigata,


Gaba ɗaya duk sun kashe ma ishaq baki yama rasa abun cewa,tsananin baƙin ciki da takaici ya hanashi cewa uffan,jikinshi sae faman tsuma yake yi,burinshi kawai yaji abunda suka aikata ma yaran,da har suka tsorata da ganinsu,tabbas sai sunci Ubansu,muddin yaji wani da ba dai dai ba,don bazai yarda suja mashi tozarta ba a idon ƴan uwanshi,


Aunty Azmee ce ta taimaka wurin ɗebo ruwa suka yayyafa ma Aunty babba a fuskarta,ae tana farfaɗowa kamar wata zautacciya tayi zumbur ta miƙe,ko waiwayonsu ba tayi ba,ta watsa aguje,tayi cikin gidan,Allah kaɗae yasan inda ta kutsa kanta,


A fusace General ishaq zai bi bayanta,Abbansu junaid yayi saurin ruƙo hannunshi tare da cewa"kada ka bita,yakamata mubi komai a sannu,yanzu bamu kaɗai bane a wurin nan ba,akwai ƙannenka kuma akwai bare a wurin nan,"

  Jinjina kanshi kawai yayi ba don ya haƙuri ba,

  Batare da sanin kowa ba,hafsat ta zame jiki daga wurin,saboda wani irin mugun kallo da taga Daddynta nayi mata,bashi kaɗae ba hatta Marshal kallon tuhuma yake yi mata,hakan ne yasata ta sulale tabar wurin,sauƙinta ma basu ambaci sunanta ba,amma tasan dole sunanta ya fito aciki,kuma daddynta in ya tashi yanke hukunci hada ita zai haɗa ya yanke mawa,tabbas tayi dana sanin biye ma mahaifiyarta wurin cutar dasu hosana,gayanan sunja ma kansu,

  Ruƙo hannun hosana yayi tare da janyota,ta dawo ta gabanshi,fuskarnan tayi jawur,sae faman kuka takeyi tana faɗin"ya Omar a koreta tabar gidan nan,bana son ganinta,bata da Imani,itace ta rufe mu acikin store tayi mana horon yunwa,ta dinga bugunmu da bulala,kuma ta dinga samu aiki,har gadon asibiti sai da aka kwantar dani.......'

Cikin sauri Omar ya sanya tafin hannunshi ya toshe mata baki,cikin lallashi yace"its ok hosana,na fahimce ki,zansa sojoji su koreta daga gidan nan hakan yayi maki,"

  ɗaga mashi kai tayi alamar eh,sannan yace"kada na sake jin kukan ki to,ya isa haka,kalli fa ki gani duk kin 6ata kwalliyarki da hawaye,"

  Curo handkerchief Abusufyan yayi daga gaban aljihunsa,ya ruƙo hosana,tare da sanyashi a fuskarta yana goge mata hawayenta,"Daddy matar can bata da Imani ko kaɗan,taso ta kashe ni,dan Allah ku sakar mata karnuka su rakata bakin gate,tabar gidan nan,"

  Muryar abusufyan tamkar zaiyi kuka yace"Kiyi haƙuri kinji hosanata,zansa a koreta kamar yadda kikeso,amma yanzu kiyi shiru da bakinki,ki daina magana,banason ganin hawayenki,"

  "Daddy bakasan yadda nakeji bane,zuciyata tafarfasa takeyi,raɗaɗi takeyi mun kamar ana rura garwashin wuta acikinta,wlh daddy waccen matar bazata ga Manzon Allah ba,sai ta shiga wuta,'

Hankali atashe Marshal ya daka mata tsawa har saida ta dawo cikin hayyacinta,fuskarshi a daure yace"kar na sake jin kince uffan a wurin nan,surutun ya isa haka!banace za'a kore ta ba,"

  Saboda tsoratar da tayi da tsawar da yayi mata ne yasa ta faɗa jikin daddyn nasu ta ƙankameshi,tana faman sauke ajiyar zuciya,'

  jikin kowa yayi sanyi,musamman Ishaq,bawan Allah duk yabi ya takure kansa,idanunshi sunyi jawur saboda tsabar 6acin rai,

   Abba ne yayi ƙoƙari wurin dawo dasu daidai daga yanayin da suka shiga,daƙyar aka samu hosana ta zauna itama amma duk da haka tana yawan firgita wannan ya ƙara tabbatar masu da cewa ba ƙaramin Abu Aunty laila ta aikata masu ba,wuri kowa ya samu ya zauna agaban table ɗin dake a wurin wanda ke shaqe da abinci kala kala,nan fa kowa ya shiga bama cikinsa abinci,jikin Sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,saboda ta gane dalilin dayasa su jahad suka tsorata da ganin matar,wato itace matar da Omar ya kaisu gidanta,wadda ta azabtar da rayuwarsu,kamar yadda jahad ta bata labarinta,kowa ya lura da yanayin yaran,sun kasa sakewa suci abinci sosai,ƙarshe sai dae Abusufyan ya dinga binsu one by one yana sanya masu abinci abakinsu suna ci,a haka har ya samu suka ci sosai,bayan sun kammala cin abincin,Junaid ya ɗaukko Camera ɗinsa,nan fa aka shiga ɗaukar hotuna,abun gwanin burgewa,Happy family,kowa sai da ya fito Hajiya azeema,su gwaggon katsina Saude,Dr harris,hatta ƴan matan da hajiya sarah tazo dasu,sae da suka fito akayi masu hotuna,mutun uku ne kawai babu a wurin Ammi wadda kowa ke fargabar fitowarta,bayan ita sae Haroon wanda ke ƙumshe acikin ɗakinsa,Sgr kuwa baya cikin gidan,tun wuraren ƙarfe uku yabar gidan,

  Anyi masu hoto tare da mahaifinsu sun sanyashi atsakiya,sae wanda akayi masu tare da Abbansu junaid tare dashi kanshi junaid ɗin,kowa saida yayi hoto tare dasu,hatta Su twins da fawan dasu irfan,kowannansu sae da yayi hoto dasu,sun sha hotuna ba ƙadan ba,


Basu suka kammala ba sae wuraren sallar magrib,sannan kowa ya shige ciki domin yin alwala,


Kamar jira jahad takeyi su shiga ɗaki ta rufe hosana da faɗa,tamkar zata bugeta,"Sai yanzu na tabbatar da cewar ke cikakkar zararriyace baki da hankali,meyasa ba zakiyi shiru da bakin ki ba?don me zaki tona mata asiri agaban mutane"?

Fashewa da kuka hosana tayi tana faɗin"kada ki ƙara cemun zararriya,kuma naje na tona mata asirin,Ni bazan ta6a yafe mata ba wlh,kamar yadda ta cutar da rayuwarmu itama sai ta fuskanci sakamakon abunda ta aikata mana,'

"Hosana,karna sake jin kin tada wannan maganar,idan ba so kike ranki ya 6aci ba,"

  "Wlh saina faɗima Daddy da Abba,kuma saina faɗa ma yaya Omar,sai dai duk abunda zai faru ya faru,'

  rai a6ace tayi maganar,cakumar rigarta jahad tayi,tare da yin wurgi da ita,ta faɗa saman gadon tana kuka,fitowa Sehrish tayi daga cikin toilet,ganin jahad na ƙoƙarin bugun hosana yasa tayi saurin zuwa tare da ruƙo hannunta"karki kuskura kice zaki hukunta hosana!abunda tayi dai dai ne,koda ace ita bata faɗa masu ba,to ni saina faɗa masu abunda waccan matar ta aikata maku,saboda bata da Imani,muguwace ita,muddin akace za'a cigaba da yafe ma mutane irinta to tabbas bazasu ta6a canza halinsu ba!Suna buƙatar a ladabtar dasu,a hukuntasu,idan suka aikata ba dai dai ba,Ni hakan da hosana tayi ta burgeni,!"

  Shiru jahad tayi,ta wani 6angaren zancen sehrish gaskiya ne,muddin ba'a ɗauki mataki ba akanta taga an ƙyaleta to tabbas bazata ta6a canzawa ba,amma yanzu idan suka hukunta ta dole nan gaba taji shakkar ƙara yin irin kuskuren da tayi abaya,

  

"Kin faɗi gaskiya sehrish,ni banyi tunanin hakan ba,kuma koda nake yi ma hosana faɗa,saboda 6arin zancen da tayi ne agaban mutane,bai kamata ta yi magana akan idon kowa ba,in ma faɗin ne Ya Omar yakamata ta sanar mawa,sae su yanke mata hukuncin da suka ga ya dace da ita,"

  Ta ƙarasa maganar tare da ɗauke idonta daga kan sehrish ta mayar dasu kan hosana dake baje saman gadon tana kuka,nan take taji bata kyauta mata ba,hawa saman gadon tayi tare da janyota jikinta,tana lallashinta,daƙyar ta samu tayi shiru,daga bisani suka tashi domin yin sallar magrib,


*Aunty Babba*


Tunda ta watsa a gujen nan,ɗakin hayaam ta faɗa,jikinta sae faman rawa yakeyi,zagaye tashiga yi a ɗakin tana tunanin hanyar da zata bi ta gudu daga cikin gidan tun kafin ishaq ya waiwayeta,tsoranta karya bata takardar saki,don bata shirya yin zawarci ba,hannu ta aza aka tana fadin"Nashiga uku ni laila,na jama kaina masifa da bala'e,Ina zan tsoma raina inji daɗi,"tana cikin zancen zucin nan,hafsat ta shigo ɗakin,kamar jira takeyi nan ta shiga balbaleta da faɗa ta inda take shiga bata nan take fita ba,

  "Don ubanki ki faɗa mun taya akai yaran nan suka rayu!nasan kinsan komai munafuka algunguma!"hafsat na ƙokarin buɗe baki,Aunty babba takai mata naushi a kumatunta,har sai da le6enta ya ɗan fashe,idonta jawur ta ɗago tare da kallon Mommyn nata idanunta cike taf da hawaye tace"Mommy!ni kika buga saboda zunubin da bani na aikata ba?

  A faɗace Aunty babba tace"Zanci ubanki ko ki rufe mun baki,wlh hafsat kin cuce ni!Allah ya isa tsakanina dake!ae kinsan da zaman yaran nan acikin gidan nan, shiyasa don munafunci kika sanyo nikabi uban meyasa baki sanar dani ba tuntuni don inyi takaina!Kece kika tseratar dasu daga hannun baba alamu,in ba haka ba taya akai har suka kawo kansu cikin gidan nan"!?

  Girgiza kai hafsat ta shiga yi yayin da idanunta ke fitar da wasu irin hawaye masu ɗumi,cikin shessheƙar kuka tace"banta6a dana sanin kasancewarki mahaifiyata ba sai yau!Kin jefani acikin masifa kin kuma zo kina neman ƙala mun sharrin cewa ni na tseratar dasu daga hannunshi,wlh Mommy bakiyi ba!duk wasu magayen ɗabi'u da halayen dana ɗauko naki ne,baki ta6a cemun nayi badai dai ba,baki bani tarbiya mai kyau ba,kullum gur6atamun tunani na kikeyi,saboda kar in dauko halayyar mahaifina,Ni banta6a ganin uwa irinki ba,Yanzu gashi nan daga ni harke wa gari ya waya?kuma inaso ki sani mommy,Ni bansan komai agame dasu hosana ba,bansan ya akai suka dawo hannun Ya Omar ba,Na faɗa maki hakan ne ba don ina jin tsoranki ba,sai don kisan cewar Bani na aikata hakan ba,Allah ne Ya Kamaki,ba yadda banyi ba don ki kyale yaran nan karki salwantar da rayuwarsu kika ki,kuma ni ce da hannuna na goge hotunan da hayaam ta tura maki a wayarki,saboda nafi son ki tako da ƙafafunki don ki gir6i abunda kika shuka......"

..saboda tsabar tsuma jikinta har kerma yakeyi,shaƙo wuyan rigar hafsat tayi da ƙarfin gaske,gadan gadan kasheta zatayi,kiciniyar kwace wa hafsat tashiga yi,suna cikin wannan halin,Amani da hayaam suka faɗo cikin ɗakin da gudun gaske sukayi kansu,daƙyar suka kwaci hafsat daga hannun Aunty babba,dafe maƙoshinta tayi tana faman yarfa hannu tana ambaton"ruwa!ruwa'

 Da sauri hayaam ta fita waje,sai gata ta dawo da bottle water a hannunta mai sanyi,miƙa ma Hafsat ruwan tayi,jiki na rawa ta cire marfin robar tare da yin wurgi dashi,ta kafa robar abakinta tana kwankwaɗar ruwan,hayaam ce ta zauna a wurinta,tana lallashinta,

  Rai amatuƙar 6ace tashiga fadin"ae da kun barni na kasheta don ubanta,wlh hafsat baƙin cikinki bazai ta6a kashe ni ba,Muguwa kawai,nafi kowa dana sanin haihuwarki,Ni ina kokwanton cewar Anya ba'a asibiti akayimun musanyarki ba,"

  Fashewa da dariya Amani tayi tana tafa hannayenta,

  Nan take Aunty babba ta ɗaure fuska,tana jifarta da harara,

  Tsagaitawa tayi daga yin dariyar da takeyi masu sannan tace"Wannan abun daya faru nafi kowa farin cikinsa,tamkar na zuba ruwa a ƙasa na sha,"

  "Amani baki da hankaline?kinsan me kike faɗi kuwa?wannan abun fa ya shafi kowannanmu,bai kamata ki dinga yi mana dariya ba,"Acewar Aunty babba,

    wurga mata harara amani tayi tare da cewa"yadai shafe ku!karki kuskura ki ƙara mentioning ɗina aciki,domin kuwa bansan anyi ba,lokacin da kuka tsara muguntarku kuka cutar dasu,kunyi shawara dani ne?Kuma ae har shawara saida na baki akan ki daina azabtar da yaran amma kika ƙi ji ke ga shugabar azzalumai,wlh baku da imani zuciyarku ta bushe,kwakwalwarku a toshe take,tamkar ana zuba maku dussa acikin kawunanku saboda ɗabi'unku sak irin na kafuran farko ne,....."

 Waro ido waje Aunty babba tayi tare da faɗin"Ni kike faɗama wannan maganar!"

  Amani tace"Kwarai kuwa dake nake,Muguwa macuciya kuma Azzaluma,zuciyarku ta ƙeƙashe Zalunci kawai kuka sa agaba,daku da uwarku Mammy,tsohuwar banza me shegen son kuɗin tsiya,wlh kunji haushin rayuwarku,shegen kwaɗayin abun duniya,ga baƙar zuciya,ga dogon burin tsiya ko tsoran mutuwa bakwayi..."

  Tunkan amani ta ƙarasa maganar Aunty babba ta kwashe ta da tagwayen maruka,ji kake tasss tatasss!'kafin Aunty babba ta janye hannunta daga kan kuncin Amani,itama ta daddage da iya ƙarfinta na ƙarshe ta kikkifa mata maruka a jere kusan uku ji kake fass tasss taaasss!

  dafe kumatu aunty babba tayi yayin da idanunta sukayi jawur,tunda take arayuwarta ba'a ta6a yi mata irin marin da Amani tayi mata ba,hasalima Amani shakkarta take ji,amma sai gashi yau ta cire yatsunta guda biyar cuf,ta kikkifa mata maruka,

 Koda ganin haka,sae hayaam ta miƙe tare da ɗaga hannu zata sharara ma Amani mari,aikuwa hafsat ta yunkura tare da miƙewa ta damƙo hannun hayaam tana faɗin"baki da hankaline?matar da ta iya ɗaga hannu ta mari mommy har sau uku,itace zaki mara?kina tunanin cewa zaki iya rama mata ne," dariya Amani tayi tare da cewa"ki barta inga ƙarshen rashin kunya,wlh dai dai nake da kowane shege acikin ku,Bana jin tsoranku a yanzu,tun ranar da Amal ta sanar dani komai game da ukubar da kukeyi mata tun daga ranar na ɗaura ɗamarar yin yaƙi daku,"

  Hankali tashe hayaam da aunty babba suka kalli juna jin ta ambaci sunan Amal,

  Hafsat ce tace"Amal na wurinki ne"!?

Jinjina kai amani tayi tare da cewa"Amal tana wurina!itace yarinyar dana zo da ita cikin gidan nan,kun so ku kashe mun ƙanwata,Amma Allah bai baku nasara akanta ba,Amal ta tako da ƙafafunta ta kawo kanta har cikin garin nan,"

  Shiru duk sukayi suna sauraronta,

"Haƙƙin Amal kaɗai ya isa ya jefa rayuwarku cikin masifa,laifin me Amal tayi maku da har kuka wulaƙantar da rayuwarta?yarinya ƴar ƙanƙanuwa amma kukayi mata taron dangi wurin azabtar da ita,saboda tsabar mugunta irin taku,ƙiri ƙiri kuka hanani ganin Amal,ku ka yi mun ƙaryar cewar Amal ta 6ace ba'a ganta ba,mugaye kawai ashe gidan makwabtanmu kuke kaita kuna rufeta,duk in nazo har in bar garin,tana can arufe kamar akuya,ko abinci ma baku bata,wai ku wasu irin mutanene?wace irin zuciya gare ku...? 

  Kasa ƙarasa maganar Amani tayi saboda kukan daya ciyota,nan take ta fashe da wani irin matsanancin kuka,ba ita kaɗae bama hatta hafsat sai da ta zubar mata da kwalla,baƙin ciki kamar ta binne kanta,abun kunyar da mommynta ta aikata ba ƙaramin illa yayi ma zuciyarta ba,

  Hayaam kuwa sae faman mazurai takeyi ita da aunty babba sunyi wuƙi wuƙi,basu da abun cewa,dama ance rana dubu ta 6arawo,rana ɗaya ta me kaya,

  "Wlh kaɗan kuka fara gani!haƙƙin Amal da kuma haƙƙin waɗannan bayin Allahn da kuka cutar bazai ta6a barinku ku zauna lafiya ba,in har ba zaku canza waɗannan munanan ɗabi'un naku ba,mugunta da kwaɗayin abun duniya,dogon buri,rayuwar ƙarya,duk ku kadae gashi har yau Allah bai ta6a baku nasara ba,mutumin da bai ta6a sa Allah alamurransa ba taya zaiga dai dai"?

  Tsoki Aunty babba ta buga tare da nuna mata hanyar fita daga ɗakin tace"zo ki fuce ki bamu wuri tun kafin ranki ya 6aci a wurin nan!shashasha kawai kina tunanin cewa kalamanki zasu iya tankwarani ne?duk duniya ba ayi mutumin da zai zauna yanayi mun nasiha ba,wlh ba ayi shi ba,"

  Girgiza kai amani tayi tare da juyawa a fusace tabar ɗakin tana faɗin"Jiki magayi,"


Komawa Aunty babba tayi yaraf ta zauna gefen gadon tana faman cizon yatsa,miƙewa hafsat tayi tare da fucewa daga ɗakin,

  Fitar ta keda wuya,Hayaam ta dawo gefen aunty babba ta zauna tana faɗin"Yanzu menene mafita"?

..fuskarta a hargitse tace"mafita ta wuce mu gudu salin alin batare da sanin kowa ba,"

  "Saboda me zamu gudu?hakan na nufin cewa sun ci nasara akanmu kenan"?

 "Hayaam ba zaki gane ba,ina tsoran in sake yin arba da hosana ne,bata da hankali,zata ci gaba da tona mun asirine a bainar jama'a"

  "Amma Aunty laila,taya akai yaran suka zauna a wurinki har hakan ya faru?meyasa baki kashesu ba tun lokacin"?

  Guntun tsoki taja tare da kawar da kanta gefe cike da takaici tace"sai yanzu nake danasanin barinsu araye,meyasa ban kashesu ba tun lokacin da suke a wurina ba?wancan shashashan mutumin dana bama aikin zubar mun dasu a daji bansan ya akai yayi sakacin da har suka ku6uta daga hannunshi ba,kuma tun ranar dana bashi su nake ta jaraba kiran wayarshi akashe kullum har na gaji na daina kira,duk shi ya kwafsamin wlh,yanzu yawo acikin gidan nan ma ya haramta agareni,Allah yaso Hafsat ta siya niqabi a kasuwa,zan kar6e shine in sanya a fuskata saboda gudun kar waccen mai ta6in hankalin cikin sun ta ganni.....'

    Shiru suka ɗanyi na wani lokaci,zurfin tunani ta shiga yi kwatsam ta tuna da maganar nan da hajjaju ta ta6a sanar da ita kwanakin baya can da suka wuce lokacin su hosana na a gidan,

  "Idan kin toshe waɗannan hanyoyin,ita kuma waccen ɗayar hanyar da ta riga isa inda baki so fa ya zakiyi da ita'

 Jinjina kai Aunty babba tayi tare da faɗin"Allah ya isa tsakanina da hajjaju,sarai tasan komai game da rayuwar yaran nan amma taƙi sanar dani,babu yadda banyi da ita ba,amma taƙiya saboda tsabar baƙin hali irin nata,da tun farko ta sanar dani cewa ƴan ukune yaran akwai ɗaya dake  aiki a gidan da tuni nasan abunyi,


wannan masifar har ina"?


"Amma kina ganin Ammi zata barsu ne acikin gidan nan?Jiya munyi plan ɗin cewa zaki kirata a waya ki sanar da ita cewa yaran shaggu ne,kin sanar da ita hakan," ta ƙarasa maganar tana kallon fuskar aunty babba wadda ke a hargitse,jin maganar hayaam yasa ta ɗan jinkirta,kamar me nazarin wani abu can ta ɗan washe baki tare da cewa"Hakane!Wannan ita kaɗae ce hanyar da ta rage mun,jiya na kira ammi a waya kuma na sanar da ita cewar Abusufyan ne ya ta6a yi ma wata fyaɗe harta samu ciki ta haifesu,ina da tabbacin cewar AMMI bazata barsu su zauna ba,dole ta koresu ƴan jakar uban,wlh na tsani yaran can,na tsani mahaifinsu duk shine silar komai,ya tashi yayi aure batare da sanin kowa ba,gayanan ya jefa mu acikin masifa,ni duk bama wannan ba,taya akai AMAL ta gudo daga gida tazo Abuja wurin waccen baƙar munafukar?ta ya akai Mammy da Abrah su kayi gangancin da har AMAL ta gudu daga gida ta dawo wurin Amani?

Hayaam tace"Nima abunda nake tunani kenan,don ko aranar da zan bar gidan Amal na ƙunƙume aɗakinmu,zazza6i ya rufeta,Ni babban baƙin cikina ma,muna nan sake da baki,Amal na iya zuwa ta aure wani daga cikin matasan gidan,kinga ae shikenan mukuma tamu ta ƙare,maƙiyanmu za suyi ta cin nasara akan mu,'

  "Insha Allah hakan ma bazata faru ba,in har ɗaya daga cikinku ke da abra bai auri ɗaya daga cikin matasan gidan ba,to sai dai ayi Ragas,Uban kowa ya rasa,itama Amal ɗin tarasa,ita kuma waccen ƴar iskar sai nayi silar mutuwan aurenta,tunda har ta iya ɗaga hannu ta kikkifamun mari,wlh saita gane kuranta,kuma wlh billahil azeemu,muddin Ishaq ya sake ni,itama sai Abbas ya sake ta,inyaso sai muyi zawarcin atare,"ta ƙarasa maganar tana faman sakin huci,tayi danasanin zuwanta gidannan!


   *Boss Bature*


      ❤🤍❤


turo ƙofar ɗakin da ammi ta sauka akayi,Azmee ce ta shigo hannunta ɗauke da kakkauran tea ɗin data haɗa mata,a zaune ta same ta saman darduma jikinta sanye da hijabi,yayin da hannunta ke ruƙe da cazbaha,da alama sallah ta kammala yi,

  Cike da girmamawa azmee ta ƙarasa tare da zuƙunnawa ta gaishe ta,"Ina yini Ammi,ya gajiyar tafiya," 

  da buɗar bakinta sae cewa tayi"Ina Abusufyan yake"?

Azmee tace"sun fita sallar magrib,amma nasan yanzu suna kan hanyar dawowa gida,nan bada jimawa ba nasan zasu shigo ciki,"

  Jinjina kai tayi tare da kai hannu ta ɗauki cup ɗin da azmee ta miƙa mata,abaki takai cup din ta kur6e sa kusan sau uku sannan tace"Idan sun dawo,kice su jira ni a palour gaba ɗayansu,inason ganinsu,"

  Tuni Azmee tasha jinin jikinta,aranta tace"tashin hankali,'a fili kuma tayi saurin cewa"Za'a sanar masu,"sannan ta mike ta kama hanyar fita daga ɗakin,har azmee ta ruƙe handle din ƙopar zata fita,muryar Ammi ta katse mata hanzarinta da cewa"Next time idan zaki haɗamun tea,bana son sugar yayi yawa,sannan madarar tafi bornvitan yawa,da fatan za'a kiyaye,'

   "insha Allah za'a kiyaye,ko akwai wani abu da kike buƙata"?

  "Idan ina buƙata zan sanar dake ne,basai kin tambaye ni ba,zaki iya tafiya,"

  jinjina kai azmee tayi kafin ta buɗe kopar ɗakin ta fuce,babban falo ta nufa tana tafiya tana jinjina wa izza irin ta Ammi,saboda tsabar masifa,ko bornvita azmee bata zuba a tea din ba,madara kawai ta sanya mata amma saboda hali irin na ammi,da ba'a iya yi mata gwaninta,ta buga warning akan madara tafi bornvita yawa,ko ta ina taga bornvitan"?akan tea ma tayi ƙorafin anyi ba dai dai ba,inaga In taji abunda Abusufyan ya aikata batare da saninta ba,tabbas akwai matsala,rayuwarsu sehrish tana cikin garari,don wannan guyababbiyar matar bazata barsu su zauna lafiya ba,acikin gidan nan,

Jin sautin muryoyinsu,yasa Azmee dawowa daga zurfin tunanin da ta shiga,dawowarsu kenan daga masallaci kowa bakin shi ɗauke da sallama suka shigo cikin Main palour din,Abba ne tare da Abusufyan sae junaid atare,bayansu kuma su Abbas ne da ishaq,Mg Osman da kuma Captain Adam,sai kanal yousouf da kuma Marshal wanda ke tare da Dr harris,a bayansu kuma akwai Fawan,twins,jabeer,irfan,khaleed dukansu dai suka shigo ciki,

  ƙarasawa Azmee tayi wurinsu tanayi masu sannu da dawowa,daga bisani ta isar masu da saƙon ammi,nan fa kowa ya shiga fargabar dalilin tarasu da Ammi tace ayi,musamman Abusufyan yafi kowa shiga damuwa,tsayawa su kayi a tsaye kowa yana ta zullumin fitowarta,Abba dae sai ƙarfafa ma abusufyan gwiwa yake,akan ya jure,kada tsoro ya hanashi yi ma Ammi bayanin komai yadda zata fahimta,

Jin takun  takalminta kwas kwas!yasa su yin saurin kai idanunsu akanta,fuskarta na manne da farin glass,kwata kwata babu annuri a fuskarta,yayin da hannunta ke ruƙe da sandar nan ta alfarma,Ƙarasowa tayi tare da samun wuri ta zauna saman 3 seater,sannan ta aza ƙafarta ɗaya bisa ɗaya,tare da kallonsu tace"Ku zauna,"

  A ƙasa su fawan suka zauna,yayin da Abbansu junaid,da abusufyan suka zauna asaman ɗayar 3 seater ɗin,ishaq da abbas suka zauna asaman 2 seater,Dr harris da Omar suka zauna a ɗayar 2 seater,dama 2 set ne na sofa a babban falon,manyan ne suka zauna saman kujerun,yayin da ƙananan daga kan Kanal yousouf suka zauna aƙasa,

Tsit falon yayi na wani lokaci,kai kace mutuwa ce ta gifta,ko motsin mutun bakaji a wurin,kowa ya kame kanshi,

  ɗaya bayan ɗaya Ammi ta dinga binsu da kallo,kowa sae faman noƙe kai yake,shi dai abusufyan ya gaza sakewa,don ko idonshi bai ɗago ya kalle taba,

  ɗaga sandar hannunta tayi tare da nuna Ayan tace"wannan dogon gashin fa?sai kace wani ɗan daudu meyasa baka aske shi ba?

cikin sauri Ayan yace"ƙuraje ne ke fitomun akaina duk in nayi yunƙurin aske gashin"

  Ta6e la66anta tayi,kafin ta janye idonta daga kan Ayaan ta mayar dasu kan fawan,sunnar da kai ƙasa yayi yana ƴan kame kame,

  "Ƴa'ƴan fatima kenan,ba zaku ta6a canzawa ba,yadda kasan sun haɗa jinsi da ibliss,ji bi ɗan iskan askin dake akanshi,hada kala ma ka canza mashi kaiga ƙeƙasasshe ko"?

  Fawan akeyi ma faɗan Amma Abbansu ne ke jin maganar har cikin zuciyarshi,bakomai ya ɗan 6ata mashi rai ba,sai kalmar data faɗi na cewar kamar sun haɗa jinsi da iblis,abun ya tsaya mashi arai,jurewa kawai yakeyi,

  ɗaya bayan ɗaya haka ta dinga sharrance su,har sai da tazo kan junaid wanda keta faman sakin murmushi kamar wani zautacce,

  "Iko sai Allah!kai zonan,"da sandar hannunta tayi mashi nuni da yazo,miƙewa junaid yayi ya koma ƙasan kujerar da take ya zauna,hannu tasa tare da jan kunnanshi tace"Bakasan nazo bane?kowa na zuwa ya gaishe ni,amma banda kai,Abbanku ya sangarta ka ko?shiyasa ka fara jin kanka wani shege,"dafe hannunta yayi yana dariya yace"Ammi dan Allah ki sakarmin kunne na,Da zafi fa,Abba kana gani ko,"?

  "Me Abban naku zai iya yimun bakasan cewa ni na tsugunna na haifesa ba,"

  Zumbura mata baki junaid yayi tare da murguɗa mata baki,

  "Fiye da haka ma zaka iya yimun tunda ubanka ya ɗaure maka mazauni,dole ka murguɗamun baki,ae bazan bar gidan nan ba,sae nasa an tura ka aikin soja,sannan hankalina zai kwanta,"

  Bubbuga ƙafa junaid ya shigayi yana yi mata ƙunƙuni,hakan ba ƙaramin dariya yaso ya bata ba,amma bata bayyana hakan akan fuskarta ba,"

  Shiru ta ɗanyi na wani lokacin kafin tace"kai irfan,tashi ka kiramun gwaggonku,tare da Auntynku Azeema inason ganinsu,"cikin sauri irfan ya miƙe tare da barin wurin ya wuce ɗakinsu gwaggo,

  Bada jimawa ba,sae gashi ya dawo tare da gwaggo da hajiya azeema abayan shi,duk wannan surutun na gwaggon katsina,yau tsit kake jin bakinta,sae faman wurga ido take,wuri suka samu suka zauna,a saman sofas ɗin dake cin mutun ɗaya,

  Bayan kowannansu ya natsu,Ammi ta tsayar da idanunta akan Abusufyan,wanda tunda suka zauna a falon,bai ɗago ya kalleta ba,

  gyaran murya ta ɗan yi tare da ambaton sunanshi"Abusufyan"a firgice ya ɗago yana kallonta,bawan Allah harya fara haɗa gumi,ga yatsun hannunshi dake ta kerma,duk wasu alamu na rashin gaskiya sun bayyana a tattare dashi,Abba sai tausarshi yakeyi yana faɗin"ka kwantar da hankalinka,ka natsu dan Allah,duk kabi ka firgice,hakan ma zaisa taƙi yadda da hujjojin da zamu bata,"ƙasa ƙasa yake yi mashi maganar don karta ji shi,

   ɗakyar Abusufyan ya iya amsa kiran da tayi mashi"Na'am Mommy,"

  "Meyasa kabar ƙasar nan,batare da ka sanar mun ba?laifin me na aikata maka da har kake gudu na?sai kace bani na haifeka ba?bansan me ka ɗaukeni ba,'

  muryarshi na rawa yace"Kiyi haƙuri Ammi,Nima bada son raina na tafi na bar ƙasar nan ba,nasan ni mai laifine a wurinki,ki yafe mun....'saukowa yayi daga saman sofa ɗin ya dawo ƙasa ya zuƙunna yana bata haƙuri,

   "idan har dagaske kasan cewar kai mai laifine,meyasa da ka dawo Nigeria bakazo gida ka same ni ba,don ka nemi yafiyata ba"?

   Shiru yayi yayin da idanunshi ke cike tab da kwalla,gaba ɗaya ya rasa inda zai tsoma ranshi,babbar damuwarshi shine,yadda zai fara yi mata zancensu sehrish,

..hmmmm ta furta sautin tare da mayar da idanunta kan gwaggon katsina tace"Saboda yardar da nayi dake ne yasa na ɗamƙa maki Amanarshi,don ki ladabtar mun dashi,a tunanina zaki canzamin shi,ashe bansan nayi aikin banza ba,"

ɗaure fuska gwaggon katsina tayi,alamar ranta ya 6aci,

    "Ammi dan Allah komai ya wuce,just forget about the past,haba dan Allah,komai ya wuce mana,taya za'a zauna ana ta faman nanata abunda ya riga ya faru.,.,.."

  Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,jin abunda Jahan ke cewa,yadda kasan wanda yasha giya haka ya shiga sambatu yana faman jan guntun tsoki ƙasa kasa,yunƙurawa Marshal yayi da nufin ya buge masa baki,Ammi ta dakatar dashi"basshi ya ƙarasa,ba laifinsa bane,gado yayi wurin Uwarsa,ae ni bansan yaushe ne ƴa'ƴan fatima zasu fara girmamani ba,amatsayina na wadda ta haifi ubansu,"

  Rai a6ace jahan ya miƙe zai bar wurin Abbansu ya daka mashi tsawa tare da korosa yace"Koma ka zauna,Allah yasa inga ka ƙara cewa uffan a wurin nan,"

  Komawa yayi gefen ayaan ya zauna yana faman hura hanci,

Jinjina kai Ammi tayi tana kallonshi tace"Nan gaba fa,in ban bi asannu ba,bugu yaran nan zasu fara kaimun,To Allah ya kyauta gaba,"

  Abba yace'Insha Allah hakan ma bazata ta6a faruwa ba"

  Shidai abusufyan har lokacin yana zuƙunne asaman guiwowinsa,cike da zullumin me zai biyo baya,

  "Uncle ka tashi ka koma ka zauna,jikinka sai kerma yakeyi,Ammi fa ba abunda zata iyayi maka,"Sakin baki abbansu yayi yana kallon junaid dake magana,yana ƙoƙarin kashe wutar da jahan ke ƙoƙarin kunnawa shi kuma zai hura wata wutar,

  Girgiza kai Ammi tayi tare da wurga ma Abbansu harara tace"Bazan iya zama agidan nan ba,yaranka sunfi ƙarfina,"sunnar da kai ƙasa abba yayi kafin ya ɗago yana kallon junaid da yayi maganar ya ɗan jefa mashi harara,

  Suna cikin wannan Zaman sai ga hosana ta shigo cikin falon,tana neman warin ɗan kunnanta daya faɗi,'tashin hankali,gaba ɗaya hankalin kowa ya koma kanta,abusufyan kuwa arazane ya ɗago yana kallonta,ammi duk bata lura da ita ba har sai da Hosana ta buɗe baki tayi magana"Daddy ɗan kunnena ya faɗi a falon nan ban ganshi ba,'juyawa ammi tayi tare da kai idanunta kan hosana dake tsaye tana magana,a wani slow ta sanya hannu ta zame glass ɗin dake a fuskarta,tashiga ƙare ma hosana kallo,cike da mamaki tace"Ina kuka samu matashiyar yarinya acikin gidan nan"?sunnar da kai ƙasa Abusufyan yayi yana faman zare ido zuciyarshi tamkar zata faso kirjinshi ta fito saboda razana,

  Shiru kowa yayi mata aka rasa wanda zai buɗe baki ya bata amsa,

  Jin sunyi banza da ita yasa ta kira hosana da hannunta"Zo nan,"

  Shiga ciki hosana tayi tare da tsayawa agaban Ammi tace"Gani,"

  "Wanene mahaifinki a wurin nan"tayi maganar tana nunasu da sandar hannunta,

...murmushi hosana ta saki tare da ɗaga yatsan hannunta ta nuna abusufyan sannan tace"Gashi nan,shine daddynmu,ni dasu Sehrish da Jahad,"

..a wayance Ammi tace"Oh harku nawa ne a wurinshi"?

  Hosana tace"Ƴan ukune mu,ko in kira maki su jahad ki gansu?"

Cike da mamaki Ammi tace"kira mun su in gansu,"da gudu hosana ta nufi ɗakinsu don ta kira su jahad,

   Tashin hankali,

Wani irin gumi ne ya shiga fesowa daga jikin abusufyan,gaba ɗaya duk yabi ya kama kansa,jikinshi sae faman kerma yakeyi,bashi kaɗae ba hatta sauran dake a wurin zaune,kowa saida yasha jinin jikinsa,musamman Kallon da Ammi ta dinga binsu dashi ɗaya bayan ɗaya,kallon tuhuma,

  Lokacin da hosana ta faɗa corridor ɗin ɗakunansu,hayaam na tsaye a wurin,tana ganinta tasha gabanta tare da cewa"daga ina kike"?

  Murguɗa mata baki hosana tayi kafin tace"Ni bansan wacece keba,ki bani hanya in wuce,su jahad zan kira,wata tsohuwa ce fara tass take son ganinsu,"

   Jin haka yasa hayaam ta gane cewa cewa AMMI ce ke son ganinsu,shu'umin murmushin nan nata tasaki,kafin ta matsa ma hosana hanya ta wuce,jinjina kai hayaam tayi tana faɗin"hada wani zumuɗin Ammi ta kirasu,basu son cewa watan korarsu daga gidan yayi ba,"tana ƙarasa maganar ta nufi ɗakin da Aunty babba take,tana shiga ta sanar da ita cewar ga Ammi can tasa a kira mata ƴa'ƴan Abusufyan,jiki na rawa Aunty babba ta taso,suka fito daga ɗakin domin suje yin la6e,don su ga irin korar karen da ammi zatasa ayi ma su Sehrish,


Bada jimawa ba,Hosana ta fito hannunta ruƙe dana sehrish,ɗayan hannun kuma ruƙe da hannun Jahad,jikinsu na sanye da hijab don tunda su kayi sallar Magrib basu ciresu ba,hosana ce kawai ta cire hijabin jikinta,ta yafa mayafi akanta,


da sallama a bakunansu suka shigo cikin falon,ya salam ae tuni Abusufyan ya zauna ƙasa dirshan yana lazimi,Abba kuwa sae faman jinjina kai yakeyi,gwaggon katsina kuwa tana ganinsu jahad ta shiga zare na mazurai don tasan cewa ƙarshe abun kanta zai ƙare ita da ta sanya mashi hannu ta ɗaure mashi mazaunai wurin yin auren batare da sanin Ammi ba,kowa dai yashiga zullumin abunda zai biyo baya,

  Aunty babba kuwa suna la6e ita da hayaam sun kasa kunne suna jiran jin mai zai biyo baya,jikinsu sae faman tsuma yakeyi,

  Zuba masu ido Ammi tayi tana kallonsu,one by one,ganin yadda matar ta ƙura masu ido yasa duk suka sha jinin jikinsu,daƙyar suka iya haɗa baki wurin gaishe da ita"Ina yini,"

  Bata amsa masu gaisuwar tasu ba,sae nuni da tayi masu da sandar hannunta alamar su zauna,wuri suka samu agaban kujerar da su Omar ke zaune,suka zauna daga ƙasa tare da lankwashe ƙafafunsu,zaman cin tuwo,

   Nuna Sehrish tayi da sandar hannunta tace"Ya sunanki"

  Jiki asanyaye sehrish ta bata amsa da cewa"Sunana Sehrish,"

  Ammi ta kuma cewa"wanene mahaifinki"?

  wurga idanunta tayi akan Abusufyan ta nuna shi da hannu tare da cewa"Gashi nan,shine mahaifinmu"

  jinjina kai Ammi tayi tare da kallon abusufyan wanda keta faman zubda gumi a fuskarsa,duk sanyin A.c din dake akwai a falon,

...hmmmm janye idanunta tayi daga kan Sehrish ta mayar dasu kan Jahad tace"Kefa ya sunanki"?

  "Sunana jahad,"

 "Wanene mahaifinki acikinsu,"

 Juyawa jahad tayi tare dakai hannu ta nuna abusufyan tace"Shine daddynmu,"

   Rai amatukar 6ace Ammi ta daka masu tsawar da ta gigitasu gaba ɗayansu duk suka razana,a tsiwace tace"Kowa ya zuba mun ido yana kallona,ba zaku faɗamun a ina kuka samo su ba?taya akai Abusufyan ya zama ubansu!"

  Abba ne yayi ƙoƙarin buɗe baki yace"Ya'yanshi ne dagaske,kamar yadda suka faɗa Ammi,"

  Aruɗe Ammi tace "Ni kake faɗama cewa ƴa'ƴanshi ne?kada ku raina mun hankali ta gidan ubanwa Abusufyan yayi aure da har zai haifi waɗannan balagaggun ƴan matan!"?

  Fashewa da kuka hosana tayi,sehrish da jahad kuwa tuni hawaye sun soma wanke masu fuskarsu,jikin Marshal ba ƙaramin sanyi yayi ba,haka zalika sauran dake zaune a wurin,

  "Abusufyan!ka faɗamun taya akai ka samu yaran nan?Na yarda cewa ƴa'ƴanka ne koda basu faɗamun da bakinsu ba,saboda ina ganinsu nasan cewa Jinina ne su,ko ba don kamanninka dake akan fuskarsu ba,So nake naji TAKUN hanyar da aka Same su!?nasan halinka tun fil azal baka rabuwa da mata,ka faɗamun gaskiya,ka ta6a yin mu'amala da wata ƴa' mace ne har ta samu cikinka"?

  A kiɗime abusufyan ya shiga yi mata rantsuwa yana faɗin"Wlh Ammi tunda nake arayuwata ban ta6a kusantar zina ba,Nasan cewa zaiyi wuya ki yadda dani,amma wlh saida na auri mahaifiyarsu sannan na same su,ga gwaggonan itace shaidata,"

  Tamkar zata rufashi da duka haka tashiga balbaleshi da masifa"Bazan ta6a yadda da kalamanka ba,karka kuskura ka ƙara cewa ta hanyar aure ka same su,in ba haka ba saina ci maka mutunci a wurin nan!dama najima ina zarginka abusufyan,banta6a tunanin zakayi mun haka ba,ka cuce ni,bazan ta6a yafe maka ba,rashin jin maganarka har yakai ka kawo mun Shaggu acikin zuri'ata,bazan ta6a lamun ta ba......'

  Rai a6ace gwaggon katsina ta katse mata hanzarinta da cewa"Ya isa haka,babu laifin abusufyan acikin wannan lamarin,Nice na aura mashi yarinyar da ta haifa mashi waɗannan ƴa'ƴan,don haka kidaina ambaton sunansu da shaggu saboda baki da hujjar yin hakan,bazan ta6a yarda a tozarta ƴa'ƴan abusufyan ɗina a gabana ba ehe," kowa yayi mamakin yadda gwaggon katsina ta mayar ma Ammi martani,tamkar wata mai cikakken hankali,

  "Dan Allah Ammi ki daure ki fahimce shi,rashin sanar maki da basuyi ba,shine babban kuskuren da Abusufyan da gwaggo suka yi,Gwaggo ta aikata hakanne saboda son da takeyi ma abusufyan wannan dalilin ne yasa ta aura mashi mahaifiyarsu batare da saninki ba,saboda tasan halinki,kin tsani auren bare,gashi shi kuma abusufyan ya kwallafa rai akan yarinyar,wannan ne yasa ta aura mashi ita,saboda gudun karya faɗa halaka.....  "Wani irin kallo da Ammi ta jefa mashi ne yasa shi dakatawa da yin maganar da yake,wato Abbansu junaid,

  Aunty babba dake la6e ita da hayaam suna sauraronsu,saboda tsabar farin ciki kamar su zuba ruwa a ƙasa su sha,burinsu kawai Ammi ta koresu Jahad,

  Kowa saida ranshi ya 6aci a wurin nan,saboda yadda ammi ta haƙiƙance akan cewar bazata kar6i shaggu ba acikin zuri'arta,a ƙarshe tace"na riga da na yanke hukuncin korarsu daga cikin zuri'ata,banason ganinsu,kuma duk wanda yayi yunƙurin binsu acikinku wlh saina tsine mashi yabi duniya,kuma zan yafe shine acikin ƴa'ƴa Na,

  Wani irin matsanancin kuka su jahad suka fashe dashi,haka abusufyan ma kuka yake yi tamkar ƙaramin yaro,ƙiri kiri za'a rabashi da ƴa'ƴanshi,su Abba kuwa gaba ɗaya jikinsu yayi mugun sanyi,Hankalin Omar ba ƙaramin tashi yayi ba,haka zalika sauran kowa hankalinshi yayi mugun tashi,

  Su aunty babba kuwa dake la6e,jin an kori su sehrish,yasa suka daka uban tsallen farin ciki,saboda tsabar dariyar mugunta,hada hawaye,da gudu suka koma cikin ɗaki,suna faman dariya,burinsu ya cika,


"Ku tashi ku fuce daga cikin gidan nan tunkafin insa ayi waje daku,"jiki asanyaye suka miƙe tsaye jahad ta ruƙo hannun sehrish da jahad acikin nata,tafiya sukeyi kamar wanda aka zarewa laka,yayin da hawaye ke gangarowa daga idanuwansu,yunƙurawa abusufyan yayi da sauri zaibi bayansu,aikuwa abba yayi hanzarin damƙo rigarshi ya janyoshi,ya dawo da shi saman sofa din,a haukace ya shiga kiciniyar kwace kanshi yana fadin"Ka barni yaya hossein wlh sai dai ta tsinemun amma bazan bari rayuwar ƴa'ƴana ta wulakanta ba,duk inda zasu je ƙafata kafarsu,"ganin abusufyan na ƙoƙarin zaucewa yasa su Marshal Omar dasu ishaq da abbas suka rurrukeshi,sai faman hargowa yakeyi,yana kokarin kwacewa don yabi bayansu sehrish,


bazasu iya jurar ganin halin da mahaifinsu ke ciki ba,hakan ne yasa suka fuce waje da gudu suna kuka,tamkar ransu zai fita,sae faman shessheƙar kuka sukeyi,


Suna cikin wannan yanayin Motar SGR,ta shararo da gudu cikin gidan,a tsiyace su kayi parking ɗin motar,tunkan Amstrong ya buɗe mashi motar,ya sanya kafarshi tare da harba murfin motar,ya fito daga ciki,kai tsaye ya nufi wurinsu Sehrish dake a tsaye suna kuka,kwata kwata basu lura dashi ba,sae dai suka ji an ruko hannayensu,Jahad da hosana,a firgice suka ɗago suna kallonshi,"ku wuce mu shiga ciki,"yayi maganar tare da jan hannunsu,sehrish ma tabi bayansu suka koma cikin falon,jin sallamar Sgr yasa hankalin kowa komawa kansu,ganin ya dawo dasu sehrish yasa kowa ya shiga sauke ajiyar zuciya,Zuba mashi ido Ammi tayi tana kallon ikon Allah,

  ƙarasawa cikin falon yayi tare ce masu sehrish"Ku samu wuri ku zauna,"jiki asanyaye suka samu wuri ƙasa suka zauna,suna faman sauke ajiyar zuciya,

  Zama sgr yayi asaman sofa,tare da aza ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya,yayin da yake fuskantar Ammi wadda ta zuba ma sarautar Allah ido,

  Sai da ya mula yasha iska sannan ya soma magana

   "dama saida raina ya bani cewa hakan zata iya faruwa,that's the reason why na tanadin hujja ɗaya kuma kwakkwara wadda zata wanke zargin da kikeyi akan abusufyan da kuma waɗannan triplet ɗin,"

  Ƙarasa maganar yayi tare da sanya hannunshi cikin aljihun wandon jeans ɗin dake ajikinshi,ya zaro wayar shi,

   

  *mu haɗu On monday don jin yadda zata kaya,*

  


_har yanzu wasu basu gode mun akan long page ɗin da nake sawa,in banda ma rashin godiyar Allah irinta ɗan adam,a ƙalla yawan one page da nake sawa Yayi fiye da 3 page na wasu masu rubutan,Allah har mamaki nakeyi in naga page ɗin wasu writers din,duk read More 3 ne amma ni kaga page mai read more 9 har 12 ina sakawa,ƙaramin page ɗina shine zaka ga read more 6,zama nakeyi inyi rubutu kamar zan kashe kaina,amma wasu saboda rashin godiyar Allah suna zuwa sunayi mun complain ɗin wai adinga posting sau biyu?a iya sanina Vip ne ma ake sanya 2 page,amma ni ina sanya maku kusan 3 page a hade duk da hakan baiyi maku,idan so kuke sai in dinga raba maku shi uku,saboda na lura hakan yafi maku,kunfiso ku ganshi arabe,bakomai ne yasa ma nakeyin page masu tsayi ba face don in samu intakaita labarin saboda yana da tsayi,idan kuma aka cigaba da raina abunda nake sanyawa wlh zan mayar dashi ne read more uku in tafi dai dai da kowa👍_

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





Saman Gadon ta haye ta  kwanta tare da jan bargo ta lullu6e,zuciyarta cike da wani irin farin ciki,sai faman sakin kayataccen murmushi take,daƙyar bacci 6arawo yayi awon gaba da ita,❤


Wuraren sallar asuba,jahad ta farka tare da tashin su hosana,atare bayan sunyi alwala su kayi salla,bayan sun kammala suka koma saman gadon suka dasa wani sabon baccin don bai ishe su ba,


Ƙarasowa hafsat tayi ƙopar bedroom ɗin nasu,jikinta sanye da dogon hijabi,hannu tasa ta ɗan bubbuga ƙopar ɗakin,shiru ba'a buɗe ba,ƙara bugawa tayi,bugun ya isa cikin kunnan sehrish,cikin bacci tace"Wanene"?

Hafsat tace"Ni ce,"

"Kece wa"? Sehrish ta tambaya a yayin da ta miƙe tare da tunkarar ƙopar ta buɗe,Tun daga ƙasa har sama sehrish ke bin ta da kallo don batasan wacece ita ba,amma tabbas ta ta6a ganin fuskarta,kuma jiya taga gifcinta acikin gidan,ga kuma kamannin fuskar Yaya ishaq a fuskarta,

  ƴan kame kame hafsat ta shiga yi,muryarta na inda inda tace"am...um..jahad.." katse ta sehrish tayi da cewa"ba ita bace,Ni sunana sehrish,jahad tana ciki tana bacci,"

  "In ba damuwa inason ganinta,"

Matsa mata hanya sehrish tayi,ta shiga cikin ɗakin nasu,rufe ƙopar sehrish tayi sannan ta koma ciki itama,sae faman kallon kallo suke ita da hafsat,duk tabi ta kama kanta,kana ganin fuskarta zaka fahimci cewar bata da gaskiya,

  Wuri ta samu gefen gadonsu ta zauna,idanunta na akan su jahad da hosana dake ta sharar bacci,

  Muryarta a sanyaye tace"in ba damuwa,dan Allah ki tashe su daga baccin inason yin wata magana dasu mai mahimmanci,"

  Batare da musu ba,Sehrish tace toh,sannan ta haye saman gadon tana ambatan sunayensu,gami da bubbuga ƙafafuwansu"jahad!hosana!ku tashi ana son ganinku,"

  cikin bacci hosana ta buga tsoki tana fadin"dan Allah a ƙyale ni,kar a takuramin,"

  Jahad kuwa tuni ta farka,tana faman mutsustsuka idanuwanta,wurga idanunta tayi kan sehrish tace"Wai lafiya"?

  "Wannan ce ke son magana daku,"tayi maganar tana nuna hafsat dake zaune,

  Juyawa jahad tayi tana kallonta,cike da mamaki ta ambaci sunanta"Aunty hafsat!" sunnar dakai ƙasa hafsat tayi,fuskarta dauke da matsananciyar damuwa,daƙyar ta iya amsa mata"Na'am jahad,"tashi zaune jahad tayi,suna fuskantar juna ta sake ambatar sunanta"Aunty hafsat,"

  "Kinsanta ne"? Sehrish ce tayi tambayar,jahad tace"Niko na santa,itace ɗiyar wannan matar da nake faɗa maki wadda ta azabtar da rayuwarmu,kuma wannan itace ta ɗauke mu acikin motarta,ni da Hosana ta kai mu hannun wannan mugun mutumin wanda ya kai mu daji har yayi ƙoƙarin cutar da Hosana,"

  Jin wannan maganar yasa ran sehrish ya 6aci,harara ta wurga ma hafsat tare da nuna mata hanyar fita daga ɗakin tace"Dan Allah malama tashi ki fita ki bamu wuri!bamu son ganinki!mugaye kawai Azzalumai,kun cutar da rayuwar ƴan uwana,saboda son zuciya irin naku,basuyi maku laifin komai ba,Amma kuka tsangwamesu,saboda kunga basu da gata,Insha Allah sai kunga sakayyar da Allah zaiyi masu,kuma sai kun ɗanɗana irin uƙubar da kukayi masu,"

  Hawaye ne suka shiga zarya a fuskar hafsat,dama saida ranta ya bata cewar dakyar ne su yafe mata,

  Janye idanunta tayi daga kan sehrish ta mayar dasu kan Jahad,cikin shessheƙar kuka tace"dan Allah ku yafe mun Jahad,nasan mun cutar daku,amma inaso ku sani bada son raina ba,na kaiku wurin wannan mutumin,Mommy ce ta sanar dani cewa Gidan marayu za'a kaiku,shiyasa har na ɗauke ku,kuma nayi hakan ne saboda tsoran karta halakar daku acikin gidan nan don ba yadda banyi ba akan ta kyale ku amman ta kiya,shiyasa ma na amince da akaiku gidan marayun ashe zubar daku tasa ayi,'

  "Ba zamu ta6a yarda da kalamanki ba,saboda tun farko baki nuna kina son mu zauna acikin gidan ba,ke da mommynki,shiyasa kuka haɗa baki ke da ita,kika fara yaudararmu kina nuna kamar kina son mu ashe,so kuke ku fitar damu daga cikin gidan,saboda rashin Imani Aunty hafsat kika damƙa mu a hannun wannan mutumin,to bari kiji Ya Omar ya kashe shi har lahira!!

  Gabanta ne ya faɗi rassss!hankalinta yayi mugun tashi,a kiɗime tace"Ya kashe shi!"

  Jahad tace"kwarai kuwa Ya Omar shi ne ya kama shi da hannun shi acikin gidan gonarsa,lokacin da yake ƙoƙarin keta haddin hosana,aikuwa ya fasa mashi kai,anan wurin ya zama gawa,'

    Tana kai ƙarshen maganarta sehrish ta ɗaura da cewar"tun yanzu kwara kusan inda dare yayi maku!don wlh Ya Omar bazai sassauta maku ba!muddin yaji cewar kune kukayi silar da har wannan mutumin ya ɗauki su jahad ya kaisu daji,sannan ku fara tunanin irin hukuncin da kuma zaku fuskanta a wurinshi!"

  Wani irin wahalallan yawu hafsat ta haɗiya,tsananin tsoro ne ya bayyana akan fuskarta,ba don komai ba sai don jin cewa An kashe mutumin nan!tun da har Omar zai iya kashe rai akan su hosana,tabbas ba ƙaramin so yake masu ba,kuma akansu zai iya hukunta kowa,yanzu su menene sakamakonsu?

  "Baku da wata mafita,shawara nake baku tun kafin hosana tayi maku tonan asiri,kwara kusan abunyi,don tace saita sanar ma Daddy da Ya Omar abunda kukayi mana!" jahad ce tayi maganar,

  Gaba ɗaya duk sun bi sun tsoratar da ita,la66anta har kerma suke wurin rokonsu tana cewa"Dan Allah ku yafe mun,wlh nayi dana sanin duk wani abu da mu kayi maku,har ga Allah ni bada sanina ba,mommy ce ta shirya duk wannan,Allah shine shaidata,bazan yi maku ƙarya ba,"sosai hafsat ke kuka,

Ruko hannun jahad tayi acikin nata tana fadin"jahad nasan kina da sauƙin kai,dan Allah ki yafe mun,wlh nayi nadamar abunda mu kayi maku ni da mommyna,nasan naƙi ku da farko amma daga baya naso ku sosai,kuma nayi kukan rashinku atare dani,lokacin da nagane cewa Mommy ba gidan marayu tasa akaiku ba,har faɗa sai da mu kayi da ita,ko isasshen bacci bana samu a lokacin saboda tunanin wani hali kuke ciki......"ƙarasa maganar tayi tare da sanya hannu tana share hawayen dake zuba a kan fuskarta,

  Shiru su kayi da alama jikinsu ya ɗanyi sanyi,Sehrish tace"Jahad,idan kinyi niyya ki yafe mata,'jinjina kai jahad tayi tare da cewa"Ni dama ban ruƙe ki araina ba Aunty hafsat,na yafe maki Allah ya yafe mana gaba ɗaya,"

  Amsawa tayi da "Amin,sannan tace"Hosana fa?dan Allah ku tashe ta inaso in nemi yafiyarta,"

  Hannu Sehrish takai tare da bubbuga ƙafarta,farkawa hosana tayi,idanunta sunyi suntum saboda bacci,

  "Hosana ki tashi,ga Aunty hafsat nan tana son magana dake,"jin an ambaci sunan Aunty hafsat yasa ta wartsakewa ta miƙe daga zaune,koda idanunta su kayi arba da fuskar hafsat,nan take ta murtuke fuska rai a6ace tace"Ni bana son ganinta,na tsaneta kamar yadda suka tsane mu ita da Mommynta,Aunty hafsat muguwace bata tsoron Allah,itace takai mu wurin wannan mummunan mutumin wanda yakusa kashe ....."katse ta jahad tayi da cewa"pls hosana just forget about the past,forgive her pls,Aunty hafsat tayi nadama,kuma bada son ranta ba ta kaimu wurin mutumin nan ba,Mommynta ce ta shirya wannan," 

  Maƙe kafaɗa hosana tayi alamar bata yarda ba,harara ta wurga ma hafsat ɗin tana murguɗa mata baki tace"Allah saina faɗama Ya Omar da daddy,ko kukan jini zatayi sai dai tayi,amma saina faɗa,saboda rashin Imani kamar wasu dabbobi haka kuka rufe mu acikin store babu abinci ga ƙishin ruwa,ko iska babu,amma ko ajikin ku mu rayu ko mu mutu wannan ba matsalarku bace,zafi kamar zai kashe mu,adaren ranar da muka kwana a store,ba don jahad tayi mun fifita ba da Allah kaɗae yasan me zai biyo baya don rashin imani ku kuna can kuna shan A.c,wlh saina faɗama daddy....."fashewa hosana tayi da kuka,hada bubbuga ƙafarta,daga gani abun ba ƙaramin ciwo yake yi mata ba,ya tsaya mata arai,

  Gaba ɗaya jikinsu yayi wani irin sanyi,musamman hafsat,duk yadda taso ta shawo kanta amma abun yaci tura,hosana ta rantse ta maya akan cewar saita faɗa ma Ya Omar,hatta jahad sai da taso ta lallasheta,amma ina ƙarshe sai ta dinga ƙoƙarin bugun jahad din,

  Ganin haka yasa sehrish kallon hafsat tare da cewa"dan Allah kiyi haƙuri ki tafi kawai,hosana batasan ganinki,idan tana kallonki haukanta zai iya tashi,"

    Jiki asanyaye Hafsat ta mike,tana tafiya tana waiwayonsu yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,a haka har ta isa ƙopar ɗakin ta buɗe ta fuce da gudu tana kuka,

  Hannu Sehrish tasa tare da janyo hosana ta rungumeta sosai ajikinta tana lallashinta,da ƙyar ta samu hosana tayi shiru,sai faman sauke ajiyar zuciya take yi,komawa su kayi suka kwanta kowa da abunda yake saƙawa aranshi,


*Aunty Babba*


Suna kwance ita da hayaam sai faman sharar bacci sukeyi suna jan minshari yadda kasan bijimayen sa,sun cika gadon su biyu kawai,babu wanda ya farka acikinsu balle suyi tunanin yin sallar asuba,can cikin bacci Hayaam ta dinga jin ana bugun ƙopar ɗakin nasu tamkar za'a balle ta,dogon tsoki taja tana faman yatsina fuska alamar an takurata,a ƙule tace"Wai dallah wanene ke buga ƙopar ɗakin nan"!?

  Muryar hafsat tajiyo daga waje cikin shessheƙar kuka tace"Ni ce,ki zo ki buɗe mun ƙopa,"

  Jiki na rawa hayaam ta saukko daga saman gadon ta ƙarasa tare da buɗe ƙopar,gabanta ba ƙaramin faduwa yayi ba ganin fuskar hafsat sharkaf da hawaye,hankali atashe tace"Meya faru ne kike kuka"?

  A tsiwace hafsat tace"Ba dole inyi kuka ba!kun jefani cikin masifa!ki bani hanya na wuce,Da Mommy nake so inyi magana,"tana faɗin hakan ta bangaje hayaam tare da wuce wa ciki,duk tabi ta ruɗe,wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare ma hafsat maƙoshinta,lokacin da tayi arba da Aunty babba,baje saman gadon tana sharar bacci,wato hankalinta kwance ita,batasan wainar da ake toyawa ba,

  Da karfi ta ambaci sunanta"Mommy!Mommyyyyyyyy!

  A firgice Aunty babba ta farka,agigice ta tashi zaune tana faɗin"Lafiya hafsat kike mun irin wannan kiran"?

  "Ina fa lafiya mommy!ashe ke kina nan kina sharar bacci,ni kin barni cikin tashin hankali,jiya ko isasshen bacci ban samu ba,saboda tunanin hukuncin da Ya Omar da daddy zasu yanke mana..."

  Jin wannan maganar yasa Aunty babba fashewa da dariya tana tafa hannu,

  Hakan ba ƙaramin fusata hafsat yayi ba,muryarta na rawa tace"Mom...my dariya ma kike yi"?

Aunty babba tace"to me kikeso inyi in banda dariya,ke bakisan meya faru ba jiya"?

  Zuba mata ido hafsat tayi tana kallonta,

  "Hayaam zo ki faɗa mata da alama batasan meya faru ba,ae mu yanzu bamu da sauran damuwa,hankalinmu a  kwance yake kamar muna cikin jirgi gobara ta kama," tana magana tana faman washe baki,

  Ƙarasowa inda hafsat take a tsaye,hayaam tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli hafsat tare da cewa"ke bakisan cewa jiya Ammi ta kori su Jahad daga gidan nan ba?korar ma korar wulaƙanci,ae shiyasa kika ga mun saki baki muna bacci hankalinmu kwance,saboda bamu da sauran damuwa yanzu,"

  Wani irin kallo hafsat ta wurga mata tare da cewa"Amma dae a mafarki hakan ya faru ko"?

  Aunty babba tace"Wani mafarki,jiya agabanmu Ammi ta korasu,da gudu suka fita daga gidan nan suna kuka,"

  Tsabar takaici ya hana hafsat cewa komai,

    Hayaam tace"Ae kawai ki kwantar da hankalin ki kema,babu mai tuhumarki akansu,Yaran da yanzu ba'asan ma inda suke ba,"

   "Mommy!dama tunanin da kuke kenan?shiyasa baku damu ba,ko kaɗan"

  ""Kwarai kuwa akan me zamu damu"?

Hannu hafsat tasa tare da dafe kanta,tana faɗin"Ya salam!Wlh Mommy idan mafarki kike toh ki farka!domin kuwa jahad da hosana suna acikin Gidan nan!babu inda suka je!!

  Wani irin bugu zuciyar Aunty babba tayi ji kake daraam,a ruɗe tace"Kamar ya kenan"?

  "Mommy Jahad da hosana suna nan!Yanzu haka daga bedroom ɗinsu nake,naje ne domin in nemi yafiyarsu akan laifin da muka aikata masu,"

  Saboda tsabar tashin hankali har suna haɗa baki Ita da hayaam wurin cewa"Jahad da hosana suna acikin gidan nan!!!"

  Jinjina kai Hafsat tayi kafin ta ɗaura da cewar"mun shiga uku mommy,mun ja ma kanmu bala'e da masifa!Ashe Ya Omar shine ya taimake su hosana acikin gidan Gonar mutumin nan,kuma a dai dai lokacin da yake ƙoƙarin yin raping ɗin hosana!

  Hannu Aunty babba ta aza aka tana fadin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"

  Hayaam kuwa sai faman zazzare ido take,

  "Mommy,bugu da ƙari,a nan wurin Ya Omar ya tarwatsa kan mutumin nan ya mutu har Lahira,"tunkan hafsat ta ƙarasa maganar Aunty babba ta saukko daga saman gadon,hannayenta asaman kanta take fadin"Nashiga ukuna,Na bani na lalace,na ru6e!hafsat dan Allah ki faɗamun gaskiya,!dagaske baba alamu ya mutu!kuma Omar ne ya kashe shi saboda su Hosana!ashe shiyasa kenan naita neman number wayansa daga baya ban samu,wannan wata irin masifa ce!,

   Zarya tashiga yi acikin ɗakin tana faman cizon yatsa,Hayaam tace"Aunty laila don Allah ki kwantar da hanlinki...."

  Hankali tashe Aunty babba tace"taya zaki ce in kwantar da hankalina?bayan ga kashi cike a wandona,ni bansan wani irin hukunci Omar zai yanke mun ba" tana magana zufa na gangarowa a fuskarta,

  Ita kanta hayaam,duk a tsorace take duk da ba ita ta aikata laifin ba,amma ta razana da jin cewar Omar ya kashe mutumin da Aunty babba tasa ya zubar mata da yaran,

  "Yanzu hafsat menene mafita"!tayi maganar muryarta tamkar zata fashe da kuka,

  Kafin hafsat tace wani abu hayaam ta rigata cewa"Ni ina ganin kawai Aunty laila,ku tattara kawai kubar gidan nan ke da hafsat,"

  Wani irin kallon rainin wayau hafsat tayi mata tare da cewa"Mu tattara mubar gidan nan fa kika ce?ke kuma fa?ko kina tunanin cewa In asirin mu ya tonu,ke bazai shafe ki bane?tun wuri kusan inda dare yayi maku ke da Mommy!saboda kune baku da alaƙa da gidan nan!Ni kuwa ba inda zanje saboda nasan cewa duk hukuncin da daddy zai yanke mun bazai ta6a korata ba a gidan nan,saboda Ni ƴarsa ce,nan kuma gidan kakana ne,"

  Zuru zuru hayaam tayi jin abunda Hafsat tace,Aunty babba kuwa batasan ma me suke magana akai ba,saboda kanta ya ɗau chargy,sae faman zagaye ɗakin takeyi,ta rasa inda zata tsoma ranta taji daɗi,

   "Wlh da nasan yaran nan suna acikin gidan nan,da tun jiya da daddare zanbi dare,in taushe masu hanci da pillow har sai sun bar duniya don ubansu,yara sun zame man bala'e!"

  Girgiza kai hafsat tayi tana kallonta,har yanzu dae babu alamun dana sani atattare da ita,

  "Tunda nake ban ta6a shiga tashin hankali ba arayuwata sai akan waɗannan yaran!komai nasa agaba sai naci nasara akanshi,amma waɗannan tsinannun yaran sun tarwatsa mun duk wani plan ɗina,Ba kowa nafi jin haushi ba,face Ubansu,duk shine silar daya auri uwarsu a 6oye harta haifo mana mugun abu,Allah danasan da zaman yaran tun suna cikin ciki zansa a markaɗe munsu,don karsu duniya,'

  "Mommy dan Allah kidaina wannan soki burutsin!kin ishemu da surutu kamar wata zautacciya,duk waye ya jefa mu cikin halin nan in ba ke ba?maimakon ma kiyi tunanin sama mana mafita,Sai wasu sambatu kike marasa kan gado,ni bazan iya jurar jin waɗannan munanen kalaman da kike jifar su jahad dashi ba,inaso ki sani su ɗin ƴan uwana ne," 

  Juyowa Aunty babba tayi tamkar zata rufe hafsat da bugu,"Don Ubanki Har ni zaki faɗama cewar ƴan uwanki ne!sun fini kusanci dake ne?Ko ciki ɗaya kuka fito tare dasu ne?

  "Wlh mommy da ace ciki ɗaya na fito dasu dana fi kowa farin ciki,tun daga kan halayansu da ɗabi'unsu zai tabbatar maka da cewar mahaifiyarsu ta basu tarbiyyar daya dace,kuma ita mai kyakkyawar zuciyace shiyasa ƴa'ƴanta ma suka kasance masu kamar yadda take,Ni ce dai nayi babbar asara,dana fito daga jikin ki!gashi nan yanzu sai danasani nake....."kasa ƙarasa maganar tayi,a hanzarce ta watsa da gudu tabar ɗakin,saboda yadda taga Aunty babba ta tunkarota azafafe,yadda ranta ya 6aci ɗinnan komai zata iya aikatawa,

ƙafafunta ne suka fara yi mata raɗaɗi ba arziƙi ta koma daga gefen gadon ta zauna,idanunta sunyi jawur saboda tsabar 6acin rai,zuciyarta sae faman tafarfasa takeyi mata,tamkar zata fasa ƙirjinta ta fito waje,zama hayaam tayi daga gefenta,kowannansu yayi zuru zuru,

  "Aunty laila!ni ina ganin kawai ki gudu batare da sanin kowa ba,in ba haka ba,inajiye maki tsoron abunda zai biyo baya,"

   Cike da takaici Aunty babba tace"Hayaam naso ace hada Amani muka aikata wannan laifin,saboda banaso taci galaba akaina,yanzu in ishaq ya sake ni,ni kaɗae zanyi zawarci na,bakowa nafi jin haushi ba face hosana!mahaukaciyar banza,ina zaman zamana lafiya na,ta nemi tozarta ni agaban kannen mijina,wlh in har ta tona mun asiri,ni kuma sai nayi silar mutuwarta!!!!!!!!!!!!!!

  "Dan Allah Aunty laila kidaina kira mana mutuwa,muji da abunda ke damun mu,duk yadda za'ae yanzu kada ki bari kuyi arba da hosana ɗin, yunwa nata cinsu,amma saboda gudun haɗuwarta da Omar ko Ishaq,yasa ta gaza ko ɗan leƙawa waje,


Bayan fitar Hafsat tashi suka yi suka zura Hijabs ajikinsu,sannan suka fito atare suka nufi ɗakin daddynsu,kamar yadda Sehrish ta basu shawarar su je su gaishe da daddynsu da Ammi da su hajiya Azeema,


Abusufyan na kwance saman gadonshi yaji ana knocking door ɗin ɗakinsa,miƙewa yayi tare da ajiye wayar hannunshi saman side drawer,ƙarasawa yayi yasa hannu ya buɗe ƙopar,zuba masu ido yayi yana kallonsu,sam baiyi tsammanin zai gansu ba,abun ba ƙaramin burgeshi yayi ba sunsha hijabai ajikinsu,sae faman murmushi suke sakar mashi,

  "My triplets"ya ambaci hakan tare da basu hanya don su shiga ciki,rufe ƙopar yayi bayan sun shiga daga ciki,

  Saman gadonshi hosana ta haye,jahad da sehrish kuwa a ƙasa suka lankwashe ƙafafunsu suka zauna,

  Wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana kallonsu,

  "Ina kwana daddy,an tashi lafiya,"

Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Lafiya lou my daughters,Nayi mamakin ganinku,waye acikinku ya bada shawarar azo agaishe ni ne"?yayi maganar yana kallon fuskokinsu,

Jahad ce ta nuna sehrish da hannu,

  "Kinyi tunani mai kyau,dama yanzu nake shirin zuwa in taso ku,don muje ku gaishe da Modibbo,da Ammi da sauransu,abunda ya dace ne,kullum da safe ku dinga zuwa kuna gaishe dasu,"

  Atare suka haɗa baki wurin cewa"In shaa Allah zamuyi hakan daddy,"

  Juyawa yayi tare da kallon hosana dake kwance,hada rufe ido tana minsharin ƙarya,don yayi tunanin cewa bacci ne ya ɗauke ta,

  Hannu yasa tare da jan kumatunta,nan take ta fashe da dariya,shima dariyar yayi kafin daga bisani,yace"ku tashi mu tafi ɗakin Ammin atare don ku gaisar da ita,

Saukowa hosana tayi daga saman gadon,ya ruqo hannunta dana jahad,suka jera tare suka fuce,


Suna tsaye a ƙopar ɗakin Ammi,sae ga Junaid,yana hangosu ya shiga sakin murmushin nan nashi,jiki na rawa ya nufi wurinsu,Gaisar da Abusufyan ya fara yi"Gm Uncle,"cike da zolaya Abusufyan yace"a haka zan baka auren ƴa ta?kana gaisar dani daga tsaye sai kace wani tsaranka ba wani respect"?jin haka yasa junaid saurin duƙawa ƙasa,sannan yace"Ina kwana Uncle"?

 Dariya su kayi gaba ɗayansu,ganin yadda ya zuƙunna,

  "Lafiya lou in law ɗina,ko kaifa,miƙe tsaye toh tunda ka ƙaraso sae mu shiga ciki atare,"mikewa yayi fuskarshi a washe,duk a tunanin Abusufyan junaid wasa yake yi masa yawan zancen zai bashi auren ɗaya daga cikinsu,baisan dagaske shi kamu yake yi ba

 da sallama a bakunansu suka shiga cikin ɗakin,koda ammi taji muryoyinsu,da sauri ta kashe tabar da take zuƙa,ta sanya ta acikin Ashtray dake ajiye ƙasa,da ƙafarta ta tura shi ƙarƙashin gado,duk akan idon Abusufyan abun yaso ya bashi dariya,lallai Ammi ta kimtsu tunda har ta fara jin kunyar jikokinta su ganta tana zuqar sigari,

   A saman carpet,kowannansu ya zauna tare da lankwashe ƙafa,Abusufyan ne ya fara gaisar da ita"Ina kwana Ammi,kun tashi lafiya?Ya gajiyar tafiya"?

"Lafiya lou Alhamdulillah,"ta amsa mashi,Sannan su Jahad suka haɗa baki wurin miƙa gaisuwarsu,da murmushi a fuskarta ta shiga amsa masu ɗaya bayan ɗaya,a ƙarshe ta tsayar da idanunta kan Hosana tace"Kin tashi lafiya"?

  Murmushi hosana ta saki tana faman noƙe kai tace"lafiya lou,"

      Janye idonta tayi daga kan hosana ta mayar dashi kan junaid tace"Sarkin Murmushi,Angona nakaina naga kayi kyau sosai ka kuma ƙara haske,faɗamun menene sirrin"?

  "Kishiya zanyi maki ne"yayi maganar yana murmura mata ido,ɗan waro ido waje tayi tare da cewa"Wacece ita"?

  ɗagowa yayi yana kallonsu,Sehrish har sai da ya gano jahad sannan ya nuna ta da hannu yace"Gatanan,"

  Ammi tace"Kin shirya yin kishi dani ko"?

  Girgiza kai jahad ta shiga yi alamar a'a,

  "To kaji bazata iya kishi dani ba,sai ka haƙura da auren gaba ɗaya,don ni bazan zauna da kishiya ba,"

  "A'a wlh Ammi sai dai ki haƙura dani in aurota,"

Yadda yayi maganar ba ƙaramin dariya ya basu ba,don har saida suka dara,

Ammi tace"wato Ni zaka juya ma baya ko?saboda ka samu zankaɗeɗiyar budurwa sabuwa gal cikin leda,Ni kuma nayi maka tsufa,"gyaɗa kai tayi tare da cewa"bakomai na haƙura,"

  Murmushi suka saki gaba ɗayansu,mayar da idonta tayi kan Abusufyan"Yanzu ya ake ciki game da zancen Mahaifiyar yaran nan"?

  Jin an sako zancen abu yasa shi gyara zama,sannan yace"Muna nan muna shirya waɗanda zasu je kano domin binciko gidan da suka zauna acikinsa,saboda muna sa ran zamu samu wasu muhimman bayanai a wurin makwabtansu,"

  Jinjina kai Ammi tayi"hakan yayi kyau,banason a tsaya 6ata lokaci nafi son ayi komai tun da wuri don ba'a san halin da take ciki ba,"

  "In sha Allah zamuyi hakan,daga nan suka miƙe tare da yi mata sallama suka wuce ɗakin Modibbo,ba ƙaramin daɗi yaji ba daya gansu,sun jima a wurinshi,kafin daga bisani suka wuce ɗakin gwaggon katsina,sun sha barkwanci a wurinta,daƙyar suka samu tabarsu suka fito,ɗakin hajiya azeema suka wuce,sun jima a wurinta suna shan fira,ɗaya bayan ɗaya haka suka dinga bin ɗakunansu kafin daga bisani,Lokacin yin breakfast yayi suka hallara gaba ɗayansu a dining,kowa saida yazo banda Sgr,saboda yasa ma ranshi cewar za'a kawo mashi ne har part ɗinsa,Azmee ce takai mashi,saboda Sehrish ta sanar da ita cewar,bazata samu damar kai mashi ba,tana so tabi Umarnin mahaifinta ne,


Lokacin da Azmee ta shiga part ɗinsa,yana daga kishingiɗe saman Sofa mai mazaunin mutun ukku,jikinshi na sanye da jallabiya,shigowa ciki tayi gabanta na faɗuwa don tasan cewa dole ya tuhumeta akan me ya hana sehrish zuwa,lalla6awa tayi ta ajiye masa tray ɗin a asaman table,gudun karya tuhumeta yasa tayi saurin ja da baya zata gudu tabar ɗakin,har takai baƙin ƙopar ɗakin tajiyo muryarshi yana fadin"ke zo nan,"dakatawa tayi da tafiyar hannunta dafe da saitin zuciyarta,jiki asanyaye ta dawo ta tsaya agabanshi,kwata kwata idanunshi na a lumshe,wayarshi na ajiye asaman wide chest ɗinsa,

  dakyar ta iya cewa gani yalla6ai,

"Bana ce kar na sake ganinki a part ɗina ba da sunan aiki?ko bata faɗa maki bane"?

  Shiru azmee tayi,tana faman zazzare ido,ranta ne ya bata cewar kawai ta sanar dashi gaskiyar zance,

Don haka tace"Sehrish ta sanar dani cewar bazata ƙara aiki a part ɗin ka ba...."tunkan ta ƙarasa maganar ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu,nan take azmee tasha jinin jikinta,

  "Ita da bakin ta,ta faɗi hakan"?

Muryarta na kerma tace"Eh,

  Ya kuma cewa"ta faɗa maki dalilin yin hakan"?

"Eh,tace tana son bin Umarnin mahaifinta ne,"

   ɗan ciza gefen la66ansa yayi tare da cewa"its Okey,just leave........" da sauri azmee ta juya tare da kama hanya ta fuce daga part ɗin nasa,


Wuraren ƙarfe goma sha biyu modibbo ya shirya tafiya,Kanal yousouf ne tare dasu Irfan suka kai shi har Airpot ya hau jirgi,



Yinin Ranar Aunty babba na ƙumshe a cikin ɗakin Hayaam,tsoro ya hanata fitowa waje,da yunwa ta addabe ta Hayaam ce ta ɗebo mata abinci ta kawo mata a ɗakin,hosana kuwa kar take dasu,don taci alwashin sai ta tona masu asiri wurin daddynsu,da kuma Ya omar,


Hankalin sehrish ba ƙaramin kwanciya yayi ba,jin Cewa sgr bai nemeta ba,duk da ta damu akan son ganinshi,jurewa kawai takeyi,


A ranar Talal Da captain najeeb suka ƙaraso,murna a wurin ƴan uwansu kamar zasu haɗiye su don farin ciki,musamman junaid daya kasance rival ɗinsa ne ya dawo wato Talal,da yake shima autane a ɗakinsu Omar,



After 1 day 



*Boss Bature*


 Around 2:00 pm,


Zaune take a hakimce saman 2 seater,jikinta na sanye da turkish dress Riga da wando,a launin fata fara ce amma hasken nata hada na bleaching tayi 6au sosai,babbar mace ce a ƙalla zata kai shekara 35,gaba ɗaya idanunta na akan plasma tv din da take kallo aciki,yayin da hannunta ke ɗauke da cup na coffee,lokaci bayan lokaci take kur6asa,ta aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,wuyan kafarta na sanye da ziririyar sarƙa,sai faman karkaɗa kafar takeyi,Tana da manyan idanu dara dara,ga dogon hanci wanda ke manne da nose ring,kai kana ganinta zaka san cewar cikakkiyar ƴar bariki ce,

Jin ringing din wayarta dake ajiye asaman hannun kujerar da take ne yasa ta Ajiye cup din hannunta asaman madaidaicin table din dake a kusa da ita,sannan tasa hannu ta dauki wayar,hidden number ce aka kirata da ita,picking call ɗin tayi ta kanga wayar a kunnanta,cikin harshen fulatanci take magana,


Tana cikin yin wayar taga inuwar mutun tsaye akanta,ɗagowa tayi a hankali don taga wanene,sauke ajiyar zuciya tayi ganin Amrish ce,jikinta na sanye da uniform,ta goya school bag dinta a abayanta,dawowarta kenan daga school,fuskarta a ɗaure kwata kwata babu annuri acikinta,


Rejecting call ɗin tayi tare da ajiye wayar asaman sofa din,sannan ta mayar da hankalinta sosai akan Amrish,

  "Welcome back my daughter,Am really glad to see u,"

  Tayi maganar tana buɗe mata hannunwanta don tazo ta rungume ta,rai a6ace tace"Mommy na tsani ganinki wlh,banason ki,saboda baki da halin kirki,so kike ki kashe mun rayuwata da hannunki,"tana maganar hawaye na gangarowa akan fuskarta,

  Maimakon ta nuna damuwarta akan hakan sai ma ɗan ta6e la66anta tare da cewa"Kamar yadda baki so na,Nima haka bana son ki,donni a tsarin rayuwata ban shirya haihuwa ba saboda bana son ƴa'ƴa don su takura ne,na samu cikinki batare dana shirya ba,babu yadda banyi ba don na zubar da cikin,amma ya liƙe ya nace sai ya zauna a mahaifata,a ƙarshe nayi deciding zuwa ƙasar waje a markaɗe mun shi,mahaifinki ya hana hakan,nayi takaici a wannan lokacin kamar nayi suicide,"

  Hankalin Amrish ba ƙaramin tashi yayi ba,jin abunda mahaifiyarta ke faɗi da bakinta,tuni wasu zafafan hawaye suka shiga wankowa a saman fuskarta,cikin shessheƙar kuka tace"ki faɗamun!Su wanene iyaye na!don ina da tabbacin cewar bake kika haife ni ba,"

  Fashewa da dariya matar tayi yayin da take karkaɗa kafafunta,

  Jin tayi banza da ita yasa ta daka mata tsawa tare da cewa"Mommy ki faɗamun su wanene iyaye na?In ba haka ba zan je na kashe kaina!"

  Yunkurawa mommyn tayi tare da mikewa tsaye ta daddage ta kifa ma Amrish mari tare da cewa"Sai me idan kin kashe kanki!?wa kikayi ma asara!shashasha kawai,"

  Fashewa da kuka Amrish tayi yayin da zuciyarta ke tafarfasa tace"Mommy yau ke da kanki kika mare ni"?

  Dogon tsoki taja tare da cewa"Har kashe ki ma zan iyayi,Saboda kinyi mun tsawa,ko iyayena da suka haife ni basu ta6a gigin daka mun tsawa ba,balle ke ƴar dana haifa,idiot"

  Ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta ɗauki wayarta,sannan tabar falon tana fadin"kafin gobe in samu gawarki dan Allah,"tayi maganar cikin halin ko in kula,

  Da gudu Amrish ta watsa,izuwa bedroom dinta dake a upstairs,datse ƙopar ɗakin tayi,bayan tayi wurgi da school bag dinta,ta shiga neman igiyar da zata shaƙe kanta don ta mutu,ganin bata samu ba yasa ta buɗe kopar ɗakin,ta fita,bada jimawa ba sai gata ta dawo cikin ɗakin hannunta dauke da insect powder,buɗe murfin tayi da sauri sauri ta daga robar tare da zazzagawa acikin bakinta,


Mommyn na acikin bedroom ɗinta,ta jiyo wata irin razananniyar ƙara mai rikitarwa,sakin wayar dake hannunta tayi,da gudun gaske ta fito daga bedroom ɗinta dake a downstairs,tamkar za tayi tuntu6e ta fadi kasa haka take gudun,lokacin da ta ƙarasa bedroom din Amrish,hannu tasa ta dinga bubbuga ƙopar tana faɗin"AMRISH!AMRISH!!baki da hankali ne,bakisan wasa ba,me kika aikatawa kanki!ba zaki zo ki buɗe mun ƙopa ba!!Amrish gaba daya duk tabi ta rikice,

  Shiru amrish bata buɗe mata ƙopar ba,hakan yasa ta dawowa wurin window ɗin ɗakin ta buɗe ta don ta gane ma idonta,

  A gigice ta fasa uwar ƙara tare da aza hannyenta asaman kanta tana fadin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!na shiga uku!!!!zubewa tayi ƙasa saman guiwowinta tana faman zabga kuka,hawaye jaga jaga a fuskarta,tana cikin wannan yanayin,taji shigowarsu Zeenat da sofia ƙawayen Amrish cikin falon gidan,mikewa tayi da sauri har tana tuntu6e ta saukko downstairs,tunkararsu tayi tana fadin"Nashiga uku!!Amrish ta kashe kanta!!bansan ya zanyi da rayuwata ba!!

  Kallon juna sukayi hankalinsu a matukar tashe suka haɗa baki wurin cewa"Am...Amrish!!meya faru da ita!taya akai ta kashe kanta!!!

  Kasa bude baki tayi don tayi masu magana,da hannu ta dinga nuna masu bedroom ɗinta,nan suka gane cewar tana acikin ɗakinta,da gudu suka nufi upstairs ɗin,itama tabi bayansu,nan fa suka shiga ƙoƙarin 6alle ƙopar ɗakin nata,

[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋 Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




               ❤🤍❤


Daƙyar suka samu ƙopar ta buɗe nan suka same ta a kwance rai hannun Allah,wani irin ruwan kumfa kumfa ne ke fitowa daga bakinta,gaggawar ɗaukarta su kayi,su biyu suka cuccu6eta sai cikin motar Mommyn,da kanta tayi driving ɗin motar,yatsun hannunta nata kerma tana yi tana dan bugun steering,Su zeenatu kuwa dake a back seat na motar,sae kuka sukeyi suna jijjigata don karta mutu basu isa asibitin ba,



Suna ƙarasawa asibitin,da sauri suka cuccu6eta suka shiga da ita mommyn na fadin"Emergency pls doc,nurse....!"reception Nurses ne suka kar6eta da sauri da sauri suka shiga da ita ɗaki,anan aka kwantar da ita,doctors suka taru a kanta.


Zama sofia da Zeenatu su kayi asaman waiting seat,yayin da Mommyn Amrish ke ta faman zarya a corridor din,jikinta sai faman kerma yake yi,sam bata ta6a tunanin cewa Amrish zata iya yunkurin kashe kanta ba sai yau da ta tabbatar mata,tasha faɗin cewa zata kashe kanta in bata faɗa mata wanene mahaifinta ba,bata ta6a ɗaukar abun serious ba,sae yau,ta tsorata da irin hukuncin da Amrish ta yanke wa kanta,

  "Mommy wai meya faru ne?Nasan cewa Amrish bazata ta6a yunƙurin kashe kanta ba,batare da anyi mata wani abu daya 6ata mata rai ba!"

Zeenat ce tayi maganar,yayin da idanunta ke fitar da hawaye,

  "Ni banyi mata laifin komai ba,kan dai maganar nan ce da take yawan faɗamun na cewar ta tsane ni bata sona,in faɗa mata su wanene iyayenta ko ta kashe kanta,ta 6ata mun raine yau saboda tayi mun tsawa shiyasa na kwashe ta da mari sannan nace taje kafin gobe in samu gawarta,shine fa ta fusata har ta aikata hakan,"

   Cikin shessheƙar kuka zeenat tace"meyasa ba zaki iya lallashinta ba?saboda me zaki sa hannu ki mare ta?kuma kika furta mata cewar taje ta kashe kanta bayan kinsan cewa ita yarinyace ba wayau tacika ba,yanzu gashinan kinja zamu rasa ta gaba ɗaya"cike da takaici Zeenatu ta ƙarasa maganar tare da komawa saman waiting seat ɗin ta zauna tare da kifa kanta saman laps ɗinta tana cigaba da matsar kwalla,hannu sofia tasa tana ɗan bubbuga bayanta,ɗagowa tayi da idanunta waɗanda suka rune jawur dasu,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Mommy yakamata ki sanar da yayanta halin da ake ciki,tun kafin rai yayi halinsa,"

   A tsananin tsorace Mommyn tace"bazan sanar da kowa ba,idan ma ta mutu bazan bari wani ya sani ba,guduwa kawai zanyi in yaso daga baya sunji labari,don wlh bazasu ƙyaleni ba,"

  "Saboda me kika ce haka mommy"?

"Zeenat mubar zancen kawai,ni kaɗai nasan halin da nake ciki,"tayi maganar tare da kifa kanta jikin bangon da take tsaye,

  Jikinsu ba ƙaramin sanyi yayi ba,

"Amma mommy meyasa kike 6oye mana abubuwa da dama game da Amrish?har yau bamu ta6a ganin mahaifinta ba,bayan wannan bamu ta6a ganin wani acikin dangin ku ba,sae mutun ɗaya kawai,yayanta dake zuwa wurinta ...."

  Kasa ƙarasa maganar tayi saboda ganin irin juyowar da mommyn Amrish tayi a ruɗe,la66anta har rawa sukeyi wurin cewa"Kar na kuskura na ƙara jin kinyi mun wannan maganar!baida amfani sanin wanene mahaifin Amrish!Ni ɗin nan ni ce Mahaifinta kuma ni ce mahaifiyarta!!

  Shiru sofia tayi,batare da ta ƙara cewa Komai ba,,,,,,,,


Ranar dae A asibiti suka yini har dare ya ritsa dasu,


*Boss Bature*

    

     ❤🤍❤


Fitowarsa kenan daga cikin toilet jikinshi na sanye da bathrobe,hannunsa kuma na ruƙe da short towel yana ɗan matse sumar kanshi,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga jikinshi,tamkar wanda aka tsamo daga ruwan turare,saboda ƙamshi,gaban dresssing mirror ya tsaya yana ƙarasa tsane sumar kan tashi,ɗan dakatawa yayi tare da wurga eye balls ɗinsa ta cikin mirror yana kallon Shimfiɗeɗen gadonsa,bedsheet ɗin duk yayi  squeezing,ga blanket ɗinsa dake a cukurkuɗe saman gadon,komai ya hargitse ba don komai ba sai don rashin mai gyara,2 days kenan ba'a gyara mashi part ɗinsa ba,a ƙa'ida duk rana sai an canza mashi bedsheet da Blanket amma yau har 2 days ba'a musanyasu ba,mutun ne shi mai tsaftar gaske,ga ƙyanƙyami,gashi ko kaɗan baijin zai iya ɗaga yatsanshi da sunan zai gyara bed ɗin nasa,ba don komai ba,sae don saboda kasancewar shi mutun mai matuƙar Ji da kanshi,a wurinshi wannan tamkar ƙasƙanci ne da matsayinshi ya zuƙunna da sunan zai gyara bedroom ɗinsa,tamkar ƙaskanci ne namiji yayi aikin da mace ya dace tayi shi,ko ba don wannan ba shi tun yana yaro ko tsinke wannan acikin gida kawar masa shi akeyi,sam bai iya aikin gida ba,wanka ne kawai yakeyi ma kanshi,amma da zarar ya fito daga toilet akwai masu taimaka mashi wurin yin dressing na Outfits ɗin da zaisa,


Yana cikin tsayuwar nan,Yaji sallamar Azmee daga cikin palour ɗinsa,bai amsa mata sallamar ba,hannu yasa tare da ɗaure igiyar Bathrobe ɗinsa sosai,sannan ya juya tare da nufar ƙopar fita daga bedroom ɗin,adai dai bakin ƙopar ya tsaya tare da goya hannayenshi asaman wide chest ɗinsa,


Azmee kuwa tunda taga ya fito gabanta ya shiga faɗuwa,dama zuwa tayi don ta gyara mashi part ɗinsa,

  "Where's she"? Ya tambaya batare da ya aza eyes ɗinsa akantaa ba,

  Tunda ya ambaci hakan ta gane cewa akan sehrish yake magana,don haka tace"Tana a bedroom ɗinsu,"

  "Okey,call her right now,"

Yayi maganar cike da bada Umarni sannan ya juya tare da shigewa cikin bedroom ɗinsa,.  

  Juyawa Azmee tayi da sauri ta fuce daga part ɗin nasa,downstairs ta saukko kai tsaye ta nufi ɗakinsu Sehrish,hannu tasa tare da knocing ƙopar,a lokacin duk sunyi nisa acikin baccinsu,can cikin bacci Sehrish taji bugun ƙopar ɗakin nasu,buɗe idanunta tayi a hankali sunyi mata nauyi saboda wani irin bacci da take ji,jikinta a kasalance ta yunƙura daƙyar ta sauko daga saman gadon ta buɗe ƙopar tana tambayar wanene,


Tunda taga Azmee taji gabanta ya faɗi rass,duk da batasan meya kawota ba,

"Aunty azmee lafiya?tayi tambayar tana yin hamma,

Azmee tace"ina fa lafiya,Sgr ne ke son ganin ki,yace in kira mashi ke yanzun nan"

Daram taƙara jin gabanta ya faɗi,"nashiga uku ni yau,"ta faɗi hakan tana yarfa hannu,

   "Yakamata kiyi sauri kije tun kafin ya hasala,don da alama yau ranshi a 6ace yake,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta bar ƙopar ɗakin nasu,

  Jiki a sanyaye sehrish ta koma cikin bedroom ɗin nasu,gaban wardrobe taje,ta buɗe ta ɗauko mayafi ta yafa shi asaman kanta,kayan bacci ne ajikinta,


Fitowa tayi daga ɗakin,ƙafarta na sanye da slipper,tana tafiya cike da zullumin me zai biyo baya,ba komai take hangowa ba face tafin hannun Sgr,ya wanka mata mari,har runtse ido takeyi saboda ganin abun take kamar dagaske,tana ƙoƙarin giftawa ta babban falon ta wuce sama,kwatsam Abusufyan ya fito daga bedroom ɗinsa ya hango gifcinta,tsayawa yayi yana ƙare mata kallo daga inda yake,jinjina kanshi yayi tare da lalla6awa yabi bayanta,cikin sanɗa batare da ta sani ba,

  Hayewa tayi saman stairs ɗin,sannan ta wuce part ɗinsa,bakinta ɗauke da sallama ta shiga ciki,babu kowa a falon nasa,tsayawa tayi a tsakiyar Sofas ɗin,don bazatayi gangancin shiga bedroom ɗinsa ba,ƙwara daganan idan taga ya harzuƙa ta watsa da gudu,amma in can ciki ne zai iya kama ta,

  Tana cikin tsayuwar nan zuciyarta na ɗar ɗar,taji motsinshi da sauri takai idanunta kan ƙopar bedroom ɗinsa,gabanta ne ya faɗi rass ganin shi a tsaye,hannunshi ɗaya ruƙe da waist ɗinshi,yayin da yake sanye cikin sleeping dress white color ba ƙaramin kyau su kayi mashi ba,Amma fuskar nan fa babu annuri ko misƙala zarratin,

  Da hannu yayi mata alamar tazo,hakan yasa ta nufi wurinshi ɗan nesa dashi ta tsaya sannan tace"Gani,"

Hakan da tayi ba ƙaramin 6ata mashi rai yayi ba,maimakon tazo kusa dashi saita tsaya nesa dashi,

   "Ni kike so in ƙaraso inda kike"!?

Girgiza kai tayi alamar a'a,jinjina kanshi yayi tare da matsa mata hanya yace"shiga ki gyara mun bedroom ɗina,"

  kasa motsawa tayi saboda alƙawarin da ta ɗaukarwa kanta na cewar bazata ƙara zuwa part ɗinsa ba,da sunan yin aiki,saboda umarnin mahaifinta,

  Ja da baya ta ɗanyi tare da girgiza mashi kai gabanta na faɗuwa ga tsoro amma ahaka ta daure ta cije tace"daddy ya hanani,"

Wani irin kallo da yayi mata ita kanta saida ta girgiza,tausasan la66ansa har kerma sukayi wurin furta"Ni kike faɗama cewa Daddy ya hanaki"?

..shiru tayi tana faman zare ido,hakan ya ƙara fusata shi,gadan gadan ya tunkarota,ƙoƙarin juyawa tayi amma ina kafin tayi wani yunƙuri tuni ya ruƙo mayafinta nan take ya zame ƙasa,kwakkwaran damƙa yayi ma gashin kanta,hakan yasa tayi screaming saboda Zafin da taji,

  Jijjiga kan nata yayi,tamkar wata Ƴar babyn roba haka ya ɗaga ta gaba ɗayanta da hannu guda,kuma ta hanyar gashin kanta daya damƙa,wutsil wutsil tashiga yi da ƙafafunta,hawayen azaba na gangarowa akan  fuskarta,fashe mashi da kuka tayi  muryarta na rawa ta shiga faɗin"Wayyo Allah na!Babban yaya dan Allah kayi haƙuri ka sauke ni ƙasa,wlh bazan ƙara ba,zan gyara maka ɗakin,'

  Zuba mata ido yayi yana kallonta tun daga ƙasa har sama,wata ƴar ƙarama da ita,mamakinsa a ina ta samu ƙwarin guiwar gaya masa magana batare da jin shakkarshi ba,

  "Babban yaya dan Allah ka sauke ni!Wayyo Allah da.. daddy,nashiga uku,zai kashe ni,gashin kaina zafi,zai cire mun gashina,"saboda tsabar kuka hada majina,fuskarta tayi jaga jaga da hawaye,sai da ta galabaita sosai sannan ya saki gashin kan nata,gaba daya ta zube saman guiwowinta saboda jikinta da ba ƙwari,

     Zura hannayenshi yayi acikin aljihun dogon wandon dake ajikinsa,sannan yace"Tashi ki shiga ciki,ki gyaramun bedroom ɗina"

  Jikinta na kerma ta miƙe da sauri da sauri ta tunkari ɗakin nashi tana faman shessheƙar kuka,tana ɗaga ƙafarta zata shiga ɗakin taji an dakatar da ita,

  "Karki kuskura ki shiga ɗakin nan"!!!! Rass taji gabanta ya faɗi jin Muryar daddynsu,a firgice ta juyo don ta shaidawa idanunta,

  Shigowarshi kenan cikin palourn yayi maganar,a wani sukwane Sgr ya wurga eye balls ɗinsa akanshi,takawa yayi har zuwa gabanshi ya tsaya suna Facing ɗin juna,sannan yace"meyasa kake son takura rayuwarta ne?yarinyar nan ba ƴar aiki bace,ƴata ce!kuma ni ne na bata Umarnin cewa ta daina aiki acikin gidan nan!akan me kakeso ta fifita Umarninka akan na mahaifinta?matsayinmu ɗaya ne a wurinta ne"? 

Wannan maganar ta Abusufyan ba ƙaramin Fusata shi tayi ba,Yadda kasan zaki haka ya shiga fitar da huci ta hancinsa,ya ma rasa amsar da zai ba Uncle ɗin,saboda zuciyarshi da ta hasala,don har bugu zai iya kai mashi,muryarshi na kerma yace"Un...cle!Are u telling me dat matsayinmu ba ɗaya ba a wurinta!"jinjina kanshi ya shiga yi yana fama ciccije la66ansa,ran manya ya 6aci,yaci gaba da cewa

  "Of course our position is not the same,but she's my younger sis,ina da right ɗin da zan sanyata aiki tayi mun,why kake so kajamin raini a wurinta"! daƙyar voice ɗinshi ke fita saboda tsabar 6acin rai zuciyarshi har wani tafarfasa takeyi,

  "Ba raini nakeso naja maka ba a wurinta!tabbas ƙanwarka ce ita halak malak,kuma kana da ikon da zaka sanyata abu tayi maka,wannan gaskiya ne,amma Ni mahaifinta na hana haka!ban amince ba,tayi aiki a ƙarƙashin kowa ba,Azmee itace mai aikin gidan nan!ita yakamata ace tana yin duk wani aikin daya dace,idan ma Aikin azmeen ke baka so,Zan iya sawa a ƙaro wasu masu aikin da zasu rika yi maka,amma ba ƴa taba,saboda ita ba ƴar aiki bace......"tunkan ya ƙarasa maganar Sgr ya daka mashi wata irin gigitacciyar tsawa,a tsiwace yasa hannu tare da toshe ears dinsa yana faɗin"ENOUGH!Enough!banason ji,banaso,she must execute my Command,that's may final say" ya karasa maganar yayin da idanunshi ke aruntse ruff ya rufesu

  Abusufyan yayi ma tsawar,amma gigitar da sehrish tayi,tamkar zata zauce,ƙanƙame jikinta tayi,cike da fargaba,

   Zuba mashi ido abusufyan yayi yana kallonshi,a hankali ya zame tafin hannayensa daga toshe kunnuwansa da yayi,a hankali ya ɗan ware blue eyes ɗinsa,tare da juyawa ya kalli wurin da Sehrish ke tsaye a ƙopar ɗakinsa yace"Wuce ciki ki gyaramun bedroom ɗina"!babu wasa a fuskarshi yayi maganar,wannan ƙarfin halin na Sgr ba ƙaramin mamaki yaba Abusufyan ba,a tsananin tsorace ta wurga idanunta kan daddynsu don taji me zaice,

   "Karki kuskura ki sanya ƙafarki a ɗakin nan!idan har na isa dake"!!wannan shi ake kira da tashin hankali,zazzare idonta tayi tana kallonsu,ta rasa Umarnin wa zata bi,A zarihi dae tafi tsoran Sgr,a baɗini kuwa tafi son tabi umarnin mahaifinta saboda sanin matsayin da yake dashi a wurinta,sa6a mashi zai iya haifar mata da gagarumar matsala a rayuwarta,haka zalika sa6ama sgr ba ƙaramar matsala zaija ma kanta ba,ta rasa inda zata tsayar da kwayar idonta,idan ta kalli Sgr sai ta kalli abusufyan,kowannansu ita yake kallo,daga ganin fuskar Abusufyan zaka san cewar hankalinsa ba a kwance yake ba,babban abunda yake fargaba shine Sehrish taƙi bin Umarninsa,duba da yadda ta gaza motsa jikinta,tabbas zai kunyata sosai kuma darajar da yake da ita ta mahaifinta zai zube ne a idon sgr,zai cigaba da ganin kanshi ne amatsayin Sarki,wanda ke bada Umarni kuma dole abi, 

  Wata irin tsawa sgr ya daka mata,wadda har sai da jikinta ya girgiza sosai tabi ta rikice,a fusace yace"won't u go in!"

  Yana rufe bakinsa,Abusufyan yace"idan har kika kuskura kika shiga ciki,zan yafe ki ne acikin ƴa'ƴana,babu ni babu ke!"

  Jin wannan maganar yasa ta fashe da matsanancin kuka,baiwar Allah tana a cikin tsaka mai wuya,yarfa hannunta tashiga yi tana faɗin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un Ya Allah ka kawomun ɗauki!daddy!!babban yaya!!bansan ya kukeso inyi da kaina ba!!dan Allah ku ƙyale ni!kubarni in ba haka ba zuciyata zata iya bugawa in mutu,"

  Tuni jikin Abusufyan yayi wani irin sanyi,idanunshi suka cika tab da hawaye,tsananin tausayinta ne ya kamashi,kamar yaje ya rungumota ajikinshi ya lallasheta,Amma yaci alwashin cewa bazai ta6a bari Sgr yaci nasara akanshi ba,

  A 6angaren Sgr kuwa,ya gama hasala tunda yake a rayuwarshi bai ta6a bada umarni aka tsaya yi mashi jayayya ba sai yau,sau ɗaya yake bada command kuma dole abi batare da anyi mashi musu ba,runtse idanunshi yayi tare da tura yatsun hannayenshi cikin sumar kanshi yana cakuɗata,yayin da yake ɗan cizon lips ɗinsa,wani irin huci ke fita daga hancinsa,wannan ɗabi'arsa ce aduk lokacin da ranshi ya 6aci sosai,steps uku ne matakin hauhawarshi,idan yakai step na ƙarshen the most dangerous kenan don tamkar aljani yake komawa kuma kowaye gabanshi bai gani tamkar makaho yake komawa,a wannan step ɗin idan ya damƙi mutun a hannunshi yana bugunshi sae yaga gawarshi,kuma babu mai iya control ɗinsa har sai lokacin da Allah yasa zai dawo hayyacinsa,amma zaiyi wuya yakai wannan step ɗin sai in ya damƙi mai laifi zai hukunta shi,iya step na biyu yake tsayawa,mataki na farko shine zaka ga yana huci yana zagaye wuri,na biyu kuma Shine yake cizon la66ansa sosai,ya runtse idonshi ya kuma cusa yatsun hannunshi acikin sumar kanshi yana faman sakin huci tamkar mayunwacin zaki,


Jini ne ya shiga ɗiɗɗigowa daga saman pink lips ɗinsa hakan ba ƙaramin tayar ma sehrish da hankali yayi ba,ita da bata saba ganin yana yi ba,Abusufyan kuwa hankalinshi kwance saboda yasan sgr sarai tun yana yaro yasan shi da wannan baƙar zuciyar,idan ya cije la66ansa har sai ya fasa su,

   Fashewa ta kuma yi da wani sabon kukan cikin shessheƙar kuka tashiga cewa"Dad..ddy dan Allah ka ce mashi ya daina,yana fasa la66ansa da kanshi,!"Shi yake fasa la66ansa amma raɗaɗin ita take jinshi ajikinta saboda tsabar ƙaunar da takeyi mashi,

  Da wata irin murya ya kuma cewa"ki wuce ciki nace,karki bari na ƙara maimaita maki hakan!" saboda tsabar ruɗu ta juya zata shiga ɗaƙin,aikuwa abusufyan ya daka mata tsawa,a ruɗe ta juyo tana kallonshi yayin da hawaye ke fita a idanunta,hanya ya nuna mata da hannunshi yace"Zoki wuce"

  A tsorace take kallon Sgr wanda idanunshi ke arufe,sosai ya runtse su,ganin haka yasa tayi tunanin watsawa da gudu tabar ɗakin don tabi Umarnin mahaifinta,tasan cewa kafin ya buɗe idanunshi tabar falon,

  Daddagewa tayi da gudun gaske ta watsa aguje ta nufi hanyar fita daga falon,sae dai ina kafin ta ankara sgr ya zabura a hargitse yabita,abusufyan na ƙokarin taroshi aikuwa yayi wurgi dashi gaba ɗaya,yayi gefe guda ƙasa,A zafafe ya damƙi waist ɗinta,wani irin ruƙo yayi mata ruƙo bana wasa ba,ya ɗaɗɗagota sosai ya manna ta da jikinshi,bedroom ɗin shi ya nufa da ita,wannan ƙarfin halin har ina,ran abusufyan ba ƙaramin 6aci yayi ba,miƙewa yayi da sauri ya tari Sgr kiciniyar kwace Sehrish ya shiga yi da hannunshi,nan fa suka kacame ma juna,

  "Subhanallahi me nake gani haka"!!muryar Abba ce ta karaɗe kunnuwansu,gaba ɗaya suka juyo kowa na huci suna kallonshi,a lokacin Sgr ya saki sehrish daga hannunshi,da gudu ta miƙe tana kuka,ta nufi wurin Abba,gaba daya ta faɗa jikinshi,rungumeta yayi yana ɗan bubbuga bayanta,yayin da idanunshi ke akan Sgr da Abusufyan,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,yadda sgr ya manta wanene abusufyan a wurinshi,har yake ƙoƙarin yin dambe dashi,hauka maganinka Allah,


"Abusufyan da hankalinka kake kokoyi da Rafayet kamar wasu tsararrakin juna?duk akan menene kuke wannan faɗan"?

  Yayi tambayar tare da mayar da idanunshi kan Sgr wanda ke tsaye har lokacin sama yake bai sakko ba"Rafayet ka bani mamaki!ka rasa dawa zakayi dambe sae Kawunka,ƙanin mahaifinka!Anya baka fara shaye shaye ba?nafara zarginka," afusace ya juya tare da shigewa cikin bedroom ɗinshi yaja ƙopa ya rufe,


"Bansan me rafayet ya ke ɗaukar kanshi ba,Taya zan ba yarinya umarni A matsayina na mahaifinta sannan yace dole saita take umarni na don tabi nashi?saboda haka fa ya ke ƙoƙarin buguna sai kace wani tsaransa"da alama ran abusufyan ya 6aci sosai,yana maganar yana nufo inda su Abban suke tsaye shi da sehrish,hannunta na ruƙe cikin na abban,wani irin zazza6i ne ya rufar mata mai zafin gaske,ga ciwon kai mai tsanani da take fama dashi,duk don saboda tashin hankalin da suka jefa ta ciki,kuma har lokacin kukan take yi,


Sam Abba baiji daɗin abunda ya faru ba,"kayi haƙuri Abusufyan abunda yayi bai kyauta ba,duk da ba laifinsa bane irin rayuwar da aka saba mashi da ita kenan tun yana yaro,komai yi mashi akeyi,kuma in ya bada Umarni bi akeyi duk don tsoran kada ranshi ya 6aci,"

Gyaɗa kai kawai Abusufyan yayi tare da cewa"babu komai,Ae nasan halinshi sarai shiyasa banji zafin abun sosai ba,inayi mashi uziri ne,"

   Ya ƙarasa maganar tare da kallon sehrish wadda ke ta faman matse kwalla,suna haɗa ido dashi ta sunnar dakai ƙasa,

  "am really sorry my daugher,banyi hakan don na 6ata maki rai ba,"

Cikin shessheƙar tace"Ammm..ma daddy,cewa fa kayi zaka yafe ni acikin ƴa'ƴanka,idan har nabi umarninsa,"

   Murmushi ya ɗan saki akan fuskarshi kafin yace"wasa fa nake maki,banda hankali ne,ae koda ace kin bi umarnin nasa bazan faɗi hakan ba,zan dai ji ɗaci araina,na faɗi hakan saboda ina gudun ki ƙi bin Umarni na,"

  "Daddy nidai banason wannan wasan,dan Allah kada ka ƙara faɗamun hakan," yadda tayi maganar ba ƙaramin dariya yaso ya basu ba,don har sai da ta bubbuga ƙafafunta ƙasa,don ya tabbatar da cewar bataso,

  "In sha Allah bazan ƙara ba,kinyi haƙuri ko"?

  ɗaga mashi kai tayi alamar Eh,

"Wato kun sasanta tsakaninku,ni kuma kun barmun yaro na,cikin wani hali ko"?Abba ne yayi maganar cikin zolaya,hada ɗaure fuskarshi,

  Abusufyan yace"Yaya ai kai kaɗai kasan yadda zaka shawo kanshi,don yanzu duk wanda yayi gigin zuwa wurinshi,ba ƙaramar matsala za'a samu ba,"

Murmushi Abba yayi kafin yace"Shikenan zanje in lallashi abuna,kai kuma kaja ƴarka ku wuce ku bamu wuri,"

  Hannun Sehrish Abusufyan ya ruƙe,tare da janta suka bar part ɗin yana dariya,


  A bakin ƙopar bedroom ɗinsa ya tsaya cike da zullumin taya zai shawo kan sgr,hannu yasa yayi knocking ƙopar,shiru Sgr bai buɗe masa ƙopan ba,hannu yasa ya ƙara knocking ɗin ƙopar yana kiran sunanshi"Rafayet!ka zo ka buɗe mun ƙopa,inason magana dakai,"shiru bai ji motsinshi ba,babu alamun zai buɗe masa ƙopar,kwantar dakai abba yayi ajikin ƙopar cikin lallashi ya soma magana"haba rafayet ɗina,ni fa ne abbanka,so kake yau in gaza runtsawa?idan har bakazo ka buɗe mun ba anan zan kwana,"ya ƙarasa maganar tare da zuƙunnawa ƙopar ɗakin nashi,abu kamar wasa ya fara gyangyaɗin bacci,duk in ya ɗan farka sai ya ambaci sunan Shi Rafayet ka buɗe mun ƙopa,so kake na kwana anan?


Duk wannan surutan da Abbansu ke yi kaf a kunnan sgr,wanda ke zaune saman front chair na dressing mirror ɗinshi,ya kifa kanshi asaman Dressing mirror,gaba ɗaya sumar kanshi ta rufe mashi side by side na fuskarshi,zuciyarshi ba ƙaramin tafarfasa take mashi ba,ranshi yayi mugun 6aci wai har shi zai bada Command aƙi bin umarninsa?bakowa yafi ji ma haushi ba fa ce Uncle ɗin nasu,don me zaiyi iko da Sehrish?saboda kawai ya haifeta?wani irin huci ne ke fita akanshi tabbas sai ya nemi matsayin dake asama dana mahaifinta ba don komai ba sai don yayi iko da ita,akan idon mahaifinta kuma,

  Yana cikin yin wannan zancen zucin yaji Muryar Abbansu kamar ta wanda yasha giya,saurarawa yayi yana sauraron waƙar da Abbansu ke rera masa daga waje,tun yana yaro idan aka 6ata mashi rai,ya fusata da gudu yake shiga bedroom ɗinsa ya rufe ƙopa,idan abbansu naso ya sauko daga fushin da yake yi sai yazo ƙopar ɗakinshi yana kwankwasawa yana raira masa waƙa,cikin ƙankanin lokaci yake saukowa daga wannan fushin,

  Jikinshi ba ƙaramin sanyi yayi ba,ɗan ɗagowa yayi da kanshi ya wurga eyes ɗinshi kan agogon bangon dake a manne ƙarfe kusan ɗaya na dare,Abbansu na waje yaƙi tafiya,kuma in har bai buɗe mashi ƙopar nan ba,to anan wurin zai kwana,saboda ya ta6a yi mashi haka,miƙewa yayi jikin shi babu ƙwari ya ƙarasa tare da jan ƙopar ya buɗe mashi,jin an buɗe ƙopar yasa Abbansu miƙewa jiki na rawa,suna haɗa ido da sgr,yasa hannunshi a idanunshi yana yi mashi kukan ƙarya wai ya barshi a waje,sanyi ya bugeshi,hakan da yayi ba ƙaramin dariya yaso ya ba Sgr ba,

    Juyawa Sgr yayi tare da shigewa cikin bedroom ɗin,abban yabi bayanshi,a gefen gadon suka zauna suna fuskantar juna,

  "Yanzu faɗamun,me yake damunka"?

Shiru ya ɗanyi tamkar bazai tanka masa ba,daƙyar ya iya buɗe bakinshi yace"Abba,Uncle ya gama dani!har ni zan ba yarinyar can Umarni,ya hanata,don kawai yana taƙamar cewar shi mahaifinta ne"?yana magana muryarshi na shaƙewa saboda tsabar 6acin rai,

  "Rafayet!ni bansan me zance maka ba,ka san dai inason farin cikinka,duk wani abu da kake so ni mai iya yi maka shi ne,amma banda wannan!zan iya iko da Abusufyan amma bazan iya iko da ƴarsa ba,shi mahaifinta ne dole tabi Umarninsa tayi mashi biyayya,bijire mashi zai iya sa ta fuskanci matsala arayuwarta....."

 Bai ƙarasa maganar ba Sgr yace"That means ba wanda ya isa yayi iko da ita sai shi kawai?kenan Ni bani da wani matsayi a wurinta?bamu isa mu sata abu ba tayi kenan?

  Jinjina kai abbansu yayi tare da cewa"Hakane!maganar gaskiya babu wanda ya isa yayi iko da ita a halin yanzu bayan mahaifiyarta sai kuma shi"

  "Abba babu wani sama dasu wanda zai iya iko da ita fiye da mahaifanta"?yayi maganar ranshi a ɗan 6ace yana kallon Abban nasu,

   Gyara zama abbansu yayi,fuskar nan tashi ɗauke da wani 6oyayyen murmushi yace"duk duniyar nan bayansu mutun ɗaya ne!wanda zai iya yin iko da ita,fiye da iyayenta!'

   "Wanene shi"?ya tambaya Yana jiran jin amsar da Abban nasu zai bashi,

   "MIJINTA,shine wanda zai iya yin iko da ita fiye da iyayenta!Mahaifinta zai iya kiranta tazo gida mijinta ya hana,kuma dole ta hanu,ko tana so ko bataso,"

  Hannu Sgr yasa tare da dafe gefen kanshi,yana faman sauke ajiyar zuciya,muryarshi ƙasa kasa yace"Abba!babu wata hanyar sai wannan"?

  Jinjina kai Abbansu yayi tare da cewa"that's the Only solution,"!

    Ya ƙarasa maganar yana kallon fuskar SGR,Acikin zuciyarshi kuwa Allah Allah yake akan ya amince zai auretan,Shikenan burinshi zai cika ganin cewa Rafayet yayi aure,

   "She's too young for me,Ni bazan iya auren yarinyar da ko Secondry school bata kammala ba,wannan abun kunya ne agare ni,da matsayi na in aureta?da wani ido duniya zata kalleni"?

   Zuru Abbansu yayi yana sauraronshi,wato Sgr har yanzu yana nan da wannan ji da kan nashi,

  Hannu Abbansu yasa tare da dafa shoulder ɗinshi sannan yace"Rafayet!nima ban goyi bayan hakan ba!idan har ka aureta girmanka zai faɗi ne!Amma ga wata shawara"?

  ɗan ɗagowa yayi da idanunshi masu ɗauke da bacci ya kalli abban nasu"Wane shawara ne wannan"?muryarshi a akasalance yayi maganar,

  Abba yace"Me zai hana kuyi auren yarjejeniya atsakaninka da ita yarinyar"?

    "Kamarya kenan"?

 Ƙayataccen murmushi Abbansu ya saki yana kallonshi kafin ya ɗaura da cewar"Wata nawa ya rage maku ku koma U.S"?

   "Remain 3 Months,"ya bashi amsa,

Abba yace"Yawwa,before 3 months ɗin nan su cika,me zai hana ka aureta,a matsayin Contract marriage,don tayi maka aiki kawai na tsawon wata uku,kamar yadda kake so da zarar time ɗin ya cika,kawai saika bata divorce letter ɗinta,Amma ya kake gani"?

  Shiru Sgr ya ɗan yi yana nazarin maganar Abban nasu,kafin yace"Abba bacci nake ji,i will think about it before tomorrow,"

  "Ba damuwa,kafin gobe dae yakamata kayi tunanin abunda ya dace,zan jira jin amsarka da safe," ya ƙarasa maganar tare da juyawa ya fuce daga ɗakin nashi,

  Blanket ɗinsa yaja ya lullu6e jikinshi har zuwa neck ɗinsa,maganar Abbansu ce ke tayi mashi yawo acikin kanshi,ga bacci yana ji amma yaƙi ɗaukarsa,sae faman juyi yake yi asaman gadon,tabbas in ya aureta zaici galaba akan Uncle ɗinsu Abusufyan,yana so ya dinga commanding ɗinta akan idon mahaifinta kuma ba yadda zaiyi dashi,na biyu kuma Yana so yarinyar taci gaba da aiki a ƙarkashin ikonshi,har zuwa lokacin da zai koma U.S!!idan har yana so hakan ya faru kenan dole sai ya aureta!?OMG!


  "That could not be possible for me as a Surgeon General to marry a young girl who has not even finished her secondary school,"ya furta hakan tare da jan blanket dinsa ya rufe fuskarshi  daƙyar bacci 6arawo yayi awon gaba dashi,


*Boss Bature*


Saukowa down abba yayi fuskar nan tashi ɗauke da murmushi,anan ya samu abusufyan tsaye yana jiranshi,yana ganin ya tunkare shi,

  "Ina sehrish ɗin take ne"?

Abusufyan yace"Tun ɗazu ta wuce ɗakinsu,Nima kai nake jira muyi sallama kafin inje in kwanta,Amma ya kuka ƙare da rafayet ɗin?ina fata dai ya sauko daga fushin nan nashi"?

Fuskar abba ɗauke da murmushi yace"daƙyar na shawo kanshi,yanzu haka ma ya kwanta,sae kayi haƙuri da surukin naka,"

  Dariya abusufyan yayi kafin yace"ae ni bansan ya zamu ƙare da rafayet ba,lamarin ya fara bani tsoro,ƙoƙarin buguna fa yake yi ne?ahaka zan zama surukinsa?yana yi mun kallon tsaransa?Lokacin dana shiga ɗakin nasa samun shi nayi fa ya damƙi gashin kanta ya ɗaga ta sama kamar wata ƴar babyn Roba,yarinya sae kuka take tana bashi haƙuri amma ko ajikinshi,"

   Abba yace"Ae rafayet sae addu'a,amma abun nashi ƙara gaba yake yi,yana ji Da ƙarfin nan nasa,bakowa zai iya jure zama dashi ba," suna tafiya suna fira har suka zo ƙofar ɗakin Abba,anan su kayi sallama da abusufyan ya wuce nashi ɗakin,

   Fuskarshi a washe ya shiga ɗakin kamar ance ya ɗaga idanunshi karaf suka sauka akan Junaid dake baje saman gadon yana bacci,ga Mommynsa agefe,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,daga fitarsa har ya shigo ɗakinshi,Anya kuwa junaid shi kaɗai ne?yaro kamar mai iska,har leƙa ɗakinshi yayi ya same shi kwance yana sharar bacci shi da Talal,amma yanzu daga dawowarshi ya same shi a ɗakinshi,

  Cike da takaici ya shiga cikin ɗakin,gefen gadon ya zauna tare dasa hannu ya bubbugga ƙafarɗarshi""Junaid!junaid"! Da ƙarfi yake ambaton sunan nashi,yatsina fuska junaid ya shiga yi yana faɗin"Wai wanene ke son takuramin"!

  Yayi maganar yana ɗan ware idanunshi masu ɗauke da bacci,

  Harara abbansu yaa jefa mashi tare da cewa"Ubanka ne,buɗe idonka ka gani mara matunci" koda yaji muryar. abbansu sae ya ƙara tamke fuska,yana faman murguɗa masa baki,Abba yace "Eyyyeh!ni kake murguɗa ma baki," zumbura masa baki yayi,hada sa hannu ya toshe kunnuwansa don karma yaji muryar abban nasu,

  

"Nasan maganinka yaro"yayi maganar tare da kai hannunshi saman side drawer ya ɗauko bottle water ɗin dake ajiye a sama,buɗe murfin robar ya shiga yi yana faɗin"Zaka tashi ko saina watsa maka ruwan nan,"

  Wuri wuri yayi masa da ido,yana jira yaga in dagaske abban nasu ruwan zai watsa mashi,

  Jin yayi banza dashi yasa shi ɗebo ruwan a murfin robar,ya watsa masa shi da sanyinsa asaman fuskarshi,aikuwa a gigice ya tashi zaune jikin shi na kerma,hankalin abbansu ba ƙaramin tashi yayi ba ganin yadda ya tsorata daga watsa mashi ruwa a fuska,abu kamar wasa sai ga junaid yana kuka hawaye jaga jaga a fuskarshi,

  Tsawa abbansu ya ɗan daka mashi tare da cewa"Yi mun shiri rigimamme kawai,"

  Wannan maganar da abbansu yayi ba ƙaramin ƙona mashi rai tayi ba,saukowa yayi daga saman gadon yana shassheƙar kuka yace""kuma Allah tunda ka kore ni,ɗakinsu sehrish zanje na kwana,"yayi maganar tare da bubbuga ƙafarshi ya fuce,

  Sakin baki abbansu yayi yana kallonshi har ya fuce daga ɗakin,girgiza kai kawai yayi tare da gyara kwanciyarshi,


Junaid kuwa bayan fitarshi daga ɗakin Abbansu,bedroom ɗinsu sehrish ya wuce kai tsaye,cikin sa'a ya samu ƙopar ɗakin a buɗe,hannu yasa ya tura door din,sannan ya shige ciki,


Sun cika gadon su uku abunsu,sae faman sharar bacci sukeyi banda mutun ɗaya wadda ta rufe idanunta tamkar maiyin bacci, gaba daya hosana ta yaye masu bargon da suka lullu6e dashi,dama ita bata iya kwanciyar bacci ba,zaiyi wuya ta kwanta batare da ta faɗo ƙasa ba,dalilin dayasa suke sanyata tsakiya kenan saboda gudun karta faɗo,sehrish na kwance a left hand,hosana tana a middle ɗinsu,yayin da jahad ke a right hand,saitin inda yake tsaye,hannu yasa tare da kashe masu hasken ɗakin da sehrish ta bari a kunne,lalla6awa yayi ya haye saman gadon,gefen jahad ya kwanta, tare da ja masu bargon ya lullu6esu duka,cikin ƙankanin lokaci bacci ya ɗaukeshi,tabbas Sehrish taji lokacin da aka kashe masu hasken ɗakinsu,amma batayi tunanin ta buɗe idanunta ba don taga wanene,saboda halin da ta shiga,Zuciyarta ba tayi mata daɗi ga hawaye sae faman shararowa suke yi daga cikin idanunta,babban abunda ke damunta shine wani hali sgr yake ciki?Yayi bacci ko idonshi biyu?bataso abunda ya faru ba,sai dae ba yadda ta iya dole tabi umarnin mahaifinta  da wannan zancen zucin bacci ya sace ta,

tashin hankali,Junaid fa ya shige acikinsu sae faman sharar baccinsa yake,sun manne ma juna shi da jahad,duk a tunaninta sehrish ce,hada ƙara rungumoshi ajikinta,



   *mu haɗu on monday donjin yadda zata kaya don kuwa akwai ƙura! Amrish zata Rayu ko kuwa akasin hakan?Wai ma wacece Amrish ɗin nan?su waye iyayenta?shin Sgr zai amince da auren sehrish?a yadda yake jin kanshi ɗin nan?Me zai faru idansu jahad suka Tsinci junaid acikin ɗakinsu saman gadonsu?*😨😱

   *Su aunty babba manya Naki na nan tafe*🤣[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: *💋 Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




Wuraren ƙarfe 3:00 na dare,Jahad tayi wani kwakkwaran juyi cikin bacci zata gyara kwanciyarta,aikuwa taji an ƙanƙameta sosai an matse ta,numfashinta har wani kokawar ɗaukewa yake yi,ƙoƙarin janye jikinta ta shiga yi amman hakan ya faskara,saboda ruƙon da akayi mata bana wasa bane,cikin baccin ta dinga faɗin"Sehrish!ki sake Ni!kin matseni,numfashi na zai ɗauke" daƙyar sound ɗin ke fita saboda throat ɗinta da ke abushe,saboda thirsty da take ji,tun tana ambaton hakan ƙasa kasa har takai ga ɗaga muryarta "Sehrish!!dan Allah ki sake ni,baki ji nace kin matse ni ba? Shiru babu mai bata amsa domin kuwa duk bacci suke yi,



Jahad kuwa tuni ta gama galabaita hakan yasa ta tattare iya ƙarfinta na ƙarshe ta ingije junaid daga jikinta,ya ɗan yi baya,hakan yasa ta samu sarari,hannu tasa tare da zame bargon ta fiddo da kanta,tana faman sauke ajiyar zuciya,zufa duk ta wanke mata jikinta duk da weather ɗin nasu akwai sanyi,matsuwar da tayi ne yasa ta zubda gumi,juyawa ta ɗan yi tare da kallon gefen hannun hagunta,kasancewar akwai hasken electric bulbs ɗin da suka gauraye gidan daga waje da kuma na corridor ɗinsu gana main palour,Sune suka ɗan bama ɗakinsu haske,duk da an kashe Globe ɗin ɗakin nasu,dama kuma Sehrish ta lalata bedside lamp ɗin ɗakin,lokacin baya data kwala ma Haroon a goshinsa,


Ƙura ido jahad tayi tana ƙare masu kallo,gani take tamkar idonta ba dai dai suke nuna mata ba kamar mutun biyu ne kwance a gefen hagunta,hannunta ta miƙe tare da yaye masu Sehrish bargon da suka rufa dashi,gabanta ne ya faɗi rass!ganin Sehrish ga kuma hosana baje suna ta sharar bacci,nan take hankalinta yayi mugun tashi,wani irin tsoro ne ya lullu6eta,tabbas akwai mutun ɗaya 6angaren damanta,wanda suka kwana rungume da juna a ƙanƙame,wanda yayi silar taushe numfashinta,tashin hankali! kasa juyawa tayi don taga wanene saboda tsabar tsoro,sae dai ta zura hannayenta dake ta faman kerma ta laluba don taji in da gaske wani ne kwance a wurin,Sumar kan junaid ta shafo da hannunta,a razane ta zame hannunta,la66anta na kerma ta shiga furta"La'Ila ha'illah Anta subhanaka,Inni kuntu minazzalumin,"daga bisani ta shiga faɗin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un!!,


Muryarta na kerma ta shiga kwalama su sehrish kira kaɗan kaɗan don kada aljanin ya farka,"Hosana!Sehrish!!dan Allah ku tashi!Mutum mutumi acikin ɗakinmu saman gadonmu!ina tunanin Aljani ne ya faɗo ɗakinmu don ya cutar damu,Wayyo Allah na" babban tashin hankalinta aljanin na akusa da ita,in ma cutar dasu yazo yayi toh ta kanta zai fara tunda itace a kusa dashi,


Tuni zufa ta gama wanko mata a fuskarta,numfashi kanshi daƙyar take fitar dashi don kada aljanin yaji yasan cewar idonta biyu,

  "Sehrish!Sehrish!!hosana!wai ba zaku tashi ba?dan Allah ku tashi kuga abunda na gani,asaman gadon mu,"tana magana hawaye na sauka daga idonta,don ita ta riga ta sallamawa kanta cewar ajalinta ne yazo,


   Duk wannan surutan da Jahad ke yi kaf a kunnan Sehrish,wadda ke lamo tayi nisa cikin zurfin tunanin da take yi,Duk a tunaninta Jahad mafarki takeyi shiyasa take sambatu,wannan dalilin ne yasa bata motsa ba,kuma bata tanka mata ba,idanunta ne kawae ke arufe amma idonta biyu,likimo kawai tayi,


Jahad na cikin wannan yanayin taji an aza mata hannu asaman waist ɗinta,a wani irin Firgice ta fashe da wata irin gigitacciyar ƙara,wadda tayi silar tashin hosana daga bacci,hatta sehrish sai da ta razana,a tare suka tashi zaune ita da hosana suna kallon Jahad dake ta ihun neman agaji,ai koda Hosana da sehrish suka ga hannun mutum a saman qugun jahad,a gigice suka duro daga saman gadon da gudun gaske har suna tuntu6e wurin tunkarar ƙopar ɗakin don su buɗe ta su gudu,jahad kuwa sam taƙi motsawa,sai ihu take tana kuka,waɗanda take tunanin cewa zasu taimaketa sun gudu sun barta asaman gadon ita kaɗai,jikinsu sae faman kerma yakeyi burinsu su buɗe ƙopar su gudu amma taƙi buɗuwa,hakan yasa Sehrish watsawa da gudu,ta shige toilet taja ƙopar ta rufe,ganin haka yasa hosana tunkarar wardrobe ɗinsu,ta buɗe gidan ƙasa da babu kaya sosai acikinsa sae bedsheets,Ta faɗa ciki tare da jan murfin wardrobe ɗin ta rufe shi,kowa yayi ta kansa kenan,duk wannan budurin da akeyi Junaid bai sani ba,domin kuwa ba ƙaramin abune ke iya tashinshi daga bacci ba,irin mutanen nan ne masu nauyin baccin tsiya,


Jahad na cikin wannan halin na firgici,taji an aza mata ƙafa asaman jikinta,firgitar da tayi ne yasa tayi wurgi da junaid gaba ɗaya,ya tafi dama yana dab da bakin gadon,aikuwa ji kake timmmm!ya ƙundumo ƙasa kanshi ya bugu sosai saman tiles,

raɗaɗin da yaji ne yasa shi farkawa daga baccin,ya fashe da matsanancin kuka,


   Gaban jahad ne ya faɗi rass!!jin sautin kukan Junaid,rarrafowa tayi ta dawo gefen gadon tare da ɗan leƙawa don ta tabbatar ma kanta abunda kunnuwanta ke ji,Zaro ido waje tayi cike da mamaki take kallonshi,yadda kasan wani jinjiri ya 6are baki sai kuka yake yi,da ƙarfi ta ambaci sunanshi"JUNAID"dakatawa yayi daga yin kukan da yakeyi jin an ambaci sunanshi,wurga idanunshi yayi akan jahad,yayi mata wuri wuri da ido yana kallonta,

  Muryarta na rawa tace"juj..junaid!dama kai Ne?me kake yi acikin ɗakin mu?

 cikin shessheƙar kuka yace"Nifa Zuwa kawai nayi don in taya ku kwana,"

...zuba mashi ido kawai tayi tana  kallon fuskarshi don abun ya fi ƙarfinta,

  Daga cikin toilet ta jiyo Muryar Sehrish tana ce wa"Jahad wai dagaske junaid ne?Naji kin ambaci sunanshi"?

  A ƙule jahad tace"Bansani ba,ku fito ku gane ma idonku,kunaji ina kukan neman taimako amma duk kuka watsa a guje kuka barni,yanzu da wani mugun abunne ba junaid ba,da Allah kaɗae yasan me zai biyo baya," 

  buɗe ƙopar sehrish tayi tare da fitowa daga cikin toilet ɗin,hosana ma ta buɗe wardrobe ɗin tare da fitowa daga ciki,suka tunkari inda junaid yake kwance yana faman sauke ajiyar zuciya,sae faman lumshe ido yakeyi,saboda baccin dake a idanunshi,

  "Junaid!" sehrish ce ta kira sunanshi,ware idanunshi yayi akanta yana kallonta,

.."junaid me kake yi a ɗakin mu?waya kawo ka?anya baka fara shan ƙwaya ba"

  Harara ya wurga mata tare da murguɗa mata baki yace"bansani ba,duk kun bi kun takura rayuwata,hakanan kawai ina baccina kun tashe ni,laifi ne in na kwana aɗakinku,ni ba ɗan uwanku bane"? Sakin baki sukayi suna kallonshi,hosana tace"wlh saina faɗa ma Daddy da Ya Omar,ince ka shigo ɗakinmu ka kwanta mana asaman gadonmu,ƙato dakai,"tana kai ƙarshen maganarta,junaid yace"idan kin tashi ki faɗama Kaka ƙarewar daddyn,mai kan kurciya kawai" wannan maganar ba ƙaramin fusata hosana tayi ba,jikinta har rawa yakeyi wurin dauko pillow daga saman gadonsu,ta buga mashi asaman fuskarshi,koda ganin hakan,sehrish ma ta ɗauko pillow ta shiga taya hosana,jahad tace"wlh nima bazan ƙyale ka ba,junaid saboda ka bani tsoro,kuma babu kyau ma tsoratar da musulmi,"tasa hannu ta ɗauko pillow itama,nan fa suka tasa junaid kamar sun samu jaki,suka dingi jibgarshi da pillows,tun yana yi masu magiyar su daina har ya sake fashe masu da kuka yana bubbuga ƙafafunshi,suna cikin bugun nan nashi,suka ji tsit junaid ya daina motsi,cikin sauri Jahad ta kalli jikin pillown hannunta,Ɗigon jini ta gani,ɗagowa tayi da nufin ta nuna ma su Sehrish aikuwa karaf idonta ya sauka akan pillown dake hannun sehrish da hosana,duk ɗigon jini ne ajikin pillown hannunsu,Tashin Hankali!

  Gaba ɗayansu ba ƙaramin kiɗima suka yi ba,ƴan hanjin cikinsu suka kaɗa,zagaye shi su kayi a zuƙunne suna kallon fuskarshi,

  Fashewa hosana tayi da kuka tana faɗin"Wlh babu ruwa na!bani na kashe junaid ba!"maganar da tayi ba ƙaramin tsoratar dasu tayi ba,tuni ido ya raina fata,daga wasa!?

  Jijjigashi suka shiga yi atare suna ambaton sunanshi"Junaid!junaid!!!ka tashi!dan Allah junaid ka tashi!!Wayyo Allah munshiga ukun mu!!dan Allah baby junaid ka tashi," ko motsi wannan junaid baiyi ba,matsawa sehrish tayi tare da kanga kunnanta asaman hancinshi don taji in yana numfashi,ɗufff taji babu numfashi da sauri ta sanya tafin hannunta asaman kirjinshi saitin zuciyarshi nan ma taji zuciyar tashi tadaina bugawa,a wani irin sukwane ta ɗago da idanunta waɗanda sukayi luhu luhu cike tab da hawaye tana kallonsu Jahad da hosana,jiki a mace tace"ZUCIYAR JUNAID BATA BUGAWA HAKAN NA NUFIN MUNYI SILAR MUTUWAR JUNAID"!!! 

  Girgiza kai jahad ta shiga yi tana cewa"Junaid bai mutu ba,dan Allah ki daina faɗan hakan,kada ya tabbata dagaske,"tayi maganar a yayin da take kai hannu tana tatta6a fuskarshi"junaid!junaid!ka tashi dan Allah ka tashi junaid,"

   Ganin yaƙi motsi yasa suka fidda rai da cewar junaid zai tashi,kifa kai sukayi su duka ukun suna shessheƙar kuka,ɗan ɗagowa jahad tayi tare da kai idonta kan fuskarshi,Abun mamaki sae ga murmushi ya bayyana akan fuskarshi,dimples ɗinsa guda biyu sun lotsa,Wani irin ihun farin ciki ta saki tana fadin"Bai mutu ba!junaid wasa yake yi mana,gayanan yana murmushi,'jin haka yasa su sehrish saurin ɗagowa da kawunansu suna kallonshi,sae faman wangale baki yakeyi yana dariya,abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yayi ba,

  "Junaid"sehrish ce ta ambaci sunanshi,a hankali ya buɗe manyan idanunshi yana kallonsu one by one,sai faman 6a66aka dariya yakeyi,

  Har suna haɗa baki wurin cewa"Kai junaid!meyasa zakayi mana haka?wlh ka tsoratar damu sosai,"

  "Wanda yasa kuka bugeni,ko tausayina bakuji,kun wani taru akaina kuna jibgata kamar kunsamu jaki amale,shiyasa nima na rama da gangan na ɗauke numfashina don kuyi tsammanin kona mutu"yayi maganar yana murguɗa masu baki,Ajiyar zuciya suka shiga saukewa,

  "Junaid dan Allah kayi haƙuri,bazan ƙara bugunka ba,kada ka faɗama kowa,"acewar hosana,

  Harara ya jefa mata tare da ƙara tamke fuskarshi,

  Cikin sanyin murya jahad tace"junaid baka da lafiya ne?mun ga jini ajikin pillow lokacin da muke bugunka,kuma da alama daga hancinka muka gogo shi,"

  Shiru ya ɗan yi yana kallonta kafin yace"Lafiyata ƙalau Ni,nose bleeding ne ba wani abu ba dama ina yawan yinshi,yafi zuwa mun da daddare,shiyasa baku ta6a gani ba"

  "Amma ka faɗama Abba ko wani game da nose bleeding din"? Girgiza kai yayi alamar a'a,da alama baison maganar,don haka yace"pls nidai mubar wannan zancen,kusan yadda za kuyi dani don Allah bazan iya komawa bedroom ɗina ba,tsoro ma nakeji,"yayi maganar ashagwa6e,

  Jiki asanyaye jahad ta kalli su sehrish tace"kuje ku kwanta,bari ni na rakashi ɗakin nashi," mikewa su kayi atare da ita da hosana suka koma kan gadon suka kwanta,tare da jan bargo suka lullu6e,

    Miƙewa daga zaune junaid yayi yana cewa"Allah sai dai ki goyani,don na riga dana faɗa maki cewa ƙafafuna ciwo suke yi mun bazan iya taka stairs ba," 

  Murmushi jahad tayi tare da cewa"shikenan,zan goya ka amma ka bari sai munje wurin benen tukunna in goya ka," amsa mata yayi da toh,sannan ya mike tare da ruƙo hannunta cikin nashi yace"Tashi muje,"mikewa tayi suka fita atare,suna tafiya tana satar kallon gefen fuskarshi kamar wani zautacce sai faman sakin murmushi yake yi,hakanan ta dinga jin gabanta na faɗuwa,lamarinsa ba ƙaramin mamaki yake bata ba,kokonto ta shiga yi anya wannan ɗigon jinin da suka gani na ha6o ne? Yanayin yadda abun ya afku tamkar ba jinin ha6o bane,tabbas akwai dae wani abu dake damunshi wanda baison kowa ya sani,

Tana cikin zancen zucin nata taji yace"Mun ƙaraso wurin stairs ɗin,yanzu ki goyani,ki kaini har bedroom ɗina,kuma ki kwantar dani,"

  Amsa mashi tayi da toh,sannan ta zuƙunna,ya daddage ya haye saman bayanta,tare da kwantar da kanshi luff kamar wani jinjiri,zagayo da hannayenshi yayi ta saman stomach ɗinta,hakan ba ƙaramin yanayi ya jefa ta ba,ji tayi tamkar bazata iya miƙewa tsaye ba,saitin kunnanta taji daddaɗar muryar nan tashi mai haɗe da shagwa6a"jahad ki tashi mu tafi,bacci nake ji,"

  Daƙyar ta iya mikewa tsaye goye dashi abayanta,hannu tasa ta tallaboshi sosai,sannan ta haye saman benen,tana tafiya tana tangal tangal har ta ƙaraso ɗakin nashi,hannu tasa ta ɗan tura ƙopar sannan ta shige ciki,Talal suka samu kwance yana ta sharar bacci,ƙarasawa tayi tare da sauke junaid saman gadon,ya gyara kwanciyarshi,bargo taja ta rufe mashi body ɗinsa zuwa neck ɗinsa,tana ƙoƙarin juyawa tabar wurin,taji ya ruƙo hannunta cikin nashi,jimmm tayi tana jiran jin me zaice mata,

  "Jahad"ya ambaci sunanta da wata irin murya ta mai jin bacci,

  "Na'am,"ta amsa mashi kiran a yayin da take juyowa" murmushi ya sakar mata tare da sanya yatsan hannunshi acikin dimple ɗin fuskarshi yace"Kiss me pls," bakomai ya faɗo mata aranta ba,face abunda ya ta6a faruwa atsakaninsu,cikin motarshi,daga zuwa manna mashi kiss a side face ɗinsa,bakinta ya goce izuwa cikin bakinsa,a ranar zauce mata yayi,

  Maƙe masa kafaɗa tayi alamar bazatayi mashi kiss ɗin ba,bubbuga ƙafarshi ya shiga yi yana yi mata shagwa6a,hakan ba ƙaramin burgeta yayi ba,saboda wani irin kyau da yake bayyana akan fuskarshi aduk lokacin da yake shagwa6a,tamkar tayi hugging ɗinshi ajikinta haka ta dinga ji,

   "Baza kiyi mun ba ko"?yayi maganar.yayin da idanunshi ke ƙoƙarin lumshewa,

   "Shikenan,zanyi maka,amma ka rufe idanunka," da sauri ya rufe su yana jiran jin la66anta asaman fuskarshi,tsayawa tayi asaman kanshi,tana karanto addu'o'i tana tattofa mashi akan fuskarshi,daga ƙarshe ta haɗe yatsun hannunta guda biyu na hannun damanta,a hankali ta aza yatsun nata asaman la66ansa,sannan ta furta sautin kiss ɗin da bakinta,wani irin farinciki ne ya lullu6e junaid,duk a tunaninshi bakinta ne ta aza asaman nashi,baisan cewa wayau tayi mashi ba,tasa yatsun hannunta amatsayin la66anta,

 rufe mashi fuskarshi tayi da bargon,sannan ta kama hanyar fita daga bedroom ɗin,

   "I Love u so much jahad," muryar junaid ce ta katse mata hanzarinta,dakatawa tayi tare da ɗan juyawa tana kallonshi,yana acikin bargon ya furta mata wannan kalmar,

   "Kina sona jahad"?

Wani irin ƙayataccen murmushi ne ya sauka akan fuskarta,bata bashi amsar tambayarba,cikin sauri ta fuce daga ɗakin nashi,ta koma bedroom ɗinsu ta kwanta zuciyarta cike fal da farin ciki,ta ji daɗin kalmar da junaid ya furta mata,duk da bata da tabbacin cewar ko dagaske yake yi mata," da wannan tunanin bacci ya ɗauketa,


  *Boss Bature*


    🤍❤🤍

Washe Gari,


Kwance take asaman katifarsu,ta saki baki tana ta sharar baccinta,sae faman jan minshari takeyi kamar Ragon layya ga miyan bacci dake gangarowa ta cikin bakinta da ta bari a buɗe,tana cikin baccin nan taji Ringing ɗin wayarta da ƙarfin gaske har cikin dodon kunnanta,hannu tasa tare da toshe kunnanta tana faman buga tsoki,alamar an takura mata,bata ɗaga kiran ba,har ya katse kuma sai ga wani kiran ya ƙara shigowa,a hargitse Abra ta miƙe ranta a matuƙar 6ace,tasa hannu ta dauki wayar dake ajiye gefenta,picking call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta Cike da masifa tace"Wai Uban wanene ke kirana tunda sanyin safiya"?

  Kafin ta rufe bakinta taji ance"Ubanki ne!" har sai da gaban abrah ya faɗi rasss,cikin sauri ta janye wayar daga kunnanta tare da kallon screen ɗin wayar don ta shaida mai kiran nata,Sunan Aunty babba ta gani,yatsina fuska tayi kafin ta mayar da wayar a kunnanta,"ina kwana aunty,an tashi lafiya"

  Rai a6ace Aunty babba tace"Ruƙe gaisuwarki,sakarya daƙiƙiya zaman uban mi kike ke da Mammy da har kuka bari AMAL ta gudo daga mai duguri tazo Abuja wurin Amani?!" jin wannan maganar yasa abrah ta zabura,don har sai da ta daki ƙirjinta da hannunta,Hankali atashe tace"Aunty laila dagaske Amal tana abuja wurin Amani!"

  "Ƙarya zan maki ne?Kuna nan sake da baki har yarinya ƙarama tayi maku wayau ta gudu,Yanzu baki ga yadda Amal ta koma ba,Yarinya ta zama ƴar hutu kamar wadda ta taso a gidan naira,Tamkar bata ta6a shan wahala ba,Irin rayuwar dana so ace ke kika same ta,sae gashi ƴar kishiyar da muka tsana ita ta samu wannan damar,ina nan dake in har mu kayi sake AMAL sai ta auri ɗaya daga cikin ƴa'ƴan Alexandra,"

  Saboda tsabar takaici Hannu ɗaya abra ta aza asaman kanta tana faɗin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un!

Aunty babba tace"kaɗan ma kika gani!duk laifinku ne!da alama su Amani sunfi mu Jinin Nasara,shiyasa suke ta cin galaba akan mu,"

  Muryar abra tamkar zatayi kuka tace"Wlh aunty laila har shawara sai da naba mammy tun kafin amal ta gudu nace mata mu 6alle ƙafarta guda ɗaya,don ta zama gurguwa kinga in mukayi hakan ba yadda za'ae ta gudu,Amma saboda shegen son kuɗi irin na mammy tace Wai mu barta da ƙafafunta,saboda tana so Amal ta auri mai kuɗi don ta rinƙa tatso mana kuɗi a wurinta,Yanzu gashi nan Mammy taja mana"

  Shiru suka ɗanyi na wani lokaci kafin Aunty babba tace"Abra inaso kiyi gaggawar tattara kayanki kibar gidan nan!kema ki dawo Abuja gidan surukanmu da zama!wannan kaɗae ce hanyar da zamu iya cin nasara akansu,"

  "Aunty in dawo nan fa kika ce?Aunty hayaam fa?zata dawo gida ne"?

"Bazata dawo ba,zama ma yanzu ta fara shi har sai an shafa fatihar aurenta da Babban yayansu,kawai abunda nakeso dake,ki tattara kayanki ki dawo gidan da zama,saboda ni bani da tabbacin cewar zama na zaiyiyu acikinsa,atakure nake,"

  Jinjina kai Abra tayi tamkar tana agabanta tace"Shikenan Aunty laila,da yaushe kikeso inzo nan ne?kuma ya zamuyi da mammy?kinsan fa bata da lafiya tana can kwance,"

  Dogon tsoki Aunty babba taja tare da cewa"Wake ta wani mammy?ae kawai ki tattara kayanki yanzun nan ki biyo motar Abuja ta kawoki,Ita kuma mammy Allah ya bata lafiya shine kawai,"

  Fuskar Abra ɗauke da murmushi tace"aikuwa yanzun nan zan shirya,zan ma iya sa ɗaya daga cikin samari na,ya kawoni gidan don duk suna da Mota,"

  Aunty babba tace"Yawwa cikin sauƙi ma,ki kira ɗaya daga cikinsu,ya kawoki,"

  "In sha Allah Auntyna," abra ta amsa mata kafin sukayi sallama,


Duk wannan wayar da Aunty babba keyi kaf a kunnan Hafsat da hayaam dake kwance saman gado,ita kuma tana zaune asaman Stool dake agaban mirror,

   "Mommy wannan abun kunyar har ina?taya zaki ce abra tadawo gidan nan da zama?bayan ga hayaam kuma!Nan fa gidan surukanku ne ba gidan ƙanin mahaifinku ba...." a fusace Aunty babba ta jefa ma hafsat wayar hannunta cikin sa'a tasamu gefen goshinta,dafe wurin hafsat tayi saboda zafin da taji,

  Rai a6ace tace"Hafsat ki fita daga idona in rufe!kina yimun shisshigi acikin lamurrana,Ina ruwanki da zaman su Abra acikin gidan nan?ke zaki ciyar dasu ne?ko saman kanki zasu zauna ne"?

  Shiru hafsat tayi batare da ta tanka mata ba,hayaam dae bata sanya masu baki ba,saboda gudun rashin kunyar hafsat don bata raga ma kowa acikinsu,


Wuraren ƙarfe tara,Azmee da Saude suka kammala girke girken breakfast na gidan,yanzu ta samu sauƙi wurin yin aiki don Saude ba ƙaramin taimaka mata takeyi ba,dayake itama kwararriyace wurin iya girki tana son yin girki,bayan sun kammala,Azmee ta shiga jera mata Warmers acikin tray tana kaiwa saman dining table,cikin lokaci ƙanƙani suka kammala jera abincin,


ɗaya bayan ɗaya matasan gidan suka shiga fitowa daga bedroom ɗinsu,su Kanal yousouf,Irfan jabeer khaleed twins,fawan,sune waɗanda suka fara hallara daga baya,Abbansu tare da Mommynsu junaid suka fito,kafin wani lokaci kowa ya fito,hadasu Dr haris su Captain adam,najeeb talal da kuma junaid,da sauransu duka dai,Mutun ɗaya ne bai fito ba,bakowa bane fa ce Surgeon general Rafayet,


Bayan matasan sun hallara Azmee taje ɗakinsu Sehrish ta taso su daga bacci,atare suka fito bayan sunyi brush su uku kowacce sanye da hijabi ajikinta,tun ta sallar asuba ce da suka sanya ajikinsu basu cireta ba,bacci yayi awon gaba dasu,

  Gaishe dasu Abba suka fara yi,fuskar kowannansu ɗauke da murmushi haka suka shiga amsa masu gaisuwar,daga bisani suka shiga gaisar da yayyensu,kowa da irin yadda yake amsa masu gaisuwar cike da zolaya,don wasu ma hada kwaikwayon Muryarsu,hakan ba ƙaramin nishaɗi ya sanyasu ba,


Komawa su kayi tare da samun wuri suka zauna a dining chairs ɗin da Abusufyan ke zaune,atare suka haɗa baki wurin cewa"Daddy ina kwana?ka tashi lafiya,"

ɗagowa yayi tare da kallon fuskokinsu ɗaya bayan ɗaya kafin yace"Lafiyalou Alhamdulillah!"


Natsuwa kowa yayi,yayin da Azmee da saude suka shiga zuzzuba masu abincin,kowa na faɗin abunda yake so yaci,

  Gyaran murya Abba yayi tare da kallon azmee yace"An kai ma Ammi nata breakfast ɗin"!?

  azmee tace"Eh nakai masu,a ɗakin gwaggo don acan tace mun zatayi kalacinta,ita da ƴar uwarta,"

  Murmushi ya ɗan yi don ba ƙaramin daɗi yaji ba,

  "Azeema fa"? Ya kuma tambayarta,

"Itama tana atare dasu,can ɗakin gwaggon,"

Jinjina kai abba yayi kafin ya kuma cewa"Aunty saratu fa?da ƴanmatan ta suma ankai masu nasu"?

  Saude ce ta kar6e da cewa"Ni nakai masu a ɗakinsu,"

  Abba yace"Aikin ku yayi kyau,"ya ƙarasa maganar tare da kai hannu ya ɗauki plate ɗin dake hannunsa yaci gaba da cin abincinsa da azmee ta zuba mashi,

  Abbas yace"Azmee banga su Amal ba?ko ankai masu nasu ne"?yayi maganar ayayin da yake ƙoƙarin ajiye spoon ɗin dake hannunshi,?

      "Na kai masu a bedroom ɗinsu," ta bashi amsa,

  Ganin Abbas ya tambayi iyalinsa ne yasa Ishaq yin gyaran murya yace"Azmee wai ni ina ƴata hafsat ne?ko an manta dasu ne?naga ban gansu ba!?

  "Ni kaina inata so in tambayesu,tun shekaran jiya rabon da in Sanya su a cikin idona,tamkar basa a cikin gidan nan"!Acewar Abbansu,

  "Bari na kirasu,"Azmee ta faɗi hakan tare da juyawa ta nufi ɗakinsu laila,

  abinci take ci,amma hankalinta ba akwance yake ba,Yau tunda ta tashi daga bacci gabanta ke ta faɗuwa rasss!rasss!mafi yawancin lokutta in taji gabanta na yawan faɗuwa to tabbas wani abune zai faru da ita!mai kyau ko mara kyau,sam takasa cin abincinta,sae faman jujjuya cokalin hannunta takeyi acikin plate ɗin dake agabanta,

   A hankali ta ɗago da idanunta tare da azasu akan Hosana dake ta faman cunkusa Burger acikin bakinta,yadda kasan zata 6ara bakin ko gajiya da Ci ba tayi,Allah sarki rayuwa kenan,Allah mai yadda yaso,kamar basu bane waɗannan yaran ba,masu yawo babu takalmi a ƙafafunsu,kawunansu babu ɗan kwali,Kayan jikinsu duk a yayyage,babu mai son su,rayuwarsu a wulaƙance kowa gudunsu yakeyi,Amma yanzu komai ya canza!Yanzu gasu acikin danginsu,kowa sonsu yakeyi,suci mai kyau su sha mai kyau,su kwana a mai kyau,suturar sawa ma sai sun za6i wadda suke so su sanya ajikinsu,duk mai yajawo wannan, haƙuri!sun rungumi ƙaddararsu sun cinye jarabawar da Allah yayi masu,basuyi gajan haƙuri ba,kullum cikin kai kukan su wurin Allah suke,saboda sun san cewa shi kaɗai ne zai iya share masu hawayensu,duk irin ƙuncin rayuwar dasu Sehrish suka shiga,basu ta6a ƙasƙantar da kansu ba don suyi bara,ko su siyar da mutuncinsu don su samu kuɗi,kamar yadda wasu mutanen keyi,


Janye idanunta tayi daga kan hosana ta mayar dasu kan jahad,wadda ke ruƙe da bread a hannunta,tana goga mashi butter,abun ya ɗaure mata kai kowa sai cin abinci yake yi hankali kwance,amma ita takasa Cin nata,to ko dai bata da lafiya ne? ta ƙarasa zancen zucin tare da juyawa,karaf idanunta suka sauka akan Fuskar Abusufyan wanda ke kallonta,har sai da ta ɗan razana kaɗan,sunanshi ta ambata abakinta a hankali"daddy,"

..murmushi ya ɗan sakar mata tare da cewa"Daughter,tun ɗazu ina kallonki,kin ƙi cin abincinki,kin tasa ƴan uwanki gaba kinata kallonsu ɗaya bayan ɗaya,faɗamun meke damunki ne'?

  "Daddy am not feeling well,gabana sai faɗuwa yakeyi,bansan meyasa ba,shiyasa ma nagaza cin abincin"muryarta akasalance tayi maganar,

  Jahad tace"Daddy,jiya ma batayi wani isasshen bacci ba,"

  "Saboda me"?yayi tambayar yana kallonta,

  "Nikaina bansan meyasa ba,kawai bana jin daɗi ne," 

  Jinjina kai yayi tare da cewa"Kada ki damu in sha Allah wannan faɗuwar gaban da kikeji Alkhairi ne zai faru dake,"

  "Allah yasa haka ne daddy" ta ƙarasa maganar tare da kai hannu ta ɗauki cup of tea ɗin dake agabanta,ta shiga kur6arsa a hankali,ba don tana jin daɗinsa ba,


Suna cikin cin abincin nan,sae ga Azmee tare da hafsat,sun shigo dining area ɗin,Aunty babba na a bayansu ta sanya Niqab a fuskarta,hayaam dai bata fito ba,saboda gudun karsu haɗu da Sgr a wurin,da hannu Azmee tayi masu nuni da su zauna a inda su Jahad suke,saboda nan ke akwai empty chairs guda biyu da suka rage,da yake table ɗin mai mazaunin mutun Shida ne,

  Tunda suka zo wurin,idon kowa ya koma akan Aunty babba dake sanye da niqabi,abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yayi ba,sai da suka fara gaishe dasu Abba,sannan suka samu wuri suka zauna,hankalin Aunty babba sam ba'a kwance yake ba,bata so fitowa ba,Azmee ce ta sanar da ita cewa Ishaq yace su fito dining suci abinci,tayi mata hakan ne saboda ta rama Wulaƙancin da sukayi mata,


Daƙyar ta iya gaishe da Abusufyan,batare daya ɗago ya kalleta ba ya amsa mata,hafsat tace"Uncle ina kwana,"?

  "Lafiya lou hafsat,ashe kuna acikin gidan,ae nayi tunanin kun koma Kaduna ne,"

  Murmushin yaƙe tayi,sae faman zazzare ido takeyi,duk sunbi sun tsargu,ita da mommynta,ita dai Sehrish ta zuba ma sarautar Allah ido,so take taga ta yadda Aunty babba zataci abinci da niqabi a fuskarta,ba ita kaɗae ba hatta jahad abunda take jira kenan,Ishaq kuwa tuni ranshi yayi mugun 6aci,sarai yasan cewa da gangan ta zura niqabi a fuskarta bayan tasan cewar abinci zata ci,alamun rashin gaskiya duk sun bayyana atattare dasu,ita da hafsat,

  Serving ɗinsu Aunty azmee tayi,ta tura masu plate ɗin abincin agabansu,hafsat dai tayi kokarin cin abincin,kaɗan kaɗan take tura chips abakinta,Aunty babba kuwa kamar gunki haka ta ƙame saman kujerar taƙi motsi,fargabarta kada hosana ta gane cewa itace,

  Murmushin mugunta sehrish ta saki,tare da yin gyaran Murya tace"Aunty,ki cire niqabin mana,in ba haka ba,bazaki ji daɗin cin abincin ba,gashi yana ta hucewa,bazaiyi maki daɗin ci ba inya salafce,"

  Mazurai Aunty babba tashiga yi ta cikin niqabin,ƙululun baƙin ciki kamar ta shaqo sehrish ta rufe ta da bugu,ƙin magana tayi saboda gudun kar Hosana taji Muryarta,ta kara tona mata asiri,hakan yasa Jahad cewa"Na ji tayi shiru,kodai bacci ne bai isheta ba"?tayi maganar tana faman ƙumshe dariya abakinta,sehrish tace"inaji tayi bacci ne a zaune,bari na cire mata niqabin don tasha iska kada numfashinta ya sarƙe," yunƙurawa Sehrish tayi tare da kai hannu zata zame niqabin dake a fuskar Aunty babba,ae kuwa a firgice Aunty babba ta zabura ta miƙe tsaye tana faɗin"Karki kuskura ki ta6amun niqabi na," rai a6ace tayi maganar,aikuwa Hosana najin Muryarta,ta daddage ta fasa uwar ƙara,tare da yin wurgi da kofin dake a hannunta,a gigice ta miƙe tana ƙokarin guduwa,gaba daya hankalin kowa ya dawo kanta,Omar ne ya miƙe da sauri ya ruƙo hannunta yana tambayarta lafiya,

   A tsorace tashiga fadin"Banason ta!na tsane ta!wlh ya Omar muguwace matar nan,tazo nan ne don ta kashe mu,dan Allah ku koreta daga gidan nan,wayyo Allah na....."ta fashe da matsanancin kuka,tashin hankalin da ba'a samashi date!nan fa kowa ya miƙe tsaye yana bin Aunty babba da kallo,saboda tsabar ruɗu muryarta na kerma tashiga cewa"wa...wallahi Billahil azimu Ni bansanta ba!bansan laifin me na aikata mata ba,yarinyar nan fa mahaukaciya ce tana da ta6in hankali,shiyasa take wannan sambatun...."tunkan ta ƙarasa maganar Abusufyan ya daka mata tsawa tare da cewa"karki kuskura ki ƙara kiran ƴata da sunan mahaukaciya!in ba haka ba ranki zai 6aci a wurin nan ne!hosana bazata ta6a tsangwamar mutun hakanan ba batare daya aikata mata wani mugun abun ba," ya karasa maganar tare da jan dogon tsoki,

  "Ya Omar dan Allah ku sakar mata karnuka su fiddata daga cikin gidan nan,wlh babu Allah aranta!so take takashe maka hosanarka,"cikin shesshekar kuka take maganar,Marshal sai ƙokarin rufe mata bakinta yakeyi don ta daina amma ina hosana taƙi rufe bakin,don har cizon hannunshi takeyi,in yayi ƙoƙarin toshe mata baki,Aunty babba kuwa sae faman zabga salati takeyi,jikinta sae kerma yakeyi,tuni zufa ta jika ta sharkaf,ƴan hanjin cikinta kuwa sae faman kaɗawa sukeyi,hankalin General ishaq ba ƙaramin tashi yayi ba,tsoranshi kada ace wani mugun abunne laila ta aikata ma yarinyar da har take tsoron ganinta,

   Lalla6awa Aunty babba tayi da gudu tabar dining area ɗin ta koma cikin dakinsu,tana shiga ciki ta aza hannayenta asaman kanta tana faɗin"Na shiga uku!Na bani!na lalace!Waccen mahaukaciyar yarinyar tana son taja mun bala'e ina zaman zaman lafiyata,"tana magana tana cizon yatsan hannunta,"Aunty laila meya faru,"hayaam ce tayi mata tambayar,

  "Hayaam ta faru ta ƙare!yarinyar can ta gama dani!"muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,hannu tasa tare da zame niqabin fuskarta,tayi wurgi dashi ƙasa,sannan tashiga zagaye ɗakin tana faman cizon yatsanta,


"Dan Allah kowa yayi haƙuri ya koma ya zauna,ina tunanin ciwon hosana ne ya motsa,ba wani abu ba shiyasa take ta sambatu,"Omar ne yayi maganar don ya kwantar masu da hankalinsu,

  Fashewa da wani sabon kukan hosana tayi tana faɗin "Wlh ya Omar Ni da hankalina,da tunani na!nasan me nakeyi,wannan matar itace ta...."kasa ƙarasa maganar tayi saboda tsawar da Omar ya daka mata "Shut up hosana!bana son na ƙara jin maganarki a wurin nan!in ba haka ba saina sa6a maki," tafin hannunta tasa tare da toshe bakinta,tana yin kuka ƙasa kasa,

  "Ka daina yi mata tsawa Omar,tabbas akwai abunda akayi ma yarinyar nan,wanda ya ƙona mata zuciya shiyasa take wannan sambatun,ya kamata mu lallasheta,muji menene matsalarta"? Acewar Abba,

   Ishaq yace"hakane,In ba damuwa Inason ganinka Omar tare kuma da yaran,"

  Ya ƙarasa maganar tare da shigewa gaba,Omar yabi bayansa hannunshi ruƙe dana hosana,jahad kuma na abayansu,


Bayan tafiyarsu,kowa ya koma ya zauna,wasu suka cigaba da cin abincinsu,wasu kuma suka bar dining ɗin waɗanda suka ƙoshi da abincin kenan,wurin yayi tsit kowa da abunda yake saƙawa aranshi,


A 6angarensu General ishaq kuwa,a farfajiyar gidan suka zauna saman wasu ƙayatattun kujeru na shakatawa,kowa ya zauna,Hosana da jahad suna fuskantar Ya Omar da kuma ya ishaq,

  Gyaran murya ya ɗan yi tare da kallonsu yace"dalilin dayasa na buƙaci ganinku,saboda inason jin menene alaƙar dake atsakaninku da Laila matata?shin taya akai hosana ta santa da har take tsoran ganinta"?

  Kafin su bashi amsa Omar yayi hanzarin cewa"Ae farko sun ta6a zama a wurinta,Ni na kaisu gidanka,a lokacin kayi tafiya,na damƙa amanarsu a wurin laila,saboda ina da tabbacin cewar zasu samu kyakkyawar kulawa a wurinta,tun da ita mace ce,zasu fi sakewa a wurinta,"

   Tunda ishaq yaji hakan gabanshi ya fadi,saboda yasan halin laila sarai,bata da mutunci,saboda mugun halinta yasa masu aiki suke gudun gidan,duk ƴar aikin da sukayi ƙarshe guduwa takeyi daga gidan saboda masifarta,

  janye idonshi yayi daga kan Omar dake magana,ya mayar dasu kansu jahad da hosana,yace"Ina sauraronku?A zaman da kukayi tare da laila me ya faru?

  Jahad tace"babu komai,munyi zaman lafiya tare da ita,"tana rufe bakinta hosana tace"wlh ƙaryane!jahad ƙarya takeyi maku,batason ta faɗi gaskiya ne,"ta ƙarasa maganar tana matse kwallar data zubo mata a idanunta,

  "Jahad!kinsan banason wasa!faɗamun gaskiyar abunda ya faru acikin gidan,bayan na barku," Marshal ne yayi maganar fuskarshi a ɗaure babu alamun wasa tattare dashi,hakan ne yasa jahad ta natsu ta shiga kora masu bayani,

  "Ya Omar,tun lokacin da ka tafi kabarmu a gidan,Aunty laila ta rufe mu acikin wani tsohon store,babu ci babu sha,iska kanta daƙyar muke shaƙarta saboda wurin a ƙuntace yake,babu window,ga ƙwari dake yawo acikin store ɗin,ranar acikinsa muka kwana,hosana ko bacci bata samu ba......"gaba ɗaya jahad ta kwashe duk abunda ya faru dasu agidan Aunty babba,tun daga A har Z ta sanar masu,a ƙarshe ta fashe da kuka,

 Ishaq kuwa ba abunda ke fitowa daga bakinshi sai kalmar innalillahi'wa inna ilaihirraji'un,'Muryarshi har kerma takeyi wurin cewa"Omar meyasa ka kaisu gidana ne?wlh da ace ka sanar dani tunda farko,da banbari ka kaisu wurin laila ba,saboda nasan halinta,hakanan nake zaune da ita,matar nan bata da imani!muguwace!yanzu ni bansan ya zanyi ba!da wani ido zan kalli Abusufyan da sauran ƴan uwana idan sukaji wannan Zaluncin da laila ta aikata ma Yaran nan!!

   Yana magana,huci na fitowa daga bakinshi,ranshi yayi mugun 6aci idanuwanshi sunyi jawur,

 Marshal Omar kuwa saboda tsabar 6acin rai,ya gaza buɗe baki yayi magana,tamkar ya haɗiyi zuciya ya mutu saboda takaicin abunda laila ta aikata ma su jahad,yaran da ya damƙa mata amanarsu,sai yanzu ya gane dalilin da yasa duk in yaje gidan a lokacin da suke wurinta,sai yaga fuskokinsu babu walwala ashe bayin Allah azabtar dasu takeyi,

  Daƙyar ya iya buɗe baki yace"Amma Laila ta cuce Ni!ban ta6a tunanin zatayi mun haka ba,Meyasa zatayi mun haka?laifin me kuka aikata mata?kawai saboda taga baku da gata ne,don nace mata marayu ne ku shine ta ƙuntata rayuwarku?Ashe itace ta sanya wannan fasiƙin mutumin ya ɗauke ku acikin motarshi don ya zubar mata daku acikin dajin,har yayi ƙoƙarin Yima hosana fyaɗe acikin gidan gonarshi.... " sai yanzu ya gane dalilin da yasa Major yaƙi sanar dashi gaskiyar lamarin daya afku,koda ya tambayeshi a lokacin baya sai cewa yayi yalla6ai banso in shiga tsakaninka da Matar yayanka ne,Ashe mugun abu ta aikata masu,

  A fusace Ishaq ya daki table ɗin dake agabansu,ya miƙe azabure yana ƙokarin zame belt ɗin wandonshi,a ƙoƙarinshi na ya shiga cikin gidan yayi ma Aunty babba bugun tsiya,

  Da sauri Omar ya ruƙo hannunshi,"Ya ishaq,ba anan yakamata ka yanke mata hukunci ba,koba komai ita uwar ƴa'ƴanka ce,mutuncinta zai zube agaban kannenmu,da sauran mutanen gidan,inaso taci albarkacin wannan,"

  Runtse ido ishaq yayi wani irin huci ke fita daga bakinsa,damƙar hannun Omar yayi tare da janye shi daga ruƙon da yayi mashi,ko waiwayenshi baiyi ba ya shige cikin gidan,


Jiki ansayaye Omar ya mayar da idanunshi kan su hosana dake tsaye,wani irin tausayinsu ne ya lullu6eshi,matsawa yayi tare da janyosu ya rungumesu ajikinshi,tamkar ya zubar masu da hawaye haka yake ji,Yayi danasanin kaisu wurin laila,bakomai ne yaja hakan ba fa ce rashin sani,cikin sanyin Murya yace"kuyi haƙuri ku yafe mun,duk laifina ne dana kaiku wurinta,wlh danasani kai tsaye Abuja na kawoku gidanmu,Ni duk atunanina zaku fi samun kulawa a wurinta,ƙaddarace kawai ta riga fata,Amma wlh da ace kun sanar dani tun lokacin da nake zuwa gidan,da saita ɗanɗani kuɗarta," ya ƙarasa maganar a lokacin da yake ƙoƙarin raba jikinshi daga nasu,

  Jahad tace"Ya Omar kadaina ɗaura ma kanka laifi,dama can Allah ya ruga da ya ƙaddara faruwar hakan,kuma yanzu ae komai ya wuce,ni wlh ba don hosana ta fara tona mata asiri ba,da babu wanda zaiji wannan maganar abakina,don har gargaɗin hosana nayi akan kada ta sanarma kowa amma bataji ba,"

  Murmushi Omar ya ɗan yi tare da kallon hosana dake ta faman sauke ajiyar zuciya,ruƙo hannunta yayi cikin nashi sannan yace"Hosana tayi mun dai dai jahad!idan har aka biye ta taki,bazaki ta6a bari a hukunta mara gaskiya ba,saboda tausayinki,abunda nakeso ki gane jahad,Irin waɗannan mutanen masu baƙar zuciya,idan har ba'a dinga hukunta su ba,to basu ta6a gane kuskurensu,balle har suyi nadamar abunda suke aikatawa su daina," jinjina kai jahad tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Hakane ya Omar,kayi gaskiya,Sehrish ma ta ta6a fadamun hakan,lokacin da nayi ƙokarin hukunta hosana akan tonan asirin da taso tayi ma matar Ya ishaq,' sun jima atsaye suna magana kafin daga bisani Omar ya ruƙo hannayensu tare da shigowa dasu cikin gidan,



Hankalin aunty babba fa yaƙi kwanciya,babban abunda takeyi ma fargaba shine kada Hosana ta tona mata asiri agaban surukansu,kusan sau uku tana shiga toilet saboda cikinta daya katsa,har wurin ƙarfe 2:30,bata daina safa da marwar nan ba,acikin ɗakin,ƙafafunta har sai da suka fara yi mata raɗaɗi sannan ta samu wuri ta zauna daga gefen gadon tana faman sakin huci,shigowa hafsat tayi cikin ɗakin,fuskarta jawur sae faman kuka takeyi,aunty babba na ganinta ta miƙe hankalinta a matuƙar tashe ta shiga tambayarta Meya faru,Cikin shessheƙar kuka hafsat tace"daddy ne,Yayi mun faɗa sosai akan abunda muka aikata masu hosana,har mari na sai da yayi,kuma yace daga yanzu babu ni babu shi,In nemi wani uban,!"

Hannu aunty babba ta aza asaman kanta tana ambaton"Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un!wayyo!nashiga uku!shikenan Hosana ta gama dani ta tona mun asiri wurinsu ishaq,Wayyo Ni laila,Zawarci ba fashi," tana magana tana cizon yatsanta,

  Fitowar hayaam kenan daga cikin toilet taji suna wannan maganar,jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,babban abunda take ji ma tsoro shine Ishaq ya saki Laila,saboda tasan cewa muddin ya saki aunty babba,to zamanta a gidan ya qare!!tunda bata da wata aƙala dasu,!Tashin hankali,ishaq bai ta6a gigin ta6a jikin hafsat ba,duk irin girman laifin da take aikatawa,amma yau akansu hosana Tasha mari,idan har hakane menene hukuncin aunty babba?ita da ta ɗauki nauyin shirin gaba daya,OMG!! Rungumota hayaam tayi ajikinta tana lallashinta,daƙyar ta samu hafsat tayi shiru, 


*Boss Bature*


  ❤🤍❤

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



Wuraren ƙarfe shida na marece,ta fito daga cikin toilet,jikinta na sanye da towel fari ta ɗaure shi a saman ƙirjinta,da alama wanka tayi aciki,jahad ta samu zaune saman gadonsu,hannunta ɗauke da wayarta tana ɗan daddanawa,tsayawa tayi a ƙopar toilet ɗin ta ruqe ƙugunta tare da ɗan ɗaure fuskarta tace"Jahad!bana hanaki ɗaukarmin waya ba?kin manta abunda ya faru ran nan?kika kusa kashe mun waya gaba ɗaya!,yanzu da ace ta lalace dashi kenan wa zai siyamun wata"?

  Fuskar jahad ɗauke da murmushi tace"Daddy mana!ae yace zai siya mana Phones gaba ɗayanmu,hada ke ma zai canza maki wata,hada ma laptop xai siya mana,"

  Washe baki Sehrish tayi tare da cewa"Wai dagaske"?

  "Eh,mana,shi da kanshi ya faɗi hakan,Kuma yace next week zamu koma school da kanshi zai mayar damu,don kada wani ya ɗaga mana yatsa,"ta ƙarasa maganar fuskarta dauke da dariya,sehrish kuwa tunda jahad tayi maganar school ba kowa ya faɗo mata aranta ba,face ƙawarta AMRISH,lokaci guda ta faɗo mata acikin ranta,nan take kuma taji gabanta ya faɗi rass,

  Ganin fuskarta da alamun damuwa atattare da ita,yasa jahad kiran sunanta"Sehrish,meya faru ne?maimakon inga kina farin ciki?ko baki son komawa school ne?baki gaji da zaman kashe wando ba acikin gida?

   Muryarta asanyaye tace"ba haka bane jahad,kawai na tuna da wata school friend ɗita ne,Nayi missing ɗinta sosai,Yarinyar tana sona sosai,itace take ƙarfafa mun guiwa akan in ringa yin karatu,in daina bacci a class,Gaskiya banyi mata adalci ba,sam na manta da ita,ni nasan cewa amrish ta neme ni har ta gaji,"

  Jahad tace"Eyya,gaskiya baki kyauta mata ba,gashi sunan ku shigen iri ɗaya ke da ita,ni tun kafin ma in ganta har naji ina sonta,saboda tana son ƴar uwata sosai,Amma meyasa ba zaki jaraba kiranta ba tunda ga waya ko baki da numbarta ne?

  "Ina da numbarta,kinsan kwanakin nan hankali na duk ba'a kwance yake ba,tun lokacin da muka daina zuwa school,ban ƙara bi takan wayar ba,sai ma na ganta a hannunki ne sannan nake tunawa da cewar ina da waya,Allah sarki Amrish ɗina,bansan wani hali take ciki ba,gashi bansan gidansu ba,"

  Mikewa jahad tayi ta nufi wurin da Sehrish take tsaye,mika mata wayar tayi tare da cewa"Ki jaraba kiranta mana,sai mu gaisa,"

  Kar6ar wayar Sehrish tayi,ta shiga cikin contacts ɗinta,ta lalubo numbar amrish,sae dai kash tana kiran layin taji wayar akashe,ɗayan layinta na Airtel ta kira shima akashe yake,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,

   "Bansan meyasa ba'a samun layinta ba,amma mu bari da anjima sae mu jaraba kiranta mu gani kilan ta kunna wayar,"tayi maganar tare da miƙa ma jahad wayar ta kar6a,sannan ta koma gefen gadon ta zauna,ita kuma ta wuce gaban wardrobe tana lalubar kayan da zata sanya,

  Turo ƙopar ɗakin nasu hosana tayi,da sallama abakinta,juyowa sehrish tayi tana kallonta haka itama jahad,

  Nuna Sehrish tayi da yatsanta manuni,kafin tace"RISHI KIZO INJI DADDYN MU YACE KI SAME SHI A ƊAKIN SHI,KADA KI WUCE MINTI BIYAR"

  Rasss!taji gabanta ya faɗi,

"Hosana dagaske ni daddy ke kira?kuma ni kaɗai yace inzo"?

  "Eh,ke kaɗae yake son gani,"

Cikin sauri ta juya tare da zura hannunta cikin wardrobe ɗin,ta lalubo wasu pakistan riga da wando,rigar fara ce,har guiwa daga ƙasanta kwalliyar duwatsu ne,wandon kuma pink colour ne,bai da kwalliya ajikinsa,irin falazun nan ne burgujeje,mayafin kayan ta yafa Shima pink colour,gaban madubi ta koma ta ɗauki flower bomb ɗinta,ta feshe jikinta dashi,sai da ta fara kallon fuskarta a mirror ta ɗan sakarwa kanta murmushi,sannan ta kama hanyar fita daga ɗakin,

Jahad tace"Allah yasa alkhairi ne!kullum in daddy zai kiramu atare yake kiranmu amma yau ke kaɗae kawai yake son gani,"ta ƙarasa maganar tana nuna bayan sehrish da hannunta,

  Murmushi kawai ta saki kafin ta buɗe ƙopar ta fuce,

Da sauri da sauri take tafiya don karta wuce minti biyar ɗin da Hosana tace,tana ƙarasawa baƙin ƙopar ɗakin takai hannu kenan zata buɗe,taga an ja ƙopar daga cikin ɗakin,da alama wani ne zai fito,zubama dogayen yatsun hannunshi ido tayi,farare tass ya ruƙe handle ɗin ƙopar dasu,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga ɗakin,nan take ta gane Cewa BABBAN YAYA NE,mamaki ta shiga yi mai ya kawo babban yaya a ɗakin daddynsu?bayan sa6anin da suka samu a tsakaninsu,ko sun shirya ne,?

Bata ƙarasa zancen zucin nata ba,SGR ya ƙarasa fitowa daga cikin ɗakin Abusufyan,wankan suit ne ajikinshi farare,kyau iya kyau,

   Tsayawa yayi cak kamar an dakatar dashi,Sehrish kuwa tuni gabanta ya shiga faɗuwa,tun daga ƙasa har sama yabi ta da kallo,Yarinyar ko ƙafaɗarshi tsayinta bai kai ba,

  Daƙyar sehrish ta iya buɗe baki tace mashi"Ina yini"

  Tamkar bazai amsa mata ba,don har sai da ya wuceta ya ɗan yi nisa sannan taji yace"Lafiya,"yana faɗin hakan ya ƙara gaba,su babban yaya irin wannan shan ƙamshi haka,

   Jiki asanyaye ta shiga cikin ɗakin da sallama abakinta,A zaune ta samu Uncle abusufyan,daga gefen gadonshi,juyowa yayi tare da kallonta fuskar nan tashi ɗauke da murmushi yace"Daughter,"

  "Na'am daddy,ta amsa mashi tare da ƙarasawa,ta samu wuri saman sofa ɗin dake fuskantar gadonshi ta zauna,suna facing ɗin juna ita dashi,sannan tace"gani daddy hosana ce ta sanar dani cewa kana nema na,"

"Eh hakane,ni na ce ta kira mun ke,"

   Natsuwa tayi tana jiran jin me zaice mata,sae faman wasa takeyi da yatsun hannunta,

   "Gobe yaushe"?yayi tambayar yana kallonta,

..fuskarta ɗauke da murmushi tace"Friday," jinjina kanshi yayi tare da cewa"Masha Allah,Juma'a babbar rana,zaifi kyau in aka kafa tarihi aranar juma'a,ina tunanin kamar zai yi wuya a manta dashi,ko ba haka ba daughter?

  Dariya sehrish tayi kafin tace"gaskiya ne daddy,juma'a itace babbar rana,duk abunda ya faru a ranar friday,zaiyi wuya a manta dashi,"

  Abusufyan yace"Shiyasa nake so gobe na ɗaura maki aure,ko bakya so"?

  Da sauri tasa tafukan hannunta tare da rufe fuskarta,tana dariya,

    "Na ƙosa na fara ganin ƴan jikoki na," cikin zolaya yayi mata maganar,

  "Dan Allah daddy,ka daina faɗin haka wlh kunya nake ji," cikin shagawa6a tayi maganar har lokacin bata zame tafin hannunta daga saman fuskarta ba,

  Miƙa hannu Abusufyan yayi tare da janyo drawer chest ɗinsa gida na tsakiya,ya ɗauko wani small box Golden Colour mai shegen kyau,sae faman ƙyalli yake yi yadda kasan da Zallar Zinari akayi shi,

   Ruƙo shi yayi a hannunshi yana jujjuya shi,ɗan ɗagowa yayi yana kallon sehrish wadda ta rufe fuskarta,

  Gyaran murya yayi mata tare da cewa"Buɗe fuskarki mana," a hankali ta zame hannunta daga kan fuskarta,kai tsaye idanunta suka sauka kan small box ɗin dake hannun Daddynsu,ɗan zaro idanunta tayi tana ƙare mashi kallo,akwatin ya burgeta sosai,jikinshi sae ƙyalli yakeyi mai matuƙar ɗaukar ido,da jan hankali,cike da zumuɗi tace"daddy wannan fa?wlh yayi kyau sosai,ban ta6a ganin irin shi ba,"

  Ƴar dariya Abusufyan yayi tare da cewa"koya burge ki ne"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

Jujjuya akwatin yayi tare da cewa"Sadakin wata Ne,aka biya da Gold,"

  Waro ido waje sehrish tayi cike da mamaki tace"daddy!dagaske ka ke dowry ne aka biya da Gold,but daddy who's she? Dariya abusufyan ya kuma yi ganin yadda tabi ta ruɗe da jin abunda yace,

  "Dagaske nake ba wasa ba,sadakin wata Mai sa'a ce,Jinin nasara,"

  "Daddy,can i see it pls"?

Miƙa mata small box ɗin yayi hannunta har kerma yake yi wurin kar6arsa,janyewa Abusufyan yayi fuskar nan tashi ɗauke da dariya yace"Da hannun hagu kuma?hannu biyu zaki sa ki kar6a,sannan in zaki kar6a ki tabbatar da kinyi bismillah,don Abun yayi albarka,"

  Murmushi sehrish tayi tare da gyara natsuwarta,sannan ta miƙa hannanyenta duka biyun,tayi bismillah kafin ta kar6e shi daga hannun abusufyan,wani irin sanyi ne taji ya ratsata,jujjuya akwatin ta shiga yi tana ƙare mashi kallo,yana da nauyi duk da ƙarantar shi,hakan ya tabbatar mata da cewar,abune mai daraja acikinsa,ƙoƙarin buɗe akwatin ta shiga yi,da sauri Abusufyan ya dakatar da ita"kada ki buɗe shi,ki adana shi a wurinki,bana so kowa ya gani,kuma kada kowa yasan inda kika ajiye shi,"

Abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,

  "Amma daddy,sadakin wata ne fa?kuma naji ka ce in ajiye shi a wurina,saboda Me"?

   Bai bata amsa ba,sae ma kwantar da bayanshi da yayi saman gadon nashi,ya ɗan kishingiɗa,ya aza kansa saman pillow,yana kallonta,ta zuba mashi ido tana jiran jin amsar da zai bata,

   Ƙayataccen murmushi ne ya bayyana akan fuskar Abusufyan,ya jima ahaka suna kallon kallo shi da Ƴar tashi,kafin yace"Zaki samu amsar tambayarki,amma ba yanzu ba,ki bani lokaci zan neme ki,yanzu zaki iya tafiya,"ya ƙarasa maganar yana nuna mata hanyar fita daga ɗakin,

  Tamkar wadda aka zarewa lakar jikinta,haka ta miƙe jiki ba kwari,wani irin faɗuwar gaba kawai take ji,daƙyar ta iya ɗaga ƙafarta,tana tafiya tana waiwayen daddyn nasu,daya zuba mata ido yana kallonta,tabbas akwai wani abu da yake 6oye mata,sai da takai bakin ƙopar ɗakin,tana ƙoƙarin buɗe kopar ta fita,taji ya ambaci sunanta

  "SEHRISH" da sauri ta juya tana kallonshi,


   "Game da abunda ya faru tsakaninki da babban yayanku,Nasan ranshi ya 6aci sosai,ya baki Umarnin kiyi mashi aiki,amma na hanaki a matsayina na mahaifin ki,inaso kije ki bashi haƙuri,'

  Waro ido waje sehrish tayi a ɗan tsorace tace"daddy in bashi haƙuri fa ka ce?wlh tsoro nake ji,jiya ranshi ya 6aci sosai,idan na kuskura naje wurinshi yau karya ni zaiyi nasan,"

  Yadda tayi maganar ba ƙaramin dariya yaso ya bashi ba,fuskarta tamkar zatayi kuka,

  "Don't worry ur self,SGR bazai ta6a gigin bugunki ba,saboda ba halayyarsa bace,"

  Haɗiyar yawu tayi,tana sauraronshi,ɗan dakatawa yayi da yin maganar,kafin ya ɗaura da cewa"daga yanzu inaso,ki cigaba da aiki a ƙarkashinsa....' tunkan ya ƙarasa maganar Sehrish tace"Amma daddy,ka hanani zuwa part ɗinsa fa"

  "A yanzu na soke wannan!inaso ki yi mashi biyayya,ki bishi sau da ƙafa,komai yake so kiyi mashi kawai!part ɗinsa kuma koda wani lokaci zaki iya zuwa ki shiga,even in the midnight,indai ya buƙaci ganinki ki je kawai,"

  Gaba ɗaya Abusufyan ya gama ruɗar da ita,la66anta har kerma sukeyi wurin cewa"dad..dy!bangane me kake nufi ba,dan Allah ka fahimtar dani,"

     "Ki tafi kawai kiyi duk abunda nace maki,idan lokaci yayi zan sanar maki,"

   Juyawa tayi tare da zura ƙafarta,tabar bedroom ɗin nashi,lumshe idanunshi yayi tare da buɗesu,ya ƙurama ceilling ɗin sama ido yana kallonshi tamkar mai karanta wani abu ajikinshi,tunani ya shiga yi acikin zuciyarshi,ya shiga tariyo abunda yaji a kunnuwansa,

  _Na amince zan aureta,bana son abun ya ɗauki lokaci,bana son taron mutane,kuma banaso kowa ya sani,saboda ba auren dundundun bane,nan da wata uku zan sake ta,zan aureta ne ba don ina sonta matsayin matata ba,sae don tayi mun aiki kafin na bar nigeria_

  Hannu Abusufyan yasa tare da ɗaukar wata takarda dake ajiye saman side drawer ɗinshi,zuba ma takardar ido yayi yana kallonta,Agreement paper ce (Takardar yarjejeniya)mai ɗauke da signatures na mutun uku,"

  Ajiyar zuciya ya sauke tare da zura ta cikin drawer chest ɗin daya fiddo akwatin nan da ya bama sehrish ya sanya takardar aciki ya ajiyeta,sannan ya mayar da ita ya datse,rufe idanunshi yayi bakowa bane ya faɗo mashi arai ba face ABU,nan take yaji kewarta ta lullu6e shi,Allah sarki abu,tana raye kota mutu?


A 6angaren Sehrish kuwa bayan fitarta daga bedroom ɗin Abusufyan,a ƙopar ɗakinsu ta tsaya,warware mayafin da ta laga akanta tayi,sannan ta lullu6e small box ɗin dake hannunta don kada wani ya gani,tura ƙopar ɗakin tayi sannan ta shiga daga ciki,babu kowa acikin ɗakin,sautin ruwan da taji ne daga cikin toilet ya tabbatar mata da cewar Jahad ce ke wanka,cikin sauri ta lalla6a gaban dressing mirror ɗinsu,ta zuƙunna gaban drawer ɗin dake ɗauke da mirror ɗin,ta janyo gida na ƙarshe,ta tura small box ɗin acikinsa can ƙurya ta turashi,sannan ta rufe,tana faman sauke ajiyar zuciya,miƙewa tsaye tayi har lokacin bata daina mamakin abubuwan da Uncle ya faɗa mata ba,abun ya ɗaure mata kai sosai,

  Safa da marwa ta shiga yi acikin ɗakin,takasa zama saboda yanayin da ta tsinci kanta aciki,


*Boss Bature*


 ❤🤍❤

 AMRISH,


Tun jiya da daddare data farka,tana bullayi asaman gadon bayan an samu nasarar ceto rayuwarta,doctor yayi mata allurar bacci bata ƙara farkawa ba,yini tayi a kwance tana bacci kamar matacciya,hankalinsu zeenatu ba ƙaramin kwanciya yayi ba,musamman Mommyn Amrish ɗin,bata ta6a tunanin amrish zata rayu ba,amma cikin ikon Allah sae gashi taji sauƙi sosai,poison ɗin da tasha bai kaiga yi mata illa ba,sunyi gaggawar kaita asibitin kuma likotoci sun taru akanta wurin ceto rayuwarta,wannan ne yasa bata jigata ba sosae,amma still da sauranta don ba ƙaramin galabaita tayi ba,yanzu haka ma ƙarin ruwa ne aka sanya mata,


Mommynta na zaune asaman plastic chair din dake agaban gadonta,fuskar nan tayi jawur da alama ba ƙaramin kuka tasha ba,ga rashin baccin da basu samu ba adaren jiya,gaba ɗaya hankalinta na akan Amrish dake kwance magashiyan tana bacci,


Zeenatu na a zaune daga gefen gadon da amrish ɗin take kwance,duk sunyi zuru suna kallonta,tunda safe Sofia ta koma gidansu,ita kaɗae ta rage saboda tace bazata koma gidansu ba har sai Amrish taji sauƙi sun koma gida,


Suna cikin zaman nan,kwatsam Amrish ta buɗe idanunta ta zazzaresu a wani irin firgice ta sanya hannu ta fizge robar ƙarin ruwan da akeyi mata,hankali atashe Zeenatu tace"Mommy amrish ta farka!ta cire ƙarin ruwan da aka sa mata,"jin wannan maganar yasa Mommyn yin firgit ta dawo cikin hayyacinta daga zurfin tunanin da ta shiga,sai dai kafin suyi wani yunƙuri,tuni Amrish ta diro daga saman gadon,ta watsa aguje,zeenatu na ƙoƙarin tarota,takai mata wani kakkwaran naushi a saitin Cikinta,nan take zeenatu ta zube ƙasa hannunta dafe da cikin,ta fasa uwar ƙara tana faɗin"Wayyo Allah na!cikina!nashiga uku,

Ko waiwayonta amrish batayi ba,hanyar fita kawai ta nufa,da gudu ta fice daga ɗakin,bin bayanta Mommyn tayi tana yarfa hannu a ruɗe take faɗin"Help!help!!dan Allah jama'a ataimaka a taro mun ita!mara lafiyace zata gudu,'

    Da gudu wasu nurses suka bi bayan amrish,hada wasu daga cikin masu zuwa dubiya,

   "Amrish dan Allah ki tsaya!wai meke damunki ne!bakiji ina magana ba!ina zaki je ne!," hankali tashe mommyn ke magana,amma ko sauraronta amrish bata yi ba,duk wanda ma yayi ƙoƙarin tarota bugu take kai mashi kamar ƴar wrestling,gashi wani irin ƙarfine da ita kamar na Doki,in ta daki mutun sai ya kusa zaucewa,duk yadda suka so su kama amrish,amma abun yaci tura,domin kuwa 6att suka neme ta suka rasa acikin asibitin,saƙo da lungu babu inda basu duba ba,amma babu ita babu alamarta,ko mai kama da ita ma babu,nan fa hankalin kowa ya tashi,hatta security guards ɗin dake tsaron gate ɗin asibitin,sae da aka tambayesu,sun tabbatar da cewar basu ga fitarta daga asibitin ba,sae dai ko a wani wurin ta 6oye,Hatta Cctv footage sae da aka bincika,amma ba aga ta hanyar da Amrish tabar cikin hospital ɗin ba,kuma ba'aga wurin da ta 6oye ba,wannan abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yayi ba,yarinya kamar mai iskokai?babban abunda zai baka mamaki ƙarfin daya zo mata,mutumin dake kwance magashiyan a gadon asibiti,amma ya tashi farat daya da irin ƙarfin nan a jikinshi❓


Saboda tsabar tashin hankalin da Mommyn Amrish ta shiga,nan take ta yanke jiki ta faɗi ƙasa asume,sai dai nurses suka cuccu6eta aka shiga da ita ciki,suka kwantar,itama zeenatu sae da suka kwantar da ita don kuwa ba ƙaramin buguwa tayi ba,naushi ɗaya tayi mata aciki,amma sae da jini ya zuba a bakinta,


*ANA WATA GA WATA!JAMA'A INA AMRISH TA SHIGA NE*?😳😳😳


*Aunty Babba*


Fitowarta kenan daga cikin toilet tana faman dafe cikinta,ɗagowa tayi tana kallon hayaam dake zaune gefen gadon ta zabga uban tagumi da hannayenta biyu,Hafsat kuwa na asaman gadon kwance ta lullu6e da bargo jikinta sae kerma yake yi,wani irin zazza6ine mai zafi ya rufar mata,tunda rana tagaza motsa jikinta,abun gwanin ban tausayi,


Kwatsam!sukaji an banko ƙopar ɗakin nasu,dafe ƙirji Aunty babba tayi tana kallonshi,sae faman huci yakeyi yadda kasan mayunwacin zaki,da ƙafarsa ya tura ƙopar ɗakin ta rufe,hayaam na ganinshi a razane ta haye saman gadon,jiki na rawa ta wuntsila daga ƙasan gadon ta 6oye,tana faman zazzare ido,

  Cikin inda inda ta ambaci sunan shi"I..ishaq!"

  A zafafe ya ƙarasa inda take,kwakkwarar damƙa yakai ma wuyanta,ya shaqeta sosai,yadda ko ihu bazata iyayi ba,saboda tsabar raɗaɗin da taji nan take ta saki fitsari a wando,wani irin gumi ne ya shiga tsattsafowa daga gefen fuskarta,idanunta sunyi jawur cike tab da kwalla,ƙwayar idon tamkar zata zazzago ƙasa,

  A ruɗe hafsat ta fasa uwar ƙara,ganin abunda daddynta ke ƙoƙarin yi,gadan gadan so yake ya kashe Mommynta,da gudun gaske ta duro daga saman gadon tana kuka,

  "Kafin ki kashe su!Ni zan fara kashe ki!muguwa kawai!Nayi danasanin aurenki laila!nayi danasanin saninki da nayi,Nayi danasanin haɗa zuri'a ɗaya dake,Allah ya isa tsakani na dake!Na tsaneki!kin fita araina!ban sonki!bansan ganinki!"daƙyar sautin muryarshi ke fita saboda tsabar 6acin rai,a fusace ya buga kanta jikin bango,nan take Aunty babba ta baje ƙasa a sume,'

  Juyawa yayi tare da aza idanunshi akan hafsat dake tsaye tana faman zabga uban kuka fuskarnan tayi jaga jaga da hawaye hada majina,nunata yayi da yatsan hannunshi sannan yace"dake da uwarki!ku tattara kayanku ku bar gidan nan!tun kafin inyi sanadin mutuwarku!muguye kawai waɗanda ba Allah aransu,"

  Hannu hafsat ta aza akanta tana ambaton"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un!"

  Juyawa ishaq yayi da sauri zai bar ɗakin,da gudun gaske ta ruƙo rigar jikinshi tare da zubewa saman guiwowinta tana kuka tana yi mashi magiya akan,karya koreta,

   "Daddy dan Allah kayi haƙuri ka yafe mun!wlh ba laifina bane,nasan mun cutar dasu,amma inaso ka sani daga baya na ƙaunace su,Daddy ka yarda dani Mommy itace take azabtar dasu,kuma itace tayi silar barin....'bata ƙarasa maganar ba sakamakon bugun daya kai mata da ƙafarshi,da sauri ta dafe gefen bakinta daya buga wurin har ya fashe,jini ya shiga ɗiɗɗigowa,dogon tsoki ishaq yaja tare da cewa"Kada ki kuskura ki ƙara kirana da sunan daddy!don ni ban haifi wata ƴa mai suna hafsat ba!tunda har kin za6i ki bi mugun hali irin na mommynki,don haka gaki ga ita,duk in da zata je ƙafarki ƙafarta,karku kuskura Dare yayi maku acikin gidan nan!don wlh sai kunyi danasanin haihuwarku da akayi acikin duniyar nan!don bazan raga maku ba,tamkar ban sanku ba,haka zan hukunta ku!kuma idan ta farka daga suman da tayi ki sanar da ita cewa NI ISHAQ NA SAKE TA,!!!!


Wani irin bugu zuciyar hayaam tayi ji kake daramm!!kamar an buga ganga,nan take ido ya raina fata,sae faman mazurai takeyi abayan gadon da ta la6e,Na shiga uku Ni hayaam An saki Aunty laila!Shikenan komai ya ƙare komai ya lalace!mun gama yawo!!


  Ya ƙarasa maganar tare da kai hannu tamkar zai 6alle ƙofar ya fuce,Amani dake la6e tana sauraronsu da gudun gaske ta watsa,sae cikin ɗakin da suka sauka,Tana shiga cikin ɗakin ta daka tsalle,bakinta awashe saboda tsabar dariyar mugunta hada hawaye ke fita a idonta,Amal dake zaune saman gado tana buga game a wayar amani,ganin yadda amani keta dariya kamar wata zautacciya,yasa ta ɗan dakata da buga game ɗin tare da cewa"Aunty Amani meya sanyaki farin ciki har haka"?

  Daƙyar ta iya dakatawa da yin dariyar tace"Amal ba zaki gane bane,Wani buri da nake dashi ne ya cika ayau ɗin nan!!waɗanda suka jima suna ƙuntata rayuwarmu,tun yau zasu fara gir6ar abunda suka shuka," tana magana tana dariya,

  Murmushi kawai Amal tayi tare da mayar da hankalinta kan game ɗin da take bugawa,



General ishaq na fita daga ɗakin,hayaam ta lalla6a ta fito,yadda kasan lagwanin fitila haka take tafiya,jikin taƙaura yayi la'asar wannan hada magriba ma,zuƙunnawa tayi gaban Aunty babba dake baje ƙasa,ta fashe da wani irin matsanancin kuka,Hafsat na kuka itama tana kuka,babu mai lallashin wani,kowa takansa yake yi,

Cikin shessheƙar kuka hafsat ta soma magana"Allah ya isa tsakanina dake Aunty hayaam,kun cuci rayuwata duk don saboda ku ne mommy ta aikata abunda ta aikata don taga ta cika muku burinku,gashi nan yanzu abun ya shafe ni,kunja daddyna ya kore ni,Ni bansan ku wasu irin mutane bane!sam baku da zuciya kare ya lashe,kun nace kun liƙe dole sai kunyi arziƙi da gumin wasu,ku bazaku tashi ku nemi na kanku ba,sam babu Allah aranku,mugunta kawai kukasa agaba,shiyasa har yau babu wani cigaba acikin lamurranku!wlh yanzu ma kuka fara gani!indai bazaku koma ga Allah ba,,ku tsaya a iya matsayin da Allah ya ajiye ku,ku daina hangen na wasu,wannan dogon burin da kwaɗayin abun duniyar ba inda zai kai ku face ya jefa ku ga halaka....." 

Itadae hayaam bata tanka mata ba,saboda bata da abun cewa,har wani zazza6i take ji ajikinta,saboda tsabar tashin hankalin da take ciki,komai ya jagule masu,


Miƙewa hafsat tayi,jiki ba ƙwari ta ƙarasa tare da janyo trolley ɗin kayansu da suka zo dashi,janshi tayi izuwa gaban wardrobe ɗin hayaam,ta buɗeta,kayansu dake aciki tashiga fitowa tana ninkesu,Cikin trolley ɗin take jerasu,


Miƙewa hayaam tayi tana tunanin inda zata samu ruwa ta yayyafa ma Aunty babba,saboda babu ruwa acikin ɗakin,kuma tana jin tsoron ta fita waje suci karo da mutumin,tana cikin wannan tunanin ta tuna da akwai fanfo cikin toilet,da sauri ta shiga ciki a tafin hannayenta ta tarbo ruwan,da sauri da sauri tazo ta yarfa mata shi a fuskarta,dogon numfashi Aunty babba taja,tun kafin ta buɗe idanunta ta shiga fadin"Ruwa!Ruwa!" jin haka yasa hayaam yin tunanin ta fita waje ta samo mata ruwan,buɗe kopar dakin tayi cikin sanɗa ta fito tana tafiya acikin corridor din dakunan nasu,cikin sa'a ta taras babu kowa a main palour din,ƙarasawa tayi wurin fridge ɗinsu,ta bude jikinta na kerma ta ɗauko robar ruwa,da gudu ta koma cikin ɗakin,

   Ƙarasawa tayi tare da taimaka ma Aunty babba ta tashi zaune sannan ta miƙa mata bottle water ɗin,A tsiyace ta 6alle murfin robar,ta kafata a bakinta,yadda kasan zata haɗa da robar duka ta cinye,abun kamar yaƙi,ta damƙi robar,sae kwankwaɗar ruwan take,kwatt!kwatt!!har sae da ta shanye ruwan duka tass,sannan ta saki robar ƙasa,sai faman sauke ajiyar zuciya takeyi,hannunta na dafe da kakkauran wuyanta sae faman Murzarshi takeyi,wurin sae raɗaɗi yake yi mata kamar an barbaɗa mata attarugu,idanuwan nan nata sunyi jawur luhu luhu,sae da tadawo cikin hayyacinta sosai sannan ta kalli Hayaam tare da cewa"hayaam meya faru dani ne?ya akai na ganni akwance ƙasa?

  Kafin hayaam ta buɗe baki tayi magana,tuni hafsat ta katse mata hanzarinta da cewa"Mommy!kina nufin cewa kin manta duk abunda ya faru?idan ma kin manta bari na tuna maki,Dadddy ne ya damƙi wuyanki ya shaqeki,sannan ya bugaki ajikin bango har saida kika suma,"

  Shiru aunty babba tayi tana tariyo abunda ya faru,

"kuma yace mu tattara kayanmu mubar gidan nan,kada mu bari dare yayi mana,bayan haka kuma ya dankara maki saki ɗaya"rai a6ace hafsat ke maganar,

Wata irin mahaukaciyar dariya Aunty babba ta kwashe da ita kamar wata zautacciya,hakan ba ƙaramin mamaki ya basu ba,miƙewa tsaye tayi tana gyara ɗaurin ɗankwalinta tace"Da sauƙi ma,Ni nayi tunanin wani mummunan hukunci zai yanke mun,sai me don ya kore ni?sakin ma da yayi mun wlh ko ajikina,yayi a banza Ae akwai sauran igiyoyi guda biyu,Ni nasan cewa muddin Abbansu yaji cewar ya sake ni,sae yasa ya mayar dani,Ae ni wlh gaba takaini gobarar titi A jos!" To fa,

sakin baki hafsat tayi galala tana kallonta,ba ita kaɗae ba hatta hayaam abun ya ɗaure mata kai,sunyi tunanin cewa in taji ishaq ya sake ta,xata haukace masu ne,amma sae gashi ko ajikinta!zuciyar ta bushe,

  Sae faman tiƙar dariya takeyi kamar sabon shiga a fagen hauka,lokaci guda kuma ta murtuke fuskarta,tare da kallon hayaam tace"Maza ki tattara kayanki,don atare dake zamu tafi,"

  Hankali tashe hayaam tace"Ni kuma?saboda me zamu tafi atare"?

  Shu'umin murmushin nan nata tasaki kafin tace"Saboda inaso,muje wurin bokan nan baba ibliss!wannan karan ba fashi,Dole in kawo ƙarshen auren Amani!kamar yadda zanyi zawarci itama haka nakeso tayi shi,sannan waccen mahaukaciyar yarinyar da tayi silar tona mun asiri har ishaq ya sanya hannunshi ya shaqe mun wuyana na kusa sheqawa barzahu wlh saina yi Ajalinta!!!sannan kuma aurenki da Sgr ba fashi!Wlh ko ta halin ƙaƙa!ko suna so ko basa so sai an ɗaura shi!In har kika ga ba'ayi auren nan ba!To sai dai in bana a doron duniyar nan!ko kuma shi RAFAYET ɗin Ya daina numfashi ne acikinta!sai dai kowa ya rasa wlh!da alama har yanzu basu san wacece Ni ba!zan nuna masu true colour ɗina!Ni dasu shege ka fasa!!" tana magana tana fitar da huci,

  Mugun abu kokayi bacci?yace idona biyu 👀!ANA WATA GA WATA,


Zuru hafsat tayi tana kallonta,abun yafi ƙarfinta,lamarin Mommyn nata sae addu'a,tunani ta shiga yi anya Mommynta bata fara shaye shaye ba?kodai tana da iskokai ne?


Suna cikin wannan tsayuwar,aka kwankwaso ƙopar ɗakin nasu,a tsiwace Aunty babba tace"Wanene"?

  "OMAR NE" koda jin muryar marshal Omar nan fa kowa ya shiga taitayinsa,

  "Hayaam je ki buɗe mashi ƙopa,muji dame yazo!in shima zuwa yayi don yaci mutunci na to bismillah!kowani shege dai dai nake dashi,"kamar wata ƴar daba haka take maganar,

  Buɗe mashi ƙopa Hayaaam tayi,tun daga irin kallon da taga Omar ya watsa mata tuni tashiga ƴan kame kame tana sunnar da kai,

  Shiga cikin ɗakin nasu yayi,yayin da idanunshi ke akan Aunty babba wadda ke tsaye ta ruƙe qugu,sae faman jijjiga jikinta takeyi kamar wata ƴar bori,

  Janye idanunshi yayi daga kanta ya mayar dasu kan hafsat,wadda ke tsaye ruƙe da trolley ɗin kayansu,ganin yana kallonta ne yasa ta ɗukar da kanta ƙasa cike da jin kunyarshi,

  "Ina zaki je ne"? Yayi maganar fuskarshi a ɗaure,

  Muryarta na rawa tace"dad..dy ne yace mu tattara kayanmu mubar gidan nan kada mu kuskura mu bari dare yayi mana anan,"

  "Ban da ke!su kaɗai zasu tafi," 

Wani irin farin ciki ne ya lullu6e hafsat,har ta gaza rufe bakinta saboda tsabar farin ciki,"

  Mayar da idanunshi yayi kan Aunty babba dake tsaye ruqe da qugu yace"Major na awaje yana jiranku,idan kun kammala shiryawa ku same shi,Nayi mashi magana zai kai ku hotel ɗin da zaku kwana kafin gobe da safe sae ku wuce maiduguri,Amma fa in kuna so kenan,sannan kuma....'ya ɗan dakata da yin maganar tare da zura hannunshi cikin aljihun jeans ɗin dake ajikinshi ya zaro bendir ɗin kuɗi na ƴan dubu dubu,a ƙalla zasu yi dubu ɗari ɗaya,ya miƙa masu,jiki na rawa hayaam ta kar6e kuɗin tana yi mashi godiya,

...murmushi Marshal Omar ya saki tare da cewa"No,ba sai kin gode mun ba,nayi ne don Allah,' 

  Yana kai ƙarshen maganar ya juya tare da fucewa daga dakin yana dariya gami da girgiza kanshi,

  Bayan fitarshi aunty babba ta buga tsoki,tana faman hura hanci tace ma hayaam"maza ki shirya mana kayanmu,naji ana kiran sallar magrib,zae fi mu lalla6a mu fuce daga gidan batare da kowa ya ganmu ba,nasan duk sun tafi salla," 

  Amsa mata hayaam tayi da toh,sannan ta juya tare da shigewa cikin toilet,

  Hankalin hafsat ba ƙaramin kwanciya yayi ba,wuri ta samu gefen gadon ta zauna tana faman sakin murmushi,dama babban tashin hankalinta shine idan tabi su Aunty babba maiduguri bazata iya rayuwa cikin gidansu ba,sau ɗaya ta ta6a zuwa,bataji daɗin zama agidan ba,muggan talakawa ne,babu wani abu na more rayuwa acikin gidan,sae ma abun haushi da takaici da zaka taras,

  Kusan minti Goma shabiyar sai ga aunty babba ta fito daga cikin toilet ɗin,da alama wanka tayi,xanin atampar jikinta ne tayi ɗaurin gaba dashi,ya jiƙe sharkaf saboda ta ɗauraye shi acikin toilet da ta shiga,

  Batare da 6ata lokaci ba,suka shirya tsaf ita da hayaam,dogayen riguna suka sanya ajikinsu,sannan suka aza mayafi daga sama,kama hanyar fita daga ɗakin sukayi,ɗan juyowa aunty babba tayi tare da kallon hafsat tace"sannu hakima yayi maki dai dai wato hankalinki kwance zaki rabu da Mommynki ko rakiya babu"?

  Miƙewa hafsat tayi tare da bin bayansu,suka fuce daga cikin ɗakin,ta ƙopar baya suka bi don kada wani yaga fitarsu,a waje suka samu Major tsaye jikin motarshi,ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi,yana ganin sun fito da sauri ya buɗe masu motar,

   "Allah ya kiyaye hanya mommy,in sha Allah gobe da safe kafin ku wuce maidugurin zan kiraki a waya,"

  Harara aunty babba ta watsa mata kafin tace"Munafuka!Hada wani raku6e fuska kamar irin zakiyi kewata ɗinnan!Ae kada ki damu ki sha kuruminki in dai ni ce zan dawo ne!nan bada jimawa ba,"tayi maganar tare da kutsa kai ta shiga cikin Motar,

  "Aunty hayaam Allah ya tsare hanya,Ni dai zan wuce ciki,"

  Murmushin yaƙe hayaam tayi,tare da janyota ta rungumeta,daga bisani ta shiga cikin motar,batare da 6ata lokaci ba,Mojar ya shiga mazaunin driver,yayi ma motar key,yaja ta da gudun gaske,Fashewa da kuka hayaam tayi tana leƙen gidan ta cikin gilashin motar,aunty babba sai lallashinta takeyi tana cewa"ke fa banzace,menene abun kuka anan?karki wani damu kanki,Ae babu inda zamuje,ko cikin garin nan bazamu bari ba,Ni nasan me nake shiryawa,AI YANZU WASAN YA FARA,

   Cikin shessheƙar kuka hayaam tace"Aunty laila bazaki gane bane,wlh banson inyi nesa da gidan nan!ji nake kamar zan rasa shine gaba ɗaya,na kwallafa raina akan Sgr,duk da bana ganinsa amma zaman da nakeyi acikin gidan nan,yana kwantar min da hankalina,at lease muna kusa da juna,ko ba don haka ba,A yanzu ni banajin zan iya rayuwa acikin gidanmu,kwara nan gidan wlh,kaci mai kyau kasha mai kyau ka kwana a mai kyau,duk da atakure nake kwara nan ɗin da can gidan mu,Jarabar mammy kaɗae ta isa ta Ramar da mutun,babban takaici na,korar wulaƙancin da nayi ma Sofwan nasan cewa yanzu kona nemi taimako awajensa bazai kulani ba,"hannu tasa tana share hawayenta,

  Tsoki aunty babba taja mtsww kefa matsakarki kenan!nace maki ki kwantar da hankalinki,ba inda zamuje amma duk kin bi kin tashi hankalinki,sannan in dai akan sgr ne ni nayi maki alƙwarin cewar saina mallaka maki shi,in dai kika ga sgr bai aureki ba to ki tabbatar cewar rayuwarshi a tazuranci zata ƙare,kuma naji kina maganar wani sofwan,uban me zaiyi mana?Ko kin manta cewar Muna da jari atare damu?daga ke harni babu namijin da zai kallemu ya kawar da kansa,Allah ya bamu hasken fata,ga dogon gashi,duk wani abu dake jan hankalin ɗa Namiji ae muna dashi Allah ya bamu,Kinga kuwa muna da hanyar da zamu samu kuɗi,don biyan buƙatunmu,'

Gaba ɗaya duk wannan surutun da sukeyi a kunnan Major,ya kasa kunne yana sauraron su,Sae faman ƙumshe dariya yakeyi acikin bakinsa,abun ban haushi abun ban dariya,

  

   *Boss Bature*

      

   ❤REESHRAF❤


A hankali take hawan upstairs ɗin,yayin da zuciyarta ke tariyo mata abunda daddynsu ya sanar da ita,na cewa taci gaba da aiki a part ɗin SGR,kuma tayi mashi biyayya sau da ƙafa,me hakan ke nufi?small box ɗin da daddynsu ya bata,dowry ɗin wanene?ya sanar dani cewa sadakin wata ne,amma dai koma wacece wannan ba ƙaramar mai sa'a bace,halan tafi kowa kyau a duniya ne?shiyasa Aka biya sadakinta da Gold,dama ni wlh,'

  Kamar wata zautacciya,sae faman surutai takeyi ita kadae abunta,


Ƙarasa hawa up din tayi,kai tsaye ta wuce part ɗin babban yaya,bata tashi jin faduwar gaba ba,sae da tazo ƙopar shiga falonsa,sannan ta tsaya tana karanto addu'o'in neman tsari,duk don kada ta fuskanci hukunci a wurinsa,bayan ta kammala addu'ar,ta shafa asaman fuskarta da kuma jikinta,kafin tasa ƙafarta ta shiga cikin falon cike da kwarin guiwa,sauke ajiyar zuciya tayi ganin babu shi acikin falon,sae dai daddaɗan ƙamshin turarensa,mai ratsa zuciya,bin falon nasa tayi da kallo,kusan 3 days kenan babu gyara,dama da shirin aiki tazo,wuce wa cikin bedroom ɗinshi tayi,nan ma babu shi aciki,da alama basu dawo daga sallar magrib ba,may be sae after isha,ko kuma ƙarfe goma sha biyun dare daya saba dawowa gida,

  Shimfiɗeɗen gadonshi tabi da kallo,zanin gadon duk yayi squeezing,ga blanket ɗinsa ma nannaɗe asaman gadon,bai ɗaukeshi ba,

  Hannu tasa tare da zame mayafin sarin dake ajikinta,ta ɗaure shi a qugunta,kwantacciyar sumar kanta na ɗaure acikin ribbon,saman gadon ta haye tare da sanya hannayenta tashiga ƙoƙarin tattaro bedsheet din nasa,Zancen zucin da takeyi ne ya fito fili,

  "Matar babban yaya ta shiga uku,na tausaya mata Allah,mutun kullum fuskarshi a daure,kamar ta sa,babu fara'a ko kaɗan,in tayi mashi laifi kuwa zata sha zallan kwaɗi,in kuwa ta fusata shi,ɗaukar ta zaiyi kamar haka,

  Tayi maganar tana tattaro bargonsa,ta ɗaga bargon sama tare da yin wurgi dashi,sannan tace"Ya jefar da ita,ko kuma yayi mata irin yadda yayi mun jiya,kamar wata ɗiyar Roba haka zai ruko wutsiyoyin gashin kanta,ya ɗaga ta sama!yana jujjuyata,

Tana cikin wannan sambatun nata,taji anyi mata gyaran Murya,a wani irin firgice ta juya don taga WANENE

 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*






Waro ido waje tayi tana kallonshi,la66anta har rawa sukeyi wurin furta"bab..babban..yaya," tsananin tsoro ne ya bayyana akan fuskarta,babban abunda ya tayar mata da hankali shine batasan tun yaushe yake tsaye abakin ƙopar ɗakin ba!in kuwa har ya jima a tsaye to tabbas yaji duk abunda tace,


Yana tsaye a bakin ƙopar,ya goya hannayenshi asaman faffaɗan ƙirjinshi,farar shirt ce ajikinsa mai dogon hannu tare da wandon suits ɗinsa fari,hannun nan nashi na sanye da agogon diamond ɗinsa,Ya ɗaure sumar kansa ta baya,fuskar nan babu annuri ko misƙala zarratin,ya ɗaureta tamau,a hankali ya furta"On My bed!"

  Jiki na rawa Sehrish ta sauko ƙasa daga saman gadon,cikin in ena tace"am..umm..dama gyara gadon nake yi,shine na hau sama don in samu in tattaro zanin gadon da bar....'

  bata ƙarasa maganar ba,ya dakatar da ita"Shut up!banason jin komai"ya ƙarasa maganar tare da shigewa cikin ɗakin,kama hanyar fita daga ɗakin tayi,muryarshi ce ta kuma katseta da cewa"are u done"?

 "A'a bangama ba,"ta bashi amsa,

"Okey,"ya ambaci hakan a yayin da yake zame agogon dake hannunshi,

  Komawa ciki tayi,sannan taci gaba da gyaran gadon,tana jin lokacin daya shige cikin toilet,da alama wanka zaiyi,ajiyar zuciya ta sauke aranta tace"Allah yaso ni baiji abunda nace ba,dana shiga uku yau,nasan cewa dole ya sanyani tsallan kwaɗi,"shaf shaf ta kammala gyara tamfatsetsen gadon,ta canza mashi bedsheet,ta kuma canza mashi bargon da zai lullu6a dashi,in ya tashi kwanciya,bayan ta kammala gyara bedroom ɗin,ta dawo falo,nan ma ta shiga gyara mashi falon,Cikin ƙankanin lokaci ta kammala gyaran,ko'ina ya koma tamkar sabo,sae ƙamshi ke tashi,


Fitowa tayi daga part ɗin nashi,ta wuce kitchen don ta shirya mashi dinner ɗinsa,a kitchen ta samu Azmee ita da Saude,sun kammala dinner suna gyara kitchen ɗin,gaishe dasu ta fara yi,fuskokinsu a sake suka amsa mata,

  "Aunty azmee a shirya mun dinner ɗin babban yaya,inaso zan kai mashi ne,"

Murmushi Azmee tasaki tare da cewa"Masha Allah,ki ce Anyi welcome back kenan,"

  Dariya sehrish tayi har fararen hakoranta suka bayyana,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"ae daddy,Ya amince na cigaba da zuwa part ɗinsa,inayi mashi aiki,"

  "Amma naji daɗin jin hakan sosai,yanzu bari na shirya maki dinner ɗin,"

  Amsa mata tayi da toh,sannan ta tsaya tana jiranta,

 Batare da 6ata lokaci ba,Azmee ta kammala shirya mata a warmers da sauran food stuffs asaman tray,ta miƙa mata,kar6a sehrish tayi tare da kama hanyar fita daga kitchen ɗin tana faɗin"nagode Aunty azmee,"


Babu kowa a main palour ɗin,yawanci duk basu kaiga dawowa cikin gidan ba,wasu kuma suna acikin ɗakunansu,tana cikin tafiya hannunta ɗauke da tray,taji maganar mutun abayanta,

  "Ƴar shila,"a ɗan firgice ta juya don taga kowanene,gabanta ne ya faɗi Rassss!cike da mamaki take bin shi da kallo yaushe rabon da ta sanyashi acikin idanunta harta manta,ita duk a tunaninta ma an tura shi aikine,ashe yana nan cikin gidan,

  Fuskar nan tashi ɗauke da wannan shu'umin Murmushin nashi,ya ƙarasa tare da cin burki ya tsaya tagabanta,Face to face suka fuskanci juna,

  Jikinshi na sanye da rigar ankara har guiwarsa,sae wandon jeans,sumar kan nan nashi yayi mata ɗan iskan gyaran gashin nan daya saba yi,an saisaye gefe da gefe na kan,tsakiyar kuma anbar sumar a tsaye ba ladabi,

  "Nayi kewarki sosai,abubuwa da yawa sun faru,bansamu isasshen lokacin da zamuyi magana ba,naso nazo na taya ki Murna na kasancewarki ƴar wurin Uncle ɗinmu Abusufyan,abun ya ƙayartar dani,"

  Sakin baki sehrish tayi tana kallonshi,abun ya ɗaure mata kai,Yadda yake tsara kalami kamar ba wannan mashayin giyar ba,wata irin natsuwa wadda bata saba ganinshi da ita ba,har wani kyau ya ƙara,yayi haske abunshi,duk da ramar da ya ɗanyi,

  "Naji kinyi shiru baki ce komai ba" 

 Jin muryarshi yasa ta dawo daga zurfin tunanin da tashiga,muryarta a ɗan ruɗe tace"amma kaine dagaske?ko an yi musayarka ne,"

  Wani ƙayataccen murmushi ya saki na gefen fuska,kafin yace"Ni ne mana HAROON ɗin da kika sani,koda yake na canza a yanzu,nayi ma kaina karatun ta natsu,saboda inaso in zama mutumin kirki,kamar kowa,inaso na shiryu,don na samu mace ta gari,a kwanakin baya kin ta6a yi mun nasiha akan cewa kinaso nazama tamkar ƴan uwana,naji daɗin maganar nan da kikayi mun,kuma nayi amfani da hakan gashi yanzu ni kaina inajin daɗin sauyawar da nayi,"


Zuba mashi ido sehrish tayi tana ƙare mashi kallo har yakai ƙarshen maganar tashi,tayi matuƙar mamakin jin abunda haroon ke faɗa mata,kokwanto ta shiga yi anya haroon ba wani plan yake shirya mata ba?

  Ganin ta tsaya tana kallonshi yasa shi gane cewar kokwanto takeyi akanshi,Cikin sauri yace"nasan zaiyi wuya ki yadda dani,saboda sanin da kikayi mun ada,amma na canza ayanzu fiye da tunaninki,"

  "Amma na daina ganinka acikin gidan nan"?

  "Masallaci nake kwana,shiya sanya baki cika ganina ba,yanzu bana jin daɗin zama ko ina,in ba masallaci ba,acan nake rayuwata,in kinga na fita daga cikin masallaci to wani abu mai muhimmanci ne ya fidda ni,kinsan na tara zunubi sosai shiyasa nake kusanta kaina da ubangiji sosae,saboda in samu yafiyarshi...." 


Yanayin yadda haroon yayi mata maganar ba ƙaramin tausayi ya bata ba,domin kuwa har hawaye sun taru acikin idanunshi,wata siririyar ƙwalla ce ta gangaro cikin idonshi,da sauri ya sanya hannu ya shareta,

  "Yaya haroon,ka daina zubar da kwallarka,tunda dai har ka shiryu ka koma ga Allah,zai kar6i tubanka ne,fata na shine Allah yasa ka daina duk wani abu mara kyau da kake aikatawa,"

 Tana kai ƙarshen maganarta,yace"In sha Allah nadaina,bazan ƙara ba,Ni dai yanzu babban burin da nake dashi arayuwata shine in samu mace tagari inyi aure,zan fi samun kwanciyar hankali,"

  "Kada ka damu,in sha Allah zaka samu,"

  Tana kai karshen maganar ta kama hanya da sauri ta nufi upstairs,

  Bin bayanta da kallo haroon yayi har sai da ta 6ace ma ganinshi,fashewa yayi da dariya,a fili yace"Mata kenan!zuciyarku da rauni take,wannan alƙawari ne na ɗaukar ma kaina,Sai na cimma burina ko da ace shikaɗae ne abunda zan aikata kafin in bar duniya,"yana faɗin hakan ya wuce bedroom ɗinshi,


Sehrish kuwa,tun bayan da tabar wurin,zuciyarta ke cike tab da tausayin Haroon,bakomai take tunawa ba fa ce fuskarshi,yadda yayi mata magana yau ba ƙaramin kashe mata jiki yayi ba,sanya ƙafarta tayi acikin falon Sgr,sannan ta shiga da sallama abakinta,ganin bai fito falon ba,yasa ta wuce bedroom ɗin nashi,sanin cewa ya shiga wanka,yasa ta shiga cikin bedroom ɗin kaitsaye batare da yin sallama ba,

  Gabanta ne ya fadi rass!!ganinshi tsaye gaban mirror daga shi sai short ajikinshi,hannunshi ruƙe da comb yana taje doguwar sumar kanshi,

 Juyawa tayi da sauri zata koma falon,ta cikin mirror ya hangota,gyaran Muryar da yayi ne yasa ta ɗan dakata daga ƙoƙarin da takeyi na fita daga bedroom ɗin nashi,


  "Where are u going?"

Muryarta na kerma tace"Falo,dama dinner ne na kawo maka,"

 "Okey,idan kin kai abincin falo,kizo inason ganinki"

  Da sauri ta amsa mashi da toh,fita daga cikin bedroom ɗin tayi,a saman table ta ajiye mashi tray din kayan abincin,sai da ta bada kusan minti 10 sannan ta koma bedroom ɗin nashi,A lokacin har ya kammala zura sleeping dress ɗinshi,Red colour sun fito da natural beauty dinshi,gefen gadonshi ya zauna,tare da aza ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya,yana karkaɗa ƙafarshi ta hannun dama wadda ya aza asaman ta hagun,yayin da hannunshi ke ruƙe da wayarshi yana daddanawa

  Da yatsan hannunshi yayi mata nuni da tazo gabanshi,cike da fargaba ta ƙarasa tare da tsayawa a tsaye tana faman zare ido,

  "Haka ya dace ki tsaya gabana?C'mon Kneel down"!

  Hankali atashe ta zube saman guiwowinta,jikinta nata faman kerma,

  Tun kafin ya kuma cewa wani abu,tayi saurin cewa"Am sorry babban yaya,daddy yace na baka haƙuri game da abunda ya faru jiya,dan Allah kayi haƙuri,"

  Banza yayi da ita tamkar baiji abunda tace ba,gaba ɗaya hankalinsa na akan wayar hannunshi,sae da ya mula yasha iska sannan yace"Wanene SA"?

  Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,hannu ta aza akai tana fadin"Innalillahi!nashiga uku,"ƙasa ƙasa tayi maganar tuni ido ya raina fata,

  "Idan har kika bari na maimaita tambayar da nayi maki,jikinki ne zai gaya maki", 

  Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"Wlh babban yaya ba dakai nake ba,su6ul da baka ne nayi bansan nace ba,kuma Allah bakai nace ma sa ba,Ni kawai nasan dai nace kullum fuska a ɗaure kamar sa,Kuma fa waƙa ce nake rairawa..."

  Bata ƙarasa maganar ba,ya katseta da cewa"Just one answer nakeso!ki faɗamun menene ma'anar kalmar SA da kika faɗi,if not u will be in serious trouble,"tashin hankali!

 Nan fa sehrish tashiga mazurai,shin tayaya zatayi mashi bayanin cewa shanu take nufi da sa!tabɗijancan,hauka ma takeyi da zata sanar dashi ainihin mai kalmar SA ke nufi,ta fahimci cewa baisan menene SA ɗin ke nufi ba,shiyasa har ya tambayeta don yaji ma'anarta,yadda zaiji daɗin hukunta ta,

  Shirun da tayi mashi ne ya 6ata mashi rai,tsawa ya daka mata wadda ta firgitar da ita,a ruɗe tace"SIR na Yalla6ai nake nufi,wani malamin mu ne na makaranta,muke kiranshi da SA,kuna kama dashi sosai,kyakkyawa ne shima,shiyasa nace fuskarka irin tashi,"

  Guntun tsoki SGR yaja,kafin yace"Tashi kiban wuri,"da sauri ta miƙe,ta fito daga bedroom ɗin nashi,gaba daya ma tabar masa part ɗin,don ta lura yau kamar asama yake,


Bedroom ɗinsu ta koma hannu tasa tare da tura ƙopar ta shiga ciki,Jahad ta samu a zaune saman gadon nasu hannunta ruƙe da wayarta,ta ƙurama screen ɗin wayar ido da alama wani abu take karantawa wanda yaja hankalinta har bata ji shigowar Sehrish ɗin ba,hosana kuwa tuni bacci yayi awon gaba da ita,tana kwance naɗe cikin bargo,


Kamar daga sama taji an fisge wayar,a ɗan firgice ta juya don taga wanene ganin sehrish yasa ta sauke a jiyar zuciya tare da cewa"Ashe ke ce,wlh har kin bani tsoro,ƙoƙarin hawa gadon sehrish tayi tana cewa"Halan karatun Novel ɗinne?tayi maganar ayayin da ta aza idonta kan screen ɗin wayar,Ganin rubutun ƙur'ani yasata cewa"Oh ashe karatun qur'ani kikeyi hakan yayi kyau sosai,'

     "Ina kika je ne?tun ɗazu ina jiranki,kizo muyi fira don bana jin bacci yanzu,"

  Shiru sehrish ta ɗan yi da alamun damuwa a fuskarta,hakan yasa jahad ta kuma cewa"faɗamun meya faru ne?na tambayeki kinyi shiru baki bani amsa ba,ko akwai wani abu ne dake damunki"?

  Shaking head sehrish ta ɗan yi kafin tace"bakomai jahad,naje part din babban yaya ne,nayi masa gyaran ɗaki dana falo,shiyasa na jima ban dawo ba,'

   Jinjina kai jahad tayi tare da cewa"amma duk da haka akwai sauran wani abu da ki ke ƙoƙarin 6oye mun,ko kin manta cewa ni ƴar uwarki ce,rabin ranki,koma nace ranki gaba ɗaya"

  Dariya sehrish tayi jin abunda jahad tace,

    "Jahad,akwai abunda ke damuna amma na barshi acikin zuciyata ne kawai,saboda baida amfani kona furta shi,kawai ki tayani addu'a "

  Ruƙo hannunta jahad tayi acikin nata,sannan tace"in sha Allah,rishi zan tayaki da addu'a,dama kuma kullum cikin yi maku addu'a nake yi gaba ɗayanku,"ta ƙarasa maganar,jikinta asanyaye saboda tunawa da mahaifiyarsu,a hankali taci gaba da magana"Ko wani hali Oumman mu take ciki a yanzu?nadamu sosai akan rashin mahaifiyarmu a kusa damu,baiwar Allah bazan ta6a mantawa da wasu kalami nata ba,tana yawan cewa ina sonku sosai ƴan ukuna,a duk lokacin dana kalleku,sai inji wani sanyi ya ratsa zuciyata,ku kaɗae ne dangin da nake dasu a duniyar nan,ina addu'a akan Allah ya raya mun ku......."kasa ƙarasa maganar jahad tayi saboda hawayen da suka shiga gangarowa daga cikin idanunta,ita sehrish nan take taji hawaye sun shiga wanke mata fuskarta,

  Sehrish ce ta ɗaura da cewar"babu tabbacin cewa zanyi tsawancin kwana,baƙin cikin wannan mutumin ma kaɗai ya isa ya halakar dani,zanyi kuka sosai,naci buri akan naga girmanku amma zaiyi matuƙar wuya hakan ya faru.........."duk wannan zancen da suke yi gaba daya kaf kalaman da mahaifiyarsu ke yawan faɗi masu ne,tun suna yara,dama kuma yaro akwai shi da ruƙo,in ya ruƙe abu aranshi da wuya ya manta shi har girmanshi,kuka sosai suka shiga yi babu mai lallashin wani,cikin shessheƙar kuka jahad tace"Oumman mu ta ta6a sanar dani cewa mu ba ƴan uku bane,Ƴan shida ne ɗaya ta mutu,biyu kuma Ya sayyadi ya kwashe su ya siyar ma ƙungiyarsu don ya samu kuɗi ........"hannu tasa tana share hawayenta a yayin da takai ƙarshen maganarta,,


  Girgiza kai sehrish ta shiga yi yayin da hawayen idanunta ke cigaba da zuba,

   "Jahad,wannan maganar ba gaskiya bace,nacewa mu ba ƴan uku bane!daga baya Oumma ta tabbatar mun da cewa mu ƴan ukune ta haifa,Ya sayyadine yayi mata ƙaryar cewar mu ƴan shida ne ta haifa,ɗaya ta mutu biyu kuma ya kwashe su ya siyar ma ƙungiyarsu,da farko ta yadda da kalamanshi saboda ta sanar dani cewa a lokacin da ta haife mu ba'a hayyacinta take ba saboda matsanancin ciwon nakuda daya taso mata gashi ita kadai ce a gidan,sae dai kawai ta farka a gadon asibiti,taga jarirai guda uku a gefenta,a yayin da shi kuma yake tsaye akanta,batasan meya faru ba,wannan dalilin ne yasa ta yarda da maganarshi daya faɗa mata,Ashe yayi hakanne kawai don ya ƙona mata rai,dama kuma rabi da kwata na kalaman ya sayyadi ƙaryane,zaiyi wuya ya faɗi gaskiya a bakinshi,mugun maƙaryaci ne,hakanan ma yana iya tsara ƙarya,ya mayar da ita tamkar gaskiya,don haka ki cire wannan aranki!"

  Wata nauyayyiyar ajiyar Zuciya jahad ta sauke,muryarta ɗauke da tsantsar farin ciki tace"Har hankalina ya kwanta wlh,bakiji yadda naji ba,ashe ƙaryane ba gaskiya ba,Amma gaskiya mutumin nan baya tsoran Allah,ni fa duk a tunani na dagaske mu ba ƴan uku bane,akwai wasu suna nan a raye,kullum zullumin da nakeyi shine Suna ina?A wane hali suke ciki su ma?kamannin fuskarsu irin namu ne sak ko kuwa?Ashe duk ƙanzan kurege ne,Ya sayyadi dai ya shiga uku,in ya mutu yana aikata waɗannan mugayen halayan nashi,'

Sehrish ta ɗaura da cewa"ae wannan mutumin bazai kai labari ba,irinsu tun a gidan duniya suke fara gir6ar abunda suka shuka,ƙaddara ce kawai tasa Oumman mu ta aureshi,Ashe shima da wani mugun nufin ya aureta,In sha Allah asirinshi sae ya tonu,kuma Ammi tayi mana al'ƙawarin cewa in aka kamoshi sae mun wanke mata mummunar fuskarshi da mari,Ranar kawai nake jira,in da rai da lafiya,nasan rayuwarmu a hannun Allah take,amma zan roƙi Allah akan ya nuna mun wannan lokacin,koda ace shikaɗae ne burina na ƙarshe da zan cika kafin in bar duniya!!"

  Jahad tace"Ni dai koda ace bana raye aka kamo ya sayyadi,alhakin marina na akan ki,Ki haɗa da nawa duka ki kifa mashi su a fuskarshi,"

  "Allah shikaɗae yasan wanene gawar fari acikinmu jahad,nima idan bana raye,Alhakin Marina na akanki Jahad,ki haɗa da nawa da naki ki kifa mashi su a fuskarsa,"ta ƙarasa maganar tana nuna ma jahad yadda zata kifa ma ya sayyadi mari a fuskarshi,

  "Allah ya kiyaye in ta6a fatar fuskarshi da hannuna!wannan ƙazamin mutumin,sai dai in sanya glove a hannuna,"jahad ce tayi maganar,tare da 6ata fuskarta,

  Sun jima suna fira atsakaninsu,kafin daga bisani,jahad ta kwanta,Sehrish kuma ta wuce toilet,bayan ta fito tayi alwala tayi sallah,komawa saman gadon tayi tare da ja musu bargo ta lullu6esu hadi da tofa masu addu'oi.           


      *Aunty Babba*


A 6angarensu Aunty babba kuwa,sam bacci ya ƙaurace ma idanunta,tsabar baƙin ciki ne ƙumshe acikin zuciyarta,tagaza samun natsuwa,tun bayan da Major ya ajiyesu a hotel ɗin,suka shiga ɗakin da aka kama masu,bata samu ta zauna ba,sae faman safa da marwa takeyi acikin ɗakin,Hayaam kuwa tuni bacci yayi awon gaba da ita asaman gadon,


Allah kaɗae yasan mugun abunda take ƙullawa acikin ranta,don kuwa taci alwashin cewa,a gobe goben nan zasu wuce dajin nan na enugu inda wannan ƙasurgumin fasiƙin bokan yake,Wato Baba Ibliss,kuɗi ne matsalarsu,amma ta yanke shawarar cewa zata siyar da sarƙar gold ɗinta da kuma awarwaron sarƙar,hadda Earrings duka zata siyar don su samu tunkarar Bokan,


   *Allah yaba mai rabo sa'a*


*Boss Bature*


   ❤🤍❤


*A washe garin Juma'a,


Cikin bacci Sehrish ta dinga jin sautin waƙa ƙasa kasa"Takusa Aure ƙara faɗa breaker!ta kusa aure ƙara faɗa breaker,"sae faman mutsu mutsu takeyi acikin bargo,ga baccin bai isheta ba,gashi kuma an takura mata,Ranta yayi mugun 6aci,shiru kawai tayi acikin bargon tayi lamo tana tunanin wani shaiɗani ne tunda sanyin safe yake raira masu waƙa acikin ɗaki,ta kasa gane muryar wacece kamar hosana kamar kuma Muryar jahad,a ƙarshe ta tsayar da tunaninta akan cewa Hosana ce,saboda itace gwanar iya raira waƙa,da wuya kaji waƙa a bakin jahad sae dai karatun ƙur'ani,bata ƙarasa zancen zucin nata ba,taji an ƙara Volume hada ma kiɗa gangan gangan acikin kunnanta"Takusa aure ƙara faɗa breaker!takusa aure ƙara faɗa breaker,"

 a fusace sehrish ta yaye bargon da ta lullu6a dashi,karaf idanunta suka sauka akan hosana,dake zaune saman front chair ɗin dressing mirror ɗinsu,ta dage da iya ƙarfinta na ƙarshe,sae faman kiɗa takeyi da hannayenta,

  "OMG!!!" pillow ta raruma ta daddage ta jefa ma Hosana,cikin sa'a ya samu tsakiyar kanta,amma ko ajikinta da alama bata ji pillown ba,lalubo wani pillow ɗin sehrish tayi da ƙarfi ta wurga mata shi,Ya daki kanta,a firgice hosana ta juya don taga menene,pillows ta gani guda biyu a ƙasa,a hankali ta ɗago da idanunta kan wanda ya jefo mata da filon,

  Daƙuwa Sehrish tayi mata da hannunta"Ungo nan don ubanki!Dama sai da raina ya bani cewa kece,Saboda baki da hankali,Mahaukaciya ce ke,Tunda sanyin safiya kin addabi mutane kin takurawa rayuwarsu,saboda tsabar rashin hankali waqa kike rairawa hada kiɗa,maimakon ki kama azkhar ɗin safe kinayi abakinki,.....".

  Muryar jahad ce ta katse mata hanzarinta da cewa"Wai dama hosana ce ke raira mana waƙa da kiɗa!Nifa nayi tunanin cewa ko ringing ɗin wayarki ne,Amma dae hosana baki da hankali bakisan ciwon kanki ba!shiyasa har yanzu haukan naki ƙara gaba yakeyi,babu abunda zai hana in yiwa Daddy magana akai ki asibitin mahaukata,don abincika notikan kwakwalwarki da suka kwance a ɗauɗaure maki su,"tana magana tana kwatanta yadda za'a ɗaure mata notikan kan nata da hannunta, 

  Tashin ta kenan itama daga bacci,Kiɗan hosana ne ya farkar da ita,

   Tunda suka fara maganar hosana ta zuba masu ido tana kallonsu tsabar bakin ciki ya hanata tanka masu,zuciyarta sae faman tafarfasa takeyi,arayuwarta ta tsani ace mata zararra ko mahaukaciya,fuskarta tacika fam ta kumbura kamar alkubus,a ƙule tace"Ni ce Zararra ko?kuma mahaukaciya"?

  Har suna haɗa baki wurin cewa"Eh ance zararra kuma mahaukaciya kiyi abunda zakiyi,"hakan da sukayi ba ƙaramin tunzurata sukayi ba,miƙewa tayi daga saman kujerar,ta shiga nannaɗe hannun rigarta,hakan ya tabbatar masu da cewar dambe zasuyi,

  Tana kammala naɗe hannun rigar,ta danƙara da gudu,ta daka uban tsalle ta haye saman gadon,kafin suyi wani yunƙuri,gaba ɗaya ta haɗe kawunansu ta bugasu jikin na juna,ƙara suka saki saboda zafin da sukaji,Ransu yayi mugun 6aci,Aikuwa gaba ɗaya suka tarar ma hosana suka shiga bugunta,ita ma kuma ta shiga kai masu naushi bana wasa ba,dama tafisu ƙarfi,don bala'e suna kuka suna faɗa su duka ukun,gashi babu mai rabasu,

  hafsat ce ta nufo bedroom ɗin nasu tun kafin ta ƙaraso ƙopar ɗakin,taji sautin kukansu da kuma sautin buge bugen da sukeyi,

  Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,bugun ƙopar tashiga yi amma arufe take,sun datse ƙopar tun jiya da daddare da zasu kwanta



Next page na nan tafe,amma fa in mutun najin bacci ya kwanta,don zai iya kai 10,😟

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*








Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,bugun ƙopar tashiga yi amma arufe take,sun datse ƙopar tun jiya da daddare da zasu kwanta,tana cikin bugun ƙopar ɗakin nasu sai ga Azmee ta shigo corridor ɗin ɗakin nasu,da alama daga kitchen take,ganin hafsat a ƙopar ɗakinsu sehrish tana ta faman yi masu magiya akan su buɗe mata ƙopar,yasa azmee yin hanzarin ƙarasawa kusa da ita tana tambayar ko lafiya,tun kafin ma hafsat ta bata amsa ta jiyo sautin kukansu Jahad acikin ɗakin,kuka fa bana wasa ba,hankali atashe azmee tace"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Meke faruwa ne!meyasa su ke kuka"?

  Fuskar hafsat ɗauke da damuwa tace"Wlh bansani ba,zuwana kenan najiyo sautin kukansu hada ma buge buge da alama faɗa suke atsakaninsu,Ni tsorona ma kada su lahanta junansu,'

  A ruɗe Azmee ta shiga bugun ƙopar tana kwala masu kira"Jahad!Sehrish!hosana!wai bazaku daina ba!Me kukeyi haka!kuzo ku buɗe ƙopar nan tun kafin ranku ya 6aci," duk wannan kwakwazon da azmee keyi a banza domin kuwa babu mai sauraronta,hasalima basu son tana yi ba saboda basu a hayyacinsu,

  "Hafsat!kije ki sanar da Daddynsu ko wani daga cikin yayyensu game da abunda ke faruwa,su taimaka suzo ko ƙopar ce a 6alle,tun kafin yaran nan su halaka kansu,"acewar Azmee wadda hankalinta ya gama tashi,

  Da gudun gaske hafsat ta fita daga corridor ɗin ɗakin,A main palour ta samu Mommynsu junaid tare da Abbansu da kuma Hajiya Azeema suna tattaunawa,wurinsu ta tunkara tana faman yarfa hannu idonta cike tab da kwalla,

  Tun kafin tayi magana suna ganinta suka miƙe tsaye suna tambayar ko lafiya,

  Muryarta na kerma tace"Su jahad ne,suke faɗa acikin ɗakinsu,gashi can suna ƙoƙarin halaka kansu,munyi munyi su buɗe ƙopar sunƙi buɗewa sae dai sautin kukansu kawai da muke ji,"

  Tun kafin ma ta karasa maganar,Jiki na rawa suka nufi ɗakin nasu,hajiya azeema hada tuntu6e saboda tsabar sauri,a ƙopar dakin nasu suka tsaya,bubbuga ƙopar ɗakin Abbansu ya shiga yi a tsawace yake ambaton sunayensu,amma shiru babu wadda ta amsa masa,sae dai sautin kukan nan da suke ji na tashin hankali,

   "Ina ganin bari na kira mahaifinsu wata'ƙil idan yayi masu magana sun ji maganar shi,'Abba ne yayi maganar tare da zura hannu cikin aljihun wandonshi ya ɗauko wayarshi,yatsun hannunshi har kerma sukeyi wurin lalubo number Abusufyan,ya danna mashi kira ta soma ringing,

  Hajiya Azeema da Alexandra duk sun bi sun ruɗe,

  "Ni babban tashin hankalina ma kada yaran nan su illata kansu,Wlh abun ya tsoratar dani sosai ya tayar mun da hankalina,"Hajiya azeema ce tayi maganar,fuskarta tamkar zata fashe da kuka,

  Hafsat kuwa tana acikin main palour ɗin,Sae faman kuka takeyi,kwatsamm taji takun takalmi,da sauri takai idanunta wurin MARSHAL OMAR ne ke saukowa daga upstairs da gudun gaske ta tunkare shi tana fadin"Ya Omar,gasu jahad can suna faɗa acikin ɗakinsu,kuma sun kulle ƙopa,anyi anyi su buɗe sun ƙi su buɗe....."

  Jin wannan maganar yasa hankalin Omar mugun tashi,da sauri ya nufi bedroom ɗin nasu,lokaci guda kowa na gidan labarin abunda ke faruwa yaje musu,hatta su Junaid dake ɗakunansu suna bacci sae da suka tashi,su fawan twins,dasu Irfan,hada Dr hariis da gwaggon katsina,da Ammi,dukkansu kowa fa amma banda Sgr dake a bedroom ɗinshi,

  A ƙopar ɗakin nasu sukayi cirko cirko,Abusufyan yafi kowa shiga damuwa bawan Allah,kamar ya zauce haka yake bugun ƙopar ɗakin nasu yana roƙonsu akan su daina kokoyin da sukeyi suzo su buɗe mashi ƙopa amma shiru babu wanda ya tanka mashi,Haka Marshal Omar ma,Tamkar zai 6alle ƙopar haka ya dinga bugun ƙopar ɗakin nasu,amma duk abanza,Junaid kuwa tuni ya fashe da kuka,yadda kasan wani ƙaramin yaro,

  Cikin shessheƙar kuka Gwaggon katsina tace"nashiga uku..Wayyo Allah na,wlh nasan duk sharrin Ya sayyadine bazai barsu hakanan ba,yanzu haka shine ya shiga tsakaninsu,Ya Allah kayi mana maganin wannan baƙin shaiɗanin....'kuka takeyi hada majina,

   Lokaci guda sukaji shiru tsit cikin bedroom ɗin nasu babu wani gunjin kuka,hakan ya tabbatar masu da cewar wani mummunan abunne ya faru dasu,nan fa kowa ya shiga kallon kallo,yayin da zuciyoyinsu keta bugawa da karfi,

   Jiki asanyaye Abusufyan ya zame ƙasa,tare da aza hannayenshi saman kanshi,yayin da bakinsa ke furta kalmar"Innalillahi wa'Inna ilaihirraji'un,'

  "Abba,ina ganin kawai a 6alle ƙopar," acewar kanal yousouf,

Omar yace"Nima abunda nake tunani kenan,amma ƙopar fa ta cije sosai,na buga na buga amman ko motsi batayi,duk irin ƙarfin da nake dashi,"

  Cikin shesshekar kuka junaid yace"Bari naje na ɗauko zarto sai a datse kubar,"

   Ya ambaci hakan tare da watsawa da gudu ya nufi weapons Room ɗinsu (ɗakin ajiye makamansu,"A rufe ya samu ɗakin,sam ya manta cewar key ɗin yana a wurin babban yayansu,sae da yayi arba da ƙopar a rufe sannan yasha kwana ya dawo da gudu ya haye upstairs ɗin,

  Faɗawa part ɗin SGR yayi,a rikice ya shiga bedroom ɗinshi,a lokacin Sgr na kwance saman shimfiɗeɗen gadonshi yana bacci,

  Junaid baibi takanshi ba saboda a ruɗe yake,side drawer ɗinsa ya tunkara,ya shiga bubbuɗeta yana neman key ɗin,duk inda ya duba babu key ɗin,saman gadon ya hau,yana kiran sunanshi"Babban yaya!Babban yaya!pls wake up!babban yaya ka tashi dan Allah,'

  Cikin bacci rafayet yaji muryar junaid dake ta faman kiran sunanshi,a hankali ya buɗe idanunshi kai tsaye suka sauka kan fuskar junaid,ganin hawaye jaga jaga a fuskar junaid yasa Sgr yin hanzarin miƙewa daga zaune,hankalinshi aɗan tashe yake kallon junaid,da wata irin kasalalliyar murya ya ambaci sunanshi"Junaid!what are u crying for?meya faru ne?.  

   "Babban yaya,key nake nema na weapon's room,inaso in ɗauko saw ne,za'a 6alle ƙopar ɗakinsu Sehrish"

  Cike da mamaki Sgr yace"For what reason?wani abu ya samu door ɗin da za'a 6alleta"?

  Ganin bai fahimci inda zancen nashi ya dosa ba,yasa shi yi mashi bayanin abunda ke faruwa,

   Saukowa Sgr yayi daga saman gadon nashi,junaid na biye da bayanshi suka fito daga part ɗin nasa,da sauri da sauri suke saukowa down stairs,

   Lokacin da suka shigo Corridor(doguwar hanyar) da ɗakunnansu sehrish suke a jere,Hankalin Sgr ya ɗan tashi musamman daya ga dandazon matasan gidan,ga kuma su Abbansu kowa atsaye cirko cirko,fuskokinsu sun nuna alamun damuwa atattare dasu,'

  Abbansu na ganinshi yayi saurin ruƙe hannunshi yana fadin"Yawwa rafayet,nasan zaku iya kai da Omar,dan Allah ku haɗu ku 6alle ƙopar nan,ko mun samu muga meke faruwa aciki,'

  A hanzarce kowa ya dare ya basu wuri,da iya ƙarfinsu Na ƙarshe suka daddage suka kaima ƙopar wani irin kwakkwaran bugu ji kake daraamm!nan take Sakatar ciki ta zame da kanta,ƙopar ta buɗe,gaba daya suka afka ciki,

  Ba ƙaramin girgiza sukayi ba,gaba dayansu musamman Abusufyan,abunda suka gani yayi matuƙar tayar masu da hankali,Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un!!!wannan shine abunda suke ambato a bakunansu,

  Sun tarwatsa komai na bedroom ɗin nasu,ɗigon jini jinin da suka gani shi yafi komai tayar masu da hankali,

Jahad ce kwance ƙasan gadon saman tiles,damtsen hannunta duk sawun cizo ne,wurin duk ya farfashe,hatta saman kumatunta cizon ne,daga can saman gadon kuwa hosana ce,baje hannunta dafe da kanta ta toshe kunnuwanta sae faman mutsu mutsu takeyi da ƙafafuwanta,alamar idonta biyu,Sehrish kuwa basu san ina ta lula ba,

  Zubewa Abusufyan yayi agaban Jahad dake kwance,hannu yasa yana jijjigata yana ambaton sunanta saboda ya gane itace,hawaye sae faman sintiri sukeyi akan fuskarshi,

   Jikin kowa yayi sanyi,zukunnawa Abbansu yayi agaban Abusufyan din yana kallon jahad dake kwance,Sawun haƙoran dake asaman fatar jahad ya tabbatar mashi da cewar faɗa ne ya 6arke a tsakaninsu har sukayi kokoyin nan,

   "Ina tunanin suma tayi ne,wani ya ɗauko mun ruwa dan Allah,"Abbansu ne yayi maganar,da sauri fawan ya fuce daga dakin,ya nufi babban falo don ya ɗauko masu ruwan da za'a yayyafa mata,

....a hankali Sgr yake bin ɗakin nasu da kallo,sunyi mashi kaca kaca,damben daga saman gadon nasu ya fara,Hatta bargon lullu6arsu duk sun jefo shi ƙasa,zagayawa yayi ta dayan gefen gadon,6angaren hannun hagu,tunkan ya ƙarasa ya hango ƙafafun mutun,hakan ya tabbatar mashi da cewar cikon ta ukunsu ce,ta wuntsila ta baya,lokacin daya ƙarasa wurin a kwance ya samu Sehrish,gefen bakinta ya ɗan fashe,ga kuma sawun haƙora asaman ƙirjinta,da kuma damtsen hannunta,zuƙunnawa yayi agabanta yana ƙare mata kallo,

  "Rafayet!wacece anan?ko cikon ƴar ukun tasu ce"?Ishaq ne yayi maganar ganin rafayet ɗin zuƙunne a wurin,

  "Itace," ya bashi amsa atakaice,da sauri Abusufyan ya miƙe tare da sauran suka nufo wurin don suga a wani hali take ciki,

  Tun kafin su ƙaraso Sgr yayi saurin kai hannunshi gaban rigarta yaja rigar ya lullu6e mata ƙirjinta daya fito sosai,

  Fashewa da kuka gwaggon katsina tayi tana fadin"Wayyo Allah ƴa'ƴan Abusufyan ɗina!ni nasan cewa ba yin kanku bane,Wlh sai Allah ya saka maku,Bayin Allah sunji jiki,kowanene yayi masu wannan ɗanyen aikin,jibi yadda aka ciccije masu fata,Yanzu haka ya sayyadine yazo masu da suffar kura yayi masu wannan aika... aikan,' Harris ne ya katseta da cewa"pls gwaggo kibarmu muji da abunda ke damunmu idan ma kina magana ƙara masu zafin ciwon kikeyi,

  Jin haka yasa tayi saurin rufe bakinta,tana cigaba da matsar kwalla a idonta,

   "Abun ya ɗaure mun kai!garin yaya haka ya faru?gaba daya kowannansu sawun cizo ne a fatar jikinsu",Abbansu junaid ne yayi maganar,a yayin da suke tsaye gaban sehrish,Sgr kuma na a zuƙunne,

   Hafsat ce ta basu amsa da cewa"lokacin da nazo ƙopar dakinsu,naji sautin Kukansu acikin ɗakin da kuma sautin bugu kamar suna dambe a tsakaninsu,ina tunanin cewa faɗa sukeyi a tsakaninsu,'

  Jinjina kai marshal Omar yayi tare da cewa"Tabbas sunyi sa insa a tsakaninsu ne har abun yakai ga fada,Kuma wannan cizon dake asaman fatar jikinsu,ba kowa bace tayi masu shi ba fa ce HOSANA!saboda nima ta ta6a cizo na a kwanakin baya,da ranta ya 6aci a asibiti,ta cije ni kuma ba ƙaramin zafi naji ba a lokacin,"

  Abba yace"No wonder!in kuka lura babu sawun cizo a fatar jikinta,indai itace kwance asaman gadonsu,ku kalli jikinta dakyau,kuma bata jigata ba,kamar yarda ƴan uwan nata suka jigata," 

   Suna cikin maganar nan,Fawan ya shigo hannunshi ɗauke da robar ruwan daya dauko masu a fridge,da sauri kanal yousouf ya kar6i bottle water din,ya 6alle murfin,tare da tarbo ruwan a tafin hannunsa na dama,ya watsa shi a fuskar jahad,Nan take taja dogon numfashi tana ambaton sunan Allah abakinta,ajiyar zuciya suka shiga saukewa,da sauri Abusufyan ya dawo wurinta,tare da zukunnawa agabanta,ya ɗago da ita ajikinshi yana ambaton sunanta"Jahad!Jahad!"koda jahad ta buɗe idanunta tayi tozali da fuskar Daddynsu saita fashe da matsanancin kuka tana cewa"daddy kaga abunda hosana tayi mana?kawai daga magana ta hau bugunmu ni da Sehrish,duk tabi ta gartsa mana ciwo a fatar jikinmu....'tana magana hawaye na zuba a idanunta,

  Runtse ido Abusufyan yayi tare da buɗesu a hankali,abun ba ƙaramin ta6a mashi zuciya yayi ba,

  Hannu Omar yasa tare da kar6ar Robar ruwan dake hannun Kanal yousouf ya taka izuwa inda Sgr ke a zuƙunne ya miƙa mashi ita,Kar6a Sgr yayi tare da kur6ar ruwan abakinshi,ya fesar dashi akan fuskar Sehrish,a firgice ta farka gami da mikewa zaune tana faman zazzare idanunta,one by one tabi su da kallo,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin Sgr,ga kuma su hajiya azeema tsaye duk akanta,tafin hannuwanta tasa tare da rufe fuskarta,tana kuka,

   "Wani ya ɗauko min FA box a medical room"Sgr ne ya ambaci hakan,da sauri irfan ya fuce daga ɗakin don zuwa ɗauko akwatin,ruƙo hannun Sehrish Hajiya azeema tayi tare da zaunar da ita gefen gadon,"sannu kinji,yi shiru ki daina kuka,"cikin lallashi takeyi mata maganar,

     Hawa saman gadon nasu Hafsat tayi,tare da kai hannunta ta ɗago da hosana ajikinta,sae faman kerma jikinta yakeyi,ciwonta ya motsa,da alama an rabu da shan magani,duk a tunanin su abun yayi sauƙi,ashe da sauranta,tabbas hosana tana buƙatar ganin likitan mahaukata,

  A faɗace Omar ya daka masu tsawa gaba dayansu yace"wai duk menene yajawo hakan!ba zaku buɗe baki kuyi ma mutane bayani ba!"

   Cikin shessheƙar kuka Sehrish tace"Hosana ce,tunda sanyin safiya tafarka,tana raira mana waƙar takusa aure ƙara faɗa breaker,kuma hada kiɗa take raira waƙar duk ta takura kunnuwanmu,har muka farka daga bacci,Don munyi mata faɗa shine ta naɗe hannun rigarta ta hau mu da bugu da cizo kamar ta samu jakuna....'

  Cike da mamaki kowa ke kallon sehrish dake kora masu bayani,Ishaq yace"Wai yanzu duk don saboda wannan ku ka kusa illata junanku?gaskiya akwai gagarumar matsala babba ma kuwa,'

   Abbas yace"dama da wuya kaga ƴan biyu ko ƴan uku suna zaman lafiya a tsakaninsu,zakaga suna tsananin son junansu,amma ta wani 6angaren basu jituwa,don akwai labarin dana ta6a ji shigen irin wannan daga kokowa suka kashe kawunansu,"

  Jin wannan maganar ta Abbas ya ƙara daga masu hankali,Abba yace"in sha Allah,ba zamu bari hakan ta faru ba!tunda abun har yakai ga faɗa da jima juna ciwo,dole a raba masu wurin kwana,shine kawai mafita,"

  "Abunda nake ƙokarin cewa kenan"acewar hajiya azeema,

  Ammi dai abun yafi ƙarfinta daga ita har Alexandra da hajiya Saratu suna atsaye sun zuba ma sarautar Allah ido,Lamarin yaran yayi matukar daure masu kai,

   Dawowa cikin ɗakin nasu Irfan yayi hannunshi ɗauke da First aid box ɗin,ya ƙaraso tare da miƙa ma Sgr akwatin,hannu yasa ya kar6e shi tare da ajiye shi a ƙasa,

   Sannan ya zauna,daga gefen gadon,suna fuskantar juna shi da sehrish,wadda ke ta faman shessheƙar kuka,wani irin kallo daya jefa mata,tuni ta nemi kukan da takeyi ta rasa,

   "Close ur eyes,"da sauri ta rufe idanunta kamar yarda ya umarta,tana ji yasa mata audiga a wurin ciwon yana goge mata jinin,a sannu ya shiga yi mata dressing din ciwon da taji,bayan ya kammala da ita,Abusufyan ya ruƙo hannun jahad,ya dawo da ita gefen Sgr ya zaunar da ita,cikin lokaci ƙankani Sgr ya kammala yi mata dressing ɗin itama,

   "Ita kuma hosana ya zamuyi da ita?kodai asibiti zamu kai ta?Acewar Abusufyan,

  Omar yace"Rafayet zai iya duba mana ita anan gida ma"

   "Omar am not a psychiatric doctor,though i've experience about their work,zan iya duba ta,Amma a ƙa'ida,psychiatric doctor ya kamata yayi checking ɗinta,bazan shiga aikin da banawa ba,"kaji turawa,ƴan bin ƙa'ida,

  Jinjina kai Omar yayi fuskarshi ɗauke da murmushi,ya juya tare da kallon Dr harris dake tsaye ya goya hannayenshi saman ƙirjinshi yace"Bismillah,"yayi maganar yayin da yake yi mashi nuni da hosana wadda ke kwance ajikin hafsat,idanunta sun birkice sae farar kwayar idon kawai,yatsunta kuwa sae faman kerma sukeyi,hada na kafafunta,

  Kallonta kawai Dr harris yayi batare daya ta6a jikinta ba,ya faɗi sunan allurar da take buƙata ayi mata,

  Da sauri Omar ya ciro wayarshi tare daddana wasu numbobi,ya kira Dr Emran na asibitin Sgr,kiran na shiga emran ya ɗauka,don haka Omar ya miƙa ma Dr harris wayar don suyi magana,

  Bayan sun kammala wayar,ya dago tare da kallon Marshal yace"Ya sanar dani cewa within 15 mins zaizo tare da allurar da kuma medicine ɗinta,"

  Omar yace"Okey,Allah ya kawo shi lafiya,


"Ku kwanta saman gadon,itama mara lafiyar a kwantar da ita before doctor din yazo,Azmee ki shirya masu breakfast dinsu,yanzu haka ma Yunwa ce ke Cinsu,shiyasa su kayi wannan damban," sae yanzu ammi ta tanka masu,saboda tsabar gatanci maimakon asamu wanda xaiyi masu faɗa da tsumagiya a Zane su, amma kowa ya rufe ido,sae lalla6a su akeyi,diyanso kenan,shalelen abusufyan,


miƙewa sgr yayi daga zaunen da yake,sannan yayi masu nuni da su kwanta,a hankali kowaccensu ta kwanta yadda kasan waɗanda suka yi wata suna Jinya don sunji jiki,a hankali Hafsat ta janye Hosana daga  jikinta ta kwantar da ita,har lokacin bata dawo hayyacinta ba,sae faman fari takeyi da idanuwanta,yatsun hannunta dana ƙafafunta sae kerma suke yi,


Haɗa baki su fawan su kayi wurin yi masu ya jiki,kafin daga bisani matasan  suka fita daga ɗakin nasu tare da Ammi da hajiya saratu,Ya rage daga Sgr sae Marshal Omar,Hajiya azeema da kuma abusufyan da kuma gwaggwon katsina sae hafsat,Azmee  ta wuce kitchen don ta shirya masu breakfast ɗinsu,within 15 mins,Dr Emran ya ƙaraso gidan,a cikin motarshi yazo,tun a waje ya haďu da dr Harris tare da kanal Yusuf a tsaye,dama shi suke jira,fitowa yayi daga cikin Motar hannunshi dauke da Ledar maganin Hosana da kuma injection din da xa'ayi mata,gaisawa  suka fara yi  fuskar kowannansu dauke da murmushi,canal Yusuf ne ya kar6i Ledar da Emran din yaxo da ita,sun so ya shigo daga ciki suyi breakfast atare dashi,Amma ya sanar dasu uzurinshi,hakan yasa suka ƙyale shi,sallama sukayi da juna sannan suka koma ciki da sauri,


Cikin bedroom din nasu,Dr Harris ya shigo ganinshi yasa Omar da Sgr suka bashi wuri donya ƙarasa gaban gadon,batare da 6ata lokaci ba,ya ɗura ruwan allurar acikin syringe,aikuwa kamar akan idon Hosana yana kai hannu zai ruƙota ta zabura,tashiga yan buge²,ganin haka yasa sgr da Omar matsawa kusa dashi,sae da suka rurruketa dakyar aka samu yayi mata allurar,yana  kammala yi mata allurar,nan take zufa ta Shiga tsastsafowa daga jikinta,Kafin wani lokaci tuni bacci yayi awon gaba da ita,hankalinsu ba ƙaramin kwanciya yayi ba,

  Juyawa dr Harris yayi tare da kallonsu Omar yace"in sha Allah,Zata ji sauƙin jikin nata,sannan idan ta farka,ga medicines ɗinta nan,bayan taci abinci,akwai direction ajikin kowani magani sae a duba,idan za'a bata,"

Amsa mashi sukayi da toh,Omar yace"aikin ka na kyau dr,"sannan ya mayar da idanunshi kan hajiya azeema tunkafin yayi mata magana tace"Zan kula dasu,idan tafarka zan bata maganin da yardar Allah,"murmushi ya saki tare da juyawa ya kalli sgr,"Muje ko?time karya ƙure mana,naga yanzu har 12 ta kusa,nan da wani lokaci xa'a shafa fati.....'bai ƙarasa maganar ba ganin irin kallon da rafayet ya jefa mashi,Dariya Omar yayi yana faɗin"Sorry bro,kada ranka ya 6aci mana,Yau fa ranar farin ciki ce agaremu,murmushi yakamata a gani akan fuskokinmu,ɗanyi murmushi mana,cike da zolaya Omar keyi mashi magana,shi kuwa Namijin sae faman tamke fuska yake yi,daga bisani suka fita daga ɗakin atare da dr harris,


Komawa hajiya azeema tayi tare da samun wuri gefen gadon ta zauna tana kallonsu,duk sun rufe idanunsu kamar masu yin bacci,

   "Bismillah gwaggo ku zauna mana,"azeema ce tayi maganar tare da yi mata nuni da saman bedside drawer dinsu,jiki asanyaye gwaggon katsina ta karasa ta zauna saman drawer din,ita dae har  yanzu bata yarda Cewar Hosana ce ta ciccijesu ba,

   "Azeeme yanzu kema kin yarda cewa yarinyar nan itace da kanta ta gartsa ma ƴan uwanta cizo har haka?Ni nafi tunanin cewa Ya Sayyadine yazo da suffar kura yayi masu wannan aika aikar,mutumin nan fa ba ƙaramin Taƙadari  bane,banbancinshi da shaiďan kaho ne kawai da babu,"wannan maganar da gwaggon katsina tayi ba karamin dariya tabasu ba,

   Girgiza kai hajiya azeema tayi fuskarta ɗauke da dariya tace"gwaggon shagali,ae in ma shine to ta Allah ba tashi ba,ki kwantar da hankalinki,Sayyadi yake kowa,ba abunda ya isa yayi masu bi'iznillahi,"

  Washe Baki gwaggo tayi da alama taji dadin abunda Azeema tace mata,

  "Allah yayi mana maganin la'ananne," 

Azeema ta amsa mata da ameen,

Sae wuraren karfe sha biyu da rabi Hosana ta farka jikinta da sauki sosai,kuma tana bude ido ta fashe da kuka tana ambaton  sunansu sehrish da jahad,sae da aka nuna mata su sannan hankalinta ya kwanta,


Tuni azmee ta kawo masu breakfast ɗinsu acikin dakin,da taimakon Hafsat da kuma hajiya azeema suka ci abincin,bayan sun kammala cin abincin,Hajiya azeema da gwaggo suka bar dakin,ya rage saura hafsat ita kaɗai,gyara masu bedroom din nasu ta Shiga yi,komai yadawo normal Ba kamar daba da suka hargitsa dakin,bayan ta kammala gyaran ɗakin,wuri tasamu saman side drawer dinsu ta zauna tana kallonsu,

  "Hosana ki ji tsoran Allah,jibi yadda kika raunata mu sae kace ba yan uwanki ba,"jahad ce tayi maganar ranta a6ace,

  A kule hosana tace"ae laifin ku ne,saboda me zakuyi mun rashin kunya?ni ba yayarku bace?oumma tace ni ce babba acikin ku,saboda majnun ya faɗa mata cewa ni ce na fara zuwa duniya,sae da na shaƙi iskar duniya da minti biyar sannan ke kika zo daga ke kuma sae waccen uwar tsiwar" "dakyar take magana,saboda har yanxu jikin nata da sauranshi,

  Guntun tsoki sehrish taja"karki kara ce mun uwar tsiwa,in ba haka ba zan nuna maki kalar nawa haukan,mara mutunci kawai,kuranya mai cin naman ýan uwanta..." 

  Tunkan ta ƙarasa maganar,da Sauri jahad ta toshe mata bakinta,"Dan Allah ya isa haka,da alama baki ji jiki ba,shiyasa kike ƙoƙarin tsokanota,salon Kija mana jinyar  ta koma a gadon asibiti,"

   Hafsat dake zaune tana sauraronsu,sae faman kunshe Dariya takeyi,


*Boss Bature*


  ❤🤍❤



Gaba ďaya matasan gidan,kowa ya Shiga yin wankan juma'a,Kafin wani lokaci duk sun shirya halarta Sallar Juma'a tsaf,kowa ya ɗauki wanka na mutunci wankan shadda,abun sai wanda ya gani,bakowa ne yasan da zancen ɗaurin auren babban yayan nasu ba ko acikin matasan  gidan,manyan su ne kawai suka son da ɗaurin auren,sauran kuwa koda zasu san da auren sai dai suji  a masallaci a yayin da ake sanarwa.


Zuba mashi ido Alexandra tayi ganin yadda  yake ta rawar jiki,yaci uban ado cikin farar shadda,ya zura malunmalun,ya sanya sabuwar hula akanshi,ga agogo sabuwa ya Sanya a hannunshi,ga haɗaɗɗun takalma masu tsadar gaske ya zura a kafafunshi,sae faman sakin Fara'a ya keyi kamar wani sabon ango,yana tsaye agaban mirror hannunshi dauke da kwalbar Turare sae bin jikinshi yakeyi ko ina yana feshe shi saƙo da lungu na jikinshi tamkar  zai ƙarar da turaren dukansa,

  Abun ya ɗaure mata kai cike da mamaki tace"Darling,irin wannan daukar wanka haka?kaji tsoran Allah kodai kishiya Zaka ƙaromin ne"? dariya abbansu yayi tare da ďan juyawa ya kalli wurin da take zaune gafen gadonsu,ta kura  mashi ido ko kyaftawa batayi,

    "Ni da nake da Alexandra,Me zanyi da wata ya' mace?Ni na isa ma nayi maki kishiya?kefa ta dabance ko acikin mata,shiyasa lokacin da kika tafi kika barni nagaza samun natsuwa,kuma naqi kula kowa,saboda son da nake yi maki,"

   ƴar hararar wasa ta jefa mashi tare da cewa"daɗin baki zakayi mun ko?

   "No,ba haka bane,am serious fa,taya zanyi aure baki sani ba?kamar dai wani munafuki,wannan fa wankar sallar juma'a ne,ko kin manta cewa Yau juma'a ne"?

  Shiru ta ɗanyi tana kallonshi,kafin ta ɗan ta6e bakinta tare da cewa"Okey,natuna,nidae duk da haka ban yarda dakai ba Allah,ji nake kamar na bika masallacin nan,"

  Dariya sosai abba yayi,bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"Ashe kina kishi ne?shine kuma kika tafi kika barni,ba kiyi tunanin cewa zan iya ƙara aure ba,a bayan idonki ba"?

  "Ae nasan cewa ba zaka iya ƙara aure ba,that's why ban damu akan haka ba,nasan wanene mijina,kuma na yarda da irin son da yake yi mun,bazai haɗa ni da wata ba," acikin zuciyarta kuwa cewa takeyi"Mutun ma ya kuskura yayi mun kishi,da kuwa na tashi gidan nan da bomb,kowa ya rasa,"

   Suna cikin magana,sae ga junaid ya faɗo cikin ɗakin,jikinshi na sanye da farar shadda,sae ƙamshi ke tashi ajikinshi,hannunshi na ruke da hularshi,mommynsu na ganinshi ta miƙe jiki na rawa,ta rungumoshi tana shafa sumar kanshi,

   "My baby boy,U look so beautiful,Har ma kaso kafi daddynku kyau,"ta ƙarasa maganar a yayin da take raba jikinta daga nashi,

  Ashagwa6e yace"Mommy,yanzu kina nufin Abba ya fi ni kyau?kallar ni fa dakyau ki gani tun daga ƙasa har sama,son kowa ƙin wanda ya rasa,"

  Dariya sukayi gaba ɗayansu,Abbansu yace"To fa!junaid kishi kake dani"?

  Turo baki yayi yana faman ƙunƙuni,irin na shagwa6a66un nan,

   Alexandra tace"wasa nake nima,kafi shi kyau nesa ba kusa ba,"

  Ƙayataccen murmushi ya saki jin abunda tace,

  Mayar da hankalinshi yayi kan abban nasu tare da cewa"Abba mu tafi,kada lokaci ya ƙure mana,"

  "Toh,Uban sauri,mu tafi," yayi maganar tare da ruƙo hannunshi,

  "Madam mu zamu wuce"

 Murmushi tasaki tare da ɗaga masu hannu tace"Adawo lafiya,in anje anyi mana addu'a,"

  Junaid yace"kada ki damu mommy zanyi maki addu'a akan Allah yasa daddy ya ƙara maki kishiya,"

  ɗan zaro ido waje tayi tana kallonshi,da sauri yaja hannun abbansu suka fuce suna dariya,


A main palour Matasan gidan suka hallara ga6a dayansu,sae ƙamshi ke tashi,kowannansu fuskarshi na ɗauke da murmushi,musamman abusufyan,shigowa abba yayi cikin falon hannunshi cikin na junaid,tunkan ya ƙaraso ya lura cewa babu Rafayet acikinsu,

  Kowa sai tambayar ina babban yaya yake,saboda sun saba tafiya masallacin juma'a atare,gaba ɗayansu suke hallara a babban falon nasu duk juma'a before su wuce masallaci,shiru babu rafayet,sae Faman duba agogon hannuwansu sukeyi suna kallon lokaci,har sai da Marshal Omar yace"bari naje bedroom ɗinshi yanzu haka bai kammala shiryawa bane,"da sauri ya tunkari upstairs ɗin yana ƙoƙarin hawa saman benen,Suka jiyo sautin takalmansa,

  Gaba ɗayansu suka ɗaga idanunsu sama suna kallonshi,Cike da tsananin mamaki,tunda suke arayuwarsu basu ta6a ganin sgr ya sanya shadda ajikinshi ba,this is the first time daya fara sanya shadda ajikinshi,tabarakallahu ahsanul khaliƙin,Getzner ce sky blue mai ɗaukar ido,wadda sehrish ta ta6a ɗauko mashi a kwanakin baya,donya sanya amma yaƙi sanyawa,To yau dai itace ya sanya ajikinshi,Babu hula akanshi amma ba ƙaramin kyau sumar kanshi tayi ba,yayi mata gyara na musamman,hannunshi kuwa na sanye da Wannan diamond watch ɗin tashi,yayin da ƙafarshi ke sanye da penny loafers,tunkan ya ƙaraso down stairs din ƙamshin turarenshi ya gauraye ko'ina,yadda kasan tauraro acikin taurari haka ya bayyana,tafiya yakeyi gently tamkar baisan taka ƙasa,fuskar nan tashi aɗaure babu fara'a ko miskala zarratin,sae kace ba yau zai angwance ba,


A hankali yake tattaka stairs ɗin, yayin da yake manna links ɗin hannun rigarshi,koda ya ƙaraso cikin falon,batare daya kalli kowannansu ba,ya nufi hanyar fita daga main falo ɗin,Murmushi abbansu ya saki aranshi yace"Rafayet kenan"

  batare da 6ata lokaci ba,Suka fito waje gaba dayansu,dama already motocinsu na nan a jere,Nan kowa ya buɗe motarshi ya shiga,A jere motocin suka fuce daga cikin gidan ɗauke da jiniya,

  

*💃💃💃ALHAMDULILLAH, A YAU JUMA'A  DUBBAN JAMA'A SUN SHAIDA ƊAURIN  AUREN RAFAYET SALAHUDDEEN HOSSEIN,TARE DA AMARYARSA  SEHRISH SALAHUDDEEEN ABUSUFYAN💃💃💃*,


bayan kammala sallar juma'a aka ɗaura auren nasu,Sae dai muce Allah ya basu zaman Lafiya atsakaninsu❤


*Finally Rafayet weds sehrish*🥳🥳🥳😘

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina 08103884440❤_





Fitowarta kenan daga cikin toilet taji gabanta ya faɗi rasss!da sauri takai hannu ta dafe saitin zuciyarta,ƙamewa tayi abakin toilet ɗin batare da ta motsa ba,jahad dake zaune saman darduma,da alama ta kammala sallah,jikinta na a sanye da hijab Maroon colour,ta ɗaga hannayenta sama tana addu'a,tunkan ta kammala ta lura da halin da Sehrish ke ciki,tana shafa addu'ar da sauri ta miƙe ta tunkareta,

    "Sehrish!lafiya meya faru ne? A ɗan ruɗe ta tambayeta,

   Sehrish kuwa sam ta gaza buɗe bakinta tayi magana,saboda yanayin da ta shiga,gaba ɗaya jikinta yayi wani irin sanyi,

    Ruƙo hannunta jahad tayi tare da cewa"sehrish!wai lafiya?ki amsa mun mana"? 

  Lumshe ido sehrish tayi a hankali ta shiga sauke ajiyar zuciya,daga bisani ta ɗan ware idanunta tana kallon fuskar jahad,dake tsaye agabanta,

  "Ko kin fama ciwonki ne"?

Girgiza kai sehrish tayi alamar a'a,tukunna tace"Jahad,ina fitowa daga cikin toilet ɗinnan,naji gabana ya faɗi rass,kuma naji jikina gaba ɗaya yayi mun sanyi,bansan meya jawo hakan ba,"

   "Ki cigaba da ambaton Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un acikin zuciyarki,In sha Allah babu abunda zai faru dake fa ce alkhairi,"ta ƙarasa maganar tare da janyo sehrish ɗin har izuwa gefen gadonsu ta zaunar da ita sannan tace"Ki kwantar da hankalinki,bari na ɗauko maki kayan da zaki sanya,".  

  Amsa mata tayi da toh,kafin ta mayar da idanunta kan farin towel ɗin dake sanye ajikinta ta ƙura mashi ido tana kallonshi zuciyarta cike fal da fargaba,ita kanta batasan dalilin faruwar hakan ba,


Jin an turo ƙopar ɗakinsu yasa tayi saurin ɗagowa don taga wanene,Hajiya azeema ce ta shigo hannunta ruƙe da shopping bag fara fuskar nan ɗauke da murmushi kamar wadda akayi ma albishir da gidan aljanna,murmushi sehrish ta saki da sauri ta miƙe tsaye tana gaisheta"Ina yini Aunty azeema,"

  Bata amsa mata gaisuwar ba sae cewa tayi"me nake gani haka?Amarya sanye da towel,ko baki san cewa an ɗaura ba"?

  A ruɗe sehrish tace"Aunty azeema,bangane me kike nufi ba,naji kince an ɗaura"?

  dariya azeema tayi tare da cewa"su6ul da baka ne fa,Bansan ma na faɗa ba,inaso ince ko an ɗaura abincin lunch ne,ashe azmeen bata a cikin ɗakin nan,"

    "Ina yini Aunty azeema,"jahad ce tayi maganar a yayin da take ƙarasowa wurinsu hannunta ruƙe da wasu riga da wando na turkey,da ta ɗaukko ma sehrish,

   "Lafiya lou jahad,in ce ko ke zaki sanya waɗannan kayan na hannunki,"

  Girgiza kai jahad tayi tare da nuna sehrish tace"A'a bani zan sanya ba,Sehrish na ɗauko masu don ta sanya"

   Cike da Zolaya Aunty azeeema tace"kin ta6a ganin inda Amarya ta sanya waɗannan kayan a ranar ɗaurin aurenta"?

  Cike da mamaki suka haɗa baki wurin cewa"AMARYA KUMA!!"?

   da sauri Azeema tace"Kai,mantawa fa nakeyi,wani film na kalla yanzu,to yarinyar cikin film ɗince aka ɗaura ma aure,a yau juma'a batare da saninta ba,abunne ya tsayamun arai shiyasa nake ta sako zancen,"

  Murmushi suka saki gaba ɗayansu,Jahad tace"Amma gaskiya na tausaya mata Aunty,meyasa za'ayi mata aure batare da saninta ba?To idan ita bata son Mijin da aka aura mata zata iya kashe kanta fa,'?yanayin yadda jahad tayi maganar fuskarta da alamun tausayi,

  Sehrish tace"Nima abunda nakeson cewa kenan,zai iya yiwuwa akwai wanda take so,hakan ba ƙaramin illa zaiyi mata ba,"

  Murmushi hajiya azeema tayi tana kallonsu,har sai da suka kai ƙarshen maganar tasu,sannan tace"kun ce wani abu anan,amma idan mijin ya kasance kamar babban yayan ku fa?kuna tunanin akwai macen da zata iya rejecting ɗin aurenshi"?

  Kallon juna suka kuma yi,kafin jahad tace"Gaskiya zaiyi wuya Aunty azeema,ae babban yayanmu na daban ne shi ko acikin maza,zan iya cewa ma duk macen da ta mallake shi ba ƙaramar mai sa'a bace,ƴar baiwar ce,kuma ita jinin nasara ce,da ƙafar dama ta shigo duniya,"

  Dariya sosai hajiya azeema tayi,jin yadda jahad ke zuzuta SGR,

   "Duk da ance abincin wani gubar wani,Zai iya yuwuwa ita yarinyar bata ra'ayin namiji irinsa,ba wai don bai kai ba...."

  Katseta hajiya azeema tayi da cewa"kamar ya kenan"?

  Sehrish taci gaba da cewa"yanzu kamar ace ita yarinyar,tafi son baƙin namiji dogo,sannan wanda baya tara sumar kai,kuma tafi son namiji mai yawan fara'a a fuskar shi,ko kuma ace ita yarinyar tafi son ta auri wanda bai ruƙe da muƙamin soja,Ya abun zai kasance?zatayi farin ciki idan ta samu kamar babban yayanmu,amma ta wani 6angaren baiyi dai dai da ra'ayinta ba,"

  Tana kai ƙarshen maganar,Azeema tace"kamar ke kenan!kina nufin bakison namiji kamar babban yayan ku"? Tayi tambayar cike da fargabar amsar da Sehrish zata bata,

  Sunnar dakai ƙasa sehrish tayi tana wasa da yatsun hannunta,yayin da fuskarta ke ɗauke da ƙayataccen murmushi,wannan ya tabbatar mata da cewa Tana RA'AYINSA,

  Dariya hajiya azeema tayi tare da ɗago da shopping bag ɗin dake hannunta ta miƙe ma sehrish,

  "Wedding gown ce aciki,tare da takalmanta,Zuwa bayan la'asar,da zarar an kammala sallar,Zanzo in taimaka maki wurin sanya rigar,sannan da kaina zanyi maki kwalliya," 

  A ruɗe sehrish ke kallonta don bata gane inda zancen nata ya dosa ba,ita kanta jahad abun ya ɗaure mata kai,

  Ganin yadda suka saki baki suna kallonta,yasa tayi saurin cewa"Oh,na manta ban sanar daku ba,Wani wasan kwaikwayone zamu yi yau acikin gidan nan don nishadi,that's why we choose you to be our bride in the drama,"

Wani irin farin cikine ya lullu6e sehrish,cike da zumuɗi ta kar6i bag ɗin,tana fadin"Amma abun zai ƙayatar sosai,dama inason inga na sanya wedding gown,Ashe da rabon yau in sanyata,

  Jahad tace"gaskiya abun zai bada citta,yau kam zamu sha hotuna,"

   "Har ma video idan kunaso zaku iyayi,Ni bari na wuce kitchen wurin Azmee,". 

  Tana ƙoƙarin fita,ta tuna da hosana da sauri ta juyo tare da kallonsu tace"Ya jikin hosana?naga sae bacci take tayi tunda nashigo,da alama jikin yayi sauƙi kenan"?

  Jahad tace"eh,taji sauƙi sosai,"

  "To,ku ya jikin naku"?

"Ae mu munji sauƙi,"suka haɗa baki wurin bata amsa,

  Jinjina kai tayi tare da kama hanyar fita tana cewa"Allah ya ƙaro sauƙi,"

Suka amsa mata da cewa"Ameen,"

   A saman gado sehrish ta ajiye shopping bag ɗin,sannan ta kar6i kayan da jahad,ta ɗauko mata batare da 6ata lokaci ba ta zura riga da wandon ajikinta Red colour ne ba ƙaramin kyau suka yi mata ba,gaban dressing mirror taje wurin da ta ajiye ribbom ɗinta before ta shiga wanka ɗaukarsa tayi tare da zura shi acikin hannunta,sai da tafara tattara gashin kafin ta sanya ribbom ɗin ta ɗaure shi tamau,

  "Ko dai in tashi hosana,tayi wanka itama?kin ga ko sallah batayi ba,"acewar jahad,

  Sehrish tace"ko baki tasheta ba,Yunwa zata tayar da ita,kibarta kawai,kada ki tado mana jangwamgwam,"

  "Baiwar Allah ni tausayi take bani,duk in na tuna yadda ta samu ciwon haukanta,sai inji idanuna sun cika tab da kwalla,"acewar jahad,

  Sehrish tace"Ni kaina ina tausaya mata sosai,Amma inaji araina cewa,Wata rana hosana zata dawo cikin hankalinta ne,sannu a hankali,Haka muke fata in sha Allah,

  Suna cikin magana,Jiniyar motocin dake shigowa cikin gidan ta karaɗe kunnuwansu,da ƙarar gaske har cikin dodon kunnuwansu,

   "Su babban yaya ne suka dawo daga sallar juma'a,bari in leƙa inga wankan daya ɗauka yau,!"

  Cike da farin ciki sehrish tayi maganar tare da juyawa ta nufi window,jahad ma tabi bayanta,janye labulan sukayi sannan ta zuge masu glass ɗin,Baza idanunsu sukayi suna kallon abunda ke wakana a farfajiyar gidan,

  Da gudun gaske motocinsu ke shararowa saman titin da zai kawo ka har wurin parking space na gidan,tun daga bakin gate titin ya fara,

  "Wlh abun kamar a shirin film" jahad ce tayi maganar,abun ba ƙaramin burgesu yayi ba,

   Lokacin da motocin suka ƙaraso ciki,a wani slow suka tsaya a jere,

   "Ko wanene zai fara fitowa,bari mu zuba ido muga wankan su babban yaya,"acewar sehrish,

  Jahad tace"Ni har na ƙosa,in ga wankan da daddynmu ya dauka yau da kuma wankan Baby junaid,"

    Suna cikin magana,wani gabjejen soja mai ƙirar samudawa,ya buɗe motar farko,Abbansu junaid ne ya fito,other side ɗin kuma Uncle Abusufyan ne,fuskokinsu ɗauke da murmushi,yadda kasan Gonar auduga,

Bayansu kuma sae motar da ke bin bayan tasu,Abokin Abbansu ne Tafeeda tare da abokin Omar,Adams da kuma shattima,daga motarsu sae motar Marshal Omar,zuba ido su Sehrish su kayi suna kallon Ya Omar dinsu,ganin ya fito daga cikin motar ya kuma zura hannayenshi acikin motar,jimm kaɗan sae gashi ya kinkimo junaid tare da aza shi asaman kafaɗarshi,

  Waro ido waje su sehrish sukayi Jahad tace"Mun shiga uku!meya faru da baby junaid ɗinmu?kodai bashi da lafiya ne?kalli fa yadda ya Omar ya ɗaukoshi asaman kafaɗarshi,"

   "Yanzu haka rigimarshi ce,nasan junaid sarai,har goyashi zai iya cewa ayi,yadda yake jin kanshi kamar jinjiri,"Sehrish ce tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya,

  Jahad tace"wannan fa ba abun dariya bane,tunda kika ga an ɗaukoshi asaman kafaɗa to tabbas akwai abunda ya faru dashi,nidai Allah yasa kafiyarshi ƙalau,

  Sehrish na ƙoƙarin buɗe baki tayi magana,ta hango Amstrong ya fito daga cikin motar Sgr,da sauri ya zagaya tare da buɗe mashi motar,zuba ido tayi tana jiran fitowarshi,

  A hankali ya zuro ƙafarsa ɗaya waje,almost 5 mins,tukunna ya ƙarasa fitowa daga cikin motar gaba ɗaya,

  Gabanta ne taji ya faɗi rass!ba ita kaɗae ba hatta jahad ya tafi da imaninta,a rude sehrish ta shiga yarfa hannu tama rasa abunda zata ce,just speechless,

  Jahad ce tayi ƙoƙarin cewa"Tabarakallahu Ahsanul khaliqin!gaskiya babban yayanmu duniya ne!Irin wannan ɗaukar wanka haka!Ni tunda nake a rayuwata ban ta6a ganin mutumin da shadda tayima kyau sosai irin Babban yayanmu sae kuma Ya Omar,Wankan shadda ba ƙaramin kyau yake yi masu ba,ko don suna da ƙirar jiki mai kyau ne,!koda yake shima fa Ya yusouf ba ƙaramin kyau shadda takeyi mashi ba,kinsan shi wani irin sanyin kyau ne dashi na miskilai,hatta su twins da fawan kowa ma yana yin kyau idan suka sanya shadda amma ba kamar yaya Rafayet ba,da ya Omar,junaid kuwa na dabanne shi,"

   Jahad sae faman zuzuta su takeyi,duk a tunaninta Sehrish na sauraronta,batasan cewa sehrish ta lula wata duniyar ba,gaba ɗaya Sgr ya tafi da Imaninta,ya janye hankalinta,babban farin cikinta shaddar daya sanya ajikinsa,saboda tana kwaɗayin son tagan shi sanye cikin kayan hausawa,kuma ta gane cewa shaddar nan ce wadda ta ta6a dauko mashi a kwanakin baya,Ya ƙi sanyawa saboda baya sanya kayan hausawa sai nasu na turawa,

   Yadda kasan tauraro acikin taurari haka ya bayyana,fuskar nan babu annuri,ya tamketa tamau,kamar wanda aka ɗaura ma aure da Mutuwa,hannunshi na ruƙe da hular da abbansu ya sanya mashi kafin su shiga masallaci,don a ganshi da mutunci,amma ɗan tahalikin nan kamar jira yakeyi a kammala sallar,suna fitowa daga masallacin bayan ɗaurin auren ya tumbuƙe hular,don shi arayuwarshi ya tsani duk wani abu da zai rufe mashi sumar kanshi,ba ƙaramin ji yake da ita ba,zaiyi wuya kaga Sgr da hula akanshi,sai dai Facing cap ko kuma in ya sanya jacket mai hula ajikinta shine zakaga ya sanya hula,hatta shaddar dake ajikinshi atakure yake da ita duk da shi kanshi ya shaida irin kyan da yayi acikinta,ya saba da kayansu marasa nauyi shiyasa yake jinshi duk atakure,Ƴan uwanshi kowa farin ciki yake yi gashi ya hana kowa ya furta kalmar nan Wato ango kasha kamshi,ya tsani yaji an ambaci hakan,ko kuma a kirashi da sunan Ango,kowa so yake ya ɗanyi mashi wasa da dariyar nan da ƴar zolayar nan da akeyi ma angwaye amma rafayet ya hana hakan!yaƙi jinin akirashi da sunan ango,


Gaba ɗaya suka tunkari ƙopar da zata sadaka da babban palourn gidan,"

   Jiki asanyaye sehrish ta zuge glass ɗin windown,ta gyara labulen,

     Zuba mata ido jahad tayi tana kallonta,ganin yadda ta sauya lokaci guda kamar wadda aka zarewa lakar jikinta,

  Gefen gadon ta koma ta zauna,sam tagaza samun natsuwa acikin zuciyarta,ganin rafayet da tayi ya fama mata ciwon dake acikin zuciyarta,

  "Sehrish wai meya faru ne?Yanzun nan fa muke raha dake,amma lokaci guda kin canza,ko baki lafiya ne"? Ta ƙarasa maganar,tare da samun wuri gefen sehrish ɗin ta zauna,

   Muryarta tamkar zata yi kuka tace"bakomai,kawai zuciyata ce har yanzu bana jin daɗinta,"

   "Dan Allah ki kwantar da hankalinki rishi,Ki saki jikinki,ko zaki kwanta ne?ki ɗan samu bacci may be Ki samu natsuwa acikin zuciyarki,"cike da kulawa jahad keyi mata maganar,

..Sehrish na ƙoƙarin buɗe baki tayi magana,suka ji an kwankwaso ƙopar ɗakin nasu,

  Da sauri Jahad ta miƙe tare da tunkarar ƙopar tana tambayar wanene,

  Daga waje taji ance"Daddynku ne"

Jin haka yasa jahad yin saurin buɗe mashi ƙopar,

   Shigowa ciki Abusufyan yayi fuskarshi ɗauke da ƙayataccen murmushi,zuba mashi ido jahad tayi tana kallonshi baki asake,from head to toe,irin kallon ƙurullar nan,

  A ruɗe tace"daddy!kaine!"

  Dariya ya ɗan saki tare da cewa"Ni ne mana,me kika gani"

  A susuce tace"Wow daddy kayi kyau Over,kamar matashin saurayi ɗan shekara ashirin da biyar,"

  Wannan maganar ta jahad,ba ƙaramin dariya ta bashi ba,ta wani 6angaren yaji daɗin yabon da tayi mashi,

   Miƙewa Sehrish tayi jin maganar daddynsu nufo wurinsu tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Masha Allah,daddy kayi kyau sosai Allah,kamar irin sabbin ƴan dubu dubu ɗin nan,kasan yadda suke da ɗaukar ido,ga kyau,gasu da burgewa,"

  Fashewa da dariya Abusufyan ya kuma yi bakin shi yaƙi rufuwa sai faman hura mashi kai sukeyi,

  daƙyar ya samu ya tsagaita da dariyar yace"har kun tuna mun da mommyn ku,duk in naje ɗaukarta daga islamiyya in aka tashe su,Ƙawayenta suyi ta santin wankan da na ɗauka,Har leƙena akeyi ta cikin mota ana nuna ni ga mijin abu nan yazo,Ya iya ɗaukar wanka,ya haɗu sosai,Mommynku ta tsani taji suna yabona,abun haushi yake bata,idan na kuskura na fito daga mota ina jiranta,haka zasu zagaye ni suna kallona,harma suyi mun magana mu gaisa,da zarar abu tazo fuskarta a ɗaure,a fusace take ruƙo hannuna ta tura ni cikin mota,mu tafi,hakan ba ƙaramin dariya yake bani ba Inajin daɗin kishina da takeyi sosai,amma kishin da takeyi mun yajawo rabuwarmu da ita ba don naso ba......"kasa ƙarasa maganar yayi,saboda wani abu da yaji ya taso mashi mara daɗin ji acikin zuciyarshi,tuni idanunshi sun cicciko da kwalla,

  tsananin tausayin Abbansu ne ya kamasu duk jikinsu yayi sanyi,daƙyar jahad ta iya buɗe baki tace"daddy,dan Allah kayi haƙuri da duk abunda ya faru tsakaninka da Oumman mu,nasan cewa abun yana yi maka ciwo acikin zuciyarka,Oumman mu bata kyauta maka ba,gashi sanadin hakan ta jefa rayuwarta cikin haɗari da kuma rayuwarmu,sau dayawa takan zauna tayi ta kuka,musamman da daddare ko runtsawa bata iya yi,kullum cikin ambaton sunanka takeyi tana cewa haƙƙin Abusufyan ne yake bibiyar rayuwarta,na cutar dashi sosai,Mijina yana so na amma na butulce mashi,saboda baƙin kishi na,nayi danasanin rabuwa dashi sosai,Ya Allah ka yafemun,mu lokacin duk bamu san abunda take nufi ba...."tuni hawaye sun shiga wanke mata fuskarta,itama sehrish hawayen ne suka soma shararowa daga cikin idanunta,Hannu Abusufyan ya sanya tare da janyo su ya rungumesu sosai ajikinshi,sae lokacin ƙwallar dake cike taf cikin idanunshi ta shiga wanke mashi fuskarshi,muryarshi a kasalance ya soma magana"Oummanku yarinya ce sosai,Ko a lokacin ban ruƙe ta a raina ba,saboda akwai ƙuruciya sosai atattare da ita,Nasha wahala sosai akanta,saboda Allah ya jarabce ni da tsananin sonta,ina sonta sosai,har yanzu soyayyar da nake yi mata na nan yadda take,babu abunda ya canza,Nayi kukan zuciya a lokacin dana rasa ta,kamar in zauce,lokacin dana ji zancen aurenta da sayyadi,Allah kaɗae yasan ƙuncin dana ji acikin zuciyata,bakomai nake tunawa ba,fa ce Amanarta da mahaifinta ya damƙa mun,ya yarda dani sosai baba buzu,yasan cewa banajin magana,ga ƙuruciya dake ɗibana amma a haka ya toshe kunnuwansa Ya aura mun ƴarsa,Naji daɗi sosai,A lokacin kamar kamar me,Allah ya jiƙanshi,

  Atare suka amsa mashi da Ameen,ɗagowa dasu yayi daga jikinshi yana ƙoƙarin kai hannu ya share hawayen dake zuba akan fuskarshi,da sauri suka riga shi sanya tafukan hannyensu suna goge mashi hawayenshi,

  Murmushi ya saki,don ba ƙaramin daɗin hakan yaji ba,

   "Dama nasani wata rana zaku share mun hawaye na,gashi Allah ya nuna mun ranar da raina kuma da lafiyata,"

   Yayi maganar tare da sanya hannayenshi duka biyu,asaman fuskokinsu yana share masu hawayensu,bayan ya kammala goge masu hawayen,yace"oh namanta,ban baku tsarabar masallaci ba,"da sauri ya zura hannunshi cikin aljihun wandon jikinshi,

  Farar leda ce ya curo mai ɗauke da dabino da goro,

  Miƙa masu yayi tare da cewa"hada aya da kwakwa nasiyo maku amma ta hosana ce ita kaɗae zan bamawa,wannan dai gashi ku raba a tsakaninku,"

  Kar6ar ladar jahad tayi fuskarta ɗauke da murmushi,sehrish tace"dama na lura kafi ji da hosana,"

   Abusufyan yace"eh mana,saboda itace autarku a yanzu,nafi sonta,kuma nafi ji da ita,"

  Zumbura baki sehrish tayi tare da cewa"yanzu duk irin cizon da tayi mana a jikinmu baka gani ba?

  "Nagani mana,ae gwaggo ta tabbatar mun da cewar ba yin kanta bane,Ya sayyadi ne yazo da suffar kura yayi maku wannan aika aikar....."karasa maganar yayi tare da fashewa da dariya,suma dariyarce ta kufce masu,

    Wucewa cikin ɗakin nasu,yayi tare da zama daga gefen gadon yana kallon hosana dake kwance tana bacci,baki a buɗe,

   Da sauri ya sanya hannunshi,a cikin aljihun ya curo ledar dake ɗauke da yankakkar kwakwa da ƙullin aya acikinta,

    Kwakwar ya ciro,cike da tsokana ya zurata cikin bakin hosana,cikin bacci hosana ta kama kwakwar ta shiga taunarta abakinta,

  Dariya sosai sukayi abun ba ƙaramin nishaɗi ya basu ba,

   Wuri suka samu suka zauna,suna kallon tsokanar da Daddynsu ke yi ma Hosana,

   gaba ɗaya ta cinye kwakwar daya sanya mata abakinta,wata kwakwar ya kuma curowa,tare da zura mata abakinta,kamar wata kura haka ta kama kwakwar tana gartsa,tana taunewa acikin bakinta,

  "Daddy,ɗan janye kwakwar mu gani ya zatayi,"acewar jahad,

  A hankali ya shiga ƙoƙarin janye kwakwar daga cikin bakinta,ta cije ta da haƙoranta,yana ja tana rurruƙeta,dariya sosai Abusufyan yake yi abun ba ƙaramin nishaɗi yake sanyashi ba,

   Da ƙarfi ya janye kwakwar aikuwa a firgice hosana ta farka,fuskarta a yamutse,zuba mashi ido tayi tana kallonshi,muryarta a kasalance ta ambaci sunanshi"daddy!"

  "Na'am,hosana,"ya amsa mata,yunƙurawa tayi dakyar ta miƙe daga zaune tana ƙare mashi kallo kafin ta kwantar da kanta asaman kafaɗarshi,tana faman lumshe ido saboda baccin da tasha,

   "Kin tashi lafiya?ko baccin bai isheki bane?

  A shagwa6e tace"Ya isheni,yunwa ma nake ji,Cikina babu komai,gashi ko wanka banyi ba,Su jahad duk sunyi wanka basu tashe ni ba,balle inyi nima,"ta ƙarasa maganar tana kallonsu sehrish dake a bakin gadon,murguɗa masu baki tayi tare da harararsu,

   "Shikenan,bari in na fita yanzu zanyi ma azmee magana,sae ta shirya maki lunch ko"?

..ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

  Miƙa mata ledar kwakwar yayi"kar6i nan,tsarabarki ce,ta masallaci kada ki ɗanma kowa kinji ko"?

  Fuskarta ɗauke da murmushi ta kar6i ledar daga hannunshi

     "Nagode sosai daddyna,kuma bazan ɗan masu ba,"

   Wurga mata harara jahad tayi tare da cewa"Sannu ko?daddynmu zakice ba daddyna ba,ae bake kaɗae bace a wurinshi ba,"

  Gatsina mata hanci hosana tayi tare da ƙara rungumo Abusufyan ajikinta don suji haushi,hakan ba ƙaramin dariya ya bashi ba,

   "Daddy,ƙamshin turaren jikinka akwai daɗi sosai Allah,"tayi maganar tare da sanya hancinta ajikin rigar shaddar jikinshi tana shaƙar ƙamshin turaren kamar wata mayya,

   "Idan kinaso ma,zan ɗauko maki kwalbar turaren gaba ɗaya,sae ki dinga shafawa kema hakan yayi maki"?

   Girgiza kai tayi"a'a daddy,kabarshi kawai,Ya Omar ya hanani shafa turare,idan na shafa wannan turaren zaiyi ƙamshi sosai,kuma idan Yaji bazaiji daɗi ba,zaice hosana bakijin maganata ko?to daga yau babu ni babu ke,ni bazan zauna da mai kunnan 6era ba,'

  Fashewa da dariya su jahad sukayi,tuni hosana ta ɗaure fuskarta tana harararsu,Abusufyan yace"yayi kyau babyn Omar,yana da kyau ki dinga jin maganarshi,kina yi mashi biyayya,kada ranshi ya 6aci,"

   Cike da jin kunya hosana ta janye jikinta daga na Daddynsu,ta janyo pillow ta rufe fuskarta dashi,

   Wayar Abusufyan ce ta shiga yin ringing,har lokacin fuskarshi ɗauke da murmushi,yace"Bari na shiga ciki,zansa azmee ta shirya maku launch,"

  "To daddy,"suka amsa mashi da sauri ya fuce,


   *JUNAID ROMEO*


Tashin hankalin da ba'a sama shi date,Tun wurin ɗaurin aure da junaid yaji sanarwar ɗaurin auren Babban yayansu,tare da Rishi ɗinsa,acikin masallacin ya yanke jiki ya faɗi a sume,saboda baisan da zancen ɗaurin auren ba,kwatsam yaji ana sanarwar,


A bedroom ɗinsa Omar ya kwantar dashi,bayan sun yayyafa mashi ruwa ya farfaɗo,koda ya buɗe idanunshi yaga Abbansu ga kuma yayyansu Isha da Abbas,ga Marshal Omar da sauran matasan duk suna tsaye akanshi,Fashewa yayi da matsanancin kuka mai cin rai,Cikin shesshekar kuka yace"Wayyo Allah na!Wlh an cuce ni,Abba kana sane da cewar ni ke son sehrish amma ka aura ma babban yayan mu ita,wlh bazan yarda ba,Ae ni na fara sonta,don me za'a aura mashi ita!ashe baku sona,hakanan kuke nuna mun soyayya,Wlh nidai bazan yarda ba,abba ka cuce ni sau nawa ina faɗa maka cewar inasonta,Ita nake da burin in aura amma....." bai ƙarasa maganar ba,Omar ya daka mashi tsawa wadda ta gigitar dashi,

   "Rufe ma mutane baki junaid!shashasha kawai!Abban ne kaka cewa ya cuce ka?kai ko kunyar yin zancen aure agaban mu baka ji?ubanwa zaiyi maka aure da ƙananun shekarunka?kai da ita waye zai raini wani in anyi maku auren"?

  Tafin hannayensa ya sanya tare da rufe fuskarshi,yana cigaba da kukan kuma hakan baisa ya daina sambatun da yake yi ba,

   "Ya omar ba zaka gane bane,Abun da ciwo,wlh ina sonta sosai,ina son rishi,kuma itama tana sona,wlh ba babban yayanmu take so ba,Ni take so,don me za'a aura mata shi..."

  A zafafe Omar ya zabura zai kai mashi mari a kan fuskarshi,da sauri Abba ya ruƙo hannunshi tare da cewa"Kuyi mashi uziri,wlh nasan yana sonta sosai,banta6a tunanin cewa junaid ya san so ba,ni duk a tunani na wasa yake yi mun,ashe dagaske yakeyi,dole yaji ciwo acikin zuciyarshi saboda ya saba da ita sosai," muryarshi a sanyaye yayi maganar,Abun ya ta6a mashi zuciyarshi,tsananin tausayin junaid ne ya kamashi,

   Shi kanshi marshal Omar jikinshi ba ƙaramin sanyi yayi ba,kowa yasan da irin shakuwar dake atsakaninshi da sehrish amma ba suyi tsammanin cewar dagaske sonta yakeyi ba,

  Hatta su ishaq dake tsaitsaiye cirko cirko agaban gadon nashi ba ƙaramin tausayi ya basu ba,duk yabi ya burkice,fuskar nan tayi jawur da ita,jijiyoyin jikinshi duk sun bayyana,

   Adai dai lokacin da Abusufyan ya ƙaraso kopar ɗakin junaid ɗin,kasa shiga ciki yayi saboda jin maganganun da sukeyi aciki,hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,jin cewar junaid sehrish yake so,kuma adalilinta ne ya suma a masallaci,

   Duk yadda suka so su shawo kan junaid da lallashi don yayi shiru abun ya faskara,hancinsa har ya fara bleeding,hankalinsu yayi mugun tashi,

    Matsawa sukayi kusa dashi suna lallashinsa,Ja da baya ya dinga yi asaman gadon har ya ƙure ma head board ɗin gadon,sautin muryarshi ashake saboda tsabar kukan daya sha,

  "Ku rabu dani,bana son ganin kowa!ba kunfi so na mutu ba!to zan mutu ne yanzun nan sae hankalinku ya kwanta,"

  Hawaye ne suka cicciko tab a idanuwan kowannansu,

  "Junaid dan Allah kayi haƙuri,Allah ya riga daya ƙaddara faruwan hakan,dama can ita ba matarka bace," Acewar Abbas,

  Girgiza kai ya shiga yi yana cewa"yaya abbas,bazaku gane bane,bakusan yadda nake ji acikin zuciyata bane,tafarfasa take yi mun,wlh bazan iya jurewa ba,inason rishi sosai,idan har kuna so kuga farin ciki na,to akwance ɗaurin aurenta da babban yayanmu a aura mun ita shine kawai,in ba haka ba mutuwa zanyi,Wayyo Allah rishi ɗina,"yana magana yana shessheƙar kuka,

    Abbas yace"Calm down ur mind junaid,akwai mata da yawa agari suna yawo kyawawan gaske,ga ƙanwar matata nan Amal,baka ganta ba ƴar ƙarama dai dai kai,idan kayi hakuri zaka samu wadda tafi ta ma,"

  Bubbuga kafafunshi yayi asaman gadon tare da cewa"Ya Abbas wlh banson kowace mace in ba ita ba,Sehrish itace juliet ɗina ita kawai nakeso,kodai aban rishi ko kuma in haɗiyi zuciya in mutu,"to fa,!junaid ya tashi hankalin kowa,yaƙi saurarar kowa,yau an ta6a romeo shugaban ƴan soyayya,

   Cikin lallashi Abbansu ya ambaci sunanshi"Babyn Abbanshi,"

  Wani irin kallo ya wurga ma abban nasu idanuwan nan sunyi luhu luhu saboda tsabar kukan daya sha,

   "Ni ba babynka bane,Romeo ɗin mommynsa ne,saboda baka sona Abba,"ya karasa maganar yana faman matse kwallar dake sharara daga cikin idanuwanshi,

  Shiru Abbansu yayi bai ƙarasa maganar tashi ba,junaid yafi jin haushinshi akan kowa,saboda yasan da cewar yana sonta amma ya ɗaura mata aure,duk da shi bai ɗauki maganar tashi serious ba,sae yau daya haukace masu,

   Turo ƙopar Abusufyan yayi jikinshi duk ya mutu,tsabar tausayin junaid ne ya kamashi,

  Juyowa suka yi suna kallonshi,matsa mashi hanya sukayi ya wuce,har izuwa gaban gadon junaid din,

   Zuba mashi ido yayi yana kallonshi,duk ya fita cikin hayyacinshi ya zama abun ban tausayi,wannan ya tabbatar mashi da cewar ba ƙaramin son sehrish yake yi ba,

  ɗagowa junaid yayi tare da kallon Uncle ɗin nasu,Cikin shessheƙar kuka yace"Un..cle!hada kai aka ɗaura ma rishi ɗina aure da babban yayan mu,bayan kunsan cewa ina sonta sosai,"

   Hawa saman gadon abusufyan yayi tare da janyo junaid ya rungumoshi ajikinshi yana ɗan bubbuga bayanshi da hannunshi,cikin lallashi yace"Junaid,Ni bansan cewa kana sonta ba,da banyi kuskuren aura ma rafayet ita ba,kasan cewa inason ka sosai,kowa ma yana sonka,kuma zamu iya yin komai saboda farin cikinka,hatta rayukan mu ma zamu iya badawa domin ceto rayuwarka,balle kuma ƴar uwarka?sae ita zata gagara?"

  "Amma..uncle..meyasa ku ka ɗaura mata aure da babban yayan mu?maimakon ni"?daƙyar yake magana,

   "Kayi haƙuri junaid,dama Allah ya ƙaddara cewar ita ba matarka bace,Matar babban yayanku ce,"

   ɗagowa yayi daga jikin Abusufyan din fuskarshi jaga jaga da hawaye hada majina,yana kallon uncle ɗin yace"yanzu kuna nufin cewa,babu ni babu rishi?in haƙura da ita kawai?kun za6i ku rasa ni kenan"?

  ruƙo hannunshi abusufyan yayi tare da sassauta muryarshi yace"haba junaid,in sha Allah ba zamu rasa ka ba saboda sehrish,ae ba ita kaɗai bace ba,Ko ka manta cewar su ƴan ukune?kuma kamanninsu ɗaya,Idan kayi haƙuri zan baka auren ɗaya daga cikinsu,"

  Da sauri Marshal Omar ya katse mashi hanzarinshi da cewar"Wacce acikinsu,"?

  dariya abbansu yayi ganin yadda omar ya ɗan tashi hankalinshi,

  Abbas yace"Uncle,kada fa kayi mashi alƙawarin auren ɗaya daga cikinsu,saboda junaid bai da wayau baisan wasa ba,kuma koda za'ayi mashi aure ba yanzu ba,sae yayi hankali nan da in ya kai shekara talatin,"yana kai ƙarshen maganarshi,Ishaq ya ɗaura da cewar"Bazai yiwu ba ayi ma junaid aure a yanzu,bayan ga yayyensa nan duk sun manyanta kowa na bukatar aure,yayi haƙuri dai akwai matar abokina na nan,yanzu haka tana dauke da ciki,idan ta haifi jinjirin muka ga mace ce,sae ayi masu magana,su ajiye mashi ita,in ta girma lokacin yayi hankali sai a aura mashi ita,"

  Suna cikin maganar nan,Junaid ya sume,a jikin Abusufyan,a ruɗe abusufyan ya shiga jijjiga shi yana kiran sunanshi"Junaid!Junaid!!"

  Hankalin Abbansu atashe yace"Duk laifinku ne!meyasa bazakuyi shiru da bakinku ba,gashi nan ya ƙara sumewa,kuma ina da tabbacin cewar maganganun da kuke gaya masa ne suka ƙona mashi rai,"

  Hannu Omar yasa tare da ɗauko bottle water ɗin dake ajiye saman side drawer dinsa,ya cire murfin tare da mika ma abusufyan,A hannu ya tar6o ruwan sannan ya watsa mashi a fuskarshi,

  Dogon numfashi yaja tare da sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya,

  Shafa fuskarshi Abusufyan yayi tare da cewa"Junaid,"

   Tunkafin ya buɗe idanunshi yace"Uncle mutuwa zanyi,"

  "Junaid dan Allah kadaina kira mana mutuwa,Indai kan sehrish ne,NI NAYI MAKA ALƘAWARIN CEWA ZAN AURA MAKA ƊAYA DAGA CIKINSU IN HAR TANA SONKA,"

  Muryarshi a kasalance yace"Uncle nasan wasa kake yi mun,kada kayi mun alƙwarin da bazaka iya cika mun ba,Zan haƙura kawai in rungumi ƙaddarata,"_

   Wannan maganar da junaid yayi ba ƙaramin kashe masu jiki tayi ba,

Tuni hawaye suka cicciko a idanuwan Abusufyan,muryarshi na kerma yace"meyasa kace haka junaid"?

  "Uncle,bani da wayau,ni yaro ne har yanzu,kowa yana yi mun kallon sakarai,kuma bani da aikin yi,a haka zaka bani auren ƴarka""?

   A hankali wasu siraran hawaye suka shiga gangarowa a saman fuskar Abusufyan,daƙyar ya iya buɗe baki yace"Junaid!duk rashin wayonka baka kaini ba lokacin da ina yaro,bana jin magana har sa'insa nake yi da Mahaifiyata,na iya rashin kunya saboda ni bana jin kunyar kowa,ni ina mu'amala da mata muje party,muje night club,Ka faɗamun ɗaya daga cikinsu wanne kake yi?

  "Ko ɗaya bana yi"ya bashi amsa,

Murmushi abusufyan yayi kafin ya cigaba da cewa"kana da kyakkyawar zuciya junaid kai mutumin kirki ne,kana son kaga farin ciki a fuskar kowannan mu,saboda me Ni zan gaza sanya ka farin ciki?Duk da banajin magana amma ahaka Mahaifin Oummansu Sehrish ya bani auren ƴarsa,Nima don haka daga yau ka sanya aranka cewar na baka Auren JAHAD!idan ma akwai mai sonta cikin yayyenka sai dai yayi haƙuri yabar maka,

   Wani irin Farin Ciki ne ya lullu6e junaid,lokaci guda ya nemi kukan da yake yi ya rasa,bashi kaɗae ba hatta sauran ƴan uwan nasa dake tsaye a wurin ba ƙaramin daɗi suka ji ba,Musamman Abbansu,Yaji daɗi har cikin ranshi,

   Cike da zolaya abusufyan ya kallesu tare da cewa"Ko akwai mai ja acikin ku ne"?

   Fashewa sukayi da dariya gaba ɗayansu,tare da haɗa baki aurin cewa"Mu mun isa?Uba ya mallaka ma ɗansa auren ƴarsa?waya isa yaja daku?ae magana ta ƙare"

   Sae lokacin junaid ya fashe da dariya har fararen haƙoransa suka bayyana masu ɗauke da matsakaiciyar wushirya siririya,mai kyan gaske,

  "Surukina,fadamun me kakeso yanzu"?

  Cikin shagwa6a junaid yace"Maganin ciwon kai,sannan ina jin yunwa sosai,"

   "Bari inyi ma jahad magana takawo maka,hakan yayi maka"?

  Cike da jin kunya junaid ya rufe fuskarshi da tafukan hannayenshi,yana dariya ƙasa ƙasa,

   Zolayarshi suka shiga yi,har sai da suka sanya shi farin ciki sosai,sannan suka bar cikin bedroom ɗin nashi,ya kasance shi kaɗae ne acikin ɗakin kwance asaman gadon,kamar wani zautacce sae faman sakin murmushi yake yi,bakinshi yaƙi rufuwa,

   Turo ƙopar ɗakin nashi,akayi da sauri yakai idanunshi wurin,Azmee ce ta shigo hannunta ruke da tray,lunch ne ta shirya mashi,ƙarasawa tayi tare da ajiye mashi tray ɗin saman front table din gadonshi,

  Mikewa yayi daga zaune,yana gaisar da ita,

   "Ina yini Aunty azmee,ya aiki,"

  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Lafiya lou junaid Alhamdulillah,"

   Ta karasa maganar tare da ɗaukar plate ta buɗe warmer mai dauke da chicken pepper soup serving spoon ta sanya tana ɗaukar cinyar kazar tana sanya mashi a plate,kallonta yakeyi sae ya dinga ganin kamar jahad ce,saboda tsabar son ya ganta musamman da yaji an mallaka mashi ita,

    "Idan ka kammala ci,ga magani nan Uncle ɗinku ne yace na baka kasha,"tayi maganar tana nuna mashi maganin dake ajiye asaman tray ɗin,

   "Nagode sosai Aunty azmee,"

 "Na lura kamar kana cikin farin ciki sosai yau,"_

   Murmushi ya saki tare da cewa"Aunty azmee,Am so,so happy today,Uncle abusufyan ya bani auren Jahad,Ya mallaka mun ita,"

  Waro ido waje Azmee tayi cike da mamaki tace"Wai dagaske"?

   ɗaga mata kai yayi alamar eh,Hannayenta ta daga sama cike da tsantsar farin ciki tace"Alhamdulillah!Allah na gode maka!ashe dae ina da rabon ganin aurenka junaid,Allah ya nuna mana lokacin,"

  "Ameen ameen,"ya amsa mata,

 "Dan Allah kaci abincin nan sosai,kaci ka koshi angon jahad,"

  Rufe fuskarshi yayi yana dariya ƙasa ƙasa, itama dariyar ce ɗauke akan fuskarta har ta kammala zuba mashi abincin,sannan ta kama hanyar fita daga ɗakin,sae da junaid yaji alamun ta bar bedroom ɗin nashi sannan ya buɗe fuskarshi yana faman sakin murmushi



  *Haroon*


Motarshi na qoqarin shiga cikin hotel yaji an ambaci sunanshi"Ya Haroon,"gabansa ne ya faɗi rass jin Muryar mutum mai mahimmanci a wurinshi,da sauri yaci burki tare da zuge glass ɗin motar a slow,


   Tsaye take jikinta na asanye da Uniform,yadda kasan mahaukaciya,gashin kanta duk ya tarwatse ya hargitse,babu gyara,ƙafafunta babu takalma,tayi buɗu buɗu da ita,waro ido waje haroon yayi yana kallonta,tamkar a mafarki,kusan minti 5 kafin ya buɗe motar,ya fito har lokacin kayan jiya ne ajikinshi,a hankali yake tunkararta yana ƙare mata kallo,ita kuwa da gudun gaske ta tunkareshi,faɗawa tayi saman ƙirjinshi tare da zagayo da hanneyenta ta bayanshi,ta ƙanƙame shi sosai,lokaci guda ta fashe da matsanancin kuka,

  Lumshe idanunshi yayi tare da sanya hannunshi abayanta,yana ɗan bubbuga bayan nata,a hankali ya ambaci sunanta"AMRISH"

   Boss tabarku da tunani,Bashin friday ne na biyaku,kowa yasan cewa weekend banayin posting,Don haka mu haɗu On monday,in Allah yakaimu da rai da lafiya,don jin Yadda zata kaya👍

    *SALON NA DABANNE🔥*

*kada fa ku manta har yanzu muna acikin Littafin Abban Sojoji ne Takun ƙarshe wanda Ni hafsat Bature Na rubuta*








   

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina pls banda kiran waya,bana amsa shi,Just message za'ayi mun ta whatsapp in sha Allah zan amsa,don bana shariya indai ina online 08103884440❤Masu kirana ƙarfe goma na dare kuna son jamun wlh😡_





Cikin shessheƙar kuka ta amsa mashi"na..am yaya haroon" raba ta yayi daga jikinshi tare da sanya hannayenshi ya tallabo fuskarta,daƙyar take iya buɗe idanunta waɗanda ke jike sharkaf da hawaye,zuba mata ido yayi yana kalllonta,fuskarta duk ta kumbura tayi haske,gashi ta ɗan yi rama wannan ya tabbatar mashi da cewar tana cikin matsananciyar damuwa,yana ƙoƙarin buɗe baki yayi mata magana idonshi ya sauka akan hannunta,kanula ya gani,a ruɗe yace"Amrish!Wannan fa?faɗa mun meya faru?Kinyi rashin lafiya ne"?

   daƙyar ta iya buɗe baki tace"Poison nasha,Saboda na gaji da zaman duniyar nan,Mommy ta 6atamun rai,ba ta sona ba ta damu dani ba......".

  Bata ƙarasa maganar ba,yaja hannunta izuwa wurin motarshi,buɗe mata motar yayi ta shiga back seat ta zauna sannan shima ya shiga mazaunin driver,shiga cikin Hotel ɗin ya ƙarasa shiga da ita,bayan yayi parking ɗin Motar ya fito ya buɗe wurin da amrish take ya shiga daga ciki,

   Cikin sanyin Murya yace"faɗamun abunda ya faru tsakanin ki da ita"?

  Nan ta labarta mashi abunda ya faru tsakaninta da mommynta tun daga farko har ƙarshe,

     "Amrish!ashe baki da hankali?saboda kawai ta gaya maki wannan ƴar maganar sai ki nemi kashe kan ki?suwa kika yi ma asara?

  Shiru tayi yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,

    "So kike narasa ki ko"?da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a,

   "Bazan ƙara ba,yaya haroon mommy ce ta 6ata mun rai,kuma ni bansan zama wurinta,Na tsaneta bata kwanta mun araina ba,dan Allah kada ka mayar dani wurinta,ka kaini gidanku kawai in zauna tare daku,"

  Waro idonshi ya ɗan yi kafin yace"gidan mu!in kaiki a matsayin wa?so kike kija mun?yayyena fa gaba ɗayansu maza ne kuma sojoji ne,bazaiyiwu ba ki zauna acan,"

  Fuskarta tamkar zata yi kuka tace"Ya kake so nayi da rayuwata ne?ni babu wurin da nake jin daɗin zama,Ka kaini kawai gidan ku in zauna,idan ina ganinka sai hankalina yafi kwanciya,amma ni bazan koma wurin mommy ba,in ba so kake ka rasa ni ba gaba ɗaya,"tayi maganar aɗan shagwa6e,

   Shiru ya ɗan yi yana tunanin mafita,don kuwa ya santa da baƙar zuciyar nan ta gado,in har yaƙi yi mata abunda take so to tabbas zata aikata abunda ta faɗa ne,

   Ajiyar zuciya ya sauke tare da kallonta yace"It's Okey,zan kai ki gidan mu amma kafin nan,Ki fara zama a wurina,Ni abunda ya ɗaure mun kai,taya ya har kika gano inda nake?"

  Sae lokacin ta ɗan saki murmushi akan fuskarta,kafin tace"Ae nasan duk wani wuri da kake zuwa,kaine baka sani ba....".  

   "Wato bibiyata kikeyi ko"? Dariya tayi,tana ɗaga mashi gira,

    "Zanyi maganinki,mai ɗan kumatu,"

  Sosai ya shiga zolayarta,har sai da yaga farin ciki akan fuskarta,atare suka fito daga cikin Motar hannunshi acikin nata,wucewa yayi da ita VIP,inda room ɗinsa daya kama a hotel ɗin yake,bayan sun shiga ciki wanka ya sanyata tayi sannan ya daukko mata kayan da zata sanya ajikinta,dama ɗakin nasa na sharholiyarsa ne,akwai duk wani abu da mace zata buƙata,tunda nan yake kawo ƴan matansa da samarinsa duka dae,bayan ta kammala shirya kanta,order ya bada na abincin da zataci,

  Bayan an kawo mata abincin,taci ta ƙoshi,sannan yace ta kwanta ta huta,Cikin ƙankanin lokaci bacci ya ɗauke ta asaman gadonshi,

  Safa da marwa ya shiga yi acikin ɗakin tunanin shi,taya za'ae yakai amrish gidansu!?Yasan cewa ba wani abun tashin hankali bane,kuma in ya kaita zasu kar6eta hannu bibbiyu,amma bazai bari su ganshi ba da sunan wanda ya kawota,in ba haka ba zai zama abun zargi a wurin ƴan uwansu,

  Sae faman zirga zirga yakeyi acikin ɗakin,lokaci zuwa lokaci yakan ɗan juya ya kalli amrish dake kwance saman gadon nashi,hankalinta kwance sae sharar bacci take yi,bai ta6a ganin yarinyar da ta yarda dashi ba kamar amrish,kwata kwata ba ta jin tsoranshi don ta rungumeshi,ba wani abu bane a wurinta,duk da shi ya koya mata hakan,har kwana saman gado ɗaya suna yi da ita,amma wani abu bai ta6a shiga tsakaninsu ba,sae dai ƙawayenta su Zeenatu,babu wadda bai yi lalata da ita ba acikinsu,kuma har yanzu yana tare da kowaccensu,duk in ya buƙace su zasu kawo mashi kansu ne,


❤🤍❤


After La'asar,


Tsaye take agaban dressing mirror tana ƙare ma kanta kallo yadda kasan wadda za ta je gasar Kyawun duniya,Wedding gown ce a jikinta  fara ƙal,tabi shape ɗin jikinta,hips ɗinta ya fito sosai kamar zai fasa rigar haka daga saman rigar net ne,sosai fatar ƙirjinta ta fito mai matuƙar jan hankali,Daga bayan Rigar lace tattoo ne wanda ya ƙara fito da kyawun rigar,fuskarta na ɗauke da light makeup,ta shafa jan baki red colour,Hannunta na sanye da haɗaɗɗiyar wrist watch ta diamond da Aunty azeeema ta saka mata,mai haɗe da ring da kuma chain ƴar ziririya fara,ga earrings ɗinta,wani irin daddaɗan kamshi ne ke fitowa daga jikinta Kamar wadda aka tsamo daga cikin ƙogin turare,gaba ɗaya bedroom ɗin nasu Ƙamshin turarenta ne ya karaɗe ko'ina,ƙafarta na sanye da stilleto,matsiyacin high heels ne mai shegen tsini,shima launin rigar jikinta ne,ƙafafunta sun fito ɗass acikinsa,


   "Wow masha Allah,Tabarakallahu Ahsanul khaliƙin!"hajiya azeema ce ta ambaci hakan,jahad kuwa hannunta na ɗauke da Wayar sehrish ta shiga Camera sae video take yi mata,ita ma hosana hannunta na ruqe da wayar hajiya azeema I phone 13,Sun taru sai video suke ɗaukar sehrish,

Ƙoƙarin juyowa tayi da sauri hajiya azeema ta dakatar da ita"Kada ki juyo yanzu,bari na aza maki net ɗin nan asaman kanki zai ƙara maki kyau sosai,Bayan ta kammala sanya mata mayafin sannan tace"Sannu a hankali zaki juyo ba da sauri ba," a natse Sehrish  ta soma juyowa a wani slow,Hosana na kallonta ta cikin camera sai faman sakin Murmushi take yi,

  Hajiya azeema tace"Yawwa My photographers ku ɗaukarmun ita da kyau,ta fito sosai acikin Video ɗin,yadda zanji daɗin ɗaurawa a status ɗina,

  Ƙarasa juyowa sehrish tayi,fuskar nan ɗauke da ƙayataccen Murmushi,ita kanta tasan tayi kyau over,Zuciyarta cike fal da farin ciki,kamar wadda akayima albishir da gidan Aljanna,dama hannunta akwai zanen jan lallen da akayi masu na walima,yana nan raɗau a hannunta bai goge ba,ta ruƙe yar purse ɗinta a hannunta,

  Tun daga ƙasa Hosana ta fara ɗaukarta ta cikin camera ɗin har izuwa saman fuskarta,

   "Turn ur back,yadda zasu ji daɗin ɗaukarki da kyau,"acewar Azeema,

  Juyawa sehrish tayi a hankali suka ɗauki bayan,sannan ta sake juyowa,Jahad sae faman zuzuta ta take yi tana cewa"wlh yadda kasan Amaryar Gaske,Sehrish kinyi kyau sosai kamar dollars"

  Dariya hajiya azeema tayi jin abunda jahad tace,

  tace"Wato kuɗi sune suka fi komai kyau kenan?shiyasa ake kwantanta su da mutumin da yayi kyau ko"?tayi maganar tana kallon Jahad dariya sukayi gaba ɗayansu,

  Suna cikin rahar nan wayar hajiya azeema tayi ringing,sunan Abba ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,da sauri hosana ta miƙa mata wayar,hannu tasa ta kar6i wayar bayan ta ɗaga kiran ta kara wayar a kunnanta,

   Tun kafin tayi sallama taji muryar abba yace"Azeema kina ina ne"?

   "Ina a ɗakinsu sehrish ne yanzu haka,na kammala yi mata kwalliya ne harma ta sanya rigar amaren...."

  Katse ta yayi da cewa"Karki kuskura,kice zaki kai yarinyar nan ɗakin Rafayet!".  

   Hankalinta atashe tace"Saboda me Yaya hossein"?tun daga kan muryar Abba ta tabbatar da cewar yana cikin matsananciyar damuwa,

   "Tun farko sai da na faɗa maki cewar wannan auren na sirri ne,kuma na faɗa maki dalilin dayasa ya aureta ba don yana sonta ba fa ce don tayi mashi aiki,.." a ɗan ruɗe hajiya azeema ta dago tana kallon Sehrish,jikinta ne yayi wani irin sanyi har cikin zuciyarta taji babu daɗi,

  Da sauri tace masu"Ina zuwa" tana faɗin hakan ta fuce daga ɗakin,a nan cikin corridor din ta tsaya,Muryarta asanyaye tace"Yanzu yaya kana nufin cewa yarinyar nan bazata tare aɗakin Mijinta ba!"

   "Azeema so nake ki fahimce ni,!ki natsu ki saurare ni,!rafayet wani irin bauɗaɗɗan mutunne mai wuyar sha'ani,Wlh bazai bari yarinyar nan ta zauna a part ɗinsa ba,da sunan amaryarshi,Yanzu haka zancen da nake yi maki,Ya hana uban kowa ya ɗauki hoto tare dashi!gaba ɗaya babu wanda ranshi bai 6aci ba saboda rafayet!"

   Muryar hajiya azeema tamkar zatayi kuka tace"Amma ba'ayi ma yarinyar nan adalci ba!Meyasa tun farko ba'a shawarce ta ba?kafin a ɗaura mata aure dashi!yakamata ace tasan da zancen auren da za'ayi mata da kuma dalilin yin auren!me kuke tunanin zai faru idan har yarinyar nan taji cewar an aurar da ita ne don tayi aiki kawai a ƙarkashinsa"?

  Shiru Abba yayi batare daya ce mata komai ba,

  Jinjina kai kawai hajiya azeema tayi tare da cewa "Shikenan kawai,Zansa ta cire rigar dana sanya mata,Amma dae banji daɗi ba,Kuma in sha Allah rafayet sai yayi danasanin yin hakan da yayi!"tana kai ƙarshen maganarta,tayi rejecting kiran,Tuni idanunta sun cicciko da kwalla,Ranta yayi mugun 6aci,

    "Aunty azeema!"hosana ce ta ambaci sunanta,da sauri takai idanunta ƙopar ɗakin nasu,tsaye take fuskar nan ɗauke da murmushi tace"Munata jiranki,Kince zamu je kai amarya,"

   "Kada ki damu hosana,Yanzu zan shigo ciki,"

  Amsa mata tayi da toh,sannan ta koma cikin ɗakin,Kusan 15 mins hajiya azeema tana tsaye batare da ta motsa ba,sae da zuciyarta ta lafa,sannan ta wuce cikin ɗakin nasu,

    A tsaitsaye ta samesu suna jiran dawowarta,gaba ɗaya duk sai taji ba daɗi,Musamman yadda taga Sehrish sae faman sakin Murmushi takeyi,tsananin tausayinta ne ya kamata,Shin wata irin rayuwa yarinyar zatayi a ƙarƙashin Sgr?mutumin da baisan Soyayya ba,Tabbas zata sha wahala a hannunshi,Domin kuwa zai mayar da ita tamkar baiwarshi ne,su yaya hossein sunyi kuskuren aura mashi ita,da sunan tayi mashi aiki,wannan tamkar ƙasƙanci ne,kuma yarinyar bazata ji daɗi ba,ranta zai 6aci sosai idan ta gano cewar aure akayi mata,auren ma na sirri,tamkar wata mara gata,babu walima babu wani party,babu taron mutane,babu wedding pics,dole abun ya ta6a Zuciyarta,na biyu da sa hannun iyayenta suka aura mata shi da sunan tayi aiki a ƙarƙashinsa ba matsayin matarshi ba,tabbas an gama cutar da ita,


    Mamaki abun ya ba su Jahad ganin hajiya azeema tayi tsaye agabansu,kuma ta ƙurawa sehrish ido tana kallonta,Kamar mai nazarin wani abu,

   Jahad ce ta ambaci sunanta"Aunty azeema,"

  Firgita tayi lokaci guda ta ɗan saki murmushin yaƙe tare da cewa"Am sorry fa,wlh na shafa'a ne,Yanzu mai ya rage mana muyi"?

   Hosana tace"Kai amarya mana,ki faɗa mana a ina zamu kai rishi ɗin,"

   Hajiya azeema tace"Ae wannan shirin drama ne!ba dagaske ba,A nan zakuyi wasan ga wayata ma idan kuna buƙatar yin hotuna,Ni yanzu inaso zan wuce ciki ne,"

  Da sauri Hosana ta kar6i wayar daga hannun hajiya azeeman,sallama tayi masu da sauri ta fuce daga cikin ɗakin,

  "Kamar yanayinta ya canza ko"?jahad ce tayi maganar tana kallon sehrish,

   "Nima na lura da hakan,Hosana wanene ya kira ta a waya nasan kinga sunan daya bayyana akan screen ɗin,Zai iya yiwuwa wani abu aka sanar da ita wanda ya 6ata mata rai,"acewar sehrish,

   Hosana tace"Ni dai naga Sunan Yaya hossein,amma bansan wanene ba,"

  "Sunan Abbansu Junaid ne,Allah yasa dae ba wani abu ya faru ba,"sehrish tayi maganar fuskarta ɗauke da damuwa,

  "Kodai naje najiyo mana abunda ke faruwa cikin gidan"?Hosanar tayi tambayar tana kallonsu,

  Jahad tace"A'a,babu ruwanki,tunda ba kiran mu akayi ba,"


Cigaba da ɗaukar hotuna sukayi acikin ɗakin,Shigowa junaid yayi fuskar nan tashi ɗauke da murmushi,Suna ganinshi suka haɗa baki wurin cewa"Baby Junaid!"

  Ɗaure fuskarshi yayi tare da ɗan turo bakinshi ashagwa6e yace"Ni ku daina Kirana da sunan baby,In ba haka ba,ran kowa zai 6aci a wurin nan,"ya ƙarasa maganar tare da aza idanunshi kan Sehrish dake tsaye tasha Kwalliya abunta,sakin baki yayi galala yana kallonta,a ruɗe ya ambaci sunanta"Reesh,"

  Murmushi Sehrish ta sakar mashi,tare da yi mashi fari da ido,sannan tace"Na'am,Junaid ya kaga wankan nawa,"?

   daƙyar ya iya cewa"reesh,yanzu kina sane aka ɗaura maki aure da babban yayan mu bayan kinsan da cewar Ina sonki"?

  Gabanta ne ya faɗi rassss!!Ba ita ba hatta su Jahad da hosana a ruɗe suka haɗa baki wurin cewa"Aure kuma,da Babban yayan mu!"

  Shi kanshi junaid ɗin sae da gabanshi ya faɗi,tunani ya shiga yi anya Sehrish tasan da auren kuwa?Yanayin yadda ya ga ta razana ya tabbatar mashi da cewar batasan da zancen auren ba!acikin ranshi yace"meke faruwa ne?Mommy batasan da auren babban yaya ba,kuma itama rishi dasu jahad basu san da auren ba!Abba ya 6oye masu kenan!aikuwa saina tona masu asiri kowa yaji,dama ya 6ata mun raina yau,duk irin amanar dake tsakanina da Abba ya rasa dame zai sakamun sai da wannan,"

  "Junaid dan Allah kayi mana bayani dalla dalla yadda zamu fahimta!"acewar jahad,

   Kallon fuskar sehrish yayi ganin ta zuba mashi ido tana kallonshi,kalmar daya furta masu ce take ta maimaitawa acikin zuciyarta

   "nidai baza aji mutuwar sarki abakina ba,Abba yace kar na faɗama kowa cewa an ɗaura aurensu,"yayi maganar tare da sanya hannu ya toshe bakinshi,

  Hankali atashe suka shiga kallon juna atsakaninsu,

   "Don Allah junaid ka faɗamun auren wa aka ɗaura"? muryarta tamkar zata yi kuka tayi maganar,

   "Sehrish kiyi haƙuri bazan iya sanar dake ba,Amma idan kina son samun ƙarin bayani,kije wurin Uncle ki tambayeshi,


  Jiki na rawa sehrish ta kama hanyar fita da sauri Hosana tabi bayanta,suka fita atare,

    Matsawa yayi kusa da jahad,tare da ruƙo hannayenta yace"Jahad!Albishirinki"?

"Goro,"ta bashi amsa fuskarta ɗauke da murmushi,

"Fari ko Ja"? Wurga ido ta ɗan yi sama kafin tace"Fari,"

    "Uncle ya bani aurenki,"jin wannan maganar yasa hankalin jahad ya tashi,lokaci guda ta ɗaure fuskarta,tare da fisge hannunta daga cikin nashi,

   Gabansa ne ya faɗi,ganin yadda ta canza mashi lokaci guda tsoranshi kada ace jahad ba son shi take yi ba,

  "Jahad baki sona?bakison ki aure ni ko"?

  Shiru jahad tayi tana ƙare mashi kallo daga ƙasa har sama,

   Tuni idanunshi sun cicciko da kwalla,fargabarshi wata amsa jahad zata bashi,in har bata amince ba shikenan zai rasa damar da yake da ita,na mayar da gurbin rishi ɗinsa daya rasa,

   Motsi ta soma yi da la66anta daƙyar ta iya cewa"Junaid!dagaske kake mun ko wasa?tell me the truth pls,i know u are just teasing me,'

    Girgiza kai yayi tare da cewa"Am serious jahad,Bazan 6oye maki ba,da farko sehrish nake so sosai,in har ba zaki manta ba,lokacin dana ɗauko ki a school matsayin sehrish,idan zaki iya tunawa sunanta nake ambata a matsayin ke,nayi tunanin itace shiya sanya na sanar dake abunda ke acikin zuciyata,Amma yau batare da sani na ba,A masallaci naji sanarwar ɗaurin Auren Sehrish da babban yayan mu,har sai da na kusa zaucewa ƙarshe a masallacin na yanke jiki na fa....."

  A razane jahad ta katse shi da cewa"Wai dagaske an ɗaura auren Sehrish!kuma da babban yayan mu!?

   ɗaga mata kai yayi alamar eh,kafin ya ɗaura da cewa"Ni kaina bansan da zancen auren nasu ba sae a masallaci dana ji ana sanarwar,abun ba ƙaramin ta6a zuciyata yayi ba,na shaqu sosai da sehrish,

  Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba,jin zancen auren Sehrish da Sgr,ta rasa gane a wane yanayi take ciki,farin ciki ko kuwa akasin hakan!babban abunda ya ɗaure mata kai shine yadda aka 6oye masu ba'a sanar dasu ba,Ko meyasa?Yanzu shikenan an ɗaura auren rishi ɗinsu?ta zama married woman?

   Runtse idanuwanta tayi tare da sanya hannu ɗaya ta dafe gefen goshinta,a hankali ta furta"Ya salaam,"

   "Jahad,inason naji amsar tambayar da nayi maki"?muryarshi a kasalance yayi maganar,don ya qagara yaji amsar da zata bashi,

   A hankali ta ware kyawawan idanuwanta akan fuskar junaid,tana kallonshi tace"junaid Daddy da kanshi ya baka aure na?kuma ya tabbatar maka da cewar bada wasa yake maka ba"?

   Bubbuga ƙafafunshi yayi saboda hasalar da yayi,a ƙule yace"eh mana,shi da kanshi ya mallaka mun ke agaban kowa da kowa,yaji tausayina ne saboda halin dana shiga,"

.....fuskarta aɗaure tace"Meyasa daddy zai yi mun haka?nace mashi ina sonka ne?kuma ya rasa ma wazai ba aure na sai kai?junaid kayi mun ƙanƙanta!Ni bazan iya zaman aure dakai ba,nafison namijin daya mallaki hankalinshi ba shagwa6a66e ba sangartacce irinka...."tun kafin takai ƙarshen maganarta,hawaye suka fara wanke mashi fuskarshi,cikin shessheƙar kuka yace"au haka ma zaki ce jahad?shikenan babu komai,"da sauri junaid ya juya tare da nufar kopar ɗakin nasu gwanin ban tausayi,

  Yana ƙoƙarin kai hannu ya buɗe ƙopar,da gudu jahad ta faɗa bayanshi tare da rungumoshi sosai tana dariya,wata irin nauyayyiyar ajiyar zuciya junaid ya sauke,kwantar da kanta tayi asaman bayanshi,magana ta soma yi mashi anatse"junaid,ko da yake yanzu na canza maka suna,Ka tashi daga junaid ka koma Babyn jahad,Ina fata hakan yayi maka,"

  Tafin hannayenshi ya sanya tare da share hawayenshi,wani irin sanyi ne ya ratsa cikin zuciyarshi,Calmly ya ambaci sunanta"Jahad,Kin amince da aure na?a yadda nake?zaki iya haƙuri dani?ki zauna dani amatsayin Mijin ki uban ƴa'ƴanki kuma"?

  Lumshe idanunta tayi yayin da hancinta ke shinshinar ƙamshin turaren jikinshi,

   "I accept ur love junaid,I love u so much,nayi farin ciki sosai da daddy ya baka aurena,a ashirye nake dana baka kulawar daya dace junaid,"

  Saboda tsabar farin ciki bakin junaid yaƙi rufuwa,hannunta ya ruƙo tare da zagayo da ita,ta dawo gabanshi suna facing ɗin junansu,zuba ma juna ido sukayi na wani lokaci,batare da sun sha Wahala ba,Sun amince ma junansu kowa ya samu abunda zuciyarshi ke muradi,janyota yayi ta faɗa asaman ƙirjinshi,zagayo da hannayenshi yayi ta bayanta,sosai ya rungumeta,tamkar zai mayar da ita cikin cikinshi,lokaci guda suka kamu da tsananin son kasancewa da junansu,

  


*Boss Bature*


  ❤🤍❤

  


"Rafayet!Ka 6ata mun rai!ka ƙuntatamun!Amma kai ko ajikin ka?meyasa zakayi mun haka"?Abbansu ne yayi maganar a yayin da yake tsaye acikin bedroom ɗin Sgr,Idanuwanshi sun cika tab da hawaye,

  "Abba,don me zaka tashi hankalin ka akan auren nan!You know the reason why I married her,Saboda inaso taci gaba dayin aiki a ƙarƙashina,ni ban shirya yin rayuwar aure ba,Babu wannan a tsari na," yana magana huci na fita a bakinshi,saboda tsabar 6acin ran da ya ke ciki,ji yake gaba ɗaya sun takura rayuwarshi,ba don komai ba sai don saboda sun nemi Alfarmar ya taimaka yayi koda hoto ɗaya ne shi da Sehrish don su ajiye na tarihi,

  Gyaɗa kai Abbansu yayi tare da cewa"A haka kakeso kai ayi maka biyayya,bayan Ni ban isa na sanya ka abu kayi mun ba,narasa gane kai wani irin mutunne!ka ce yarinya bazata zauna a part ɗinka ba!kuma ba zaka ɗauki hoto ba atare da ita,nasan meyasa kayi hakan!saboda kada hotonku ya shiga duniya a dinga nunata a matsayin matarka!saboda kai a wurinka wannan ƙasƙancine aganta a matsayin matarka,saboda ka fi ƙarfin ta ko"?

  Yayi maganar ranshi a 6ace,Sgr kuwa ko ajikinshi,yana daga tsaye agaban dressing mirror ɗinshi ya juya ma Abbansu baya,har lokacin bai canza kayan jikinshi ba,babu wanda baizo yayi mashi magana ba akan ya amince da buƙatar mahaifinsu amma yaƙi yarda,hatta Ishaq da Abbas sunyi sunyi har sun gaji sun ƙyale shi,haka Marshal Omar sunyi barambaram dashi,saboda ya 6ata masu rai,

  "Zan tafi na bar maka ɗakin ka,Amma inaso na ƙara tunasar dakai cewa Abusufyan ya baka tsawon wata ɗaya kacal akan ka canza ra'ayinka game da auren yarjejeniyar nan,Zaka iya soke shi in har kana so acikin ƴan kwanakin nan,Amma idan har ka bari wata ɗaya ya wuce baka canza ra'ayin ka ba,duk abunda ya biyo baya kada kayi kuka da kowa ka kuka da kanka!kuma babu ruwana Na zame hannu na aciki,

  A fusace Sgr ya juyo tare da kallon Abban nasu yace"bazan ta6a canza ra'ayi na ba akan hakan!Idan ma yana tunanin hakan to ya daina!Bana buƙatar wani time nayin tunani!wata uku na cika zan sallame ta ne!

  Abba na ƙoƙarin buɗe baki yayi magana,ta wutsiyar idonshi ya hango mutun atsaye,a ɗan firgice ya juya don yaga wanene,

  Sehrish ce atsaye tana kallonsu,gaba ɗaya jikinta ya gama mutuwa,domin kuwa taji duk abunda suka ce kaf acikin kunnanta,Jikinta har kerma yakeyi,wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga gangarowa akan fuskarta,

  Jin shessheƙar kukanta yasa Sgr Juyawa tare dakai idanunshi wurin da take tsaye a ƙopar ɗakin nashi,tun daga ƙasa har sama yabita da kallo,

  A hankali Abbansu ya ambaci sunanta"Sehrish!"

  Juyawa tayi da gudun gaske tabar ƙopar ɗakin nashi,gaba ɗaya tabar part ɗin nashi,saukkowa tayi downstairs,Su fawan ne tsaitsaye acikin babban falon,koda suka ji shessheƙar kukanta sae hankalinsu ya koma akanta,kowa ya shiga tambayarta lafiya,

  Bata tsaya sauraronsu ba,da gudu ta wuce bedroom ɗinsu,tana shiga ciki ta samu junaid da jahad azaune gefen gadonsu suna shan soyayya,jin shigowarta yasa suka mike tsaye hankali atashe suka shiga tambayarta Lafiya,

  Bata basu amsa ba,kai tsaye ta nufi toilet ta buɗe ƙopar ta shige ciki,da ƙarfi ta datse ƙopar,sannan ta tsugunna ƙasa tana kuka tamkar ranta zai fita,


Gaba ɗaya Jahad da Junaid suka nufi ƙopar,Suna kwankwasawa suna kiran sunanta"Sehrish!Sehrish!dan Allah Rishi ki buɗe mana kopa!

  Turo kopar ɗakin nasu akayi,Abusufyan ne tare da hajiya azeema suka shigo ciki hankalinsu atashe,basu jima da shigowa ba,sai ga Abbansu junaid,dama tunda yaga ta watsa aguje tana kuka ya biyo bayanta,

  A bakin kopar shiga toilet ɗin suka tsaitsaya cirko cirko

   "Dama nasan abunda zai biyo baya kenan!"acewar hajiya azeema,

  Abusufyan yace"Ni bansan waya faɗa mata ba,Naso ace ni na fara sanar da ita,"

  Fuskar Abba a yamutse yace"wlh bansan da ita ba!Yanzun nan fa naganta a ɗakin Rafayet,muna cikin magana dashi akan zancen auren nasu,kawai naji shessheƙar kukanta,ashe duk taji abunda muka ce,"

   Jikinsu ba ƙaramin sanyi yayi ba,musamman Abusufyan har cikin zuciyarshi ya ke jin kukan nata,

   Ƙoƙarin lallashinta suka shiga yi amma ina,Sehrish taƙi sauraron kowa kuka sosai takeyi kamar ranta zai fita,tana jin muryoyinsu a waje sai faman yi mata magiya sukeyi akan ta buɗe masu ƙopar,

   Junaid duk yabi ya ruɗe sam baisan cewa abun zai ta6a zuciyarta ba har haka,Ita kanta jahad ba ƙaramin tausayin Sehrish taji ba,kowa sai da yasha jinin jikinshi,babban abunda suke ji ma tsoro kada ta illata kanta,


Bakomai ne ya ƙona mata rai ba,Fa ce abunda kunnuwanta suka jiyo mata,gaba ɗaya taji ta tsani kanta,komai ya fita aranta,tabbas tana son Sgr sosai har cikin ranta,kuma babu abunda ya canza acikin zuciyarta,tayi farin ciki mara misaltuwa na kasancewarta matarshi,wannan babbar kyauta ce agareta,sae dai kash bataso ya aureta batare da yana sonta ba!Sam bata ta6a ra'ayin hakan ba,tafi son ta auri wanda take so kuma yake sonta,bawai wanda takeso ba,Shi baya sonta,bugu da ƙari kuma ya aureta ne don taci gaba da aiki a ƙarkashinshi na wata uku kacal!

    "Idan ba damuwa inaso ku ɗan bani wuri in shawo kanta,"hajiya azeema ce tayi maganar,

   Abusufyan yace"kina ganin zaki iya shawo kanta kuwa?

  "Ku je kawai,Ni nasan yadda zanyi da ita,ku ɗan bamu wuri,"

  Kama hanya sukayi gaba ɗayansu hadasu jahad suka bata wuri,kamar yadda ta bukaci su fita daga dakin,

  Zuƙunnawa hajiya azeema tayi abakin ƙopar toilet ɗin,Saboda ranta ya bata cewar sehrish tana zuƙunne a ƙasa,ta gane hakan ne ta hanyar sautin kukan nata,

  Cikin lallami ta ambaci sunanta"Sehrish,"

  Cikin shessheƙar kuka tace"Na'am,"

  "Inason magana dake!dan Allah ki bani haɗin kai,kada ki bani kunya,inaso kizo ki buɗe mun ƙopar nan!,"

   Miƙewa sehrish tayi,jikinta sai faman kerma yake yi,daƙyar ta iya sanya hannu ta buɗe kopar toilet ɗin,

  Sauke ajiyar zuciya hajiya azeema tayi tare da mikewa tsaye tana kallonta,fuskar nan tayi suntum da ita,gaja gaja da hawaye,idanun sun kumbura,janbakin da ta shafa duk ya 6ata mata fuskarta,mascara ɗin da aka shafa mata asaman eye lashes ɗinta,duk ya jike sharkaf da hawayenta ya 6ata fuskar da baƙin,kayan jikinta ne kawai basu 6aci ba,

  Ruƙo hannunta hajiya azeema tayi tare da zaunar da ita daga gefen gadon nasu,itama ta zauna suna fuskantar juna,

"Haba amaryar babban yaya,kuka bana ki bane,Farin ciki ya kamata na gani akan fuskarki,"cike da zolaya hajiya azeema tayi mata maganar hada jan kumatunta,

Fashewa ta kuma yi da wani sabon kukan cikin shesshekar kuka tace"Am...amma..Aunty azeema..meyasa za'ayi mun haka?saboda me za'a ɗaura mun aure tare da babban yayanmu batare da an sanar dani ba?Nasan cewa sun isa dani!Amma yakamata ayi mun adalci,Auren wata uku fa?kawai saboda buƙatar kanshi"?

  Ruƙo hannunta hajiya azeema tayi cikin sanyin murya tace"Inaso na tambayeki wani abu,amsa ɗaya kawai nakeso ki bani,kuma ki faɗamun gaskiya,'

Dakatawa sehrish tayi da yin kukan tare da mayar da hankalinta kan Aunty azeema tana sauraronta,

   "Inaso ki faɗamun gaskiya,Shin kina son Sgr ko bakya son shi ne"?

  Shiru sehrish tayi yayin da idanunta ke akan yatsun hannunta da ta harɗesu wuri guda tana murzasu,

  "Kinyi shiru baki ban amsa ba"?

ƙasa kasa tayi da muryarta tare da cewa"bazan 6oye maki ba Aunty azeema,ina son Yaya rafayet sosai,fiye da yadda nake son kaina,"

   Murmushi hajiya azeema ta ɗan yi,dama saida ranta ya bata cewar tana sonshi,

  "In har dagaske kina son shi bai kamata kiyi kuka ba don an ɗaura maki aure dashi,"

  "Aunty azeema ba baƙin ciki nake yi ba,bakomai ne ya 6ata mun rai ba fa ce irin auren da akayi mun dashi,Saboda kawai nayi  aiki a ƙarƙashinshi,na tsawon wata uku?meyasa za'ayi mun haka?idan aka barni ma zan iya yin aiki a ƙarkashinshi ba sai ansa ya aure ni ba,ba bisa son ranshi ba,tunda ba sona yake yi ba,ni kaɗaice nake ɗawainiya da son shi tun kafin nasan wanene shi,Wahala kawai zansha a hannunshi,Ni ban ta6a son na aureshi ba batare da yana Sona ba,"

  Jinjina kai hajiya azeema tayi tare da cewa"hakane kin faɗi gaskiya,ba'ayi maki adalci ba,Ni kaina bansan dalilin yin auren ba sai daga baya nake ji a wurin Abbanku,Amma kiyi haƙuri dan Allah kada hakan yasa ki bijire ma iyayenki,kiyi masu biyayya in sha Allah zaki ci ribar yin hakan,"

  Batare da musu ba Sehrish tace'Shikenan,in sha Allah zanyi masu biyayya,kamar yadda kika ce,kuma koda baki faɗamun haka ba,Ni bazan yi kuskuren bijire masu ba,"

  Murmushi hajiya azeema tayi tare da sanya hannunta ta shafa gefen fuskar sehrish,

   "Good girl,Naji daɗi sosai da kika amince zakiyi masu biyayya,Ni kuma nayi maki alƙwarin cewa atare zamu yaƙi sgr,acikin waɗannan watannin guda uku kacal,Zamu canza mashi ra'ayinshi,don ya gane kuskurenshi,kinsan ance DUK ƘYAN TAKALMI ƘAFA CE KE TAKASHI,So nake ki take mun wannan tsadaddan takalmin da ƙafafun nan naki ya taku sosae,"

Sae lokacin Sehrish ta fashe da dariya,har hakoranta suka bayyana,maganar da hajiya azeema tayi mata ta ƙarshen nan ba ƙaramin dariya ta bata ba,


Cigaba da magana hajiya azeema tayi"domin aikin mu yayi kyau muna buƙatar mu shirya plan A da kuma plan b zuwa c,zamu fara jaraba plan A,idan har akaci nasara akan shi kinga basai mun buƙaci plan B ba,Abunda nakeso dake yanzu shine muna buƙatar satar amsa,kuma ke kaɗae ce zaki iya samo mana wannan satar amsar da muke buƙata a wurinshi,

  A tsorace sehrish tace"Ni kuma!"hajiya azeema tace"kwarai kuwa,ba wani abun tashin hankali bane,just akwai bukatar musan me yake so da kuma abunda baya so don mu kiyayesu,Ni dae a iya sanina Sgr mutunne maison abi umarninshi ba'ayi mashi musu,yafi so ayi mashi biyayya abishi sau da ƙafa,sannan mutunne shi mai tsaftar gaske,ya tsani ƙazanta,bayan haka kuma Yana son abinci mai daɗi,shiyasa yake cin girkin azmee saboda tana da tsafta kuma ta iya girki,yakama ki koyi kalar girke girkenta,"

  "Ae na fara koyo a wurinta,Kuma na iya waɗansu,amma zanyi mata magana akan ta ƙara koyamun wanda ban iyaba,"

  "Yawwa haka nakeson ji,ki dage sosai,Nidae ta 6angarena zan baki gudummuwa sosai,""  

  Sun jima suna fira atsakinsu tamkar ba uwa da ƴa ba,har sae da aka fara kiran sallar Magrib,sannan aunty azeema tayi mata sallama,

  Hankalin sehrish ba ƙaramin kwanciya yayi ba,ta samu ƙwarin guiwa sosai a wurin Hajiya azeema kuma taci alwashin zata ɗaura ɗamarar zama da sgr,har na tsawon wata ukun


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 12 na dare,tana a tsaye cikin ɗakinsu,sae faman zagaye zagaye takeyi,tana jiran dawowar Sgr,tun bayan sallar isha'e bai dawo cikin gidan ba,har lokacin wedding gown ɗince a jikinta,ta gyara kwalliyar fuskarta,sannan ta daure gashin kanta da ribbom,

  Jahad da hosana sun jima da yin bacci ita kaɗae ta rage batayi bacci ba,zuciyarta cike take da damuwa,sam tagaza samun natsuwa babban abunda takeyi ma fargaba shine taya zata fara tunkarar SGR a matsayin Mijinta?shin zata iya jure zama dashi?tasan cewa dole ta fuskanci ƙalubale dayawa a wurinshi,

  Tana cikin wannan zancen zucin taji shigowar motocinsu,ajiyar zuciya ta sauke tare da komawa gefen gadonsu ta zauna tana jiran su ƙarasa shigowa cikin gidan,

  Almost 30 mins,sannan ta miƙe tare da buɗe ƙopar ɗakin ta fito waje,babu kowa kai tsaye ta nufi kitchen,batare da 6ata lokaci ba,ta shirya mashi dinner ɗinshi a saman ƙayataccen tray ta ruƙo shi da hannayenta,a hankali take tafiya saboda tsinin takalman dake a ƙafafunta,bata saba tafiya da irinshi ba,babu kowa a main palour ɗin hakan yasa ta wuce upstairs part ɗinsa,

   Da sallama abakinta tashiga falon,babu kowa aciki sae dae kamshin turaren nan nashi,kama hanyar zuwa bedroom ɗinshi tayi,a bakin ƙopar ta tsaya tare da yin sallama"Assalamu alaikum"

  "Who's there"abunda taji yace kenan,

daƙyar ta iya cewa"Ni ce"

  "Okey,Come in"

 A hankali ta zura ƙafarta cikin ɗakin nashi,samun shi tayin kwance asaman katafaren gadon nan nashi na mulki,ko takalman ƙafarshi bai cire ba,still shaddar ce ajikinshi,

   Ƙarasa shiga ciki tayi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman table,kamar wata mara gaskiya ta juya zata kama hanyar fita daga ɗakin muryarshi ta katse mata hanzarinta da cewa"Baki iya gaisuwa bane?"

  dakatawa tayi tare da ɗan juyo ta saci kallon fuskarshi,A lumshe ta samu idanunshi tamkar maijin bacci,

   Muryarta na rawa tace"Ina yini"

 Ta6e la66ansa yayi tare da cewa'zonan""

Jiki asanyaye ta tunkareshi,da hannu ya nuna mata gaban gadon nashi,sannan yace"kneel down"

     Tattare rigar jikinta tayi,tare da zubewa saman guiwowinta,

  "Kukan me kikeyi ɗazu?ko don saboda kinji abunda muke tattauna da Abba ne?"

  Girgixa kai tayi'a'a ba haka bane,""

   "Okey,"

Shiru ya ɗanyi na wani lokacin kafin yaci gaba da magana"Na aureki ne saboda inaso ki cigaba da aiki a ƙarƙashin ikona!Idan har bakya ra'ayin hakan zan iya sakin ki,"Ya ɗan dakata da yin maganar yana jiran jin amsarta,

  

   

   

  

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina 08103884440❤_



Not edited,



"zan cigaba da aiki a ƙarƙashin ka,"ta ƙarasa maganar,tana faman sauke ajiyar zuciya,

  "Good,"ya furta hakan tare da miƙe wa daga zaune,Ya jingina bayanshi a jikin pillow,har time ɗin idanuwanshi na a lumshe bai buɗesu ba,

   "Now you are under my control, you must follow my rules,"dakatawa yayi da yin maganar,tare da kai hannu ya zaro hanky daga front pocket na rigar shaddar jikinshi,

  Miƙa mata yayi tare da cewa"Oya,goge wannan fentin dake a saman lips ɗinki,from now bana buƙatar naga make up a face ɗinki,in dai zakiyi aiki a part ɗina,"

   Hannu tasa ta kar6i hanky ɗin,tare da kaishi saman lips ɗinta,a hankali ta shiga goge jan bakin da tasha fa,

   Cigaba da magana yayi"i won't restrict ur life,You still ave ur right,don na aure ki ba hakan yana nufin zaki ɗauki kanki as a married women ba,No just normally zakiyi rayuwarki,Kuma zaki iya kula duk wanda kikeso koda namiji ne i don't care about that,'

  Zaro ido waje sehrish tayi tana kallon fuskarshi,cike da mamakin jin abunda yace mata,Lamarin sgr ya fara bata tsoro,sae ka ce ba musulmi ba!da aurenta kuma ya amince mata ta kula duk wanda takeso?Anya bai fara shaye shaye ba?kodai yana da Iska ne ajikinshi?Abun yayi confusing ɗinta sosai,

  "Idan ma kina da tsafta ki ƙara akan wadda kike da ita,part ɗina ya kasance kullum a tsaftace ya ke,"

  Kasa kunne sehrish tayi tana sauraron shi,guiwowinta har sun fara yi mata raɗaɗi,magana yake yi tamkar baisan motsa la66ansa,balle har yayi sauri ya kammala ko ta samu ta miƙe,

   "Banason wani ya ƙara girkamin abincin da zanci,da hannunki zaki girka mun,sannan ba kowani kalar abinci nake ci ba,Ki nemi bayani a wurin Asmee,"

  Dakatawa ya ɗanyi da maganar,hannu ya miƙa tare da ɗauko wayarshi dake ajiye saman side drawer ɗinshi,ya shiga daddanata,

   Ganin haka yasa sehrish tayi sauri Zama dirshin a ƙasan,kota rage raɗaɗin da guiwarta keyi mata,

     "Where's ur phone"?yayi tambayar tare da ɗan dakawata,da dannar wayar da yake yi,

   Da sauri tace"na barta a bedroom ɗinmu,"

  "Okey,"ya ambaci hakan tare da kai hannu ya buɗe drawer chest,memo ya ɗauko tare da biro,Ya buɗe empty page,a natse ya shiga yin rubutu asaman paper ɗin,. 

  Zugudum sehrish tayi,aranta tana tunanin ko taya zata iya gane hand writting ɗinshi?kwanakin baya,daya ta6a yi mata rubutu bata iya gane komai ya rubuta ba,har haroon ya yaudareta,

   Bayan ya kammala rubutun,Yayi tearing paper ɗin tare da miƙa mata,hannu tasa ta kar6a,

   "Phone number ɗina ne,Cos at anytime zan iya kiranki,even in the midnight indai ina buƙatar wani abu"

   Amsa mashi tayi da toh,

"Your work will start from tomorrow!U can leave now,"

  Jiki asanyaye sehrish ta miƙe dakyar take ɗangyasa ƙafarta tana tafiya,har sae da takai bakin ƙopar bedroom ɗin nashi sannan ta ɗan dakata da yin tafiyar,juyowa tayi tare da aza idonta akanshi,a lokacin harya sauko daga saman gadon,yana ƙokarin cire kayan jikinshi,da alama wanka zaiyi,

   Gyaɗa kai kawai tayi tare da sanya ƙafa ta fito daga bedroom ɗin nashi,

  Bata tashi jin hawaye ba,sae da ta hau saman staircase din,tana taka benen a hankali,bakomai yafi ƙona mata rai ba fa ce abunda ya ce mata,Zata iya kula duk wanda takeso koda Namiji ne shi bai damu ba,tsabar takaici kamar ta haɗiyi zuciyarta haka take ji,taci alwashin saita koya mashi hankali,kuma zata jajurce ne wurin ganin ta gudanar da aikinta kamar yadda yakeso,daga baya kuma ta shiga tunanin komai yasa ya hanata shiga part ɗinshi da makeup?mai jan bakinta yayi mashi ne da zaisa ta goge?da alama so yake ya dinga ganinta kamar gardi,shiyasa yayi mata hakan,


Ƙarasa saukowa tayi daga saman stairs din,sannan ta tsaya tare da juyawa tana kallon upstairs ɗin"


In sha Allah,Wata rana Sai kayi kneel down agabana,Kamar yadda ka saba sanya ni in duka agabanka,koda baka zubar da hawayenka ba,zakayi kukan zuciya ne wanda yafi ciwo,Wannan alwashine na ɗaukarma kaina,In har ban tabbatar da faruwar hakan ba,To ni ba jinin Abusufyan bace da abu!!kuma ban cika mace ba,"

  Tana magana hawaye na shararowa akan fuskarta,ranta ya 6aci sosai


  *ATAƘAICE*


Acikin waɗannan ƴan kwanakin Sehrish ba ƙaramin jiki taji ba,domin kuwa sgr baiyi mata da sauƙi,Aiki takeyi tuƙuru,ba ƙaramin ƙoƙari take yi ba wurin ganin ta kiyaye duk wani abu da zai haɗa ta dashi,Aranar monday abusufyan ya mayar dasu school,da kanshi yakaisu acikin motarshi,basu samu matsala ba,sae dai an wuce su abubuwa da dama,Domin kuwa suna dab da fara'a Exams,abubuwa duk sun haɗe mata,ko karatu takeyi hankalinta na akan agogo,don kada ta shiga lokacin aikinta batare da ta sani ba,tun da sanyin safiya take shiga part dinshi tunkafin ma ya tashi daga bacci,ta gyara mashi toilet ɗinshi da falonshi,bayan ya tashi daga bacci ya shiga wanka,ta zauna ta gyara bedroom ɗin nashi,Sannan ta shiga kitchen ta haɗa mashi breakfast ɗinshi,Mafi yawancin lokutta a makare take zuwa makaranta,Saboda aikin sgr,Sae yaga damar sallamarta tukunna,abun ba ƙaramin 6ata ma abusufyan rai yakeyi ba,sae daga baya ya dinga danasanin ƙulla auren yarjejeniyar da sukayi,kullum Shi yake ja masu yin late a school,saboda dole sai sun jira sehrish ta kammala aiki a part din sgr,sannan su wuce school,baiwar Allah suna dawowa daga school da zarar tayi sallah,ko abinci bata ci,indai sgr na a cikin gidan sae ta fara zuwa ta gyara mashi part ɗinshi ta kuma kai mashi lunch ɗinshi,ta kuma yi serving ɗinshi abincinshi har sai ya mula yasha iska tukunna ya sallame ta,sannan fa take samun damar cin abincinta,Cikin lokaci ƙankani sehrish ta soma fita hayyacinta,Duk ta rame,kullum ne sai ta farka tsakar dare,ta zauna tayi ta kuka ba wanda ya sani,ita kaɗae tasan irin raɗaɗin da take ji acikin zuciyarta,gashi in tayi kuskuren yi mashi laifi,Hukunta ta yakeyi da tsallan kwaɗi,babu wanda bai fara jin tausayinta ba acikin gidan,shiru kawai sukeyi,bakomai ne ya jawo mata hakan ba fa ce rashin Hajiya azeema domin kuwa tun sati daya da yin auren,Tabar ƙasar izuwa dubai inda tasaba yin harkokin kasuwancinta,Amma tayi mata alƙawarin cewa bazata wuce One month ba zata dawo nigeria saboda ita kawai,Duk da haka kullum sai sunyi waya da ita,kuma tana ƙara ƙarfafa mata guiwa,kullum tana kara tunasar da ita akan cewa Karta kuskura ta karaya tun yanzu,Taci gaba da hakuri wata rana sai labari,mahaƙurci mawadaci ne,Sannan ta dage da addu'a kuma taci gaba da kyautata mashi,sgr bai tsaya a iya nan ba,idan dare yayi dama wannan ƙa'ida ne saita kai mashi coffee da kayan marmari around 12,toh yanzu takai ga,sae tana bacci wuraren 1:30 na dare ko biyu,ringing ɗin wayarshi ke tashinta daga bacci,daga ta ɗaga zaice mata Coffeee,yana furta hakan zai katse kiran,Dolenta ne ta tashi takai mashi ga bacci a idanunta,duk in taje part dinsa a wannan lokacin zata same shi ne yana yin nafilfilin dare,ko kuma ta same shi bayan ya kammala yin sallar yana karatun alƙur'ani,a rana ta farko data fara ganinshi yana karatun kur'ani abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,Ita duk a tunaninta babu ilmin addini akanshi,Ashe kullum saiya tashi in midnight don yayi sallar dare da kuma karatun alƙur'ani,tun daga ranar da ta fara ganinshi yana yin sallar nan,itama sai ta koma yin sallar daren da karatun al'kur'nin,saboda su dinga samun ladar atare,tunda ya katse mata baccinta,


A 6angaren Amrish kuwa,Daƙyar haroon ya samu ta amince zata koma wurin Mommynta da zama,Da kanshi ya mayar da ita gidansu,Sannan ya gargaɗi mommynta akan ta kiyaye 6acin ranta,itama amrishi ɗin sai da yaja mata kunne akan karta ƙara yunkurin kashe kanta,da haka ya samu ya sasanta tsakaninsu,har ta koma school,Ranar da suka haɗu da sehrish a makaranta kamar zasu haɗiye junansu saboda tsabar farin ciki,sun sha kuka sosai,saboda sunyi kewar junansu,abun ba'a magana,


Soyayyar junaid da jahad kuwa kullum ƙara ninkuwa takeyi acikin zukatansu,sun shaƙu sosai koda yaushe suna manne da junansu,baya gajiya da ɗaukarta su fita shan ice cream,Junaid ya iya soyayya sosau,yaci sunanshi romeo,saboda ya iya caring,ga zumuɗi kamar sabon ango,A ƙagare yake da aɗaura mashi aure da jahad,Bawan Allah duk safiyar Allah sai yayi shiga ta mutunci yaje gaisar da Abusufyan,hakan ba ƙaramin daɗi yakeyi ma abusufyan ba,tun daga haka ya gane cewa junaid zai ruke mashi ƴarshi dakyau duk da ƙuruciyarshi,amma yana da hankali sosai,



A 6angaren Marshal Omar kuwa,Hosana ta tada mashi 6alli,saboda sehrish tayi aure ita bai aure ta ba,duk yadda yaso ya shawo kan hosana akan ta bashi lokaci amma yarinyar nan taƙi yarda,ƙarshe tace mashi in har baije anyi maganar aurensu ba,zata tona mashi asiri ne,gabanshi ya faɗi ya shiga tunanin wani asiri ne hosana take ikirarin zata tona mashi,koda ya matsa mata akan ta faɗa mashi abunda take 6oyewa,sae cewa tayi ae Ya ta6a yi mata fyaɗe hada nuna mashi Zoben diamond ɗinshi daya manta a ranar,kuma tace zata sanar dasu Abbansu ne,Hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,ƙoƙarin fahimtar da ita ya shiga yi akan cewa shi fa ba fyade yayi mata ba,kawai tsautsayine yasa yayi ƙoƙarin raping ɗinta a lokacin,daƙyar ya samu ya lallasheta,sannan ta haƙura,a hakan ma sai da yayi mata alƙawarin cewa za'a daura masu aure,


lokacin da Haroon Ya ji Auren Sehrish da sgr,tamkar zai zauce saboda tsabar tashin hankalin daya shiga,don shi dagaske son Sehrish yake yi,daga baya ne ya gano cewar Auren Nasu na wata uku ne,tunda yaji hakan sai hankalinshi ya kwanta,Kuma yaci alwashin cewa Sai ya samu soyayyar Sehrish,in ba haka ba sai yabi duk hanyar da zai bi wurin ganin ya biya bukatarshi da ita,don ya jima da kwaɗayin son kasancewa da ita,tashin hankali,


Wannan kenan


A ranar wata Juma'a ne,Allah yayi ma modibbo rasuwa,Mutuwarshi tayi matuƙar girgizasu gaba ɗayansu,Musaman Ammi kamar zata zauce don kuwa har suma saida tayi lokacin da saƙon mutuwar nashi ya isar masu,Rashin lafiya yayi na rana ɗaya kuma Allah ya kar6i abunshi,Sunji mutuwarnan kamar kamar me,Ashe babu rabon komawarshi saudiya,duk da yaci nasara akan abunda ya kawo shi nigeria ya haɗa kan zuri'arsu,ya ƙulla zumunci mai ƙarfi atsakaninsu,Allah ya jiƙan Modibbo,


Gaba ɗayansu suka shirya zuwa Damaturu domin halartar jana'izarshi,Banda su sehrish saboda Exams da sukeyi a school ta Second term,amma matasan gidan dukansu abbansu ya tattarasu sun tafi can,gidan ya rage daga Azmee sae su sehrish,baƙaramin daɗin tafiyar sgr sehrish taji ba,Duk da ranta na bata cewar daƙyar zai wuce 1 week bai dawo cikin gidan ba,ta dan samu hutu,Kullum daga taji dirar mota jiki na rawa zata je ta leƙa ta window taga wanene ya dawo,Fargabarta kar ace shine ya dawo,da zarar taga bashi bane,Daɗi take ji,duk da tayi kewar shi sosai,Ko bacci takeyi sai ta dinga jin muryarshi acikin kunnanta yana cewa"Oya kneel down" har mafarkinshi takeyi,❤

  Yau Ya kasance wata ɗaya cuf da yin aurensu,batare da sgr ya soke yarjejeniyar ba,yanzu kwana biyar kenan da tafiyarsu Damaturu,dama abbansu yace sai sun zaga dangi,tunda sun jima basu je sun sada zumunci ba,


*Boss Bature*


   ❤🤍❤


Wuraren ƙarfe 3 na rana,sehrish na kwance saman gadonsu,tayi nisa acikin baccinta,baiwar Allah ba ƙaramar gajiya ta kwaso ba,Yau suka kammala Exams ɗinsu,tunda suka dawo daga school Ko Uniform ɗin jikinta bata samu ta cire ba,ga yunwa na cinta amma ahaka ta kwanta saboda baccin da take ji,


Jahad kuwa tana a garden suna video call da junaid,tun bayan da suka tafi,kullum ne saiya kirata video Call,idan suka fara wayar nan sai sunyi fiye da one hour suna magana,Idan da daddare ne kuwa ya kirata suna kaiwa har wurin asuba,basu runtsa ba,Soyayyarsu ba ƙaramin burge sehrish takeyi ba,wani sa'in sai taji dama itace take samun irin kulawar a wurin sgr,ɗan tahalikin nan tunda suka tafi kullum ne saita tura mashi Text message amma babu reply,bai ta6a mayar mata da amsa ba,kuma hakan baisa ta daina tura mashi ba,



Cikin bacci ta dinga jin jiniyar motoci acikin kunnanta,A firgice ta farka tana faman zare ido,tsoranta kada ace Sgr ne yadawo Cikin gidan,Sai da tadawo cikin hayyacinta sosai sannan ta gane cewa ashe wayarta ce ke ringing,Wata irin nauyayiyar ajiyar zuciya ta sauke,Hannu takai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman pillow,sae hamma takeyi saboda yunwar da take ji,duba screen ɗin wayar tayi,Sunan Daddy ne ya bayyana,Murmushi ta ɗan saki tare da answer kiran,ta kara wayar a kunnanta,

   "Assalamu Alalikum daddy,"

Muryar abusufyance ta amsa mata da cewa"Wa'alaikum salam,Daughter ya kike?tun ɗazu inata jaraba kiran wayar jahad line busy,ke ma kuma na kira wayarki kusan sau biyu tana ringing ba'a ɗaga ba,dafatan kuna lafiya,"

   "Bacci nakeyi ne shiyasa banga kiranka ba,Jahad kuma tunkafin na kwanta,ta sanar dani cewa junaid ya kirata,nasan yanzu haka dashi takeyin waya a garden,"

   "Okey,hosana fa?tana ina ne?itama na kira layinta a switch off,"

   "Daddy hosana fa,bata amfani da wayarta,tun ranar daka siya mana su bata ƙara bi takanta ba,tafi mayar da hankali akan laptop ɗinmu,yanzu haka ma kallo takeyi acikinta,"_

  Abusufyan yace"Na kira ne dama don inji ya ku ke,"

  Murmushi tayi kafin tace"Alhamdulillah daddy,muna lafiya,fatan kaima haka"?

.."ina lafiya nima,Ya Exams ɗin taku?kunyi abun kirki ko?

  dariya ta ɗanyi tare da cewa"Yau dai muka kammala,Result muke jira yanzu,amma fa daddy kasan a ƙurarren lokaci muka koma school,duk an wuce mu a karatu,duk yadda kaga result ɗinmu kawai kayi shiru da bakinka,ka sanya mana albarka,"

  Tana jiyo muryar abusufyan ta cikin wayar yana dariya,bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"Oh,kina nufin cewa ba kuyi abun kirki ba ko?oh ni abusufyan kada ace ƴa'ƴana basu da ƙoƙari,"

   "A'a daddy ae ba laifinmu bane,yakamata ayi mana uziri,saura fa two weeks a fara exam ka mayar damu school,"

   Abusufyan yace"hakane kuma fa,baki tambayeni yaushe zan dawo ba?ko bakiyi missing ɗina bane"?

   Muryarta da ƴar shagwa6a tace"I really missed u alot daddy,kamar na janyoka ta cikin wayar nan,inyi hugging ɗinki,"

  Dariya yayi sosai kafin yace"this Week zamu dawo ae,zuwan bazata zanyi,kuma a washe garin ranar da nadawo zamuje kano,Zan ɗauki ɗaya daga cikin ku mu tafi kano,saboda inaso muje gidan makwabtan nan naku ya ma sunansu?

  Da sauri tace"gidansu maman sadeeq"?

  Yace"eh nan nake nufi,zamu je ne domin munyi bincike akan mahaifiyarku,Nasan zamu samu ƙarin bayani a wurinsu,"

  Wani irin farin cikine ya bayyana akan fuskar sehrish,fuskarta dauke da murmushi tace"daddy inaso dan Allah ku tafi tare dani mana,"

  "Kina tunanin cewa Babban yayanku zai bari na tafi tare dake ne"?

  Shiru tayi tuni idanunta sun ciko da kwalla,muryarta tamkar zatayi kuka tace"Amma daddy,ni ya kamata a tafi tare dani,saboda zanfi gane kwantancen gidan nasu,"

  "Shikenan idan har kinason mu tafi tare dake,toh ki fara sanar da babban yayanku,idan har ya amince zamu tafi atare,in kuwa ya hanaki zuwa sai dai ki haƙura mu tafi tare da Jahad,"

   Jikinta ne yayi sanyi harma ta fidda rai don kuwa tasan cewa Daƙyar ne sgr ya barta ta tafi kano,

  Cikin sanyin murya tace"Shikenan daddy,zan jaraba tambayarshi idan ya dawo,Allah yasa yabarni,wlh dana ji sosai,"

  Sun jima suna waya dashi kafin sukayi sallama,ajiye wayar tayi asaman side drawer,sannan ta sauko daga saman gadon,direct ta wuce toilet domin yin wanka,within mins ta fito jikinta sanye da bathrobe,ta saki gashin kanta a bayanta,yanzu tsayinshi yakai har mid back ɗinta,

  Gaban mirror ta tsaya,tare da ruƙe qugunta,bakowa bane ya faɗo mata a ranta ba fa ce Sgr,a duk lokacin daya sanya bathrobe ɗinshi ba ƙaramin kyau rigar take yi mashi ba,yadda kasan donshi akayi rigar,


   Hannu tasa tare da janyo gashin kan nata,ta dawo dashi ta gabanta,tana kwaikwayon yadda sgr yakeyi in ya fito daga wanka,ta daure fuskarta kamar yadda yake tamke fuskarshi,a ƙarshe ta fashe da dariya,

  Tana cikin rahar nan,hosana ta turo ƙopar ɗakin nasu,Ta cikin mirror take hangenta,Hannunta na ruke da system ɗinsu,jikinta na sanye da doguwar riga ta material,

   "Sehrish ga lunch ɗinki can a dining,Aunty azmee ta ce idan kin gama baccin lalacin naki kije ki ci,"

   Ta ƙarasa maganar a yayin da take zama daga gefen gadon nasu,

   Juyowa sehrish tayi tare da kallon hosana tace"daddy ya kira wayarki a switch off,wai ina kike ajiye ta ne"?

  Yatsina fuska hosana tayi kafin tace"Oho,nima bansan inda take ba,nemanta na keyi ruwa ajallo,dan Allah ki tayani nemanta,inaso in kira Ya Omar,nayi nayi da jahad ta kira munshi amma taƙiya,dama kece mai ɗan mutuncin,"

  Harara sehrish ta watsa mata tare da cewa"Sai yau kikasan da haka?bayan kinsaba cewa nafi kowa tsiwa,bayan duk acikinmu ni ce innocent,"

  Marairaice mata fuska hosana tayi,"pls rishi komai ya wuce,dan Allah ki bani aron wayarki yanzu dai in kira Ya omar,2 days banji Voice ɗinshi ba,Ni fushi nakeyi dashi ma,ko ya kira yaji ya nake,amma bai kira ba,"rai a6ace tayi maganar,

   "Kada ki isheni da surutu,don nasanki bakya gajiya,ga wayar nan ki ɗauka,salon ki cinyemun katina,"

   Cike da zumuɗi hosana ta ajiye system ɗin asaman gadon,sannan ta ɗauki wayar da sauri ta fuce daga ɗakin,

   Gaban wardrobe ta koma tare da buɗewa,tana neman kayan da zata sanya,shirt ce ta ɗauko off shoulder Ash colour tare da dogon wandon Jeans,batare da 6ata lokaci ba ta zura kayan ajikinta,bayan ta kammala sanya kayan ta koma gaban mirror, tana shafa powder,sannan ta ɗan shafa lip gloss,murza la66an tayi,tana cikin sharce sumar kanta,Jahad ta turo ƙopar ɗakin,

   Hannunta ruƙe da wayarta,fuskar nan awashe sae faman sakin murmushi take yi,

   Juyowa sehrish tayi tare da kallonta tace"Sai yanzu kika kammala shan Love ɗin?Ni wannan soyayyarta ku tana ɗaure mun kai wlh,ko gajiya bakuyi,yadda kasan Romeo da juliet,kullum kuna a manne da juna,"

  Jahad tace"da alama baƙin ciki kikeyi mun Allah,"

   "In rasa dawa zanyi baƙin ciki sae dake?kin manta wa nake aure?Ni fa matar Surgeon general ce,ke fa?Ni har kunya ma nake ji,ki rasa dawa zakiyi soyayya sae wannan shagwa6a66an..."

  Tunkan takai ƙarshen maganar jahad tace"Auren da yanzu saura 2 month ya mutu!dashi har kike tutiya,"

  Gaban sehrish ne ya faɗi rasss!lokaci guda jikinta yayi wani irin sanyi,yayin da idanunta suka ciko tab da kwalla,

   Ita kanta jahad,bataso ta faɗi hakan ba,ranta ne ya 6aci saboda ta tsani a kushe mata baby Junaid ɗinta,Wannan ne yasa har ta faɗi maganar da tayi,

  "Jahad!ni kike faɗa ma haka"?

Da sauri jahad tace"dan Allah kiyi haƙuri,wlh bansan na faɗi hakan ba,raina ne ya ɗan sosu,"

  "Kinayi mun fatan aurena ya mutu kenan"? Tayi tambayar hankalinta aɗan tashe

  "Dan Allah rishi kidaina faɗin wannan maganar,nace maki ba a son raina na faɗi hakan ba,"tayi maganar tare da ƙarasawa wurin sehrish ɗin,ta ruƙo hannunta,

   "Pls kada ki bari hawayen nan sun fito daga cikin idanunki,kinsan cewa bazan ta6a yi maki fatan aurenki ya mutu ba,kuma wlh ban faɗi hakan ba donna 6ata maki rai ba," fuskar jahad tamkar zatayi kuka saboda tausayin sehrish,

   Tuni hawaye sun shiga wanke mata fuskarta,cikin sanyin murya ta wanda ya karaya tace"kin faɗi gaskiya jahad,bai kamata inyi prouding da aurenshi ba,Ni sam na manta ashe yau saura 2 month babban yaya ya sake ni,ni nama ƙosa ya sake ni in huta,'

   Hannu jahad tasanya tana share mata hawayenta"in sha Allah Babban yaya bazai ta6a sakin ki ba,banayi maku fatan rabuwa da junanku,Nafison ku kasance atare na har abada,Daso samu ne kawai wani abu ya shiga atsakaninku,Ana saura sati daya auren ya mutu,aga kina amai kinga shikenan babu zancen saki,Sae dai a fara tanadin suna,"cike da zolaya jahad tayi maganar,aikuwa nan take sehrish ta fashe da dariya,

  Ganin tafara dariya yasa jahad taci gaba da tsokanarta"gaskiya naƙosa in ganki da ciki,cikin ma na babban yayanmu,Wayyo Allah na bansan wani irin farin ciki zanyi ba aranar,zanso naga babynku,wlh ba ƙaramin kyau zaiyi ba,idan ya biyo kowannanku,"

  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Najima ina burin wannan ranar,bazan 6oye maki ba jahad,inaso inga nima na haifi ɗan babbyna,Amma nasan ba yanzu ba,"

   "Dont worry ur self,Very soon zaki haifa ma babban yayanmu twins ko triplet,tunda muma triplet ne,nasan acikinmu baza'a rasa wadda zata haifi ƴan biyu ba ko ƴan uku,"Acewar jahad,

  Shiru sehrish ta ɗanyi tana murmushi,duk da tasan abune mai wuya amma taji daɗin maganar nan ta jahad,

   "Inaso naje naci abinci,yunwa nake ji,"

   Ta ƙarasa maganar tare da kama hanyar fita daga ɗakin,Bin bayanta jahad tayi da sauri tare da ruƙo hannunta cikin nata,

   "Mu tafi atare,nima ae banci abincin ba,"

  Dining suka nufa,Wuri suka samu asaman dining chairs ɗin kowa ya zauna,Tray ne mai faɗi azmee ta ajiye masu asaman dining ɗin,Warmers ne guda biyu babba da ƙarama ta miya ajiye asaman shi tare da plate,sae drinks data ɗauko masu,

   Da yake mutanen gidan duk basu nan shiyasa bata girka abinci dayawa ba kamar yadda ta saba,ita kanta ta ɗan samu hutu yanzu,

   "Munyi waya da daddy,"sehrish ce tayi maganar a yayin da take ƙoƙarin buɗe warmer ɗin,

   "Ya faɗa maki ranar da zasu dawo ne"?_

  "A'a bai faɗamun ba,sai dai yayi mun albishir mai daɗi,"

  Cike da zumuɗi jahad tace"Wani albishir kenan"?

   Murmushi ta ɗanyi a lokacin ta kammala buɗe warmer ɗin,wainar shinkafa ce acikinta,

   "Ya sanar dani cewa da zarar sun dawo daga damaturu,A washe garin ranar zasu tafi kano,wurin nemo oumman mu,"

  Maimakon taga farin ciki akan fuskar jahad,sai taga idanunta sun ɗan ciko daa kwalla,


   "Meyasa bakya farin ciki ne"?

"Sehrish farin ciki fa kika ce?Bana Farin ciki,Idan har kika ga nayi farin ciki,toh An samu oummaan mu ne da ranta kuma da lafiyarta,ina fargabar abunda zaibiyo baya,idan suka je nemanta,Kinsan yadda oumman mu take tsananin son mu sosai,Amma lokaci guda aka nemeta aka rasa,tsorona kada ace ya sayyadi ne yayi mata wani abun,dama yasha faɗin cewa zai kashe ta idan har bata daina bin ƙwaƙƙwafin da takeyi mashi ba....."dakatawa jahad tayi da yin maganar,jikinsu duk yayi sanyi,

   "Addu'a yakamata muyi mata akan Allah yasa su samota,Amma nikaina ina fargabar a wani hali zasu same ta,"

    Duk sunsha jinin jikinsu,zuba masu wainar tayi acikin plate,sannan ta buɗe ƙaramar warmer ɗin,Miyar ganye ce,taji ganda lu6u lu6u acikin,Tuni ƙamshinta ya gauraye wurin,

   Daƙyar suke iya cin abincin,kamar waɗanda akayi ma dole suci,


   *HAROON*


Fitowarshi kenan daga cikin bedroom ɗinshi,yana ƙokarin barin wurin,Yaji an ambaci sunanshi"Haroon"!gabanshi ne ya fadi,duk a tunaninshi Amrish ce ta kuma biyo shi,da sauri ya juya don yaga wacece,tun daga ƙasa har sama ya soma binta da kallo,Jikinta na sanye da atampa,riga da skirt ne sun matseta sosai,gaba ɗaya surar jikinta ta fito ɗass,bakowa bace wannan fa ce Hayaam,fitowarta kenan daga ɗakinsu na hotel da Omar ya kama masu,Ashe tun ranar basu tafi ba,Zama suka cigaba dayi acikinshi sun ƙara biyan kuɗin ɗakin,don aunty babba taci alwashin cewa babu inda zasu tafi,daga abuja sai Enugu wurin bokan nan,Yanzu haka kuɗi suke harhaɗawa,duk ta siyar da gold ɗinta,yanzu ma shirye shiryen tafiya sukeyi,

  Sakin baki haroon yayi yana kallonta,da wata irin kasalalliyar Murya yace"Ke!me kikeyi anan"!?

  Cike da kwarkwasa Hayaam ta ƙarasa gabanshi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Kayi mamakin ganina ne?nikaina bansan da zamanka anan ba,yanzu kawai ina fitowa na ganka,kana ƙoƙarin fitowa daga ɗakinka,"

   Lokaci guda haroon ya saki wannan shu'umin murmushin nashi,a wayance yace"Amma nadaina ganinki a gidanmu,nayi tsammanin cewa kin koma gidanku ne?but me kikeyi acikin hotel ɗin nan"?

   Shiru ta danyi tana tunanin abunda zata faɗa mashi,

Shi kuwa gogan gaba daya ya aza kwartayen idanuwan nan nashi akan Ƙirjinta,

   "Naji kin yi shiru,idan ba damuwa mu shiga daga ciki mana,"yayi maganar yana nuna mata ƙopar daƙinshi,

  Gaba yayi tabi bayanshi,buɗe masu ɗakin yayi suka shiga ciki,

   A gefen gadonshi suka zauna,suna fuskantar juna,

   "Kinyi kyau sosai,"yayi maganar yana wasa da harshen shi asaman la66ansa,

  Murmushi hayaam tayi,batare da tace mashi komai ba,

  "Ko kina buƙatar abunsha ne kona ci haka insa akawo maki"?

  Girgiza kai tayi"a'a,a ƙoshe nake,bana jin yunwa,

  ta6e bakinsa ya ɗanyi,kafin ya kuma cewa"Ƙamshin turarenki yayi mun,"

  Dariya tayi tare da cewa"Allah ko"?

  "Da zaki bani dama ko sau ɗaya ne,just inaso in ɗan shaƙi ƙamshinne a hancina,"

   Batasan wanene haroon ba,saboda tasan halayen matasan gidansu,tayi tunanin cewa shima duk irinsu ne,hakan yasa tace mashi"Mezai hana,"

  Matsawa yayi kusa da ita,tare da kai hancinshi saman fatar ƙirjinta,yana ɗan shinshinar ƙamshin turaren,nan take taji wani irin yanayi atattare da ita,zagayawa yayi da hannunshi ta bayan rigarta,abu kamar wasa,ya zuge zeep ɗin rigarta a hankali,saboda tafara fita hayyacinta,

  ɗagowa yayi da hancinshi izuwa saman wuyanta kamar wani maye,haka ya shiga shinshina wuyan nata,da wata irin kasalalliyar murya yace,"Wannan turaren na wani company ne"

    Shiru tayi batare da ta bashi amsar tambayarshi ba,dama da biyu yayi mata maganar don yaji idan har lokacin tana acikin hayyacinta,Shirun da tayi mashi ne ya tabbatar mashi da cewar,tafara fita hayyacinta,

   Bata ankara ba,taji hannunshi ta cikin rigarta saman boobs ɗinta,A zabure ta kwace kanta daga jikinshi tare da ja da baya,tana ƙokarin gyara rigarta,ɗagowa tayi tana kallonshi,Murmushi ta gani akan fuskarshi,

   Hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ma,duk a tunaninta mutumin kirki ne shi ashe shima ɗan harka ne,

   Miƙewa tayi da sauri ta nufi hanyar fita daga ɗakin,Hannu tasa ta ruƙo kopar zata buɗe,taji ƙopar adatse,hakan yasa tayi saurin juyawa tare da kallonshi,Nuna mata key ɗin yayi a hannunshi yana dariya,

   Fuskarta aɗan ɗaure tace"pls,ka buɗe mun kopa inaso na tafi,Aunty laila na jirana,"

  Mikewa haroon yayi tare da takawa izuwa gabanta ya tsaya,sannan yace"Ganinki da nayi gaba daya kin tayarmun da sha'awata,na kwaɗaitu da son kasancewa tare dake,kallo ɗaya da nayi maki na gane cewa ke ba ƙaramar ƴar bariki bace,Don haka kada ki 6oye mun true colour ɗinki,kizo kawai muyi harka,"

  Zuba mashi ido tayi tana tunanin ta wata hanya zata 6ullowa haroon don ta samu ta tsere mashi,bakomai take ji ma tsoro ba fa ce aunty babba,saboda ta hanata kula maza,'

    "Koda ace ina kula maza,bazan kula irinka ba,Kuma ni ba ƴar iska bace kamar yadda kake tsammani,Ka buɗe mun kopa in fita,in ba haka ba zanyi maka illa,"a tsiwace tayi maganar hada rufe idanunta,

  Dariya haroon yayi tare da sanya hannushi ya ɗaga wandon jikinshi,ya tura key din acikinsa,sannan yace mata"Zoki ɗauki key din idan kin isa,ƙaramar ƴar tasha kafin kiyimun illa ni zan illata ki idan har baki taimaki kanki ba"

  Tsabar takaici ne ya cika hayaam,tayi danasanin yi mashi magana,da duk hakan bata faru ba,

   

   

   

   

   



    

  

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina pls banda phone call just message ta whatsapp,08103884440❤_






*Aunty Babba*


Guntun tsoki taja,yayin da idanunta ke kallon agogon dake manne acikin ɗakin,kusan ƙarfe 6 na marece babu hayaam babu alamarta,har ta fara gajiya da jiranta,tun ɗazu take traying numbar wayarta amma Still Switch off,hakan ba ƙaramin 6ata mata rai yayi ba,tunani tashiga yi ko ina ta shiga?daga zuwa curo kuɗi a banki shiru kake ji wai malam yaci shirwa,

   Ruƙe qugu tayi tare da yin ƙwafa,ta koma gefen gadon ta zauna,tana jiran shigowarta,tuntana sa ran dawowarta harta fara fidda rai,lokaci sai gudu yake yi har wurin ƙarfe 7,hayaam bata dawo ba,duk tana azaune har 8 ta buga,

  "Allah yasa ba gantalin nata ta tafi ba,daga zuwa curo kuɗi a banki kamar na aiketa wata uwa duniya,tabi duk ta rufe layinta,Mtsww"ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki,


Yayin da aunty babba ke zaman jiran hayaam,ita kuma tana can rai hannun Allah a ɗakin haroon,Lokacin daya hanata fita daga ɗakin ya zura key a wondonshi yace ta taimaki kanta,tayi tsammanin cewa zata iya kwatar kanta saboda tasa ba gara sofwan saurayinta,hakan yasa cikin salon wayau ta zura hannunta acikin jakarta,batare da ya ankare ba,Ta curo kwalbar turare ta fesa mashi asaman fuskarshi,kai tsaye ya ta6a idanuwanshi,raɗaɗi yasa yayi saurin kai hannu yana murza idanun nashi,ganin ya fita hayyacinshi yasa tayi ƙoƙarin zura hannunta acikin wandonshi,aikuwa batayi wani aune ba yayi mata ƙwaƙƙwarar damƙa,Ya yayyaga kayan jikinta da hannunshi,tundaga tsaye ya fara biyan buƙatarshi da ita,cikin rashin imani haroon yayi mata kaca kaca,Karshe yayi wurgi da ita saman gadonshi,Ya tu6e kayan jikinshi kamar yadda ya cire nata gaba ɗaya,sannan yabi ya danneta kamar wani bakure haka yakai mata Hari,wa'iyazubillah duk yadda taso ta ƙwaci kanta amma hakan ya faskara,Tun tana ihu tana kuka har bakinta ya mutu ƙarshe ta sume....."


*Boss Bature*


  ❤🤍❤


*SEHRISH*


Wuraren ƙarfe 10 na dare,tana a kwance saman gadonsu,ta ƙudundune cikin bargo,bacci harya fara ɗaukarta,tajiyo ringing ɗin wayarta,a hankali ta zame bargon tare da miƙa hannu ta dauki wayar dake ajiye saman mattress din,daƙyar ta iya buɗe idanunta masu ɗauke da bacci,ƙurawa screen ɗin ido tayi yayin ta zuciyarta ke bugawa,Sunan My Boss Man ne ya bayyana da manyan haruffa,Gabanta ne yayi wani irin bugu rass!lokaci guda ta miƙe daga zaune tana faman zare ido,hannayenta har kerma sukeyi,Amsa kiran tayi tare da kara wayar a kunnata,Tunkafin tayi sallama Sexy voice ɗinshi ta katse mata hanzarinta da cewa"Am back,"yana faɗin hakan yayi rejecting call ɗin,

   Yadda kasan gunki haka sehrish tayi kasaƙai,fuskarnan tamkar ta fashe da kuka,ɗan hutun da ta samu na kwana biyu ya ƙare,

   Jiki asanyaye ta sauko daga saman gadon bayan tayi wurgi da wayar saman mattress ɗin,Sleeping dress ne ajikinta white colour masu ɗige ɗigen baƙi ajikinsu,sunyi matuƙar yi mata kyau,Riga da wando ne,


Kaitsaye ta nufi wurin windown don ta leƙa taga idan dagaske ya dawo din,hannu tasa ta janye labulen tare da zuqe glass ɗinta,

   daga inda take ta hango motorshi a parkin space,wannan ya tabbatar mata da cewar ya dawo yana a cikin gidan,hannu tasa tare da dafe goshinta a hankali ta furta"OMG!"

  Gyaɗa kawai tayi tare da cewa"Ae shikenan,Za'a koma ƴar gidan jiya kenan,

   Juyawa tayi ta nufi shoe rock ɗinsu,flat shoe ta ɗauko ta zura a ƙafafunta,sannan ta nufi hanyar fita daga ɗakin,buɗe kopar ɗakin tayi bayan ta fita ta datse ɗakin,

   Fitowa tayi daga corridor din ta wuce kitchen,gidan tsit babu kowa,duk babu daɗi,tayi kewarsu sosai,musamman ɗan baby junaid ɗinsu,

   Batasan ko zai buƙaci abinci ba,tun da yanzu ya dawo,Hakan yasa ta hado mashi Coffee kawai don tasan dole ya bukace shi,a cikin plate ta aza cup ɗin,ta fito daga kitchen ɗin,ta nufi upstairs,tunani tashiga yi ko ina su jahad suke,yanzu haka suna a ɗakin aunty azmee dama kwana biyun nan,duk in dare yayi suna zuwa fira ɗakinta,wani lokacin acan bacci yake ɗaukarsu,sae wurin asuba suke dawowa dakinsu,

  A hankali take taka staircase ɗin harta haura sama,wuce wa part ɗinshi tayi,a baƙin kopar shiga falon ta tsaya,kamar yadda tasa ba,sae da fara karanta addu'o'in neman tsari daga sharrinshi sannan ta shiga ciki da sallama abakinta,

  Babu kowa acikin falon,bedroom dinshi ta wuce zuciyarta na ɗar ɗar,sallama tayi mashi,daga ciki taji ya amsa mata,tare da bata Iznin shiga,

Shiga cikin ɗakin tayi cike da fargabar ganin fuskarshi,agaban mirror ta same shi tsaye,yana sanye da bathrobe,jikinshi da alamun danshin ruwan da yayi wanka,bata samu damar ganin fuskarshi ba saboda ya juya mata baya,

  Ƙarasawa ciki tayi tare da ajiye mashi coffee ɗin saman table sannan tace"Sannu da dawowa babban yaya ya gajiyar tafiya"?

   Tamkar bazai amsa mata ba,har sai da ta fidda rai da zaiyi mata magana sannan yace"Am ok,"ɗaya daga cikin abunda ke ƙona mata rai kenan,Saita saki baki tayi mashi magana mai tsayi ya bata amsa in short,

   "Ga coffee nan,bansan ko zaka buƙaci wani abu ba,bayan wannan,"

    "No,need,"ya ambaci hakan tare da juyowa ya koma daga gefen gadon ya zauna,tsayawa tayi saboda tasan halinshi,in har bashi ya sallameta ba,toh bata isa ta tafi ba,

   Ɗagowa tayi ahankali ta saci kallon fuskarshi,yayi haske sosai la66an nan nashi sunyi pink tamkar ya shafa jan baki,ya ɗaure fuskar tamau kamar wanda aka aiko ma saƙon mutuwa,

   Mayar da idanuwanta tayi akan fatar ƙirjinshi,ganin yana ƙokarin dagowa yasa tayi saurin kawar da idonta gefe guda,

     Hannu yasa tare da daukar Cup of coffee din,sae faman tiririn zafi yake yi,saitin bakinsa yakai cup ɗin a hankali yake kur6arshi,

   ɗan dakatawa yayi da shan coffee ɗin batare da ya ɗago ya kalleta ba yace"Ɗaukomin sleeping dress ɗin da zan sanya,"

  Amsa mashi tayi da toh,Sannan ta juya,kamar  ance ya ɗago idonshi karaf ya sauka akan Wandon jikinta,ɗigon jinin daya gani ne yasa shi yin wurgi da Cup ɗin hannunshi ya faɗi ƙasa ya fashe,wani irin tashin zuciya ne yazo mashi,da gudun gaske ya mike tare da tunkarar toilet ya faɗa ciki,

  Hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,batasan meyasa shi jin amai ba,ita dae kawai taga yayi wurgi da cup kuma ya nufi toilet,tuni tasha jinin jikinta,tsananin tsoro ne ya bayyana kan fuskarta,tunkafin ma taji meyasa shi yin amai,

  Gaban Basin ya tsaya,sae faman kakarin amai yakeyi,tamakar ƴan hanjin Cikinshi zasu fito waje,Wani irin ƙyanƙyami ne dashi,gaba ɗaya duk yabi ya burkice,almost 8 mins yana acikin toilet ɗin,tanajiyo sautin aman da yake yi,zugudum tayi tana jiran fitowarshi,

  Hannu yasa tare da buɗe ƙopar toilet ɗin ya fito,jikinshi sae kerma yake yi saboda tsabar 6acin rai,idanuwanshi har sun canza launi,

   A zafafe ya tunkareta,ganin haka yasa sehrish tashi ga ƙoƙarin ja da baya,tana ƙoƙarin guduwa daga bedroom ɗin nashi, damƙo wuyan rigar jikinta yayi,tare da janyota yayi  wurgi da ita,ta bugi bangon ɗakin,

   Raɗaɗin da taji ne yasa ta fashe da matsanancin kuka,ware hannayensa yayi da nufin ya mare ta,runtse idanuwanta tayi da sauri tana kuka,

  Yarfar da hannun yayi gefe guda,tsabar 6acin rai ya hana ya buɗe baki yayi mata magana balle har tasan laifin data aikata mashi,cikin shesshekar kuka tace"Dan Allah kayi haƙuri bansan laifin dana aikata maka ba,"

    Tamkar ya rufe ta bugu haka yake ji,daƙyar ya iya buɗe baki yace"karki kuskura ki ƙara shigomin part ɗina da wannan ƙazantar a jikinki!ki tsaya har saikin kammala"

  a ruɗe sehrish tashiga tunanin wata ƙazanta ce yake magana akai,da sauri ta shiga bin jikinta da kallo,a ƙoƙarinta nata gano abunda ya kira da ƙazanta,

.  hakan ba ƙaramin fusata shi yayi ba,a fusace ya buga  mata tsawa wadda tayi matuƙar girgizata,ta zaburar da ita kuma ta tsoratar da ita,Nan take taji zubar jini acan under ɗinta,tare da matsanancin ciwon mara lokaci guda ya farmata,Sae lokacin ta gane cewa period ɗinta ne yazo mata,jinin ne ya fara zuwa shiyasa batayi noticing ɗinshi ba,sae daga baya raɗaɗin ciwon ya taso mata,

  Dogon tsoki yaja,tare da juyawa ya nufi cikin ɗakin,

   Sehrish kuwa tuni ta soma fita hayyacinta,idanuwanta sunyi jawur da su,kamar daga sama yaji tace"AMMA BAKA DA IMANI"_

   gabanshi ne ya faɗi rass,dakatawa yayi da yin tafiyar tamkar antokare shi,

   "Tunda nake arayuwata banta6a ganin mutun mara imani mara tausayi ba irinka!Jinin daka gani ajikina lalura ce bani na ɗaurama kaina ba,nikaina bansan dashi ba,da bazan bari ya zuba ajikin kayana ba balle har ka gani,duk irin ƙoƙarin da nakeyi wurin ganin na faranta maka rai baka ta6a gani ba,Nifa ba tsoranka nake ji ba!Allah kaɗae nake tsoro,Idan taƙamarka ƙarfi kazo ka buge ni,kaga in zan mutu,Na rayu da wanda yafi ka rashin Imani da tausayi,Kuma na jure zama dashi,naga tashin hankalin daya fi wanda nagani a wurinka,kuma duk na jure hakan....."

  Tashin hankali,Sanƙamewa sgr yayi atsaye,hankalinshi yayi matuƙar tashi,a arazane ya juyo don ya tabbatarwa kanshi da abunda kunnuwanshi ke juyo mashi,Jikinshi sae faman tsuma yakeyi,abun yayi matuƙar girgizashi,abun Yayi mugu mugun ɗaure mashi rai,Zuba mata ido yayi yana kallonta cike da mamaki,

  "Dame ka ke taƙama ne?kaifa mutunne ɗan adam,mai hannu biyu mai ƙafa biyu,hancin ɗaya,da baki ɗaya,idanuwa guda biyu kamar nawa,Wanda idan yayi bacci sai yarda akayi dashi,idan ya mutu kuwa duk  kyanshi duk mun dukiyarshi duk ji dakanshi acikin farin yadi mafi arha za'ayi mashi sutura,ƙarshe ya zama abincin tsutsa,"

   Waro ido waje sgr yayi hankali atashe yake kallonta,tunda yake arayuwarshi wata ƴa mace bata ta6a tsayawa agabanshi ba,kamar haka tana gaya mashi magana,Ido cikin ido batare da jin shakkarshi ba,yadda kasan mai iskokai haka sehrish ta rufe shi da faɗa,abun yayi matuƙar ɗaure mashi kai,har ya fara tunanin kodae Tasha ƙwaya ne?to ae ko wanda yasha ya bugi da giya bai ta6a kallon cikin idonshi ba ya gaya mashi magana,

   "Burin ka kawai ka wulaƙanta rayuwata,shiyasa ka aure ni don in cigaba da aiki a ƙarƙashinka,Inayi maka biyayya ne ba don inajin tsoranka ba,kaima ka sani,ni ba baiwarka bace baiwar Allah ce,Kuma idan yau naga dama zan iya barin gidan nan,kuma baka isa ka dawo dani ba,dana so tuntuni wlh dana tafi nabar gidan nan,Ƴanci nane,"

.. Tana magana hawaye na shararowa asaman fuskarta,with confidence takeyin maganar,batare data girgixa ba,

   "Zan tafi kuma kada kayi tunanin cewa idan na kammala ƙazantar zan dawo part ɗinka da sunan aiki,Bazan ƙara zuwa ba,kuma kada kayi tunanin cewa zanji tsoranka in gudu daga gidan nan ko inzo in baka haƙuri,Wlh bazan ta6a karaya ba,ka yi duk abunda kaga dama,ƙarshe kace zaka hukuntani ko,Idan ka tashi dan Allah kada kabarni da raina,ka kashe ni,"

  Ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki,a fusace ta juya tabar cikin bedroom ɗin nashi,

   Sai lokacin sgr ya runtse idanunshi,la66ansa sae kerma sukeyi kaf kaf,saboda tsabar 6acin rai,Hannunshi ya cusa acikin sumar kanshi ya shiga cakuɗata,gaba ɗaya ya hargitsar da gashin kan nashi,Cizon la66ansa ya shiga yi,nan take le6en ya fashe jini ya soma ɗiɗɗigowa daga jikinsu,Zuciyarshi har wani boiling take tana burning,wani irin zafi ne ya taso mashi gadan gadan,jiri ya dinga gani acikin idanunshi harya fara tangal tangal zai faɗi ƙasa,

  Daƙyar ya iya takawa izuwa gafen gadonshi ya zube ƙasa saman guiwowinshi tare da aza kanshi saman gadon,Tashin hankali Ran manya ya 6aci sosai,ƙoƙari yakeyi ya dakatar da bad temper ɗinshi saboda gudun karya aikata kisan kai,don muddin yakai matakin ƙarshe zaibi bayanta ne kuma sai yayi mata mummunar illa,

  A hankali ya shiga furta"Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un"!ya ambaci hakan kusan sau talatin,


Sehrish kuwa bayan ta fita daga part ɗinshi,daƙyar take ɗaga ƙafafunta saboda matsanancin ciwon marar da takeyi,Gaba ɗaya duk wannan maganganun da ta gaya ma Sgr ba'a cikin hayyacinta tayi su ba,batasan ma ta furta mashi su ba,Zafin raɗaɗin ciwo ne yasa ta zazzaga mashi masifa,dama kuma a ƙule take dashi saboda ya ƙuntata mata sosai,kuma ya kira jinin da takeyi da ƙazanta abun yayi matuƙar ƙona mata rai,hada ƙarin hakan yasa ta balbaleshi da faɗa,

Tun tana tafiya da ƙafafunta har suka gaza ɗaukarta,ƙarshe a bakin shiga corridor ɗin ɗakinsu,ta yanke jiki ta faɗi ƙasa saman tiles tana birgima,hannunta dafe da mararta,gashi babu wani a kusa balle ya kawo mata agaji,


Kamar yadda sehrish ta kwana waje saman tiles,haka sgr ya kwana zuƙunne saman guiwowinsa,kanshi na asaman gadonshi,Aranar bai runtsa ba,bacci ya ƙauracewa idanuwanshi,


Wuraren sallar asuba,Jahad ta fito daga ɗakin azmee tana ƙoƙarin shiga bedroom ɗinsu,idonta suka sauka akan sehrish dake kwance a ƙasa,gashin kanta duk ya rufe fuskarta,da ƙarfi ta ambaci Sunanta SEHRISH,da gudun gaske ta ƙarasa tare da zubewa saman guiwowinta agaban sehrish ɗin,

  "Innalallahi'wa'innalairrahiji un,Sehrish!meya faru dake ne!nashiga uku!Aunty Azmee!!!"duk tabi ta ruɗe,musamman data ga jini ya 6ata wandon sehrish ɗin,sai tayi tsammanin kodai taji wani mummunan rauni ne,Jijjiga jikinta tashiga yi tana cigaba da kwalama Azmee kira,

   "Aunty azmee!Hosana!dan Allah kuzo ku dubamin!meya faru da sehrish ne!"

   A ruɗe ta miƙe tare da tunkarar ɗakin azmee,tura ƙopar tayi ta faɗa ciki a hargitse,Adai dai lokacin Azmee ta kammala sallar asuba,juyowa tayi tana kallon jahad ganin hawaye asaman fuskarta yasa ta miƙe da sauri ta tunkareta tana tambayarta 

   "Jahad lafiya meya faru ne"

  Muryarta har shaƙewa takeyi wurin ambaton sunan sehrish"Aunty azmee sehrish!bansan meya faru da ita ba,gata can kwance a ƙasa bata motsi,ga jini a jikin wandonta....."tunkan taƙarasa maganar Azmee ta zabura da gudu ta fita daga ɗakin,itama jahad ɗin tabi bayanta da sauri,

  Ƙarasawa azmee tayi wurin da sehrish take akwance,ta zuƙunna tana ƙare ma jikinta kallo,tsananin tausayinta ne ya kamata,Allah kaɗae yasan tun yaushe take kwance a wurin cikin halin ha'ula'e,

   Hannu tasa tare da shafa fuskarta,busassun hawayene asaman fuskarta,la66anta duk sun bushe ƙamas dasu,

ɗagowa tayi tare da kallon jahad dake tsaye tana kuka,

   "Ki kwantar da hankalin ki,ina tunanin suma tayi ne sakamakon Ciwon cikin da tayi,Jinin dake ajikinta na al'ada ne,"

  Jin haka yasa jahad ta tsagaita da yin kukan,har hankalinta ya ɗan kwanta duk da akwai sauran damuwa atattare da ita,

  "Aunty azmee duk laifin mu ne ni da hosana,da ace bamu tafi mun barta a ɗaki ita kaɗai ba,da duk hakan bata faru ba,Allah kaɗae yasan tun yaushe take kwance a wurin nan,"

   "ɗaukomin ruwa,in yayyafa mata,"

Da sauri jahad ta nufi fridge dinsu,hannunta har kerma yakeyi wurin yin saurin ta buɗe,bottle water ta ɗauko,sannan ta dawo wurin azmee ta miƙa mata,kar6a tayi ta 6alle murfin ta ɗan kur6i ruwan abakinta sannan ta fesar dashi asaman fuskar sehrish,

  Dogon Numfashi taja,tare da sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya,muryarta ƙasa ƙasa tashiga fadin"Cikina zafi,Ciwo yakeyi mun!dan Allah abani magani nasha,kada na mutu,"

  "Jahad dauko mata magani,yana nan ajiye saman drawer ɗina,"juya jahad tayi da gudu ta nufi ɗakin azmee,

    Hannu azmee tasa tare da ɗago da kan sehrish ta azata asaman laps ɗinta,kafa mata ruwan tayi abakinta,a hankali tashiga kwankwaɗar ruwan,dama makoshinta a bushe yake,

   Dawowa jahad tayi hannunta ɗauke da maganin ta miƙa ma Azmee, bayan ta kar6a ta curo mata shi guda biyu ta sanya mata abakinta,tare da ruwan ta haɗiya,

  Bayan ta kammala sha,ta mika ma jahad robar ruwan"ki mayar dashi a fridge,bari na taimakata mu shiga daga ciki,"

   Dakyar ta cuccu6i sehrish,don ma ba wani nauyi ne da ita ba,cikin bedroom ɗin nasu ta shiga da ita,Jahad tabi bayansu,

  Toilet tashiga da ita,jahad sae faman zirga zirga take yi acikin bedroom ɗin nasu,duk wannan budurin da akeyi hosana nacan ɗakin azmee naɗe cikin bargo tana bacci,

   Muryar azmee tajiyo daga cikin toilet ɗin tana yi mata magana"Pad zaki miko mun,tare da pant ɗinta,"_

  Jiki na rawa jahad,ta ƙarasa gaban wardrobe ɗinsu,wurin kayan sehrish ta ɗauko mata pant,sannan ta haɗo mata tare da pads,

   Abakin ƙopar toilet din ta tsaya tare da ɗan knocking kopar,zuro hannu azmee tayi ta kar6i kayan,

  Komawa jahad tayi saman gadonsu,ta zauna tana jiran fitowarsu daga cikin toilet ɗin,

  Within mins,Azmee ta fito daga cikin toilet ɗin,hannunta dafe da sehrish,duk ta rurruketa gudun karta faɗi,Waist dinta na ɗaure da farin towel,sae faman cizon la66anta takeyi,saboda raɗaɗin da take ji har lokacin bata dawo cikin hayyacinta ba,

  Asaman bed ɗinsu Azmee ta kwantar da ita,jahad ta yafa mata bargo asaman jikinta ta lullu6eta,

  "Sannu sehrish,Allah ya baki lafiya," acewar jahad,

   Dama ance ciwon ƴa mace na ƴa mace ne,su da suka son zafin abun gashinan sun taimaka mata,saboda suma sunayi kuma sunsan cewa lalurace,sannan sunsan irin raɗaɗin da takeji ajikinta,dayawa Wasu mazan basu son ya abun yake ba,tunda bayi sukeyi ba,shiyasa har suke ganinshi amatsayin ƙazanta,kuma basu yi ma mata uziri,aduk lokacin da sukayi kuskuren da jini ya bayyana ajikinsu,Wasu mazan nake nufi ba duka aka taru aka zama ɗaya ba,Haka matan ba,bakowa bace ke taimakon ƴar uwarta ba,acikin irin wannan yanayin na period,

   "Sannu Allah ya baki lafiya,"azmee ce tayi maganar,yayin da idanuwanta ke akan sehrish,wadda ta runtse idanunta tana ta faman ciccije la66anta,

   Bata bar ɗakin nasu ba,har saida bacci ya ɗauki sehrish sannan tayi masu sallama,

  Kwanciya jahad tayi agafenta,suna fuskantar juna,zuba mata ido tayi tana kallonta,cike da so da ƙauna,

   A haka har bacci ya dauketa,


A 6angaren Sgr kuwa,ko sallar asuba bai samu ya halarta ba,Acikin bedroom ɗinshi yayi sallar,komawa yayi saman katafaren gadonshi ya kwanta yayin da blue eyes dinshi ke kallon Ceilling,Kalaman sehrish ne suka shiga dawo mashi acikin zuciyarshi,bakomai ne yafi tsaya mashi aranshi ba fa ce kalmomin nan guda biyu da ta kirashi dasu,MARA TAUSAYI MARA IMANI!sannan kuma tayi comparing ɗinshi da wannan fasiƙin mutumin, yaji raɗaɗin abun sosai acikin zuciyarshi,tayi matuƙar ɗaure mashi kai,Ko a ina tasamu ƙwarin guiwar gaya mashi magana?duk irin yadda take jin shakkarshi?yarinyar da ko cikin idonshi tsoran kallo takeyi,balle har ta ɗaga mashi yatsa,

    Gyara kwanciyarshi yayi,ya koma yana fuskantar right hand ɗinshi,sannu a hankali bacci ya dauke shi batare da ya shirya yin shi ba,


  Wuraren ƙarfe Takwas na safe,jahad na cikin bacci,taji shessheƙar kuka acikin kunnuwanta,buɗe idanuwanta tayi tare da wurgasu wurin da take jin sautin kukan,Sehrish ta gani zaune ta jingina bayanta a head board ɗin gadon,sae kuka takeyi kamar wadda ta rasa wani mai mahimmanci arayuwarta,

  Da sauri jahad ta miƙe zaune,tana kallonta tace"Sehrish!lafiya kike kuka?ko haryanzu ciwon cikin ne"?

  Girgiza kanta tayi alamar a'a,

"To ki faɗamun meke damunki ne"?da damuwa a fuskarta tayi maganar,

  Cikin shesshekar kuka Sehrish ta soma magana,

   "Jahad!na shiga uku!najama kaina bala'e,Jiya nayi ma babban yayanmu rashin kunya,batare da sanina ba,wlh sai yau da safe na tuna duk abunda ya faru,nasan cewa bazai ƙyaleni ba,Dole ya hukunta ni"ta karasa maganar tare da sa hannu tana matsar hancinta,

  Hankali atashe jahad tace"Sehrish!kodai mafarki kikayi ne?ae babban yayanmu bai dawo ba,kin manta sun tafi damaturu ne"?tayi maganar tana ƙoƙarin fahimtar da ita,

  "Wlh jahad ba mafarki nayi ba,jiya ya dawo acikin gidan nan,yana nan a part dinsa,"

   Hannu jahad tasa tare da dafe saitin zuciyarta adan tsorace tace"Munshiga Uku!garin yaya har kikayi mashi rashin kunya?kuma kina acikin hayyacinki babu magagin bacci atare dake"?

  "Bana acikin hayyacina jahad,zafin ciwone yasa na balbaleshi da masifa,har ina nuna shi da yatsa..."kaf ta kwashe duk abunda ya faru a tsakaninsu ta sanar ma jahad,

   Hannu jahad tashiga tafawa tana faɗin"wlh babu ruwana!sehrish kin shiga uku,mai kwatarki a hannunshi yau sai Allah,hukuncinki yafi ƙarfin ayi maki shi acikin gidan nan sai dai yakai ki can headquater dinsu,"

Jin wannan maganar,ya ƙara ɗaga hankalinta,fashewa ta kuma yi da kuka,

  Lallashinta jahad ta shiga yi"Am sorry,zolayarki nakeyi,amma gaskiya sehrish Anya baki sha Codine ba?Yo ni ko giyar wake nasha,ae bazan iya tunkarar babban yayanmu ba,balle har in gaya mashi irin zafafa kalaman da kika yada mashi,"

   Cikin shesshekar kuka tace"dan Allah jahad ki bani shawara,kodai in gudu in bar gidanne?kinga su daddy basu nan,zai iya kashe ni,"

   Shiru jahad tayi tana saƙa wani abu aranta,sehrish kuwa ta zuba mata ido tana jiran jin shawarar da zata bata,

  "Kinsan me!kada ki kuskura kije bashi haƙuri,Dama kin faɗa mashi cewa kada yayi tunanin zaki gudu kibar gidan ne,ko kuma zaki zo bashi hakuri,Sannan kuma kince mashi ba zaki ƙara zuwa part dinshi ba koda ace kin kammala ƙazantar ne,Inaso ya tabbatar da cewar dagaske kike mashi bada wasa ba,hakan zaisa abun ya tsaya mashi acikin ranshi kuma zaiji shakkar ƙara faɗa maki irin waɗannan kalaman saboda gudun kar girmanshi ya faɗi,sannan idan yaga kwana biyu baki je yi mashi aiki ba,ina da tabbacin cewar zai nemeki ne,Amma muddin kika je bashi hakuri,wlh sai kinyi danasani ne,"

  "Amma jahad,rashin kunya fa nayi mashi,yakamata na bashi hakuri in ba haka ba Zai gane cewa ina acikin hayyacina na gaya mashi magana,kuma zai dinga yi mun kallon mara kunya ƙarshe ma ya tsane ni gaba daya,"

  Murmushi jahad tayi tare da cewa"indai bazai ta6a lafiyar jikinka ba toh da sauki,ƙwara yayi maki kallon mara kunyar,akan dai kije bashi haƙuri,nasan bazaki fahimce ni ba,A yanzu amma nan gaba zaki ga amfanin yin hakan da kikayi,"_

  Zugudum sehrish tayi tana doubting akan abunda jahad ta faɗa mata,Anya kuwa jahad ba hanyar banza takeson ɗaurata ba?in ba haka ba saboda me zata hana ta zuwa bashi haƙuri,bayan itace mai laifi,A matsayin shi na mijinta kuma yayanta,bai kamata tayi mashi hakan ba,sannan kuma taƙi zuwa bashi hakuri,

Shigowar azmee ne ya katse mata zancen zucin nata,atare suka juya suna kallonta,

   "An kammala breakfast,yana a dining yana jiranku,"

  Ta karasa maganar tare da kai idanunta kan sehrish tace"Ya jikin naki"?

"da sauƙi alhamdullah,nagode ssai da irin kulawar da kuka bani,"

  "Kada ki damu ae duk yiwa kaine,Amma naga kamar hawaye akan fuskarki,Ko haryanzu akwai ciwon ne"?

  "A'a,naji sauƙi sosai,"

Murmushi azmee ta saki,kafin ta juya ta fuce daga ɗakin,

   "Jahad kije kawai kuyi breakfast ɗin,Ni zan zauna a ɗakine,kada mu haɗu da babban yaya,Don nasan bazaiyi mun da kyau ba,"

    "kada kisa damuwa aranki mana,duk kin bi kin tashi hankalin ki,Da yunwa zakiyi ta zama ne?bazaki ci komai ba"?

   Shiru tayi ba tare da tace komai ba,

  "Okey,zan kawo maki breakfast ɗin aɗaki sai kici hakan yayi maki"?

  Ɗaga mata kai sehrish tayi"Eh,ki kawomin anan,zan fi samun kwanciyar hankali,akan in fita wajen,"

  Saukowa jahad tayi daga saman gadon,ta buɗe kopa ta fuce daga dakin,

  Ajiyar zuciya sehrish ta sauke,tunani ta shiga yi ko a wani hali babban yaya yake ciki,Yayi bacci jiya ko baiyi ba,Allah yasa dai kalamanta basu ta6a mashi zuciyarshi ba,


shigowa jahad ta kumayi hannunta ɗauke da madaidaicin tray,kayan tea ne sai chips da sauran abunda baza a rasa ba,Asaman drawer ta ajiye mata shi,sannan ta juya ta fuce daga ɗakin,

  Matsawa tayi kusa da trayn,sannan takai hannu ta ɗauki cup of tea ɗin tana ɗan kur6arshi,

   Cikin ƙankanin lokaci ta kammala yin breakfast ɗin nata,

   Zama tayi cike da fargabar abunda zai biyo baya,

   Ranta ne ya bata cewar,ta jaraba kiran aunty azeema ta sanar da ita abunda ya faru atsakaninta da sgr,may be ta samu shawara mai kyau a wurinta,

  Da sauri ta ɗauki wayarta dake ajiye saman gadon,contact ta shiga ta lalubo numbarta,ta danna mata kira,tana fara ringing,Azeema ta ɗaga kiran nata,

  Tunkafin tafara magana hajiya azeema tace"2 days ba hello ba hi ko?har kin fara mantawa dani ko,"

  Murmushi sehrish tayi tare da cewa"ba haka bane,Aunty azeema kusan kullum ne saina nemi layinki,amma baya shiga,"

  Azeema tace"Hakane fa,nifa wayata indai bani na kira mutun ba,da wuya ne a same shi,kullum busy nake,"

  Shiru sehrish tayi tana tunanin ta ina zata fara kora mata jawabi,

  "Ina sauraronki,Har yanzu ba wani cigaba a zamanki dashi"?_

   Nan fa sehrish ta samu ƙwarin guiwar sanar da ita duk abunda ya faru atsakaninsu daren jiya,

  Tayi tunanin aunty azeema zatayi mata faɗa ne,amma da buɗar bakinta sai cewa tayi"Very Good!hakan da kikayi mashi yayi mun dai dai wlh,"

   Sakin baki sehrish tayi tamkar tana agabanta,kusan bakinsu ɗaya da jahad,

  "Kada ki kuskura kije bashi haƙuri!nafi so ya gasgata kalamanki"

  Cike da mamaki sehrish tace"Aunty azeema dagaske kike?kada na bashi haƙuri"?

  "Ƙwarai kuwa,ina goyon bayan hakan ɗari bisa ɗari,kuma kada ki kuskura kije part dinshi da sunan aiki,Ki rabu dashi,dama ae yace kada ki koma mashi har saikin kammala kazantar kibarshi a hakan,kada ki wani ji tsoro,"

  Lumshe ido sehrish tayi tare da ware su fuskarta da dan murmushi tace"Shikenan aunty azeema bazanje ba in sha Allah,"

  "Namanta ban sanar dake ba,nafa dawo nigeria,tun jiya amma na wuce damaturu,bazan samu zuwa nan ba yanzu saboda abunda ya faru na rasuwar modibbo,amma kada ki damu zan bada saƙo ta wurin junaid,naji yace zai biyo Abusufyan idan ya tashi dawowa,zan bashi ya kawo maki har gida,Sannan zanyi maki bayanin yadda zakiyi amfani dasu,koda ta wayane,"

   "Nagode sosai Aunty azeema,Allah yasaka da alkhairi,Amma yaushe zaki dawo nan?don nayi kewarki sosai,"

  Dariya hajiya azeema tayi tare da cewa"Very soon zan dawo,"

  Sehrish tace"to shikenan,Allah ya kaimu lokacin,"

  "Ameen my daughter,"

  Sun jima suna waya kafin daga bisani ta ajiye wayar,har hankalinta ya kwanta,duk da akwai sauran fargaba atare da ita,


 saukowa tayi daga saman gadon,Wardrobe ta nufa,hannu tasa ta buɗe,Arab gown ce ta ɗauko pink colour,tare da mayafinta shima pink ne amma bai ciza ba,kamar na rigar,zura kayan tayi ajikinta,sannan ta koma gaban mirror ta zauna,zuba ma mirror din ido tayi tana kallon fuskarta,ta cikin madubin,yayin da zuciyarta ke tariyo mata abunda ya faru adaren jiya,


A 6angaren Sgr kuwa,wata irin matsiyaciyar yunwa ce ta farkar dashi daga bacci,saukowa yayi daga saman gadon,Jallabiya ce ajikinshi,wuce wa yayi wurin closet ɗinshi,withins mins ya shirya kanshi cikin jeans da t shirt Maroon colour,rigar ta fito da surar jikinshi saboda ta ɗanyi tighting ɗinshi,Ƙafarshi na sanye cikin Canvas sneakers,

   fitowa yayi daga part ɗinsa,Ya nufi downatairs,a natse yake taka staircase din har ya sauko down,Su jahad na zaune ita da hosana saman Sofa mai mazaunin mutun uku,suka jiyo takun takalmanshi,


  ɗagowa sukayi atare suna kallonshi,lokacin da ya ƙaraso wurinsu,da sauri suka haɗa baki wurin gaisar dashi,

  Batare daya kallesu ba,Ya amsa masu gaisuwarta su,fuce wa yayi daga cikin main palour ɗin,Kaitsaye Motarshi ya nufa,Amstrong na ganin shi da sauri ya ƙarasa tare da buɗe mashi motar ya shiga daga ciki,sannan shima ya bude driver seat ya zauna,

   Kafin ya tashi motar,ya ɗan dago tare da kallonshi ta cikon mirror yace"Sir,Where are we going"?

   "Restaurant,"ya bashi amsa atakaice,

    Shiru amstrong yayi batare daya tashi motar ba,Hakan yasa shi cewa"what are u waiting for"?

  Cikin harshen turanci amstrong yace"Sir,kayi haƙuri da abunda zance,Amma zuwa restaurant ba naka bane,da matsayinka aganka a restaurant ka je cin abinci?kaida ya kamata ace a gida ake girka maka,idan ba damuwa zanje nakawo maka,ka koma ciki pls"

   Tunda ya soma magana sgr yayi shiru yana sauraronshi,saboda amstrong yana ɗaya daga cikin waɗanda suke Control dinshi,"

  Amsa mashi yayi da okey,sannan ya buɗe motar ya fuce,

  Duk wannan abun dake faruwa sehrish na tsaye a wurin window tana leƙen motarshi,taga lokacin daya shiga cikin motar,kuma sai taga ya fito daga ciki,

  Aranta tashiga tunanin ko lafiya,

Dawowa cikin gidan yayi,Part ɗinshi ya koma ya zauna saman sofa yana jiran dawowar Amstrong,dan bala'e ga abinci acikin gidan amma yafi ƙarfin yayi ma wani magana ya kawo mashi abincin,tunda ya ƙori mai aikin tashi,

  Cikin minti goma sha biyar,Amstrong ya shigo cikin gidan hannunshi dauke da ledojin,Su jahad na ganinshi suka shiga gaisar dashi,fuskarshi ɗauke da murmushi ya amsa mashi,sannan ya wuce upstairs sashen sgr,

  Yana barin wurin da gudu jahad ta nufi ɗakinsu,tura kopar tayi ta shiga ciki tana faman ƙwala ma sehrish kira,

   tsaye ta same ta hannunta ruke da wayarta,ganin jahad ta faɗo ɗakin babu sallama yasa tace"Lafiya"?

   Jahad tace"Yanzu naga wannan sojan wanda yake yin driving ɗin babban yayanmu,Hannunshi dauke da ledojin kuma na restaurant ne don naga sunan ajiki,"

   Cike da mamaki sehrish tace"to fa!ko meyasa ya aika akawo mashi abinci bayan ga wanda aka girka agida"?

  Jahad tace"Yanzu haka saboda abunda ya faru atsakaninku ne jiya,shiyasa yaƙi cin abincin gidan,"

   Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,

   "Yanzu haka,saboda yana ƙyamar girkina ne saboda ina yin period,shiyasa bazaici abincin gidan ba,"acewar sehrish,

  Jahad tace"Amma ae bake kikayi girkin  ba,Aunty azmee ce ta girka,Gaskiya nafi tunanin cewa wani abunne daban yasa bazaici abincin gidan nan ba,"

   Murmushi sehrish ta ɗanyi tare da cewa"kinsan Allah babban yaya bazai iya cin abincin nan ba,Ina nan dake ƙarshe sai dai azubar da shi abanza"

     Jahad tace"Mu zuba ido mu gani,zaici ko bazaici ba,"


***


Excuse sir!muryar amstrong ce ta dawo dashi daga zurfin tunanin da ya faɗa,

   Muryarshi a kasalance yace mashi"Come in,"

  Shiga ciki yayi tare da ajiye mashi asaman table dinshi,Sannan ya sara mashi,kafin ya fuce daga ɗakin,

  

  Kusan minti 5 bai motsa ba,kamar ba yunwa yake ji ba,Hannu yasa tare da curo bugger daga ciki,yana ƙokarin kaita a bakinshi ,Ya tuna da jinin daya gani ajikin wandon sehrish,aikuwa nan take Ya sake ta ta faɗi saman table din,Wani irin yunƙurin amai ne ya taso mashi,da sauri ya miƙe ya nufi cikin toilet,ya shiga kwara amai agaban basin,Ba ƙaramin galabaita yayi ba,ƙyanƘyami ya hana yaci abincin ga yunwa na cinshi,har zazza6i ya fara kamashi,

Tap ya kunna ruwa ya shiga kwararowa,tarba hannayenshi yayi ya shiga kuskure bakinsa,kafin ya wanke face ɗinshi,

   Fitowa yayi daga cikin toilet,yana faman sauke ajiyar zuciya,komawa yayi saman gadonshi ya kwanta,wasa wasa Zazza6i ya rufe shi,temperature ɗin jikinshi yayi zafi sosai,

   

Kasa samun natsuwa sehrish tayi,tunda taga an kira sallar magrib da isha'e,sgr bai fito daga part ɗinsa ba,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankalinta yayi ba,jiki na rawa ta fito daga ɗakinsu ta wuce kitchen,Anan ta samu azmee tana ƙarasa gyara kitchen din ita da hosana,

   Ganinta yasa azmee tace"Ya jikin naki"?

   "Da sauƙi aunty azmee,sai dai...."shiru ta ɗanyi bata ƙarasa maganar ba,

   Tunkarota azmee tayi tare da ruƙo hannunta suka ja daga gefe sannan tashiga tambayarta meya faru,

  "Aunty azmee,wani abu ya faru jiya tsakanina da babban yaya ban sanar maki ba,"

  "Faɗamun meya faru,Allah yasa dae ba wani laifin kika aikata masa ba,"

   Nan sehrish ta kwashe duk abunda ya faru ta sanar mata,

  "Ya salaam,' azmee ta ambaci hakan hankalinta aɗan tashe tayi maganar,

  "Wlh aunty azmee ba laifina bane,bana acikin hayyacina ne,shiyasa nayi mashi rashin kunya,"

  Muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,

   Cigaba da magana tayi"Ni babban abunda yafi tayar mun da hankali,har aka kammala sallar magrib da isha'e,banga ya fito daga cikin part dinshi ba,kuma inajin tsoran in tunkare shi,saboda nasan dole ya hukunta ni,kuma nayi shawara da aunty azeema tace kada na kuskura naje bashi haƙuri,haka jahad ma tace mun,"

   "Sehrish idan kikace zaki ɗauki shawarar Azeema,zata kaiki ta baroki ne,saboda ita wata irin wayayyiyar maca ce,Bazan hana ki ɗauki shawararta ba,amma inaso ki tuna matsayinshi a wurinki,Yayanki ne shi kuma Mijinki,jiya ya kwana da fushinki acikin zuciyarshi haka yauma ya tashi da fushinki,tabbas zaki jefa kanki cikin matsala ne,in har bakiyi hanzarin neman afuwarsa ba,Yakamata kije ki bashi haƙuri,kuma ki sanar dashi cewa ba a hayyacinki kike ba!"

. "yanzu aunty azmee kina nufin inje in bashi haƙuri"?

   "Eh,haka nake nufi,"

"Amma fa yace mun kada na kuskura na ƙara zuwa part ɗinshi har saina kammala period ɗina,"

  "Kada ki damu da wannan kije kawai,in sha Allah babu abunda zai faru,"

  Tashin hankalin da ba'a sama shi date,Shin shawarar wa kuke tunanin zatayi ma sehrish amfani?Shawarar Azeema da Jahad,ko kuwa shawarar Aunty Azmee,





  



  

  

  




   

   


  

  



   


     





   

  

    

  

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana ta whatsapp dan Allah banda kiran wayar,bana ɗagawa 08103884440❤_




Nagode da shawararki Aunty azmee,in sha Allah zanyi amfani da ita"

   "Yawwa haka nake son ji" azmee tayi maganar tare da komawa cikin kitchen,Sehrish kuwa bata wuce part ɗinshi ba,bedroom ɗinsu ta wuce,sam takasa samun natsuwa,ta rasa shawarar wa zata ɗauka acikinsu,bakomai yafi sata fargaba ba,fa ce abunda zai biyo baya idan tayi kuskuren zuwa sashen shi,


Har wuraren ƙarfe goma sha biyu na dare bata runtsa ba,tana zaune saman gadon nasu,yayin da wayarta ke ruƙe a hannunta,Hosana na kwance a gefenta tana bacci cikin bargo hankalinta kwance,Jahad kuma na can ɗakin azmee,

   Wani tunani ne yazo mata acikin zuciyarta,da sauri ta shiga contacts ta lalubo layin Aunty azeema,ta danna mata kira,cikin sa'a ta ɗaga kiran nata,

  Kara wayar tayi a kunnanta,tare da yi mata sallama,

   "Assalamu Alaikum,"

Aunty azeema tace"Wa'alaikum salam daughter,me kikeyi har yanzu baki yi bacci ba,"?

   "Na kasa yin bacci ne,ina cikin damuwa"acewar Sehrish,

  Azeema tace"kodai duk fargabar babban yayan naku ne?

"Ba haka bane,Aunty azeema,na ɗan shiga damuwa ne,yau babban yaya bai fito daga part ɗinshi ba,har akayi sallar La'asar da magrib,bai fito ba,"

  Maganar sehrish ta ɗan tashi hankalin hajiya azeema,

  "Amma ya ci abinci kuwa"?

Sehrish tace"baici abincin gida ba,ɗazu dai yasa an kawo mashi abincin restaurant,amma bani da masaniya akan yaci ko bai ci ba,"

  Shiru hajiya azeema tayi na wani dan lokaci,haka itama sehrish ɗin,Kowa da abunda yake saƙawa aranshi,

  "Kina jina"muryar hajiya azeema ce ta katse mata zancen zucin da ta shiga,

  "Ina sauraronki Aunty,"

"Gaskiya akwai matsala,saboda ba ƙaramin abu bane zai hana Sgr zuwa masallaci ba,Ina da tabbacin cewa zuciyarshi ta motsa,Allah kaɗae yasan halin da yake ciki,gashi babu kowa agidan idan baku ba,dama ace su Abbanku suna nan ne ko Omar zasu iya shawo kan matsalar,Amma yanzu haɗari ne wani ya tunkare shi,tunda ba'asan halin da yake ciki ba,wani irin zafin zuciyane dashi idan ya fusata kowa tsoran tunkararshi yake yi,Amma idan akaci sa'a,Ya yanke jiki ya faɗi ya suma a lokacin da zuciyar tashi ta motsa,to tabbas koda ya farfaɗo bazai tashi da wannan fushin ba......"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar,tana sauke ajiyar zuciya,

  "Yanzu ya zamuyi kenan"?sehrish ta tambaya,fuskarta dauke da damuwa,

  "Abunda za'ae yanzu shine,inaso kije part ɗin nashi kiga a wani hali yake ciki,Amma fa kada ki bari ya ganki,a 6oye zaki je,in ba haka ba a tsinto ƙasusuwanki a dakinshi,"ta karasa maganar cike da zolaya,

  Dariya sehrish ta dan yi duk da tsoron daya kamata,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Shikenan Aunty azeema,zanje in sha Allah,"

  Azeema tace"yawwa daughter,idan kin dawo duk abunda ya faru ki sanar dani pls,"

  "Toh Aunty,"

Daga nan sukayi sallama,saukowa daga saman gadon Sehrish tayi,bayan ta ajiye wayar saman side drawer,ta zura slipper ɗinta dake ajiye nan ƙasan,ta gyara mayafin jikinta sannan ta fito daga dakin nasu,

  Tunkafin ma ta hau upstairs din gabanta ke faɗuwa rass rasss,tamkar wadda zata tunkari wani zombie,


A hankali take taka staircase ɗin harta samu ta haura sama,tana tafiya tana ambaton"La'ilah ha illa antas subhanaka inni kuntu minazzalimin,"har tazo bakin ƙopar part dinshi,kamar wata 6arauniya haka ta leƙa cikin falon,ganin baya ciki yasa ta sauke ajiyar zuciya,cikin sanɗa ta zura ƙafarta ciki,a hankali take tafiya,gudun kada yaji sautin takalminta yasa ta zuƙunna tare da ciresu ta ruƙesu a hannunta,


A ƙopar bedroom ɗinshi ta tsaya,har lokacin bata daina ambaton La'ila ha illah anta subhanala inni kuntu minazzalimin,acikin zuciyarta ba,saboda tsabar tsoro,zuciyarta tamkar zata fito daga ƙirjinta,saboda bugun da take yi mata,daraam!daraaam,

    A hankali ta ɗan zura kanta tare da leƙawa cikin ɗakin nashi,

  Kwance yake saman gadon,gangar jikin na asaman gadon,yayin da head ɗinsa zuwa wuyanshi suka zuro daga gefen gadon,Sumar kanshi ta zubo har saman floor,

  Gabanta ne ya faɗi rasss!tun daga kan yadda yayi kwanciyar ta gane cewa babu lafiya,gaba ɗaya zufa ta wanke jikinshi tamkar wanda ya watsa ruwa ajikinshi,ta ko'ina zufar ke tsastsafo mashi,gaba ɗaya ga66an jikinshi sun sake,

   Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,batasan ko bacci yake yi ba,ko suma yayi,Allah wa'alamu,

   Zura ƙafarta tayi yayin da gabanta ke ci gaba da faduwa,Shiga cikin bedroom ɗin tayi,har zuwa wurin gadon nashi,Yanayin kwanciyar tashi ma,Zata iya haifar mashi da matsanancin ciwon wuya,saboda yadda ya yi sadda kai,

    Zuba mashi ido tayi tana kallon fuskarshi,daga gani ba ƙaramin jiki yaji ba,

   Tunani ta shiga yi,kodai ta ɗaukko ruwa ta yayyafa mashi,duk da bata da tabbacin cewar ko suman yayi ne,amma ga dukkan alamu ya suma ne......  ,

  Da sauri ta juya ta koma palour,fridge ta nufa da sauri sauri ta buɗe shi ta ɗauko robar ruwa,Sannan ta dawo cikin ɗakin nashi,Tashin hankali,Tsayawa tayi tana tunanin taya ma zata fara yayyafa mashi ruwan batare daya ganta ba?kyau tana watsa mashi ta watsa da gudu kafin ya murmure,

   Jikinta sae kerma yake yi,a haka ta buɗe robar ruwan,ta tarfa ruwan a hannunta,Ja da baya ta ɗan yi,sai da taba da interval sosai a tsakaninsu,daga inda take ta yarfa mashi ruwan akan fuskarshi,yaraf!ya saukar mashi,Aikuwa nan take ya shiga sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya,da gudun gaske sehrish ta 6oye acikin labulen ɗakin nashi,zuciyarta na ɗar ɗar,

  Sannu a hankali ya buɗe blue eyes ɗinshi,yana faman sauke ajiyar zuciya,bin kasan bedroom ɗin nashi yayi da kallo,kafin yayi yunƙurin mayar da kanshi saman Gadon nashi,saman pillow ya aza kanshi,yasa hannu yana murza wuyanshi saboda raɗaɗin da ya ji a wurin,lumshe idanuwanshi yayi tare da sake buɗesu,jikinshi babu ƙwari amma zazza6in ya sauka daga jikinshi,dakyar ya iya miƙewa daga zaune,ya jingina bayanshi a head board ɗin gadon,Yayin da idanuwanshi ke a lumshe,

  Sehrish dake 6oye bayan curtains ɗin ɗakin,tana jin duk wani moving ɗinshi,ta toshe bakinta da hancinta da tafin hannunta,saboda gudun kar ya gane akwai mutun aɗakin nashi,

   Almost 15 mins yana a zaune bai motsa ba,tun da yake a arayuwarshi bai ta6a shiga matsanancin halin daya shiga ba irin na yau,kamar wani mara gata,sae kace ba Surgeon General ba,Yau ya ɗanɗani zafin kadaici,duk a sanadin kalaman da sehrish ta gaya mashi,

   Saukowa yayi daga saman gadon,Ya tsaya atsaye tare da sanya hannu ya tu6e shirt ɗin dake ajikinta,Yayi wurgi da ita saman gadon,Zame belt ɗin wandonshi yayi ya jefar dashi saman rigar,sannan ya zame dogon wandon,Ya rage daga shi sai short light blue,

   yana tafiya cike da rashin ƙwarin jiki,a haka har ya buɗe toilet ya shige ciki,Sehrish na jin motsin buɗe kopar toilet,Jiki na rawa ta lalla6a,saɗaf saɗaf ta fito daga cikin bedroom din,Hannunta riƙe da bottle water din,Saman fridge ta ajiye robar ruwan sannan ta kama hanyar fita daga falon,Har ta kai bakin kopar dakin ta juyo ta kalli kayan Breakfast ɗin da Armstrong ya kawo mashi,nan ta gane cewa bai ci komai ba,

   Fitowa tayi daga part ɗin nashi,ta saukko downstairs da sauri ta nufi ɗakinsu,bayan ta shiga ciki ta ɗauki wayarta,tare da danna ma Aunty azeema kira,nan take ta ɗaga kiran,

  Da sauri ta sanya wayar a kunnanta,tun kafin tayi magana Hajiya azeema tace"Ya ake ciki ne?

  Sehrish tace"Naje part ɗin nashi,na same shi a sume saman gadonshi,gaskiya ba ƙaramin jiki yaji ba,nasamu dae na yayyafa mashi ruwa batare da ya ganni ba,na lalla6a na fito daga ɗakin nasa,naji ya shiga toilet da alama wanka zaiyi,Amma fa naga kayan abincin da aka kawo mashi daga restaurant,Da alama bai ci komai ba,"

  Hajiya azeema tace"Good!,naji daɗi da bai ganki ba,Kuma naji daɗin suman nan da yayi,saboda zai samu sauƙi acikin zuciyarshi,duk da nasan dole ya ƙullace ki a aranshi,"

  Murmushi sehrish ta ɗan yi kafin ta kuma cewa"duk yau baici komai ba,"

"Kada ki damu da wannan,ita yunwa bata da hankali,Ina nan dake wannan abincin da ya bari wanda aka kawo mashi na restaurant,Shi zai nema ina nan dake,yanzu dae ki kwanta kiyi bacci',

  Hankalin sehrish ba ƙaramin kwanciya yayi ba,

   "Ki kwanta kiyi bacci,Sae Allah ya kaimu gobe zamuyi magana," sallama sukayi da ita,Sehrish ta kwanta saman gadon tare da ajiye wayarta saman stomach ɗinta,yayin da idanuwanta ke fuskantar ceilling ɗin dakin,


Sgr kuwa,bayan ya fito daga wankan da ya shiga,jallabiya ya zura ajikinshi ash colour,har wani jiri yake gani saboda tsabar yunwar da ya ke ji,ba arziƙi ya dawo palour saman sofa ya zauna,tare da kai hannu ya ɗauki burger ɗin nan,da ya ajiye saman table,Turata yayi cikin bakinsa ya shiga cin ta har yana shaƙewa,a ƙa'ida baya cin abincin da ya sha iska wanda aka bari a buɗe,Amma yau ba kanta,Ci kawai yakeyi,tass ya cinyeta,Miƙewa yayi da sauri ya nufi wurin fridge don ya daukko drink din da zaisha,hannu yakai tare da ɗaukar bottle water ɗin da Sehrish ta bari asaman fridge ɗin,6alle marfin yayi ya kafata a bakinshi yana kwankwadar ruwan,sae da yayi rabin ruwan dake acikinta,sannan ya dakata da shan ruwan da yake yi,Sai lokacin ya ankara da inda ya ɗauki robar ruwan,Shiru ya ɗan yi tare da zubawa robar ruwan dake hannunshi ido yana kallonta,Shi dai yasan bai ajiye ruwa asaman fridge ba,tunani ya shiga yi,Yanayin yarda ya farka duk da akwai zufa ajikinshi,amma tabbas yaji Saukar ruwa akan fuskarshi wannan ya tabbatar mashi da cewar wani ya shigo cikin part ɗinsa,Hannu yasa tare da buɗe fridge ɗin ya saka robar ciki,Sannan ya ɗauki coke mai sanyi,

  Komawa yayi saman sofa din,ya zauna tare da kai hannu ya buɗe daya daga cikin ledojin,take away ya curo ya buɗe shi Chips ne aciki duk yayi sanyi,amma ahaka ya shiga turashi acikin bakinshi yana ci,bai ta6a shiga yanayi irin wannan ba a rayuwarshi,tass ya cinye duk wani abu dake a wurin,bayan ya kammala cin abincin,mikewa yayi ya koma cikin bedroom ɗin shi,ya ɗauko wayarshi,Sannan ya dawo saman sofa ɗin ya kwanta tare da miƙar da ƙafafunshi saman hannun kujerar,

  Zubama screen ɗin wayar ido yayi yana kallonshi batare da ƙyaftawar ido ba,yama rasa wa zai kira yaji sanyi aranshi,numbar Abbansu ya lalubo ya danna mashi call,Ringing din farko Abbansu ya ɗaga kiran nashi muryarshi da alamun bacci yace"My son,Me kake yi har yanzu baka yi bacci ba"?

   batare da ya amsa mashi tambayarshi yace"Daddy,when zaku dawo?gida duk ba daɗi,"

  Tsananin mamakine ya kama Abbansu,Yau Sgr da kanshi yake cewa Gida babu daɗi saboda basu nan,ta wani 6angaren kuma yaji daɗin hakan sosai,

   "Kayi missing ɗinmu ne"?Abba ya tambayeshi,

muryarshi akasalance yace"Yeah,especially you,I missed u so much,"

  Farin ciki ne ya cika Abbansu,kamar ya janyoshi ta cikin wayar ya rungumeshi,

    "Pls Daddy,just come back home,if not zan biyoku damaturun ne,in yaso saimu dawo atare,"

  Sgr na jiyo sautin muryar Abbansu yana tiƙar dariya,

   "Are u laughing at me"?

Tsagaitawa Abbansu yayi da yin dariyar yace"dole nayi dariyar Farin ciki mana,Yau ya kasance rana ta farko daka nuna kayi kewarmu sosai,naji muryarka wani iri tamkar zaka yi kuka,tell me what's wrong with u,wani ya ta6a mun kaine"?

  Sgr yace"bana jin daɗin zuciyata ne,ko zaka sanyani farin ciki?

  Abba yace"yanzun nan kuwa,bari na tuna maka wani abu,lokacin da kana ɗan jinjiri dakai cikin towel,kyakkyawa da kai,Na ƙwallafa rai sosai akan ka, kai kuma ga kyuyar tsiya,ka ƙi jinin baƙin mutun ya ɗauke ka,koni da nake mahaifinka ban isa na ɗauke ka ba,in ba bacci ya ɗaukeka ba,Sae in lalla6a in shiga ɗakinka,In zauna saman gadon in zuba maka ido inta kallonka,araina ina cewa Yanzu wannan mallakina ne,Allah ya bani Halak malak,Haka zan tasaka gaba ina kallonka,da zarar ka farka kuwa,mukayi ido biyu,kamar kaga wani 6arawo haka zaka fasa ihu kana ambaton sunan Mommynka,"

   Lumshe ido Sgr yayi yana sauraron Abbansu,fuskarshi asake tamkar zaiyi murmushi,wata irin natsuwa yaji acikin zuciyarshi,

  "Amma daga baya,saboda irin kulawar da nake baka sae ka gane cewa ni mahaifinka ne,kuma inason ka sosai fiye da kowa,sae gashi da kanka,kake zuwa wurina don in ɗauke ka,mu tafi yawo atare,"

   jikin Sgr ba ƙaramin sanyi yayi ba,kalaman Abbansu sunyi matuƙar ta6a mashi zuciya,

   "Amma ni sai inga kamar baka sona,baka damu dani ba kamar yadda na damu da kai...."

  Tunkan ya ƙarasa maganar Sgr ya katse shi da cewa"Daddy kadaina faɗan hakan bana jin daɗi,duk duniya bani da tamkarka,kaine mahaifina,Jigona kuma ginshiƙi na,Abun alfaharina,madubin dubawana....". 

  Wani irin farin cikine ya lullu6e Abbansu,bai ta6a jin irin wannan yabon daga bakin Sgr ba,sai yau har ya fara tunanin anya kuwa cikin hayyacinshi yake gaya mashi waɗannan kalaman?ko kuwa ya ɗan kora wani abune,Gashi ya saki jiki sai surutu yake yi mashi kamar ba wannan miskilin ba..."

  "Pls Rafayet,ka maimaita mun kalaman nan daka faɗamun,inaso nayi recording ɗinsu,"

  fashewa da dariya Sgr yayi,hakan ba ƙaramin ɗaurewa Abbansu kai yayi ba,

  Cike da mamaki yace"Rafayet,dariya kakeyi mun,dan Allah faɗamun kodai kasha kwaya ne yau,"

   "Daddy bansha komai ba,lafiyana ƙalou,kawai ina jin daɗin waya da kaine,ka bari idan ka dawo gida zan sake maimaita maka sai kaji a kunnanka,"

  Cikin raha sukayi wayar gwanin ban sha'awa hira irin ta da da mahaifi suka yi wadanda suke cikin begen juna,a karshe sukayi sallama,sauke ajiyar zuciya yayi tare da aza wayar saman chest ɗinshi,wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarshi,still kalaman Sehrish nadawo mashi acikin ranshi,waɗannan kalaman dae su suka fi ta6a mashi zuciya,Mara tausayi mara Imani,da kuma danganta shi da ya sayyadi,


Tariyo abunda ya faru tsakaninsu ya shiga yi cikin ranshi,Yadda ya damƙo wuyan rigarta tare da yin wurgi da ita ta bugi bango,har ta fashe da kuka saboda zafin da taji,da kuma munanan kalaman da ta jefa mashi,da alama nazarin wani abu yake yi,dangane da abunda ya faru jiya atsakaninsu,


Ya jima asaman Sofa ɗin,kafin daga bisani ya koma cikin bedroom ɗinshi,darduma ya dauƙo ya shimfiɗa tare da kabbara salla,Sae da ya fara biyan bashin sallolin da baiyi ba,sannan ya ɗaura da yin nafilfilin daren daya saba yi,bayan ya kammala ya ɗauki qur'ani ya shiga karantawa,nan take yaji natsuwa tazo mashi acikin zuciyarshi,bashi ya kwanta bacci ba,har sae wuraren ƙarfe biyu na dare,sannan ya haye saman gadonshi ya kwanta,bacci 6arawo yayi awon gaba dashi,


Itama Sehrish,sae da tayi sallar daren,kafin ta kwanta bacci,


Abunda ya faru daren jiya da Aunty babba ta zauna zaman jiran Hayaam....


tunda ƙarfe goma ta buga hayaam bata dawo ba,nan hankalinta yayi mugun tashi,fitowa tayi daga bedroom ɗinsu,ta shiga zarya acikin hotel ɗin,ko Allah zaisa taga gifcinta,amma shiru babu ita har receptionists taje ta tambaya ko sunga fitarta suka tabbatar mata da basu ganta ba,ƙarshe da ta gaji da biɗiɗin nemanta,komawa tayi ɗakin nasu zuciyarta a ƙuntace ta kwanta,duk da halin da ta shiga na rashin hayaam,hakan bai hanata yin bacci ba,harda minshari,

  Haroon kuwa tun da ya kammala yi mata wannan aika aikar,ya tattara yabar Hotel ɗin ya gudu gaba ɗaya,don kuwa daƙyar in hayaam zata ƙara moruwa,Ya naƙasata sosai,a saman gadon ya barta a yashe,


Wuraren Sallar asuba,Wayar Aunty babba dake ajiye gefenta ta soma ringing,can cikin bacci ta dinga jin ringing ɗin wayar,dama ta kwana da tunanin hayaam zata iya kiran ta in ta buɗe wayarta,hakan yasa ta farka da sauri takai hannu ta ɗauki wayar,duba screen ɗin wayar tayi da 6oyayyiyar lamba aka kirata,cike da mamaki tace"To fa,waye ya kirani a irin wannan lokacin da 6oyayyiyar number?kodai hayaam ce ta kira,bari na ɗaga na ji,

   Picking call ɗin tayi ta kara wayar a kunnanta,

  Tun kafin tayi sallama taji ance"Madam,barka da warhaka"

  gabanta ne ya ɗan faɗi rass,amma ta dake tace"yawwa,dan Allah wanene ke magana,"

   "Babu bukatar ki sani,dama na kira ne don in yi aikin lada,Nasan kina ta neman hayaam ido a rufe,to hayaam dae a halin yanzu addu'arki take buƙata,idan kina son sanin inda take,yanzu zan turo maki da message na address ɗin inda take,sae ki hanzarta zuwa don ki kai mata agaji,Allah ya bata lafiya,idan ta samu ciki dan Allah a ajiyemun abuna,inaso" yana faɗin haka,yayi rejecting kiran,"

  Waro ido waje Aunty babba tayi,a hargitse ta saukko daga saman gadon hannunta riƙe da wayar,jikinta har kerma yakeyi,zarya ta shiga yi acikin ɗakin tana jiran shigowar saƙon,

  A fili tace"Allah yasa dae hayaam ba wani taje taba ma kanta ba yayi amfani da ita,Sae da naja mata kunne akan ta daina kula maza,amma da ya ke karya ce gaya nan tana son ja mun bala'e,ina zaman zaman lafiyana,"


Tana cikin wannan zullumin,taji ƙarar shigowar message da sauri ta duba top of the screen ɗin wayar,

  "Vip,Room 34,"shine abunda taga an rubuta acikin message ɗin,kuma babu numbar wanda ya tura,anyi hidden number,

   Sai da tayi zurfin tunani sannan ta gane cewa numbar ɗakin hotel ne aka turo mata,hakan na nufin cewa hayaam tana acikin hotel ɗin,

   Jiki na rawa ta ƙarasa wurin trolley ɗin kayansu dake ajiye,gefen wardrobe,buɗe wa tayi ta dauko mayafi ta lullu6a asaman kanta,  

  Sannan ta tura kopar ɗakin ta fito,tafiya takeyi cike da zullumin abunda zai biyo baya,sae bin ɗakunan dake a wurin takeyi tana bin numbobin jikinsu,cikin sa'a batare da tasha wahala ba tazo kan numbar ɗakin da aka turo mata,sae da ta duba dakyau taga Room 34 ne,Hada key aka ajiye mata ajikin ƙopar,wannan ya tabbatar mata da cewa da gangan aka sanya key ɗin,saboda in tazo ta buɗe ta shiga,

   Gabanta sae faɗuwa yakeyi,a hankali ta sanya hannunta ta ɗan murza key ɗin ɗakin ya buɗe,cike da fargaba ta tura ƙopar ɗakin a wani slow kopar ta soma buɗewa ƙiiiiiii,tun kafin ma ta sanya kafarta acikin ɗakin ta hango pant yashe a saman tiles,Rass taji gabanta ya faɗi,wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,dakyar ta shiga cikin ɗakin,karaf Idanuwanta suka hango mata Bra din hayaam dake sagale ajikin mirror,tun daga nan tasha jinin jikinta,wurga idonta tayi gefen hagunta,Handbag ɗin hayaam ta hango yashe a kasa,da alama wurgi akayi da jakar kayan cikinta suka watse akasa,hada wayarta ma duk screen ɗin ya fashe,

..arazane Aunty babba takai idonta saman gadon,mutunne a kwance an lullu6e shi da bargo,

  A tsananin tsorace ta ƙarasa gaban gadon,sanya hannunta tayi tare da zame bargon a hankali,tana buɗe bargon da sauri ta mayar ta rufe,saboda tashin hankalin da ta gani,hannu ta aza akai ta fasa ihu tana faɗin"Nashiga uku!Wayyo Allah na,Hayaam wani marar imanin ne yayi maki wannan aika aikar!hayaam waye ya yashe ki haka!La'ila ha'illallahu muhammadur rasulillahi!Amma kowaye wannan anyi haihuwar asara,Uwarshi ta haifo mana Bala'e" ta inda take shiga bata nan take fita ba,Muryarta har shaƙewa takeyi saboda tsabar baƙin ciki,tamkar ta haɗiyi zuciya ta mutu,

..a karshe ta fashe da matsanancin kuka,tare da hayewa saman gadon,tana cigaba da sambatu,da alama ta fara zaucewa,

   "mun shiga uku mu yau,Wllh dana san haka zata faru da bamu zauna a hotel ɗin nan ba,ƙaddara ce kawai ta riga fata,Hayaam kowaye wannan ya gama damu,ɗan jarin da muke taƙama dashi ya kwashe komai babu,ya yashe ki,ya karya mana tattalin arziƙin da yayi mana saura,Ya takaita mu don ubanshi,wlh koma wani jarababben ne,Sae Allah ya toni asirinshi,Ni na ta6a ganin jaraba irin wannan,bai bar komai ba,yayi mata wanwar ɗan jakar uban,haihuwar asara haihuwar titi,haihuwar kwararo...."kasa ƙarasa maganar tayi,wani irin ƙululun baƙin cikine ya tokare mata maƙoshinta,nan tashiga yin kakarin amai,ta saukko daga saman gadon agalabaice ta nufi toilet ɗin cikin ɗakin ta shiga,Sosai tayi amai tamkar ƴan hanjin cikinta zasu fito waje,ta jima acikin toilet ɗin kafin ta fito,tana tafiya ƙafafunta na harɗewa,

  Fitowa tayi daga ɗakin ta koma ɗakinsu,Trolley ɗin kayansu ta buɗe,Jallabiya ta ɗaukowa hayaam tare da Mayafi,Sannan ta koma can ɗakin,taci wahala haka ta kinkimi hayaam ta shiga da ita toilet,wani wurin ma ajikinta,baya ta6uwa sae dai anje asibiti duk ya jagule babu kyan gani,hatta la66anta duk sun faffashe hada busasshen jini,nipple ɗinta na right breast kuwa,sai jini yake yi,ƙiris ya rage ya 6alle,haƙika haroon ya cutar da ita,ya zalunce ta,Da mugunta yayi mata hakan,Dama babu Imani aranshi,duk ya faffasa mata skin ɗinta da Nails ɗinshi,saboda baya yanke akaifa,doguwar ƙumba ne dashi,

  Aunty babba tasha kuka,Tuntana kukan fili har ta koma yin kukan zuciya,wanda yafi ciwo,Sai da ta nemi taimako a hotel ɗin,sannan ta samu aka ɗauki hayaam,Suka kaita wani private hospital saidai sam bata sanar dasu haƙiƙanin abunda ya sameta ba don tasan karshe reporting za'ace ayi wurin yansanda ita kuma bata son asirinsu ya tonu har abun ya kai kunnan su Ishaq,tafi son in hayaam din ta farfado ta fadi wanda yayi mata hakan don ta tabbatar ba da karfi aka jata dakin ba don wanda ya kira ta ya sanar da ita halin da take ciki har sunan hayaam din ya ambata hakan kuma na nufin ya santa ne,


 Tunda aka shiga da ita ciki,Likitoci suka taru akanta,Aunty babba na zaune zugudum saman waiting seat,tashin farko sae da suka fara kar6ar kuɗin gadon kusan Naira dubu 50,Sannan za'ayi mata aiki ciki da waje a ƙalla za'a cajesu kuɗi kusan Dubu ɗari biyar,Bayan haka akwai alluran da za'ayi mata ajikinta kuɗinsu ya kai kimanin dubu 20,

  Abun yayi matuƙar girgizata,ita babbar damuwarta,ba halin da hayaam ke ciki ba,Kuɗinsu da suke tattalawa zasu je wurin boka,Har an yashe kusan rabinsu,wasu mutanen dai ba imani aransu,ɗaya daga cikin halin ɗan adam kenan,Duk yadda take da hayaam same parents,Amma harta fara tunanin guduwa ta barta a asibitin saboda gudun kar su talauta ta,Kuma ta yanke shawarar zata yi ma Abra magana tazo su tafi wurin bokan tare da ita,Tunda ita hayaam ta gama lalacewa,babu wani amfanin da zata yi mata,ƙarshe ma taja masu asara,yini tayi a asibitin tana zirga zirga,Yayin da zuciyarta ke saƙa mata,ta gudu tabar asibitin,tun da ta samu ta biya mata kuɗin aikin Can su ƙarata,


Har wuraren ƙarfe Goma na dare,lokacin an kammala yiwa hayaam aikin,Amma bata farfaɗo ba,tsayawa Aunty babba tayi abakin ƙopar shiga ɗakin tana kallon hayaam dake kwance,hancinta na sanye da Oxygen,

  Komawa tayi saman waiting seat din,inda tabar handbag ɗinta,ɗaukar jakar tayi ta buɗe ta,biro ta curo tare da memo,aza takardar tayi saman kujerar sannan ta soma rubutu Kamar haka

  _Hayaam sae dai kiyi haƙuri,Wlh bazan iya cigaba da zama acikin asibitin nan ba,duk laifinki ne,Sai da na gargaɗeki akan karki kuskura ki ƙara kula wani ɗa namiji,amma da yake ke karyace ba'a raba ki da maza,Gashi nan kin jawowa kanki wanda yafi ƙarfinki,Ya gama dake yayi maki kankat,babu abunda yayi saura ajikinki balle har insa ran zakiyi mun amfani,Shiyasa na yanke shawarar zanyi ma Abra magana,zamuje wurin bokan tare da ita,Don bazan bari burina yaƙi cika ba har su Amani suyi nasara,In dana gode ma Allah bake kaɗai bace ƙanwar da nake da ita ba,Wlh dana ji kunya_

  Tana kammala rubuta short note ɗin,Ta ɗauki handbag ɗinta,Sannan ta shiga cikin ɗakin da aka kwantar da hayaam ɗin,A gefenta ta ajiye wasiƙar,Sannan ta curo bandir ɗin kuɗi dubu hamsin ta ajiye mata a gefenta,a hankali ta furta Allah ya baki lafiya hayaam,Idan kuma kin riga mu gidan Gaskiya,Allah ya jiƙanki da rahama,

  Tana kai ƙarshen maganar,da sauri ta juya tabar ɗakin,batare da 6ata lokaci ba,ta gudu tabar asibitin,

  Rayuwa kenan,


*Boss Bature*


   ❤🤍❤


Tunda sanyin safiya ringing ɗin wayarta ya farkar da ita daga bacci,cikin bacci takai hannu tana laluban wayar harta samu ta cafkota,janyota tayi cikin bargon tare da buɗe idanunta masu ɗauke da bacci,Sunan Mommy Azeema ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,da sauri ta miƙe daga zaune,har time ɗin doguwar rigar jiyace a jikinta pink ɗin nan,picking call ɗin tayi ta kara wayar a kunnanta,

  "Assalamu alaikum,"

On the other hand Aunty Azeema tace"Babyn Rafayet,kin tashi lafiya,"

  Murmushi sehrish ta ɗan yi tare da cewa"lafiya qalou Alhamdulillah,"

"Yawwa my Daughter,dama na kira ne about abunda ya faru a tsakaninki da Rafayet,"

  Natsuwa Sehrish tayi tana sauraronta 

  Ci gaba da magana tayi,"Jiya na hana ki bashi haƙuri,Saboda nasan cewa yana cikin fushi,kuma haɗari ne ki tunkareshi a wannan lokacin,kafin nan abunda nakeso in sanar dake,duk yadda kike tunanin rafayet ba haka yake ba,mutunne shi mai ƙyanƙyami sosai,kuma yana da zuciya shiyasa a lokacin ranshi ya 6aci ne sosai,har yayi yunƙurin bugunki,kinsan in ran mutun ya 6aci zai iya aikata komai ba'a hayyacinshi ba,sae yadawo cikin hankalinshi kuma yazo yana danasani,Akwai ire irensu,Ni nasan ba ason ranshi yayi maki hakan ba,don ba halinshi bane wulaƙanta mace,Zuciya ce ta fisge shi har yayi wurgi dake,ya kuma yi yunƙurin marinki......"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar na wani lokaci kafin ta ɗaura da cewa"Kin riga da kin faɗi abunda ke cikin ranki ba'a hayyacinki ba,ina mai tabbatar maki da cewar yanzu zai yi ƙoƙarin gyara mu'amularshi dake ne,Saboda ki daina yi mashi kallon mugu,Amma fa idan har kina son hakan ta faru dole sai kinje kin bashi haƙuri,sai daga baya na zauna nayi wani tunani,muddin baki bashi haƙuri ba,to akwai gagarumar matsala,tunda bai fara sonki ba,zai iya aikata komai daga ciki hada divorce tun kafin ma lokacin ya cika kin ga mu kuma ba haka muke so ba,Kuma idan kin bashi haƙuri ba hakan yana nufin cewa kin zubda ajinki bane,Darajarki zata ƙara daukaka a wurinshi,zai san cewa tabbas kina da hankali sosai tunda har kinsan kiyi laifi kuma ki nemi yafiya,kawai abunda nake so dake koda kinje bashi haƙuri karki nuna cewa ba'a hayyacinki kikayi maganar ba,"

  Zuru sehrish tayi tana sauraronta,hankalinta yayi mugun tashi,Shin ta yaya zata tunkari Sgr da sunan zata bashi haƙuri?

  "Aunty azeema,still akwai matsala,Babban yaya ya hanani zuwa part ɗinshi fa,saboda period ɗin da nake yi,Nasan idan ya ganni zai tuna da jinin da ya gani ajikin wandona ƙarshema yayi mun korar kare in bai bugeni ba,"muryarta tamkar zata yi kuka haka tayi maganar,

  "Kada ki damu da wannan,In sha Allah babu abunda zai faru dake,sannan idan zaki je part ɗin nashi,ki gyara jikin naki sosai,Kuma ki shafe shi da turare"

  Gyaɗa kai kawai tayi tare da cewa"Shikenan zanje in sha Allah,duk yadda mukayi dashi zan sanar maki,"

   "Okey,saina ji ki,"

Tayi rejecting kiran,Ajiye wayar sehrish tayi saman gadon,Saukkowa tayi tare da nufar toilet ta shiga,Cikin mintina tayi wanka ta fito jikinta sanye da undy taja shi saman ƙirjinta,hannunta ruƙe da Short towel,Goge ruwan jikinta tayi dashi,bayan ta kammala,ta zauna gaban mirror tana shafa body cream ɗinta,Bayan ta gama ta shafa powder afuskarta,tare da murza man baki,Comb ta ɗauka tana sharce gashin kanta,

  Turo kopar akayi,ta cikin mirror ta kalli wurin ƙopar don taga wanene,Jahad ce ta shigo hannunta ɗauke da plate meat balls ne aciki tare da Cup na coffee,

  "Allah yasa nawa ne,"acewar Sehrish,

  Murmushi jahad ta saki tare da cewa"Naki ne mana,nayi tunanin ma baki tashi daga bacci ba," tayi maganar tare da nufar wurin mirror ɗin ta tsaya,hannu tasa ta ɗauki meat ball din guda daya tace"Buɗe bakinki in saka maki,kiji idan yayi daɗi,"

  Buɗe baki Sehrish tayi,Jahad ta tura mata shi cikin bakinta,taunarshi ta shiga yi tana jinjina kai alamar daɗinshi yana kai mata karo,

  "Baby junaid nayi mawa,Ya kika ji ɗanɗanon"?

.Sehrish tace"Bangane ba,wani junaid ɗin bayan basu nan?ko kin manta ne"?

   Jahad tace"Ae munyi waya dashi,Ya sanar dani cewa,Yau ko gobe zasu dawo,Amma basu duka ba,Shi dai yace bazai iya jure rashina ba,In ma basu dawo dashi ba,ko a ƙafa ne sai ya tako,"

..fashewa da dariya Sehrish tayi,itama jahad ɗin dariyar ce akan fuskarta,

  "Gaskiya junaid na dabanne,yaci sunanshi Romeo,ga kuma juliet ɗinshi tsaye agabana,"

  Tayi maganar tana nuna Jahad dake atsaye,

 Murmushi jahad ta saki tare da cewa"Oh Ni sehrish,Wlh bansan ya zamu qare da junaid ba,idan munyi aure,Kina ganinshi ɗan ustazi ko,ba ƙaramin jarababbe bane,"

  Sehrish tace"gaskiya sai kin jure don kula da junaid ba abu bane mai sauki,a kwanakin baya can da jimawa,lokacin daya gane cewa ni mace ce,Mun ta6a yi dashi zamu haɗu a garden,Ni kuma na manta,kinsan Allah tun wurin magrib junaid ya zauna a garden ɗin nan yana jiran zuwana,maimakon da ya ji ni shiru ya dawo cikin gida,sae yaƙi shigowa saboda munyi alkawarin haɗuwa dashi,Ni kuma na manta,ɗan tahalikin nan,tsakar dare akayi ta nemanshi aka rasa,ashe yana can garden yana jirana,ga asthma ɗinshi ta tashi,da ace ban tuna ba naje wurin nan ba,da Allah kaɗae yasan abunda zai faru dashi....."

  Jin wannan maganar ba ƙaramin tayarwa jahad da hankali tayi ba,

  "Kice Majnun zan aura ba Romeo ba,junaid bashi da hankali wlh,"acewar jahad,

  Sehrish tace"yana da hankali mana,Junaid yana da mutunci sosai,ya kyautatamun sosai,bazan ta6a mantawa da halaccin da yayi mun ba,ina taya ki murna jahad,idan har kika auri junaid,babu ke babu yin aikin wahala,zan so naga rayuwar aurenku,tamkar comedy haka zata kasance,Zaki samu nishaɗi sosai,"

  Ba ƙaramin farin ciki jahad taji ba,sae faman sakin murmushi takeyi,

  Hannu sehrish tasa tare da ɗaukar cup ta kaishi bakinta tana kur6ar coffee,sae da ta shanye sannan taci gaba da ɗaukar Meatballs ɗin tana jefawa a bakinta,Duk jahad na atsaye ta ruƙe mata plate ɗin,

   "ki zauna mana,ƙafafunki basu ciwo ne"?

   "A'a,So nake in koma kitchen,Ina taya Aunty azmee aikin gida ne,"

  "Hosana fa?tunda mukayi sallar Asuba,dana koma bacci ban ganta ba lokacin dana farka,"tayi maganar a yayin da takai hannu gaban mirror,ta yago tissue tana goge bakinta,

  Jahad tace"Tana a dining,kinsan ta bata gajiya da ci,Ae ina tausayin Ya Omar,Don hosana saita ƙarar mashi da duk wani tattalin arziƙin da yake dashi,Gashi don ubanta ko girki bata wani iya ba,ci kawai ta sani,"

  Dariya Sehrish tayi sosai kafin tace"Sauƙinta ma,Ya Omar mutunne mai haƙuri,Kuma yana da kyakkyawar zuciya,Shi kaɗai ne zai iya control ɗinta,Amma fa zaiyi fama wlh,"tayi maganar tare da miƙewa ta koma gaban wardrobe,

  Buɗewa tayi tana neman kayan da zata sanya ajikinta,

  Suna cikin magana,Hosana ta faɗo ɗakin tana kuka,bakinta cunkushe da Donuts,Ga wani a hannunta ta ruƙo,ɗayan hannun na ruƙe da wayarta,

  Juyowa sukayi atare suna kallonta,hankali atashe suka tunkareta har suna haɗa baki wurin cewa"Hosana,Me ya faru!me kikeyi ma kuka haka?Wani ne ya rasu"?

  Ɗaga masu kai tayi alamar eh,

Gabansu ya faɗi rass,A sukwane suka kalli juna,kafin suka mayar da idanuwansu kanta,

  "Hosana faɗamun!waye ya rasu!"jahad tayi maganar jikinta na kerma,

  Sehrish tace"ki buɗe baki kiyi mana magana,ko wani ne bashi da lafiya,"?

  Sae lokacin ta taune donut ɗin bakinta tana matsar kwalla tace"Yayi Hatsarin Mota ya mutu"!

  Kallon juna sukayi atare kafin su kuma mayar da idanuwansu kanta,arazane suka haɗa baki wurin cewa"Wa?

..cusa donut ɗin hannunta tayi acikin bakinta,Cikin shessheƙar kuka tace"wani Mai yin comedy,Yanzu nake gani acikin wayata,yayi hatsarin mota ya rasu"

  Sauke ajiyar zuciya su kayi atare,Duk atunaninsu wani ne ya rasu Cikin waɗanda suka tafi damaturu,

  "Hosana ba kuka zakiyi mashi ba,Addu'a yakamata kiyi mashi don ita yake bukata,Allah ya jiƙanshi,Ya gafarta mashi zunubban shi,Allah yasa aljanna ce makomarshi,Amma idan kikayi mashi kuka to ke ba cikakkiyar masoyiyarshi bace,"

  "Nadaina kukan,Idan nayi sallah zanyi mashi addu'a,"

   ta ƙarasa maganar,tana cigaba da taunar donut ɗin dake a bakinta,sannan ta juya ta fuce daga ɗakin,

  Jiki asanyaye Jahad ta koma gefen gadonsu ta zauna,Sehrish kuma ta koma wurin wadrobe ɗin,Tana ɗaukar kayan da zata sanya,

  "Hosana ta tayar mun da hankalina sosai,Jikina duk yayi sanyi,"

  "Kin gane wa take nufi ne"?sehrish tayi mata tambayar,ayayin da take zura skirt ajikinta,

  "Kamal Aboki take nufi mana,Wanda yayi wannan comedy ɗin nan,na matar soja,yana rera waƙar india shi da wani,akwae ma wani wanda yake cewa gayuna kun ga Alert,su kuma sauran sai suce a'a,kin tuna shi"?

  Shiru sehrish tayi tana ƙoƙarin tuna comedy ɗinsa,can tace"Nagane shi,ya iya comedy sosai,Na ta6a ganin video ɗinshi a wayar Amrish,dayake ita mayyar kallon Comedy ce,Ni kinsan bancika amfani da waya ba,"

   Jahad tace"naji mutuwarshi sosai,ya tsaya mun araina,rayuwar kenan kana taka Allah yana nashi,shiyasa wasu mutanen in suna aikata abunda suka ga dama har mamaki suke bani,sun manta cewa duniyar nan ba wurin zama bane,Jin daɗinta ƙalilan ne,da zarar ka mutu za'a kai ka grave ɗinka,daga kai sai Halinka,mai kyau ne ko mara kyau,idan na tuna cewa zan mutu in bar duniyar nan,ko inaso ko banso sai inji komai ya fita raina,ina rage duk wani dogon burin da nake dashi akan duniyar nan,Kuma ina ƙara kusanta kaina wurin Allah,...'

   Sehrish tace"Wata rana muma babu mu,masu karanta labarin ma babu su,Mai bada labarin ma babu ita,Allah yasa dae mu cika da kyau da imani"_

  Jahad ta amsa mata da"Ameen" sannan ta miƙe tare da nufar ƙopar fita daga ɗakin tana cewa"Ni zan wuce wurin Aunty azmee,kada mu barta da aiki ita kaɗae,"

  "Nima idan na kammala shiryawar zanzo na tayaku aikin"acewar sehrish,"

   Shaf shaf ta kammala shirya kanta,Cikin Skirt red colour,Asymmetrical Yana da baza ajikinshi,Gaban skirt ɗin bai kai bayanshi tsayi ba,yayi matuƙar yi mata kyau,Halter shirt ta sanya ajikinta white colour tayi tighting ɗinta,Red & white abun ba'a magana,Takalma ta zura a ƙafarta t-strap yana da ɗan tsini amma ba sosai ba,Launin skirt ɗinta ne,komawa tayi gaban mirror ɗin,ta ɗauki kwalbar turarenta tabi jikinta ta feshe ko'ina,saƙo da lungu,nan take ƙamshin ya gauraye ko'ina,bata sanya mayafi akanta ba,sai gashin kanta da yayi mata rumfa abayanta,

  Fitowa tayi daga ɗakin,ta shiga cikin palour bata samu kowa ba,Suna can cikin gidan suna gyare gyare,

  Tunda ta hau saman staircases(matattakalar bene)gabanta ya shiga faɗuwa,lokacin da ta ƙarasa part ɗin nashi bata shiga daga ciki ba,

  Gabanta sae faɗuwa yake yi rass rass!leƙawa tayi ciki babu kowa Sae dae kayan abincin nan daya ci,'

  Runtse idanuwanta tayi tare da ɗaga hannayenta izuwa saitin fuskarta,

  "Ya Allah Kana ganin baiwarka,acikin wani hali na firgici da tsoro,Allah ka tsare ni,Wllh idan naga ya nufo ni zai bugeni,Sae in watsa da gudu,Amma takalmana masu tsini ne,kada suja inyi tuntu6e in faɗi ƙasa,"

  Dakatawa tayi da yin zancen zucin nata,Sannan ta ɗan buɗe idanuwanta tana ƙara leƙa cikin palourn nashi,

   Jaraba yadda zata bashi haƙuri ta shiga yi,

   _babban yaya,Am sorry bazan ƙara ba,nasan nayi maka laifi,amma banyi hakan da niyyar na 6ata maka rai ba,Ba yin kaina bane,kuma ba hali na bane,Allah shine shaidata,ni bana yi ma na gaba dani rashin kunya,tsautsayine kawai da ƙaddara,A iya nan zan tsaya na baka haƙuri,saboda ka hanani shiga part ɗinka,har saina kammala period ɗina,Shiyasa bazan samu damar shigowa daga ciki in baka haƙuri ba_

  Tana cikin tsara yadda zata sanar dashi,Kwatsam taji ƙamshin turarensa acikin hancinta,gabanta ne ya faɗi Rasss!waro ido tayi waje,ta zazzaresu,hankalinta yayi mugun tashi,

  Kasa juyawa tayi ta kalli bayanta,saboda tana da tabbacin cewar,SGR YANA TSAYE ABAYANTA!Ashe baya cikin part ɗin nasa,Tashin hankalin da ba'a sa mashi date! Ko ya sehrish zata ƙare!?


Sanƙamewa tayi a tsaye,ko motsi ta gaza yi,jira kawai take taji yayi wurgi da ita,

   "Excuse me,"muryarshi ce ta katseta,jiki na rawa taja gefe guda,yayin da  idanuwanta ke kallon ƙasa taƙi yarda ta ɗago balle har su haɗa ido dashi,jikinshi na sanye da kaftan  shirt har guiwa tare da trouser ɗinta brown  colour,ya saki sumar kanshi ta baya,wani irin daddaɗan ƙamshine ke fitowa daga jikinshi,Slowly ya wuce cikin palourn batare da ya kalleta ba,abun ya yi matuƙar bata mamaki,tayi tsammanin tashin farko zai daka mata tsawa ne ya shako wuyanta,Sae gashi ko kallon inda take bai yi ba,Wuri ya samu saman Sofa ya zauna,tare da jingina bayanshi a jikinta,

   Tunani Sehrish ta shiga yi Ko ya ji abunda tace ko baiji ba Oho,Allah Wa'alamu,ranta ne ya bata cewar ta juya ta tafi kawai,tunda ba damar ta shiga ciki,ya riga da ya hanata,tana ƙoƙarin barin wurin,kwatsam taji yace"Zo nan,"

  Rasss taji gabanta ya faɗi,nan take taji fitsari ya matseta,daƙyar ta daure ta cije,ta dake sannan ta juya ta shiga cikin palourn,nesa dashi ta tsaya,saboda gudun kar ya shaƙota,

    Idanuwanshi na akan agogon hannunshi daya dafa sofa hand dashi,

  "Laifin me na aikata maki,da har na cancanci a kira ni,da mara IMANI mara TAUSAYI"?he said calmly,

   Wuƙi wuƙi sehrish tayi da ido,sae faman murza yatsun hannunta take yi,batasan amsar da zata bashi ba,

   "Also,kinyi comparing ɗina da wannan fasiƙin mutumin,Why"?

  Shiru tayi tana ta faman mazurai,

Miƙewa yayi daga zaunen da yake gadan gadan ya nufi wurinta,ja da baya Sehrish ta shiga yi tamkar ta watsa da gudu tabar falon sai dai ba dama,har saida suka ƙurewa bangon falon sannan ta tsaya,tare da ƙankame jikinta,tsoronta kada yace zai bugeta,

   Rumfa yayi mata da faffaɗan ƙirjinshi,duk tabi tasha jinin jikinta,Acikin zuciyarta sae faman ambaton La'ila ha'illah anta subhanaka inni kuntu minazzalimin takeyi,gaba ɗaya ƙamshin turaren jikinshi ya hanata sukuni,ga fargabar da ta shiga,

    "look at my face!nayi maki kama da mara tausayi,Mara imani"? Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,dakyar ta iya buɗe baki tace"A'a,“

   "But Why u said so"?

Girgiza kai ta shiga yi,batare da ta furta komai ba,

    "Shekarunki nawa"?

Muryarta na kerma tace"Na shiga sha takwas,"

   Gwauron numfashi ya saki tare da zura hannunshi na dama cikin sumar kanshi a hankali ya furta"Ya Allah"!abun yayi mashi ciwo,ƙaramar yarinya na so ta caja mashi kwalwa,

    Zame hannun yayi daga cikin sumar,tare da dafe bangon da tafin hannun,

   "In my life,Wata ƴa mace bata ta6a gigin gaya mun magana ido cikin ido ba,batare jin shakkata ba,Sae ke,"yayi maganar yana nuna ta from head to toe,

    Hankalin Sehrish yayi mugun tashi,Hukuncin da zai yanke mata kawai take jira,"

   "A ina kika samu ƙwarin guiwar yin hakan"?yayi tambayar yana kallon fuskarta,

  Shiru tayi,tana faman haɗiyar yawu,

   Jinjina kanshi yayi tare da ja da baya ya juya,Saman sofa ya koma ya zauna,

   "Come close"ya furta hakan yana nuna mata gefen table ɗin dake agabanshi,

  A hankali ta tako tazo gabanshi ta tsaya,sae lokacin ta ɗan saci kallon fuskarshi,karaf idanuwansu suka shiga cikin na juna,irin kallon da taga yanayi mata ne yasa tayi saurin duƙar da kanta ƙasa,ta ƙurawa takalman ƙafarta ido,

   "Don't judge me,till u know me well,"

  Jinjina kanta tayi,batare da ta ɗago ba,

    "Idan har akwai abunda nake maki,Wanda yasa kike yi mun kallon wicked,mara tausayi mara Imani,lemme know,"

   Da sauri tace"babu komai,"


"I don't trust u,If u can't say it,ki rubuta mun a Text message"


  Abun yayi matuƙar ɗaure mata kai,yadda tayi tsammani ba haka ta gani ba,kokonto ta shiga yi anya Sgr ɗin da ta sani ne kuwa?kodae mafarki take yi ne,ta kasa yarda cewa da gaske ne shi yake yi mata,

    A hankali ta furta mashi toh,

Juyawa tayi ta kama hanyar fita daga falon,tafiya take yi tana wasi wasi acikin zuciyarta,

   "Idan ina takura maki ne,Remain just 2 months na bar ƙasar,Zan sallame ki ne,kiyi rayuwarki kamar yadda kika saba,".  

   dakatawa tayi da yin tafiyar ta ɗan juya tare da kallonshi,

   ba ita yake kallo ba,idanuwanshi na a lumshe,ci gaba da magana yayi"Ki dawo ki ci gaba,da yin aikin ki a part ɗina,"

  Tayi matuƙar yin mamakin abunda yace mata,hatta kalamansa ya tausasasu bakamar yadda yake yi mata magana ba ada,

    "Am waiting for my breakfast,then bedroom ɗina yana buƙatar gyara,"

  "Amma ka hanani yin aiki a part ɗinka ayanzu,"

   "Nayi cancelling,"

Nauyayyiyar ajiyar zuciya ta sauke,ta wani 6angaren taji daɗi sosai,duk da bata ji daɗin kalaman da ta faɗa mashi ba a jiyan nan,da alama sun ta6a mashi zuciyarshi sosai,

   Komawa cikin falon tayi,gaban table ɗin sa taje,ta kwashe ledojin nan da aka kawo mashi na restaurant,

 Sannan ta juya ta nufi ƙopar fita daga falon,tana tafiya tana waiwayenshi har wani ƙara leƙen fuskarshi takeyi,Saboda abun ya ɗaure mata kai sosai,

    

   

    

  

    

  

   

 

   

  

   

  

   

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




Batare da 6ata lokaci ba,ta shirya mashi breakfast ɗinshi,takai mashi a falonsa,yadda tabarshi haka ta same shi a zaune,Sae da tayi serving ɗinshi ya ci ya ƙoshi,Sannan ta wuce bedroom ɗinshi,Ta shiga gyara mashi,lokacin da ta kammala gyara Bedroom ɗinsa da Toilet,ta fito palourn, Komawa cikin bedroom ɗin yayi after some minutes ya fito jikinshi sanye da trouser na army tare da shirt,tana cikin gyaran yazo ya wuce ta,Gyara palourn tayi ko'ina yayi fess sae ƙamshi dake ta tashi,turo mashi ƙopar falon ta ɗan yi,Sannan ta saukko down da sauri ta wuce bedroom ɗinsu jiki na rawa,Don a ƙagare take da ta sanar Wa Aunty Azeema,


  Tura ƙopar ɗakin tayi tare da sa ƙafa ta shiga ciki,jahad ce kwance saman gadon Kunnanta manne da waya,suna waya da junaid,juyowa ta ɗan yi tare da kallon ƙopar don taga wanene ya shigo,Ganin Sehrish yasa ta mayar da kanta inda take fuskanta taci gaba da yin wayar,

   Wayarta dake ajiye saman drawer ta dauko,contact ta shiga ta lalubo layin hajiya Azeema ta danna mata kira,Wayar na shiga ta ɗaga kiran ,

  "Daughter,ya ake ciki ne?tun ɗazu  nake tasa ran ganin kiran ki,"Aunty Azeema tace,

  Murmushi sehrish ta ɗan saki tare da cewa"Yau babban yaya yayi matuƙar bani mamaki,Abun da ban ta6a tsammani ba,'_

   "har na ƙosa naji meya faru,ae tunda naji muryarki,nasan cewa an dace,halan bai yi maki komai ba"?

  "Baiyi mun komai ba,ƙarshe ma cewa yayi in rubuta mashi duk wani abu da yake yi mun wanda bana so in tura mashi ta message da ya tambaye ni abunda yake man nace ba komae,Sannan kuma yace in ci gaba da aiki a part ɗinsa,"ta ɗan dakata da yin maganar,tana jiran jin me Auntyn zata ce,Sautin dariyarta tajiyo ta cikin wayar,

   "Dama sae da raina ya bani cewar Rafayet,bazai yi maki komai ba,Gaskiya naji daɗin hakan sosai,wannan ma wani matakin nasarar ne,Yanzu me kika yanke shawara akai"?

   Sehrish tace"game da me kenan"?

"Ina nufin me zaki rubuta mashi"

   "Nikaina,bansan me zan rubuta mashi ba,amma ki bani shawara,"ta ƙarasa maganar tare da samun wuri,saman drawer ɗin ta zauna,tana ci gaba da sauraronta,


"abunda nakeso dake,kada ki ji tsoron komai,ki natsu ki kwantar da hankalinki,ki rubuta mashi duk wani abu da kika sani wanda baki so yana yi maki,wannan dama ce kika samu,"_

   Ajiyar zuciya ta sauke tare da gyaɗa kai tace"shikenan,Zan rubuta mashi yanzu,"

  "Yawwa my daughter,take care of ur self for me,Sai kinji daga gare ni,"

  Daga nan sukayi sallama tayi rejecting kiran,

   Juyawa tayi gefen hagunta tare da kallon jahad tace"Juliet,inason magana dake,idan kin kammala wayar,"

  Juyowa jahad tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Ae mun kammala yin wayar ma tun ɗazu,wayarce kawai ban cire a kunne na ba,saboda ban gajiya da jin Voice ɗinshi,Expecially idan yanayi Mun shagawa6ar nan tashi,kamar in janyoshi ta cikin wayar,in manna mashi kiss,"

  Fashewa Sehrish tayi da dariya,gami da girgiza kai,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Gaskiya ne,Juliet Matar Romeo,abun naku azimunne,"ta ƙarasa maganar a yayin da take komawa gefen gadon ta zauna,kafin ta kuma cewa"Am looking for ur advise,My lovely sis,"jin haka yasa jahad ta miƙe zaune daga kwancen da take,ta jingina bayanta jikin head board ɗin gadon,tana facing sehrish sannan tace"Shawarar me kike so in baki ne"?

  Calmly sehrish tace"yau naje bama babban yaya haƙuri,Kinsan meya faru"?

Hankali aɗan tashe jahad tace"Sae kin faɗa,"

  Murmushi sehrish ta ɗan saki kafin ta cigaba da cewa"bai yi mun komai ba,ko yatsa bai ɗaga mun ba,Yanzu haka ma zancen da nake maki,Yace na rubuta mashi text message na duk abunda banso yana yi mun,"_

  Wani irin ihun farin ciki jahad ta saki tare da furta"Yess!yess!"da alama abun ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,

   "Wlh naji daɗi sosai!dama nifa koda nace kada kije ki bashi haƙuri saboda tsoran karya Bugeki ne,Amma yanzu Alhamdulillah,komai ya wuce,gashi har an samu ci gaba,"

"Yanzu me kike ganin ya dace na rubuta mashi?Mommy azeema tace kada naji tsoran komai na rubuta duk abunda nake so ya daina yi mun,"

Murmushi jahad tayi,tare da cewa"ta kwana gidan sauƙi,Ae yanzun nan zamu tsara mashi text message,Amma inaga kamar mu rubuta mashi ta whatsapp ko?zaifi tsayi rubutun ba kamar na text message ba,

  Sehrish tace"Ni damuwata ma,kada musha wahalar rubutawa yaƙi karantawa,Saboda na ta6a tura mashi message,bai rubutomin reply ba,"

  Jahad tace"kinsan shi mutunne mai jama'a,mutun mai farin jini irinshi bazai rasa dubban saƙonnin Masoyanshi ba,Shawarar da zan baki shine,Idan kin rubuta mashi message ɗin saiki jaraba kiran layinshi,idan ya ɗaga saiki sanar dashi cewa kin tura mashi,"

  Jinjina kai Sehrish tayi,"kin kawo shawara mai kyau,"

  "Yanzu dame dame Yake yi maki wanda bakya so"?Jahad tayi tambayar tana kallon fuskar Sehrish dake kallonta,

  "Abu na farko,nidai bana son wannan tsawar da yake yi mun,na biyu bana son tsallan kwaɗin da yake sanya ni don ba ƙaramar wahala nake sha ba duk in nayi shi,Na uku kuma,banason yana hana ni zuwa part ɗinshi da make-up a fuskata....,"haka Sehrish ta shiga lissafa mata abubuwan da bataso,Bakomai yafi bama jahad dariya ba,fa ce Make-up da sehrish tace bata so yana hanata,cike da zolaya tace"in banda abunki,bashi kike yiwa kwalliyar ba?kuma yace bayaso,sae ki daina kawai,Kinsan ba ko wani namiji bane keson wannan ƙyaleƙyalen namu na mata,wani namijin ma baison ƙamshin turare,kowa fa da irin nashi ra'ayin,"

  Harara sehrish ta ɗan wurga mata tare da cewa"Amma lokacin baya before wedding ɗinmu,ina yin make-up in shiga part ɗinsa bai ta6a hanani ba,sae bayan da aka ɗaura auren,"

Jahad tace"saboda yanzu ne yake da cikakken iko akan ki,Shiyasa ya hana ki,'

  Ta6e baki sehrish tayi kafin ta mayar da idanuwanta kan wayar,Ta shiga whatsapp ɗinta,Contact ɗinsa ta nemo wanda tayi mashi saving da *My Boss man*,ta shiga Cikin Chat ɗinsa,sau ɗaya ta ta6a yi mashi sallama,bai duba ba,"

  A hankali ta soma rubuta mashi saƙon,

   "Sehrish,me zai hanaki ki ɗan rubuta mashi cewa,ya dinga sakar maki fuska,koda bazaiyi murmushi ba"?

  Wani bazawarin kallo sehrish ta jefa ma Jahad,a ƙule tace"idan ya tashi cin ubana,ae baki a kusa balle ki kawo min agaji,Ni na isa in sanya wannan fuskar tashi,ta dinga yi mun murmushi,?kina ganin ko su Abba in yana tare dasu baya murmushi,shifa naturally haka face ɗinshi take,a tamke,"

Dariya jahad tayi tare da kai hannu ta dafa shoulder ɗin Sehrish "Kada ki damu My own sister,Very soon fuskar yaya rafayet,zata koma kullum a washe,amma fa sai ranar da kika haifa mashi baby,"

  Fashewa tayi da dariya,jin abunda jahad tace mata,

  Can kuma tace"Anya,Babban yaya yana son ƴa'ƴa kuwa?irinsu fa kamar basu damu da haihuwa ba,yawanci ma basu son matansu su haihu,Akwai wani American film dana ta6a kallo,Bature ne mutumin har yakai shekara 80 bai ta6a haihuwa ba,Saboda yana da wani ɗan karensa,shiya ruƙa a matsayin ɗansa,yawanci kuma zaki ga basu son haihuwa da yawa,ɗaya zuwa biyu,sae kiga sun kwallafa rai akan ƴa'ƴan nan,"

  Jahad tace"Amma shi Half cast ne!(ruwa biyu)ba dole bane komai ace irin nasu ya ɗauko,Duk da yafi ƙarfi ta 6angaren Mommynsu,kuma acan ya taso duk ɗabi'unsa da halayansa,in kika lura irin nasu ne,Amma daga gani kamar zaiso ƴan babies,ke in ma baiso,to akan ki zai fara son ƴa'ƴa,"ta ƙarasa maganar tana dariya 

Murmushi sehrish tayi a yayin da idanuwanta ke akan screen ɗin wayarta,har tayi nisa cikin rubuta mashi saƙon,

  "Jahad,bansan meyasa kikeso in samu ciki ba,kullum baki da zance sai na in samu ciki,in haifa ma babban yaya baby,bayan kinsan cewa nan da wani ɗan lokaci auren zai mutu,"tayi maganar muryarta a sanyaye,

  Jahad tace"saboda na ta6a yin mafarki ne,kuma acikin mafarkin na ganki da ƙaton ciki,sai gashi kuma kin haihu,Kinsan me?tayi tambayar batare da tajira amsar sehrish ɗin ba taci gaba da cewa"babyn da kika haifa Triplets ne kuma dukkansu maza ne,Ƙwayar idonsu blue ce kalar ta babban yayanmu,gashin kansu ma kwantacce ne irin nashi,hasken fatarsu da komi irin nashi ne.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda jin saukar pillow da tayi asaman fuskarta,wanda Sehrish ta jefa mata shi,

  "Maƙaryaciya kawai,daga jin wannan ƙirƙirarran labari ne,babu wani mafarkin da kika yi,"_

  Dariya sosai sukayi,ba ƙaramin nishaɗi suka samu ba 

Bayan ta kammala rubuta mashi saƙon,Miƙa ma jahad wayar tayi don ta duba ta gani in akwai abunda ya dace su ƙara,Kar6ar wayar jahad tayi tana karanta message ɗin har yazo karshe,Sannan tace"komai yayi yadda akeso,tura mashi sakon sai ki kirashi,"

  Tura saƙon sehrish tayi bayan ta kunna WI-FI ɗinta,nan take saƙon ya isar mashi,phone call ta shiga tare da danna mashi kira,

   Kusan sau biyar tana kira ba'ayi picking ba,

Jahad tace"mu haƙura zuwa anjima yanzu haka suna aikine,"


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 6 na marece,wata danƙareriyar mota tayi parking a cikin wani katafaren hotel,a parking space motar ta tsaya,jim kaɗan wata matashiyar budurwa ta fito daga cikin motar,jikinta na sanye da riga bubu ta material,ƙafarta kuwa na sanye cikin high hills,ta coge ɗaurin kallabin nan na rashin ɗa'a,Sae faman taunar cingam takeyi abakinta,

   Hannunta na ruƙe da ƴar purse ɗinta,ta sagala mayafin asaman kafadarta,

....fitowa wani matashi yayi daga gaban motar,daga ganinsa zakasan cewa ba ƙaramin shege bane,kuma tantirin ɗan iska,

  Zagayawa yayi tare da buɗe boot ɗin motar ya ɗauko mata trolley ɗin kayanta,sannan ya kalleta tare da cewa"Babe,Mu shiga ciki ko?in ɗan taka maki"

Murmushi Abrah,ta saki tare da nuna mashi hanya tace"bismillah,"gaba tayi yabi bayanta,suna tafiya yana yi mata sambatu,"Gaskiya zanyi kewarki sosai baby,bansan ya rayuwata zaka kasance ba,idan babu ke,zan zama tamkar maraya,"_

  Abra tace"hmm,dama ka daina yi mun wannan daɗin bakin naka wlh,Don na sanka,mayen mata ne,Allah kaɗai yasan yawan matan da kake mu'amala dasu,Ni bansan ma tanawa bace,"_

   "Subhanallah,Zargina kikeyi ma kenan?babu kyaufa,"

  "Ba zarginka nake yi ba,zahiran na gani ae,"suna magana suna tafiya har suka shiga cikin reception,mutane ne ke ta safa da marwa a wurin,Batare da sun sha wahala ba,ta hango Aunty babba tana tunkarosu,Fuskar nan aɗaure babu annuri,Amma tana hango saurayin da Abra tazo dashi,nan take ta ɗan saki fuskarta,ƙarasowa tayi wurinsu,

  "Sannunku da zuwa ya gajiyar tafiya,"

   Saurayin ya amsa mata"Alhamdulillah,Mun same ku lafiya,"

  "Lafiya lou,"kafin ta mayar da idonta kan abra tace"Wanene wannan kuma?yakamata a gabatar mun dashi,ko da yake bari mu shiga daga ciki,'tayi maganar tana yi masu nuni da hannunta,

  Saurayin yace"kash,bazan samu shiga ciki ba,ina sauri ne zan wuce wurin wani uncle ɗina dake anan,Urgently yake nemana,"

   Aunty babba tace"Amma banji dadi ba,duk irin wannan ɗawainiyar da kayi mana,bazaka shigo daga ciki ba ka huta,ko lemu ne ka ɗan sha,'

  "Kada ki damu Aunty,Idan kuka dawo daga tafiyar zanzo ne sai mu gaisa dakyau,"

   "Aunty wannan shine Bobby ɗin da nake baki labarinshi,Yana da kirki sosai,Saboda yana kyautatamun,"ta ƙarasa maganar,fuskarta dauke da murmushi,

  Aunty babba tace"Ma sha Allah,naji daɗin ganinka sosai,Allah dae ya nuna mana ranar aurenku,Musha biki,'

  Murmushi ya saki yana faman shafa keyarshi da hannunshi,

    "Bari mu shiga daga ciki,Sae munyi waya,"acewar Abra,

   "Okey babe,ki kulamun da kanki,Sae kinga saƙona,"

   Ya ƙarasa maganar tare da juyawa yabar reception din,Aunty babba tayi gaba Abra tabi bayanta,Har izuwa cikin ɗakin da ta kama,

    Suna shiga cikin ɗakin abra ta saki trolley din kayan,ta faɗa saman gadon ta kwanta tana faman sauke ajiyar zuciya,

    Daga gefen gadon Aunty babba ta zauna,tare da kallonta tace"kun sha tafiya,toh ya ku ka baro su mammyn'?

  "Tana can,rai hannun Allah,ae na faɗa maki cewa bata da lafiya,Amma da sauƙi dae,tunda tana ɗan mikewa har ma ta zauna,Matsalar dae babu mai kula da ita,Shima Abie ya tattara yana shi yana shi yabar gidan,yanzu ita kaɗai ce acikin gidan,bansan ya zata ƙare ba,"hankalinta kwance take yin maganar,

  Shiru Aunty babba ta ɗan yi,batare da ta janye idanuwanta daga kan fuskar abra ba,

  "Aunty kinyi shiru,ba kice komai ba?wai nikam Ina Aunty hayaam ne'?nayi tunanin zan ganku atare ne,kuma nayi mamakin ganinki a hotel"

   Harara ta ɗan watsa mata tare da cewa"in ba a hotel ba,a ina kikeson ki ganni ne?Ko bakisan cewa aure na ya mutu ba"?

...ƙumshe dariya Abra tayi,

    "Kiyi mai isarki lokacinki ne ƴar rainin hankali,Muna nan cikin tashin hankali,ke kina can kina holewarki,wato kin samu duniya ko"?

  Turo baki abra tayi tana fadin"matsalar kenan fa,yanzu nasha wahalar tafiya,ko ruwa ban sha ba,Amma zaki fara yi mun faɗa,Allah in naji ban iyawa,sae dai ki neme ni ki rasa,"

   Sakin baki Aunty babba tayi tana kallonta,kafin tace"lallaine wuyanki ya isa yanka,fiye da haka ma zaki iya faɗamun,"

    murguɗa baki abra tayi tare da cewa"na tambaye ki Aunty hayaam amma baki ce komai ba,tana ina,"?

   Ta6e baki Aunty babba tayi kafin tace"Ae hayaam ni kaina bansan inda take ba,kinsanta bata gajiya da yawo,yau kusan kwana uku banganta ba,sae dai ta kirani mu gaisa,Amma ni kona kirata a kashe nake samun wayarta,"

  Saboda rashin tsoran Allah,Aunty babba ta zauna tana shirgawa Abra ƙarya,don tasan cewa muddin Abra taji cewa,hayaam na kwance gadon asibiti ba lafia,baza ta ta6a yarda suyi tafiyar nan da ita ba,Sai ta tsaya tayi jinyarta,kuma in taji cewar ta bar ƴar uwarta a asibiti babu mai kula da ita,to tabbas ranta zai 6aci sosai,"

   "Kai Aunty hayaam,ita ma dae kamar wadda taci ƙafar kare,bata nan bata can,"

  Aunty babba tace"Ni duk ba wannan ba,Kinsan dai dalilin dayasa nace kizo ko"?

  "Eh nasani,"ta bata amsa,

"Yawwa,Jibi nakeso mu shirya mu tafi,lokacin kin huta sosai,"

  Yatsina fuska Abra tayi,tana ɗan gatsina hanci tace"Oh ni,yanzu haka zamu kwasa mu tafi wurin boka har enugu,cikin dajin Allah,Kamar waɗanda basu da mafaɗi,Kuma dae babu tsoran Allah..... "

  Tunkan ta ƙarasa maganar Aunty babba tace"Rufe mun baki,Uwar surutu sai kace aku,Duk ba don ku akeyi ba?don rayuwarku tayi kyau," fuskarta aɗaure tayi maganar,

  Zumbura baki abra tayi,tare da yin ƙasa ƙasa da muryarta tace"mutun yayi sallar dare mana,ya roƙa wurin wanda ya halicce shi sai wani boka can"

  "Me kikace"Aunty babba tayi tambayar tana kallonta,Don tajiyo ƙusƙus ɗin da take yi,

 Abra tace"Ni Bance komai ba,idan ma nayi magana to akan abinci ne,yunwa nake ji,"ta ƙarasa maganar tana shafa stomach ɗinta,

   "Okey,bari nayi mana order,sae muci atare,don nima banci komai ba,"

   

Wuraren ƙarfe 7,Motoci guda biyu suka shigo cikin gidan a jere,a lokacin Jahad da Sehrish suna a kitchen tare da Aunty azmee suna tayata aiki,Azmee na agaban gas cooker,Sehrish da jahad,suna yanke yanken kayan lambu,

  Jin dirar motacin nan yasa Sehrish saurin cewa"Ga babban yaya nan ya ƙaraso gida,"

  Jahad tace"Anya kuwa shi ne?Junaid fa ya sanar dani cewa yau ko gobe zasu dawo,Allah yasa su ne,kada abunda na haɗa mashi ya lalace,"

  Murmushi sehrish ta saki,tana cewa"Mrs romeo,Ae koda bai dawo ba,mu zamu cinye kayan daɗin da kika haɗa mashi,". 

  Muryar azmee suka jiyo daga bayansu tana cewa"Nima hadani za'aci daɗin,"

  Dariya su kayi gaba dayansu,

Jahad tace"idan zaki ci Aunty azmee babu damuwa,Amma Allah koda bai dawo yau ba,ƙwara na zuba shi a dustbin da dai inba su rishi suci"

  Harara sehrish ta ɗan watsa mata da yake suna facing ɗin juna na,tace"saboda baƙin hali irin na ɗan adam,'

   "Aunty azmee ina da tambaya dan Allah,"acewar jahad,

  Azmee tace"Allah yasa na sani,"

Murmushi jahad ta yi tare da cewa"Tsakanin babban yaya da Junaid waya fi wani kyau,"

  Har sai da gaban azmee ya faɗi rass,Saboda girman tambayar da tayi mata,jinjina kai tayi na wani lokaci kafin tace"tashin hankali,Kuma ni kike so in amsa maki tambayar,"

  Jahad tace"Eh,saboda nasan kinsan menene kyau,zaki iya fadin wanda yafi kyau acikinsu,"

  Sehrish tuni ta dakata da yankar lettuce ɗin da takeyi,hannunta ruke da wuqa,duk ta qagara taji amsar da azmee zata basu,

  "Ni ko a school,ban ta6a haɗuwa da question mai wuyar Amsawa ba irin wannan,To ae dukkansu kyawawane na bugawa a jarida,Junaid kyau rafayet kyau," 

  Dariya sukayi jin yadda azmee keta nanata maganar,da alama sun caza mata kai,

   "Amma ni a ganina,kamar junaid yafi kyau,saboda shi fuskarshi kullum asake take,Kuma wannan murmushin nashi ba ƙaramin kyau yake ƙara mashi ba,"acewar Sehrish,

Jahad tace"Amma ae bai kai yaya rafayet tsayi ba,duk da shi ma dogone,kuma baida irin surar jikin babban yayan mu,"

  Sehrish tace"Ae da ace shima junaid ɗin zai dinga motsa jiki,in a short time zaki ga ya koma kamar babban yayan mu,ae su maza daga sun fara ɗaga ƙarfe Jikinsu ke buɗewa,"

  Azmee tace"hakane kema kince wani abu anan,Gaskiya dukkansu zan iya cewa babu wanda yafi wani kyau,idan don saboda murmushi zaisa junaid ya ɗare rafayet a kyau,to ae shima rafayet ɗin idan yayi murmushi sai kin kusa zaucewa,kilan bai ta6a yin murmushin bane kun gani,sannan kuma ga surar jiki ta ko'ina dae su duka biyun sai dai ace ma sha Allah..."zugudum sehrish tayi tana sauraron abunda azmee ke cewa,aranta tace"Kutmelesi,Su Aunty azmee har ansan su babban yaya nada kyawun sura,da kyakkyawan murmushi,ba dai kalle mun mijina takeyi ba,"ta ɗan yi maganar hada tamke fuska,can kuma ta fashe da dariya...,


  Suna cikin tattaunawar nan,Suka jiyo Muryar Junaid yana sallama,aikuwa jiki na rawa jahad ta ajiye knife din dake hannunta,da gudun gaske ta fito daga kitchen din,

  Yana a tsaye,jikinshi sanye da shadda brown colour,hannunshi ruke da trolley,fuskar nan ɗauke da ƙayataccen murmushi,duk a tunaninta shi kaɗai ne,hakan yasa ta nufe shi da gudu zata rungume shi,ƙiris ya rage ta ƙarasa,Sae ga Marshal Omar da Uncle abusufyan sun shigo,da sauri taci burki,tana faman sauke ajiyar zuciya,Fashewa junaid yayi da dariya yana kallonta,saboda ya gane abunda taso tayi,Su uncle sunyi mashi buƙulu,

.....hannu tasa ta rufe fuskarta,tana dariya,

Murmushi marshal ya saki,haka shima abusufyan ɗin,Jahad sarkin kunya,

   Fitowa sehrish tayi daga cikin kitchen ɗin,fuskarta ɗauke da murmushi,da sauri ta ƙarasa wurin abusufyan,hugging ɗinshi tayi tare da cewa"sannu da dawowa Daddy,ya gajiyar tafiya,"?ta ƙarasa maganar tare da ɗagowa daga jikinshi,

Hannu yasa tare da shafa fuskarta yace"lafiyalou My Daughter fatan na same ku lafiya,"yayi maganar yana miƙa ma jahad hannu,cike da jin kunya ta ƙarasa wurinshi,ya rungumota ajikinshi,

  Marshal Omar yace"Oh ni,babu mai yin hugging dina,daddynku kawai kuka sani,babu komai nasan da hosana na nan,da gudu zata bani hug" dariya sukayi gaba ɗayansu,haɗa baki sukayi wurin gaishe dashi,Ya amsa masu fuskarshi a sake,

  "Lah ya Omar,"muryar hosana ce ta katse su,ɗagowa su kayi gaba ɗaya suna kallonta,Da alama daga bacci ta taso,sae faman lumshe ido takeyi,

  Kai tsaye ta tunkarosu,kamar yadda yayi tsammani,ko Daddynsu bata runguma ba,wurinshi ta wuce,ta rungumeshi tare da kwantar da kanta saman wide chest ɗinshi,'

  Jinjina kai Abusufyan yayi tare da cewa"Hosana ko kallo ban isheki ba ko?,hankalinki na akan Omar," Yayi maganar yana kallonta,

   Murmushi ta saki tare da ɗagowa daga jikin Omar ta koma wurinshi,zata rungumo shi da sauri yaja da baya yana cewa"bana so,babu ruwana dake,ki koma wurin Omar ɗin,Ae ni baki damu dani ba,burina kawai in dawo gida don saboda ke,Amma shine kika watsa mun ƙasa a ido,"

  Dariya suka shiga yi gaba dayansu,hosana kuwa bubbuga ƙafa ta shiga yi muryarta tamkar zata yi kuka tace"pls daddy,let me hug u,wlh nayi missing ɗinka sosai,kawai dae nayi alƙwarin cewa,zan fara tarbar Ya Omar ne kafin kai,kuma banso in karya alƙawarin dana ɗauka,"

   Abusufyan yace"ae gashinan ko?Dama na yafe mashi ke,Ni ga ƴan tagwaye na nan,su da suka damu dani,'yayi maganar yana nuna su sehrish,

  Zumbura baki tashiga yi,tana murmura masu baki,

  Ruko hannun Omar tayi tare da jan shi tace"Mu tafi ya Omar,kayi wanka kaci abinci,Sannan ka kwanta ka huta,"Bin bayanta Omar yayi fuskarshi ɗauke da Murmushi,

  Girgiza kai Abusufyan yayi tare da cewa"Allah ya shirya min ke Hosana,Abun naki sai addu'a,"

  Ya ƙarasa maganar tare da ruƙo hannayensu Sehrish suka wuce cikin palourn,sun ɗan zauna anan suka ƙara gaisawa da daddyn nasu kafin daga bisani,suka barshi ya wuce bedroom ɗinshi don ya huta,


Wuraren ƙarfe 12 na dare,lokacin har sun kammala dinner ɗinsu tuni,Sun koma cikin bedroom ɗinsu,batare da 6ata lokaci ba,Su ka shirya cikin kayan baccinsu,sun kwanta ajere cikin lallausan bargonsu,

  Kwankwasa ƙopar ɗakinsu akayi kwankwan,

    "Wanene"?jahad ce tayi tambayar,saboda itace ta rage  idonta a buɗe,

  "Zo ki buɗe mun kopa,"da sauri ta saukko daga saman gadon jin muryar junaid,

  Hannu tasa tare da buɗe kopar,Yana tsaye cikin sleeping dress dinsa white colour,hannunshi ruƙe da Shopping bag,".  

  Junaid dama ba kayi bacci ba?tayi tambayar tana ƙare mashi kallo,sae hamma yake saki,

   Ashagwa6a yace"Na fara bacci mana,Mommy azeema ce ta tashe ni,saboda kawai wannan saƙon na rishi da tace na kawo mata,"

  Yayi maganar yana nuna mata ledar hannunshi,

   "Eyya,Amma banji daɗi ba,but am sorry,kawo saƙon na ajiye mata,don har bacci ya ɗauketa,"

  Miƙa matar bag din yayi,ta sanya hannu ta kar6a,sannan ta juya zata shiga ciki,da sauri ya ruƙo hannunta tare da janyota ta faɗo jikinshi,hugging ɗinta yayi tightly tare da cewa"I really missed u my Juliet,"

  Lumshe ido jahad tayi tana shaƙar ƙamshin turaren jikinshi tace"I missed u too my Romeo,"_

Kiss ya manna mata asaman cheek dinta,sannan ya raba jikinta daga nashi,tare da juyawa yabar bedroom ɗin,

Har sai da ya 6ace ma ganinta,Sannan ta tura kopar tare da shigewa ciki,A gefen gadon daga ƙasa ta ajiye bag ɗin,batare da ta buɗe taga menene aciki ba,ta haye saman gadon ta kwanta fuskarta dauke da murmushi,

   "Jahad har yanzu yaya rafayet bai dawo ba"!?

  Muryar Sehrish ce ta katse ta,da sauri ta juya left hand ɗinta tana kallonta,a rufe ta samu idanuwanta tamkar mai yin bacci ashe likimo tayi,

   "My own sis,ashe bakiyi bacci ba,"?

  "Idona biyu jahad,baccin ne yaƙi zuwa,"

   Jahad tace"Yakamata kiyi bacci,kinsan da anjima idan babban yaya ya dawo zai tashe ki ne,so it's better ki kwanta yanzu,ko kin samu bacci na minti 30,"

  "Ae baccin ne yaƙi zuwa,"tayi maganar tana ƙoƙarin buɗe idanuwanta,

  "Wanene ya shigo ɗakin nan?ko daddy ne,"?

  "Junaid ne,ya kawo saƙo yace naki ne,Inji Aunty azeema"jin haka yasa sehrish miƙewa daga zaune,tana faɗin"ina sakon yake,"

Hannu jahad tasa tare da ruƙo hannun bag ɗin,ta ɗago da ita,izuwa saman gadon ta miƙa ma Sehrish,hannu tasa ta kar6a,tare da ajiyeta agabanta,tana faman yin hamma,kamar mai jin yunwa,

  Buɗe shopping bag ɗin tayi,tare da ɗan leƙa kanta tana kallon kwalaben dake acikinta tare da robobi,aranta tace"ko na menene wannan,bari dai na ajiyesu,zuwa gobe nasan zatayi mun bayani akansu,"ta ƙarasa maganar tare da matsawa ta ajiye bag ɗin saman side drawer,sam bata son bacci ya ɗauketa,saboda tasan cewa lokacin dawowarshi yayi harma ya wuce,jingina bayanta tayi ajikin head board din gadon,Sae faman yin hamma takeyi tana gyangyaɗi amma taƙi yarda bacci ya ɗauketa,tana yi tana kallon wall clock,kusan ƙarfe ɗaya,amma basu dawo cikin gidan ba,duk yadda taso ta hana bacci ɗaukarta,amma hakan ya faskara a zaune ta fara baccin,itama jahad tuni bacci yayi awon gaba da ita,Hosana dama tuntuni ta ƙundundune cikin bargo tana sharar baccinta,


A round 1:30 na dare,Motarsu ta shigo cikin gidan da gudun gaske ta shararo har izuwa parking space,tsayar da motar Armstrong yayi tare da fitowa,da hanzarinsa ya zagaya tare da buɗe mashi kopa,a hankali ya zuro da ƙafarshi,after some minutes ya ƙarasa fitowa daga cikinta,Hannunshi na'a dafe da forehead ɗinsa yayin da idanuwanshi ke a lumshe,da alama babu cikakkiyar lafiya atattare dashi,tun daga kan yadda yake fitar da numfashinsa,

   "Sorry sir,idan ba damuwa zan iya taka maka,mu shiga daga ciki,naga kamar ba zaka iya ƙarasawa ba".  

   A hankali ya furta"don't worry ur self,Zan iya tafiya da kaina"yayi maganar tare da kama hanya ya wuce cikin gidan,tsayawa armstrong yayi yana kallonshi har saida yaga shigar shi kopar falon gidan,Sannan yabar wurin motar,


  Babu kowa a main palour ɗin,dakyar yake tafiya har ya samu ya hau saman staircases ɗin,Ya wuce part ɗinsu,hannu yasa ya tura kopar,ya shiga daga ciki,Direct ya wuce bedroom ɗinshi,zame t-shirt ɗin dake ajikinshi yayi tare da yin wurgi da ita saman gadon,daƙyar yake fitar da numfashi mai hucin zafi,idanuwanshi kansu daƙyar yake iya buɗe su,.

  Hannunshi yakai tare da ruƙo belt ɗin wandon jikinshi ya cireshi,ya duka ya cire takalmansa,sai da ya rage daga shi sae Short ajikinshi,yana ƙoƙarin zame safar ƙafarsa,kira ya shigo cikin wayarshi,hannu yakai tare da daukarta,inda ya ajiyeta saman side drawer dinshi,duba screen ɗin wayar yayi,da hidden number aka kirashi,Abun yayi matuƙar daure mashi kai,muddin aka kirashi da hidden number sai Ainihin sunan mai number ya bayyana,amma wannan kiran a haka ya shigo mashi,

   Picking call ɗin yayi tare da kara wayar a kunnanshi,Shiru ba'ayi mashi magana ba,shima kuma bai tanka ba,yana ƙokarin rejecting kiran yaji shessheƙar kukan mace,kuka fa sosai tamkar zai fasa screen ɗin wayar,da sauri ya janye wayar daga kan kunnan shi ya zuba ma screen ɗin wayar ido yana kallonshi,cike da mamakin wacece wannan ta kirashi tana raira mashi kuka a irin wannan lokacin"? Rejecting kiran yayi,yana ƙoƙarin ajiye wayar,text message ya shigo wayarshi,on the top of the screen message din ya bayyana,

  Karanta saƙon ya shiga yi kamar haka,

  _Rafayet bazan ta6a bari na rasa ka ba,Zan iya yin komai akanka don na mallake ka,koda kuwa kisan kaine,Na jima da sha'awar son kasancewa tare da kai,alƙawarine wannan na ɗaukarwa kaina_

  Bai damu da saƙon daya gani ba,Saboda yasha haɗuwa da ire-irensu,sun yi nacin har sun gaji sun daina,Amma wannan baisan dame tazo ba,hada ikirarin zata iya yin kisan kai akanshi,koma wacece wannan ba ƙaramar ƴar daba bace da alama,

  wurgi yayi da wayar saman gadonshi,Sannan ya juya daƙyar yake ɗaga ƙafarshi har ya samu ya shige cikin toilet,


*Sehrish*


Firgit ta farka lokaci guda ta miƙe a hanzarce ta wurga idanuwanta kan agogo,ƙarfe kusan 2 na dare,durowa tayi daga saman gadon hankalinta aɗan tashe,sai da ta fara zuwa window ta leƙa taga Motarsu,sannan ta fito da sauri,riga da wandone ajikinta,kanta kuma na sanye da mayafi ta ɗaureshi amatsayin kallabi,tafiya takeyi tana sambatu ga bacci da bai bar idanuwanta ba,

Kitchen ta shiga,jim kaɗan ta fito hannunta ruƙe da tray,Coffee ne asaman shi tare da Fruit,tana ƙokarin hawa upstairs taji ance"Sannu da ƙoƙari," Cak ta tsaya da tafiya,yayin da zuciyarta tayi wani irin bugu ji kake rasss!,a hankali ta juya don taga wanene yayi mata maganar,Waro ido waje tayi ganin babu kowa a babban falon,kuma tabbas taji anyi mata magana,ranta ne ya bata cewa kodai kunnuwanta ne suka jiyo mata hakan,tuna wannan yasa ta sauke ajiyar zuciya ta wuce part dinshi,a bakin kopar shiga bedroom ɗinshi ta tsaya ta fara yin sallama,jin bai amsa mata ba yasa tayi tunanin ko bacci ya ɗauke shine ko kuma ya shiga cikin toilet ne,

  Sanya kafa tayi ta shiga cikin ɗakin,Ƙarasawa tayi wurin table ta ajiye mashi tray ɗin,Sannan ta ɗan jinkirta tana jiran fitowarshi daga cikin toilet ɗin,har lokacin bata daina yin hammar bacci ba,idanuwanta kuma na rufewa,da alama baccin zata cigaba da yi atsaye,

  Tana cikin tsayuwar nan tajiyo sautin aman shi daga cikin toilet,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,bakomai ya faɗo mata arai ba,fa ce abunda ya faru tsakaninta dashi a daren shekaranjiya,kada ace har yanzu ƙyanƙyamin jinin daya gani ajikinta ne yake sa shi yin amai,Nan take taji jikinta yayi wani irin sanyi.........."bata ƙarasa zancen zucin nata ba,Taji motsin fitowarshi daga toilet,

  Tsautsayi da ƙaddara ne yasa Sehrish yunƙurin juyawa don taga a wani hali yake ciki,Aikuwa A gigice ta fasa ƙara,firgitar da tayi ne yasa ta yanke jiki ta faɗi ƙasa a sume,Da sauri Sgr ya koma cikin toilet,tare da jan kopa ya rufe,sam baiyi tsammanin akwai mutun a bedroom ɗin nashi ba,Shiyasa ya fito a naked ɗinsa,babu kaya ajikinshi,Sehrish taga abunda yafi ƙarfin idanuwanta,

  Bada jimawa ba,ya kuma fitowa daga cikin toilet ɗin,Waist ɗinshi ɗaure da towel,ya saki sumar kanshi ta baya,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,yadda ta yanke jiki ta faɗi a sume saboda kawai taganshi babu kaya ajikinshi,kamar taga wani mugun abu?ko kaɗan baiji kunyar komai ba da ta ganshi a haka din,sae ma mamakin sumewarta da yayi,sam baya jin ƙarfin jikinshi,Ƙarasawa yayi wurin da take a sume ƙasa,ya zuƙunne saman guiwarsa ɗaya,Hannayensa ya sanya tare da ɗaukkota ya kinkimota A saman shoulder ɗinshi,A ƙoƙarinsa na yakai ta bedroom ɗinsu,yana ƙoƙarin miƙewa tsaye da ita dauke a kafaɗarshi,Cikin rashin sa'a ƙafafunshi suka harɗe a jirkice ya saki jikinshi gaba ɗaya suka faɗa saman katafaren gadon nashi yaraff nan take mayafin da ta rufe hair ɗinta dashi yabar kanta,kwantacciyar sumar kanta ta tarwatse asaman gadon,


Tunda suka faɗa saman gadon sehrish ta farfaɗo sakamakon ruwan daya Yarfo mata asaman fuskarta,Ruwan sumar kanshi ne daya fito daga wanka bai tsaneta ba,numfashin mutun ta dinga ji da ɗumi duminsa asaman fatar ƙirjinta,tarasa gane maiya faru da ita,meya ke faruwa ne?taji an danneta,wani irin nauyi tamkar an ɗaɗɗaure jikinta haka ta dinga ji,

   A hankali ta buɗe idanuwanta,kai tsaye suka fuskanci ceilling,gabanta ne ya faɗi rass,hannu tasa don taji menene ajikinta,kai tsaye hannunta ya sauka akan lallausar sumar kanshi,shafa sumar ta shiga yi,lokaci guda ta tuna cewa a ɗakin Sgr take,A matuƙar tsorace ta ambaci sunanshi"Ya Rafayet,"shiru bai amsa ba,hakan ba ƙaramin ruɗu ya sanyata ba,

   ƙoƙari yake don ya tashi daga jikinta,Amma hakan ya faskara,a karo na biyu yayi yunƙurin miƙewa,ɗagowa yayi da kanshi yana faman cizon la66ansa,a hankali ya ware sexy blue eyes ɗinshi,kai tsaye suka sauka akan ƙirjin sehrish,Nan take ya tsinci kanshi da bin surar kirjinta da kallo,gaba ɗaya rigar jikinta ta zamo,sakamakon faɗawar da sukayi saman gadon da hannunshi ya zame rigar batare daya sani ba alokacin da yake ƙoƙarin ɗaga jikinshi daga nata,dukiyar fulanin nan nata a tsaitsaye dasu tubarkalla ma sha Allah full ɗinsu,gwanin ban sha'awa,

  Lokaci guda yabi ya susuce,ya tsinci kanshi a wani irin yanayi,Sehrish kuwa tunda ya ɗago da fuskarshi,hankalinta yayi mugun tashi,duk tabi ta ruɗe ta firgita,jikinta sae kerma yake yi,Sam bata lura da abunda yake kallo ba,sae faman lumshe idanuwanshi yakeyi yana buɗesu a hankali,yayin da maƙoshinshi ke motsi,kamar yana swallowing wani abu,wata irin zufa ce ta shiga tsastsafo mashi a gefen fuskarshi,ganin haka yasa ta ƙara tsorata,saboda tunawa da abunda ya ta6a faruwa a tsakaninsu,lokacin da haroon ya bata allurar nan,tuna wannan yasa hankalinta ya ƙara tashi,la66anta sae kerma sukeyi,a hankali ta furta"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un..."sautin muryarta ne yaja hankalinshi,mayar da idanuwanshi yayi akan fuskarta,wani irin kallo ya shiga bin ta dashi,

   Moving face ɗinshi yayi saitin fuskarta,da sauri ta runtse idanuwanta yayin da ta ke ci gaba da ambaton hakan,numfashinsu ne ya shiga haɗuwa dana juna,tana ƙoƙarin buɗe idanuwanta,taji tausasan la66ansa asaman nata la66an,tongue ɗinshi ya zura acikin bakinta,lokaci guda Sehrish tabi ta rikice ta susuce,ta fita hayyacinta,kamar yadda shima ya fita nashi hayyacin,haɗa bakinsu su kayi cikin na juna,suna exchanging saliva ɗinsu,hot french kiss ya shiga mata,tun daga kan lower lip ɗinta ya soma tsotsarshi sosai,laushinsu yasa shi ƙara zabura,gaba ɗaya yabi ya rikice,hannayenshi kuwa tunda ya damƙi boobs ɗinta dasu,ya shiga murzarsu,gaba ɗaya ya kara susucewa,ya zauce ya soma sakin nishi,almost 30 mins ya zame mouth ɗinshi daga nata,ya mayar dashi saman nipples ɗinta,ya kama tamkar jinjiri ya shiga sucking ɗinsu,bada wasa ba,Jikinshi har wani kerma yake yi,tamkar wanda ya shekara da yunwa atattare dashi,raɗaɗin da tafara ji ne ya dawo da ita cikin hayyacinta,a lokacin har yana ƙoƙarin Zame towel ɗin jikinshi bcos all he needs at dat moment was to do it,da alama ya manta halin da amaryar tasa ke ciki na rashin yin salla,a wani irin firgice da iya karfinta na ƙarshe,ta daddage ta ingije Sgr daga jikinta,a wani irin kasalance yayi gefe guda yana faman sauke ajiyar zuciya,jikinta sam babu ƙwari haka ta miƙe da sauri ta dira daga saman gadon,har tana tuntu6e wurin ƙoƙarin guduwa daga bedroom ɗin nashi,tamkar wadda zombie ya biyo,ko mayafinta bata tsaya dauka ba,boobs dinta ma da hannuwanta ta tar6esu sai daga baya ta janyo rigarta da ta zame kasan stomach dinta,ta zura hannun rigar,gudu gudu sauri sauri tabar part ɗinshi,duk ta bi ta ruɗe ta rasa in da zata dosa,Allah dae ne ya kawota ɗakinsu,don kuwa bata cikin hayyacinta,lamarin ya girmi tunaninta,a wani sukwane ta faɗa bedroom ɗinsu,a edge of the bed ɗin,ta zube jikinta naci gaba da yin kerma,hakoranta har gamewa suke yi dana juna kaf kaf,tamkar wadda sanyi yayi ma mugun kamu,ƙanƙame jikinta tayi yayin da idanuwanta ke rurrufewa,wata irin matsananciyar sha'awace ta rufe ta,

Ita kenan,A 6angaren Sgr kuwa tun bayan da ta bar part ɗinsa,bai iya motsa koda yatsansa ba,jibgewa yayi saman gadon tamkar kayan wanki,ga wani irin raɗaɗi da yake ji a kasan mararsa,abun da bai ta6a yi ba arayuwarshi yau ya ɗanɗana ma kanshi,bazai iya tantance meke faruwa dashi ba,wata irin kasalace ta rufeshi,ya jima yana juye juye asaman gadon,cikin wani irin mawuyacin hali kafin Allah ya kawo mashi sauƙin jikin nashi,har bacci yayi awon gaba dashi,


*Boss Bature*


Wuraren sallar asuba,azmee ta kwankwaso ƙopar bedroom ɗinsu,kwankwan,dogon numfashi Sehrish taja tare da buɗe idanuwanta,waɗanda suka canza launi izuwa ja,tamkar wadda tayi ciwon ido,har cikin kunnanta take jin bugun ƙopar ɗakin nasu,amma ta kasa buɗe baki tayi magana,

  Jahad ce ta farka daga bacci tana tambayar wanene,Muryar  azmee tajiyo daga waje tana cewa"Aunty azmee ce,Lokacin sallah yayi,bansan ko kun tashi ba,"

  "Yanzu muka tashi Aunty azmee,muna godiya sosai,"juyawa azmee tayi tare da barin ƙopar dakin,

  "ku tashi rishi lokacin sallah yayi,dan Allah a hanzarta tashi,Sallah tafi bacci da minshari alkhairi,"cike da zolaya takeyin maganar kamar yadda ta saba yi in zata tashe su,zura hannunta tayi abayanta tana ƙoƙarin lalubo sehrish dake kwanciya abayanta wayammm taji babu kowa,ranta ne ya bata cewar kodai ta shiga toilet ne,gyara kwanciyarta tayi tana jiran fitowar sehrish daga toilet ko ta samu itama ta shiga tayi al'walar,duk wannan surutun da jahad keyi A kunnan sehrish tana sauraron Muryarta,


Lalla6awa tayi da rarrafe ta nufi toilet,daƙyar ta iya miƙewa tsaye,a hankali ta tura kopar ta shige ciki,batare da tabari jahad ta ankara da ita ba,


After some minutes,ta fito jikinta ɗaure da towel,jin motsin fitowarta,yasa jahad saukowa daga saman gadon,

     Ta nufi wurinta,tunkan ta ƙarasa wurinta taga alamun ruwa ajikinta,yana ɗiɗɗigowa,fuskarta ɗauke da mamaki tace"Wanka da asuba"?shiru sehrish tayi batare da tace komai ba,

Jahad ta kuma cewa"da ruwan sanyi kikayi wanka ne?naga jikinki yana ta kerma,"nan ma tayi shiru bata tanka mata ba,

   A hasale tace"Sehrish magana fa,nake yi maki,"

   Muryarta a kasalance tace"Jahad,Am not feeling well"tayi maganar tare da wucewa izuwa gaban wardrobe,

  "Meya ke damunki ne"?jahad tayi tambayar tana binta da kallo,

  Shiru tayi ba tare da ta bata amsar komai ba,gyaɗa kai jahad tayi kafin ta wuce cikin toilet,don ta lura kamar sehrish batason zancen,



   

  


  

  




   



  

  

  

  

  




   

   


 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



*AMAREN BANA*


*DR MMN YUSUF (LIKITAR MATA)* 🩺💉💊🚑

07069711327 call or Whatsapp


*Shawara gareki amarya* 🧕👈🏼 *akan babbar matsalar da take damun mu ta addabemu watau ciyon sanyi ( infection)*


Shin kinsan illar da sanyi yake da ita ajikinki kuwa??  hmmm sanyi Yana haifar  Mana da matsaloli Kashi Kashi ciki kuwa harda rashin kwanciyar hankali agidan mazajenmu , miyasa yanzu matsaloli sukayi yawa agidajen aurenmu ne ??? Wannan tambaya ce da kowacce mace yakamata tayiwa kanta saboda yadda abun yazama ruwan dare ,musamman duba da iyayenmu kakaninmu Sam basu fuskanci irin wannan matsalar ba to mu mi yake kawo Mana rashin zaman lafiya da mazajenmu ne duk da mafi yawanmu auren soyayya mukayi sa'banin iyayenmu da mafi yawa auren Hadi ake masu Amma sunfimu kwanciyar hankali shin Ina matsalar take ne ??????


Tabbas duk maccen da take da ciyon sanyi to zataci gaba da fuskantar matsaloli agidan aurenta , saboda sanyi Yana tafiyar da duk wata ni'imar mace yana hanata jin sha'awar mijinta Yana Hana jin Dadin auratayya tsakaninta da mijinta , zata dinga jin ciyo wajan saduwa wani lkcn har da mijin ma zafin zai rinka ji a maimakon yaji Dadi , kinga kuwa doli akwai k'atuwar matsala musamman in kinada kishiyar da zaiji Dadi a wajanta, 

Ciyon sanyi Yana haifar da ciyon Mara Mai tsanani Yana Hana haihuwa idan yayi yawa ajiki yanasa mace budewar gaba Koda kuwa budurwace wadda Bata taba sanin namiji ba to sanyi kansa gabanta ya bude ,yanasa tusar gaba, kuraje, kaikyin gaba, da sauransu , 


Shawarata anan itace kowwace amarya Budurwa ko bazawara ta tabbatar tayi amfani da maganin sanyi kamun komai ,saboda duk.gyaran da zakiyi to aikin banza ne matukar kinada sanyi to ba gyaran da zaiyi maki wani tasiri yadda akeso zai kasance kinyi 'barnar kudinki a banza ne kifara yin maganin sanyi kamun kiyi komai ,


Ina matan da suke cewa duk abunda zanyi amfani da shi na kayan Mata bayamun aiki ????? To kusani bakomai ne matsalar ba sai (infection) matukar kinada sanyi to ba abunda zakiyi amfani dashi kiga aikinsa saidai kiyi ta barnar kudinki a banza ba biyan bukata👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

Wannan yasa nazo maku da sahihin Kuma ingantaccen maganin sanyi na Mata da maza , maganine da yake fara aiki cikin gaggawa matukar kikayi amfani dashi to kinyi bye bye da matsalar sanyi da izinin Allah ,kina fara amfani dashi to kema zakiji canji ajikinki , 

Na Sha ne da sabulun tsarki da Wanda Zaki dafa kina tsarki sai Kuma oil Wanda Zaki rinka shafawa ,

Na.maza Kuma gari ne Wanda za'a rinka dafa mashi cokali daya atace asha ruwan da ikon Allah kun rabu da matsalar sanyi kenan , don Yana da kyau in kinada sanyi to.kiyi magani keda mijinki tunda abune da ake dauka kar kiji sauki shikuma yanada shi kinga anyi ba'ayi ba kenan ,


TAKUCE YAR MUTAN SOKOTO MMN YUSUF MAI KAYAN MATA 😍😍😍😍😍😍😍


Don samun ingantattun magunguna na nemini ta wannan number 07069711327 pls in Baki shirya siya ba kibari sai kin shirya kimun magana pls🤗🤗🤗🤗🤗🤗





*RISHRAF*




A cikin kitchen ta ƙarasa shan kukan nata,ta matse ƴar kwallarta,kafin ta shirya mashi dinner ɗinshi,Asaman Tray tana kan hanyar komawa upstairs,Kwatsam Sai ga haroon ya faɗo cikin falon,ba daga waje ya shigo ba,Acikin gidan yake,amma batasan daga ina yake ba,har sai da gabanta ya faɗi lokacin da tayi arba dashi,yayi jaga-jaga dashi ya jigata sosai,daƙyar yake iya ɗaga ƙafarsa idanuwan nan sunyi jawur dasu tamkar garwashin wuta yadda kasan na Mujiya sun yi luhu luhu,Jini sai ɗiga yake yi daga hancinshi,

  Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,musamman da ya ƙaraso wurinta,duk tabi tasha jinin jikinta,

   Tsayawa yayi kusa da ita yana kallonta,nuna mata fuskarshi yayi da yatsan hannunshi yace"haka kike so ko"?

   Sunnar da kai ƙasa tayi,jikinta yayi wani irin sanyi,

   "Saboda kawai na mareki,Shine aka yanke mun wannan ɗanyen hukuncin,bansan meyasa kowa yake ƙi na ba,An tsane ne ba'a son rayuwata,yau idan na faɗi na mutu alhakina bazai ta6a barinku ba" yana magana yana share hawayen dake shararowa akan fuskarshi,Wani irin tausayinshi ne ya Kamata,

  "Nasan nayi laifi,Amma sau ɗaya na mareki su kuma har sau uku suka mare ni,Bayan wannan Hada wani horon aka ƙaramin,just because of You!Kuma laifi kika yi mun,Kin haɗani da dabba dole raina ya 6aci,ni kaina bada son raina na mare ki ba,Kin ƙuleni ne,"

Tuni idanuwanta suka cicciko da kwalla,muryarta na kerma tace"Dan Allah kayi haƙuri ya haroon....". 

   Bata ƙarasa maganar ba ya katse ta"Haƙuri fa kika ce?hmmmmm,bansan shi ba,Wlh tunda har suka ta6a lafiyar jikina sae uban kowa ya ɗanɗani kuɗarshi acikin gidan nan!Irin ƙuncin da suka ƙumsa mun acikin zuciyata sai sun ga martanin da zan mayar masu,Sun ta6o ma kansu bala'e da masifa,Zaman lafiya ya ƙare acikin gidan nan!Zan kashe musu farin cikinsu na har abada,Zan ƙuntata rayuwarsu,Zanyi silar da zuciyar wasu zata buga,"

  Gabanta ne ya faɗi rass,gaba ɗaya tabi ta razana da kalamansa,Cos in a serious matter yayi maganar,babu wasa a kalamansa,

  Jan ƙafarshi yayi daƙyar yake ɗangyasawa,kama hanyar zuwa part ɗinsu yayi,

    Har yayi nisa da tafiya ya ɗan dakata tare da juyowa ya kalleta,adai dai lokacin itama ta juyo tana kallonshi,

   Nuna ta yayi da yatsanshi"ke kuma!ki kuka da kan ki"!

  Yana ambaton hakan yasa kai da sauri yabar wurin,

  Tashin hankali!

Jikinta har kerma yake,tray ɗin hannunta da ta ruƙo kamar zai faɗi ƙasa,dakyar ta iya ɗaga ƙafarta,jiki amace kamar wadda aka zarewa laka,


Lokacin da ta shiga bedroom ɗin nashi,Har ya fara yin bacci,ƙarasawa tayi ta ajiye mashi dinner ɗinsa asaman table,kasa tashin shi tayi daga baccin,sam babu natsuwa atattare da ita,Kalaman haroon sunyi matuƙar girgizata,har cikin ranta take jin fargaban abunda haroon zai shirya masu,Wannan lokaci ne mai haɗarin gaske a rayuwarsu,tayi zurfi acikin tunaninta,Shessheƙar kukan da take yi ne ƙasa ƙasa Sounds ɗin ke kai mashi cikin kunnanshi,a hankali ya ɗan buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci,direct suka sauka akanta,zuba mata ido yayi yana kallon ikon Allah,Hawaye wasu na bin wasu fuskarta ta jiƙe sharkaf,ta shiga wani irin yanayi na tsoran halin da zasu shiga,


"Lafiya"?yayi maganar a yayin da yake ƙoƙarin miƙewa zaune,jin tayi shiru bata bashi amsa ba yasa shi kai hannu ya daki table ɗin gabanshi,A firgice ta dawo cikin hayyacinta zuba mashi ido tayi tana kallonshi,da sauri ta sanya tafin hannunta tare da wiping tears ɗinta,

  "Hawayen menene asaman fuskarki"?

da sauri tace"babu komai,"

  "Saboda na hana ki zuwa Kano"?

Girgiza mashi kai tayi alamar a''a,

  "To na menene"?

Shiru tayi saboda ba ta da amsar da zata bashi,taso ace zata iya sanar dashi game da kalaman Haroon Wata'ƙil suyi ƙoƙarin dakatar dashi,Amma ina bazata iya ba don bata san miye zai aikatan ba,jin tayi mashi shiru yasa shi miƙewa tsaye ya koma wurinta ya tsaya,Hannu biyu yasa ya tallabo fuskarta,

   "Tell me whats wrong with u?who touch u"?

   girgiza mashi kai ta ƙara yi"babu komai,Bana jin daɗin jikina ne,'

    "ina ke maki ciwo"?

Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,Ae yasan cewa tana period,tuna haka yasa tayi saurin cewa"Marata,ke yi mun ciwo,Amma da sauƙi,"

   ta ƙarasa maganar tare da ɗagowa don ta saci kallonshi,idanuwanshi na akanta tamkar zasu lumshe saboda yanayin da yake jin kanshi a lokacin,

     Zame hannuwanshi yayi daga kan fuskarta,ya mayar dasu saman waist ɗinta,gabanta ne ya faɗi rass,tunani ta shiga yi komai zai yi mata,ɗaukarta yayi cak tare da sauketa saman katafaren gadon nashi,hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba ga wani irin tsoro da taji,

    Ja da baya yayi ya taka izuwa wurin switch ya kashe light ɗin ɗakin gaba ɗaya nan take furniture ɗin ɗakin suka Soma bada haskensu different colours,hatta gadonshi da ya kwantar da ita,tunawa tayi da lokacin da ta ta6a kashe light ɗin ɗakinsa,ranar tayi mamaki sosai abun ya ruɗar da ita kuma ya ƙayatar da ita,Yadda komai na kayan ɗakinshi ke ƙyalli suna bada haske launi launi daban daban da zarar an kashe hasken ɗakin,

    daga inda take kwance take hangen fuskarshi ba ƙaramin kyau yayi mata ba,gaban dressing mirror ɗinshi ya tsaya,ya zura hannayensa acikin trouser pocket ɗinsa,ya jima tsaye a wurin,kafin ya dawo saman gadon daga gefe ya zauna,Da kanshi ya shiga yin serving abincin yana ci atsanake,

  Lumshe ido Sehrish tayi,tunda take a arayuwarta bata ta6a jin bed mattress mai ɗan bala'en laushi da daɗin kwanciya ba irinta Sgr,irin gadon da mutum ko baya jin bacci ya haushi,nan take baccin zai zo mashi,

  tun tana kallonshi biji biji har ya kammala cin dinner ɗin nashi ya miƙe ya wuce cikin toilet daga nan ta fara bacci sama sama,lokacin da taji motsi ta ƙara buɗe idanuwanta,samunshi tayi a tsaye saman Darduma yana yin nafilfilin daya saba,Abun ba ƙaramin tafiya yayi da ita ba,komai nashi burgeta yake yi ba kaɗan ba,a hankali bacci ya ɗauke ta,

    tana cikin baccin nan,taji daddaɗan ƙamshin turaren nan nashi acikin hancinta,Slowly ta buɗe idanuwanta Unexpected eyeballs ɗinta suka sauka cikin ƙwayar idonshi a matuƙar tsorace ta buɗe baki zata yi ihu da sauri ya sanya tafin hannunshi ya rufe mata bakin,

  Ta tsorata ne da ganin yadda blue eyes ɗin nashi ke shining kuma sunyi blue sosai,dama idan dare yayi kalarsu tana ɗan ƙara cizawa,

    "It's me,"a hankali ya furta mata hakan,lokaci guda ta shiga sauke ajiyar zuciya,kallon junansu suka shiga yi,launukan hasken ɗakin dake ƙyalla fuskokinsu ba ƙaramin ƙayatar da abun yayi ba,

  A hankali ya zame tafin hannunshi daga bakinta ya maye gurbinsu da tausasan la66ansa,sosai ya shiga kissing lower lip ɗinta,har izuwa upper,gaba ɗaya Sehrish ta soma fita hayyacinta ɗago da ita yayi tare da zagayawa da hannunshi ta baya ya zuge zip ɗin rigar jikinta ya soma shafa bayan romantically,kafin ya ƙarasa zame rigar zuwa saman stomach ɗinta,Lokaci guda yabi ya susuce saboda halittar ƙirjinta ba ƙaramin fisgarshi sukeyi ba,tayar mashi da sha'awarshi suke yi gaba ɗaya,duk da yana ƙoƙarin Controlling ɗin kanshi saboda period ɗin da takeyi,da sauri sauri numfashinsu ke fita,ga wani irin dumi da temperature ɗin jikinsu yayi,moving hands ɗinshi yayi izuwa saman mararta a hankali ya shiga shafa wurin,hakan ba ƙaramin gigitar da ita yayi ba,Lumshe idanuwanta tayi yayin da wasu siraran hawaye ke fitowa daga cikinsu,mayar da harshen shi yayi cikin bakinta,gaba ɗaya suka kacame ma juna,ita kanta batasan ta zura hannayenta cikin sumar kanshi ba,Duk ta hargitsar da ita,ta cukuikuye mashi ita,zame tongue ɗinshi yayi daga cikin mouth ɗinta,passionately ya shiga bata hot kisses asaman wuyanta,runtse idanuwanta tayi sosai kamar ta fasa ihu haka take ji,A wata irin duniya ta fara jin ta wadda bata ta6a ziyarta ba sai a wannan karon,da Yayan Romeo ya fara sanyanta a hanyar zuwanta,

   Hucin numfashinshi ta dinga ji asaman wuyanta ya lumshe idanuwanshi yana jin wani irin feelings,da bai ta6a ji ba arayuwarshi,ɗan ta halikin nan ya jima yana cutar rayuwarshi saboda ego,almost 30years duk da bai ƙarasa ba,babu aure ba soyayya ta kowace hanya ya haramta ma kanshi mace,But this time around ya fara dawowa cikin hayyacinshi,ya jima bai motsa ba,almost 15 mins,kafin ya mayar da mouth din sa saman nipple ɗinta,kamawa yayi a hankali ya shiga sucking ɗinshi,A ruɗe Sehrish ta zabura,gudun kada tayi mashi irin na jiya yasa ya rufeta gaba ɗaya babu ta hanyar da zata tsere mashi,Sosai ya shiga biyan buƙatar shi da ita,sama sama cikin wani irin yanayi na shauƙi Bacci ya ɗaukesu a rungume da juna,ƙanƙame fa irin sosai ɗinnan,


A 6angaren jahad kuwa ta gaza runtsawa,tunda Daddynsu yace mata ta shirya gobe zasu je kano,kwata kwata bata son zuwa kano,Har acikin ranta ta tsani zuwa garin saboda rayuwar da suka yi acikinshi,Ga fargabar halin da zasu tsinci mahaifiyarsu aciki,Araye ko a Mace?Ko a wani mawuyacin hali na rayuwa,ga kuma babynta Junaid,basu jima da yin waya ba har kuka saida yayi mata akan cewa karta tafi tabarshi saboda ya shirya masu outing gobe,Abubuwa da yawa sun bi sun cunkushe mata,tsaye take acikin ɗakin sai faman safa da marwa ta ke yi,ta gaza kwanciya,har wuraren ƙarfe ɗaya jahad bata runtsa ba,Hosana kuwa tana ƙudundune cikin bargo,hankalinta kwance baiwar Allah,ita da babu cutar so ajikinta,


Ta jima a haka kafin daga bisani ta samu Solution na matsalar,komawa tayi saman gadonsu ta kwanta tare da jan bargo ta ƙudundune,taso ta jira dawowar sehrish amma shiru bata dawo ba,bata damu da hakan ba saboda tana da tabbacin cewa duk inda take tana acikin ƙoshin lafiya,


*Junaid Romeo*..


In midnight (Cikin tsakar dare)


*Wuraren ƙarfe 2:30 na dare*


Yayi nisa acikin baccinshi yaji an ambaci sunanshi da ƙarfin gaske da wata irin murya mai matuƙar razanarwa,tashin hankali,A firgice junaid ya ware idanuwanshi shi kaɗae asaman gadonshi,Gabanshi ne ya faɗi rass!sakamakon Mutun daya gani tsaye agaban mirror ɗinshi sanye da baƙar jallabiya mai hula,a wani irin firgice junaid ya miƙe zaune tare da toshe kunnanshi ya fasa ƙara mai sautin gaske yana ambaton sunan Daddynsu maimaikon sunan Allah,

   Sosai ya shiga ja da baya,Hankalin shi a matuƙar tashe la66ansa na kerma ya shiga faɗin"Daddy!Mommy!Ya Rafayet!ya Omar!kuzo ku taimake ni!nashiga uku!dodo acikin ɗakina!Kashe ni zaiyi,'

   Ƙwayar idonshi tamkar zata faɗo waje saboda tsabar tsoro,

   Mutumin dake tsaye agaban madubin,wasu irin zaƙwa zaƙwan Akaifune a hannunshi,tsininsu tamkar na wuƙa,Ga uban gashi ajikin fatar hannunshi,juyowa yayi junaid na ganin fuskarshi ya rikirkice ya ruɗe,uban gashi ne ta ko'ina asaman fuskarshi,Ga wasu irin dogayen haƙora dake gareshi har sun sauko daga bakinshi,Idanuwanshi kuwa wa'iya zubilla,

  Gadan gadan ya tunkari junaid,A wani irin Sukwane,junaid ya wuntsilo daga saman gadon har yana tuntu6e wurin ƙoƙarin fitowa daga cikin bedroom ɗinshi,fisgar ƙopar yayi dama a buɗe ya barta,da gudun gaske ya fito tare da nufar bedroom ɗin Sgr yana kuka,Sai dai kafin ya ƙarasa wurin part din nashi,Sai ga wannan Mutumin ya bayyana,A gigice junaid ya fasa ƙara ya canza hanya ya nufi part ɗin marshal Omar,Nan ma kafin ya isa,Sai ga mutun ya ƙara bayyana,A galabaice ya sauko daga downstairs,bawan Allah Ya rasa wurin wa zashi,gashi duk ihun da yake yi yana kuka babu mai jin shi,

  *Junaid*!

Muryar jahad ce ta katse shi,da sauri ya juya wurin da sautin ya fito,a tsaye take tana kallonshi da gudun gaske ya nufeta tare da faɗawa jikinta ya ƙankameta yana faɗin"dodo!dodo!"

   

Bugun ƙafarshi da akayi ne yasa shi yin firgit ya farga daga baccin da yake yi,Duk zufa tabi ta jiƙa jikinshi sharkaf,kukan da yake yi acikin mafarkin har azahiri yake yinshi hannunshi rungume da pillow,

  Biji biji ya fara gani acikin eyes ɗinshi kafin idon nashi su washe,

  A hankali ya ambaci sunanta"Aunty Azmee,"yayi maganar tare da tashi daga zaune yana kallonta,

   "Meya faru dakai ne junaid?tunda nashigo nagan ka kana ta koke koke cikin bacci,"ajiyar zuciya ya sauke tare dakai idonshi kan wall clock ƙarfe 9 na safe,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,Ko sallar asuba baiyi ba,

  Cike da damuwa yace"Aunty Azmee wani mummunan mafarki nayi wallahi,Na tsorata sosai,Amma dana farka na ganki sae hankalina ya kwanta,Allah na gode maka da ya kasance ba gaske bane,da yanzu shikenan Na rasa rayuwata,"

   Zama azmee tayi daga gefen gadon mashi,cike da kulawa tace"Junaid!Anya kayi addu'a kafin ka kwanta bacci?

  girgiza mata kai yayi alamar a'a

"Ni nasani ae,tun lokacin baya nake fama dakai akan yin addu'ar bacci before ka kwanta,amma kaƙi jin maganata,"

  Muryarshi tamkar zai yi kuka yace"Aunty azmee,wlh inaso nima na dinga yin addu'ar,amma bansan meyasa ba,karatu baya zama cikin brain ɗina,bazan 6oye maki ba,ban iya komai ba,ko a karatun sallah iya surori biyarne akaina dasu nake yin sallah,amma bayansu wlh ban iya wani abu ba,komai na karanta bai zama acikin kaina,"

  Tsananin tausayinshi ne ya kama azmee,har cikin ranta ta damu da halin da junaid yake ciki,tana jinshi tamkar ɗan cikinta,

   "Junaid ita addu'a,zaka iyayinta da ko wani irin Yare,Allah yana ji kuma zai amsa maka ne,Inaso ka dage da yin addu'a,nima kuma zan tayaka in sha Allah,"

  Ba ƙaramin daɗin maganarta yaji ba,

"In sha Allah Aunty Azmee zan dage da addu'a,nagode sosai da irin kulawar da kike bani,"

  Murmushi azmee ta saki tare da cewa"kada ka manta fa,nifa na shayar dakai,Na so ka sosai junaid,tun lokacin da kana jinjirinka,ban mantawa Abban ku ya ke kawomin kai,

 yini kake a wurina,lokacin yayyanka na zuwa aiki wasu kuma ba su kammala secondary ba,mu kaɗai muke kasancewa acikin gidan,Inyi maka wanka,in shafe maka jikinka da mai in gyara maka sumar kan ka,sannan in canza maka kaya,idan na kammala yi maka wannan,sai in shayar da kai,har bacci ya ɗauke mu saman gado,Kasan me"?

  Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"a'a sai kin faɗa,"

  Taci gaba da cewa"idan na farka naga babu kai a kusa dani kamar in zauce...."

  "Saboda me"?Yayi tambayar da ɗan mamaki a fuskarshi,

   "Saboda na tsani araba ni dakai,Su fawan da zarar sun dawo daga school,har ɗakina suke zuwa su ɗauke ka,"

  Fashewa yayi da dariya sosai har dimples ɗinshi suka lotsa,Bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"Ni bansan meyasa kowa ke sona ba,Ina da farin jini sosai,ko yau muka haɗu da mutun cikin ƴan mintina sai ki ji yace ina burgeshi,"yayi maganar with proud,

  Murmushi Azmee ta saki,kafin tace"Because of ur Glamorous personality,kana da kyakkyawar zuciya,shiyasa ka ke sace zuciyar mutane cikin ƙankanin lokaci,"

..cike da zolaya yace"Shiyasa jahad ta zauce akan sona,"yayi maganar yana dafe saitin heart dinshi,

  Dariya azmee tayi tare da miƙewa tsaye tana cewa"Ga breakfast can yana jiran ka a dining,Jahad ba ta nan balle ta kawo maka a ɗakinka

  Dafe saitin zuciyarshi ya kuma yi hankali a ɗan tashe yace"Aunty Azmee kina nufin cewa,Juliet dina bata nan?yanzu saida Uncle Abusufyan ya tafin mu da ita ko"?a shagwa6e ya ƙarasa maganar yana ɗan bubbuga ƙafarshi,har cikin ranshi baiso tafiyar jahad ba,Yaci burin su fita shan ice cream yau,

  Fucewa Azmee tayi daga cikin ɗaƙin tana dariya,

  Saukowa yayi daga saman gadon jiki asanyaye ya wuce cikin toilet,


*Boss Bature*


  ❤🤍❤


*Marshal Omar*


Fitowar shi kenan daga cikin toilet,Waist dinshi ɗaure da towel hannunshi kuma na ruke da wani short yana goge ruwan dake ɗiɗɗigowa daga jikinshi,

  "Ya Omar"muryar hosana yaji acikin kunnanshi,da sauri ya juya don yaga ko itace,Kwance ya sameta saman gadonshi ko kayan baccinta bata cire ba,

  Cike da mamaki yace"Kee!me kike yi acikin bedroom ɗina"?

   "Ya Omar nifa zuwa nayi kawai don na gaishe ka"tayi maganar a ɗan shagawa6e,

   "Haka ya dace kizo gaishe dani?ko sallama babu,kawai sai dai na fito daga toilet na same ki a kwance saman gadona,"Yayi maganar fuskarshi aɗan daure,

  Murguɗa mashi baki tayi tare da cewa"Ae ɗakin Mijina ne"

  Harara ya watsa mata"waye mijin naki?Allah ya kiyaye in auri mai ɗan kai irin naki,"

  Gwalo tayi mashi tare da cewa"Oho dai,a haka ka gani kuma kake so,"_

  ƙiris ya rage ya fashe da dariya,amma sai yayi saurin kawar da dariyar don kada taga kamar ma wasa yake yi mata,

   "Get out from my bedroom!"a ɗan tsawace yayi maganar tare da nuna mata hanyar fita daga bedroom ɗin,

  Maƙe mashi kafaɗa tayi,"Wlh ba inda zani ya Omar,Kazo ka ɗauke ni,ka fitar dani idan ba ka son gani na,"

  girgiza kai kawai yayi tare da ƙarasawa gaban mirror dinshi,

   "Kaya fa zansa,pls ki fita daga waje idan na kammala saiki dawo,kin ji My baby"

   "Ae wlh ba inda zani je,Ae ba wani abu bane don ka sanya kaya agabana,tunda aure zamuyi,"

  Shiru yayi bai kara tanka mata ba,

Jin yayi banza da ita yasa ta kuma cewa"Ya Omar"shiru yaƙi amsa mata kiran nata,

  Ci gaba da magana tayi"Wai ya Omar,idan munyi aure,to taya zamu haihu muma"?

  Banza yayi bai tanka mata ba,

Bata damu da hakan ba,sai ma ci gaba da maganar tayi,

  "Ya Omar,kana ganin nima zan iya haihuwa?Kuma ma Taya za'ae na samu cikin"?

  Hauka maganinka Allah,ya furta hakan acikin Zuciyarshi,

   "Ji ya Omar ina magana ka wani share ni,idan baka faɗamun ba,to taya zan sani,"?

  Ƙin tanka mata yayi,a hasale tace"Shikenan tunda ba zaka bani Amsa ba,wlh idan Daddy ya dawo zanje in tambayeshi ne,don ni bazan bari ayi abun kunya ba,Ayi mun aure bansan komai ba,

  A ƙule ya juyo tare da kallonta yace"Ke,Tashi ki fuce mun daga ɗaki"

  Maƙe mashi kafaɗa ta kuma yi"anƙi a fita Ya omar,"

  Abun ya ɗaure mashi kai,ita ko shakkarshi bata ji,neman ma abunda zata yi mashi ya bugeta take yi don tasan cewa bazai iya ta6a lafiyar jikinta ba,

  "Idan kanaso in fita cikin lalama,to ka fara faɗamun taya zan samu ciki idan munyi aure"

  "Shine abunda kikeson sani"?yayi tambayar yana kallonta hadi da dage mata gira,ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

Aikuwa Nan take ya sanya hannunshi ya zame towel ɗin daya ɗaure qugunshi dashi,

  Tashin hankali! A gigice Hosana ta fasa wata irin razananniyar ƙara,Kafin kace me kamar walkiya haka tabar ɗakin da gudu tana kuka,ta firgita sosai

  Mayar da towel ɗin yayi ya ɗaure waist ɗin sosai,sai faman tiƙar dariya yake yi,har da dafe cikinshi,

  "Maganinki kenan,nasan daga yau ba zaki sake yi mun irin wannan question ɗin ba,Yarinya sai kace mai iskokai,Ni bansan ya zan ƙare da ita ba,A haka dai nakeso,kuma zan kula da abuna"ya ƙarasa zancen zucin fuskarshi ɗauke da murmushi ya wuce wurin wardrobe ɗinshi,sai daga baya ya dinga tunanin kada hosana fa taje ta faɗa ma wani abunda ta gani tunda ba hankali gareta ba,Tuna wannan yasa yayi saurin ɗauko jallabiya ya zura ajikinshi,da sauri ya sauko downstairs yana nemanta,


Azmee ya hango tana jera kayan abinci asaman Dining na breakfast dinsu,da sauri ya tunkareta,tunkan ya ƙarasa wurinta tajiyo takun takalmin mutun,ɗagowa tayi tare da kallonshi,ganin Marshal yasa ta saki fuska tare da gaisar dashi,

   "Barka da safiya Omar,an tashi lafiya,"

A gaggauce ya amsa mata"lafiya lou,amman pls ko kinga gifcin Hosana,"?

  "kamar dai naso naga giftawarta,lokacin ina ƙoƙarin fitowa daga kitchen,kuma naji kamar shessheƙar kuka ta ke,"

  "Ina kike tunanin ta shiga ne,"

Shiru Azmee ta ɗan yi tana tunanin wurin da taga hosana ta nufa,

  "Yawwa,ina tunanin bedroom ɗinsu ta nufa,"

  Tunkan ta ƙarasa maganar ya kama hanya da sauri da sauri ya nufi ɗakinsu,a buɗe ƙopar take hannu yasa ya turata,tunkan ya shiga ciki,Ya jiyo shessheƙar kukan Hosana,Yana yin sallama taji muryarshi da gudun gaske ta sauko saman gadonsu ta faɗa toilet ta datse ƙopar,tana ci gaba da yin kukan,

..Sehrish na kwance saman gadon,ta ƙudundune cikin bargo,tun da Asuba da ta farka asaman gadon Sgr lokacin ya shiga toilet domin yin alwala,ta saɗaɗa tabar bedroom ɗin nashi,ta dawo ɗakinsu,


Kaitsaye ya wuce ƙopar toilet ɗin ya tsaya tare da ambaton sunanta"Am really sorry Hosana,nasan ban kyauta maki ba,ke ce kin takuramin that's why nayi maki hakan,kuma ni fa amsar tambayarki kawai na baki ba wani abu ba,

  Cikin shessheƙar kuka yaji tace"Ya Omar baka da kunya wlh,Ni babu ruwana dakai,Wlh bansan ganinka,bansan ganin wannan abun naka"

Hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,

  A ruɗe ya shiga faɗin"hosana!baki da hankaline?so kike ki tona mun asiri,har wani ya ji mu?kin manta ni zan aureki,"?

   A tsiwace tace"wlh saina faɗama daddy idan ya dawo,ince ka nuna mun abunka,"

  Hannu yasa tare da dafe kanshi,ya furta"Wayyo Allah na,Ni Omar,naja ma kaina,"

  Ƙasa ƙasa yayi da muryarshi cikin lallashi ya soma magana,

   "My Hosana pls,ki yafe mun,bazan ƙara ba wllh,kome kikeso zanyi maki,"

   "Wlh ya Omar,ko kukan jini zaka yi saina faɗama daddy cewa kai ɗan iska ne,Ni bazan aure ka ba,"

  Tsawa ya daka mata tare da cewa"Ki faɗima duk wanda zaki faɗimawa ƴar rainin hankali,Wlh kuma kika kuskura kika faɗama wani sai na sa6a maki,kuma babu ni babu ke,Ƙasar ma zan bari gaba ɗaya in tafi can in auri baturiya,".  

  Rai a6ace ya juya tare da barin ɗakin nasu,

  Sai da taji alamun fitarshi daga ɗakin,sannan ta wanko fuskarta ta,ta buɗe ƙopar toilet ɗin ta fito waje,abun ya dameta sosai buɗe ƙopar ɗakin tayi ta fuce,A dining ta same shi zaune shi da junaid suna yin breakfast,Azmee na yin serving ɗinsu,

  Kamar wadda aka zarewa lakar jikinta haka ta ƙarasa ta samu wuri kusa dashi ta zauna,

    "Aunty Azmee ina kwana"?fuskar Azmee ɗauke da murmushi ta amsa mata,"Lafiya lou Jahad,kin tashi lafiya...."da sauri junaid yace"Aunty azmee wannan ce jahad?kalli fa ƴan kumatun fuskarta ki gani,Hosana ce,"

  Dariya azmee tayi,shi kanshi Omar yaso ya ɗan dara,ita kuwa tsuke fuska tayi tare da jifarshi da harara tace"ina ruwanka da kumatuna"?

   murguɗa mata baki junaid yayi dama basu jituwa atsakaninsu,Ƴar tsama sukeyi,

    juyawa ta ɗan yi gefenta tare da kallon Marshal,Ya tamke fuskar nan babu annuri acikinta,

   Saitin kunnanshi takai bakinta cikin sanyin murya tace"Ya Omar bazan ƙara ba,kuma bazan tona maka asiri ba,dan Allah kada ka tafi ka barni,"

  side smile yayi tare da cewa"Its okey,nima wasa nake yi maki,bazan iya tafiya nabarki ba,"

  Murmushi ta saki,har hankalinta ya kwanta,

    Hannu Azmee takai zata ɗauki plate ta zuba mata abinci,ganin ta zura hannunta acikin plate ɗin Omar suna ci atare yasa ta fasa,Abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,


*KANO TA DABO TUMBIN GIWA KODA ME KAZO AN FI KA* acewarsu ba,Don ni ban yarda ba,







   

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*






Bayan *Jahad* ta fito daga toilet, hijab ta ɗauko cikin wardrobe ta zura ajikinta,wurin gadonsu ta koma ta haye sama tare da kai hannu tana bubbuga hosana,

   "Get up hosana,Time ɗin sallah yayi,"

  hosana bata motsa ba,sae ma cigaba da jan minsharinta da tayi,

  "Hosana ki tashi mana!ba zaki tashi ba wai,kullum sai kin bani wahala idan nazo tashin ki daga bacci"tayi maganar fuskarta a ɗaure,

  Hosana kuwa,gyara kwanciyarta ta ƙara yi,har wani ƙara jan minsharin takeyi da ƙarfi don ma jahad tasan cewa tayi nisa a baccinta,alhalin tun a first call da tayi mata ta farka,

    A ƙule jahad tace"kada Allah yasa ki tashi,kuma saina faɗa ma ya Omar cewa baki yin....."tunkan taƙarasa maganar,hosana ta diro daga saman gadon da gudun gaske ta nufi toilet ta buɗe ta shige ciki,dariya jahad tayi sosai kafin ta sauka daga saman gadon ta koma ta shimfiɗa carpet ta kabbara sallah,


Sehrish kuwa tana a ƙudundune cikin bargo tayi lamo tana faman sauke ajiyar zuciya,kokwanton abunda ya faru tsakaninta da Sgr takeyi,ta kasa gasgata abunda ya faru last night,shin dagaske ne ko kuwa mafarki ne tayi,Don tasan cewa hakan zai yi wuya ya kasance gaskiya,Abun ya matukar ɗaure mata kai,ya caza mata brain ɗinta,tana cikin wannan zancen zucin bacci yayi awon gaba da ita,


*Junaid Romeo*


Bude ƙopar bedroom ɗinsa yayi tare da fitowa daga ciki,Still kayan baccin jiya ne ajikinshi,ya kara wayarshi a saman kunnanshi,hakan na nuni da cewar waya yake yi,Ashagwa6e yake magana yana faman tura baki,

  "Abba pls come back Soon,nafiso na ganka a kusa dani,"ya ɗan yi maganar yana bubbuga ƙafarshi ƙasa,

  On the other hand,Abbansu yace"ka ji tsoron Allah junaid!Nafa gano ka,So kake in dawo gida,saboda ayi maganar aurenka ko"?

  Murmushi junaid ya saki yana ɗan sosa ƙeyarshi da ɗayan hannunshi"eh dan Allah Abba,nidai duk atakure nake,Allah jina nake kamar a prison,Ayi mun aure kawai in ana son zaman lafiya,"

  Abba yace"idan ba'ayi maka auren ba fa"?

   Ƙuƙuni ya shiga yi ƙasa ƙasa yana cewa"zan addabi kowa ne,in kuma kama ɗaki a hotel....."

Bai ƙarasa maganar ba,Jin dariyar Abbansu ta cikin wayar,ashe duk yaji abunda yake cewa,  

   "Junaid wa kayi mawa?kasan cewa yayyenka gaba ɗaya soldiers ne,Wlh kayi kuskuren yin badai dai ba,kai kasan inda za'a kai ka,".  

  Jin wannan maganar ta Abba yasa shi ɗaure fuskarshi,

  Yana tafiya yana waya,da alama part ɗin Sgr zai wuce,saboda can ya nufa,

  Lokacin daya shiga falonsa,babu kowa,a saman sofa ya zauna,sai da ya kammala yin wayar da Abba,Su kayi sallama,Sannan ya miƙe tare da wuce wa bedroom ɗin Sgr,

  Sallama yayi mashi,jin shiru yasa shi shiga cikin ɗakin kaitsaye,a kwance ya same shi saman katafaren gadon nashi,ya lullu6e jikinshi har zuwa chest ɗinshi,jallabiya ce sanye ajikinshi,tun daga kan yadda yake yin baccin nashi zai tabbatar maka da cewa,yana cikin kwanciyar hankali da natsuwa,

  Lalla6awa Junaid yayi ya ƙarasa kusa da gadon,yana ƙoƙarin hawa idanuwanshi suka sauka asaman bargon Sgr,turus yayi ya tsaya yana kallon ikon Allah,Ya jima yana tunanin kome ya jawo hakan,abu dai gashi nan kana ganinshi ta cikin bargon,hawa sama yayi har zuwa saitin fuskarshi sannan ya tsaya tare da furta sunanshi a hankali"Babban yayanmu,"shiru bai amsa mashi ba,ƙara ɗaga murya yayi'babban yaya,"

  Hannu ya kai tare da shafa gefen fuskarshi ya sake cewa"Babban yaya..,"

  Har cikin dodon ears ɗinsa yaji kiran nashi,daƙyar ya iya ware blue eyes ɗinshi,biji biji ya fara gani kafin idanuwan suka ɗan washe,da wata irin kasalalliyar murya ya ambaci sunan shi"Junaid,"

  Murmushi junaid yayi tare da cewa"nazo ne don na takura maka,Jiya na jira naga dawowarka,amma baka dawo gida ba,har bacci ya ɗauke ni,'_

  Zuba mashi ido Sgr yayi yana kallonshi,

   Hakan yasa junaid ya ɗan tsuke fuskarshi yace"haba yaya rafayet,in zauna in tayi maka zuba kamar parrot maimakon ka mayar mun da martani saika zuba min ido kana kallona,"

   a hankali ya lumshe idanuwanshi kafin ya sake ɗan waresu akan Fuskar junaid ɗin,

  "Me kake so ne"?

Muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"Yanzu babban yaya sai inason wani abu zanzo wurinka?jiya fa na dawo daga tafiya,ko farin cikin ganina ma baka yi ba,"

  Ruƙo hannunshi Sgr yayi tare da janyoshi ya kwantar da kanshi saman ƙirjinshi,yana ɗan shafa bayanshi yace"Am glad to see you,Ya gajiyan tafiya,?kayi mun tsaraba"?

  Ashagwa6e junaid yace"Eh mana,munyi tsarabar fura,da zuma,da sauransu dai,idan kanaso zan yi ma rishi magana ta dama maka fura kasha,Wlh akwai daɗi sosai,nima in nasha kunne na har rawa yake yi,'

   Ya ƙarasa maganar tare da ɗagowa daga jikinshi,da buɗar bakin Sgr sai cewa yayi"you mean tafi abun da nasha last night daɗi"?

A ruɗe junaid yace"babban yaya,me kasha jiyan?Ae ni bansan shi ba balle in san cewa ko yafi furar daɗi,

  Shi kanshi baisan ya furta hakan ba,it was just slip of the tongue,saboda ya kwana da abun aranshi,kuma yanzu haka ma shi yake tariyowa acikin brain ɗinsa,abun ya tsaya mashi arai,yadda har surar jikinta taja ra'ayinshi har ya fita hayyacinshi ya fara romancing ɗinta,ƙiris ya rage jiya ayi abun kunya,

(Allah yaso bai ƙarasa headquater ɗin ba,da shikenan an buge boss,(in jini ba,don na lura wasu in ina kara wannan bayanin suna tsammanin cewa Sune sukeyin zancen zucin,sometimes ina ƙarawa da nawa bayanin)


"Yaya rafayet,"junaid ne ya ambaci sunanshi,ganin ya shiga zurfin tunani, hankalinshi yayi wani wurin,mayar da idanuwanshi yayi kan junaid tare da cewa"don't disturb me pls,Inaso na ɗan huta junaid,"

  Ranshi ya ɗan sosu,jiki asanyaye ya juya zai sauko daga saman gadon,Sgr ya dakatar dashi"Wait,'ɗan tsayawa yayi tare da juyawa yana kallonshi,

  "Tell me what do u want from me"?

Shiru junaid yayi yana lissafin adadin kuɗin da zai kar6a a wurinshi,Don sunyi da jahad zasu fita yawo,gashi ƴan kuɗaɗen acct ɗinsa duk sun ƙare,Yayi broke,'

  ɗaga yatsun hannunshi yayi yana yin lissafin,hakan ba ƙaramin dariya yaso yaba Sgr ba,dama sai da ranshi ya bashi cewar wani abu ne ya kawo shi bedroom ɗinshi,tunda sassafe ko wanka bai yi ba,balle aje ga maganar breakfast,A tsiyacen shi yazo,

  "Zan koma bacci,tunda naga lissafin na ka bamai ƙarewa bane,"

  Da sauri yace"pls babban yaya kada ka koma bacci,yanzu ma daƙyar na tashe ka,". 

  ta6e lips ɗinshi yayi tare da nuna wurin dressing mirror ɗinshi da hannunshi,Yace"idan kuɗine kake buƙata a wurina gasu can ka ɗauki iya yadda kakeso,idan ma na cikin nan isn't enough for u,Zan ƙara maka ta acct,hope hakan yayi maka"?yayi tambayar yana kallonshi,.  

  Washe baki junaid ya shiga yi yana cewa"Babban yaya nagode sosai,wlh duk gidan nan kafi kowa sona,har Daddy ma kafi shi sona,"

  Harara Sgr ya ɗan jefa mashi kafin yace"Saboda ina baka kuɗi ko"?_

  fashewa junaid yayi da dariya,tare da saukowa daga saman gadon ya nufi wurin dressing mirror,


Mayar da idanuwanshi yayi ya lumshe su,shikaɗai yasan irin feelings ɗin da yake ji,kamar yayi hauka,Kuma shi irin mutanan nan ne,waɗanda basa wasa da lafiyar jikinsu,Komai yaji jikinshi na bukata yinshi yake yi don ya samu cikakkiyar lafiya,shiyasa gashi nan ta ko'ina masha Allah,tun daga kan skin ɗinshi zakasan cewa ba ƙaramin gyara take sha ba,haka sumar kanshi,da sauran parts na jikinshi,yanzu kuma ga wani new abu da yake bukata Urgently,


Zuƙunnawa junaid yayi agaban drawer ɗin,ya buɗe middle ɗinta,Dollars ne ya gani a jere,cike fam da ita,har wani ƙyalli kuɗin sukeyi acikin idanunshi,murza hannunshi ya shiga yi,har wani ƙaiƙayi suke yi mashi,Bandir ukku ya ɗauko ya tura su daƙyar cikin aljihun wandonshi,duk da haka basu isheshi ba,sae daya ƙara da naira,A gida na ƙarshe daya buɗe ajikin drawer chest din,kuɗin nigeria ne,Suma ya ɗauki Bandir uku na dubu dubu kusan dubu ɗari uku kenan,Ya turasu cikin ɗayan aljihun daƙyar suka shiga,Bayan ya kammala ya rufe mashi ita,yana ƙoƙarin miƙewa,idonshi ya sauka akan hoton daya faɗo ƙasan tiles,baisan daga ina hoton yake ba,duk a tunanin shi hoton Babban yayansu ne,

  Zukunnawa yayi tare da kai hannu ya ɗauki hoton da ya kife,ya juyo dashi yadda zai ganshi da kyau,

  Da karfi ya furta"Sehrish!"miƙewa yayi tare da tunkarar wurin gadon hannunshi ruƙe da hoton yaci gaba da cewa"wlh itace," jin sambatun da junaid keyi ne yasa Sgr ya ɗan buɗe idanuwanshi tare da wurga eye balls ɗinsa wurin junaid dake tunkaroshi

   Zama yayi daga gefen gadon fuskar nan tashi awashe cike fal da farin ciki,ya kuma yace"Wlh itace,Yaya rafayet ina ka samu hoton rishi tana ƴar ƙarama,"

  "Junaid what are u talking about"?yayi tambayar a yayin da yake ɗan miƙewa zaune,tare da jingina bayanshi akan gadon,

   "Sehrish mana!wadda take yi maka aiki,"

  Cike da mamaki Sgr yace"Kana nufin itace a pic ɗin"?

  Jinjina kai junaid yayi"ƙwarai kuwa itace,"

  Cike da mamaki Sgr ya kuma tambayarshi "taya akai ka gane cewa itace?cos i even asked her last time,amma ta sanar dani cewa ba ita bace'

  Junaid yace"ae duk cikinsu,babu mai ɗigon tawada asaman wuyanshi sai ita,duk sauran basu dashi asaman neck ɗinsu,Idan ka kalli hoton nan dakyau,zaka ga ɗigon baki asaman wuyanta,'. 

  "Lemme see"ya buƙaci ganin hoton,da sauri junaid ya mika mashi,hannu yasa ya kar6a,sannan ya ƙura ma hoton ido yana kallonshi,ɗigon tawadar ya gani asaman wuyanta,closing eyes dinsa ya ɗanyi,yana tariyo kallon da yayi ma ƙirjinta adaren jiya,har izuwa saman wuyanta,tabbas yaga black point ɗin nan,amma abun ya daure mashi kai,ta yadda har ita kanta,bata gane cewa ita bace a hoton,

Buɗe idanuwan nashi yayi akan fuskar junaid sannan atsanake yace"Junaid,dama kallonta kakeyi?" cike da tuhuma yayi mashi tambayar,

  Sunnar da kai junaid ya ɗan yi yana sosa ƙeyarshi yace"Nifa ba kallonta nake yi ba,tun lokacin baya ne,kafin ta bayyana amatsayin mace,muna da kusanci sosai da ita,shiyasa ma har nayi mata wannan kyakkyawan sanin,"

   "Its okey" ya furta hakan,tare da mayar da idanuwanshi kan hoton,Abun ya daure mashi kai,sai lokacin ya shiga tunanin ko meyasa Uncle Abusufyan ya basu hotonsu shi da Omar?

  Muryar junaid ce ta katse shi da cewa"Ka taso muje dining muci abinci pls,nasan kana jin yunwa,'

  Runƙo hannun Sgr yayi,har sai da ya samu ya sauko daga saman gadon,Sannan suka fito atare,har lokacin hoton na hannunshi,daga bayane ya zura shi cikin aljihun jallabiyarshi


Saukowa downstairs suka yi,tunkafin su ƙarasa dining ɗin,suka hango Uncle Abusufyan tare da Marshal Omar,ga Jahad da Hosana ma,duk suna azaune suna cin breakfast ɗinsu,Azmee ce atsaye take yin serving ɗinsu,

  koda suka ƙarasa,da sauri su jahad suka gaisar dashi"babban yaya ina kwana,an tashi lafiya,"?

"Lafiya,sannunku"ya ambaci hakan kafin ya samu wuri ya zauna,junaid ma ya zauna a kusa dashi,

   "Big bro,jiya na jira dawowarka gida baka dawo ba,ina fata kana cikin ƙoshin lafiya,"acewar Marshal Omar,

  "Am ok,"ya bashi amsa atakaice,dama fushi yake yi dashi saboda yaso su dawo gida atare,Amma Omar yace sai ya ɗan ƙara kwanaki,

  Juyawa ya ɗanyi tare da kallon Abusufyan,wanda shima kallon nashi yake yi,jira yake yaga iya gudun ruwan nashi,zai gaisar dashi ne?ko kuwa jira yake yi shi ya gaishe da shi Ne?

   a hankali ya furta"Uncle,ya gajiyar tafiya,jiya kun dawo time ɗin bana nan"

  Murmushi Abusufyan ya ɗan saki tare da cewa"lafiyalou Alhamdulillah,gajiya tabi jiki,'

  Matsawa azmee tayi ta ɗauki plate ta shiga zuba masu abincin da zasu ci,

  Hosana tace"Daddy,rishi fa?kada acinye ita bata ci komai ba,"

  Jahad tace"bacci takeyi tun ɗazu,kuma har tashinta nayi tazo muci abinci,amma tace mun in ƙyaleta,bata jin daɗin jikinta,'

  "Me ya ke damunta ne"?Omar yayi tambayar,

  "Nima bansani ba,tunda asuba dai kamar bata da lafiya,duk ta canza mun,har tambayarta nayi meke damunta amma bata sanar dani ba,"

  Abusufyan yace"bai kamata a ƙyaleta ba,yakamata ku kirata tazo muji menene matsalarta,"

  Jiki na rawa junaid ya miƙe zaije kiranta,karaf idanuwanshi suka sauka kan fuskar Sgr,wani irin kallo ya wurga mashi mai kama da harara,batare da kowa ya lura ba,komawa junaid yayi ya zauna,tare da cewa"Jahad kije ki kirata mana,"_

  "Amsa mashi tayi da toh,kafin ta mike cikin sauri ta wuce bedroom ɗinsu,

  Cike da zolaya Marshal yace"Wato har ka fara bata Command ko"?_

  Kunyace ta rufe junaid,har ya kasa shan Tea ɗin da ya ke sha cikin cup,Satar kallon Abusufyan yayi,Suna haɗa ido nan fa ya ƙara kame kanshi,

Hakan ba ƙaramin dariya ya basu ba,Hosana tace"Ya Omar,wai yaushe ne abun nan?kace idan kuka dawo za'ayi magana nifa na kagara wlh,"

  Gabanshi ne ya fadi rass,Hankali aɗan tashe ya ɗago ya kalleta,ko ajikinta sae ma tura pancake takeyi acikin bakinta,wata irin kunyace ta rufe shi,.  

  Shi kanshi Abusufyan,kunyarce ta rufeshi,sai faman jujjuya fork yake acikin plate,ya kasa cin Abincin,

  Sgr kuwa har ɗagowa yayi ya kalli Hosana da tayi maganar,

  Ƙiris ya rage azmee ta fashe da dariya,jurewa kawai takeyi,

  Junaid ne yayi ƙokarin dakatar da ita ta hanyar yi mata raɗa acikin kunnanta,

  "Hosana waike baki da burki ne?meyasa zakiyi mashi haka,Duk kinsa sunji kunya,daga shi har Daddy ɗin naku,bai kamata kice haka ba,"_

  Turo baki ta ɗan yi tare da cewa"zunubi na aikata ne?kawai kawai saboda nace....."bata ƙarasa maganar ba,sakamakon kallon da taga Omar yayi mata,nan take ta shiga taitayinta,


After some minutes,Jahad ta shigo Dining area ɗin,tunkan ta karaso Junaid yace"ina rishi ɗin take ne"ganin ta dawo ita kaɗai batare da Sehrish ba,

  "Tana aciki,yanzu zata fito,"ta karasa maganar tare da samun wuri ta zauna,


A hankali ta zuro da kafarta,har yanzu jallabiyar ce ajikinta,ta laga gyale akanta,ƙafarta kuma na sanye da flat shoes,jikinta sae kerma yake yi,saboda zazza6in daya rufar mata,amma bata so kowa ya gane halin da take ciki,hakan yasa tun kafin ta ƙaraso wurinsu,ta daidaita natsuwarta sosai,sannan ta shigo dining area ɗin,takun takalminta ne ya janyo hankalinsu,duk suka juyo suna kallonta,gabanta ne ya faɗi Rasss ganin Sgr zaune,aikuwa a ruɗe ta juya zata koma ciki,.  

  Abusufyan ya dakatar da ita,ta hanyar ambaton sunanta"Sehrish,"tsayawa tayi cak,batare da ta ƙara ɗaga ƙafarta ba,wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,kafin a hankali ta juyo ta ci gaba da tafiya,hankalinta duk yabi ya tashi kamar taga wani mugun abu,

   Wurin Abbansu ta tsaya,tare da gaisar dashi,"daddy ina kwana,". 

  Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"lafiyalou Daughter,meyasa baki fito ba tun ɗazu,"?

   "Bana jin daɗin jikina ne,Amma naji sauƙi yanzu"

   "Alhamdulillah,samu wuri ki zauna,"cike da kulawa yayi maganar,

  Gabanta sai faɗuwa yakeyi,ta rasa ta ina zata zauna,inda bazata fuskance shi ba,balle har su haɗa ido,

  Ganin taƙi samun wuri ta zauna sai ƴan dube dube takeyi,Hakan yasa Omar nuna mata gefenshi yace"Zo ki zauna,"hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,saboda yana a left hand ne kuma suna fuskantar su Sgr dake ta dama,kuma kujerar da zata zauna,ita ke fuskantarshi,jiki a mace ta ƙarasa gefen Marshal ta zauna,muryarta na kerma ta gaisar da Marshal"ina kwana yaya Omar,"

  Da fara'a a fuskarshi ya amsa mata,"lafiyalou sister,ya jikin naki,"

  "Da sauƙi,"ta bashi amsa,

"Allah ya ƙara sauki,"

  "Ameen"

"Yaya rafayet,ina kwana,"daƙyar ta iya gaishe shi,sai dai ko kallo bata ishe shi ba,balle har tayi tsammanin zai amsa mata gaisuwarta,lokaci guda ta gane dalilin dayasa yaƙi amsa mata gaisuwar saboda bashi ta fara gaisarwa ba,a matsayinshi na boss ɗinta,wanda ke asama da mahaifinta,

  "Bro baka ji ana gaishe dakai bane"?acewar Omar

   Batare daya ɗago ya kalleshi ba yace"Naji,"yayi maganar tare da ɗaukar cup na coffee yana sha,

  Murmushi marshal yayi,saboda ya gane reason ɗin dayasa yaƙi amsa gaisuwarta,

   Zagayowa azmee tayi kusa da ita,ta ɗan duƙa saitin kunnan sehrish tace"Amaryarmu,me kikeso a zuba maki ne?farfesun nama ko Snacks,"?

    Murmushi sehrish tayi har dimple ɗinta ya lotsa,sannan tace"Aunty azmee pls kidaina zolayata,yanzu idan yaji fa?ni zaki jamawa,"cikin raɗa tayi maganar don kada suji mai take cewa,

  Azmee tace"Shikenan Mrs rafayet,na daina,yanzu dai me kikeso"?

  Sehrish tace"farfesun zaki samun,saboda bakina babu daɗi,"

  Su6ul da baka azmee tayi wurin cewa"kice mun kusa samun ƙaruwar baby kenan,"karaf maganarta ta sauka akan kunnan Sgr,kuma cikin whispering tayi maganar,amma wani iko na Allah yaji abunda tace,ko kuwa yayi amfani da motsin la66anta ne Oho,

  Kamar daga sama taji yace"Keee!"a ɗan firgice azmee ta ɗago,ba ita kaɗai ba hatta su Uncle sai da suka ɗago suna kallonshi,ya haɗe fuskar nan babu annuri acikinta,.

    Da cokalin hannunshi yayi mata nuni da tabar wurin,Jiki asanyaye azmee ta juya da sauri tabar wurin,

  Sam sehrish bata ji daɗin hakan ba,duk sai taji babu daɗi,bata so Sgr ya kori Azmee ba,agaban kowa da kowa wannan kamar Cin fuska ne,Su kansu sauran dake zaune a dining ɗin basu ji daɗin hakan ba,shiru kawai su kayi,tunda basu da yadda zasuyi dashi,

   Ganin ya sallami Azmee yasa ta shiga ƙoƙarin yin serving ɗin kanta,plate ta ɗauko acikin jerin plates ɗin dake ajiye saman table din,Warmers din tashiga bubbuɗewa harta buɗo wadda ke ɗauke da farfesun naman kaza,serving spoon ta sanya,ta shiga ɗibarta tana zubawa acikin plate din,sai da tacika shi,sannan ta rufe warmer ɗin,


Sosai ta shiga shan farfesun,har wani lasar baki takeyi saboda daɗinshi da takeji,cinyar kaza ta ɗauko tana ƙoƙarin kaiwa bakinta,Sgr ya ɗago da idanuwanshi,karaf suka shiga cikin nata,nan take tasha jinin jikinta,kasa ƙarasa kazar tayi cikin bakinta,cak ta tsaya,tana kallonshi,

  Wannan karon kallon da yake yi mata yasha bambam da irin kallon daya saba yi mata a baya,gaba ɗaya sun shagala da kallon junansu,babu wanda ya lura a wurin,tunani tashiga yi komai yasa yake kallonta har haka batare da ya janye idanuwanshi ba?

  Shikuwa gogan jira yake ta kawar da idonta daga kallon da takeyi mashi,kada raini ya fara shiga tsakaninsu,saboda abunda ya faru jiya,musamman da ta ganshi tsurararshi babu kaya a jikinshi,

   ƴar harara ya watsa mata,tare da janye idanuwanshi daga kanta,kawar da nata idon tayi,mayar da cinyar kazar tayi cikin plate,gaba ɗaya taji komai ya fita ranta,ba don ta ƙoshi ba,ta miƙe zata bar dining ɗin,

  "Whe're u going"muryarshi ce ta dakatar da ita,

   daƙyar ta iya buɗe baki tace"Na koshi,"

  Zuba masu ido Abusufyan yayi yana kallonsu,

    "Koma ki zauna,"Yayi maganar yana nuna mata seat ɗinta,Tamkar ta fashe da kuka haka taji,juyawa ta dan yi suka haɗa ido da daddynsu,kafin ta zauna,taci gaba da shan farfesun da ta rage,

  Hannu yasa ya yago tissue,yana goge mouth ɗinsa,kafin daga bisani ya miƙe ya wuce part ɗinsa,

   Sai da ya bar wurin sannan,ta samu natsuwa,

  "Daddy,ya maganar zuwa kano?sehrish ta faɗamun cewa,da zarar kadawo daga damaturu zaku wuce kano,Wurin neman Oumman mu,"jahad ce tayi maganar,

  "In sha Allah gobe nake son tafiya,tunda Asuba before ku tashi daga bacci ma"

  Yana kai ƙarshen maganarshi,Hosana tayi saurin cewa"daddy,pls dani za'a tafi,wlh inason zuwa kano,"

  Harara marshal ya ɗan wurga mata kafin yace"a haka za'a tafi dake?me kika sani?Faɗamun a wata unguwa kuka zauna a kano"

   Wurga ido sama tayi tana ƙoƙarin tunano anguwar da suka zauna a kano

  Yatsina fuska tayi tare da cewa"Dawanau ko"?

me zasuyi in ba dariya ba,gaba ɗayansu suka fashe da dariya,ɗaure fuskarta tayi,don ita ba ta faɗi don ayi mata dariya ba,bilhaƙƙi da gaske take ita,

  Jahad tace"kai  hosana dawanau fa kika ce?Anan ne muka zauna?,' murguɗa mata baki tayi batare da ta ƙara cewa komai ba,

   "Daddy dan Allah ka tafi dani,nafi kowa son naje,"acewar sehrish,

  Mayar da idanuwanshi yayi kanta tare da cewa"Kin tambayeshi ne?ko kin manta yadda muka yi dake,"_

  Jin haka yasa ta ɗan ɗaure fuskarta don tasan cewa,daƙyar ne Sgr yabarta ta tafi kano,

  "Ki je ki tambayeshi,idan ya barki tun yau ki fara shiri don da asuba zamu tafi,idan kuma ya hana to zan tafi da jahad ne"

   Tuni idanuwanta suka ciko tab da kwalla saboda tasa ran zuwa kano,

  Mikewa tayi daga saman kujerar tace"shikenan daddy,zan tambayeshi,Allah yasa yabarni,"ta ƙarasa maganar tare da barin wurin da sauri ta wuce ciki,


Bayan sun kammala yin breakfast ɗin,kowa ya kama gabansa,


A 6angarensu Aunty babba,tafiya ta kankama,Domin kuwa tun yau sun kammala shirinsu na tafiya Enugu,sun kimtsa kayansu da zasu tafi dasu,da asussuba zasu bar Abuja,da farko zasu fara sauka a hotel ne,a washe garin ranar zasu wuce,Cikin dajin da Bokan yake,taci alwashin cewa Sai taga bayan Hosana,saboda itace silar tonuwar asirinta,kuma A sanadinta ne tarasa igiyar auranta ɗaya,Bayan haka kuma taci alwashin saita Sanya soyayyar Abra acikin zuciyar Sgr,fiye da yadda ya Ke son iyayenshi,

  Tashin hankali!Rayuwar hosana na cikin haɗari,


Shin ina hayaam dake a kwance gadon asibiti cikin mawuyacin hali,har yau ba ta dawo cikin hayyacinta ba,Gashi likitocin sun nemi wani makusancinta sun rasa,babu wani atare da ita,baiwar Allah,bamu son ya zata ƙare ba,


Gab da sallar magrib,Wayarta dake ajiye saman gadonsu ta shiga ringing,a lokacin tana acikin toilet,Jahad ce kawai acikin bedroom ɗin nasu,tayi zaman cin tuwo saman gadon,ta ƙura ido tana kallon k-drama acikin system dinsu,Hannu tasa tare da daukar wayar Sehrish,ta duba mai kiran nata,Sunan Aunty azeema ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,picking tayi tare da manna wayar a kunnanta,

  "Assalamu alaikum,mommy azeema"

On the other hand azeema tace"Daughter,kin ga saƙo na"?_

Murmushi jahad tayi kafin tace"Aunty azeema yanzu baki gane muryoyin mu?Jahad fa ce ba rishi ba,"

  Hajiya azeema tace"wlh naso in ɗauki muryarki,Ashe second daughter ce,To ya kike"?

  "Lafiya lou Alhamdulillah ina lafiya,"

  "Madallah,Amaryar junaid,"

Cike da jin kunya jahad tace"Aunty azeema waya faɗi zancen nan,"

   Dariya hajiya azeema tayi kafin tace"oh kin manta matsayina a wurin daddynku ne?Ae shi da kanshi ya sanar dani,kuma naji daɗi wlh,Junaid zai samu kamilar mace wadda zata kula da rayuwarshi,"_

  kayataccen murmushi jahad ta saki,ba ƙaramin daɗin maganar taji ba,

   "Ina fata zaki kula mana da bugun zuciyar mu?

  Dariya jahad tayi tana faɗin"in sha Allah,zan kula maku dashi,"

  Hajiya azeema tace"Yawwa My daughter,but akwai abunda nakeso na tattauna tare dake game da junaid!amma ki bari zan kira wayarki,ko zuwa anjima ne,"

  "To Aunty Allah yakaimu anjiman lafiya,"

  "Ameen daughter,ina sehrish ɗin take ne?inaso nayi magana da ita ne,"

  Jahad na ƙoƙarin bude baki tayi magana,sai ga sehrish ta fito daga toilet din,jikinta sanye da bathrobe,wankan marece tayi,dama duk in tana period,kusan sau uku take yin wanka,'

   Ganin wayarta a hannun jahad yasa ta tunkarota tana tambayarta wanene ya kirata,

  Mika mata wayar jahad tayi"kar6i nan,Mommy azeema ce keson magana dake"

  Jiki na rawa ta kar6i wayar,da sauri ta koma gaban mirror,ta zauna saman kujerar,sannan tayi mata sallama,

  "Daughter,ya ake ciki ne?ina fata kinga saƙona ko"?

..Sehrish tace"nagani,junaid ya kawomin su,nagode sosai,"

  "Yawwa,Zaki ga turarurruka aciki,Tun yanzu zaki fara amfani dasu,akwai wasu sirrika atattare dasu,sannan akwai mayuka na gyaran fata,dana gyaran gashi,Original ne,Cikin one week,kina fara amfani dasu zaki ga sauyi a jikinki,Sannan akwai sauran kayan da ba yanzu zakiyi amfani dasu ba,suna da haɗarin gaske,su kansu turarurrukan nan,Shu'umaine na gaske,Fisgar mutun sukeyi kamar magnet,ƙarfi ne dasu,duk in zaki shafasu ki bari sai in zaki part ɗinsa,idan ba haka ba gaskiya za'a iya samun matsala,"

  Natsuwa sehrish tayi tana sauraronta,sun jima suna waya kafin daga bisani su kayi sallama,

   Kasa yin amfani da turaren tayi,tsoranshi ma take ji,tunda taji ance fisgar mutun yake yi,kada ta jama kanta bala'e tana zaman zamanta lafiya,

   bata shafa turaren ba,Amma ta fara amfani da mayukan gyaran jikin,

  Shaf shaf ta shirya cikin Doguwar riga ta material black colour,mai zanen manyan flowers a jikinshi launin ash,rigar tabi shape ɗin jikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba gaban mirror ta koma ta zauna,powder ta murza a fuskarta,Sannan ta shafa man baki,la66anta sae salƙi sukeyi,

   Bata yafa komai akanta ba,Iya sumar kanta ce data sauko har gadon bayanta,high hills ta zura a ƙafarta,

  Kama hanyar fita daga ɗakin tayi da sauri jahad tace"Ina zuwa?

  "Zanje part ɗin babban yaya ne,Inaso na gyara mashi ne,"

  Murmushi jahad ta saki tare da mayar da idonta kan system ɗin gabanta,

  "Kinyi kyau sosai,kada fa ki zautar mana da babban yayanmu a rasa gane kanshi,"

  dariya sehrish tayi batare da tace komai ba,ta fuce daga dakin,


Babu kowa a falon,da alama duk sun tafi yin sallar magriba ne,tana cikin tafiya,kwatsam taji an ruƙo sumar kanta ta baya,a firgice ta juya don taga wanene,Gabanta ne ya faɗi rass!ganin Haroon kamar wani maye haka ya kama dogon gashin kanta,yakai shi izuwa saitin hancinsa yana shinshinar ƙamshinshi,

  A wani irin tsorace sehrish ta buge hannunshi,sam batasan cewa zata hadu dashi ba,da batayi kuskuren fitowa daga dakinsu ba,batare da ta sanya mayafi ba,

   Fuskarta a daure tace"Dan Allah menene haka"?

  Shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da cewa"Shauƙi,"

  Harara ta watsa mashi,aranta tace"Mai hali bai ta6a canzawa dama saida raina ya bani cewa karyane tuban da yace mun yayi,"

  Guntun tsoki taja,da hanzari ta juya zata wuce saman stairs din,aikuwa da sauri ya sha gabanta ƙiris ya rage ƙirjinta ya daki nashi,hakan ba ƙaramin daga mata hankali yayi ba,

  "Ka bani wuri na wuce,banason wannan rashin wayon naka,Bakasan cewa ni matar aure bace,"

  Ta6e bakinshi yayi tare da cewa"And then so what idan ke matar aure ce?Nafa son komai,auren yarjejeniya ne,mutumin nan fa da kika kwallafa rai akanshi ba sonki yake yi ba,Ni ne mosayinki,inason ki sosai,kuma ashirye nake dana aureki da zarar ya sake ki...."

  Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshinta,tuni idanuwanta suka cicciko da kwalla,ta tsani taji ance mata haka,

  Ranta a matuƙar 6ace tace"Wlh koda ace mazan duniya sun ƙare duka kaf babu su,kai kaɗae ne ka rage sai dabbobi a cikinta,to na ƙwammace in auri Biri da in aure ka,"

  Waro ido waje yayi yana kallonta a hasale yace"Ke!ni kike gayawa wannan maganar?baki da hankali ne?ki rasa dawa zaki haɗani sai biri,kina nufin cewa biri yafi ni mahimmanci a wurinki"?

   "Ƙwara shi dabbane,kaifa mutunne mai hali irin na dabbo...."_

  Bata ƙarasa maganar ba,a fusace haroon ya sanya tafin hannunshi ya ɗauke ta da mari,Sae dai kafin ya janye hannunshi daga saman kuncin ta,yaji shima an dauke shi da wani irin zazzaffan mari,Kuma kafin yayi wani yunƙuri yaji tafukan hannaye again har biyu asaman fuskarshi,Tashin hankalin 


Wasu irin baƙaƙen taurari ya gani acikin idanuwanshi,tsabar raɗaɗin da ya ji ne yasa shi sakin ihu,yana tangal tangal zai fadi,gaba daya duk yabi ya susuce,har fitsari sae da ya saki a wondonshi,saboda tsabar raɗaɗin daya ji,

    A galabaice yace"Na shiga uku!Meke faruwa dani ne!dan Allah ataimakamin duhu cikin idanuwana,"

   Shessheƙar kuka kawai sehrish keyi hannunta dafe da kuncinta,mutum biyu ne suka mari haroon,shigowarsu kenan Suka ganshi ya sharara mata mari,aikuwa da gudu Abusufyan ya ƙaraso ya kwashe shi da mari,Marshal Omar kuwa,Hannu biyu yasa ya ɗauke shi da Mari ta baya,hakan yasa yaji duuuuum acikin kunnanshi,babu wani sauti kwata kwata,kamar ya kurmance,

  Ruko hannunta Marshal yayi"kiyi haƙuri kinji,dan Allah ki daina kuka," side hug yayi mata yana dan bubbuga bayanta,Abusufyan kuwa sam ya kasa magana sai faman huci yakeyi,ranshi yayi mugun 6aci,

  "Banaso Sgr ya shigo yaji wannan aika aikar da haroon yayi,don wlh sai ya ɗanɗana kuɗarshi,Sehrish ki wuce bedroom ɗinku,ki barni dashi,zaici ubanshi ne,"

.. Cikin shessheƙar kuka tace"Part din babban yaya zanje in gyara mashi"

   Tayi maganar tare da wuce wa upstairs da sauri tana ci gaba da yin kukan,

 "Uncle,dan Allah ka shiga daga ciki,Ni zanji dashi,"

  Jinjina kai kawai Abusufyan yayi tare da juyawa yabar falon,

   Kwakkwaran damƙa Marshal yayi ma wuyan rigar haroon dake a zube ƙasa yana birgima,ɗaɗɗago dashi yayi ya jashi,har izuwa ɗakin da suke hukunta mai laifi,lallai haroon ya ta6o ma kanshi,


Lokacin da sehrish ta faɗa cikin palourn shi,Saman sofa ta zauna tana cigaba da yin kukan,taji zafin marin da haroon yayi mata sosai,abun ya tsaya mata aranta,tsanarshi ta ƙara ninkuwa acikin zuciyarta,ta jima a zaune batare da ta motsa ba,har aka kira sallar isha'e,sae bayan da aka kammala sallar sannan ta miƙe ta wuce cikin bedroom ɗinshi,toilet ta fara shiga ta gyara mashi,kafin ta dawo bedroom ɗin nashi tana gyarawa,har lokacin bata daina yin shessheƙar kukan ba,


Bayan ta kammala gyara mashi part ɗin nasa,kasa tafiya tayi saboda a ƙagare take daya dawo,saboda tayi mashi maganar zuwansu kano,Addu'arta Allah yasa yabarta taje,

  Safa da marwa ta shiga yi acikin bedroom ɗin nashi,gajiya tafara yi da yin yawon,wuri ta samu daga gefen gadon ta zauna,gyangyaɗi ta fara yi a ƙarshe bacci ya kwasheta,bata ƙara sanin meke wakana ba,


*SGR*


Around 12 ya dawo cikin gidan,Army trouser ne ajikinshi,sae farar shirt mai dogon hannu,Lokacin daya shiga bedroom ɗinshi bai ankara da ita ba,rage kayan jikinshi yayi kafin ya shiga toilet,bayan ya kammala yin wankan,Ya fito sanye da bathrobe ajikinshi,gaban mirror ya tsaya sai da ya kammala shafe jikinshi da tsadaddun mayukan jikinshi,ya gyara sumar kanshi sosai,kafin ya koma wurin closet ɗinshi,after some minutes ya dawo cikin ɗakin jikinshi sanye da Sleeping dress Red colour,yayi wani fresh dashi,tunanin kiranta yayi a wayarshi don ta kawo mashi dinner ɗinshi before ya kwanta,Yana ƙoƙarin juyawa don yaje ya ɗauki wayarshi daya ajiye saman drawer ɗinshi,wayar ta shiga ruri,da sauri ya ƙarasa tare da ɗaukar wayar,duba screen ɗin wayar yayi sunan*Uncle donald*ne ya bayyana,

Picking call ɗin yayi a natse ya kara wayar a kunnanshi,Cikin harshen Spanish suka soma yin maganar,wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana cigaba yin wayar,fuskarshi asake da alama ba ƙaramin farin ciki yake da kiran ba,

    Sun jima suna magana da uncle ɗin nashi,kafin sukayi sallama,mayar da wayar yayi saman side drawer ɗin ya ajiyeta,sauke ajiyar zuciya yayi tare da kwantar da bayanshi asaman laps ɗin sehrish batare da saninshi ba,lumshe idanuwanshi yayi a hankali ya ɗan waresu,ƙoƙarin juyawa yayi karaf eyes ɗinshi suka sauka akan hannunta,Har sai da gabanshi ya ɗan faɗi rass saboda baiyi tsammanin ganin  mutum a cikin bedroom ɗinshi ba,kuma farat ɗaya bai gane cewa ita bace,A sukwane ya miƙe zaune yana kallonta,cike da mamaki,Hankalinta kwance sae sharar baccinta takeyi,Abun ya ɗaure mashi kai har saman gadonshi,

  Clapping hands ɗinshi yayi,A firgice sehrish ta farka,Sakamakon sautin da taji na tafin da sgr yayi mata,A Ruɗe ta miƙe daga zaune,sumar kanta duk ta yarfo ta saman fuskar ta rufe mata idanuwanta,hakan yasa bata iya tantance wanene ba,Amma ranta na bata cewar mamallakin ɗakinne ya dawo,Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,tsoro ya hana ta janye gashin kanta daya rufe fuskarta don taga wanene,

  Shi kuwa boss man ɗin ya zuba ma sarautar Allah ido,ganin ta kaza yin motsi yasa shi yin magana

   "Bacci asaman gadona"?wani irin wahallan yawu ta haɗiya,

   Muryarta na kerma tace"Am Sorry yaya rafayet,wlh bansan bacci ya ɗauko ni ba,Asaman gadonka,Na tsaya ne saboda inason yin magana dakai,"

   Matsawa yayi kusa da ita,ta maƙure ajikin head board ɗin gadon,

   A hankali ya sanya hannu tare da ruƙo doguwar sumar kanta,Ya yarfar da ita gefe guda,ta sauka asaman kafaɗarta,runtse idanuwanta tayi da sauri saboda bazata iya jurar kallon cikin nashi idanuwan ba,Ƙwayar idonshi ba ƙaramin rikitar da ita takeyi ba,Hada ƙarin ƙwayar idon yasa take jin tsoranshi,

     "Neman me kike yi mun"?yayi tambayar a yayin da yake saukar da idanuwanshi saman lips ɗinta,

  "Dama,na tura maka saƙo ta whatsapp ɗinka,bansani ba ko ka gani,"tayi maganar tare da buɗe idanuwanta,suka sauka kan fuskarshi da sauri ta kawar dasu izuwa saman yatsun hannunta data aza asaman laps ɗinta,

   "I saw it already,naji complain ɗinki,Bayan wannan tashinki da nake yi in midnight,baya takura maki"?

   "A'a,Nima ina samu nayi sallah,"

  Jinjina kanshi yayi tare da cewa"Okey,je ki kawomin dinner ɗina,'

  Amsa mashi tayi da toh,kafin ta sauko daga saman gadon,tayi mamakin yadda yake yi mata magana cikin sanyin Murya babu wannan faɗan,tayi tunanin cewa,Zai ɗauke ta da mari ne,amma sai taga akasin hakan,

  Har ta kusa fita daga bedroom ɗin nashi ta ɗan dakata da yin tafiyar,ta juya tare da kallonshi a lokacin harya kwanta,

   "Yaya rafayet"ta ambaci sunanshi,

Har cikin kunnanshi,tsayar da idanuwanshi yayi akanta,Yana jiran jin me zatace,

     "dama gobe daddy zai tafi kano,kuma yana so ya tafi tare dani,"

  Shiru ya ɗanyi na wani lokacin kafin yace"dole sai dake za'a je kano ɗin ne? ba wani wanda zai iya replacing ɗinki"?

tunda taji haka,jikinta yayi sanyi,

   Muryarta tamkar zata yi kuka tace"Akwai,"

  Bai ƙara tanka mata ba,kama hanya tayi ta fuce,sai da ta sauko downstairs sannan ta fashe da wani sabon kukan,Ta kwalfa rai akan son zuwa Kano,


*tawaga biyu zasu yi tafiya gobe in Allah yakai mu,Tawaga ta farko zasu tafi neman wani da suka rasa a rayuwarsu,Tawaga ta biyu kuma zasu tafi wurin boka neman sa'a,*😱😳

  

  








    

   

  

    




  






    

  

   



   

  


  

  




   



 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




Na biya bashi😏


Masu buƙatar littafin Suyi mun magana direct ta layina amma fa message ta whatsapp kawai,Ko an kira ba'za a samu ba, 08103884440


❤🤍❤


Tun wuraren ƙarfe Goma,Motarsu Abusufyan tayi dirar mikiya acikin jahar Kano,Da kanshi yake yin driving ɗinsu,Jahad na manne a kafaɗarshi tana sharar baccin da bata ƙarasa ba a gida,

  Tunda suka shigo cikin garin murmushi ya wanzu akan fuskarshi,Bakomai yake tunawa ba fa ce irin rayuwar da yayi acikin garin tun lokacin ƙuruciyarshi,

   "Jahad!ki tashi mun ƙaraso fa,"cike da farin ciki yayi maganar,

Sai da ya ambaci sunanta kusan sau 5 kafin ta amsa mashi,tare da miƙewa daga zaune tana yin hamma,ta cikin face mask ɗin dake a fuskarta,

  Buɗe idanuwanta tayi tare da juyawa tana ƙarewa garin kallo ta cikin glass ɗin Motar,hakanan ta dinga jin faɗuwar gaba rass!rasss!lokaci guda kuma tashiga tariyo abunda ya faru acikin rayuwarsu azamansu garin,


NASARAWA G.R.A


Shine Sunan Unguwar da hajiya Ameenatu Wato Gwaggon katsina tayi rayuwa acikinta tare da ahalinta,a hankali motarsu ta shigo cikin unguwar da matsakaicin gudu,A dai dai jerin wasu manyan gidaje na masu hali,Abusufyan ya tsayar da Motar a bakin gate,

   "Daddy wannan gidan wanene'?tayi tambayar tana kallon fuskarshi,

  murmushi ya ɗan yi tare da cewa"Wannan gidan da kike gani acikinsa nayi rayuwa tare da mahaifiyarku,Kuma anan kakan ku Marigayi baba buzu yayi gadi,Allah ya jiƙanshi da rahama,

  Amsa mashi tayi da Ameen,kafin suka fito daga cikin motar,

  "Allah sarki,Kullum idan nadawo a wancan lokacin,Baba buzu nake samu zaune saman benci yana dafa ruwan bununsa,da zarar ya hango motata zai fara yi mun kirari,Ya buɗe mun gate don in shiga daga ciki," acewar Abusufyan,

Jefi jefi mutane ke giftawa acikin unguwar,tun bayan da suka bar kano a lokacin baya,Mijin Gwaggon katsina ne ke zama a cikin gida kafin Allah yayi mashi rasuwa,Tun daga lokacin kuma babu wanda ya ƙara zaman gidan,ko Dr harris idan yazo kano ya kwammace ya kama hotel ya zauna acikinsa,

   Hannu ya zura acikin aljihunshi ya curo key ɗin gidan,Ya ƙarasa tare da zura key ɗin ajikin ƙopar dake manne da gate ɗin gidan,Wurin har ya fara tsatsa,ya ciccije daƙyar ya samu ya buɗe ƙopar,

  Ya ruƙo hannunta suka shiga daga ciki,

   Zuba ma gidan ido tayi tana kallonshi,A ranta tana ayyana irin rayuwar da mahaifiyarsu tayi acikin gidan,Ya haɗu duk da ginin Ya tsufa sosai,akwai fili sosai,Ga wurin buga ball nasu Abusufyan,Ga moto park,da sauransu,

Kaitsaye suka nufi Ƙopar da zata sadaka da Babban falon gidan,ita kuwa ta zuba ido tana ƙarewa gidan kallo,Uwar yanace ta ko'ina yayi datti,ga tarin ƙura musamman ajikin glass ɗin windows dana doors,

  Buɗe masu ƙopar yayi da key ɗin hannunshi,Yayi gaba tabi bayanshi,Kamar mai jin tsoro haka ta zura ƙafarta ciki,Matsakaicin falo ne,Yadda kasan bola,ledoji,yayi da sauran tarkace a kasanshi,Tiles ɗin kuwa duk yayi dirty kura ta rufe shi,Sofas ɗin dake a ɗakin duk sun gajarce sunyi ƙanƙanta,yadin jikinsu yayi diƙiƙi,

  "Daddy,ina ɗakin da Oumman mu tayi rayuwa acikinshi?ka nuna mun inaso naga ɗakin,"

  Da yatsan hannunshi ya nuna mata bedroom ɗin da abu tayi rayuwa,da sauri ta nufi ɗakin,shima yabi bayanta,A datse ƙopar ɗakin take amma babu key ajikinta,da ƙarfi yasa hannu ya turata,ji kake ƙiiiiiiii,ta buɗe a slow,

  Faɗawa cikin ɗakin tayi tana bin kayan cikinshi da kallo,labulayen duk sunyi ƙura,sun nannaɗe sun cukuikuye,Carpet ɗin bakin kofar ya fita hayyacinshi,Single bed ne acikin ɗakin,sai wardrobe ta bango,itama duk tayi ƙura,book shelve,Da dressing mirror da sauran tarkace,komai yafita hayyacinshi,

   Qur'ani ta hango saman bedside drawer ɗin gadon,

  Tun kafin tayi magana Abusufyan yace"Wancen qur'anin da kike gani na mahaifiyarku Ne,mace ce mai son addini tana ƙoƙari sosai,bata wasa da ibada,da haka ta sace mun zuciyata,"

  Hawaye ne suka soma sintiri akan fuskarta,ƙarasawa tayi gaban drawer ɗin ta sanya hannu tare da shafa al'qur'anin,ta kakka6e ƙurar dake akanshi,ɗago dashi tayi a hankali ta manna mashi kiss,

   "Daddy inason qur'anin nan sosai,zamu tafi dashi,"ta ƙarasa maganar tare da buɗe handbag ɗin dake hannunta,ta zura shi ciki,"

  School bags ta hango guda biyu,Anyi hanging ɗinsu a saman bango inda aka bubbuga ƙusa,

  Da sauri ta ƙarasa tare da kai hannu ta curo jakunkunan,ta sauko dasu ƙasa,ta zuƙunna tare da buɗe jakar,Littattafan addini ne cikinsu,Ahlari ne,Tajweed,Fiqhu,da sauransu,ɗayar jakar kuma da ta buɗe Littattafanta ne na boko da take zuwa school dasu,komai nata mai tsari,

  Abusufyan kuwa wurin wardrobe ɗin kayanta ya wuce,buɗewa yayi yana kallon jerin wasu daga cikin kayanta,Uniform ɗin  islamiyyarta ya ɗauko,tare da rungumesu a ƙirjinshi,Sae lokacin hawaye suka shiga zarya akan fuskarshi,

   Bazai ta6a mantawa ba,da rana ta farko daya fara sanyata acikin idanuwanshi,a lokacin tana kan hanyar dawowarta daga school,

   "Jahad,"ya ambaci sunan ta tare da juyawa yana kallonta 

  "Na'am Abba,tayi maganar tare da miƙewa ta ƙarasa gabanshi,

   "Kin ga waɗannan kayan,dasu ne na fara ganin Oummanku,Uniform ɗinta ne na islamiyya,"

  Murmushi ta saki tare da sanya hannu ta kar6i kayan,Rungumesu tayi ajikinta,Sae ta dinga jin tamkar Oumman tasu ta rungume,

  6ata lokaci sukayi sosai suna bincike acikin ɗakin Zainabu abu,

Daga bisani ne Yunwa ta fara kamasu gashi gidan babu abinci,Yanke shawarar zuwa nemo masu abincin yayi,ya barta acikin gidan,Gyara masu ɗakin oummansu ta shiga yi,Taci baƙar wahala sosai,Bayan ta share ɗakin har wanke shi tayi,A kitchen ta samu bokiti da ledar detergent,ga ruwa available,sosai ta wanke ɗakin sai ga tiles ɗin yayi haske sosai,Cire zanin gadon tayi ta ɗauko wani acikin wadrobe,Ta shimfiɗa masu bayan ta kakka6e gadon,ta goge jikinshi,


Hatta glass door din sai da tabi tayi scrubbing ɗinsu,ta goge yanar ɗakin,lokaci guda kamanin ɗakin suka canza,Komai na son gyara,Toilet ta shiga nan ma tataras dashi duk sai a hankali,sae da ta fara gyarashi fess,Sannan ta samu ta ɗan watso ruwa tare da ɗauro alwala,

  Darduma ta dauko cikin wadrobe ta shimfiɗata,ta kabbara sallar azhar,A tsanake tayi sallar tana kammalawa,agalabaice bacci ya ɗauketa saman dardumar,


Wuraren ƙarfe 2:30 Abusufyan ya shigo cikin gidan hannunshi ɗauke da Ledojin da yayi masu take away na restaurant,

  Da sallama ya shiga cikin falon,wuce wa bedroom ɗin yayi,ba ƙaramin mamaki yayi ba,ganin yadda Jahad ta gyara ɗakin tsaf,komai yayi fess,kamar lokacin da Zainabun shi na nan,

  Murmushi ya saki tare da samun wuri kasa gefenta ya zauna,Ya ajiye ledojin,Hannu yasa abayanta ya ɗan bubbugi kafaɗarta"Jahad!tashi muci abinci,"

  Firgita tayi ta farka tana Sambatu"Ya Rafayet,baisan na taho ba...,"

  Ƙiris ya rage yaji abunda tace,

Hannu tasa da sauri ta toshe bakinta,tana kallonshi,Shima kallon nata yake yi,

   "Me kika ce"?girgiza mashi kai ta shiga yi,tana faɗin"bakomai Daddy,Ashe ka dawo,nagaji ne shi ne na ɗan kwanta don in huta,"

  Murmushi yayi tare da cewa"Ae naga aikin da kikayi,kin yi ƙoƙari sosai,"

  "Bari na ɗauko mana plate,"ta miƙe tare da nufar hanyar fita daga ɗakin,

  Sai da tafito sannan ta dafe saitin zuciyarta tana faman sauke ajiyar zuciya,a ranta tace"Allah yaso daddy baiji abunda nace ba,dashi kenan zai gano ni,"_

Tayi maganar tare da yin saurin wuce wa cikin kitchen ɗin,A cikin kwandon wanke wanke ta samu tray da plates tare da cups,gaban basin taje ta wanke su tass da klin da soso,ta ɗaurayo su,bayan ta kammala wankesu saman tray din ta jera su,Ta ruƙosu a hannunta sannan ta dawo cikin bedroom ɗin,

  "Salamu Alaikum"Ta kwaɗa sallama ta shiga ciki,Zuƙunnawa tayi ta ajiye trayn agaban Abusufyan,

  Janyo ledar tayi ta buɗe,tare da sanya hannu ta curo fried meat(tsiren nama)ta jera masu shi asaman tray,hannu yasa ya taimaka mata wurin ɗauko sauran kayan,Cool Drinks ne da sauran kayan maƙwalashe,atare suka shiga ci suna fira gwanin ban sha'awa,bayan sun kammala cin abincin,Abusufyan ya tattara kayan abincin da sukayi amfani dashi,Ya wuce dasu kitchen yabarta zaune tana shan lemu,bayan ta shanye,ta sanya robar a dustbin,komawa tayi saman gadon ta kwanta,cikinta yayi haƙe² saboda cin muguntar da ta yi,wani baccin ne ya sake ɗaukarta,


*Boss Bature*


  ❤🤍❤


Wuraren ƙarfe 3 na rana Sgr ya dawo cikin gidan,Tun bayan da ya fita da safe Ko breakfast bai nema ba,saboda Emergency call ɗin da akayi mashi acan headquater ɗinsu,Jikinshi na sanye da Tank Top,light green,Tare da wandon kaki,Yayin da kunnanshi ke manne da wayarshi,Cikin harshen faransanci yake yin waya,

  Da sauri da sauri ya haye upstairs,direct ya wuce part ɗinshi,tunkan ya shiga ciki ya fara jin daddaɗan ƙamshi nakai mashi ziyara acikin hancinshi,gaba daya yayi tsammanin  cewa zai same ta ne a part ɗin nashi amma baiga Kowa ba Wayaam,Bedroom ɗinshi ya shiga,Shaf shaf ya rage kayan jikinshi ya faɗa cikin toilet,After some minutes ya fito waist ɗinshi ɗaure da towel,Yana tsaye agaban mirror yaji motsin mutun acikin falonshi,

   "Who's there"?yayi tambayar yana jiran amsa,

  "Sehrish ce,"

Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"Come in,"

  Hannunta na ruƙe da tray na Lunch ɗinshi da ta shirya mashi,tana tafiya gabanta na faɗuwa rass rass 

  Sallama ta fara yi mashi ya amsa,kafin ta sanya ƙafa ta shiga ciki,sum sum ta lalla6a ta ajiye mashi tray asaman table,Jiki na rawa ta juya zata bar ɗakin,

  Zuba mata ido yayi ta cikin mirror yana kallonta,tana ƙoƙarin ɗaga ƙafarta tabar ɗakin taji ya Ambaci sunanta kai tsaye"JAHAD"

  DARAAAM!!!!!!Taji gabanta ya faɗi,sanƙamewa tayi atsaye,hankalinta a matukar tashe,tuni zufa ta shiga wanke mata fuskarta,Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya abakinta,Abun ya ɗaure mata kai,farat ɗaya Sgr ya gane cewa ba Sehrish bace,Hatta junaid yau bai ganeta ba,kowa ɗaukar sehrish yake yi mata,saboda sunsa ma ransu cewa da jahad aka tafi,Shiyasa basu natsu sun gane cewa itace ba,"

   Wata irin zufa ce ta shiga gangarowa asaman fuskarta,ƙiris ya rage ta saki fitsari a wando,

Slowly ya juyo tare da tunkararta,jikinta sae kerma yake yi,hannunta ya ruƙo tare da juyo da ita ta gabanshi ya kasance suna fuskantar juna,wuƙi wuƙi tayi mashi da idanu tana faman mazurai na rashin gaskiya,

   Abun ya ɗaure mashi kai,Wai harshi zasuyi wa wayau,kamar wani soko,An gaya masu cewa a banza yakai muƙamin da yake dashi a yanzu,

   goya hannayenshi yayi asaman wide chest ɗinshi,Ya zuba mata ido yana kallon Ikon Allah,

   Saboda tsabar rashin gaskiya tun kafin ma yayi mata magana,murya na kerma tace"Amm...um..babban..yaya pls dan Allah kayi haƙuri ka yafe mun,Wayyo Allahna na shiga uku,"a ruɗe tayi maganar,tana yarfa hannuwanta,tsoranta kada ya kwashe ta da mari,

  Ruke ha6arsa yayi cike da mamaki yake kallonta from head to toe,

   Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,tun kafin ma taji hukuncin da zai yanke mata,Zuciyarta sae bugawa take yi ba ƙaƙƙautawa,

   "Where's she"?fuskarshi a ɗaure yayi tambayar,

  Sunnar dakai tayi kamar munafuka,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Wlh baban yaya ni bani nace ta tafi ba,yau ne dama da asuba,ta same ni cikin damuwa take tambayata lafiya shi ne na sanar da ita cewa Ni banso nabi Daddy kano,bansan zuwa garin saboda abunda ya faru damu acikinshi...."

  Tunkan ta ƙarasa maganar yace"What!tafiya tayi without My Permission,"ranshi a matuƙar 6ace yayi maganar,

  "Ya salam"ya furta hakan tare da zura hannunshi cikin sumar kanshi,

Ya runtse idanuwanshi,

"Am sorry,babban yaya bazan ƙara ba,"_

Jinjina kanshi yayi tare da ware idanuwanshi akan fuskarta,yana kallonta duk tabi ta susuce,

   "Kin iya frog jump ko"?

Waro ido tayi tana kallonshi,girgiza kai tashiga yi alamar a'a,

...ruko hannunta yayi ya fito da ita cikin falonshi,fuskarshi a daure yace"Oya,start from here,karki kuskura ki tsaya,if not zaki ga abunda zai biyo baya,"

   Jahad tamkar zata fashe da kuka,Zuƙunnawa tayi tare da kama kunnanta kamar ɗan kwaɗo haka tafara yin tsallan tana zagaye kujerun,tun a first round jikinta ya fara gaya mata,Komawa yayi cikin bedroom ɗinshi ya ɗauki wayarshi daya bari agaban Mirror,Numbar Uncle Abusufyan ya lalubo,ya danna mashi Call,


A lokacin Abusufyan,Na acikin kitchen ya tu6e rigarshi daga shi sai shorts,ya dage sai aikin goge goge yake yi da ƴan wanke wanke,ya gyara kitchen ɗin tsaf,

  Fitowa Sehrish tayi hannunta ruƙe da wayarshi,har tuntu6e take yi wurin yin sauri donta kai mashi wayar,tana baccinta mai daɗi ringing ɗin wayar shi ne ya tashe ta,


"Daddy,ana kira,"ta ƙarasa maganar yayin da take shiga kitchen ɗin,hannu abusufyan yasa ya kar6i wayar,duba screen din wayar ya fara yi,

   *My first in-Law* Shi ne sunan daya bayyana akan screen ɗin,Yayi mamakin ganin kiran Sgr,Picking call ɗin yayi ya kara wayar a kunnanshi,

   "Assalamu Alaikum"

On the other hand,Sgr ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,Uncle kun isa Lafiya"?

.  "lafiya Lou,ae tun ɗazu muka ƙaraso,"

   "Okey,inason magana da sehrish ne,tana a kusa"?

   Murmushi abusufyan yayi tare da cewa"Ae bada ita muka zo ba,ko ka manta ne?

   "Uncle,Da ita ka tafi bada Jahad ba,yanzu haka jahad tana a part dinta,Sunyi musaya ne,"

  Cike da mamaki abusufyan yace"Jahad tana a gida!"

  Gaban Sehrish ne ya faɗi rass,wuƙi wuƙi tayi da ido,ɗagowa abusufyan yayi tare da kallonta,Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,sai lokacin ya shaida cewa Sehrish ce,ya ɗauko amatsayin Jahad,Ko ya akai suka shirya Wannan batare da kowa ya ankara ba,

  Sunnar dakai ƙasa tayi,ganin irin kallon da daddynsu yake yi mata,

  Rai a6ace ya miƙa mata wayar"Kar6i nan,"

  Hannunta na kerma ta kar6i wayar,hankalinta a matuƙar tashe,ta sanya wayar a kunnanta,muryarta tamkar zata yi kuka tace"Ya rafayet........"

   Tunkan ta ƙarasa maganar ya daka mata tsawa"Shut up!"nan take ta shiga taitayinta,

    "da iznin wa kika bar garin nan"?_

  Idanuwanta ne suka cicciko da kwalla,Sae faman kallon uncle take yi,sam baiji daɗin abunda sehrish tayi ba,don yasan ƙarshe kanshi abun zai ƙare,

   "Am sorry ya rafayet,dan Allah kayi haƙuri,Bazan ƙara ba,"

  dogon tsoki yaja,Kafin yace"Come back home,In ba haka ba,Ranki zai 6aci,"yana faɗin hakan yayi rejecting kiran,

  Fashewa tayi da matsanancin kuka,

Hannu abusufyan yasa ya kar6e wayar,

  "Koma meya laifinki ne!Ashe baki da hankali Sehrishi!Why kike son Jamin ina zaman lafiyana?,Taya zaki kamo hanya batare da iznin Mijinki ba,?"

   Cikin shesshekar tace"dan Allah daddy,kayi haƙuri,na kwallafa raina ne akan son zuwa,nasan nayi laifi,Kuma nayi danasanin yin hakan,Amma dan Allah daddy,Ka roƙan mun alfarma a wurinshi,Yabarni in zauna,Saboda yace in koma gida yau ɗin nan,"ta ƙarasa magana tare da sanya hannu tana share hawayenta,

  "I can't Call him Sehrish,rafayet bazai saurari kowa ba a halin yanzu,Kawai kije ki shirya kayanki,in kaiki tasha ki hau mota,"

Jin haka yasa ta ƙara fashewa da matsanancin kuka,tana faɗin"dan Allah daddy,kada ka mayar dani,Nashiga ukuna,"

  Sosai take kuka,Shi kanshi ya tausaya mata,duk yadda take shakkar Sgr amma ta kama hanya ta baro gidan batare da izninshi ba,tabbas ba ƙaramin son zuwa takeyi ba,

   Muryarshi a sanyaye yace"Kiyi hakuri daughter,babu yadda zamuyi dole ki bi umarnin Mijinki,lokaci yana ƙurewa,ki je ki shirya kayanki,mu tafi tasha,"

  Juyawa tayi da gudun gaske,Ta koma ɗaki,Saman gadon ta faɗa tare da fashewa da wani sabon kukan,


Jikin abusufyan ba ƙaramin sanyi yayi ba,yaso ace akwai wata hanyar da zai iya taimaka mata,don ta zauna a kanon,Amma ba halin yin hakan,

  yana cikin wannan zancen zucin wayar shi ta shiga ruri,da sauri yakai idonshi kan wayar dake hannunshi don yaga mai kiran nashi,Sunan Yaya Hossein ne ya bayyana akan screen din wayar,

  Da sauri ya answer kiran ya kara wayar a kunnanshi"Assalamu Alaikum,Yayana na kaina"_

  On the other hand,Abba yace"wa'alaikum salam ƙanina na kaina,Ya kake fatan kun isa kanon lafiya,"

  Fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Mun ƙaraso tun wuraren goma,"

  Abba yace"Madallah,naji daɗi sosai,kai dawa kuka tafi ne"?

   Shiru ya ɗanyi yana tunanin halin da sehrish take ciki,ranshi ne ya bashi cewar Ya sanar ma Yayan nashi,May be ya iya dakatar da Sgr ɗin,

   Calmly ya soma magana"Ya hossein,Wlh an samu matsala,Da jahad na shirya tafiya,bansan ya akai ba,su ka yi musaya ita da sehrish,dama ta kwallafa rai akan son zuwa kano,To yanzu haka zancen da nakeyi maka,Muna tare da Sehrish ɗin,Kuma Sgr ya gane cewa da ita muka zo kano,ya bada umarnin ta koma yau yau ɗinnan,baiwar Allah tana cikin damuwa,yanzu haka tana can tana kuka,"yaƙarasa jawabin yana jiran jin amsar da abba zai bashi,

   "Kada ka damu,Ka lallasheta ta kwantar da hankalinta,Ni zanyi mashi magana,duk yadda mukayi dashi,in sha Allah i will inform you,"_

  Ajiyar zuciya abusufyan ya sauke tare da cewa"Nagode sosai,Yayana nakaina Allah yabar zumunci atsakaninmu,"

   "Ameen Ameen,ƙanina,"abba ya amsa mashi before suyi sallama,

   Har hankalinshi ya ɗan kwanta duk da yana zullumin amsar da abban zai bashi,don yasan halin Sgr wani lokacin idan ya burkice,mai tankwarashi sae Allah,


A lokacin da kiran abban ya shiga wayarshi,Yana zaune asaman sofa,ya aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,Yana sanye cikin jeans da t~shirt,yayin da jahad ke zukunne agabanshi,Tayi kneel down fuskar nan tayi jaga jaga da ita,tasha kuka har ta gode wa Allah,

   Hannu yakai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman front table din gabanshi yayi picking call ɗin,tare da kara wayar a kunnanshi,Ya furta"assalamu alaikum,"

   Acan 6angaren abba ya amsa mashi"Wa'alaikum salaam,My son ya kake ya gida,ya kuma aiki"

   "Alhamdulliah"

Abba yace"Yawwa,Rafayet dama game da yarainyar nan ne,Sehrish,"tunda yaji ya ambaci sunanta,Ranshi ya bashi cewar sunkai ƙararsa ne,

    "Dan Allah rafayet,ka ƙyale yarinyar nan ta zauna,ba jimawa zasuyi acan ba,Yarinyar nan ta kwallafa rai akan son zuwa can shiyasa harta tsallake ta tafi ba tare da saninka ba,Amma kai shaida ne akan yarda takeyi maka biyayya sau da ƙafa,duk wani abu da zai 6ata maka rai,tana ƙoƙari don taga ta faranta maka rai,pls rafayet ta ci albarkacin wannan,"

  shiru yayi batare da yace komai ba,

  Har sai da abban ya sake cewa"Rafayet naji kayi shiru,"

  Ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa"its Okey daddy,na haƙura,"Yanayin yadda yayi maganar,bada son ranshi ba,

   Muryar abba ɗauke da farin ciki yace"Ko kaifa,Wlh har naji daɗi acikin raina,Allah yayi maka albarka "

"Ameen"daƙyar ya iya furta hakan,Sallama su kayi ya janye wayar daga kunnanshi,

  mayar da idanuwanshi yayi kan jahad yace"U can go" 

  Miƙewa tayi tana faman ɗangyasa ƙafarta,tabar falon nashi,ba ƙaramin jiki taji ba,Saukowa tayi downstairs tana cigaba da yin shessheƙar kukan,

  adai dai lokacin junaid ya faɗo cikin falon,Tsayawa yayi yana kallonta,ƙarasawa yayi da sauri wurinta yana faɗin"rishi lafiya meya faru"?

...ɗagowa tayi da idanuwanta waɗanda sukayi ja saboda kukan da tasha,Waro idonshi ya ɗanyi tare da ambaton sunanta"JAHAD"

   Cikin shesshekar kuka ta amsa mashi"Na,am"

   Hannu yasa ya tallabo fuskarta,"Dama bada ke aka tafi kano ba"?

  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,sannan tace

"Tare da sehrish aka tafi,amma dani muka shirya tafiya,Shine mukayi musaya ni da sehrish,yaya rafayet ya gano ni,Shine ya hukunta ni Hada tsallan kwaɗi ya sani,"

   Hannuta ya ruko,tare da samun wuri saman sofa suka zauna,

   Ranshi aɗan 6ace yace"Allah dana son da haka bazan bari Babban yaya ya sanyaki yin tsallan kwaɗi ba,Meyasa zai sanya juliet ɗita,Aikin wahala,'?

   hannu yasa yana share mata hawayen dake sauka akan fuskarta,cikin lallashi yace"stop crying my juliet,Allah in baki daina zubar da hawayenki ba,Nima zan fara kukan,".  

  Cike da zolaya,ya sanya hannunshi yana murza idanuwanshi,kamar zaiyi kukan,

  Da sauri ta ruƙo hannunshi tana faman sauke ajiyar zuciya tace"Nadaina".

  murmushi ya saki tare da cewa"Yaushe zamu fita yawo?Da anjima ko gobe"?

  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Mu bari sai gobe,Yanzu har la'asar tayi,Nafiso mu fita da wuri,mu zaga garin nan,"

   "Yadda kikeso haka za'ayi,"ya karasa maganar,tare da kai la66ansa zai sumbaci gefen fuskarta,Karaf idanuwanshi suka sauka akan na SGR dake ƙoƙarin saukowa downstairs,da sauri ya janye la66ansa,ya shiga ƴan kame kame,

  girgiza kai kawai sgr yayi don yaga abunda junaid ɗin ke ƙoƙarin yi,Fita yayi daga cikin falon batare daya tanka masu ba,


   

*Boss Bature*


*Sehrish*


hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,jin cewa an barta ta zauna a kanon,taji daɗi sosai acikin ranta,duk da tana fargabar hukuncin da Sgr zai yanke mata idon suka koma gida,


Bayan sallar la'asar,Suka shirya tsaf domin zuwa hotoro,Unguwar da sukayi rayuwa a cikinta,Abusufyan ne ke driving ɗinsu,tana zaune a gefenshi tana latse latsen wayarta,Yayin da can ƙasan zuciyarta ke cike fal da fargabar zuwa anguwar,A hankali Motar ta shararowa da matsakaicin gudu,izuwa cikin unguwar bai direta a ko'ina ba sai a ƙofar gidansu,don bai manta da kwatancen gidan ba,duk da yaɗan so ya ruɗe saboda sabbin gine ginen dake a wurin,kasa fitowa sehrish tayi daga cikin motar,Saboda yanayin da tashiga,ta tsani yin toxali da unguwar,Saboda bata son duk wani abu da zai tuna mata rayuwarsu ta baya,


Fitowa abusufyan yayi daga cikin motar ya zagaya,ya bude mata ƙopar,"Daughter,mun ƙaraso fa,"jiki asanyaye ta fito daga cikin motar,yayin da idanuwanta ke cike tab da kwalla,A wani slow ta wurga kwayar idonta akan gidajensu,Ginin ya tsufa sosai,duk fentin ya ƙoƙe,ya gajarce,An garƙame gidan da ƙaton ƙwaɗo,duk yayi tsatsa,da alama anjima ba'ayi amfani da gidan ba,mayar da idanuwanta tayi akan gidansu maman sadeeq,A rufe yake gidan da makulli,Gidan ya tsufa shima Amma bai kai gidansu tsufa ba,saboda an canza mashi fenti,


Hawaye ne suka soma shararowa akan fuskarta,juyawa ta ɗanyi tare da kallon abusufyan dake tsaye,jikinshi duk yayi sanyi,Saboda tunawa da wasu abubuwa da suka faru a rayuwarshi,

  Mutanen dake kai komo acikin Layin nasu sai faman leƙensu sukeyi,musamman ƴan yaran anguwar,

  "Daddy,Kamar basu nan fa,naga gidan a rufe,"

  Uncle yace"Bari na samu yaro na tambayeshi,Muji ko sun tashi ne,"

  Yana ƙoƙarin rufe bakinshi,Yaji anyi mashi sallama ta bayanshi,Muryar wani dattijo ne,juyawa yayi tare da kallon mutumin,tsoho ne amma ba irin tukuf ɗinnan ba,jikinshi na sanye da koɗaɗɗen yadi,ƙafafunshi na sanye da wasu siɗaɗdun silifas duk sun fita hayyacinsu,kamar mahaukaci,

   Da sauri abusufyan ya miƙa mashi hannu donsu gaisa,

 Dattijon ya maƙe hannunshi tare da cewa"Haba Alhajin Allah,baka ga yadda hannuna yake ba duk datti a haka zaka gaisa dani,"

  Murmushi abusufyan ya sakar mashi,"dan Allah kada ka hanani gaisawa dakai,"

  Mika mashi hannun tsohon yayi suka gaisa,Sannan yace"bawan Allah,ban ta6a ganinka acikin unguwar nan ba,Kuma da alama kamar wani ku ke nema ko"?

  abusufyan yace"ƙwarai kuwa,wannan Ƴa tace,Munzo daga abuja ne,Muna neman..umm....."bai ƙarasa maganar ba,saboda ya manta da sunan mutumin,

  Sehrish ce ta ƙarasa mashi maganar"Malam nura muke nema,malamin makarantar islamiyya,"

  Dattijon yace"Ae nan ne gidan shi,Sae dai kash,Sunyi tafiya zuwa kankia wurin jana'izar Wani kawunshi daya rasu,"

  Jin haka yasa yanayin fuskar abusufyan ta ɗan canza,zuwa damuwa,

  "Amma,tun yaushe suka tafi"?

  Dattijon yace"tun makon daya gabata,Amma jiya munyi waya dashi ya sanar dani cewa Yau ko gobe zasu dawo,"

  Ba ƙaramin daɗi suka ji ba,don har sai da abusufyan ya ɗanyi murmushi,

  Hannu yasa cikin aljihunshi ya zaro kuɗi sababbin ƴan dubu dubu kusan dubu goma sha biyar ya miƙa ma dattijon,

Washe baki tsohon yayi tare da sanya hannu biyu ya kar6i kuɗin,tare da cewa"yalla6ai kamar ka sani wlh yau gidana da yunwa muka tashi,yara sai kuka sukeyi,Hakanan na gaji da zama cikin gidan, nace bari na fito na nemi na abinci,Ashe arziƙi ne ke kirana,Allah na gode maka,da ka haɗani da wannan bawan naka,Ya Allah kamar yadda ya farantamun rai,kaima ka faranta mashi nashi,ka biya mashi buƙatunshi na alkhairi,'yana addu'ar hada ƴar kwalla akan fuskarshi,

   Atare suka dinga haɗa baki suna Amsa mashi"ameen ameen,

  Abusufyan yace"baba taimakon da zakayi mana,idan sun dawo dan Allah ayi gaggawar sanar damu,Bari na baka lambar wayata,

  Ya ƙarasa maganar tare da zura hannunshi cikin aljihun wandonshi ya ɗauko wayarshi,

  Hannu dattijon yasa,a gaban aljihun rigarshi,Ya curo ƴar ƙaramar wayarshi tecno,taji jiki duk tafita hayyacinta,miƙa ma abusufyan wayar yayi"kar6inan yaro,sanya mun numbarka,kayi mun saving ɗinta da sunan Mai mutunci,Zanfi ganewa,Da zarar sun dawo in sha Allah,bi'iznil lahi,koda ƙarfe ɗayan dare ne zan kira in sanar dakai,"

  Murmushi suka saki gaba ɗayansu,kar6ar wayar abusufyan yayi,madannan jikinta duk sun nutse ciki,daƙyar ya samu ya rubuta mashi numbar,yayi mashi saving da Mai mutunci,Sanna ya mayar mashi da wayar"Gashi baba,mun gode sosai,Sai naji ka,Allah yasa adace,"

  Tsohon ya amsa mashi da ameen ameen,ae tunda ka farantamun raina,Kaima sai Allah ya faranta maka naka,har addu'a sai nayi maka idan nayi sallah,

  "Ina godiya sosai,"ya karasa maganar tare da ruƙo hannun sehrish suka shige cikin mota,key yayi ma motar,a hankali yayi reverse,tare da karya kwana,da gudun gaske ya fuce daga cikin unguwar,

  Nasarawa suka koma,a bakin gate din gidan ya sauke sehrish,Saboda zuwa masallaci,An fara kiran magrib,Miƙa mata key ɗin gidan yayi"kar6i nan,ki rufe gidan da kyau,Bazan dawo da wuri ba,Saboda inaso naje nayi mana siyayyar kayan abinci,dana amfani,"_

  "Toh daddy adawo lafiya"tasa hannu ta kar6i key din,kafin ta juya ta nufi cikin gidan,tsayawa yayi acikin motar yana kallonta,har saida ta 6ace ma ganinshi,ya tabbatar da ta rufe ƙopar gidan,Sannan ya tashi motar ya fuce,


   A 6angarensu Aunty babba kuwa,basu isa Enugu ba sai wuraren ƙarfe sha ɗaya na dare,Sunsha uwar tafiya,ba ƙaramin jiki suka ji ba,Acikin garin suka kama ɗaki a hotel,Tunda suka shiga ɗakin,kowaccensu ta baje saman gadon ɗakin,suka shiga sharar bacci kamar wasu matattu,Ga uwar yunwa na cinsu,sai da sukayi bacci mai isarsu,Kafin suka farka neman abunda zasu sama cikinsu,Oder sukayi aka kawo masu lafiyayyan abinci,kamar wasu kuraye haka suka tasarwa abincin suna Ci,Sai da suka ci suka ƙoshi,tukunna suka koma saman gadon,Suka dasa wani sabon baccin,ba tunanin yin sallah,a ƙagare suke washe gari yayi su wuce cikin dajin,

  

*Boss Bature*


   ❤🤍❤


Har Wuraren ƙarfe 12,Abusufyan bai dawo cikin gidan ba,gashi yabarta ita kaɗai,da farko bata damu ba,falo ta dawo ta zauna saman sofa,daya ke akwai nepa,hasken globe ya gauraye ko'ina,hannunta na ɗauke da littafin oummansu tana karantawa,Kalaman soyayya ne acikinshi,a cikin drawer ta samu littafin,Wani page ta buɗo acikin littafin Sunan oummansu ne akai dana Ya sayyadi,Aikuwa rai a6ace ta sanya hannu ta yage takardar tare da yin wurgi da ita,Mayar da hankalinta tayi sosai akan littafin tana karanta love messages ɗin dake aciki,da zarar taga wanda ke ɗauke da sunan ya sayyadi,jikinta har rawa yake yi wurin sanya hannu ta yage shi,


Tana cikin wannan karance karance,kwatsam!Aka ɗauke da wutar nepa,nan take duhu ya gauraye ko'ina,babu haske ko misƙala zarratin,gashi ta baro wayarta saman drawer cikin ɗakin,Sanin kanku ne sehrish muguwar matsoraciya ne,Tuni ido ya raina fata,Hankalinta yayi mugun tashi,jikinta ya shiga yin kerma,kamar gunki haka ta ƙame a zaune ta gaza motsawa,tana cikin wannan yanayin na tashin hankali,Tajiyo takun takalmin mutum,A matukar tsorace ta shiga ambaton sunan Daddynsu da ƙarfi"Daddy!daddy!dan Allah kana ina,nashiga uku,'

  Gabanta ne ya fadi lokacin da ta tuna cewa,daddynsu da Motarshi ya fita,da ace shine ya dawo cikin gidan to tabbas zata ji sautin ƙarar shigowar motarshi,

   Wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,jin motsin mutumin na tunkarota,a razane ta saki littafin dake a hannunta,ta miƙe daga saman sofa ɗin tashiga ja da baya,tana tafiya saɗaf saɗaf,hawaye duk sun wanke mata fuskarta,zuƙunnawa tayi ta soma yin rarrafe a hankali tana ƙoƙarin gano ƙopar ɗakin oummansu,cikin rashin sani takai hannunta saman wani gwangwanin maltina,aikuwa ya bada wani irin sauti rakwakwas,a gigice sehrish ta miƙe,gudu gudu sauri sauri,ita kanta batasan inda zata tunkara ba,Unfortunately tayi tuntu6e da wani abu,gaba ɗaya ta tafi zata faɗi ƙasa,ta saki wata irin razananniyar ƙara,

  Sai dai kafin takai ƙasa,Taji an damƙi qugunta,kwakkwaran ruƙo akayi mata,kafin aka janyota da ƙarfi,ta faɗa saman ƙirjin mutumin,koma waye wannan ba ƙaramin mutun bane,ƙarƙarfan gaske,

  Tashin hankali domin son sanin wanene wannan mutumin,Mu haɗu gobe inda rai da lafiya,In Allah yasa muna da rabon ganinta kenan



💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐

*_INFECTION BABBAN CIYO NE_*


Ciyon da yake shiga tsakanin ma'aurata ya hana masu zaman lafiya. Da kwanciyar hankali a zamantakewarsu ta aure , ciyo ne da yake kassara martaban mace harma da mazan Kansu , ciyo ne mai hadarin gaske Wanda duk take dashi to ba ita ba jin dadin aure , saboda yana dauke ni'imar mace gaba daya yana hana mace jin sha'awar mijinta yana saka ciyon Mara mai tsanani idan yayi yawa , Wanda zuwa gaba yake hanawa mace daukar ciki. Ko kuma yawan 'barin ciki  Sannan duk abunda mace zatayi domin gyaran kanta to bazai mata wani amfani ba saboda wannan ciyon wannan zaisa mace taga tana ta faman shan maganin mata amma baya mata aiki, 


*KADAN DAGA ALAMOMINSHI*

Bushewar gaba

K'aikayin gaba

Fitar kuraje agaban mace

Fitar farin ruwa mai kamar madara ko mai kamar majina 

Ko fitar ruwa mabanbanta kala 

Rashin sha'awa 

Rashin jin dadin kwanciyar aure 

Yana haifar da budewar gaba,

Ciyon Mara da sauransu ,


wannan yasa mukazo maku da sahihijn 

maganin sanyi wato infection yana wanke duk wani dattin Mara yana maganin sanyi sosai tareda saukowa mace niima maganin 3in1 ne na sha da sabulun tsarki da Wanda zaki dafa kina tsarki dashi , akwai kuma maganin sanyi na maza daban Wanda yanada kyau duk wacce ta siyama kanta to ta siyawa mijinta don kar ayi badi babu rai don ko kinji sauki in shi mijin yanada zai iya shafamaki .......*

07069711327 mmn Yusuf mai kayan mata sokoto🥰🥰

   

 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*







Am really sorry,🙏



Tayi matuƙar tsorata dashi,kasa ɗagowa tayi daga jikinshi,jikinta sae kerma yake yi,lokaci guda daddaɗan ƙamshin turarenshi ya daki hancinta,nan take ta ruɗe tana ƙoƙarin gano a ina tasan ƙamshin nan,duk duniya mutun ɗaya ne ta sani mai irin wannan ƙamshin turaren mai matuƙar ratsa zuciya,Ruɗewa tayi tana so ta canko wanene,kuma tana kokwanton anya hakan zai iya kasancewa gaskiya?zame hannayenta tayi daga saman waist ɗinshi da ta ruƙe,ta matsar dasu har izuwa mid back ɗinshi,Gabanta ne ya faɗi rass jin ta shafo doguwar sumar kanshi,muryarta na kerma ta furta sunanshi"BABBAN YAYA..!"tana ambaton hakan,Wutar ɗakin ta dawo nan take haske ya gauraye ko'ina tamkar da Rana,zuba mashi ido tayi tana kallon kyakkyawar fuskanshi wadda ke sanye cikin face mask black colour,Launin rigar jikinshi ya lumshe idanuwanshi,slowly ya ɗan waresu akan fuskarta,Ae tana ganin blue eyeballs ɗin nan nashi,Ta ƙara tabbatar da hasashenta,abun yayi mugun ɗaure mata kai,kallonta yake yi from head to toe,fuskarta duk tayi zufa saboda tsabar firgicin da ta shiga,ga hawaye jaga jaga a fuskar,duk don saboda an ɗauke da wutar nepa ta ganta acikin duhu,


Sai faman sauke ajiyar zuciya take yi,hankalinta har ya kwanta da ta tabbatar cewa shine,Tayi tunanin wani mugunne yazo don ya cutar da ita,tayi farin cikin ganinshi sosai kamar tayi ihu,Amma ta wani 6angaren tsoran hukuncin da zai yanke mata take yi,duk a tunaninta yazo ne don ya hukuntata,tunda ya bata Command taƙi bi,

   Ganin irin kallon da yake yi mata ne yasa tayi saurin sunnar da kanta ƙasa,tana wasa da yatsun hannunta,

    Hanky ya zaro daga cikin trouser pocket ɗinsa,Ya miƙa mata tare da cewa"Take it,"hannu tasa ta kar6a,ta shiga goge fuskarta sosai,

   "In kawo maka ruwa kasha"?cikin sanyin murya ta ambaci hakan,

   Girgiza mata kai yayi alamar a'a,kafin ya wuce cikin falon,Ya zura hannayenshi biyu acikin aljihun wandonshi,

  juyowa tayi tana kallonshi,A dai dai lokacin suka jiyo sallamar Abusufyan"Assalamu Alaikum",

   Amsa mashi su kayi da"Wa'alaikum salaam,"

  Shigowa cikin falon yayi,hannunshi ruƙe da key ɗin Motarshi,

  Koda yayi arba da Sgr,cike da mamaki yace"Rafayet!Ashe dagaske ne,Abban ku ya sanar dani cewa,zai yi wa Omar magana ko shi ko kai wani yabiyo bayanmu don yaso yana nan muzo dashi,Banyi tsammanin cewa kaine zaka zo ba,Yanzu kawai ina karyo kwana da motata naga sojoji zagaye da gidan nayi ta mamaki cikin raina,Gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba," ya karasa maganar a yayin da yake ƙoƙarin rungumarshi,da alama Abusufyan ba ƙaramin daɗi yaji ba,Sai murmushi yake yi,

   "Na same ku lafiya,"?

"Lafiya lou Alhmdllh,Naje masallaci ne,na biya naga wani Abokina daga can kuma na wuce wani store zanyi mana siyayyar kayan abinci,Inata fargabar nabar yarinya ita kaɗai acikin gida",

  Sgr yace"nayi mamakin ganinta ita kaɗai zaune acikin gidan,time ɗin dana shigo kuma bansan meya faru ba,duhu ko'ina,so sai daga bayane hasken ya dawo,"

  Abusufyan yace"Ae ɗaukewa su kayi da wutar ne,yanzu nima ina kan hanyar dawowa naga sun dawo da ita,"

  wurga idonshi yayi kan Sehrish dake tsaye hannunta ruƙe da hanky dinsa,ta kammala goge hawayen,

  "Daughter,zonan mana,"ya kirata da hannunshi,wurinsu tazo ta tsaya tana facing din Abusufyan,

   "Faɗamun meya faru?bayan na tafi"?

 murmushi ta ɗan yi,batare da tace komai ba,

   Mayar da idanuwanshi yayi kan Sgr yace"Amma dai ba  nan zaka kwana ba ko"?

   "I will spend the night here,"

Abusufyan yace"ba ka ga yadda gidan yake ba ne?Ni nasan bazaka iya bacci acikinsa ba,Yakamata ka wuce hotel kawai,ina ganin zaifi maka daɗin zama,"

  Girgiza mashi kai yayi"No,i wanna stay here," gyaɗa kai abusufyan yayi tare da kallon sehrish yace

  "Sehrish ki kaishi bedroom ɗin da kika gyara,ya zauna acan,Amma dai banso ba wlh,Don nasan cewa zaka takura sosai,Ga zafi ga sauro duk da na siyo maganin sauron,Amma bana tunanin zai iya dakatar da saurayen dake acikin gidan nan,"

  Amsa mashi tayi da toh,Sannan ta juya tare da kallon Sgr tace"Mu shiga ciki,"

  Gaba tayi yabi bayanta,daƙyar yake iya taka kasan palourn,saboda daudar dake a wurin duk da sun gyara shi,

  Shiga cikin bedroom ɗin su kayi atare,Wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙarewa ɗakin kallo,

  "Kana bukatar wani abu,in kawo maka,"

   "No need"ya ambaci hakan a yayin da yake zaro wayarshi daga cikin aljihun wandonshi,

"Sehrish!"Abusufyan ne ya kwala mata kira,da sauri ta juya ta fita daga ɗakin,

  Komawa tayi cikin palourn A tsaye ta same shi,Ga kayan da yayi masu siyayya hada gass cylinder saboda yin girki,Sojoji ne suka shigo dasu,A cikin buhu guda biyu,sae cylinder ɗin da suka ajiye nan,

  Ƙarasawa tayi wurinshi,"Gani Daddy,"

   "Kunyi magana dashi ya fada maki ko yana buƙatar wani abu?"

   "a'a bai bukaci komai ba,"

Shiru Abusufyan ya dan yi,ganin damuwa akan fuskarshi yasa tace"Meya faru daddy," hannu yasa ya ɗan shafa sumar kanshi kafin yace"Daughter,bazai iya kwana acikin gidan nan ba,Ni nasan waye rafayet,Wlh nayi mamakin ganinshi banyi tsammanin cewa shi zaizo ba,Kalli fa gidan nan ki gani,babu wani shiri da mukayi,yanzu da zarar an ɗauke da wutar nepa,Shikenan zafi zai rufe mu,kuma ko kaɗan baison zafi,Gashi da ƙyankyami toilet idan bana bedroom ɗinshi ba,baya shiga na kowa,Kuma dole ya buƙaci yin wanka,Ni bansan ya zamu ƙare dashi ba,"

  Murmushi Sehrish tayi,ita kanta ta jinjina ma ƙarfin hali irin na Sgr,yadda yake da ƙyanƙyamin nan,Amma a haka yace zai kwana acikin gidan,Koya zasu ƙare,?

  "Daddy,kada ka damu,tunda yaji ya gani,zai kwana anan ɗin ka ƙyaleshi kawai,"

  Gyaɗa kai Abusufyan yayi tare da cewa"Shikenan kawai,Yanzu dai bari na shiga da kayan abincin nan kitchen,"

  Yayi maganar tare da sa hannu ya dauki buhu ɗaya,hannu tasa itama ta kama ɗayan buhun,taja shi izuwa cikin kitchen,bayan sun kammala kwashe kayan sunkai kitchen,

  Ta dube shi tare da cewa"Zan iya dafa mana ko taliya ce?

  Abusufyan yace"Kina jin yunwa ne"?

  "A'a,bana ji,saboda kai dama zan dafa,naga bamu ci Dinner ba,

  "Ki barshi kawai,akwai kayan tea dana siyo da bread,idan kina jin yunwa ki haɗa ki sha,Yanzu dae bacci nake ji,"

  Yayi maganar yana hamma,

"A ina zamu kwana"tayi tambayar tana kallonshi,

"Ki wuce inda mijinki yake mana,Ni zan kwana a palour ne,Ki dauko mun bargon da zan ɗan shimfiɗa in akwai"

  "Toh" ta amsa mashi tare da

  Kama hanya ta fuce daga cikin kitchen ɗin,Shima fitowa falon yayi ya tsaya a tsaye yana jiranta,


Lokacin da ta shiga bedroom ɗin,A kwance ta samu Sgr yana bacci ya ƙure fankar ɗakin har ƙarshe,iska ta ko'ina,hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,wurin wardrobe ta wuce ta sanya hannu ta buɗeta,daga gida na kasa blanket din suke tare da bedsheet,hada mosquito net,

   Bargo ta dauko mashi,Sannan ta koma falon,har lokacin Abusufyan na atsaye,yana jiranta,

   Ƙoƙarin shimfiɗa mashi tayi,da sauri yasa hannu ya kar6i bargon tare da cewa"Yawwa My Own Daughter,nagode sosai,"

"Sae Allah yakaimu Daddy,"fuskarta asake tayi maganar,

  "Allah ya kaimu lafiya,take care of my son,don't allow even one mosquito to bite his skin,If not ranki zai 6aci,"cike da zolaya yayi maganar,

  Fashewa tayi da dariya,tare da juyawa tana faɗin"don't worry daddy,In sha Allah i will look after him,very well,"

  Gyara kwanciyarshi yayi saman sofa ɗin,cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba dashi,

  Komawa cikin bedroom ɗin tayi,bedsheet ta dauko acikin wadrobe ta shimfiɗa a kasa,sannan ta matsa wurin gadon,ta ɗauko pillow guda ɗaya ta ajiye shi saman zanin gadon,

   Wurin switch taje,ta kashe light ɗin ɗakin,Nan take duhu ya gauraye ɗakin amma ba sosai ba,akwai hasken ƙwan dake a falo guda daya da aka bari akunne,ya ɗan haska ɗakin nasu,

    Moving tayi izuwa wurin gadon inda Sgr ke kwance yana bacci,addu'o'i ta shiga karantowa tana ɗan tattofa mashi,bayan ta kammala ta koma saman shimfiɗar da tayi,ta gyara kwanciyarta,sai da itama ta karanta addu'o'in tabi ta shafe jikinta kafin ta rufe idanuwanta,bacci 6arawo yayi awon gaba da ita,


Around 1:30 na dare,Ƴan nepa suka yi tsiyar tasu da suka saba,Tashin hankali,Ƴan sakanni da ɗauke wutar fanka ta tsaya cak,Wani irin zafi ya fara ziyarta ɗakin,Sai ga mutanen da gudun gaske sun fara kwararowa cikin ɗakin,Buuuuuuuuuu da wani irin kuka mai sautin gaske,tun yana juyi saman gadon yana kai hannu yana buge sauron dake ƙokarin attacking ɗinshi,har ya fara ƙokarin farkawa,Wata irin zuface ta soma tsastsafo mashi ajikinshi,Sharkaf ya jiƙe,tuni numfashinshi ya soma kokawar fitowa daga hancinshi,kamar an toshe shi,A firgice Sgr ya farka yana faman zazzare blue eyes ɗinshi,Hankalinshi yayi mugun tashi,arayuwarshi ya tsani sauro ko miskala zarratin baisan halittar nan,bai taso a inda ke akwai taba,Amma yasanta sarai a matsayinshi na Dr yasan irin cututtukan da take haifarwa,Gashi ya tsani duk wani abu da zai naƙasa lafiyar jikinshi,tuni jikinshi ya soma kerma,hannu yasa ya ɗebe rigarshi gaba daya,ya shiga kokawar korarsu daga kusa dashi bayan ya kunna fitilar wayarshi dakin yayi haske,ji kake fass fass!kaff kaff!!haka ya dinga bubbugesu,duk yabi ya ruɗe,


Cikin bacci Sehrish ta dinga jin muryarshi yana faɗa da sauraye yana fadin"Don't come close to me!Am gonna shoot you"tashin hankali Sgr fa ya zauce da alama,duk sun rikitashi sun mayar dashi ƙaramin mahaukaci,Idan ya sanya riga bala'e biyu,ga zafi ga sauro,idan ya cire rigar kuma Sauraye zasu sha jini,bai da choice,

  A firgice ta farka,hankalinta a matukar tashe ta mike daga kwancen da take saman bedsheet ɗin,Wurin shi ta ƙarasa,yanayin da ta ganshi gaba ɗaya ya rikice ba ƙaramin tausayi ya bata ba,gaba daya yabi ya susuce ya hargitsa sumar kanshi,

   "Ya Rafayet,"ta ambaci sunan shi da wata irin kasalalliyar murya ta mai bacci,ƙoƙarin hawa saman gadon tayi don ta taimaka mashi ta kore mashi su,kafin su san abunyi,ae tana hawa saman gadon,ya ƙanƙameta ya rungumeta sosai,A faɗace yake ce mata ta kori saurayen su fita su bar ɗakin,ko ya harbesu da bindiga,tuni taji hawaye sun cicciko mata acikin idanuwanta,tsananin tausayinshi ne ya kamata,dama sai da Uncle yace bazai iya kwana a cikin gidan ba,Amma yace zai iya,wani iko na Allah,babu halittar da Sgr ke jin shakkarta irin sauro,Gashi Yau Allah ya haɗasu,ƙananun ƙwari sun firgita babban kwaro,Shaggu sun ga Farar fata,burinsu kawai su tsotsi jininshi,Dama abu tubarkalla masha Allah,

  gaba daya hannayenta na asaman bayanshi,ya cusa kanshi a kirjinta,numfashin shi da wani irin huci yake fita,

   Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Ya rafayet,dan Allah ka natsu,zanje wurin daddy na kar6o mana maganin sauron,"tayi maganar tana ƙoƙarin janye jikinta daga nashi,ƙin barinta yayi,yaƙi yarda ta motsa daga jikinshi,gani yake kamar in tabar wurin Saurayen zasu shanye mashi jinin jikinshi ne,

  Ganin yaƙi sakinta yasa takai hannu ta ɗauki rigarshi da yayi wurgi da ita gefe saman bedmattress ɗin,Ruƙo rigar tayi a hannunta,ta shiga kore mashi saurayen dake akewaye dasu,


Duk wannan budurin da akeyi,Abusufyan na kwance saman doguwar kujerar,Shi kanshi zafi ya ishe shi ga saurayen a kewaye dashi,Amma hakan baisa ya farka ba,sae faman juyi yake yi,

   (Allah sarki,haka talaka ke fama,da zarar an ɗauke da wutar nepa lokacin zafi,Ya rasa inda zaisa kanshi,ga sauro ga zafi,yayin da masu kuɗi ke can suna shan sanyin A.c,a lokacin zafi,idan kuma na sanyi ne su kunna room heater,Talaka kuma Ya hura garwashin wuta😥)


Jikinshi sae kerma yake yi,Duk da ya ɗan ji sauƙin Zafin saboda fiffitar da take yi mashi tana kore mashi saurayen,ko gajiya bata yi baiwar Allah,Haka ta hana idonta bacci,ta zauna tana kula dashi,sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi,har lokacin yana manne da ita,

   A hankali bacci yayi awon gaba dashi,kamar wani jinjiri,gyangyaɗi ta fara yi,tana fiffitar bacci na fisgarta,idanuwan nan sunyi jawur dasu,taƙi bari bacci ya ɗauketa,saboda gudun halin da Sgr zai shiga,idan ta daina yi mashi fifitar,

   Tafin hannunta ta sanya asaman fine face dinsa,ta shafa gefen fuskarshi har izuwa saman pink lips ɗinshi,kafin ta mayar da hannun saman dogon wuyanshi,fatar wurin tayi haske sosai mai matukar jan hankali,la66anta takai asaman cheek ɗinsa ta manna mashi kiss,ɗagowa tayi tare da aza tsinin hancinta cikin sumar kanshi,daddaɗan ƙamshin dake fitowa daga wurin ta dinga shaƙa,tana faman lumshe idanuwanta,da hannu ɗaya take yi mashi fiffitar,


  Tana cikin wannan yanayin,ta galabaita sosai saboda baccin da take ji,Ƴan nepa suka dawo da wutar,a hankali fankar ta soma jujjuyawa,nan take iska ta karaɗe ko'ina na bedroom ɗin,wani irin farin ciki ne ya ratsa zuciyarta,

   "Allah na gode maka,da suka dawo da wutar nan,nayi farin ciki sosai,"

   Lokaci guda Mosquitoes ɗin nan kowa ya kama gabanshi,saboda wutar mai ƙarfi ce,iska duk ta kaɗa shaggun,

  A hankali ta lalla6a ta janye Sgr daga jikinta,ya koma saman mattress ɗin,ta dauki wayanshi ta kashe fitilar ta daura ta saman bedside drawer,gefenshi ta kwanta,tare da jan bargo ta lullu6e jikinta,banda nashi saboda ta lura dashi baisan Zafi ko misƙala zarratin,


*Boss Bature*


Wuraren Sallar asuba,Abusufyan ya farka,Saukkowa yayi daga saman Sofa ɗin,yana faman murza wuyanshi,Wurin yayi mashi zafi saboda kujerar tayi mashi karanta,ya takure kansa sosai,Ƙopar ɗakinsu yaje tare da sanya hannu yana ɗan kwankwasa ƙopar,

   Sehrish ce ta farka,saukowa tayi daga saman gadon,sai da ta fara kunna hasken ɗakin,sannan taje ta buɗe ɗakin,

  "Daddy,"ta ambaci sunanshi,

"Na'am,Daughter,"

"Wlh jiya munji jiki daddy,dama haka Yaya Rafayet ke da jin Zafi? Ga sauraye suka takura masa,jiya daga ni harshi bamu samu isasshen bacci ba,"muryarta tamkar zata yi kuka tayi maganar,

"Ae dama saida nace mashi,Yaje hotel amma yaƙiya,banji daɗi ba gaskiya,duk ban shirya ma zama gidan ba,dana sani tun kafin muzo,nasa an gyara shi,An sanya generator da A.C an kuma yi mashi feshin maganin sauro,Amma ban yi tunanin hakan ba,Wllh koni jiya naji jiki,"

  Ya ƙarasa maganar tare da cewa"Yanzu ya yake?Yana lafiya kuwa,"?yayi tambayar yana jiran amsarta,

  "Ya samu bacci,da suka dawo da wutar,bansani ba ko yana lafiya ko kuwa,Still dai bacci yake yi bai farka ba,"

  Jinjina kai Abusufyan yayi tare da cewa"je ki taso munshi,Yazo mu tafi masallaci,Lokacin salla yayi,"

  "Toh daddy"tayi maganar tare da juyawa ta shige cikin ɗakin,


Yadda tabarshi haka ta same shi,kwance yana bacci,

  Zama tayi daga gefen gadon,sannan ta ambaci sunanshi"Ya Rafayet"!shiru bai motsa ba,sake kiran nashi tayi"Babban yaya ka tashi,time ɗin sallah yayi,"_

  Ganin yaƙi motsawa yasa takai hannunta saman damtsen hannunshi,ta ɗan bubbugashi,dogon numfashi yaja a hankali ya soma ƙoƙarin buɗe idanuwanshi,

  Biji biji ya fara ganinta,kafin idanuwan nashi suka washe,

  "Ankira sallah,Daddy yana jiranka a palour,"

  daƙyar ya iya furta mata Okey,miƙewa yayi daga zaune,yakai hannu ya ɗauki shirt ɗinshi,Ya zurata ajikinshi,Hada ido su kayi da ita,da sauri ta kawar da idonta gefe guda,miƙewa tayi daga tsaye,ta bashi wuri don ya wuce,

  Saukowa yayi daga saman gadon,Ya kama hanyar fita daga ɗakin,

  "Adawo lafiya," 

"Okey,"yasa kai ya fuce,


Bayan fitarshi,toilet ta shiga,ta ɗauro alwala,bayan ta fito ta ɗauko darduma ta shimfiɗa,a natse ta kabbara Sallah,tana gama yin sallar ta ɗebe hijabin ta ninke dardumar ta turasu cikin wadrobe,

  Wani irin bacci take ji acikin idanuwanta,saboda jiya bata samu isasshen bacci ba,Cire doguwar rigar jikinta tayi tare da sagala ta saman Murfin wardrobe ɗin,

  Toilet ta wuce,Saboda jikinta duk babu daɗi,After some minutes ta fito jikinta sanye da Brazier,tare da Short,farare,ba ƙaramin kyau su kayi mata ba,dama dasu ta shiga wankan,

   Tunda ta fito kuma,baccin ya ya ci gaba da addabarta don ba karamin dadin jikinta taji ba,bata samu ta sanya kaya ajikinta ba,Saman gadon ta haye taja bargo cikin ƙankanin lokaci bacci yayi awon gaba da ita,bata ƙara sanin inda hayyacinta yake ba,


*Marshal Omar*


Yayi nisa a cikin baccin shi,yajiyo muryar Hosana tana raira mashi waƙa,

    _Wataran wata rana_

   _za'a kaika gidana_

    _matsayin mijina_

    _kaine madara na_

_na matsu!na matsu na matsu inga wannan rana_

Cike da jan faɗa take yin wakar hada matsawa saitin kunnanshi,Rai a matuƙar 6ace ya farka,tare da wurga mata uwar harara,tana zaune saman gadon tayi zaman cin tuwo,

  A faɗace yace"Hosana!bana hanaki shigomin bedroom ɗina ba?Meyasa baki jin maganata ne"

  Hura mashi hanci tayi tare da murguɗa baki tace"Haramun ne idan nashigo ɗakin ɗan uwana,?to idan ma haramun ne,Sai ka aure ni kowa ma ya huta,"

Hannu yasa tare da dafe kanshi,yana faɗin"Allahumma ajirni fi masibati,wa'aklif ni khairan minha,"

  A ƙule tace"Ya Omar,Ni ce masifar"?

  Banza yayi da ita bai tanka mata ba,

  Jin yayi shiru yana kallonta,yasa tace"haushina kake ji ko?to ka kashe ni mana kowa ya huta,"

  Yunƙurawa yayi tare da miƙewa daga zaune,yace"Meyasa kike mun haka ne?kin takurawa rayuwata Hosana,A haka kikeso na"?

  Turo baki tayi tana ɗan satar kallonshi,

  "Baki son farin cikina,kullum burinki ki addabi rayuwata kib hanani sakat,Zunubin me na akaita maki ne,"

   Ashagwa6e tace"Bakomai,"

  "Kinfi so ki ga hawaye na ko,"

Girgiza mashi kai tayi alamar,A'a,

Hannu yasa ya rufe fuskarshi yana raira mata kukan ƙarya,

  Nan fa hankalinta ya tashi,tabi ta ruɗe,

  "Ya Omar bazan ƙara zuwa ba,dan Allah kadaina kukan,yanzu zan tafi na barka,"jiki na rawa ta sauka daga saman gadon tana ja da baya baya tana faɗin"ka gani ko?tafiya zanyi,bazan ƙara dawowa ba,dan Allah ka daina kukan toh,"

  Ƙasa ƙasa ya dinga dariya batare da taji shi ba,har sai da ta fuce daga ɗakin sannan ya zame hannunshi aranshi yace"fitinanna,Allah yasa Daddy ya dawo cikin week ɗinnan zansa a ɗaura mana aure,At first night,zan koya maki hankali,duk wani hauka da kike ji asaman kanki saina sauke maki shi,"

  Yana maganar yana dariya,a yayin da yake saukowa daga saman gadon,jallabiya ce ajikinshi,toilet ya wuce,


Wuraren karfe 8,Sehrish ta farka da wata irin matsananciyar Yunwa,a gaggauce ta miƙe,ta ɗauko jallabiya ta zura a jikinta,kitchen ta wuce,batare da 6ata lokaci ba,ta ɗaura girki,bazata iya jure dafa abu mai wuyar dafuwa ba,Shiyasa ta ɗaura Indomie shaf shaf ta kammala dafuwarta,A cikin plate ta kwasota ta fito daga cikin kitchen ɗin,ta zauna a palour tana ci,sai lokacin ta shiga tunanin ko'ina su Uncle suka tafi?daga fita sallar Asuba har yanzu basu dawo gidan ba,yanke shawarar kiransu tayi idan ta kammala cin taliyar,asaman table tabar plate din da sauran taliyar,ta koma kitchen ta haɗo kakkauran Tea wanda yaji madara da bournvita,dawowa tayi falon ta zauna tana kur6arshi a hankali,


Tana cikin shan tea ɗin nan,taji dirar motarsu acikin gidan,Uncle Abusufyan ne ya fara shigowa cikin gidan,Miƙewa tayi da sauri tana fadin"Daddy,sannu da dawowa,"

  A gaggauce ya amsa mata"Yawwa Daughter,ɗaukko mayafinki mu tafi,dattijon nan ya kira ni a waya,badajimawa ba,"

  Jin haka yasa ta ajiye cup din hannunta asaman table ɗin gabanta,Jiki na rawa ta wuce ɗakin,jimm kaɗan ta dawo sanye da mayafi tayi rolling ɗinshi,hannunta ruƙe da wayarta,

  Shigowa cikin palourn tayi batare da 6ata lokaci ba,Abusufyan ya ruƙo hannunta suka fito waje wurin motarshi,Security ta gani suna tsaron gidan,tana ganinsu ta gane cewa mutanen babban yaya ne,

   buɗe motar tayi ta shiga,Abusufyan ya shiga ya zauna a mazaunin driver,tashin motar yayi tare da yin reverse ya karya kwana,da gudun gaske ya fuce daga cikin gidan,Kai tsaye suka haura saman titi,hannunshi har kerma yake yi saboda saurin da yake yi,burinshi kawai su ƙarasa cikin unguwar,

   "Daddy,ina yaya Rafayet ɗin?naga banganshi ba,"

  "Nabarshi a hotel,tun bayan da muka kammala sallar Asuba,Ni kuma na wuce gidan wani Old friend ɗina dake anan,Na jima acan,ina kan hanyar dawowa Dattijon ya kira wayata,Yake sanar dani cewa Malam Nura ya dawo"ya ƙarasa maganar adai dai lokacin da yake ƙoƙarin juya sitiyarin motar,Cikin unguwar suka shiga,a bakin bishiyar bedi yayi parking ɗin Motar cikin layin,tun kafin su fito daga cikin Motar suka hango ƙopar gidan a buɗe,bayan sun fito daga cikin Motar,Abusufyan ya daga hannunshi sama tare da cewa"Ya Allah kasa muji alkhairi!"

  Sehrish ta amsa mashi"Ameeen Daddy,"

  A ƙopar gidan suka tsaya,Abusufyan ya kwaɗa sallama,cikin sa'a suka ji an amsa masu sallamar tasu,Jimm kaɗan sai ga wani matashin saurayi dogo siriri ya fito daga cikin gidan,jikinshi na sanye da yadi,

  Miƙa ma Abusufyan hannu yayi suka gaisa,kafin yace"baƙi mukayi ne,"Abusufyan yace"Eh,baƙine,muna neman Malam nura ne,Allah yasa yana nan,"

  Tunda saurayin ya fito idonshi na akan sehrish,kallon sani yake yi ma fuskarta,ita kanta kallon nashi takeyi,kamar taso ta gane shi,da alama tasan shi tun yana da ƙuruciyarshi,Ranta ne ya bata cewar kodai Sadeeq ne ɗansu ya girma haka"!?

  "Da ace kun ƙara minti Biyar baku zo ba,da kun rasa shi,don kuwa yanzu yake shirin komawa Islamiyya,"

  Wani irin farin cikine ya lullu6e Abusufyan"taimaka kayi mana sallama dashi,". 

  "Toh,"ya amsa tare da juyawa ya shige cikin gidan,after some minutes ya dawo hannunshi ɗauke da tabarma,A cikin zauren gidan ya shimfiɗa masu ita,

   "Ku shigo daga ciki ku zauna,yanzun nan zai fito,"

  "Yawwa mun gode ƙwarai,"Abusufyan ne yayi maganar tare da ruƙo hannun Sehrish suka shiga zauren,A saman tabarmar suka zauna,Suna jiran tsammanin ganinshi,

  Wayar Abusufyan dake acikin aljihunshi ce ta soma ringing,da sauri ya zaro wayar,yana duba mai kiran nashi Sunan My first in~law ne,Amsa kiran yayi tare da kara wayar a kunanshi,

  "Uncle,A ina zan same ku"?Rafayet ne yayi maganar,

   Abusufyan yace"muna a hotoro,Amma kaɗan jira kaɗan zan tura maka da address ɗin gidan,Sai kazo,"

  Sgr yace"okey,I will be waiting,"

Rejecting call ɗin yayi,yana ƙoƙarin mayar da wayar cikin aljihunshi,Wani babban mutun ya shigo cikin zauren,bakinshi dauke da sallama"Assalamu Alaikum,"atare suka amsa mashi sallamar,yayin da suka bi shi da kallo,

  Daga ganin mutumin ya kwana biyu a duniya,ya manyanta sosai ya fara tsufa,Jikinshi na sanye da shiga ta musulunci,ta waɗanda suka amsa sunansu malamai,hannunshi na ruƙe da cazbaha,kanshi kuwa rawanine,A mutuncen shi yazo,

  Kamar yadda suke kallonshi shima haka yake kallonsu,yanayin kallon dayake yi masu kamar kallon sani ne,wuri ya samu agefen tabarmar ya zauna suna fuskantar juna,Shi dasu,

  Da sauri Abusufyan ya shiga gaisar dashi"ina kwana baba,mun same ku lafiya,"

  Fuskarshi asake ya amsashi lafiya lou,Alhamdulillah"

  Gaba daya hankalinshi na akan fuskar Sehrish,kallon ƙurulla ya shiga yi mata,nasan gano a ina yasan fuskar yarinyar,Sunnar da kanta ƙasa tayi tana wasa da yatsun hannunta,

   ɗauke idanuwanshi yayi daga kan sehrish ya mayar dasu kan Abusufyan yace"Ince dai lafiya ko?naji kunyi shiru baku gabatarmun da kanku ba,Gashi ni bansan ku ba,"

  Murmushi Abusufyan ya ɗan yi tare da gyara zamanshi,Atsanake ya soma kora mashi jawabi,

  "Ni sunana Abusufyan,Wannan kuma ƴa tace,Sunanta Sehrish,'

  Gabanshi ne ya faɗi rass,aɗan tuɗe ya maimaita sunan"Sehrish"kamar irin ya ta6a jin sunan,

  Cigaba da magana Abusufyan yayi"nasan baka gane ta ba,saboda sanin da kayi mata tun na ƙuruciya ne,Amma nasan ba zaka iya mantawa ba,Da ZAINABU ABU BUZUWA MATAR MAKWABCINKA YA SAYYADI,"

  Saboda tsabar kiɗima Malam Nura ya zabura tare da miƙewa tsaye yana kallonsu hankalinshi aɗan tashe yace"dan Allah kuyi mun bayanin su wanene ku?menene alaƙarku da zainabu abu da kuma sayyadi"?

  Miƙewa Abusufyan yayi yana ƙoƙarin kwantar mashi da hankali yace"pls baba,dan Allah ka koma ka zauna muyi magana atsanake,"

  Rai a6ace malam Nura yace"Idan maganar wannan fasiƙin mutumince ta kawoku to ku tattara kubarmin gidana!Banason ganinku,banason ganin duk wani abu daya shafe shi,ku fuce kawai tun kafin ranku ya 6aci a wurin nan "yana magana jikinshi na kerma saboda tsabar 6acin rai,

  Ganin yana ƙokarin korarsu yasa sehrish miƙewa tsaye cikin sanyin murya tace"Baban sadeeq,Ka manta da ƴan ukun zainabu abu da ta haifa"?

  Mayar da hankalinshi yayi sosai akanta yana kallonta,

  "Ni ɗaya ce daga cikinsu,nasan baka manta damu ba,Nice Sehrish ƴar uwarsu Jahad da Hosana"

   Cike da mamaki Malam nura ke kallonta,hannunshi na kerma ya nunata da ɗan yatsanshi daƙyar ya iya furta cewa"kek..ke..ƴar wurin zainabu abuce?

  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,tace"Ni ce SEHRISH Baban sadeeq,su jahad ma suna nan araye,"

  Wasu irin zafafan hawaye ne suka soma sauka akan fuskar malam nura,ruƙo hannunta yayi yana kallonta,la66ansa sae kerma sukeyi,yayi matuƙar mamaki ganin yarinyar,bai ta6a tsammanin cewa yaran zasu rayu ba,abun yayi matukar daure mashi kai,

  Cikin shessheƙar kuka yace"Allahu akhbar!Wai dagaske ƴa'ƴan abu suna araye a doron duniyar nan?Dagaske ne abunda idona suke gane mun kuma suke jiyomun!Ya Allah kasa ba mafarki nake yi ba,"kuka sosai ya fashe dashi,duk yabi ya ruɗe bawan Allah,

  Kama hanyar shiga cikin gidan yayi,yana kwaɗama maman sadeeq kira"Murja!!murjanatu!kina inane kizo dan Allah,Ki ganemun wannan abun al'ajabin,Yau gani ga jinin zainabu abu har cikin gidana,Abun da muka daɗe muna jira,yau Allah ya amsa addu'armu"

  Jin wannan maganar ta Baban sadeeq yasa Maman sadeeq ta miƙe zumbur daga zaunen da take saman sallaya,buguzun buguzun ta faɗo cikin zauren,turus ta tsaya abakin zauren tana ƙarewa Abusufyan da Sehrish Kallo,

  Malam nura yace"kin gani ko?Yaran nan sun rayu,Wahala batasa sun mutu ba,dama nasha faɗa maki cewa Allah yana tare dasu a duk inda suke,Allah shi zai kula da abunshi,Yau dai maganata ta tabbata,kalli ki gani wannan yarinyar ƴar wurin zainabu abu ce fa,Sehrish ce"yayi maganar yana nuna mata sehrish,

  Hannu murja tasa ta daki ƙirjinta tare da Ambaton sunan Sehrish da ƙarfin gaske,

  Da gudu sehrish ta ƙarasa wurinta suka rungume juna,tare da fashewa da wani irin matsanancin kuka,kamar ransu zai fita,

  Tuni idanuwan Abusufyan sun cicciko da kwalla,shi kanshi baisan lokacin da hawaye suka wanke mashi fuskarshi ba,

  Gaba dayansu sun shiga cikin wani irin yanayi na ban tausayi,kowa da abunda yake tunawa acikin ranshi,

  Cikin shessheƙar kuka Maman Sadeeq ta dafa kafaɗun Sehrish tana faɗin"Ashe rai kanga rai!Rishi kece kika girma haka?lallai Allah Al musawwir ne,Kalli yadda rayuwa ta sauyaki,Ban manta lokacin da kuke rayuwa a wulakance ko takalma babu a kafafuwanki,Ya Allah na gode maka daka nuna mun wannan ranar,Yau gani ga ƴa'ƴan aminiyata zainabu abu,Wayyo Allah farin ciki,"zubewa ƙasa tayi ta fuskanci gabas tayi sujjada tana kuka tana godewa Allah,hakan ba ƙaramin ta6a masu zuciya yayi ba,

  Sun ɗauki tsawon lokaci suna wannan koke koken,kafin daga bisani komai ya lafa,Saman tabarmar suka koma suka zauna,cike da jimami,kowa yayi shiru na ɗan wani lokaci,

Kafin Abusufyan ya soma magana"Baba waɗannan ƴaran ƴa'ƴana ne,bana sayyadi ba,Ya yaudaremu ne gaba ɗayanmu ya auri abu da cikina,batare da saninmu ba,Wannan shine silar duk wani abu daya faru a rayuwarsu...."

  Tunkan ya ƙarasa maganar Baban sadeeq yace"Dama najima ina zargin cewa,ƴan ukun nan bana shi bane ashe dagaske ne,Ya Allah kayi mana maganin Fasiƙin mutumin nan,Ka kawo mana ƙarshen shi,Mugu azzalumi ya jima yana cutar rayuwar yaran nan,In sha Allah ƙarshen shi bazaiyi kyau ba,"ranshi a 6ace yake yin maganar,

  "Sehrish ina Hosana take baiwar Allah"Maman sadeeq ce tayi maganar har lokacin hawaye ne ke shararowa akan fuskarta,

  "Duk suna nan lafiyarsu ƙalou muna atare dasu cikin danginmu,"

Murmushi Maman sadeeq ta saki tare da cewa"Allah sarki,rayuwa kenan,"

  "Baba ko kuna da labarin Abu"?Abusufyan ya jefo masu tambayar,

Gabansu ne ya faɗi atare suka kalli juna jin tambayar da Abusufyan yayi masu,

  Hakan ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba,tun daga kan irin kallon da yaga sunyi ma juna yasa shi shan jinin jikinshi,.  

  Hankalin Sehrish a matuƙar tashe tace"Dan allah,ku faɗamana a ina Oummanmu take?nasan kuna da masaniya akai,"

  Shiru sukayi batare da sun basu amsa ba,nan take Sehrish ta fashe da kuka tana cewa"dama nasani,zai yi wuya mu sameta araye,innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,"

  Ƙiriss ya rage zuciyar Abusufyan ta buga,zumbur ya miƙe yana ƙoƙarin barin wurin,hannunshi dafe da saitin zuciyarshi,

    Muryar Baban sadeeq ce ta katse mashi hanzarinshi,

   "ABU TANA RAYE,"

jin wannan maganar yasa,Abusufyan komawa dirshan ya zauna,muryarshi har shaƙewa take yi wurin cewa"dagaske abuna tana araye?dan Allah ku faɗamin gaskiya,abu tana raye?tana ina?a ina zan ganta?"

  A natse baban sadeeq ya soma kora masu jawabi,

  "Tun bayan lokacin da Hosana tayi jinya a asibiti sakamakon Buguwar da kanta yayi harta samu ta6in hankali,nasan kunji labarin nan a wurinsu Sehrish,"ya ɗan dakata dayin maganar yana kallon fuskokinsu,

  "Hakane,munji komai a wurinsu,"a ƙagare Abusufyan yayi maganar,jikinshi sae tsuma yake yi,ita kanta sehrish ta ƙosa taji abunda zaice,

   "Tun bayan da aka kwantar da Hosana gadon asibiti,lokacin ana ƙoƙarin tattara kuɗin da za'ayi mata aiki,kwatsamm aka nemi mahaifiyarsu aka rasa ƙasa ko sama,tun bayan da ta sanar masu cewa zata je gida ta sanar da sayyadi halin da yarinyar take ciki don tunda aka kwantar da ita bai leko asibitin ba da tunanin ko asamu wani abu daga wurinshi,Don acika ayima yarinyar aiki,tunda ta haura ƙafa tabar asibitin bamu ƙara jin ɗuriyarta ba,"

  Shiru ya ɗan yi yana sauke ajiyar zuciya kafin ya daura da cewa"A lokacin Hankalin mu ba ƙaramin tashi yayi ba,ga yarinya ba lafiya kwance gadon asibiti rai hannun Allah,Ga sauran ƴan uwanta dake a cikin ƙuncin rayuwa na rashin ganin mahaifiyarsu da basu yi ba har tsawon kwanaki,wannan yasa muka bazama neman abu acikin unguwar nan,Saƙo da lungu ba'a sameta ba,Gashi gidansu a garkame da kwaɗo,har muka fara tunanin cewa kodai Abu ta gudu ne tabar yaranta,wata'ƙil damuwace tayi mata yawa,shiyasa ta ta tafi tabarsu,Jinyar hosana ta koma hannun Maman sadeeq itace taci gaba da kula dasu a asibiti,"

  Dakatawa ya ɗan yi da jawabin,na wani lokaci kafin yaci gaba da cewa"Ana haka,wata rana na dawo daga masallaci,ina ƙoƙarin shiga gidana,sae ga wani yaro nan,Umari ɗan wurin makwabcinmu ne shima,Yana tsaron shagon mahaifinshi abakin hanya,shi ya tare ni yayi mun sallama,Na juya na amsa mashi sallamar,yace mun malam inason magana dakai,game da Matar mutumin nan makwabcinka,Ya sayyadi,koda naji ya ambaci hakan sai na mayar da hankali sosai akanshi nace mashi"ina sauraronka,Anan ne yake sanar dani cewa,Ya gamu da abu akan hanya tana hauka babu takalma a kafafunta babu mayafi a jikinta,tana kuka tana sambatu tana fadin cewa Ya kashe mun babana,Ya rabani da mijina!kuma zai kashe mun ƴa'ƴana,'lokacin da Umari ya sanar dani wannan maganar hankalina ba ƙaramun tashi yayi ba,tun kafin ma ya ƙarasa maganar,jiki na rawa na hau babur ɗina na koma asibiti,a gaggauce na tattara yaran nan,nasa aka kaisu katsina wurin kishiyar babata,bakomai yasa nayi hakan ba,sai don gudun kada kalaman Zainabu abu su tabbata da gaske,Saboda a nazarin da nayi,wannan sambatun da akace tana yi yana da alaƙa da haukanta,Tabbas ya sayyadi shine yayi silar mutuwar mahaifinta,shiyasa har abun ya tsaya mata aranta,kuma ya ta6a mata zuciya har ta samu ta6in hankali,wannan dalilin yasa na ɗauke yaran gaba ɗaya na mayar dasu can,saboda inajin tsoran Ya sayyadi ya halakar dasu,"


Ganin ya dakata da yin maganar yasa Abusufyan saurin cewa"Yanzu a wani hali abu take ciki?kun samu nasarar gano inda take,"

  Miƙewa Maman sadeeq tayi tare da shigewa cikin gidan,Jim kaɗan ta dawo hannunta ɗauke da tray,ruwa ta ɗebo masu acikin Jug,sae ƴan kofuna guda uku,Ajiyewa tayi agabansu,tare da tsiyaya ruwan ta miƙa ma Baban Sadeeq,hannu yasa ya kar6a tare da kai kofin bakinshi yana sha,

  Ƙara zuba ruwan tayi a sauran kofunan ta dauka ta miƙa ma Abusufyan,girgiza mata kai yayi tare da cewa"Bazan iya shan komai ba,in har banji a wani hali abu take ciki ba,"sam babu kwanciyar hankali atattare dashi,

  Miƙa ma Sehrish ruwan tayi,"kar6i kisha ƴata,"hannun sehrish na kerma ta kar6i kofin takai ruwan abakinta tana sha,




💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 *ASLM GANI FA NA SAKE DANNOWA DA SABBIN KAYA MASU SABON SALO*💃🏻💃🏻💃🏻


*takuce mmn Yusuf Dr mata mai gyaran mata ciki da wake*💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻


Ina uwargida da Amarya ina masu shirin yin aure budare da zawarawa , ina masu son su zama taurari ✨🌟ababen alfaharin mazajensu , ina mata masu kishiyoyi da ake ci masu zarafi ake wulakantasu akan kishiyoyin su ina wacce keshan wulakancin namiji , ina matan da sukeson burge mazajensu da zallan ni'ima da dandano ??? Ina matan fake fama da rashin ni'ima , budewar gaba wadan da suka faru sanadin ciyon sanyi kokuma haihuwa , ko wadda Ke fama da k'arancin ni'ima da karancin sha'awa , ??  To saurara kiji✋🏻✋🏻✋🏻


Ko kinsan Maman Yusuf Dr mata kuwa ?? Hmmm akace in bakasan gari ba to ka saurari daka,💃🏻💃🏻

*Namu na dabanne kamar yadda salonmu yake daban ingantattun kaya ne da basuda wata illa ajiki sannan ba boka ba malam zaki mallaki mijinki da dandanonki sai yadda kikayi dashi*


Duk abunda kk so a bangaren kayan mata zaki samu hajiyata daga gyaran ciki harma Dana waje 


Munada ingantaccen maganin sanyi na maza Dana mata hakama maganin Basir 


Maganin nono Dana hips 

Maganin kiba dakuma maganin rage tumbi da kibar, 

Maganin gashi 

Maganin hawan jini

Maganin sugar


Sabulun wanka na gyaran jiki

Sabulun dilka na amare

Dilkar amare


Kwallin mallaka (daga ni sai kai)

Maltinar mata

Bobintan mata

Set na lalata gindin kiahiya

Set na ukku bala'i

Set na rantse bakida kishiya,


Kalolin gumba

Kalolin gari

Kalolin matsi

Kalolin sabulan tsarki

Zumar mata

Zumar ridi 

Zumar goron tula

Tsumin mallaka

Tsumin jaraba

Tsumin sabon budurci

Tsumin kankana

Tsumin tabaje

Tsumin makalemata 

Shayin mata 

Sirrikan mallaka

Dan goshi da mahadinshi 

Dan goshi na Mara

Kyallen al'ajabu

Rakumi da akala

Bita zai zai

Dahuwar kalolin kaza zabo zakara 

Dahuwar zuciya

Dahuwar ciccibi

Dahuwar zuciya

Dambun nama

Dahuwar yan shila

Yajin mata 

Yajin maza domin Karin karfi



*Hmmmmmm in nace sai na lissafamuku zafafan kayan nan sai in wuni ina typing shawara daya zan baki uwargida in har baki jaraba kayan mmn Yusuf ba to ki garzaya ki saya da kanki zakizo kina godiya , 😉😉😉😉😉😍 wadan da suka San ya kayan suke kuwa. Basa bukatar wani Karin bayani , 

Domin Neman Karin bayani kokuma ganin kayan da nake dasu Ku tuntubeni ta wannan number 07069711327 call or WhatsApp mmn Yusuf mai kayan mata🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰


Ina bada sari ina sokoto ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah , 

Don Allah in baki shirya siyaba to kibari sai kin shirya sai muyi magana🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 07069711327

  






   









   

  

 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*


💫💥💫💥💫💥💫💥💫💥💫


*_ALBISHIRINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE , SHAHARARRAR KUMA KASAITACCIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WADDA KUKAFI SANI MAMAN YUSUF YAR SOKOTO TANA YI MAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE CIKIN FADIN NIGERIA DA NIGER KARKU MANTA MACE MAI KYARA KANTA BATA BORANCI_* 💃💃💃💃💃💃💃  07069711327


_Akwai zafafan kayan Mata masu kyau da arha cikin sauki da rahusa Kuma duk inda kike zamu aika maki kayanki cikin aminci da yardar Allah ba cuta ba cutarwa don a Dade anayi sai gaskiya uwargida da amarya ku garzayo Kar abaku labari_


Munada kalolin Kaya kamar haka💥💫💥💫💥💫👇🏻👇🏻


Maganin sanyi sahihi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata


Maganin gyaran nono domin dawo da martaban nononki hadin gargajiya da bashida illah ajiki


Maganin hips Mai tado da hips cikin kankanin lokaci


Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko dai dai misali kiyi kyau kema ki shigo cikin jerin Mata masu aji


Maganin rage kiba da tumbi Wanda zaisa ki sace ki koma Yar dai dai abin alfaharin kowane namiji,


Akwai kalolin gumbuna masu kyau da saukar da ni'ima


Maganin matsi masu ciko da gaba da matseki Kamar Yar budurwa uwa uba zasu Baki dandano Mai gamasar da maigida


Kalolin garrika masu bawa mace niima da jimawa ajiki


Kalolin tsumi Sha yanzu magani yanzu dasa Mai gida ihun Dadi


Zumar mallaka

Zumar goron Tula

Zumar ridi 

Zumar Mai rubutu


Hadin mallaka 

Turaren mallaka

Shu'umar humra

Turaren AL'AJABI

Matan gaske

Ak 49

Sirrin tafin k'afa

Turaren fuska

Hatsabibin turare

Kwallin mallaka

Zoben mallaka 

Jigidar maida tsohuwa yarinya

Maltinar Mata

Karya gado

Yajin Mata (yajin Mai ciko da mace)

Yajin maza (domin Karin k'arfi)




Muna dahuwar Kaya kamar haka💫💥💫💥👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻


Dahuwar zabo (mallaka)

Kazar Yar gata

Yan shila 

Ciccibi

Dambu

Zuciya 

Yan ciki

Kwai ukku

Tsoka Tara

Kifi 

Da sauransu



Akwai sirrika sosai da muke hadawa ga wacce kishiya ta addabeta ko wadda take fama da butsarin namiji ko mafadacin namiji ko namiji Mai yawon dare ko Wanda yake bin Mata insha Allah duk zaku samesu Kuma da yardar Allah za'asamu biyan bukata


Muna bada magani ga yarinyar da tsautsayi ya fad'a Mata ta rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji Kuma insha Allah zaadace da yardar Allah


Abubuwan da yawa gsky Wanda in nace Zan lissafasu sai nakwashi tsawon lokaci maiso tabini PC don ganin kalolin kayan da muke dasu ,


Karku manta mace Mai gyara kanta Bata boranci taku ce maman yusuf Yar mutan sokoto 07069711327

.

Don Allah wadda Bata shirya ba tabari sai ta shirya sannan tayimun magana🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼ngd 


07069711327



*Boss Bature✍️*




"Bayan komawarsu hannun kishiyar babata,Sai hankalin mu ya dawo kan tunanin a ina zamu ga uwar yaran nan,Nemanta muka bazama yi acikin unguwar nan ruwa A jallo,duk wasu gidajen masu unguwanni na kewayen mu mun cigita haka ma ofishin yan sanda,tsawon lokaci ana nemanta bamu same ta ba,Hankalinmu ya tashi,Saboda sanin cewa Yarinyar nan bata da kowa,Gashi tabar gida a wani yanayi na ta6in hankali,Ga ƴa'ƴanta dake buƙatarta,hakan yasa bamu yi kasa a gwiwa ba ni da baban umari muka kai cigiya awani gidan Redio amman shiru kake ji ba Abu babu dalilinta Allah kaɗai yasan ina ta nufa don kasan garin kano da faɗi,aƙarshe muka fara zullumin anya Abu na'a garin nan ma kuwa,hakan yasa muka hana idonmu bacci wurin rokon ubangijin sammai da kassai da ya bayyana mana ita cikin aminci ya kareta aduk inda take,tsawon lokaci muna ta rokon Allah ba tare da gajiyawa ba,Ana haka kwatsam wata rana muka samu labarin bayyanar Abu ta hanyar Sanarwa a gidajen radio dana talabijin cewa Ana neman danginta,tare da adireshin asibitin da aka kwantar da ita sakamakon motar wani bawan Allah da ta bugeta a saman titi tana gararanbarta shine ya kaita asibiti ya kuma bada ayi cigiyar danginta,koda sanarwar nan ta isar mana jiki na rawa,Ni da Maman sadeeq tare da yaron nan ɗan wurin makwabcinmu muka kwasa muka tafi asibitin,ba ƙaramin daɗi muka ji ba da muka samu abu zuciyoyinmu suka cika da farinciki,duk da babu hankali atattare da ita,A lokacin likitan dake kula da ita ya buƙaci akawo wani makusancinta,wata'ƙil adace ta dawo cikin hayyacinta idan tayi ido biyu da ƴa'ƴanta da take yawan ambaton sunansu,jin haka yasa na yanke shawarar zuwa katsina domin in taho da yaran nan,ko Allah zaisa adace abu ta dawo cikin hayyacinta,alokacin nayi kokarin kiran lambar tsohuwa don in sanar da ita game da zuwa na don a shirya ma yaran amman a kashe,hakan baisa nayi tunanin wani abu ba,don dama mafi yawancin lokutta wayar tata na kasancewa a rufe sai anyi sa'a ake samu,ahanzarce na shirya zuwa katsina,Sai dai kash!wani mummunan labari ya riskeni a lokacin da naje unguwar da suke,Na rasuwar ita mariƙiyarsu Kishiyar babata tsohuwa,Sannan kuma naji cewa an liƙa masu ƙazafin maita,wai sune suka kashe ta saboda an ga kumfa a bakinta kamar taci guba,Hankalina yayi mugun tashi saboda ina da tabbacin cewar yaran abu bazasu ta6a aikata hakan ba,Ni shaida ne akan yaran,nayi baƙin ciki sosai kamar zan haɗiyi zuciya in mutu lokacin da Makwabcinsu ya rakani police station ɗin da aka kulle yaran,ƴan sandan da muka samu a wannan lokacin sun tabbatar mana da cewa,a nan police station ɗin aka kawo case ɗinsu,sai dai daga baya sun bar hannunsu sakamakon ciwon ɗaya daga cikinsu daya tashi aka kaisu asibiti Anan ne wani babban Jami'en Soja ya kashe Case ɗin gaba ɗaya,Shine silar barinsu asibitin,kamar zanyi hauka alokacin,Saboda tsabar takaici,na nace akan dole ƴan sandan nan su haɗani da mutumin daya kar6i yaran,Amma suka sanar dani cewa su kansu basu san wanene ba,Saboda basu bane asalin waɗanda case ɗin ya mutu ahannunsu ba,waɗancan anyi masu canjin wurin aiki,A ƙarshe dana takura masu na dinga zarya a police station ɗin akan su faɗamun waye wannan jami'en sai su kayi mun barazanar idan na ƙara zuwa zasu ɗaure ni,Tun daga wannan lokacin,jiki a mace nadawo kano alokacin aka sallami Abu bayan likitan dake kula da ita ya bada shawarar amaida ita asibitin masu ta6in hankali amman muka dawo nan gidana da ita da tunanin yi mata addu'oi don alokacin ina ganin kaman harda sihiri atare da ita,haka na dukufa yi mata addu'oi ba dare ba rana amman sauki dai sai wurin Allah,yadda taga rana haka take ganin dare sam bata bacci,sai sambatun Babanta da ya'yanta,in takaice maku dai Abu buge buge ta fara tana kokarin guduwa,Babu yarda muka iya muna ji muna gani haka muka dauki Abu muka kaita Asibitin mahaukata......"daƙyar ya ƙarasa maganar saboda kukan daya zo mashi,yana kai ƙarshen maganar ya fashe da kuka,tuni hawaye sun wanke fuskokinsu gaba ɗaya,Musamman Sehrish sosai take kuka,

  Muryar Abusufyan na kerma yace"Ya..yanzu...a wani psychiatric ne aka kaita,"

  Maman sadeeq ce ta bashi amsa da cewa"Tana a Dawanau Psychiatric Hospital,ko watan daya gabata sai da muka je gano ta,baiwar Allah tana cikin halin ha'ula'e,gwanin ban tausayi,duk in muka je kai mata ziyara,haka zamu sameta tana ta kuka tana sambatun Ya kashe mata mahaifinta,Ƴa'ƴanta Suna ina,akawo mata ƴa'ƴanta,kada ya kashe mata su,"

Jin wannan maganar yasa Sehrish ta ƙara sautin kukan nata sosae,

  "Inason ganinta yanzu,"Abusufyan ne yayi maganar tare da miƙewa jikinshi na rawa yace"dan Allah idan ba damuwa,Ku taimaka ku jagorance mu izuwa asibitin,"

  Miƙewa suka yi gaba ɗayansu,Baban Sadeeq yace"nafi kowa farin cikin wannan ranar,duk da ina da uzuri a makaranta,Zan iya dakatar da komai,dan In raka ku muje a tare,"

  Ɗaga hannu Abusufyan yayi sama yana godiya ga Allah,Ita kanta Sehrish tsantsar farin cikine ya rufe ta,

  Atare suka fito daga cikin gidan,a ƙopar gidan suka tsaya,Abusufyan ya ɗauko wayarshi tare da dannawa Sgr kira,Bayan ya amsa kiran anan yake sanar dashi cewa Zasu wuce Dawanau Psychiatric Hospital,Sgr yace su haɗu acan,"


A back seat na motar Baban Sadeeq tare da Maman Sadeeq suka shiga suka zauna,Yayin da Abusufyan ya shiga mazaunin driver,Sehrish na a gefenshi,ganin yadda hannunshi ke ta kerma wurin ƙoƙarin tashin motar yasa tace"Daddy,Anya zaka iya driving ɗin nan"?

  A ruɗe yace"Daughter,ki ganni kawai,ba zaki gane halin da nake ciki ba,Am so eager to see her,Kamar nayi fiffike,"

Murmushi ta ɗan yi,Ita kanta ji take da ace tana da fiffike da ta tashi sama don ta ƙarasa asibitin da wuri,


da gudun gaske ya fisgi motar kamar zasu tashi sama,cikin ƙankanin lokaci suka ƙarasa asibitin,


*DAWANAU PSYCHIATRIC HOSPITAL*


A dai dai lokacin da Abusufyan yake ƙoƙarin shigar da motarsu cikin asibitin,Sai ga Motocin Sgr da jiniya mai sautin gaske,sun shararowa a jere,Jibga jibgan sojoji ne a saman motocin bana wasa ba,ko shugaban ƙasa albarka,tuni mutane suka dare aka bar masu hanyar su kaɗae,

A daidai bakin gate din aka tsaida jiniyar,kafin motocin suka shiga cikin Asibitin, Motar Abusufyan ce ta fara shiga sannan nasu suka rufa masa baya,wasu daga cikin sojojin dake a motar ƙarshe ne suka diddiro suka ƙame a bakin gate din shiga sai faman mazurai suke yi kowannansu hannunshi na riƙe da ƙatuwar bindiga gwanin ban tsoro,parking ɗin motocin su kayi,buɗe motar Abusufyan yayi tare da fitowa daga ciki,ya zagaya ya buɗema Su Baban Sadeeq motar suka fito,Sannan itama Sehrish ta fito,tana ƙarewa asibitin kallo,tun kafin ma su shiga ciki,ta fara ayyana yadda zata samu mahaifiyarsu,duk da tana cikin damuwar halin da zasu same ta,


Fitowa Armstrong yayi daga cikin Motarsu,ya zagaya tare da bude mashi,A hankali ya zuro ƙafarshi daga cikin motar,Kafin ya ƙarasa saukowa daga cikinta Masha Allah,Open shirt ce sanye a jikinshi white colour,rigar ta bayyana Ƙirar faffaɗan ƙirjin nan nashi,Cos bai sanya button ko ɗaya ba,a buɗe yabarta sai farar vest,Dogon wandon jikinshi black colour ne,Wankan black & white ya ɗauka,ƙafarshi na sanye cikin oxfords shoes,daga saman sumar kanshi kuma ya sanya facing cap black,Eyes ɗinshi na manne da Sunglasses,Wa'iyazubillah Ya haɗu iya haɗuwa,kamar a buga a jarida,

Duk da yanayin da suke ciki hakan baisa sun ƙi kallon wankan nashi ba,Musamman Babban sadeeq da kuma Maman sadeeq,tare da sauran jama'ar dake zarya a cikin asibitin,Yayi matuƙar jan hankalinsu,Ita kanta Sehrish sai da ta girgiza da irin wankan da ya ɗauka,


Kama hanyar shiga ciki su kayi,Baban sadeeq ne agaba shi da Maman sadeeq,Abusufyan da Sehrish na abayansu,yayin da Sgr tare da Armstrong suke a biye dasu,sai wasu daga cikin security,mutum biyu dake ruƙe da jibga jibgan bindigogi,suna take mashi baya,a bakin OPD suka ƙame,yayin da Sgr da Armstrong wanda ƙugunshi ke manne da bindigu pistol guda biyu suka shiga ciki,batare da sunsha wahala ba saboda su Maman Sadeeq sun san asibitin,suka nufi wurin da nurses suke,wato nurses station,Anan suka taras da Nurses ɗin dake Duty,koda nurses ɗin nan sukayi arba dasu,gaba ɗaya hankalinsu ya koma akan Sgr,kallon ƙurulla suka shiga binshi dashi,

Gyaran murya Abusufyan yayi masu hankalinsu ya koma akanshi,A natse ya soma magana"Sannunku da aiki,"

  Atare suka haɗa baki wurin amsa mashi"Yawwa yalla6ai,munayi maku barka da zuwa,"

   gabatar masu da kanshi yayi tare dasu Sehrish kafin yace"akwai patient ɗinmu dake anan asibitin,munzo dubata ne,'

  ɗaya daga cikinsu ce,ta kai hannu gaban drawer chest ɗin dake a jikin table ɗin gabansu,tana ƙoƙarin zaro roster ɗinsu,tace"Zan iya sanin sunan mara lafiyan naku,"

Abusufyan yace"Sunanta Zainab ibrahim buzuwa,"yayi maganar tare da kallon baban Sadeeq,don yaji idan ya faɗa dai dai,jinjina mashi kai yayi alamar eh,

  A saman table ɗin gabansu ta ajiye patients roster ɗin,tana dudduba sunan marasa lafiyan,

  "Last week,an canza ma wasu daga cikinsu wurin zama,bansan ko kuna da masaniya akan hakan ba,"acewar nurse ɗin 

  Kallon juna sukayi hankalinsu aɗan tashe fargabarsu kar ace,an ɗauke abu daga asibitin,

  "Yawwa,itace Zainabu ibrahim buzu ko"?

Har suna haɗa baki wurin cewa "eh,itace,

Murmushi Nurse ɗin tayi tare da cewa"Zainab tana a female ward B,"kallon abokiyar aikinta dake a gefenta tayi tare da cewa"kiyi masu jagora izuwa ɗakin da Zainab buzuwa take,"Amsa mata tayi da toh,sannan ta fito tare da nufar wani corridor,gaba ɗaya suka bi bayanta,kowa da abunda yake saƙawa aranshi,jikin Sehrish dana Abusufyan sae kerma yake yi,duk sun sha jinin jikinsu,


Tun kafin su ƙarasa ward ɗin,mahaukatan dake a killace suka fara kwala masu kira,

  "Yalla6ai,yalla6ai,"Sehrish ba ƙaramin tsoro taji ba,gasu nan gwanin ban tausayi,sae faman zuru hannuwansu suke yi daga cikin bars ɗin,

  "Baiwar Allah!"wata mahaukaciya ce ta kwala ma Sehrish kira,tana nuna ta da hannu,a firgice Sehrish ta juya tana kallonta,Washe mata haƙora tayi tana kashe mata ido ɗaya tace"ki ce wa mijinki ya dinga sanya Niƙabi a fuskarshi,in ba haka ba wlh za'ayi maki kwacenshi,Don mu nan da kike ganin mu ba cikakken hankali ne damu ba,"

 

  Ba sehrish ba,hatta Sgr sai da ya ɗan murmusa,ba ƙaramin dariya ta basu ba,

  Suna cikin tafiya wata mahaukaciyar kuma ta ƙara kwala masu kira tana fadin"Wayyo Allah,Farin namiji ko maye ne nidai inaso,Ya Allah ka bani fari dogo kyakkyawa,kalan yan kasan waje,In biya sadakin shi ayi mana aure,"tana magana miyau na zalala a bakinta,

  A rude Sehrish tace"Nashiga uku,Wannan wani irin kyau ne da har mahaukata ma suke santinshi"?acikin zuciyarta tayi maganar,bata ƙarasa zancen zucin nata ba,tajiyo wata mahaukaciyar kuma tana tambayar wai nawa ne farashinshi,

  "Yalla6ai..."hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,jin yadda suke ta kwaɗa mashi kira,duk da jikinta yayi sanyi,tsananin tausayin mahaukatan ne ya kamata,nan take ta shiga tunanin ko awani hali zasu samu oummansu,

  Tana cikin wannan yanayin na damuwa taji hannun Sgr a cikin nata,ɗan juyawa tayi tare da kallonshi,adai dai lokacin shima idon nashi na akan fuskarta,kallon juna suka shiga yi,bakomai ne ya faɗo mata aranta ba,face irin haukan da yayi mata adaren jiya na sauraye,yayin da shima abunda yake tariyowa kenan acikin kanshi,yadda ta tsaya kore mashi saurayen nan,ta ba shi kyakkyawar kulawa har ya samu bacci,ba ƙaramin daɗin hakan yaji ba,

  Gaba ɗaya sun shagala da kallon junansu,

  Muryar wata mahauciyarce ta kuma katse su da cewa"Ranka shi daɗe,Amma dai sabon aure ne ko?Wlh kunyi kyau kun dace da juna sosai,Wlh har kun tunamin da mijina...."tana faɗin hakan ta fashe da kuka mai sauti,atare suka kai idanunsu wurinta suna kallonta,Cikin shessheƙar kuka tace"Yalla6ai dan Allah ka kula da matarka kuyi zaman lafiya,kada ka wulaƙantata,ka bata kyakkyawar kulawa,Musamman in tasamu ciki,"ta ƙarasa maganar tana matsar kwalla,

Wata irin kunyace ta rufe sehrish,

Maman sadeeq ce ta kalli mahaukaciyar tare da cewa"baiwar Allah,meya faru da mijin naki?baki bamu labari ba,". 

  Hannu tasa ta ɗan share hawayenta kafin tace"Naso shi sosai,Munyi aure har mun haifi ƴa'ƴa dashi,babban abun takaici,A wurin haihuwarshi mahaifiyarshi ta mutu da cikinshi,"tana kai ƙarshen zancen nata ta rushe da kuka,.  

  Gaba ɗaya suka fashe da dariya,hatta Abusufyan dake acikin damuwa sai da ya ɗan yi murmushi,Haka Sgr shi kanshi baisan ya saki wannan kyakkyawan murmushin nashi ba,Zuba mashi ido Sehrish tayi tana kallonshi,dimple har biyu suka lotsa asaman fuskarshi,abun yayi matuƙar tafiya da hankalinta,koda ya gane cewa shi take kallo,nan take ya ɗauke murmushin ya tamke fuskarshi,

  A dai dai lokacin da suke ƙoƙarin karya corner su shiga wani ward ɗin,kwatsam suka ji hayaniya na tunkarosu,da sautin takalman mutane,hankalinsu a matuƙar tashe suka kai idanuwansu wurin don suga meke wakana,

  Wata mahaukaciya ce,ta 6allo daga wurin da aka killaceta,da gudun gaske,blue uniform din jikinta duk sun yayyage sun fita hayyacinsu,ƙafafunta ba takalma,gashin kanta duk ya hargitse ya rufe fuskarta gaba ɗaya,a bayanta kuwa likitoci ne da wasu ma'aikata suka biyota suma a guje,suna ƙoƙarin dakatar da ita,

  "Ki tsaya!ki dakata anan!dan Allah ataimaka ataro mana ita,mara lafiya ce ta kufce mana,"ɗaya daga cikin likitocin dake biye da ita ne yayi maganar,hannunshi na ruƙe da syringe,yayi annoucement ɗinne don asamu wanda zasu taimaka wurin damƙo masu ita,

  Duk tabi ta firgita ta ruɗe,ko kallon gabanta batayi,da dukkan ƙarfinta take yin gudun gashi sumar kanta duk ta zubo ta rufe mata har idanuwanta,ita kanta batasan wurin da zata dosa ba,burinta kawai tabar hannun masu fararen kayan dake biye da ita,

  Sai gara likitocin takeyi duk sun galabaita,gadan gadan ta tunkari wurin da su Sehrish suke,Naɗe hannun riga Abusufyan ya shiga yi,haka Sgr ma he's ready to help,ba'a maganar Armstrong da yayi shirin yi mata ɗaukan jariri, jira kawai suke ta ƙaraso wurinsu,su cafke ta,

  Tunkan ta ƙarasa wurinsu,ƙafafuwanta suka harɗe gaba ɗaya ta tafi a karkace zata kife ƙasa,da sauri Abusufyan ya damƙota,ta faɗa ƙirjinshi ta tsorata sosai,ƙankame shi tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,jikinta sai kerma yake yi,

  Ƙarasowa likitocin su kayi suna faman sauke ajiyar zuciya,

  "Yalla6ai,mun gode sosai,ba ƙaramin taimako kayi mana ba,baiwar Allah nan,daga shiga yi mata Allura ta kubce mana,ta bamu wahala sosai,"ɗaya daga cikin likitocinne yayi maganar,

   Ɗayan doctor ɗin dake a gefenshi yace"Allah ya taƙaita wahala,Da bamu son inda zata dosa ba,"

..su uku ne likitocin sae Nurse ɗaya dake a biye dasu,

  Hannu Abusufyan yasa yana ƙoƙarin 6an6arota daga jikinshi,ae kuwa a tsorace ta ƙara ƙankameshi tana faɗin"dan Allah kada ka bari su tafi dani,wlh ni ba mahaukaciya bace,da hankalina,ƴa'ƴana nake nema,dan Allah ku kaini wurin ƴa'ƴana kar a kashe mun su suma,koda sau ɗaya ne in sanyasu acikin idanuwana,"

  Rasss! yaji gabanshi ya faɗi,Hatta Sehrish sai da gabanta ya faɗi,saboda jin muryar Mahaukaciyar da tayi maganar,"

  Ƙarfi yasa ya ɗaɗɗago da kanta,daga saman ƙirjinshi,Hankalinshi a matuƙar tashe yake kallonta,ta runtse idanuwanta jikinta sae faman kerma yake yi,

    Bazai ta6a mantawa da fuskar abunshi ba,haddar da yayiwa fuskarta bamai gogewa bace,Bazai ta6a mantawa da ita ba,duk irin canzawar da zatayi,

  Muryarshi na kerma ya ambaci sunanta da ƙarfi"ABU"!gaba ɗaya hankalin Sauran ya dawo kansu,

   da ƙarfi Sehrish ta Ambaci sunanta"OUMMA!!"a firgice mahaukaciyar ta juya tana kallon Sehrish da tayi magana,duk tabi ta ruɗe,hannu tasa ta dafe kanta wani irin jiri ta dinga gani acikin idanuwanta,Nan take jikinta ya soma kerma,sumewa tayi gaba ɗaya ta tafi zata faɗi ƙasa,da sauri Abusufyan ya dawo da ita jikinshi sosai ya ƙanƙameta,Lokaci guda hawaye suka shiga wanke mashi fuskarshi,Sehrish kuwa tuni ta fashe da matsanancin kuka,Na farin cikin ganin Oummansu,

   Kowa fuskanshi ɗauke da farin cikin ganinta da su kayi batare da sunsha Wahala ba,likitocin da suka biyota,duk jikinsu yayi sanyi,musamman yanayin da suka ga mutumin ya shiga,tare da yarinyar dake a gefenshi,ta wani 6angaren kuma fargaba suka fara yi kada ace wa'adin zaman abu ya ƙare a asibitin,Saboda sun saba da ita,ko acikin mahaukatan dake a Gidan,

  Gyaran murya Sgr yayi tare da cewa"We don't ave time to waste here,Uncle zamu wuce da ita gida ne,idan yaso Dr ɗin dake kula da ita,Sai ya bi mu can,"

  Hankalin ɗaya daga cikin Dr ɗinnan ba ƙaramin tashi yayi ba,yanayin yadda ya furta"tafiya za kuyi da Zainab"?

  Jinjina kai Abusufyan yayi tare da cewa"Zamanta acikin asibitin nan ya qare,"ya ƙarasa maganar har lokacin hawayen basu daina sauka akan fuskarshi ba,gashi ya ƙanƙameta ajikinshi,ko warin jikinta baiji,

  A ruɗe Dr ɗin yace"Haba yalla6ai,mezai hana ku barta anan acigaba da duba ta,har Allah ya Bata lafi......."kasa ƙarasa maganar yayi ganin irin kallon da Sgr yake yi mashi,duk sai ya sha jinin jikinshi,

Sai lokacin Baban sadeeq ya tsoma baki,

  "Doctor,Wannan da kake gani Mijinta Ne!wannan kuma ƴarsu ce,yaran da take yawan ambato acikin bakinta,To wannan ɗaya ce daga cikinsu,Ƴan ukune gare ta,ƙaddara ce ta rabasu da ita,Yanzun kuma Allah ya haɗasu da ita,"

  Yana kai ƙarshen maganar,likitocin suka haɗa baki wurin cewa"Allahu akhbar!Amma mun tayata Murna sosai,Allah yasa silar samun saukinta kenan" gaba ɗaya suka amsa da Amin,

  Sun jima suna magana,a tsaye kafin daga bisani,Abusufyan ya ɗauketa asaman kafaɗarshi,Sai da suka fara shigar da ita medical room likita ya duba ta sosai,tare da yi mata allurorin da aka saba yi mata,aciki hada na bacci,Tsayawa suka yi acikin asibitin suna ciccike wasu mahimman bayanai da ake bukata a wurinsu,harda Malam nura su da suka kawo ta asibitin,kafin Aka mallaka masu ita, 😍


*Boss Bature*


  *Hayaaam*


Tun da Aunty babba tabarta a asibitin nan magashiyan rai hannun Allah,Sai yau ta dawo cikin Hayyacinta,duk ta bushe ta dishe ta ƙanjame,jikinta duk faci,kamar wadda tayi hatsarin Mota,Komai nata ya ƙare,tayi mamakin ganinta a asibiti kuma babu kowa atare da ita,daƙyar ta iya miƙewa zaune,jikinta sae kerma yake yi,lokaci ɗaya ta shiga tariyo abunda Haroon yayi mata,fashewa tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,duk taji ta tsani kanta kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu,cikin shessheƙar kuka take faɗin"Meyasa na farka ban mutu ba?me yayi mun saura acikin duniyar nan,Natsani kaina,Natsani komai ban sha'awar cigaba da zama  acikinta!bazan ta6a yafe mashi ba,mugu azzalumi ya cutar da rayuwata,hannu tasa ta yaye farin yadin da aka rufeta da shi,riga ce ƴar dai dai guiwa aka sanya mata blue colour kamar uniform,yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin ƙoƙarin ɗage rigar don taga menene a wurin,don tana jin kanta kamar ba dai dai ba,

  Slowly ta tattare rigar,ta dage ta,koda tayi arba da gabanta,A rikice ta mayar da rigar ta rufe tare da fashewa da wani kukan mai cin rai,

  Tana cikin kukan nan,Dr ya shigo tare da Nurse abayanshi,

   Lallashinta suka shiga yi har suka samu ta lafa,Sannan Dr ɗin ya soma magana a tsanake,

  "Baiwar Allah,Ya jikin naki"?_

Cikin shessheƙar kuka tace"da sauƙi,dan Allah ku faɗamun wanene ya kawo ni asibitin nan,yaushe aka kawoni,"tana magana hawaye na wanko fuskarta,

  "ƴar uwarki ce,ta kawoki asibitin nan,Tun last week,Sai dai tun ranar da ta kawoki,Ta gudu tabarki anan bamu ƙara jin ɗuriyarta ba,Mun nemeta sosai ba mu same ta ba,A ƙarshe sai muka samu wannan wasiƙar a gefen gadon ki,bamu karanta abunda ke ciki ba,"ya ƙarasa maganar tare da miƙa mata wasiƙar,

Tunkan ta kar6a gabanta ya shiga faɗuwa rasss!rass!buɗe paper ɗin tayi ta soma karanta abunda ke cikinta,tun da ta fara karantawa tafin hannunta ɗaya ke rufe da bakinta,hawaye sai shararowa sukeyi daga cikin idanuwanta,ƙiris ya rage zuciyarta ta buga saboda tsabar takaici,Ba ta ta6a tsammanin cewa Aunty laila zata iya guduwa tabarta a asibitin ba,Taji ciwon kalmar nan da ta kirata,Wato karya wadda ba'a rabata da maza,ta yanke mata hukunci batare da tasan ainihin abunda ya faru da ita ba,"

Dunƙule takardar tayi ta cukuikuyeta a hannunta,sai faman matsar kwalla take yi,wasu nabin wasu,

  "Lokacin sallamar ki bai yi ba,Amma ya zama dole muyi discharge ɗinki saboda kuɗin gado da aka biya sun ƙare,Sannan akwai wasu bayanai masu mahimmanci game da lafiyarki,da muke so mu samu wani makusancinki mu sanar dashi,Gashi baki da kowa,Bayan wannan akwai alluran da kike buƙata da kuma magunguna domin bunƙasa lafiyar jikinki,Ko kina da wani wanda zai iya taimaka maki"?

  Kuka sosai hayaam take yi,tunani ta shiga yi wa zata kira yanzu don ya taimake ta?Waye take dashi wanda zaiji tausayinta,A iya saninta bata da kowa,in ma akwai babu wanda zai agaza mata saboda sanin Mugun halinta,Shiyasa a koda yaushe akeso mutun ya kasance yana aikata abun kirki a rayuwarshi,ba ka son awani hali zaka tsinci kanka ba a nan gaba ba,duk wani abu da kake taƙama dashi,Walau kyau ko dukiya ko mulki,wata rana Allah zai iya kwace abunshi,Hayaam tayi dana sanin rayuwarta gaba ɗaya,abun ya tsaya mata arai,Wai har ƴar uwarta wadda suka fito ciki ɗaya,Zata iya guduwa tabarta a gadon asibiti rai hannun Allah,ta rayu kota Mutu wannan badamuwarta bace,Wannan wace irin rayuwace?ɗan uwa na gudun ɗan uwanshi,koda yake ɗa ma ya kashe ubansa,Sau nawa akayi?


"Baiwar Allah,kin yi shiru ba kice komai ba"?Dr ɗinne ya katse mata zancen zucin da takeyi,

  Cikin shessheƙar kuka tace"Dan Allah,ku taimaka mun da waya,inaso na kira ƴar uwata ne,"_

Hannu Dr ɗin yasa a aljihun wandonshi ya zaro wayar shi,Infinix ya miƙa mata,jiki na rawa ta kar6i wayar,sai da ta ruƙeta a hannunta ta shiga tunanin wa zata kira,Bakowa ya faɗo mata aranta ba,Fa ce AMANI,duk da tana jin fargabar kada Amani,ta balbale ta da faɗa sakamakon irin wulaƙancin da sukayi masu,daƙyar ta iya danna numbobin wayar Amani,da yake ta haddace numbarta a kanta,Danna mata kira tayi,nan take ya shiga,gabanta sai faɗuwa yake yi,almost 3 times Amani bata ɗaga ba,


A lokacin tana a kitchen tana shirya lunch,tajiyo muryar Amaal tana kwala mata kira,fitowa tayi daga cikin kitchen ɗin ta tunkarota tana tambayar wanene ke kiranta a waya,

Amal dake saukkowa downstairs,tace"New number ce,bansan wanene ba,ta ƙarasa maganar tare da miƙa mata wayar,zuba ma numbar ido tayi tana kallonta,a ƙa'ida bata cika ɗaukar bakuwar number ba,amma tunawa da yadda Amal tazo hannunta,ta hanyar kira da bakuwar number,yasa tayi tunanin ɗaga kiran kada ace wani abu mai mahimmanci ne,Sanya wayar tayi a kunnanta bayan ta amsa kiran,sallama tayi"Assalamu alaikum,"

  On the other hand Hayaam na jin an ɗaga kiran,jiki na rawa ta kara wayar a kunnanta,cikin shessheƙar kuka ta ambaci sunanta"Aunty Amani,"

  Cike da mamaki Amani tace"To fa,kamar muryar Hayaam nake ji,"

Murya na kerma tace"Ni ce,"shiru amani ta ɗan yi kafin tace"Lafiya kika kirani?fuskarta a ɗaure tayi tambayar kamar tana agabanta,

  Cike da fargaba hayaam tace"Aunty Amani ina gadon asibiti,nayi fiye da sati a kwance,babu wani a kusa dani,"

   Murmushi Amani ta saki tare da cewa"Sai akai yaya kenan?menene amfanin kira na?ina Laila ne?inasu Abrah?

  Jiki asanyaye Hayaam tace"Duk basu atare dani,Aunty laila itace ta kawoni asibitin,Amma ta gudu ta barni ni kaɗai,gashi ina cikin mawuyacin hali,kamar zan mutu,"

  tana kai ƙarshen maganar Amani tace"Oh Allah sarki,Allah ya baki lafiya,"

  "Dan Allah Aunty Amani ki taimaka mun,Nasan kina da kyakkyawar zuciya,"

  Fashewa Amani tayi da dariya mai sautin gaske,hada yin shewa kafin tace"Sai yau kika san inada kyakkyawar zuciya?Kin manta irin rashin mutuncin da kuka shuka mana?Ashe akwai rana irin wannan da zaki nemi taimako a wurina?bakiyi tunanin hakan ba?Saboda tsabar rashin kunya a haka kike tunanin cewa zan taimake ki,Koda yake dama ae ba kunya gare ku ba,"guntun tsoki taja mtswww kafin ta ɗaura da cewa"Karki kuskura ki ƙara kiran layina da sunan taimako,don da in taimaki Mugaye masu kafirar zuciya irin taku,wlh ƙwara na tattara duk wani abu dana mallaka,na kaishi gidan marayu,ko Allah ya bani Lada,Amma taimakon irinku,bakomai zai janyomun ba,fa ce Zunubi!"tana kai ƙarshen maganarta,tun kan taji me Hayaam zata ce mata,Nan take ta katse kiran,

  "Aunty Amani meyasa zakiyi mata haka"?Acewar Amal,wadda tuni tausayin hayaam ya kama,

  Harara Amani ta watsa mata tare da cewa"Oh harkin manta irin Muguntar da su kayi mana kenan!waɗannan mutanen da baƙin cikinsu mahaifiyar mu ta mutu,Sannan sune su kayi silar Da mahaifinmu ya Zauce,yake rayuwa tamkar mahaukaci,Bayan wannan Sune suka wulaƙantar da rayuwarki suka mayar dake tamkar dabba a haka kike tunanin zan iya taimakonsu!"?

   Cikin sanyin murya Amal tace"Aunty Amani be kamata kina tuna abunda ya faru ba,wannan su da Allah,Tunda har hayaam ta kira a waya tana neman taimakonki,Yakamata ki agaza mata,koba komai ita ƴar uwarmu ce,bai kamata mu juya mata baya a irin wannan halin na neman taimako ba,Wata'kil ya zamto silar shiriyarta,dama kuma shine abunda muke fata,duk wani wanda ke aikata badai dai ba,ya gane kuskurenshi ya koma ga Allah..."sosai Amal ta shiga tausar Amani,har ta ɗan fara saukowa,


Tunda Amani ta katse mata kira,ta fashe da wani irin matsanancin kukan,mai cin rai,Hada majina,miƙa ma Dr ɗin wayarshi tayi batare da ta iya furta mashi komai ba,Jikinsu ba ƙaramin sanyi yayi ba,shi da nurse ɗin dake atsaye suna kallonta,duk ta fita hayyacinta,

  "Am sorry sister,dukkan tsanani yana tare da sauƙi,Ki ci gaba da addu'a in sha Allah,Zaki samu wanda zai taimake ki,"ɗagowa hayaam tayi da idanuwanta waɗanda sukayi jawur tana kallon nurse ɗin da tayi maganar,cikin shessheƙar kuka tace"Allah bazai ta6a yafe mun zunubin da na aikata mashi ba,Sakayyace ke bibiyata,haƙiƙa Nayi danasanin zuwana wannan duniyar,"tana magana hawaye na zuba akan fuskarta,

  Nurse ɗin tace"Ki gode ma Allah da kika kasance araye har wannan lokacin da kika gane kuskuren da kika aikata,baki mutu kina mai aikata shi ba,Yanzu dama ce agare ki,da zaki tuba ki koma ga Allah,"

  Tana kai ƙarshen maganarta,Tabi bayan Dr ɗin suka fuce daga ɗakin,

Sosai hayaam ke yin kuka har kanta ya fara ciwo,Ga uwar yunwa dake cinta,kamar tayi hauka,zama tayi zugudum tana tunanin inda zata dosa idan likita ya sallameta,bata da kowa babu wurin wanda zata je,gashi bata da ko sisi balle ta doshi gida,ko da tana da kudin inama zata iya zaman mota zuwa maiduguri a wannan halin,saboda raunin dake a jikinta,Batajin zata iya taka ƙafafunta ma har taje wani wuri,uban tagumi ta zabga,tare da rufe fuskarta,tana cigaba da shessheƙar kukan,


Almost 30 mins bata motsa ba,tana cikin wannan halin,Ta jiyo sautin takalma,Kamar ana shigowa ɗakin da take ciki,

    "HAYAAM!"kai tsaye kiran ya shigar mata har cikin dodon kunnanta,a firgice ta ɗago don taga wanene,har sai da gabanta ya faɗi,Abunda batayi tsammani ba,Hannu tasa tana murza idanuwanta,don ta tabbatar da abunda su ke gane mata,

  Amani ce atsaye bakin ƙopar,jikinsu na sanye da jallabiya,sunyi rolling veils a kansu,Hannun Amani na ruƙe da Hand bag ɗinta,Amal kuma na ruƙe da Basket mai ɗauke da food stuffs,da suka zo mata dashi,

   Sakin baki hayaam tayi tana kallonsu cike da tsananin mamakin ganinsu,Lokaci guda kuma tasake fashewa da wani kukan na farin cikin ganinsu,

  Ƙarasa shiga cikin ɗakin sukayi,abayansu kuwa Dr Osman ne a biye dasu,likitan dake kula da ita,

   Ashe bayan fitarshi daga ɗakin Hayaam,ya wuce Office ɗinshi,bada jimawa ba,sae ga kiran Sabuwar numbar a wayarshi,Daya ɗaga kiran,suka gaisa da Amani,ta buƙaci ya bata address ɗin asibitin,Ba ƙaramin farin ciki likitan yayi ba,Saboda ya gane cewa ƴar uwar mara lafiyannan ce,Bayan ya tura mata address ɗin asibitin,After some minutes Motarsu Amani ta shigo asibitin,da kanta tayi driving ɗinsu a motarta,Bayan sun ƙaraso ta kira layin doctor ɗin,Da kanshi yazo inda suke,sannan ya jagorance su izuwa Room ɗin da aka kwantar da Hayaam,


  Wuri Amani ta samu gefen gadon ta zauna,Amal kuma ta zauna saman plastic chair ɗin dake fuskantar gadon,a ƙasa ta ajiye kwandon hannunta,

 a ruɗe Amani tace"Hayaam!meya faru dake haka?hatsarin mota kikayi ne"?

  Girgiza mata kai hayaam tayi alamar a'a,kasa buɗe baki tayi,saboda bata da amsar da zata basu ga kukan dake cinta,

    "Hayaam dan Allah ki sanar dani meya faru dake ne,Nayi mamakin ganinki ke kaɗai a asibiti a wannan halin,batare da Laila ba,"

  "Aunty Hayaam,Sannu ya jikin naki"?Amal ce tayi maganar fuskarta da alamun tausayinta,daƙyar ta iya amsa mata,Duk kunya ta rufeta,

   Cikin sanyin murya tace"Aunty Amani nayi danasanin rayuwata gaba ɗaya,Na tsani kaina,Komai ya fita raina,Ban yi tsammanin zaki zo ba,Har na fidda rai da cigaba da rayuwa acikin duniyar nan,Amma ganinku da nayi ba ƙaramin farin ciki nayi ba,"tana magana hawaye na zuba,

  Juyawa Amani tayi tare da kallon Amal tace"Ki jirani a waje,Zan kira ki,inaso muyi magana da hayaam,ki tafi da wayata,ko game ne ki buga,"

  Miƙewa Amal tayi tare da matsawa wurin Amani,ta kar6i wayarta,kafin ta kama hanyar barin ɗakin,

   mayar da hankalinta tayi sosai akan Hayaam tace"ina sauraronki,faɗamun meya faru dake?meyasa kike zaune a asibiti ke kaɗai batare da Laila ba?duk me ya jawo hakan"?a ƙagare Amani take da taji amsoshin tambayarta,

  Hayaam bata 6oye mata komai ba,Tun daga kan Abunda ya faru tsakaninta da haroon har izuwa farfaɗowarta da tayi a gadon asibiti,Hannu tasa tare da ɗaukar wasiƙar da ta cukuikuye agefenta ta miƙa ma Amani ita,kar6a Amani tayi a atsanake ta shiga karanta wasiƙar da Aunty babba ta rubuta mata,wasu irin hawaye ne suka soma shararowa daga kan fuskarta,Saboda tsabar ƙululun baƙin ciki kamar ta haɗiyi zuciya,

"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!wannan wani irin rashin Imani da rashin tausayi ne?Anya kuwa laila tana son tagama da duniya lafiya?yanzu duk don saboda neman abun duniya ta tafi ta barki a gadon asibiti rai hannun Allah?Anya matar nan tana da Hankali kuwa?Ya salam"rai a6ace take maganar,abun ya ƙona mata ranta sosai,

  Hayaam tace"bata da imani,wlh duk rashin hankalina,banajin zan iya tafiya in bar Aunty laila a gadon asibiti,Amma haka ta haura ƙafa ta barni,Sai kace ba ciki ɗaya muka fito da ita ba......"kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da yazo mata,

  Itama Amanin kukan takeyi sosai,cikin shessheƙar kuka tace"Ha..hayaam ki faɗamun sunan wanda yayi maki wannan aika aikar,inason nasan Wani mara imanin ne"?

  Daƙyar hayaam ta tsagaita da yin kukan tace"HAROON ne ɗan gidansu Ya Abbas,Mijinki,"

  Saboda tsabar kiɗima a razane Amani ta miƙe tsaye hankalinta a matuƙar tashe take maimaita sunan haroon abakinta,

  Hannu ta aza akai tana faɗin"Nashiga Uku!Hayaam kina nufin haroon shine yayi maki wannan ɗanyen aikin"?ɗaga mata kai hayaam tayi Alamar eh,

   "Wlh bazan ta6a ƙyaleshi ba,Sai na tona mashi asiri wurin Abbas!Fasiƙi kawai mugu,dama ni bai ta6a kwantamun araina ba,Allah kaɗai yasan abunda yake aikatawa"ta ƙarasa maganar tare da komawa gefen gadon ta zauna,

  "Aunty Amani ki ƙyaleshi kawai,kada kice zaki tona mashi asiri,koma me ya faru dani laifina ne,Da ace tun farko na kama mutuncin kaina,da babu namijin da zai nemi aikata fasiƙanci dani,Zan yi haƙuri in rungumi ƙaddarata,Kibarshi kawai,Allah shi zai sakamun,"

  girgiza kai Amani ta shiga yi tare da cewa"Wlh bazan ta6a ƙyaleshi ba,Shikenan yaci bulus kenan?wannan mutumin fa,ba ƙaramin mugu bane,bai kamata a dinga ƙyale irinsu ba,Suna aikata abunda suka ga dama,batare da an yanke masu hukunci ba,Yanzu kika san irin matan da ya lalata ta ƙarfi ta tsiya kamar yadda yayi maki?shiru hayaam tayi tana sauraronta,

  "Dole ya gane kuskurenshi,kuma ni bazanso duk wani abu da zai 6ata sunan family ɗinsu ba,Yana so ya zubda masu mutuncinsu ne a idon duniya,Don haka dole na ɗauki mataki akanshi,"ranta a 6ace tayi maganar,tare da kai hannunta cikin food basket din da suka zo dashi ta zaro plate tare da warmer,Buɗe kular tayi,Soyayyan naman kaza ne acikinta wanda yaji uban kayan haɗi,sae ƙamshi ke tashi,tuni jikin hayaam ya soma rawa sai faman haɗiyar yawu take yi,kamar ta kaima warmer ɗin wawura haka take ji,.  

   Acikin plate Amani ta zuba mata naman tare da miƙa mata,Sannan ta dauko mata ruwa mai sanyi na roba,tare da fresh milk,ta shiga tsiyaya mata su acikin Cup,

   ganin yadda hayaam ke taunar cinyar kazar hada ƙashin duka take haɗawa,yasa Amani cewa"Ki ci a hankali mana,kada kija ma kanki wata matsalar,"kasa natsuwa tayi saboda yunwar da take ji,

  Sosai hayaam taci naman nan,tasha fresh milk ɗin mai sanyin gaske,sai da taci ta ƙoshi,sannan ta samu natsuwa,

  "Itama Laila bazan ƙyaleta ba,nasan cewa zata nemi Abra ne don ta rakata wurin bokan,wama yasani ko har sun tafi,Kuma ina da tabbacin cewar,bazata ta6a sanar ma wani cewa tabarki a asibiti ba,don kada a tuhume ta,"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar kafin taci gaba da cewa"muguwar ashe ko ƙannenta da suka fito ciki ɗaya bata iya raga mawa,inajin tsoron tace zata kai Abra wurin fasiƙin Bokannan,don muddin takaita,zaiyi wuya bai nemi ya kusanci ɗaya daga cikinsu ba,"

  Jin wannan maganar yasa hankalin hayaam ya tashi,don ita yanzu tayi nadama,kuma tana jin tsoron halin da Aunty babba zata jefa Abra,kamar yadda tayi mata,


   "Yanzu ya zamuyi mu dakatar da Abra daga zuwa wurin bokan nan"?hayaam ce tayi maganar,

  "Ina ganin idan muka kira Abra muka sanar da ita abunda laila tayi maki na barinki a gadon asibiti,zata fasa bin ta ne,"

  Zama suka yi suna yanke shawarar yadda zasu dakatar da Abra,a ƙarshe suka yanke shawarar kiranta a waya,


*Boss Bature*


*JUNAID*


Tsaye yake a gaban dressing mirror,ya ɗauki wankan pakistan ajikinshi masu kyan gaske farare sun ƙara fito da hasken fatarshi,Fuskar nan har wani kyau ta ƙara,ya gyara sumar kanshi sosai ta kwanta luf a bayan wuyanshi,Slowly ya miƙa hannu gaban mirror ɗin ya ɗauki kwalbar turarenshi,yabi ko ina na jikinshi ya feshe shi,bayan ya mayar da ita,ya ɗauko wrist watch ɗinshi ta diamond da Hajiya azeema ta bashi,Yana ƙoƙari sanyata a hannunshi,Wayar shi ta soma ringing,da sauri ya ƙarasa sanya agogon,tare da tunkarar saman gadonshi inda ya ajiye wayar yakai hannu ya ɗauketa,tare da kollon screen ɗin wayar,Sunan Mommyn su ne ya bayyana akai,tur6une fuska yayi kafin ya ɗaga wayar,cike da shagwa6a ya soma magana"Mommy,ni fushi nake yi dake,"

On the other hand,Alexandra tace"haba romeo ɗina,why are u angry wit me?laifin me na maka da kake fushi dani"

   "Mommy,u forgot about me,tunda na dawo baki kira layina ba,babu wanda ya damu dani,"

  Cikin lallashi tace"Sorry my own son,pls kadaina fushi dani,"

  Bubbuga kafarsa yayi cikin shagwa6e yace"Nidai Mommy indai kina son farin cikina,Ki dawo gida kawai ke da daddy,dasu yaya Fawan,kowa ya dawo gida,nayi missing ɗinku sosai,"

   Alexandra tace"shi ne kawai abunda kakeso,"

  "Eh,adawo gida,acigaba da rainon baby junaid"yanayin yadda yayi maganar ba ƙaramin dariya ya bata ba,yana jiyo muryarta ta cikin wayar tana dariya,

Bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Calm down ur mind,This week zamu dawo,"

  Fuskarshi ɗauke da farin ciki yace"Mommy pls,Ki tursasa daddy,ko da baya son dawowa,ni dai ku dawo gida kowa da kowa,tare da su yaya fawan,Twins su irfan and sister hafsat,inason ganin kowa a kusa dani,"

  "Don't worry ur self,my romeo kowa zai dawo saboda farin cikinka,"

Ba ƙaramin daɗi yaji ba

  Sun jima suna waya kafin daga bisani,su kayi sallama,ajiyar zuciya ya sauke tare da yin wurgi da wayar saman gadon,kwankwasa ƙopar bedroom ɗinshi akayi,da sauri yace wanene

  "My Romeo,its Me ur juliet,am ready for the outing,"wani irin ƙayataccen murmushi ya saki jin muryar jahad,

   A ƙagare yake daya ga wankan data ɗauka,jiki na rawa ya ƙarasa tare da buɗe mata ƙopar,Gabanshi ne ya faɗi rass,Tun daga kan takalman ƙafarta ya fara kallonta,High heels ne ƙafarta,farare,abun ya bashi mamaki ganin tayi shigar white gown,launin kayanshi daya sanya,tayi rolling veil akanta,lips ɗinta kuwa Red ta sanya masu,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga jikin ko wannansu,


  Ruƙo hannunta junaid yayi tare da janyota cikin bedroom ɗin,lumshe idanuwanshi yayi tamkar maijin bacci,da wata irin kasalalliyar murya,yace"Jahad,You look so beautiful,kayan nan sunyi maki kyau sosai,"

  Hannu tasa tare da shafa side face ɗinshi"Duk kyawuna ae bankai ka ba,kaifa na dabanne,ta ko'ina Allah ya baka,".  

  Aɗan shagwa6a yace"Amma ni bana jin kaina a matsayin cikakken mutun,"

  A ɗan ruɗe tace"Saboda me,'?

Hugging ɗinta yayi tare da kai lips ɗinsa saitin kunnanta sannan yace"Saboda,ban mallake ki ba,sai dake ne zan zama cikakken mutun,'

  Wani irin matashin murmushi jahad ta saki,taji daɗin kalaminsa sosai,

   "Nikaina junaid,bana jin kaina amatsayin cikakkiya,har saina mallake ka,"

  kalaman soyayya suka shiga gayawa junansu,

Duk wannan abunda da suke yi akan idon Haroon wanda ke la6e,ya ɗan buɗe kopar ɗakin ya zuro kanshi yana kallonsu,

  Jinjina kanshi yayi tare da cewa"Ta kwana gidan sauƙi,"yana faɗin hakan,ya rufo masu ƙopar ɗakin,hannu yasa tare da zaro wayarshi,Contact ya shiga,Tare da rubuta wasu numbobi,ya danna kira,tare da manna wayar asaman kunnanshi,

  Muryar wani kakkauran mutunne yace"Ya haroon,Ya ake ciki ne?ina fata kazo mana da labari me daɗi,"

  ƙasa ƙasa da murya haroon yayi don kada wani ya juyo shi,

   "Ka saurare ni dakyau,Yanzu junaid zasu fita tare da ƴar wurin uncle ɗinmu,Abunda nakeso daku,Karku kuskura ku ta6a lafiyar jikin yarinyar saboda ba akanta zamuyi aiki ba,Junaid kawai nakeso,Ku bi ta kan motarshi da truck,Yadda ko fuskarshi ba'za a gane ba,idan tayi dameji,"

  Fashewa mutun yayi da wata irin Mahaukaciyar dariya,hhhhhhhh kamar zai fasa screen ɗin wayar,Bayan ya tsagaita da yin Dariyar yace"AN GAMA OGA,SAI DAI UWARSHI TA HAIFI WANI,"

Jinjina kai haroon yayi tare da sakin shu'umin murmushin nan nashi yace"ku kasance a ankare,Yanzu zai fito da motarshi,banaso yaron nan ya dawo gidan nan araye,Gawarsa kawai nakeson gani,jaga jaga da jini,"





  


 [3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐

*MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI*💃🏻💃🏻


Sis ko kinsan illar rama ajikin mace in tayi yawa ??? Rama Sam batayi ba mijinki kullum yana iya kokarinshi akanki amma da yawa mutane sai suyi maki kallon kina cikin matsala ne saboda ramar da kikeyi , sannan zaki zquna a abushe bawata mat'aba ajikinki 🤣🤣 wannan yasa nazo maki da maganin kiba mai inganci hajiya yadda zaki ciko sosai ki murje abunki bawai kiba mai yawa ba aa zaki ciko dai kikoma yar dai dai misali ke ba katuwaba ke ba ramamma ba yadda kema zakiji dadin yin kwalliyar da zataja hankalin mijinki agareki😉😉 mmn Yusuf fa ta shirya tsaf domin gwangwaje Ku da zafafan kayanta uwayen gida da Amare👍🏼👍🏼👍🏼👍🏼07069711327



*Boss Bature ✍️*




*HAROON*na kammala yin wayar,ya mayar da ita cikin aljihun wandonshi,da sauri da sauri ya saukko down kaitsaye ya nufi part ɗinsu,Sautin murya yaji ana raira waƙa da sauri yakai idanuwanshi wurin,Hosana ce zaune saman Sofa,ta aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,ta ɗauki wankan jeans da t shirt ajikinta sam bata lura dashi ba,jinjina kai haroon yayi tare da sakin wannan shu'umin murmushin nashi,A ranshi yace"Zan dawo kanku ne,dake da Omar ɗin,tabbas idan na ta6aki tamkar na ta6a zuciyarshi ne,don haka ta wurinki zan biyo mashi,Saina sa ya zubda hawayenshi kamar yadda nima yasa na zubar da nawa,"ya ƙarasa zancen zucin nashi tare da wuce wa part ɗinsa,bedroom ɗinshi ya shige ya fara zarya acikinshi,burinshi kawai yaji Saƙon mutuwar Junaid~


*JUNHAD*


Saukowa sukeyi downstairs hannunsu ruƙe acikin na Juna,

   "Tun ɗazu nake kiran Layin Rishi,Amma bata ɗagawa,I don't know why,nashiga damuwa,"jahad ce tayi maganar,fuskarta da ɗan damuwa,

  Junaid yace"may be tana busy ne,amma ki bari zuwa anjima sai mu jaraba kiranta,may be ta ɗaga wayar,"

  Cikin palour suka saukko,hosana na ganinsu ta miƙe tana sakar masu murmushi,

  Ba ƙaramin burgeta su kayi ba yarfa hannu ta shiga yi tana faɗin"Wow,jahad junaid kunyi kyau kamar sabbin kuɗin da Central bank suka fitar,"gaba ɗaya suka fashe da dariya,

   camera ta shiga,tare da ɗaukarsu hotuna da wayarta,kafin suka wuce tare da barin palourn,komawa hosana tayi saman sofa ɗin tana jiran dawowar Ya Omar,


Wurin motarshi suka nufa,da kanshi ya buɗewa jahad mota,ta shiga,kafin ya zagaya other side ɗin,ya buɗe ma kanshi motar ya shiga,

juyawa ta ɗan yi tare da kallon fuskarshi,Murmushi ta samu akan fuskarshi,

  Cikin sanyin murya tace"Babyna,"

  "Na'am" ya amsa mata tare da wurga idanuwanshi akanta,

  Kashe mashi ido ɗaya tayi kafin tace"Junaid,I love u so much,I can sacrifice my life for u,"

  Ƙayataccen murmushi ya saki,tare da cewa"Me too,",yana ƙoƙarin tashin motar yaji gabanshi yayi wani irin mugun bugu mai sautin gaske ji kake daraaam!har razana sai da yayi,lokaci guda yanayin fuskarshi ya canza,ganin ya kasa tashin motar yasa jahad,cewa"Babyna,Lafiya naga yanayinka ya canza"?

  Ashagwa6e yace"jahad,faduwar gaba nake ji,kamar wani mummunan abu zai faru dani,haka nake ji,"muryarshi a kasalance yayi maganar,

  Cikin sanyin murya tace"In sha Allah babu abunda zai faru da kai babyna,idan har fitar nan da zamuyi bata kwanta maka arai ba,ni inaga kawai mu koma gida..."tunkan ta ƙarasa maganar,yace"a'a,Bazamu fasa ba,na sa rai sosai akan fitar nan,"

  Jinjina kai jahad ta ɗan yi tare da zura hannu cikin ƴar purse ɗinta dake ajiye saman laps ɗinta,Phone ɗinta ta curo tare da buɗeta,adai adai lokacin app ɗin da take amfani dashi na V muslim wurin yin azkhar yayi mata alert na cewa time ɗin yin evening azkhar yayi,

  Juyawa ta ɗanyi tare da kallon junaid,wanda jikinshi duk yayi sanyi,

  "Babyna,yakamata muyi azhkar kafin mu fita daga gidan nan,"

   Ashagwa6e yace"jahad ni ban iyaba,bansan ya zanyi ba,"

  Moving tayi close to him tare da nuna mashi screen ɗin wayarta"kalli ka gani,App ne nake using dashi yana da matuƙar amfani,kuma yana taimaka mun wurin tunasar dani lokuttan yin sallah da kuma yin azhkar,koda ace baka iya ba,zaka iya yi yayin da kake kallo kana karantawa acikin zuciyarka,"

Murmushi ya ɗan saki kafin yace"Its ok my juliet,mu fara atare,"

  Nan suka shiga yin azkhar ɗin acikin zuciyarsu,har suka kammala,tukunna 

yaja motar da gudu ya nufi hanyar fita daga gate ɗin gidan,a bakin gate ɗin ma sai da jahad ta ƙara tunasar dashi akan yin addu'ar fita daga gida kuma atare suka furta"Bismillah,Tawakkaltu Alallah,wala haula wala ƙuwwata illa billah",


Fitar motarsu keda wuya,Sai ga motarsu Marshal Omar na shigowa cikin gidan,Hatta gifcinsu sai da marshal Omar ya gani,

  "Yalla6ai,kamar motar junaid ce ta wuce yanzun nan"major ne yayi maganar,

Omar dake zaune a back seat na motar yace"I think so,"

  "Amma yalla6ai,kada kace nayi shisshigi,ni dai aganina bai kamata junaid na fita yawo shi kaɗai ba without security guards atare dashi,duk da munsan Allah ke tsare bayinsa,"

shiru Marshal ya ɗan yi yana nazarin wani abu kafin yace"Ni kaina na jima ina tunanin hakan,last time har maganar mu kayi da Rafayet,amma daga baya kowa ya share maganar,"

Major yace"gaskiya yakamata aduba,saboda yaron yana da farin jini sosai,kuma kowa yasan irin son da kuke yi mashi,duk wani mai hakon family ɗinku zai iya biyowa ta wurinshi ne"_

Jin wannan maganar ta Major,yasa hankalin Omar ya tashi,saboda an sha faɗa masu cewa junaid,Shi ne lagwansu,Duk wani wanda zai kawo masu hari acikin masu son ganin bayansu,dole sai an ƙuntatawa junaid sannan za'a ta6a zuciyoyinsu,


  "Major thank u so much for ur advise,and in sha Allah zanyi wani abu akai,'


Bayan Major yayi parking ɗin motar,Ya buɗe ya fito tare da zagayawa ya buɗewa Marshal,Saukowa marshal yayi,ya nufi cikin gidan,lokacin da ya shiga babu kowa a main palour ɗin,Bedroom ɗinshi ya wuce,Shaf shaf ya cire kakin dake ajikinshi,Ya wuce cikin toilet,after some minutes ya fito daga cikin toilet ɗin,sanye da short a jikinshi,Agajiye yake ga wani irin bacci da yake ji,Saman gadonshi ya haye,in a short time bacci ya ɗauke shi,


A hankali Hosana ta turo ƙopar dakin nashi,tun tana kabbara sallar la'asar ta jiyo shigowar mota cikin gidan,jiki na rawa ta sallame bayan ta gama sallar ta fito,saboda tana da tabbacin cewar Ya Omar ɗinta ne ya dawo,murmushi ta saki ganinshi kwance da gajeran wando ajikinshi,ya baje sai faman sharar bacci yake yi,lalla6awa tayi cikin sanɗa ta haye saman gadon,saman jikinshi ta hau,har zuwa saitin fuskarshi,ta ƙura mashi ido tana kallon kyakkyawar fuskarshi,bata da da burin da ya wuce ta takura mashi arayuwarta,

   "Bari nagani,idan na toshe mashi hancinshi da bakinshi,ta ina zai yi numfashin,"

  Hannu tasa,cike da mugunta,ta toshe mashi hancinshi da bakinshi,ta danne su da tafin hannunta,aikuwa nan take numfashinshi ya soma tattokarewa,A razane ya farka lokaci guda,ya rarumeta batare da ya ankara ba,yayi wurgi da ita,da iya ƙarfinshi na ƙarshe,kai tsaye hosana ta faɗi ƙasan gadon yaraf!kanta ya bugu sosai,fashewa tayi da matsanancin kuka tana fadin"Wayyo Allah na,Ya Omar ka kashe ni wllh,"

  Tunda yaji muryarta,ranshi ya 6aci sosai,saboda ita taja har yayi mata hakan,ko kwanakin baya ta ta6a yi mashi irin hakan har yayi wurgi da ita,miƙewa yayi daga zaune tare da kai idanuwanshi wurin da take yashe a ƙasa tana kuka,

  Da wata irin kasalalliyar murya yace"Why Hosana!why!"?

   Sai faman shessheƙar kuka take yi,tama gaza ɗagowa da kanta,

  Guntun tsoki yaja,kafin ya sauko saman floor ɗin,hannu yasa ya janyota jikinshi ya rungumeta a saman faffaɗan ƙirjinshi,yana ɗan bubbuga bayanta,Cikin lallashi yace"Am so sorry My Hosana,duk laifinki ne,meyasa kike son takuramin ne?

  Cikin shesshekar tace"ya..ya..Omar,nifa wasa nake yi maka fa..."

  "Haka ake yin wasa a garinku?You are trying to kill me,and u are saying that it was a joke!"

   "Ya Omar,nima fa a wani Chinese film ne nagani,Na jakican,shi ne na kwaikwaya,"

   A ruɗe ya ɗago da kanta daga saman ƙirjinshi yace"Ke!ashe dagaske baki da hankali,saboda kawai kin kalli film kinga anyi haka sai kice nima zaki jaraba akaina?angaya maki cewa abunda ke cikin film dagaske ne?Su idan sunyi sun rayu,to ni idan kika yi mun kashe ni zakiyi,"

  Runtse idanuwanta tayi ganin yadda yake ta surfa mata faɗa,

  Tsagaitawa tayi da yin kukan da take yi"Am sorry Ya Omar bazan ƙara ba,"

  Harara ya ɗan watsa mata"kinfi kowa iya bada haƙuri,idan kikayi laifi kamar matar aure ta gari,"

  Murguɗa mashi baki tayi,lokaci guda ya samu kanshi cikin wani irin yanayi,zuba mata ido yayi yana kallon dress ɗin dake ajikinta,Jeans da t shirt sunyi matuƙar bin shape ɗin jikinta,jin yayi tsit yasa ta ɗan buɗe idanuwanta,ganin ya zuba mata ido ko ƙyaftawa baiyi ba,yasata fara tunanin kome yake kallo ajikinta,Ganin yana kallon ƙirjinta yasa tace"Ya Omar sun ƙara girma ko"?

Waro ido ya ɗan yi tare da cewa"Mekenan?"

Hannu tasa tana nuna mashi breasts ɗinta,

  "Ya salam,"ya furta hakan tare da ɗan rufe idanuwanshi yace"nifa,basu nake kallo ba,kayan jikinki ne suka burgeni,sunyi maki kyau sosai,"ya ƙarasa maganar tare da miƙewa tsaye yana kallonta,

   "Idan kana jin yunwa in kawo maka abinci"?tayi tambayar tana kallonshi,

   ɗaga mata kai yayi alamar eh,sannan yace"pls,inaso in ɗan kwanta in huta kinga baccin bai ishe ni ba,idan kika kawo mun Lunch ɗin,ki ajiyemun shi saina farka zanci,"

  Amsa mashi tayi da toh,kafin ta miƙe da sauri da sauri ta fuce daga ɗakin,saman gadon ya koma ya kwanta,bakomai bane ya faɗo mashi aranshi ba,fa ce maganar da suka yi da Major dangane da Junaid,hakanan ya dinga jin kamar yayi kuskuren barinshi ya wuce da motarshi,dama ya sani tun a time ɗin yasa security sun bi Bayan Motarshi...........



*Boss Bature*


Ƙarar shigowar Message,da ta ji ne yasa takai hannu tare da ɗaukar wayarta dake ajiye agaban mirror,yayin da take zaune asaman kujerar gabanshi,tana yin makeup,janyo wayar tayi tana karanta message ɗin daya bayyana akan screen ɗin wayar,

   _Abra,inason magana dake,amma bana so kowa ya sani,koda Aunty Laila ce_

  Mamaki ne ya kamata ganin anyi mata saƙo da new number,kowaye wannan,ɗaukar wayar tayi tare da miƙewa tsaye,a lokacin Aunty babba na cikin toilet tana yin wanka,


Arab gown ce ajikinta,pink colour abunka ga fara tass,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,fitowa tayi daga cikin bedroom ɗin nasu,ta miƙi hanya kamar zata fita daga corridor ɗin,Sai da ta bada tazara sosai,Sannan ta dannama numbar kira,tana fara ringing aka ɗaga,

  Tun kafin tayi sallama,taji muryar hayaam tace"ABRAH"!tun daga kan yadda ta kira sunanta yasa gabanta ya faɗi rass,

   "Aunty hayaam kece"?

Bata amsa mata ba,sae ma fashewa da tayi da kuka mai sautin gaske,hakan ya ƙara ɗagawa Abra hankali,a ruɗe ta shiga faɗin"Aunty hayaam meya faru dake ne?meyasa kike kuka?dan Allah kiyi mun bayani,"


On the other hand,Hayaam ta miƙa ma Amani wayar tare da cewa"kiyi mata bayani,"

  Gyaran murya Amani tayi tare da ambaton sunan Abra,

  Duk sunbi sun ɗaga mata hankali,muryarta har kerma takeyi wurin cewa"Dan Allah kuyi mun bayani,kun sanyani acikin duhu,"

  "Abrah!ki natsu ki saurareni,"jinjina kai abra ta shiga yi tana fadin"ina sauraranki Aunty Amani,meya faru ne naji Aunty hayaam tana kuka,

  Amani bata 6oye mata komai ba,game da abunda ya faru da hayaam da kuma guduwar Aunty babba daga asibitin,da kuma wasikar da ta bar mata,wasu irin zafafan hawaye ne suka soma gangarowa akan fuskar Abra,hankalinta a matuƙar tashe tace"Nashiga uku!kenan nima wata rana idan ƙaddara ta same ni,Aunty laila zata iya guduwa ta barni?

  Amani tace"ƙwarai kuwa!saboda bata da Imani kuma bata da tausayi,karki so kiga yadda na samu hayaam a asibitin nan a wulakance,kamar wadda tayi hatsarin mota amma a haka laila tabarta,saboda bata da amfanin da zata yi mata,To kema muddin kika kuskura kika bita wurin bokan nan rayuwarki ta faɗa halaka,Kuma wlh da zarar amfaninki ya ƙare a wurinta shikenan kin zama Waste product!Zata yi watsi dake ne,"jin wannan maganar yasa Abra ta fashe da matsanancin kuka,wani irin tsoro ne ya kamata,don Aunty babba ta zama abun tsoro a wurinta,ta girgiza da jin rashin imaninta,

Da gangan Amani ta dinga tunzura abra don ta tsoratar da ita akan karta goyi bayan Aunty babba suje wurin bokannan,

  "Abra!ina ƙara jan kunnanki,karki kuskura ki bi ta,Kiji tsoron Allah,ki tuna cewa wata rana zaki koma gare shi,kada kiyi silar da za'a cutar da rayuwar wasu,Aunty laila bata da Imani,tanaso ta jefa rayuwarku cikin haɗari ne,kuma tana yin amfani da ku ne don ta cimma burinta,kuma da zarar amfanin ku ya ƙare a wurinta,zata yi watsi daku ne,ta kama gabanta,Ga hayaam nan dai yanzu ta gane kuskuren da tayi,tana mai dana sanin abunda ta aikata,"

  Amani nakai ƙarshen maganarta,ta miƙa ma hayaam wayan"kiyi mata magana,"

  Kar6ar wayar hayaam tayi tare da karata a kunnanta,Kukan da Abra keyi har cikin zuciyarta,dama tasan dole taji raɗaɗin acikin zuciyarta,ɗan uwa ba wasa ba,

  Cikin Sanyin murya tace"Abra,baki ga yadda na koma ba,bani da wani abu daya rage na ƴa mace a jikina,komai ya lalace,Yanzu ma bana jin kaina amatsayin mace,"

  Wani sabon kukan Abra ta ƙara fashewa dashi,cikin shessheƙa tace"Aunty hayaam wlh bazan bi ta ba,sai dai taje ita kaɗai,Ashe ba son mu take yi ba,bata ɗauke mu abakin komai ba,Amfani kawai take yi damu don ta cimma burinta,Ni wlh bansani ba Aunty hayaam,harfa tambayarta nayi ina kike amma tace mun wai batasan inda kika tafi ba,kinacan kina yawon gantali,Ashe kina gadon asibiti rai hannun Allah,yanzu haka fa da nake yin maganar nan,tun jiya muka iso Enugu da ita,Yanzu haka ma shirin zuwa wurin bokan muke yi,

  Hayaam tace"Abra,ki natsu ki saurare ni,kada ki bari tasan da shirinki naƙin binta wurin boka,saboda bata da imani tana iya kasheki,in kika 6ata mata rai,Abunda nake so dake shi ne,Duk wani kuɗi dake a wurinta,ki tattarasu gaba ɗaya ki sanyo su acikin jakarki,muguwar rabi da kwata na kuɗin dake a hannunta nawa ne,amma saboda tsabar rashin Imani ta kwashe hada nawa ta gudu dasu,"

  Jinjina kai Abra tayi yayin da take share hawayenta,

  "Aunty hayaam,yanzu tana acikin toilet,bari nayi sauri na tattara kayana,in biyo mota in dawo nan,"

  Hayaam tace"Yawwa,kiyi sauri kada fa kiyi kuskuren da zai sa ta gane cewa guduwa zakiyi ki barta,".  

  "In sha Allah bazan bari ba,"

.daga haka su kayi sallama,


Ajiyar zuciya hayaam ta sauke tare da kallon Amani dake zaune gefen gadon,tace"Har hankalina ya kwanta,So nake Aunty laila ta ɗanɗani kuɗarta,taji irin raɗaɗin dana ji acikin zuciyata,

  Murmushi Amani tasaki,tare da cewa"Nafi ki jin daɗi Hayaam,A shirye nake dana taimaka muku wurin ganin kun gyara rayuwarku,"acikin ranta kuma tace"Ita kuma waccen bijimar,Sai nasa ta tsani kanta,duk wani makusancinta saina kwace shi ya dawo a ƙarkashin ikona,So nake ta gane kuskuran da ta aikata arayuwarta,"


A 6angaren abra kuwa,tun bayan da suka kammala yin wayar,jiki na rawa ta koma Room ɗin nasu,A hankali ta tura ƙopar ta fara leƙawa ciki,don taga ko ta fito daga wankan,Ajiyar zuciya ta sauke,ganin bata fito ba,da sauri ta faɗa cikin ɗakin,Jikinta sai kerma yake yi,asaman bedside drawer,ta samu jakar Aunty babba,hannu tasa ta ɗauki handbag ɗin,tare da zagayawa ta Other side ɗin ta ɗauko ƴar purse ɗinta,saboda tsabar sauri jin Aunty babba na motsi kamar zata fito daga cikin toilet ɗin,aikuwa a gigice ta buɗe ƙopar ɗakin ta fuce,da gudun gaske,mutanen dake kai komo a cikin hotel ɗin sai kallonta sukaye,wasu kallon burgewa suke yi mata saboda rigar jikinta,ba ƙaramin kyau tayi mata ba,gashi bata sanya mayafi akanta ba,ƙafafunta ko takalma babu,


Hankalinta bai kwanta ba,har sai da ta fito daga cikin hotel ɗin,gudu gudu sauri sauri ta miƙi hanya tana tafiya tana waiwayon bayanta kada ace Aunty laila ta biyota,Masu motoci sai parking sukeyi agabanta suna yi mata tayin shiga motarsu,amma taƙi sauraron kowa saboda gudun kada wani ya cutar da rayuwarta,kamar yadda aka yiwa Hayaam,baiwar Allah ta tsorata sosai,gashi babu wanda ta sani a garin,haka bata san ko ina ba,ba ƙaramin galabaita tayi ba,


    *Koya Abra zata ƙare?Shin ina Aunty Babba dake a cikin toilet tana wanka?Batasan an yashe ta ba*


*Boss Bature*


   ❤🤍❤


Kano state


Wuraren ƙarfe 6 na marece,Slowly motocin Sgr suka shiga cikin unguwar batare da jiniya ba,saboda patient ɗinsu da suka ɗaukko,a back seat na motar Abusufyan suka kwantar da ita,Abusufyan shi ne ke driving ɗin motar,fuskarnan tashi a washe,kamar wanda aka yima Albishiri da Gidan Aljanna,Sehrish na agefenshi sae faman sakin murmushi take yi tana waiwayawa,bakinta yaƙi rufuwa,a ƙagare take dasu ƙarasa gidan,ko ta samu ta kira sauran ƴan uwa ta sanar dasu cewa An samo Oummansu,


Bayan motar su Abusufyan Motar dake ɗauke da Baban Sadeeq ce,tare da Maman Sadeeq,ɗaya daga cikin motocin Sgr ne,wanda wani soja ke driving ɗinsu,

Mamaki yaƙi barinsu,musamman Maman sadeeq,abun ya ɗaure mata kai har tagaza rufe bakinta,

Kasa kasa tace "Baban Sadeeq kaga wani iko na Ubangiji"?

  Murmushi Baban sadeeq yayi tare da kallonta yace"dama ae naji ma ina sanar dake cewa,Allah yana tare dasu,kuma shi zai kula da abunshi,Yau nasan kin shaida maganata,"

Murmushi ta saki tunawa da wannan kalami na Baban sadeeq,a duk lokacin da ta rufe shi da faɗa kan cewa sunƙi ɗaukar mataki akan Ya sayyadi,yana ta cutar da bayin Allah,an zuba mashi,sai babban sadeeq yace mata"Bazan iya tunkarar mutumin nan ba,Mutumin da kana ja mashi ayar ƙur'ani yana fassara maka?taya zan iya tunkararshi?in dai akan yara ne Allah yana tare dasu,Kuma shi zai kula da abunshi,"

  "Amma gaskiya Baban sadeeq,nayi matuƙar mamaki,har yanzu fa ji nake yi kamar mafarki nakeyi wlh,wai yanzu waɗannan danginsu rishi ne?bayin Allah,wlh na tayasu murna sosai,"

  Baban sadeeq yace"Ni ji nake kamar nafi kowa farin cikin wannan ranar wlh,Alƙawarin dana ɗaukarwa kaina,Ya cika yau ga abu ga Ƴa'ƴanta,ga kuma danginsu,Godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata'ala,"


A bayan motarsu dasu Baban sadeeq suka,Motar dake biye da tasu,nurse ce ɗaya tare da Dr,An zo dasu ne don a nuna masu gidan,Saboda sune zasu ci gaba da zuwa suna duba lafiyarta,security guards sun sanya motocinsu a tsakiya,gaba da baya duk motocin Soldiers ɗinne,Sgr baisamu ya biyo bayansu ba,Sun wuce Hotel shi da Armstrong,


A parking space suka tsayar da motocin nasu,fitowa Abusufyan yayi tare da zagayawa ya buɗe gidan baya,Hannu yasa ya kinkimo abu,tare da azata asaman kafaɗarshi,gaba ɗaya suka kama hanyar shiga cikin falon gidan,tun kafin su shiga ciki sehrish ta fara ganin canji alamun kamar anyi gyara acikin gidan,shi kanshi Abusufyan yayi noticing hakan,


Main palour ɗin suka shiga,Nan fa suka sha mamakin ganin an canza Sofa set ɗin falon izuwa sababbi,Hatta ƙasan falon wani jigunannan carpet ne aka shimfiɗa ya mamaye ko'ina,ga wani irin sanyi na A.c dake ratsa ko'ina cikinshi,Abun ya ɗaure masu kai,

   "Abba kodai munyi mistake ne"?Sehrish ce tayi maganar,

  "Ba kuskure mu kayi ba sehrish,ni kaina nayi mamaki,daga gani aikin Sgr ne,Shi ya sanya aka gyara gidan,dama ina ta fargabar awani wuri zamu aje Oummanku"yayi maganar,a yayin da suke tunkarar Bedroom ɗin abu,ciki ya shiga da ita,nan ma an sanya A.c ɗin,daga gani duka gidan aka gyara,hatta furniture ɗin duk an canzasu,Naira tayi aiki daga safe zuwa maraice gidan ya koma tamkar na amarya,amaryar ma yar masu fada aji,a hankali ya kwantar da ita saman gadon,wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙare mata kallo cikin zuciyarshi kam hamdala yake tayi,

  Sehrish dake tsaye tana kallon fuskar Oumman tasu,sae faman sakin murmushi takeyi,ji take kamar ta faɗa jikinta ta rungumeta sosai,'

  Sehrish ki zauna gefenta,bari na fita wurinsu Baban sadeeq,mun barsu a palour,"yayi maganar tare da miƙewa ya fuce daga ɗakin,

  Wuri Sehrish ta samu daga gefen gadon ta zauna,tana kallonta,

  "Allah ya baki lafiya Oummanmu,Nasan zakiyi farin ciki sosai,idan kika ga yadda ƴan ukunki suka koma,Ashe da rabon mukai wannan lokacin araye,mu dukkanmu"?hawaye ne suka soma saukowa daga saman fuskarta,kwantar da kanta tayi daga gefen Oumman,ta sanya hannunta tare da ruƙo nata,


Lokacin da Abusufyan ya koma palourn,A zaune ya samu Malam Nura tare da Maman sadeeq saman 3 seater,Nurse ɗin kuwa tana zaune saman 2 seater ita da Doctor,


After few minutes da shigarshi palourn,Sae ga wani Soja ya shigo hannunshi ruke da manya manyan ledoji na restaurant,A bayanshi kuma wani sojan ne hannunshi ruke da Katan katan na lemunsha,Saboda tsabar farin ciki,bakin Abusufyan yaƙi rufuwa,dama tunanin da yake yi kenan,gashi sun shigo da baƙi kowa ya kwaso yunwa gidan kuma ba wani abunsha,Balle abinci,

   Ƙarasowa ciki sukayi tare da ajiye kayan a tsakiyar palourn,

   Atare suka haɗa baki wurin cewa"Sgr ne,yace a shigo maku dashi,zaizo anjima,"

  Murmushi Abusufyan ya ɗan saki tare da cewa"Okey,mun gode sosai,Allah ya kawo shi lafiya,"

Juyawa su kayi atare suka bar ɗakin,


  Sehrish ya kira,ta ɗauki ledojin takaisu kitchen,acan ta haɗo masu kayan abincin A cikin warmers ta jerasu a saman tray,Saman dining table ta jera masu su tare da drinks,Gaba ɗaya nan suka harhadu,dama kowa ya kwaso yunwa,don sun jima a asibitin nan,Nan fa kowa ya shiga ɗurama cikinshi abinci,bayan sun ci sun ƙoshi,daga bisani,wuraren sallar magrib,Nurse ɗin tare da doctor su kayi masu sallama,


Abusufyan ne ya ɗauko su acikin motarshi tare da Baban sadeeq saboda zasu wuce masallaci daga nan,'



Tun bayan da ta kammala sallar magrib,ta koma saman gadon Oummasu ta zauna tana kallonta,a ƙagare take da ta farka duk da tasan cewa,ba a hayyacinta take ba,batasan wacece ita ba ayanzu,

  "Yakamata in sanarwa su Jahad da hosana,"tayi maganar cike da zumuɗi ta dauki wayarta dake ajiye gefenta,

  Contacts ta shiga,tare da lalubo numbar jahad ta danna mata kira,Kusan sau uku tana ringing ba'a ɗaga ba,hakan yasa ta tura mata text message,

   Layin hosana,ta kira itama wayar bata a kusa da ita,tayi ringing harta katse ba'a ɗaga ba,

  Yanke shawarar kiran junaid tayi,cikin rashin sa'a ta samu wayarshi a kashe,

  Tur6une fuska tayi ranta a 6ace,taso ace itace zata fara yi masu albishirin ganin Oummansu,Amma duk sun ƙi ɗaga kiran wayarta,

  Yunƙurawa ta ɗan yi saitin fuskar Oummansu,ta ɗauketa photo da camera ɗin wayarta,kusan hoto uku tayi mata,

ta whatsapp ta tura masu hotunanta,'



Motsin mutane taji acikin palourn,ranta ya bata cewa Su Baban sadeeq ne suka dawo,bata leƙa ba,kwanciya tayi a gefen oummantasu,


Su biyu suka shigo cikin palourn,zama sukayi saman sofas ɗin suna fuskantar juna,Abusufyan yace"Bamu da wasu kalmomi da zamu iya amfani dasu wurin gode maku,kunyi matuƙar yin ƙoƙari,kun kula da rayuwar abu,tamkar ƴar cikinku,kun damu da ita sosai,Allah ne kaɗai zai iya sakamaku,"

  Baban sadeeq yace"duk yiwa kaine,idan ka taimaki rayuwar wani kaima Allah sai ya taimaki ta ka,Naji daɗi sosai,kuma nayi matuƙar farin ciki,daya kasance kaine Mijin Zainab duk da an shiga tsakaninku,kuma mahaifinsu sehrish!hankalina ya kwanta sosai,Abu zata rayu atare da mijinta ga kuma ƴa'ƴanta,uwa uba kuma ga dangin mijinta,Allahu Akhbar,najiye mata daɗi,ƙarshen wahalarta yazo da yardar Allah,"

  Murmushi Abusufyan yayi tare da cewa"Amma malam,Ya maganar sayyadi ne!?ko kuna da labarinshi"?

  Shiru Malam nura ya ɗanyi na wani lokaci yana tunani kafin yace"Ae Sayyadi tun ranar da aka nemi abu aka rasa,tun daga ranar bamu ƙara sanyashi a idanuwanmu ba,gidan ma a garƙame muka same shi da ƙaton ƙwaɗo,". 

  dakatawa yayi da yin maganar,

Hakan yasa Abusufyan cewa"dama nasan bazai tsaya ba,guduwa zai yi,"

  Girgiza kai Baban sadeeq ya ɗan yi tare da cewa"A'a,bana tunanin ya gudu,Munafukin duk inda yake yana acikin garin nan!yanzu haka ba mamaki yasan da zuwanku!ae ba ƙaramin shu'umin mutun bane,"

  "Amma taya akai kasan cewa,yana acikin garin nan?ko kun ƙara haɗuwa dashi ne"?acewar Abusufyan,

  Baban sadeeq yace"ƙwarai kuwa!Kama tuna min!ae can shekarun baya lokacin da aka nemi abu aka rasata,fitsararran ya tako da waɗannan ƙafafuwan nashi masu kama dana zabbi har ƙopar gidana,

  Lokacin na dawo daga sallar asuba,na shiga da mashin cikin gida,nadawo zan rufe ƙopa kenan ina ƙokarin rufewa,Naji an banko mun ƙopar,A firgice na kai idanuwana wurin don inga wani taƙadirinne!aikuwa sai nayi tozali dashi,A tsaye ruƙe da qugu,nan fa nashiga faɗin A'uzubillahi minasshaiɗanir rajim,"sai cewa yayi"Ni ne shaiɗanin"?nace mashi "to ae baku da bambanci da shaiɗan,ƙahonne kawai ke babu!shin me ma yakawo ka ƙopar gidana?ko kazo ne kayi mun futsarar taka daka saba ne?sai yace mun saƙo ne yazo dashi,nace saƙo kuma?yace mun eh,yasa hannu cikin aljihun jallabiyarshi ya zaro wata ƴar doguwar takarda,ya miƙo mun tare da cewa"Saƙon Abu ne,idan mun sameta,A bata wasiƙar," jin cewa sakon na abu ne yasa na amsa,to tun daga wannan lokacin da ya haura ƙafa,ban ƙara sanya sayyadi acikin idanuwana ba,hatta makarantar islamiyyar da muke koyawa atare dashi,ya daina zuwa...."

  Lokacin da ya kai ƙarshen labarinshi,Abusufyan yace"Amma kun karanta wasiƙar"?

  Baban sadeeq yace"A'a,babu wanda ya ta6a ta,Ae amana ce,yace wasiƙar ta abu ce shiyasa bamu karantata ba,"

  A ƙagare Abusufyan yake daya ga wannan wasiƙar,

   "Yanzu wasiƙar tana ina ne"?

"Tun lokacin dai,bayan tafiyar sayyadi,dana shigo cikin gida,kaitsaye wurin Maman Sadeeq na wuce,ita nabawa ajiyar wasiƙar," 

  Ajiyar zuciya Abusufyan ya sauke,

  "Gobe,in Allah ya kaimu,sai muje gidan a ɗauko wasikar,yau dai anan zaku kwanan mana,"acewar Abusufyan,

   "Akwai yaronmu fa,mun barshi a gida,"Baban Sadeeq ne yayi maganar,

   "idan mun fita yin sallah,sae mu dawo tare dashi," acewar Abusufyan

  Suna cikin tattaunawar nan aka kira sallar isha'e,atare suka fita yin salla daga can zasu wuce gidan,Su ɗaukko Sadeeq,


Fitowa Sehrish tayi daga Bedroom ɗin Oummansu,wuraren ƙarfe 8:30 na dare,a palour ta samu Maman sadeeq zaune,jikinta sanye da hijabi,

  Tana ganin Sehrish ta mike,tare da tunkararta,

  "Rishi,zonan mana,baki bani labarin ya kuka ƙare ba,bayan kun bar nan"tayi maganar tare da ruƙo hannunta,saman 3 seater suka zauna,

  Nan fa Sehrish ta shiga bata labarin rayuwarsu,tun daga lokacin da suka koma katsina  har ƙarshe,jikin Maman Sadeeq ba ƙaramin sanyi yayi ba,jin irin wahalar da suka sha,ta wani 6angaren kuma ba ƙaramin farin ciki tayi ba,  


sun jima suna firar yaushe rabo,kafin suyi sallama kowa ya wuce ɗaki,don ba ƙaramar gajiya suka kwaso ba,


Koda Sehrish ta koma ɗaya daga cikin bedrooms ɗinsu da aka gyara masu,wanda ke a upstairs,toilet ta shiga don ta watsa ruwa ajikinta,kafin ta kwanta,Maman sadeeq kuma a downstairs ta zauna,ɗakunan su Dr haris a lokacin baya,

   fitowa tayi daga cikin toilet,jikinta sanye da undi ta ja shi har saman kirjinta,ƙarasawa tayi gaban gadon,inda ta ajiye kayan baccin da ta dauko don ta sa,tare da phone ɗinta,

  Tana ƙoƙarin kai hannu ta ɗauki wayar,Ta jiyo sautin dirar mota acikin gidan,

  "Su Daddy sun dawo kenan"tayi maganar tare da ɗaukar wayar,Har lokacin fuskarta ɗauke da murmushi,bakinta fa ya ƙi rufuwa tunda aka samu Oummansu,babban burinta yanzu bai wuci Oummansu ta dawo cikin hayyacinta ba,waƙa ta kunna ta ƙure Volume,Nan fa ta shiga yin rawa,kamar wata zautacciya,juyi ta dinga yi,iska na kaɗa gashin kanta,duk cikin farin cikin ne,yaushe rabon da tayi dancing irin haka harta manta,dama can ita ba ma'abociyar yin rawa bace,duk da tana son yin rawar,yanayin rayuwane yasa bata samu wannan damar ba,a hankali ta soma bin wakar abakinta,

 _rawa da girgiza zanyi gabanka,in jujjuya,zanyi maka albishir kayi dace da mai tarbiyya,sannan zan zame maka farin ciki na nan gidan duniya,Nafi kowa saninka acikin abunsha kafi son coffee_

  Bata ƙarasa baitin ba,ta tsaya cak sakamakon mutun da ta hango tsaye ta cikin mirror,ya goya hannayensa asaman wide chest ɗinshi,gabanta ne ya faɗi rass,lokaci guda ta shiga taitayinta,duk tabi ta kame kanta kamar wata mara gaskiya,


Bakowa bane fa ce Sgr,still dress ɗin ɗazu ne ajikinshi,tun lokacin da ta fara rawar yazo ɗakin,kuma ta hanyar kiɗan wakar da ta kunna ne yasa ya gane cewa akwai mutun a ɗakin,dama kuma ita yake nema saboda ya tayata Murnar ganin mahaifiyarta,


tsayawa su kayi suna kallon juna ta cikin mirror,kunya duk ta rufe ta,saboda ɗan undi ɗin dake ajikinta sharara yake,gashi ko bra bata sanya ba,


Slowly ya soma takowa izuwa cikin ɗakin,da sauri Sehrish ta nufi wurin gadon tana ƙoƙarin ɗaukar Kayan sawarta,da ta ajiye asaman gadon,

  Sai dai kafin tayi wani yunƙuri tuni Sgr ya ƙaraso wurin,at same time suka kai hannu saman kayan nata gabanta ne ya faɗi rass,yayin da take kallon hannunshi da ya ruƙo rigarta,a ɗan razane ta cire hannunta tare da ɗan ja da baya tana kallonshi,

  ɗagowa yayi hannunshi ruke da kayan sawar nata yace"Me zaki yi dasu"?

 Muryarta na kerma tace"Am..um..sanyawa..zanyi,'

  Da buɗar bakinsa sai cewa ya yi"bayan na kammala abunda zanyi kenan"?

  Gabanta ne ya kuma faɗuwa,throwing ɗinsu yayi saman gadon,gadan gadan ya tunkareta,jiki na rawa ta shiga ƙoƙarin ja da baya,muryarta na rawa tace"Dan Allah babban yaya kayi haƙuri,wlh bazan ƙara tafiya ba,without ur permission nasan nayi maka laifi,"ita duk a tunaninta,yazo ne ya yanke mata hukunci,saboda zuwan da tayi kano batare da saninshi ba,

  "Am sorry Ya Rafayet.."wani irin kallo yake bin ta dashi,wani canji ya fara gani ajikinta,kaitsaye take fisgarshi,sai ƙokarin motsa lips ɗinsa yake yi don ya sanar da ita cewa,ba hukunta ta yazo yi ba,yazo ne don ya tayata murna,Amma ina,sam ya kasa furta hakan,duk zufa ta gama wanke mata fuska,har idanuwanta sun cicciko tab da kwalla,

  Hannayensa ya sanya asaman belt ɗin wandon jikinshi,Waro ido waje Sehrish tayi,hankalinta yayi mugun tashi,tsoronta kar ace bugunta zai yi,

  Fashewa tayi da matsanancin kuka,tare da aza hannunta asaman kanta,tana faɗin"Innalillahi,wayyo Allah na,"

   Da gangan Sgr yake zame belt ɗin wandonsa,duk don saboda ya ƙara ruɗar da ita,lokacin da ya ƙare zare belt ɗin daga jikin wandon ya curoshi yana nannaɗe shi a hannunshi,A matuƙar tsorace sehrish ta juya da nufin ta gudu,Da ƙarfi ya kai hannu zai ruƙo undi ɗin jikinta,aikuwa gaba daya,Ya zame undi ɗin daga jikinta ya sulale,kasa gashi bata sanya komai ba,babu pant bare bra,saboda tsabar kiɗima,fasa ƙara tayi sosai ta fashe da kuka,tare da ƙanƙame ƙirjinta da hannuwanta,bangon ɗakin ta ƙankame jikinta na kerma,

  Duk wannan budirin da akeyi babu wanda yasan meke wakana,saboda sun yi nesa da downstairs,

  Rumfa yayi mata da faffaɗan ƙirjinshi,ya lullu6eta sosai,nan take taji wata irin natsuwa tazo mata,daddaɗan ƙamshin turarenshi ne ya mamaye hancinta,lokaci guda ta nemi kukan da takeyi tarasa,

  "Ain't trying to flog u,"ya furta hakan da wata irin kasalalliyar murya,saboda tsabar rawar da jikinta keyi,har a jikinshi yake ji,

  duƙo da kanshi yayi dai dai saitin wuyanta,slowly ya manna mata kiss,har cikin zuciyarta taji wannan kiss ɗin nashi,kafin tayi wani yunƙuri,taji tafin hannunshi asaman ass ɗinta,laushin fatar wurinne ta soma fisgarshi,har ya fara shafata yana matsarta,almost 3 mins kafin ya zame hannun daga wurin,ya zagayo dasu ta front ɗinta,sosai yayi tighting ɗin ta ajikin wall ɗin kamar zai mayar da ita,cikin cikinshi,lokacin da taji hannunshi saman gabanta,gaba daya tabi ta susuce,ta shiga ƙoƙarin kufce mashi,ruƙon da yayi mata ne yasa ta kasa yin hakan,sosai ya shiga shafa wurin before ya janyo tafin hannun nashi izuwa saman ƙirjinta,duka hannunshi biyu ya sanya,duk irin girman tafin hannunshi,sai da boobs ɗinta suka cika su fam,har babu space,damƙarsu yayi sosai tare da runtse idanuwanshi saboda wani irin yanayi da ya fara tsintar kanshi aciki,muryarshi na kerma ya ambaci sunanta"Reesh.."for the first time da Sgr ya fara furta sunanta,tunda take yi mashi aiki bata ta6a jin ya ambaci sunanta ba,tamkar baima san sunanta ba,sosai ya cusa hancinshi acikin lallausar sumar kanta,batare da ya saki ƙirjin nata ba,da alama fa Sehrish suman tsaye tayi,gaba ɗaya sun shiga cikin wani irin yanayi mara misaltuwa,sautin kiɗan da sehrish ta kunna ne ya ƙara jefasu cikin wani yanayin na sha'awar son kasancewa da junansu,Taken waƙar Love Nwantiti ya shiga,baka jin komai sai sautin breathing dinsu dake fita da zafi zafinshi,yayin da heart ɗinsu ke beating very fast at same time,tamkar zata 6allo daga ƙirjinsu,Ya salaam!


*Boss Bature*


A 6angaren su Junaid kuwa,sunsha yawo shi da Jahad,wuraren 8 suka kamo hanyar zuwa gida,bacci cike da idanuwansu,driving yake yi slowly kamar baison yin tuƙin,

   Muryarshi tamkar zai yi kuka yace"Jahad,mun ci komae amman bafa musha ice cream ɗin ba"

   "Mu haƙura Junaid,hankalina ya koma kan gida,dare yayi yakamata ace tun 6 muna a gida,"

..."Jahad,nidai inaso nasha,na kuma baki,saboda shi na fito ma ni,"

  "Asthma fa gare ka,ko ka manta ne?ni bazan so abunda zai cutar mun dakai ba,"

    Tana kai ƙarshen maganar taji,ya dakatar da motar a gefen titi,

  Juyawa tayi tare da kallonshi,tun kafin ta tambayi dalili yayi saurin cewa"Ga mai ice cream can tsallaken titi,ki jira ni a mota yanzu zanje nadawo,if not wlh bazan yi driving ɗin ba,"zuba mashi ido tayi tana kallonshi,

  Ashagwa6e ya kuma cewa"kin yi shiru baki ce komai ba,

  Murmushi ta ɗan saki tare da cewa"Kada ka damu my Romeo tunda kana so,Ni zanje na siya mana ice cream ɗin,ka jira ni a mota,naga kaman bacci ma kake ji,yanzun nan zan dawo,"ta ƙarasa maganar tare da ruƙo ƴar purse ɗin ta,

  Tana ƙoƙarin fita daga motar,taji ya ruƙo rigarta,tsayawa tayi cak,hakanan ta dinga jin zuciyarta nayi mata wani irin bugu mara daɗin ji,

   Juyowa ta ɗan yi tare da kallonshi,lumshe idanuwanshi yayi tare da buɗesu,da wata irin murya tamkar bata shi ba,ya furta mata"I LOVE U SO MUCH,"

  har cikin zuciyarta,taji wannan kalamin nashi,dawowa tayi kusa dashi,tare da tallabo fuskarshi ta manna mashi kiss a gefen fuskarshi,tana ƙoƙarin janye la66anta,ya ruƙo waist ɗinta sosai,tare da haɗa bakinsu wuri guda,a susuce suka shiga kissing ɗin junansu sosai,almost 10 mins,kafin jahad ta janye jikinta daga nashi,da sauri ta buɗe murfin motar,ta fita daga cikinta,


Tsallaka titin tayi tana tafiya tana waiwayon motarsu,wurin mai ice cream ɗin taje,mutun huɗu ta samu a tsaye suna jiran ya zuba masu,hakan yasa ta ɗan tsaya tana jiran a sallamesu itama a bata nata,

  "Jahad,"Junaid ne ya kwala mata kira,daga cikin motar,da sauri ta juya tana kallonshi dayake akwai hasken Street light daya haskaka titin,

  ɗago mata hannu yayi fuskar nan tashi ɗauke da ƙayataccen murmushi,dimples ɗinshi sun lotsa sosai,

 Murmushi ta sakar mashi itama,sai faman kallon juna suke yi,

..."madam guda nawa za'a baki ne"?muryar mai siyar da ice cream ɗin ce ya katse ta,juyawa tayi tare da kallonshi tace"Guda biyu nake so,"

  Yana cikin zuba mata Corn Ice cream ɗin,ƙarar truck ta karaɗe wurin,Wata jibgegiyar mota ce,gadan dagan ta tunkari motar da junaid ke ciki,

  Adai dai lokacin mai ice cream ɗin ya sallameta,har ta biyashi kuɗin,tun kan ta juya mai ice cream ɗin nan ya furta"Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un!"a wani firgice jahad ta juya don taga menene ke faruwa,Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,A gigice ta fasa wata irin ƙara mai sautin gaske lokaci guda tayi wurgi da ice cream ɗin dake a hannunta,A zabure ta tunkari wurin da motar junaid take,Sai dai kash ƘADDARA TA RIGA FATA,

  Don tuni Motar nan,tabi ta kan motar junaid,Gaba ɗaya ta danne motarshi,tayi mata rugu rugu,

 Da gudun gaske mutane suka taru a wurin suna faman ambaton INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIRRAJI'UN!!!😭😭😭😭


*kullu nafsin za'ikatul maut*

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




SADDEST MOOD,


THE Greatest Lost,


Gingimarin motar nan,na sauka daga kan Motar junaid,drivern dake tuƙinta ya fusgeta da gudun gaske ko waiwaye babu,kafin mutane suyi wani yunƙuri motar junaid ta kama ci da wuta tamkar Bomb ne ya fashe a cikinta,


Wata irin razananniyar ƙara jahad ta fashe da ita,cikin fitar hayyaci ta nufi motar zata faɗa ciki,Mutane duk suka rurruƙeta,kuka takeyi kamar ranta zai fita,idanuwanta sunyi jawur dasu,jijiyoyin wuyanta duk sun firfito waje,Cizo da yakushi ta dinga kaiwa hannun mutanen dake rurruƙe da ita,muryarta adisashe take fadin"Junaid!yana cikin mota!dan allah kada ku bari na rasa shi!dan Allah ku ciro mun ɗan uwana!ina jin sautin kukanshi acikin kunne na,Dan Allah kutaimakeshi wuta tana ƙona sassan jikinshi........"tana kai ƙarshen maganar,ta yanke jiki ta faɗi asume,Mutane sunyi ƙoƙarin kashe wutar amma sai dai kash babu ruwa a kusa,lokacin da motar ƴan kwana kwana ta ƙaraso,tuni Motar junaid ta ƙone ƙurmus,Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!


Motocin Ƴan sanda ne suka zagaye wurin,tare da ƴan kwana kwanan,sun kashe wutar dake ci a motar tashi but unfortunately,basu samu komai ba dangane da junaid,domin kuwa ya ƙone ƙurmus,sai dai toka,wa'iyazubillah,


 Ƴan sandan Sun samu bayani a wurin mai siyar da ice cream ɗin nan,saboda agabanshi komai ya faru,kuma shi ne ya kira Police men ɗin,da kuma motar kwana kwanar ya basu address ɗin wurin,


A bincikensu sun gano cewa,koma waye da gangan ya aikata hakan,saboda guduwar da yayi batare da ya tsaya ba,

  Ambulance suka kira,aka shigar da jahad cikin motar,kai tsaye suka wuce da ita,asibiti,

   Cigaba da bincike ƴan sandan sukayi,ko'ina na wurin suka shiga dubawa,Anan suka samu ƴar purse ɗin jahad,tare da takalmanta,sae kuma ice cream corn ɗin da tayi wurgi dashi,

..wani Inspector ne ya ɗauki,purse ɗinta,ya zaro wayarta,dake ta ringing acikin jakar,Duba screen ɗin wayar yayi,Sunan Ya Omar ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,picking Call ɗin yayi yasa ta Hands free tare da kara wayar a kunnansa,

  "Jahad kuna ina ne!har yanzu baku dawo gida ba?nayi trying number ɗin Junaid,but na same ta a kashe," runtse ido ɗan sandar yayi,jikinshi ba ƙaramin sanyi yayi ba,

   "Jahad!"Omar ne ya sake kiran sunanta,

  Sai lokacin inspector ɗin yace"kana magana da Inspector Mukhtar ne!yarinyar da ka kira wayarta,yanzu haka an wuce da ita asibiti ne,sakamakon motar da suka hau tare da ɗan uwanta,ta hadu da hadari......"


Saboda tsabar kiɗima,marshal Omar  dake tsaye gaban mirror baisan lokacin da ya saki wayarshi ba,ta faɗi ƙasa,idanuwanshi azazzare yake kallon kanshi ta cikin mirror ɗin gabanshi,tuni jikinshi ya soma kerma kaf kaf kaf,

  Saboda tsabar kiɗima hanyar fita daga dakin ya nufa daga shi sai short ajikinshi,sae da ya ruƙo handle ɗin kopar sannan ya tuna cewa babu kayan mutunci a jikinshi,komawa yayi a hanzarce ya ɗauko jallabiya ya zura ajikinshi,sannan ya dauki wayarshi,

  Gudu gudu sauri sauri haka ya nufo downstairs,Mojar ya kira a waya tunkan yabar falon,ya sanar dashi cewa,An samu matsala su kasance cikin shiri zasu fita,


Da gudun gaske,motoci goma sha biyar na sojoji suka fuce daga cikin gidan,tare da wata irin jiniya mai sautin gaske,


Tracking layin Jahad su kayi har suka ƙaraso inda Motar junaid take,tunkan su fito daga cikin motar jikin kowannansu,yayi mugun sanyi,


A wani irin sukwane marshal Omar ya fito daga cikin Motar,da sauri mutane suka dinga darewa suna basu hanya don su wuce,Lokacin daya ƙarasa wurin da motar junaid take a ƙarmashe,ta lanƙwashe ta dagargaje,Jikinshi a mace ya zube saman guiwowinshi,komai ya tsaya mashi cak!tsit kake ji,

  Girgiza kai ya shiga yi da wata irin razananniyar murya ya shiga faɗin"innallillahi wa'inna ilaihirraji'un"!hannu yasa ya damƙi tokar dake a ƙasan wurin,Nan take ya fashe da wani irin matsanancin kuka,hawaye ne suka soma gangarowa asaman fuskarshi Major dake tsaye akansa,haka zalika sauran Soldiers ɗin dake a wurin kowannansu,idanuwansu cike taf da hawaye,tunda suke a rayuwarsu basu ta6a ganin hawayen Marshal ba sai yau,

   Cikin shessheƙar kuka ya furta"ku faɗamun meya faru dasu?ina ƙanina yake?Ina jahad"?

  Daƙyar ɗan sandar nan ya iya buɗe baki yace"Yalla6ai,A bayanan da muka samu a wurin mai siyar da ice cream ɗin da yarinyar taje,Sun tsayar da motarsu a bakin titin ne,ita yarinyar itace ta fito daga cikin Motarsu,tabar shi Yaron acikin Motar,ta tsallaka titi,kafin ta dawo ne,babbar mota tabi takan Motar,nan take kuma ta kama da wuta,koda muka iso bamu samu komai daga sassan jikinshi ba,

   Hannu Marshal Yasa ya tallabe kanshi,saboda wani irin jiri dake ɗibarshi,sai faman ambaton innalillahi wa'inna ilaihirraji'un yakeyi,Yanke jiki yayi ya faɗi ƙasa a sume,

 "yalla6ai!"major ne ya ambaci sunanshi da ƙarfi,tare da zuƙunnawa agabanshi,

  Suna cikin wannan alhinin saiga Motar journalists ta ƙaraso wurin,aikuwa tun kafin ma su sauko daga cikin motar,sojojin nan suka koresu daga wurin,a hanzarce suka ja motarsu suka koma,


  Sau uku suna yayyafa mashi ruwa,yana sake sumewa,hakan yasa suka cuccu6eshi izuwa cikin Motarsu,don su wuce dashi asibiti,


Jami'an ƴan sandar nan,sunyi ƙoƙari wurin ganin sun gano yadda abun ya faru,har street Cctv aka bincika,amma kash Camera ɗin ta jima da samun matsala,

  *Allah yajiƙan junaid,ya gafarta mashi,mutun mai kyakkywar zuciya irinta junaid,munayi mashi fatan dacewa don yayi mutuwar shahada,bawan Allah naji mutuwarshi sosai,don har hawaye saida na zubar,akan laifin da bashi ya aikata ba,Anyi silar mutuwarshi,saboda Soyayyar da akeyi mashi itace taja mashi,babu komai,wanda sukayi silar mutuwar tashi kowa zai ɗanɗani kuɗarshi ne,masu cewa junaid yayi azkhar da addu'a before ya fita,kada ku manta,idan lokacin mutun yayi koda sallah yake cikin yi ko agaban ka'aba ne hakan bazai hanashi mutuwa ba,yakamata mu tuna da wannan,bawa bai isa ya gujewa ƙaddararsa ba,ko da yayi addu'a in dae anan ajalinsa yake dole ya mutu ba makawa😭*


  *Boss Bature*


Rishraf,


Gabanshi ne yaji yayi wani irin bugu,ba arziƙi ya zame hannunshi daga saman ƙirjin sehrish,ja da baya yayi,yayin da hannunshi ke dafe da saitin zuciyarshi,hankalin shi yayi mugun tashi,lokaci guda ya rasa natsuwarshi,da sauri ya fuce daga ɗakin,hakan yaba Sehrish damar motsawa,ta ɗauki undi ɗinta dake ajiye a ƙasa,ta sanya ajikinta,wata irin kasalace ta baibayeta ga wani irin faɗuwar gaba da take ji,daƙyar ta lalla6a ta haye saman gadon ta kwanta,hannunta rungume da pillow,


Saukowa downstairs,yayi hannunshi na kerma ya zaro wayarshi,yama rasa wa zai kira gida,yaji kowa yana lafiya,ko wani abu ya faru ne?don yanaji aranshi cewa,Something is wrong,that's why yake jin bugun zuciyarshi na ƙaruwa,

  Layin Marshal Ya kira,a lokacin wayar na a hannun Major,koda yaga kiran Sgr,ƙin ɗaga wayar yayi saboda baisan taya zai fara sanar dashi ba,game da mutuwar junaid,


Almost 3 times,wayar na ringing ba'ayi picking ba,layin junaid ya lalubo ya danna mashi kira,lokacin da aka sanar dashi cewa layin daya kira a kashe yake,nan fa hankalinshi ya ƙara tashi sosai,saboda tunda yake a rayuwarshi bai ta6a samun layin junaid a kashe ba sai yau,a ruɗe ya danna ma Abbansu kira,tana fara ringing,Abbansu ya ɗaga tun kafin ma yayi mashi sallama,muryar Abbansu ta katse shi da cewa"Rafayet!wai meke faruwa ne?ina ta kiran Layin junaid akashe!hankalina yaƙi kwanciya,"

  Muryar Sgr,a kasalance yace"Daddy,i don't know why nima na kira layinshi,switched off,Na kira layin Omar ma,tayi ringing ba'ayi picking ba"

  "Dan Allah rafayet,ka bincikamun meke faruwa a gidan nan,Hankalina bazai kwanta ba,in har banji muryar baby junaid ɗina ba,wlh har bacci ya fara ɗaukata amma na farka,saboda nasama raina zai kirani ne kamar yadda ya saba kirana,duk in dare yayi kafin ya kwanta,"acewar Abbansu,

  Jikin Sgr ba ƙaramin sanyi yayi ba,daƙyar ya iya cewa"In sha Allah daddy,zan yi ƙoƙari na haɗa ka dashi,"

  Daga haka sukayi sallama,zarya ya shiga yi acikin falon gidan,tunanin zuwa Abuja yake yi,don ji yake in har bai sanya junaid a idonshi ba,to hankalinshi bazai kwanta ba,


Ranshi ne ya bashi cewar,ya jaraba kiran layin Haroon may be,yana a gidan,can kuma ya soma tunani Anya ma yana da numbar haroon?tabbas baida ita,layin Major ya kira kaitsaye don ya samu ya haɗa shi da Omar,tunda na hannun daman shi ne,

  Lokacin da kiran ya shiga wayar major,suna tsaitsaye cirko cirko a cikin asibitin Sgr,Yana ganin sunan Sgr ya bayyana akan screen ɗin wayarshi,jiki na rawa ya kashe wayar gaba ɗaya,

  Abun ba ƙaramin ɗaurewa Sgr kai yai ba,kowa ya kira ba'a picking,shi Major ma kiran ya shiga,daga baya kuma aka kashe wayar,hakan ya ƙarasa shi zargin cewa wani mummunan abunne ya faru,

  Komawa Upstairs yayi da sauri bedroom ɗin da Sehrish take ciki,tura kopar yayi ya shiga,a kwance ya sameta rungume da pillow,


   "I know u are awake,inaso ki kiramin layin wani daga cikin sisters ɗinki,i wanna talk with them "

  Yunƙurawa sehrish tayi tare da kai hannu ta ɗauki wayarta da ta aje gefenta bayan ta kashe wakar,layin jahad ta lalubo ta danna mata kira,A lokacin wayar na a hannun Major ya kar6eta daga hannun police men ɗin,koda yaga kiran My Own sis ya shigo,ta layin jahad,kin daga kiran yayi har ya yanke,hakan yasa sehrish sake kira,sai ya kashe wayar gaba ɗaya,

  ɗagowa tayi tare da kallon Sgr,tun kafin tayi magana,ya riga ta cewa"Switch off ko"?ɗaga mashi kai tayi alamar eh,tare da cewa"Bari na kira layin Hosana,"

  Numbar hosana ta lalubo,tare da danna mata kira,tana fara ringing hosana ta ɗaga kiran,muryarta da alamun bacci atare da ita,

   "Wai wanene ke kira na"?

Sehrish tace"ke nice,Ina jahad ne na kira layinta a kashe"?

   Hosana tace"tun ɗazu da suka fita da junaid shan ice cream basu dawo ba,inata jiransu har bacci ya ɗauke ni,"kafin Sehrish ta ƙara cewa wani abu,da sauri Sgr ya sanya hannu ya kar6e wayar,

  tare da karata a kunnansa"Ina Omar yake"?rass taji gabanta ya faɗi,daga kwance take,amma jin maganar babban yayansu yasa ta miƙe zaune,anatse tace"Wlh bansan inda yake ba,ko yana gida ko yana waje oho,ni dai ina ɗakinmu,"

   "Go to his bedroom right now,and see if he's around,"

Mikewa hosana tayi tare da saukowa daga saman gadon,gudu gudu sauri sauri ta wuce upstairs bedroom ɗin Omar,a buɗe ta samu ƙopar,turawa tayi ta shiga daga ciki,ko'ina ta duba,hada leƙa toilet ɗinsa,ganin babu kowa yasa ta sanya wayar a kunnanta,

  "Ya Rafayet,na duba ko'ina,amma banga ya Omar ba,"

  "Its okey,ki koma ɗaki,"yana faɗin hakan ya katse kiran,

  ɗagowa yayi da lumsassun idanuwanshi masu ɗauke da bacci ya kalli Sehrish itama kallon nashi takeyi,duk jikinsu yayi sanyi mika mata wayar yayi"take ur phone,"hannu tasa ta kar6a,

  Da sauri ya juya,jikinshi duk babu ƙwari a lokacin idonshi ya sauka kan belt din shi dake akasa,hannu yakai ya dauka ya fara kokarin maida shi jikinsa tare da fucewa ya nufi downstairs,a dai dai lokacin Abusufyan na fitowa daga ɗakin da suka kwantar da Abu,jikinshi sanye da jallabiya,

  Yana jin takun takalmi,yakai idanuwanshi wurin,yana ganin Sgr ya tunkareshi da sauri,

  "Rafayet!wai kunyi waya da Junaid ne?i ave been trying his phone number,Amma akashe!nayi traying har nagaji,since evening ya sanar dani cewa,zasu fita tare da jahad shan ice cream,inaso naji ko sun koma gida,itama kuma phone dinta akashe"

  Ƙarasa saukkowa daga saman benen Sgr yayi tare da kallon Uncle ɗin nasu yace"Uncle nima bansan meke faruwa ba,kowa na kira layinshi switched off,babu mai picking call ɗina,That's why na yanke shawarar zuwa Abuja yanzun nan zan bi jirgi naje can," ya ƙarasa maganar yana ƙoƙarin wucewa ta gefen Abusufyan,da sauri ya ruƙo damtsen hannunshi tare da cewa"A'a Rafayet!ka haƙura sai gobe mana ka wuce can ɗin,"acewar Abusufyan 

Girgiza kai ya shiga yi tare da cewa"Bazan iya jurewa ba,inaso nasan meke faruwa ne acan ɗin,na damu akan rashin jin muryar Junaid,daddy ma ya kira ni yanzu,yana cikin damuwa,ko don saboda shi inaso naje can na haɗashi da junaid,if not ko bacci bazai iya yi ba,tunda ya sama ranshi son jin muryar junaid,"

  "Zanyi magana da yaya hossein ɗin,ka ajiye tafiyar nan dare yayi,sai zuwa gobe da asuba,"

  Ba don ya so ba,a dolenshi ya haƙura,komawa sukayi saman sofa suka zauna jigum jigum,Suna jiran tsammani,kowa da abunda yake saƙawa acikin ranshi,

  

*HAROON*


Around 12 na dare,Yana zaune gefen gadonshi,message ya shigo wayarshi,da sauri yakai hannunshi ya zarota daga cikin trouser pocket ɗinsa,buɗe message ɗin yayi ya soma karanta shi kamar haka,

   _Oga Aiki ya kammalu fa!ka duba whatsapp ɗinka,mun tura maka video zazzafan gaske,nasan yau zakayi kwanan farin ciki_

  Shu'umin murmushin nan nashi ya saki,jiki na rawa ya  shiga whatsapp ɗinshi anan ya samu Video ɗin da suka tura mashi,bayan ya kunna Wi-fi ɗin wayarsa,tunkan video ɗin ya ƙarasa yin loading jikinshi keta tsuma harya ƙagara yaga Videon menene,

  Ƙura ido yayi akan screen ɗin wayar,lokacin da video ɗin ya buɗe,motar Junaid ya gani tana ta ci da wuta,ta lomatse ta rakwakkwa6e,Wani irin ihu ya fasa cike da tsantsar farin ciki ya miƙe tsaye yana faɗin"Yess!Yess!!finally Burina ya cika,ko ayanzu na mutu nasan cewa,na gama dasu,na kashe farin cikin da suke taƙama dashi!"

Ya ƙarasa maganar tare da fashewa da wata irin mahaukaciyar dariya,lokaci guda kuma ya dakata da yin dariyar,jikinshi ya soma kerma sakamakon Muryar junaid da tayi mashi gizau acikin kunnanshi

   _Ya haroon!burinka ya cika ko?ka rabani da rayuwata,laifin me nayi maka?menayi maka dana cancanci wannan ɗanyen hukuncin a wurinka!yanzu shikenan bazan sake ganin ƴan uwana ba?ka rabani da mahaifina kuma kana farin ciki?haƙƙina bazai ta6a barinka ba_ 

  A tsorace Haroon ya shiga waige waige a cikin ɗakin nashi,ba ƙaramin razana yayi ba,ganin baiga kowa ba,yasa shi sauke ajiyar zuciya,

  ɗago da wayarshi yayi tare da Calling layin waɗanda yasa su kashe mashi junaid,tana fara ringing aka ɗaga kiran,

  Muryarshi asanyaye yace"dagaske ne video ɗin da kuka turomin cewa kun kashe junaid"?

  On the other hand,mutumin yace"ƙwarai kuwa!Yaron nan babu shi yanzu a doron duniyar nan!domin kuwa da truck muka take motarshi,bayan mun tabbatar yana acikin Motar,Amma ita yarinyar bata acikin motar kamar yadda ka bamu umarni,ta tsallaka titi zata siya masu ice cream......"

  Tunkan ya ƙarasa maganar,haroon ya zube saman guiwowinsa,wata irin zufa ce ta shiga tsatstsafo mashi ajikinshi,tuni ta wanke shi sharkaf,

  "Ya Haroon!Kamar baka farin ciki?naji kayi shiru"?

  Kasa buɗe baki haroon yayi,la66ansa sae kerma suke yi,

  "Hello!hello!Oga haroon!kana a kan layi kuwa"?jin shiru bai tanka masu ba yasa suka katse kiran,

  Jikin taƙaura yayi la'asar,gaba ɗaya haroon ya shiga ruɗani,Shin farin ciki yake yi da mutuwar junaid ko kuwa baƙin ciki?Tun yanzu ya fara tsorata da gizan da muryar junaid tayi mashi,

  _Laifin me junaid yayi mun?na kasa yarda cewa ni da kaina na bada umarnin a akashe shi_

  Runtse idanuwanshi yayi sosai,yana tariyo fuskar junaid,mai ɗauke da kyakkyawan murmushi nan nashi,

  Guiwowinsa duk sun sage,ya kasa miƙewa tsaye,yayi fiye da awanni zuƙunne batare daya motsa ba........


*AUNTY BABBA*


Tun bayan da Abra ta gudu daga hotel ɗinnan,Tana fitowa daga wanka,jikinta ɗaure da towel,sam bata kawoma ranta komai ba,duk da tayi mamakin ganin babu kowa,Jinjina kai ta shiga yi tana faɗin"Ko gidan ubanwa taje?bayan na sanar da ita cewa Yanzu zamu tafi,zata dawo ta same ni,"ta ambaci hakan tare da samun wuri gefen gadon ta zauna,tun tana sa ran dawowar abra har ta fara fidda rai,tunawa da abunda ya faru da hayaam a hotel yasa hankalinta ya tashi,tsoranta kar ace itama abra,an samu wani ya ƙurmushe ta ne,hakan yasa tayi firgit ta miƙe tsaye,tare da kai hannu saman bedside drawer ta ɗauki wayarta dake ajiye a samanta,

  Yanke shawarar kiran Abra tayi,tun kafin ta shiga Contacts ɗinta,saƙon abra ya shigo cikin wayar,on the top of screen ɗin wayar,

  Janyo saƙon tayi ta buɗeshi,a tsanake ta soma karanta saƙon

  _Aunty laila sai dai kiyi haƙuri,wlh bazan iya zuwa wurin bokan nan ba!saboda ƙaryar da kika yi mun dangane da hayaam,ashe Aunty hayaam tana kwance rai hannun Allan agadon asibiti,amma kika gudu kika barta saboda kawai tsautsayi ya same ta?ashe dama amfani kike yi damu don ki cimma burinki!baki damu da rayuwarmu ba,Naji tsoro ne saboda nasan cewa nima wata rana in irin hakan ta faru dani zaki gujeni ne,ina mai baki haƙuri Aunty laila,bansan ya rayuwarki zata ƙare ba a Enugu,domin kuwa na kwashe duk wasu kuɗi da muka zo dasu,Na tafi da handbag ɗinki gaba ɗayama,kada ki sha wahalar nemanta Aunty hayaam da aunty Amani ne suka sa nayi hakan a ƙarshe ina maki fatan sa'a_

  Saboda tsabar kiɗima a hautsine ta jefar da wayar ƙasa,Dafe ƙirjinta tayi hankalinta a matuƙar tashe,ta furta"kutumar Uba!Ni Abra zata yiwa iya shege!Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Ya Allah ka rabani da mugun ji da mugun gani!Ya Allah kasa mafarki ne ba gaske ba,Abra ta yashe ni!ta gama dani!na shiga uku na ni yau! Na gama yawo!

  Tuni Ido ya raina fata,cizon yatsanta ta shiga yi,tana faman yarfa hannunta,Duk tabi ta ruɗe ta rasa inda zata tsoma ranta,

  Zuƙunnawa tayi ta ɗauki wayar da tayi wurgi da ita ƙasa,layin Abra ta kira,unfortunately ta samu wayar akashe!

  "Allahumma Ajirni fil musibati wa'aklifni khairan Minha,Meyasa Abra zatayi mun haka!Nashiga uku ni yau,Wannan wata irin Musiba ce!daga wannan sai wannan?"

  Hawaye ne suka soma saukowa daga saman fuskarta,a susuce ta shiga faɗin"Wlh baku isa ba!baku isa ku hanani zuwa wurin bokan nan ba!Wlh sai naje,Allah ya isa tsakanina Da Amani!Munafuka duk ita ta shirya mun wannan,Ita kuma waccen kingin gardawan bamma san ya akai ta farfaɗo ba,don nasan itace ta sanarwa Amani har suka shiryamin wannan tuggun,Wlh bazan ƙyalesu ba....."Aunty babba fa ta zare sai faman sakin sambatu takeyi,da alama ta fara zarewa,zagaye ɗakin tashiga yi tana safa da marwa,hannunta asaman kanta,

   Yanke shawarar bin bayan Abra tayi,a gaggauce ta buɗe trolley ɗin kayansu,ta ɗauko doguwar riga ta zura ajikinta,Ta yafa mayafi buɗe ƙopar tayi,jiki na rawa,haka ta shiga zagaye hotel ɗin tana neman Abra,har wurin receptionists taje,ta tambayesu ita,hada yi masu kwatancenta anan suka sanar da ita cewa,sunga gifcinta a lokacin da take ƙoƙarin barin reception ɗin,Jin haka yasa Aunty babba ta zabura da gudu ta fuce daga reception ɗin ta miƙi hanyar fita daga hotel ɗin,gudu gudu sauri sauri haka ta fita waje gefen titi tana Neman Abra,

  Hanya ta miƙa tana tafiya tana sambatu,tana ƙoƙarin ta tsallaka titi wata jibgegiyar Mota ƙirar Range rover tayi Awon gaba da ita,Koda mai motar nan yaga aika aikar da yayi jini har asaman glass ɗin motarshi,aikuwa a hanzarce yaja motarshi da gudun gaske ya bata wuta kamar zai tashi sama yabar Wurin!!!

  Aunty babba kuwa sai kwala ihu takeyi tana shure shuren ƙafa asaman titi,

   "Wayyo Allah!nashiga uku!na bani Na lalace!Ya kashe ni!Ya gama dani!"

  Dandazon mutane ne suka taru a kewaye da ita,sun zuba mata ido suna ta kallonta an ransa wanda zai iya taimaka mata,kowa tsoro yake ji kada ace shine yayi silar mutuwarta,Wannan dalilinne yasa aka rasa wanda zai ta6ata,kuma babu wanda yayi tunanin kiran ƴan sanda don yayi reporting akan Incident ɗin,

  Tun tana shure shuren kafarta jini na tsargowa ajikinta,har jikinta ya soma saki alamar rai zai yi Halinsa........


DAMATURU,


Wuraren karfe 1 na dare,Abba na zaune zugudum tsakiyar gadonsu ya zabga uban tagumi,zuciyarshi sai bugawa take yi,kwakkwaran juyi Alexandra tayi karaf idanuwanta suka sauka akan shi,da ya ke akwai hasken bedside lamp dake a kunne,muryarta adisashe tace"Abban Junaid!lafiya har yanzu bakayi bacci ba,"?

  Hankalinshi atashe yace"taya zan iya runtsawa?kullum junaid ya saba kirana a waya da daddare kafin ya kwanta yayi bacci,Amma yau shiru wayarshi a kashe,wayar Omar a kashe,na rasa wanda zan samu a gidan in kira shi don ya sanar dani halin da junaid ke ciki,"

  Jin wannan maganar yasa hankalin Alexandra ya tashi haiƙam,mikewa zaune tayi cike da mamaki tace"nikaina nayi mamakin rashin kirana da junaid,baiyi ba amma ban kawo komai araina ba har bacci ya dauke ni"

  Abba na ƙoƙarin buɗe baki yayi magana,suka ji an ƙwanƙwasa ƙopar ɗakin nasu,

  Atare suka haɗa baki wurin cewa"Wanene"?

  Muryar Twins ce ta amsa masu"Mommy mune,"

  Kallon juna sukayi at same time,kafin Abba yace"Ku shigo ciki,"

  Tura ƙopar sukayi atare suka shiga kowannansu sai faman hammar bacci yake yi idanuwansu a lumshe saboda baccin da suke ji,

  Aruɗe Alexandra tace"is everything alright twins?me kuke yi har yanzu bakuyi bacci ba"?

  Ayaan yace"mommy wlh ba lafiya,mun kasa runtsawa saboda yau junaid kwata kwata bai kira wayarmu ba,Ko text message ɗin da ya saba tura mana yau bamu gani ba,kuma mun bibiyi layinshi a kashe,har ya Omar mun kira muji ko lapia shima a kashe,taya hankalinmu zai kwanta,"yana kai ƙarshen maganarshi jahan ya ɗaura da cewa"Mommy,Daddy Ni da Ayaan mun yanke shawarar komawa gida gobe,dan Bazamu juri rashin junaid a kusa damu ba,"

  Tashin hankali,zuba masu ido Sukayi suna kallonsu,kowanne yasha sleeping dress ajikinshi,

  "Ku zauna"Abbansu ne yayi maganar tare da nuna masu doguwar sofa ɗin dake acikin bedroom ɗin,Zama su kayi kowa fuskarshi ɗauke da damuwa,

  "Mommy!"gabanta ne ya faɗi jin Muryar fawan,da sauri takai idanuwanta bakin ƙopar ɗakin,shigowarshi kenan,idanuwanshi sunyi luhu luhu dasu,ƙarasa shiga ciki yayi daƙyar yake iya ɗaga ƙafarshi saboda bacci,

  "Fawan!kaima baka yi bacci ba"?Abbansu ne yayi tambayar,

  ɗaga mashi kai yayi alamar eh,tare da cewa"Abba,junaid fa?ko wani yayi waya dashi acikin ku?duk yau bai kira ni ba,kamar yadda ya saba,har text yana turamun kullum amma yau shiru,ko ta whatsapp bai turo man ba,da abun na kwanta yanzu na farka still banga sakon shi ba, layinshi ma a switched off,duk na damu wlh,'

  Tashin hankali,abun fa ya fara basu tsoro,wasa wasa one by one su Irfan kowa ya shiga shigowa ɗakin yana tambayar junaid,dayake family house ne,duka danginsu na 6angaren Mahaifinsu,suna acikin katafaren gidan,wanda ya kasance mallakin kakansu,mijin Ammi,

  Aranar dukkansu babu wanda ya runtsa,mafi yawancinsu a zaune suka kwana,don sunci alwashin dawowa gida,tun da asussuba,Abbansu yafi kowa ƙagara daya dawo yaga meke faru ne,Ya ƙwallafa rai akan son ganin junaid,don da ace yana da fiffike da ba abunda zai hanashi tashi sama atsakar daren nan yadawo gida!           *Allah sarki*


Kamar yarda su Abba suka kwana a zaune,haka Sgr da Abusufyan suka kwana a zaune,cikin falon gidan,babu wanda ya runtsa acikinsu,haƙika ba ƙaramin so sukeyi wa junaid ba,Rashin kiran da baiyi masu ba a waya yasa duk sun tashi hankalinsu,inaga sunji mutuwarshi?mezai faru?kowa fa yasha jinin jikinshi,


Tunda asussuba Jirginsu Sgr da Armstrong ya ɗaga izuwa Abuja,


*Sehrish*


Bayan sallar asuba,Sehrish ta koma ɗakin Oummansu,har lokacin bata farka ba,Wuri ta samu saman gadon daga gefenta,ta kwanta abubuwa da yawa suna zuwa mata aranta,ita kanta tasan cewa tayi kewar wasu daga cikin mutanen gidan,musamman Su Hosana da Junaid,da Aunty azmee,kowa missing ɗinshi take yi,gashi batasan ranar da zasu koma gida ba,tana cikin wannan zancen zucin nata,tajiyo muryar Oummansu tana sambatu,tana faɗin"kada a ta6a mun ƴa'ƴana,dan Allah abarmun su,su kaɗai nake dasu,sune dangina,sune komai nawa,'

  Wani irin farin ciki ne ya lullu6e Sehrish,miƙewa tayi zaune tana kallonta,a hankali ta furta"Oumma" slowly abu ta buɗe idanuwanta,tare da wurgasu kan fuskar sehrish,wani irin kallo take bin ta dashi,kallon tuhuma,

  Murmushi sehrish ta sakar mata tare da ƙoƙarin miƙa hannu zata shafa gefen fuskarta,aikuwa a tsorace Abu ta miƙe zumbur tana ja da baya,girgiza mata kai ta shiga yi tare da zare mata manyan idanuwanta,wai don kada ta ta6ata,.  

  Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,

   "Oumma baki gane ni ba?Ni ce fa sehrish!Rishi ɗinki'

  A ruɗe ta shirga girgiza kanta tana cewa"a'a a'a Ni bansan wacece ke ba,bake bace rishi ɗina ba,Rishi ɗina ƙarama ce,"

   Cikin sanyin murya Sehrish tace"Oumma kallanni dakyau ki gani,nifa ce rishi ɗinki,nasan bazaki manta da kamannin fuskata ba,na ƙara girma ne kaɗan,"

  Harara abu ta watsa mata,dama tun fil azal abu mace ce mai taurin kan tsiya ga kafiya,tun tana da hankalinta balle kuma yanzu da babu hankalin atare da ita,

   Zubama juna ido sukayi kowa na kallon kowa,taƙi yarda sehrish ta kusantota,da zarar sehrish ta matsa,itama da sauri zata matsa,ganin ta kusa ƙurewa gadon gudun kada ta faɗa ƙasa,yasa Sehrish ta ƙyaleta,

  Cikin lallashi tace"Oumma!kin tuna da Hosana?da jahad?

  Girgiza mata kai tayi alamar a'a,"Ni bansan su ba,Ni ki ƙyaleni bansan kowa ba,ƴa'ƴana na sani Nemansu nake yi,yace zai kashe munsu,dan Allah akawo mun ƴa'ƴana kusa dani,"

  Murmushi sehrish ta saki tana kallonta,tsantsar son mahaifiyarsu take ji kamar kamar me,gashi taƙi bari ko rungumarta tayi,

   "Kiyi haƙuri kinji,Babu wanda zai ta6a maki ƴa'ƴanki,idan har kika bani dama,Ni dakaina zan kawo maki ƴa'ƴanki,"

   Shiru tayi bata tanka mata ba,Sai ma wani kallo da take bin ta dashi,kallon ban yarda dake ba,wayau zakiyi mun,

   Jin sallamarsu Abusufyan yasa tayi saurin amsa masu tare da saukowa daga saman gadon,ta fito daga ƙopar dakin,Su uku ne suka shigo,Baban sadeeq tare da Abusufyan sai Sadeeq ɗansu da suka ɗauko jiya,Anan ya kwana gidan,

  Fuskarta ɗauke da fara'a ta gaisar dasu"ina kwananku?Kun tashi lafiya,"

  Atare suka amsa mata"lafiyalou,Alhamdulillah,"

  "Sadeeq ka ganeta kuwa,"?Baban sadeeq ne yayi maganar yana kallon sadeeq ɗin dake tsaye agefenshi,murmushi ya ɗan saki tare da girgiza kai alamar a'a,yace"fuskarta kamar na santa,amma bazan iya tunawa ba,'

   Abusufyan yace"Ae zaiyi wuya ya ganeta saboda canzawar da tayi,ba kamar daba da yasanta,yanzu ta ɗan ƙara girma,"

   Baban sadeeq yace"Allah sarki,Sadeeq wannan fa ba kowa bace face daya daga cikin waɗannan ƴan ukun na Wurin abu,waɗanda suke yawan zuwa gidanmu su yini wani sa'in ma harsu kwana,"

  Cike da mamaki Sadeeq yace"Wai su rishi,hosana,da jahad"?sae lokacin ya ganeta,baki asake yake kallonta,don bazai manta lokacin da suke yawon zarya acikin gidansu ba,musamman in yunwa ta addabesu,wani sa'in ma shi Mamansu ke aikawa gidansu ya kai masu abinci idan tajiyo kukansu,da zarar ya kai masu abincin,Jiki na rawa suke kar6a su zauna suna ci,'

   "Rayuwa kenan,banta6a tsammnin rana irin ta yau ba,gani ga rishi,"tuni idonshi sun ɗan cicciko da ƙwalla,haka itama sehrish ɗin 

   Baban sadeeq yace"ka tuna lokacin da kake kuka saboda mamanka taba su rishi abincinka'?

  Fashewa sukayi da dariya gaba ɗayansu,

  Kunya duk ta rufeshi daƙyar ya iya buɗe baki yace"Dan Allah Abba,adaina tuna abunda ya wuce,'

   "Shikenan tunda haka kake so andaina,"

 Wuce wa Abusufyan yayi cikin ɗakin abu,Baban sadeeq ma ya wuce ɗakin da suka sauka,ya rage daga ita sai Sadeeq atsaye,suna fira,

   "Yanzu shekarunki nawa'?ya tambaya yana kallonta,

   Wurga ido ta ɗan yi kamar mai tunanin wani abu,kafin tace"sha takwas kaifa"?

  Hannu yasa tare da ɗan sosa keyarsa yace"Sha tara," harara ta watsa mashi tana ƴar dariya tace"wlh ƙarya kake yi mun nafa son shekarunka,Allah kamar ma mun girmeka,don ka ganka dogo shiyasa zaka 6oye mun shekarunka ko'?

  Murmushi ya ɗan saki tare da nuna mata sofa ɗin dake a falon yace"Mu zauna mana,nagaji da tsayuwa,baccin ma bai isheni ba Allah,naji daɗin sanyin nan ba kamar gidanmu ba,fankar ɗakina ma,6eraye sun lalata mun ita,"ya ƙarasa maganar tare da samun wuri ya zauna,itama ta zauna suna fuskantar juna,

   Sae faman bin falon yakeyi da kallo,ƙasa ƙasa yayi da muryarshi ya ambaci sunanta"rishi,"

  "Na'am"ta amsa mashi

 "Wai wannan mai mutuncin,mai kama dake ɗinnan Yayanku ne"?

  "Me hali dai bazai ta6a canzawa ba,ashe har yanzu kana nan da wannan tsegumin naka kamar mace"?cike da zolaya tayi maganar,harararta yayi tare da cewa"Ae tsegumin nawa ku ma yayi maku amfani!ko kinmanta ni ne ɗan leƙan asirin Mamanmu?ita ke cewa nazo gidanku najiyo mata idan kun ci abinci,idan nayi la6e naji kuna kukan yunwa sai in watsa da gudu inje in sanar mata.... "

 Dariya sehrish tayi har haƙoranta suka bayyana,baki asake Sadeeq yace"Wai!madarar kyau!rishi kinga yadda kikayi kyau kuwa da kika washe bakinki Fararen haƙoranki suka fito kamar na Ketrina kef?ba kamar lokacin da ba,Haƙorannan Jawur dasu kona Maclean ma babu,"

  ɗaure fuska sehrish tayi kamar ta rufe shi da bugu tace"kai Sadeeq ɗazu fa naji kana cema baban ku,adaina tuna baya,shine nikuma zaka dinga tunamun abunda ya wuce don wulakanci,"

   Fashewa yayi da dariya,bin shi tayi da kallo bakowa ya faɗo mata arai ba,fa ce junaid ɗinsu,lokaci guda taji tana kewarshi,

    "Sadeeq,mutumin da kake magana akanshi,ba yayana bane,Shi ne mahaifin mu!"tunkan ta taƙarasa maganar ya katseta da cewa"kutmelesi!Amma dai ƙarya kikeyi mun ko?idan shine mahaifinku,Wanccan mai dogon gemun fa?wanene Shi?cike da tuhuma yayi mata tambayar,

  Shiru tayi bata bashi amsa ba,tsareta yayi har sai da ta faɗa mashi komai daya faru arayuwarsu,wani Shu'umin murmushi taga yana saki,hakan yasa tace"Wai lafiya"?

  "Rishi aike yanzu hajiya ce,Ashe dama ku ƴa'ƴan masu kuɗi ne?Ae wlh bazata sa6u ba,Tunda kunyi arziƙi yanzu sai a ramama kura aniyarta koba haka ba"?yayi maganar yana ɗage mata gira,irin na ƴan duniyar nan,

  Dariya sosai tayi,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Faɗamun dame dame za'a rama maka"?

  Lissafo mata ya shiga yi"Ragowar abinci na da kuka saba cinye mun,tare da ƴan kayan sawa na da maman mu ke kwashewa tana kaima Oummanku don asanya maku kin tuna'?

  Shiru sehrish tayi bata bashi amsa ba,bakomai take tunawa ba,fa ce rayuwarsu ta baya,ya tuna mata da lokacin da Maman Sadeeq ke aiko da kayanshi don acanza masu kaya,saboda nasu duk sun yayyage,tun sunayi ma Oummansu kukan bazasu sanya kayan maza ba har suka haƙura ta dinga sanya masu,haka tsoffin takalman sadeeq haka aka dinga kawo masu don su rinka sama kafafunsu,

  Ganin hawaye akan fuskarta yasa Sadeeq saurin mikewa ya dawo gefenta ya zauna cikin lallashi yace"rishi nifa wasa nake yi maki,wlh ban faɗi hakan ba,da niyyar in 6ata maki rai ba,kawai inaso in sanyaki nishadi ne,saboda yanzu ta ko'ina Allah ya hore maku,'

  Cikin shessheƙar kuka tace"ni baka 6ata mun rai ba sadeeq,na tuna da irin rayuwar da muka yi ne abaya,kaima kasan dole inyi kuka in na tuna,"

   "Tunda baki so,mu manta da komai,bazan ƙara tuna maki ba,Yanzu dai faɗamun nawa ne acikin asusun bankin ki?nawa kika tara"?

  Fashewa tayi da dariya jin abunda yace,

  Da hannu ta nuna mashi yatsunta guda biyar,

   "ɗari biyar"?yayi guessing yana kallonta,girgiza mashi kai tayi alamar a'a,

  "Dubu biyar"?ya sake canka,cike da sa ran ya faɗi dai dai,

   Girgiza mashi kai ta kuma yi,

 "To dubu ɗari biyar,"nan ma ta girgiza mashi kai Alamar a'a,tur6une fuska ya ɗanyi saboda ya fara tunanin kamar ƙarya takeson ta shirga mashi,

  A ƙule yace"Miliyan biyar"murmushi ta sakar mashi tare da jinjina mashi kai alamar ya faɗi dai dai,

    wani kallon rainin wayau ya jefa mata tare da cewa"Alkazzubu haramun,"

    "Wlh dagaske nake maka,Ina da kuɗi sosai sunma fi miliyan biyar amma basa a hannuna,duk suna a wurin Daddyn...."kasa ƙarasa maganar tayi,ganin Sadeeq ya sauko daga saman kujerar ya dawo ƙasa saman carpet ya zauna agabanta tare da lankwashe ƙafafunshi zaman cin tuwo,

  "Lafiya naga ka dawo ƙasa,"?

  Hannu yasa tare da ɗan sosa ƙeyarshi yace"Ae matsayinmu ba ɗaya ba,kefa Millionaire ce,ni kuma Faƙiri mamallakin naira ɗari biyar acikin aljihu,bazaiyiwu mu zauna a saman kujera ɗaya ba,abun ma sam babu ladabi acikinsa,

  Fashewa Sehrish tayi da dariya,Yau sadeeq ya sanyata nishaɗi sosai,komai yayi yana tuna mata da junaid,

  "Aunty sehrish,kinji nace ina da ɗari biyar ko?

  ɗaga mashi kai tayi alamar eh , "Yawwa,wlh itama Wanki da guga nayi a shagon wani abokina aka bani ita,Nifa nan da kike gani na sai inyi fiye da wata ɗaya babu ko sisi a aljihuna,Babanmu kuwa idan kinga ya bani kuɗi to sai dai fa,idan naje islamiyya ne,haka itama maman mu,ataƙaice dai bari in fito maki a mutun,wlh Sehrish ko abun hawa bandashi,tunda keke na ya samu matsala ba'a ƙara gyaramun shi ba,naje wurin mai gyara yace sai ya ci dubu uku,tun daga nan na jingine shi gefe guda,

   Zuba mashi ido sehrish tayi tana kallonshi,yadda kasan ɗan Almajiri haka ya zauna yana zayyano mata matsolilin dayake fama dasu na rashin kuɗi,ta kasa kunne tana sauraronshi,


A 6angaren Abusufyan kuwa,lokacin daya shiga yayi arba Da abu a zaune dirshan saman gadon tana faman zazzare idanuwanta,ba ƙaramin daɗi yaji ba,ƙarasa shiga ciki yayi tare da samun wuri daga gefen gadon ya zauna,zuba mashi ido tayi tana kallonshi,

   Murmushi ya sakar mata tare da miƙa mata hannunshi,zuba ma tafin hannunshi ido tayi tana kallonshi,ta gane fuskarshi a matsayin wanda ya taimaketa,ta fito daga hannun masu fararen kayan nan,

   "Ina ƴa'ƴana suke"?muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,

   "Kada ki damu,ƴa'ƴanki suna atare dani zan kaiki wurinsu,kina so ko"?

  ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

  "A ƙarshe dai duk yawace yawacen naki,gashi kin dawo wurina abu,saboda ƙaddararki tana atare dani,kamar yadda kika zama ƙaddarata nima,Ashe da rabon zan sake ganin wannan kyakkyawar fuskartaki"?calmly yayi maganar,tsantsar sonta ne da ƙaunarta ke addabarshi,ji yake yi tamkar ya mayar da ita cikin cikinshi,

  "Abu na,Faɗamun har yanzu kina sona kamar yadda nima nakeson ki,"

  Wuƙi wuƙi tayi mashi da ido tana kallonshi,sam batasan inda zacen nashi ya dosa ba,

   "Kaine ka kashe mun babana ko?kuma ka rabani da ƴa'ƴana ko?Zaka kashe munsu ko"?

    girgiza kai Abusufyan yayi tare da cewa"ni bani bane na kashe maki mahaifinki ba abu,Nifa ne Abusufyan ɗinki,uban ƴa'ƴanki,ba zaki iya tunawa ba ko kaɗan,"

  Kallon dayaga tana binshi dashi ne ya tabbatar mashi da cewar a harzuke take,jira take yayi yunƙurin matsawa kusa da ita,Yasha bugu,

  Dariya ya ɗan yi tare dacewa"kwantar da hankalinki,



⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫

*_MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI_*


*DOMIN. DAWO DA MARTABAN NONONKI*


Shin ko kinsan nono yanada matukar muhimmanci a wajan mai gida ,? Shin ko kinsan babu abunda namiji yafiso yafi daukar hankalinahi kamar cikar k'irji , ? To nono shine babban Martaban mace a wajan mijinta , don babu namijin da zaiso mace mai yakunannen nono kamar silifas ,wannan yasa Nazo maku da sahihi kuma ingantaccen maganin nono Wanda bashida wata matsala hadin gargajiya ne , acikin lokaci kalilan zakisha mamakin yadda nononki zai ciko sosai Wanda wannan cikowar ita zata bashi damar da zai tashi sosai ta yadda kema zaki Shiga cikin jerin mata masu aji agaban mazajensu ........kedai hanzarta ki nemi mmn Yusuf mai kayan mata yar mutan sokoto zaki samu ingantattun kayan mata masu tafiyar da hankalin maigida.......don neman Karin bayani   07069711327 ......

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



Am sorry🙏




Babu abunda zan yi maki,a haka ma daɗi nake ji,kina kallona ina kallonki,"murguɗa mashi baki tayi tare da kawar da idanuwanta gefe guda,


Wuraren ƙarfe 8 na safe,nurse ɗin dake kula da abu ta ƙaraso,taimaka mata tayi wurin yin wanka a toilet ta gyara mata jikinta,da gashin kanta ko'ina ta wanke mata shi,lokaci guda Abu ta fito fess da ita,ƴar doguwar rigar material ta sanya mata,ita kanta abun sai murna takeyi da aka gyara mata gashin kanta da jikinta,taji daɗin jikinta sosai,Sehrish ce ta shirya masu breakfast gaba dayansu suka hallara a falo suka zauna suna ci,banda abu dake zaune a bedroom ɗinta tare da nurse ɗin,saboda ita kaɗai zata iya da ita,dama sune masu kula dasu a gidan mahaukatan,Sun san duk wasu dabaru da zasu bi wurin tafiyar dasu batare da sunsha wahala ba,a baki ta dinga bata abincin kalacinta tana ci,saboda bata iya ci da hannunta ba,Zubarwa takeyi a ƙasa,kamar ƙaramar yarinya haka take yin wasa da abincin,Bayan nurse ɗin ta kammala kimtsata,Dr yazo ya duba ta,bayan tafiyarshi ne ta samu bacci,


*SGR*


Da gudun gaske motarsu ta shararo izuwa cikin gidan yadda kasan zasu tashi sama,gudu bana wasa ba,Sam ya kasa samun natsuwa acikin zuciyarshi,jikinshi sai tsuma yake yi a ƙagare yake dasu ƙarasa cikin gidan,Armstrong nazaune agefenshi sai faman tausarshi yake yi ganin yadda ya tashi hankalinshi,slowly sojan daya ɗaukkosu from Airport ya rage gudun motar lokacin da ya ƙaraso wurin da zai yi parking ɗinta,saboda tsabar sauri,tun kafin a buɗe mashi ƙopa yasa ƙafarshi azafafe ya harba ƙopar,gudu gudu sauri dauri ya nufi cikin main palour ɗinsu,wayaam babu kowa tsit kake ji,A hanzarce ya haura upstairs direct ya wuce bedroom ɗin junaid,a buɗe ya samu ƙopar ɗakin hannu yasa ya tura tare da shigewa ciki,gabanshi ne ya faɗi rasss ganin babu junaid,saboda yasan cewa junaid bai zuwa ko'ina tunda sanyin safiya,adai irin wannan lokacin zaka same shi kwance saman gadonshi rungume da pillow,

  Muryarshi tamkar zata fasa maƙoshinshi haka ya shiga ƙwala mashi kira"JUNAID!JUNAID!!JUNAID!!!"a gaggauce ya nufi toilet ɗinshi yasa hannu ya tura,nan ma yaga wayaam babu kowa,jiki asanyaye ya fito daga ɗakin junaid ya wuce bedroom ɗin Marshal Omar,tura ƙopar yayi ya shiga daga ciki,babu kowa a falonsa,bedroom ɗinshi ya nufa nan ma babu kowa,tashin hankali!

  Wani irin wahallallan yawu ya haɗiya,fitowa yayi daga part ɗin Omar ya nufo downstairs,gudu gudu sauri sauri haka yake taka staircases ɗin,yana a second to the last step,yaji shigowar message a wayarshi,dakatawa yayi tare da sanya hannu cikin trouser pocket ɗinsa,duba screen ɗin wayar yayi,bayan ya sanya finger ɗinsa ya buɗe saƙon,a tsanake ya soma karantawa

  _Gm Sir,ina fata ban takura maka ba,Marshal yana kwance a gadon asibitin mu yanzu haka_

  Message from doctor Emran,Hankalinshi yayi mugun tashi,a ruɗe ya furta"Omar?kwance a gadon asibiti?

  Da sauri ya nufi hanyar fita daga falon,fitarshi keda wuya,Hosana ta fito daga bedroom ɗinsu,tasha kuka kamar ranta zai fita,saboda an barta ita kaɗai,babu Jahad babu Sehrish babu Junaid,bugu da ƙari kuma babu Ya Omar,tun ɗazu take ta zaryar zuwa ɗakin shi,don taga ko ya dawo amma babu shi,palour ta dawo ta zauna saman sofa,hawaye wasu na bin wasu,fuskar ta jiƙe sharkaf,


"Hosana"!jin muryar Azmee yasa ta miƙe tare da juyowa tana kallonta,sanye take cikin doguwar jallabiya,tayi rolling mayafi akanta,

   Tunkararta hosana tayi cikin shessheƙar kuka tace"A...aunty azmee har yanzu basu dawo ba,ni kaɗai aka bari,gidan duk babu daɗi,"

   Janyota Azmee tayi tare da rungumeta ajikinta,tana ɗan lallashinta,

  "Don't worry ur self,wipe ur tears,in sha Allah nasan nan bada jimawa ba,Ya Omar ɗinki zai dawo cikin gidan nan,Just calm down ur mind,"ta ƙarasa maganar tare da ɗago hosana daga jikinta,

   "Aunty azmee,shiru fa since yesterday night,kuma har kiran layinshi nayi wayarshi a kashe,Ni shikenan kowa ya tafi ya barni,dama ba so na akeyi ba,"tana magana hawaye na sharara akan fuskarta,ɗan murmushi Azmee tayi tare da kai hannunta saman fuskar hosana,taja kumatunta tare da cewa"Haba Babyn Omar,shalelen Abusufyan,kinfi kowa sanin yadda ya Omar ɗinki ke tsananin sonki,Ina da tabbacin cewa duk inda yake a yanzu,tunaninki yake yi,ya hosanata ta ke?me take yi a yanzu?tana kewata kuwa?

   Murmushi hosana ta saki har hankalinta ya ɗan kwanta jin abunda Azmee tace,

  "Aunty azmee kin tabbata cewa ya Omar yana tunani na yanzu haka"?

  ɗaga mata kai azmee tayi alamar eh,kafin tace"Kina aransa mana,yanzu abunda za'ayi,me zai hana mu shiga kitchen atare mu haɗa mashi lafiyayyen breakfast,da zarar ya dawo gida kinga sai ki kai mashi,Zaiji daɗi sosai,"

  Cike da zumuɗi hosana tace"Mu tafi kitchen ɗin,Hada chocolate zamu haɗa mashi,nasan zaiji daɗinshi sosai"

  Ruƙo hannunta Azmee tayi atare suka wuce cikin kitchen,Suna aiki suna fira,gwanin ban sha'awa,


  *SGR HOSPITAL*


Slowly Motarsu ta shiga cikin katafaren asibitin,bayan Armstrong yayi parking ɗin Motar,buɗewa Sgr yayi a hanzarce ya wuce cikin asibitin da saurin gaske,Armstrong na biye dashi,Tashin hankali,Soldiers ɗin da suka kawo Marshal Omar,Suna yin arba da fuskar Sgr nan fa kowa yasha jinin jikinshi,Hankalinshi a matuƙar tashe yake kallonsu one by one,Sara mashi suka shiga yi,batare da ya tanka masu ba,jiki a sanyaye yake tafiya kamar wanda aka zarewa Lakar jikinshi,tuni ya soma karaya,Zuciyarshi sai tsinkewa take yi,

  Lokacin da ya ƙaraso wurin da Major ke tsaye,Suna haɗa ido major ya saddar da kanshi ƙasa,yayin da zuciyarshi ke bugawa,Don yasan cewa dole ya tuhume shi game da kashe mashi waya da yayi,

   "Major"da wata irin raunanniyar Murya Sgr ya ambaci sunanshi,

   Batare da ya ɗago sun haɗa ido ba yace"Na'am yalla6ai,"

   "Where's Omar"?

Da hannu major ya nuna mashi medical room ɗin da aka kwantar dashi,batare da ya kuma tambayarshi wani abu ba,Ya wuce cikin ɗakin  har izuwa gaban gadon da Marshal ke kwance,babu alamun sauƙi a jikinshi,

  biyo bayanshi Major yayi tare da Armstrong suka tsaya agefe,

   Juyowa yayi tare da wurga eyeballs ɗinshi kan fuskar Major,tun kafin yayi magana a ruɗe Major ya dakatar dashi"Am sorry sir,don Allah don sonka da manzon Allah (SAW)kada ka tambayeni komai,saboda bazan iya amsa maka ba,"

 gyaɗa kai kawai yayi tare da juyawa daƙyar ya iya ɗaga kafarshi har izuwa gefen gadon ya zauna,yana kallon Omar,ya jima yana mamakin menene silar kwantar dashi gadon asibiti?A iya sanin shi ba ƙaramin abune zaisa a kwantar da Omar gadon asibiti ba,

  Turo ƙopa Dr Emran yayi ganin su Armstrong sunyi cirko cirko yasa shima yaja gefe ɗaya ya tsaya,To fa kowa tunani ya shiga yi taya zasu fahimtar da Sgr batare da ya haukace masu ba,

  "Major!"ya ambaci sunanshi, 

Hankali atashe major yace"Na'am Yalla6ai,"

  "Meya faru da ɗan uwana ne?"ƴan kame kame major ya shiga yi duk yabi ya susuce ya rasa ta ina zai fara kora mashi bayani,

   "Emran!meya faru da Omar ne"?ya sake tambayar Dr emran,Shiru Emran yayi shima ya rasa ta ina zai fara,Jin sunyi mashi shiru yasa zuciyarshi ta hasala,jikinshi na kerma ya miƙe tare da kallonsu,ranshi a matuƙar 6ace yake magana!

  "Bazaku amsa mun ba!Kun wani zuba min ido kuna kallona,kun mayar dani tamkar wani shashasha,"hankalinsu ya tashi matuƙa,kowa sai motsa la66ansa yake yi,suna so suyi magana amma fargaba ta hanasu,

  Hannu yasa ya daki ƙirjinshi da ƙarfi,lokaci guda idanuwanshi suka juye tamkar ba mutun ba,rarumar plastic chair ɗin dake agaban gadon Marshal yayi azafafe yayi wurgi da ita,nan take kujerar ta yi gefe guda ta daki ƙasan tiles,

A razane suke kallonshi,wata irin zufa ce ta soma gangarowa ta gefen fuskarshi,ɗaya bayan ɗaya yake binsu da kallo,jikinsu sai kerma yake yi,Dr Emran ma ƙoƙarin guduwa yake yi,Armstrong kuwa sai lalla6ashi yake yi akan su sanar dashi abunda ke faruwa tun kafin ya birkice masu,

   "Rafayet"!muryar Marshal Omar ce ta dawo dashi cikin hayyacinshi,jiki na rawa ya juya yana kallonshi,a hankali Omar ke buɗe idanuwanshi waɗanda sukayi jawur dasu,zufa ta ko'ina ajikinshi duk da sanyin A.c ɗin dake akwai,da sauri Sgr ya koma gefen gadon ya zauna tare da ruƙo hannunshi,

  "Omar pls tell me,what's happening wit u?meyasa na ganka a asibiti?Are u not feeling well"?daƙyar Marshal ya samu ya yunƙura tare da mikewa ya zauna,numfashinshi da huci yake fita,bawan Allah yaji jiki sosai,wasu zafafan hawaye ne suka wanke mashi fuskarshi,

  Muryarshi na rawa yace"Bro,Yaushe ka dawo Abuja?

   Muryar Sgr tamkar zai yi kuka yace"Omar duk ba wannan ba,Where's Junaid?nadamu akan son ganinshi,Daddy ma yana ta kira na saboda rashin samun Junaid a waya..."ya ƙarasa maganar yana faman haɗiyar yawu,

Marshal na ƙoƙarin buɗe baki yayi mashi magana,Karaf idanuwanshi suka sauka akan Major dake girgiza mashi kai alamar karya kuskura ya faɗa mashi,kasa magana Omar yayi,sai ma zuba mashi ido da yayi yana kallonshi,

  "Wai menene haka?kowa na tambaya sai yayi mun shiru babu magana?meke faruwa ne!in wani abu ne ya faru ba zaku sanar mun ba ne?Ni fa Musulmi ne!nayi imani da ƙaddara mai kyau ko mara kyau,ku faɗa mun mana......"ya ƙarasa maganar fuskarshi ɗauke da matsananciyar damuwa,

   Daƙyar Omar ya iya buɗe baki yace"Babu abunda ya faru,Junaid yana lafiya...."tunkan ya ƙarasa maganar Sgr yace"That's impossible!Taya zaka ce mun junaid yana lafiya kuma in yarda?To idan yana nan a nuna mun shi inaso in ganshi!Meyasa layinshi a kashe?meyasa nake ganin hawaye akan fuskarka?

  Daurewa kawai Omar keyi,saboda kukan dake cinshi,So yake ya fashe da kuka ko ya samu ya rage raɗaɗin dake acikin zuciyarshi,

   Tausasa murya Sgr yayi"pls Omar,ka sanar dani!ina ƙanina yake?wani abu ya faru dashi ne?saboda shi jiya ko bacci ban samu ba,

  Da sauri Omar ya sanya tafin hannunshi tare da share hawayenshi,

   "Rafayet!I won't hide it for u,Junaid was kidnapped...."daƙyar ya ƙarasa maganar ganin irin kallon da Sgr ke jefa mashi,kallon tuhuma,

   "Omar,ni kake faɗama cewa Anyi kidnapping ɗin junaid"?shiru Omar yayi batare da yace mashi komai ba, 

 "Omar,If it is true,Junaid was kidnapped,as a Senior Soldier with the rank of Marshal,you will be brave enough to rescue him,bawai na ganka kwance a gadon asibiti ba kana zubar da hawaye,"tausasa muryarshi yayi"don Allah Omar ka faɗa mun gaskiyar abunda ya faru,kada kasa zuciyata ta buga,Ina junaid ɗina yake?meya faru dashi?yanayin yadda yayi maganar ne yasa jikinsu kara yin sanyi lakwas,

  Daƙyar Major ya daure ya cije,ya yi karfin halin bude baki yace"Sir,Junaid ya riga mu gidan gaskiya!junaid ya koma ga mahalicci....."bai ƙarasa maganar ba sakamakon Zaburar da yaga Sgr yayi gadan gadan ya tunkareshi,yana faɗin",repeat what u just said Major!"yana magana yana naɗe hannun rigarshi alamar zaiyi dambe,da sauri Omar ya ambaci sunanshi Rafayet,wanda hakan ya dakatar dashi tare da juyawa yana kallon Omar,

  Cikin shesshekar kuka Marshal yace"Junaid has gone forever,wanda yafi mu sonshi ya kar6i abunshi,jiya da daddare around 8,Suna kan hanyar dawowarsu acikin mota shi da jahad,ta fita ta siya masu ice cream tabar junaid acikin Motar,kafin ta dawo,babbar mota tabi ta kan motarshi,Rafayet bamu samu komai daga sassan jikin junaid ba,Ya ƙone ƙurmus acikin motar........"kasa ƙarasa maganar yayi,ya fashe da wani irin matsanancin kuka mai cin rai tare da buga hannuwanshi saman gadon,

  Tashin hankali!!!Kasa motsawa Sgr yayi daga tsayen da yake,kamar an dasa mashi aya,Tsit ka ke ji,kowa yasha jinin jikinshi Sgr kawai suke kallo,

Almost 15 mins,Kafin ya motsa pink lips ɗinsa a hankali ya furta"Omar!Do you wanna say that Junaid is dead?

  Jinjina mashi kai marshal yayi alamar eh,abun mamaki sai suka ga yana murmushi gami da girgiza kanshi yace"I can't believe that junaid is gone,this is a fabricated lie, Omar you're just kidding me and I don't want it...."

  Tsananin tausayinshi ne ya kama Omar,dama yasan cewa zaiyi wuya ya yarda cewa Junaid ya mutu,

  "Sir,we are really sorry.....'Dr Emran ne ya ambaci hakan,a sukwane Sgr ya juya tare da kallonshi aruɗe yace"Sorry for what"?

  Shiru yayi baice komai ba,ɗaya bayan ɗaya yake kallonsu,a wani irin yanayi mara misaltuwa,fuskarshi duk ta hargitse,jikinshi yayi laushi,guiwarshi ta sage,ƙafafuwanshi sun gaza ɗaukarshi,ga6o6in jikinshi duk sun saki,Zuciyarshi ta raunata sosai,

   Wani farin ruwa ne ya kwanta luf acikin fararen idanuwanshi,jinjina kanshi kawai yake yi batare da ya furta komai ba,temperature ɗin jikinshi yayi zafi sosai,yadda ko mutun ya matso kusa dashi,sai yaji hucin jikin nashi,wata irin zufa ce ta soma tsastsofa mashi,a jikinshi lokaci guda ya jiƙe sharkaf,gaba ɗaya sun zuba mashi ido suna kallonshi,gwanin ban tausayi,

   "Wai Junaid ne ya mutu?tatsuniya ce ko mafarki"?muryarshi na kerma yayi maganar,

   "Enough is enough! What do you want me to say to our father? How can I inform him about Junaid's death?saboda shi  ko bacci baiyi ba jiya,Nima haka,meyasa mutuwa zata yi mun yankan ƙauna ne?

   Sulalewa yayi saman guiwowinshi wani irin biji biji ya fara gani a idanuwanshi,a hankali ya shiga furta"Innallilahi wa'inna ilaihirraji'un,Ya Allah kasa mafarki nake yi ba gaske ba,meyasa ni bata ɗauke ni ba ta ƙyale Junaid?Why!why!'da sauri Dr Emran tare dasu Major suka kewayeshi suna tottofa mashi addu'o'e asaman kanshi,wani irin jijjiga jikinshi ya soma yi,hakan ba ƙaramin ɗaga masu hankali yayi ba,a Ruɗe marshal ya saukko daga saman gadon ya nufosu jiki ba ƙwari ya zube agaban Sgr wanda tuni ya yanke jiki ya faɗi,kuka sosai Omar yake yi kamar ya haɗiyi zuciya,rungume Sgr yayi sosai ajikinshi,Ya tsorata da jin irin zafin da jikin Sgr ya ɗauka,tamkar hucin wuta ,

  "His body temperature was very high,I think he got a heatstroke,yana buƙatar Emergency treatment,"Dr Emran ne yayi maganar,batare da 6ata lokaci ba a gaggauce suka ɗaukeshi izuwa saman medical bed ɗin da Omar ya sauka suka kwantar dashi,doctors ne suka taru akanshi,ga jinin shi ya hau sosai,


Daga waje suka koma,Saman waiting seats suka zauna suna jiran tsammani,ɗage kanshi yayi jikin seat din yasa Hanky ya rufe fuskarshi,Allah kaɗai yasan irin raɗaɗin da yake ji acikin Zuciyarshi,bakowa yafi ji ma tausayi ba,Fa ce Abbansu,don muddin yaji irin Mummunar mutuwar da Junaid yayi tofa Zuciyarshi zata buga ne,A rasa duka biyun,Sojojin dake a kewaye dasu,sai tausarshi sukeyi ganin yadda kamanninshi suka sauya saboda damuwa,

  "Haƙuri zamuyi yalla6ai,nasan abun da ciwo,raɗaɗinshi yafi ƙunar wuta,Amma ya zamuyi?mutuwa ce tana akan kowa,Junaid addu'armu yake bukata a yanzu,Allah ya jiƙanshi,ya gafarta mashi zunubbanshi,Yasa can yafi mashi nan,Su kuma waɗanda suka shirya mutuwarshi,Allah ya tonu asirinsu,don bazamu ƙyalesu ba,sai sun ɗanɗani kuɗarsu,"sosai Major ya shiga tausarshi yana ƙara ƙarfafa mashi guiwa,

  a hankali Omar ya zame hanky ɗin dake akan fuskarshi,ta kumbura sosai la66ansa sunyi suntum,idanuwanshi sunyi jawur dasu luhu luhu,daƙyar ya iya buɗe baki yace"Nagode sosai Major,naji daɗi sosai,kalamanka sun dan sanyaya mun zuciyata,Amma inaso ka sani rashin Junaid atare damu babban gi6i ne,wanda babu wanda zai iya cike sa,he's our weakness!maƙiyanmu sunci galaba akanmu!Sun kashe mana duk wani ƙwarin guiwa da muke dashi!laifin me junaid ya aikata da ya cancanci wannan ɗanyen hukuncin?Yaron da baison komai ba,Soyayyar ƴan uwansa kawai ya sani,burinshi koda yaushe ya sanya kowa farin ciki,amma yau an samu wasu marasa imani,Marasa tausayi,sun yi silar mutuwarshi!wlh ɗaya daga cikinsu bazai shaba,Sai sunyi danasanin haihuwarsu da uwarsu tayi acikin duniyar nan,"yana magana hawaye na wanke mashi fuskarshi,

Major na ƙoƙarin buɗe baki yayi magana,Suka jiyo hayaniya daga can cikin asibitin,Sautin kuka suka jiyo mai sautin gaske,Gaban Omar ne ya faɗi rasss jin Muryar jahad wadda tun a jiyan su major suka sa aka maido ta nan,A hanzarce suka miƙe tsaye suna kallon wurin da sautin ke fitowa,da gudun gaske take tunkarosu nurses sun biyota da gudu,sae ihu takeyi tana faɗin"wuta!wuta!Junaid yana acikin wuta,ataimaka a fito mun da ɗan uwana,kada ta ƙona shi,"wannan shine sambatun da takeyi,tashin hankali!

  Duk da jikinshi ba ƙwari haka ya nufeta,tare da ruƙota jikinshi,idanuwanta sun juye kwata kwata bata iya gane wanene agabanta,ita dai kawai sunan junaid take ambato acikin bakinta,hankalin Omar ba ƙaramin tashi yayi ba,tsoranshi kar ace ta samu ta6in hankali,don da alama abunda ke shirin faruwa kenan,

   "Jahad!ki natsu ki kalleni,Ya Omar ne fa"

  Kuka takeyi sosai,jijiyoyin wuyanta duk sun firfito waje,don bala'e Allurar kashe jiki akayi mata,Amma babu abunda allurar tayi mata,tamkar an ƙara mata ƙarfin jikinta,baiwar Allah taga tashin hankalin da bata ta6a gani ba,kuma akan Masoyinta da take tsananin so,

  Jijjigata ya shiga yi yana ambaton sunanta"Jahad!Ina zaki je?

   Firgita tayi agigice ta dinga faɗin"Gashi can!yana kuka wuta!wuta!ke ci ajikinshi!Yana kuka,Ya Omar a fiddo shi kada ya mutu ya barni,"da ƙarfi take yin maganar tamkar maƙoshinta zai 6allo,ƙoƙarin ƙwacewa take yi daga hannunshi don taje wurin abunda idanuwanta ke hango mata,Ko ina ta kalla,sai taga motar junaid tana ci da wuta,shine abunda idanuwanta ke nuna mata,

  Hawaye ne suka kuma wanke mashi fuskarshi,tsananin tausayin jahad ne ya kamashi,gaba ɗaya babu natsuwa atare da ita,ta haukace ta gigice ta firgice,kamar wadda tayi shekara ɗaya tana hauka,

   Hannu yasa tare da sa6arta saman kafaɗarshi,saboda rashin ƙwarin jikinshi,har tangal tangal yayi kamar zai faɗi daƙyar ya samu ya tsayar da kanshi,wuce wa nurses ɗin sukayi gaba yabi bayansu,yana jin yadda jahad keta bugun bayanshi,ta dunƙule hannayenta sae ɗumarshi take yi don ya saketa,Allah sarki innocent girl kamar jahad,yau ta zauce har tana bugun Ya Omar ɗinsu,

  Er nurses ɗin suka wuce har zuwa room ɗin da aka kwantar da ita,Shiga yayi da ita ciki,a lokacin har jikinta ya fara saki,alluran da aka ɗurka mata sun fara aiki,a hankali ya kwantar da ita saman gadon,kamar matacciya haka ta koma,ko yatsanta bata iya ɗagawa,la66anta sun bushe sosai,sun farfashe sakamakon ciccijesun da tayi,tsayawa yayi daga tsaye yana kallonta,idanuwanta suna a rufe,tunda yake a rayuwarshi bai ta6a fuskantar tashin hankali irin na jiya da kuma yau ba,bai ta6a cin karo da mummunar rana ba,irin ta yau,ta ko'ina babu sauƙi,zuciyarshi har wani tafarfasa takeyi saboda ƙunar da takeyi mashi,

  Shigowa cikin ɗakin Major yayi tare da wani baturen Likita,jin sallamarsu yasa Omar juyawa yana kallonsu,da sauri ya tunkari Doctor ɗin yana tambayarshi dangane da jahad,

  "She is having a panic attack as a result of the incident"acewar Dr Antony,

   Dafe kai Omar yayi da hannu ɗaya ya ɗan runtse idanuwanshi tare da buɗesu,Muryarshi a kasalance yace"Yanzu Doctor babu yadda za'ae yarinyar ta dawo cikin hayyacinta!"

  Dr Antony yace"It will be very difficult for us to overcome her now,but we will do our best to see her regain consciousness,"

  "Pls Dr,try as much as u can"

Jinjina kai Dr antony yayi,tare da dafa kafaɗar Marshal don ya lura baya acikin hayyacinsa

   "Calm down ur mind,she will be ok,zamu yi iyakar bakin ƙoƙarinmu wurin ganin mun shawo kanta,"

   Daga haka Major ya ruƙo hannunshi suka fito daga waje,zama fa bai gansu ba,Zarya ya shiga yi tsakanin room ɗin da Jahad take ciki dakuma room ɗin Sgr,sam ya kasa samun natsuwarshi tuni ya mance da shima mara lafiya ne,ana cikin wannan tashin hankalin,Tsautsayi yasa Omar ya kar6i wayarshi daga hannun Major,Yana kunnata kwatsam!sai ga kiran Abbansu ya shigo cikin wayar kamar jira yake yi,!

  Zubawa screen ɗin wayar ido yayi,tare da ɗagowa ya kalli Major,tun kafin ma yayi magana,major ya riga shi cewa"Abba ne ko"?ɗaga mashi kai yayi alamar eh,

   "Seriously I can't pick his calls,saboda bansan amsar da zan bashi ba,if he asks about junaid,"ba don yaso ba haka ya katse kiran Abbansu,Abunda bai ta6a yi ba arayuwarshi,

   yana ƙoƙarin kashe wayar gaba ɗaya sai ga message ya shigo ta sama,hannunshi na kerma ya buɗe message ɗin,fearfully ya soma karantawa,

  _Omar kun kyauta ku dukanku,kowa yaƙi ɗaga kiran wayata,dama inaso in sanar dakai cewa,Yau zamu dawo gida_

  Saboda tsabar kiɗima,Omar baisan lokacin daya saki wayarshi ba,ta faɗi ƙasa sosai ta daki tiles ɗin,

  "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'Un!Allahumma ajirni fil masibati wa'aklifni khairan Minha"wannan shine abunda yake ambato acikin bakinshi,

   "Major menene mafita?Ka taimaka min!abubuwa sunyi mun yawa,Ya zanyi da rayuwata!Babu Junaid,Jahad ta zauce!Ga Sgr ma a kwance gadon asibiti,Na shiga uku ni yau!wannan wace irin baƙar rana ce!?

  Wani irin tausayinshi ne ya lullu6e major,janyoshi yayi ajikinshi ya rungumeshi sosai,dama a buƙace yake da ya samu kafaɗar da zai aza kanshi,Ya zubar da hawayenshi sosai,ko ya rage raɗaɗin dake acikin zuciyarshi,

  Cikin shessheƙar kuka yace"Major menene mafita yanzu?Ya zanyi da Abbansu?

  Hannu major yasa yana ɗan bubbuga bayanshi yace"Sir,in sha Allah komai zai tafi dai dai,bazamu rasa abunyi ba bi'iznillahi,"

   Ruƙo hannun Omar yayi suka koma saman waiting seat ɗin suka zauna,kwantar da kanshi ya kumayi asaman kafadar major,sai faman sauke ajiyar zuciya yakeyi,bakomai yake faɗo mashi arai ba,fa ce Fuskar Baby Junaid ɗinsu,mai ɗauke da wannan kyakkyawan Murmushin,


   *Boss Bature*


*Sehrish*


Around 1:30 na rana,

Zaune take asaman Sofa ta zabga Uban tagumi,tunda Daddynsu ya sanar da ita game da tafiyar Sgr Abuja,take jin kanta kamar ba cikakkiyar mutun ba,Bataso tafiyarshi ba,duk da ta yi mamakin tafiyar tashi,kewarshi duk tabi ta lullu6eta,ga kewar gida yau 3 days kenan suna a kano,Yanzu gidan ya rage daga ita sai Oummansu,tun kafin a fara kiran sallah,Maman sadeeq suka koma gidansu,Abusufyan ne ya ɗaukesu acikin motarshi,hannu takai tare da ɗaukar wayarta dake ajiye agefenta,Contact ta shiga tare da lalubo numbar jahad ta buga mata kira,

  Guntun tsoki taja,jin layin nata a kashe,Layin Junaid ta kira Shima a kashe,hakan ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba,Layin Hosana ta kira,a lokacin sun kammala haɗama Omar breakfast ɗinshi,har ta koma ɗaki ta shiga toilet tayi wanka,tana zaune gaban mirror tana kwalliya jikinta sanye da gown,wayarta dake ajiye saman drawer ta soma ringing,duk a tunaninta ya Omar ɗinta ne,jiki na rawa ta miƙe hada tuntu6e wurin yin saurin ɗaukar wayar,koda taga kira daga Sehrish ne,jiki na rawa tayi picking call ɗin tare da kara wayar a kunnanta,

  Tunkafin Sehrish tayi magana,hosana ta ruga ta cewa"Wai yaushe zaku dawo ne?gidan fa ba kowa ni kaɗaice,

   "Hosana wai ina jahad ne?ina kuma junaid?basu dawo daga shan ice cream ɗin bane tun jiya da suka fita?na shiga damuwa saboda rashin samunsu a waya,"

  Hosana tace"Nima bansan inda suka je ba,babu fa kowa gida,daga ni sai Aunty azmee,ya Omar bansan shima ina yaje ba,"

   Hankalin sehrish yayi matuƙar tashi,la66anta na kerma tace"Hosana!yaya Rafayet baizo nan gidan ba"?

  "Eh,baizo ba,ni banga kowa ba,"

Nan take ranta ya bata cewa wani abu ya faru acikin gidan,kuma bada kowa ya faru ba,fa ce Su Junaid da suka fita shan ice cream,saboda rashin dawowarsu cikin gidan

  "Rishi ko breakfast na gaza ci,ina cikin matsananciyar damuwa,"

  Ajiyar zuciya Sehrish ta sauke tare da cewa"Hosana ki kwantar da hankalinki,Zasu dawo cikin gidan ne,Yanzu zan sanar dake wani abun farin ciki nasan zaki ji daɗi sosai,

   Muryarta aɗan shagwa6e tace"toh faɗamun menene"

   Sehrish ta miƙe tare da nufar ɗakin Oummarsu tana faɗin"Nasan Daddy bai sanar dake ba ko"?

Hosana tace"meke nan"?

Shiga cikin ɗakin tayi wayarta manne a kunnanta,

  Video call ta mayar da kiran nasu,bayan ta samu wuri ta zauna gefen Oummansu dake ta bacci hankalinta a kwance,

  "Hosana kalli ki gani,Wacece wannan,"tayi maganar tare da saita Screen ɗin wayar saitin fuskar Oummansu,

  Ƙura ido hosana tayi tana kallon fuskar oummasu,almost 7 mins,a hankali wani kyakkyawan murmushi ya bayyana akan fuskarta,a ruɗe tace"rishi Oumman mu ce ko?

   "Eh itace,naso na sanar dake tun jiya,baki dauki wayan ba kuma bansamu halin sake kiran ba,An samu Oummanmu,Amma bata acikin hayyacinta ta samu ta6in hankali,

  Uban tsalle hosana ta daka,da gudun gaske ta fito daga ɗakinsu,kaitsaye ta nufi kitchen inda ta baro Azmee tana gyare gyare,Cikin rashin sani Hosana taci karo da haroon,ta bangaje shi sosai har wayar dake hannunta ta kubce mata,kaitsaye ta faɗi ƙasa ta daki Tiles Screen ɗin ya fashe,

  Hannu hosana ta aza asaman kanta ta fashe da wani irin matsanancin kuka,tana faɗin"Wayyo Allah wayata!Ka kashe mun wayata,Wlh bazan yafe maka ba,Allah ya isa,"

  Rai a6ace haroon ya ɗaga hannu zai mareta,adai dai lokacin Azmee ta fito daga kitchen ɗin,A ruɗe ta ƙaraso ta damƙi hannunshi,wani mugun kallo daya jefa mata sai da gabanta ya faɗi rass saboda launin idanuwanshi da sukayi jawur dasu,fuskar nan tashi tayi suntum da ita,da sauri azmee ta saki hannunshi,cikin sanyin murya tace"Allah ya huci zuciyarka,"

  Harara ya wurga mata tare da jan dogon tsoki mai sautin gaske,matsawa yayi izuwa inda wayar hosana take a ƙasa,Ya sanya faffaɗan tafin kafarsa mai sanye da takalmi,Ya take wayar ya rugurguzata,hakan ba ƙaramin ƙona ma hosana rai yayi ba,Abun ka ga mai ta6in hankali,Kamar kura ta mamayeshi tare da gartsa mashi cizo asaman damtsen hannunshi,Dama ƴar singlet ce ajikinshi,ƙoƙarin janyeta ya dinga yi amma taƙi cire haƙoranta daga saman fatar hannun,har sai da ta fasa shi,jini ya shiga tsastsafowa a wurin,waro ido waje haroon yayi ganin ta fitar mashi da jini a fatar jikinshi,ƙwaƙƙwarar damƙa yakaima Gashin kanta,Hankalin Azmee ba ƙaramin tashi yayi ba,Ga tsoron shiga huruminshi take yi don tasan halinshi ba imani ya cika ba,Yasha ɗaga hannu zai mareta,

  Wurgi yayi da hosana,gaba ɗaya ta tafi zata faɗi ƙasa,Azmee takai hannu zata ruƙota,

  Tsawa ya daka mata tare da cewa"kika kuskura kika ta6a ta abakin aikin ki cikin gidan nan!uwar shisshigi kawai,ki tsaya a iya matsayinki,"jiki asanyaye azmee ta tsaya tuni idanuwanta suka cicciko tab da ƙwalla,tana ji tana gani haka hosana ta kife ƙasa,fuskarta ta bugu sosai har hancinta ya fashe,

   Haura ƙafa yayi ya wuce Can medical room ɗinsu,saboda yayi dressing raunin da taji mashi,

  "Hosana"Azmee ce ta ambaci sunanta,tare da zuƙunnawa agabanta,tasa hannu ta janyota ajikinta,Lallashinta ta shiga yi,abun ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,Haroon ya 6ata mata rai,

  Cikin shessheƙar kuka tace"Aunty azmee,Kalli yarda ya fasa mun wayata,mutumin can baida imani shi ba jininmu bane,"hannu Azmee tasa tana share mata hawayenta,

   "Kiyi hakuri hosana,Allah shi zai saka maki,"

  Daƙyar azmee ta samu ta lallasheta,har ta rakata ɗakinsu ta kwantar da ita tana ta ajiyar zuciya,cikin lokaci ƙanƙani bacci ya ɗauketa,

  Dawowa falon Azmee tayi wurin da wayar Hosana ta fashe,hannu tasa ta ɗauki wayar tana kallon screen ɗin,Ya dagargaje sosai baka iya ganin komai,


A 6angaren Sehrish kuwa,duk tabi ta ruɗe lokacin da taji sautin kukan hosana,kafin haroon ya taka wayar ta ƙarasa mutuwa gaba ɗaya,zumbur ta mike tana zarya acikin ɗakin,kamar tayi tsuntsuwa ta tafi Abuja haka take ji,ta ƙagara tasan meke faruwa acan ɗinne ... .. '


Tashin hankali!Su marshal na zaune zaman jiran tsammani,sae ga Sgr ya fito daga room ɗin da aka kwantar dashi,Ko riga babu ajikinshi ya yageta ya cireta,ƙirar ƙarfin nan tashi mai matuƙar tsoratarwa gata nan a bayyane,Tsokar jikinshi sai rawa takeyi,miƙewa sukayi gaba ɗayansu suna kallonshi,

  "Rafayet"!Omar ne ya ambaci sunanshi tare da tunkarar shi,damtsen hannunshi ya ruƙo acikin nashi yana sake ambaton sunanshi

  "Omar!I can't believe that junaid has gone,till the day i found out those who planned his death!One by one sai na kashe su da hannuwana,daga nan ne zan yarda cewa Na rasa shi na har abada,wlh in har ban aikata abunda na faɗa ba,Sai na ajiye aiki na"daƙyar yake magana saboda zuciyarshi dake a harzuƙe,jininshi na akan akaifarshi,

  ƙoƙarin kama hanya yake yi yabar wurin Omar ya rurruƙeshi saboda baisan inda zai dosa ba,Likitocin dake kula dashi duk sun kewaye shi sae faman tausarshi sukeyi suna lallashi,Amma ina idanuwanshi sun rufe rufff,baya ji baya gani,

  "Rafayet ka kwantar da hankalinka mana!Duk yarda ka ke jin radadin mutuwar nan nima haka nake ji,nama fika jin raɗaɗi saboda Gani nake yi kamar ni ne silar mutuwarshi,Akan idona Junaid yabar gidan acikin motarshi na gaza dakatar dashi,Har Major sai da ya bani shawara amma banyi saurin ɗaukar mataki ba,Wlh kamar na haɗiyi zuciyata na mutu haka nake ji,"dakatawa ya ɗan yi da yin maganar yayin da suke kallon juna,shi da Sgr idanuwan kowannansu cike tab da Hawaye ba ƙaramin jiki suke ji ba,

  Tausasa muryarshi yayi kafin yaci gaba da cewa"Rafayet!yakamata muyi tunani akan mahaifinmu!mu nemi mafita,domin kuwa ya sanar dani cewa suna akan hanyar dawowa gida yanzu haka,kaima kasan irin yadda yake jin junaid aransa,muddin yaji mutuwarshi tofa zamu rasa shi ne,a yadda shekarunshi suka ja ɗinnan bakomai zai iya jurewa ba,"

  Jikin Sgr ba ƙaramin sanyi yayi ba,bawan Allah duk yabi ya susuce ya rasa kuzarin jikinshi,

   "Omar,yanzu ina ita yarinyar take ne"?yayi tambayar yana kallonshi,

   "Jahad ta zauce yanzu haka an kwantar da ita,ta samu bacci,"

  Jinjina kanshi ya ɗan yi,Shiru sukayi na wani lokaci,kafin Major yace"Yakamata mu nemi mafita,lokaci yana ƙure mana!"


Doctor Emran ne ya basu shawarar su shiga ɗaya daga cikin resting rooms na asibitin,yadda zasu ji daɗin tsara yadda zasu tunkari Abbansu,


Katafaren ɗaki ne ya haɗu sosai,wuri kowannansu ya samu ya zauna,Omar Da Sgr suna zaune daga gefen gadon ɗakin,Major tare da Dr Emran  da Armstrong suna zaune asaman doguwar sofa ɗin dake a ɗakin,Sanyin A.c ɗin dake a ɗakin ba karamin sanyaya masu zuciya yayi ba,almost 15 mins kowa yayi shiru babu mai magana acikinsu,Kowa da abunda ke zuwa mashi aranshi,

  "Yalla6ai mi zai hana asamu babban malamin addini ya fahimtar dashi ta hanyar tausarshi da daɗaɗan kalamai,tare da janyo mashi ayoyin al kur'ani,"acewar Major 

Dr Emran yace"that wouldn't be a solution a yanzu dai,gaskiya a yadda naji irin son da yake yi mashi muddin yaji irin mummunar mutuwar da Junaid yayi tofa wannan ba zai yi tasiri ba,zamu rasa shi,Zuciyarshi zata buga ne...."

  Armstrong yace"Koda za'a sanar dashi,Ni shawarata kada a faɗa mashi ainihin abunda ya faru,Ina nufin irin mutuwar da Junaid yayi,kawai asanar dashi cewa Ya rasu ne ta hanyar rashin lafiya na rana ɗaya..."tun kan yakai ƙarshen maganar Omar yace"idan ya nemi ganin gawarsa fa?Ya zamuyi kenan"?

  Shiru Armstrong yayi can yace"sai ace anyi burying dinta tunda dama ku baku taking time kafin ku rufe deceased" wani kallo Omar yayi mashi yace"kana ganin in ance masa hakan zan yarda ne,alhalin yana araye,sam hakan ma ba mai yuwuwa bane" shiru Armstrong yayi don kuwa bai yi nazari ba kafin ya bada shawarar,

  "To yalla6ai mezai hana kawai a 6oye mashi komai game da mutuwar Junaid ɗin!in yaso koda ya tambayeshi sai asanar dashi cewa,Sgr ya tura shi U.s ne,wurin yin training ɗin aikin soja,"Major ne yayi maganar,

  Murmushin takaici Omar yayi tare da kallonshi yace"Ita kuma jahad ɗin fa?ko itama mun turata U.s ɗinne training?

  Duƙar da kai ƙasa major yayi,Sgr dai bai tanka masu ba shi kaɗai yasan irin tafarfasar da zuciyarshi keyi mashi,

  "Gaskiya akwai gagarumar matasala!yanzu idan muka ce an tura Junaid U.s zai kar6i training ɗin soja,Jahad kuma ya zamuyi da ita?Zata tona mana asiri ne,ta hanyar sambatun da takeyi in har bata dawo hayyacinta ba,koba wannan bama Shi Abban zai iya buƙatar yin waya da jubaid!Dole fa ya nemi layin waɗanda ke a u.s don yaji ya lafiyar ɗanshi,duk kuma in hakan bata samu ba zai ce zaije can ne don ya ganshi"Marshal Omar ne yayi wannan jawabin 

  Armstrong yace"Inaso naji abunda Sgr zaice,Saboda nasan baza a rasa mafita a wurinshi ba,"

  Mayar da hankalinsu su kayi akan Sgr wada ya ɗan lumshe idanuwanshi,

  Cikin sanyin murya Omar yace"muna sauraronka ya zamuyi yanzu?Daddy yakusa dawowa,kuma da alama bashi kaɗai zai dawo ba,dukkansu zasu dawo",saboda tsabar tashin hankalin da suke ciki,Ko tunanin abinci ma basuyi,bawai don basu jin yunwa ba,

Slowly ya buɗe idanuwanshi sai lokacin ya soma magana atsanake 

   "Duk shawarwarin da kuka bayar ba masu 6ullewa bane,a karshe dai dole mahaifinmu yasan cewa ɗanshi ya mutu,Ba don naso ba,Amma ba yadda zanyi ne,ya zama dole muyi wa mahaifinmu ƙarya a karo na farko don mu ceto rayuwarshi...."dakatawa ya ɗanyi da yin maganar,yana sauke ajiyar zuciya kafin ya ɗaura da cewa"Shawarata shi ne,Za'a sanar dashi cewa,Anyi kidnapping ɗinsu su duka biyun!saboda babu junaid jahad kuma ta zauce,muddin muka mayar da ita gida asirinmu zai tonu ne,kuma mahaifin yarinyar yanzu yana cikin farin cikin ganin mahaifiyarsu,idan har ya dawo ya samu ƴarshi a cikin wannan yanayin yaya kuke tunanin zaiji aranshi?ga kuma babban rashin da mukayi na Junaid!that's the reason why ya zama dole a killace Jahad acikin asibitin nan na tsawon wasu kwanaki har asamu ta dawo cikin hayyacinta,hikimar yin hakan shi ne na farko idan daddy yaji cewa anyi kidnapping ɗinsu,tabbas hankalinshi zai tashi sosai,Amma zai sa ran bayyanar junaid a koda yaushe,kuma zamu sanar dashi cewa Junaid zai dawo Zamuyi ƙoƙari wurin ganin mun ku6utar dashi hakan zaisa Ya ɗan ji sauƙi aranshi duk da zai shiga matsananciyar damuwa,mu kuma zamuyi ƙoƙari wurin ganin mun shawo kanshi,Abu na biyu shi ne bayan wasu ƴan kwanaki idan Allah yasa Jahad ta dawo cikin hayyacinta,Zamu lallasheta ne nasan zata fahimce mu,Zamu fara sakinta ta koma gida a matsayin su kidnappers ɗin suka saketa,Wannan zai ƙara kwantarwa Abbanmu hankali saboda zaisa Ma ranshi cewa shima junaid zasu sako shi,Ta wani 6angaren Abusufyan ma zaiji sauƙi aranshi in yaga dawowar Jahad,may be ma kafin ya dawo daga kano zata koma,so daganan a hankali a hankali zamu cigaba da ƙoƙarin fahimtar da Daddy,koda zaisan cewa junaid ya mutu sai daga baya lokacin komai ya wuce kamar next 1 to 2 month haka,Sae asamu babban malami ya zaunar dashi yayi mashi nasiha sannan ya sanar dashi ainihin abunda ya faru,radaɗin da zaiji aranshi bazai kai raɗaɗin da zaiji ba a yanzu idan aka sanar dashi..."yana kai ƙarshen maganar shi,ya rufe idanuwanshi yayin da zuciyarshi keta harbawa,

  "Good Idea"!acewar Armstrong,

Major ya ɗaura da cewa"Yanzu yakamata a fara kawar da duk wani abu wanda zaisa Labarin hatsarin daya faru yaje masu,dama an kori ƴan jarida daga wurin,yanzu haka akwai sojojin dake kewaye da wurin an rufe shi,basu bari kowa ya ɗauki video ko hoton abunda ya faru ba,Zamusa su tsananta bincike akan mutanen dake a wurin dama kuma ba wasu mutane da yawa ne su kai witnessing incident din ba,ko masu wuce wa a mota babu sosae,dakuma mai siyar da ice cream ɗin nan,Hatta wayarshi za'a canza mashi saboda gudun kar ace ya dauki rahoto in ma ta kama asa ya canza wuri ne sai ayi hakan,Zamu toshe duk wata hanya da zaisa labarin mutuwar Junaid yaje kunnan mutanen gidan in sha Allah,"

Jinjina kai Omar yayi tare da cewa"hakan yayi,Yanzu yakamata a hanzarta zuwa yi mashi jana'iza,Yamu yamu zamu halarta wurin yi mashi sallah,mu binne tokarsa awurin,bayan an kammala sai a kawar da ƙarahunan Motar,A shafe duk wani abu da zai nuna cewa Anyi hatsarin mota a wurin,"cikin karyayyar murya ya yi maganar.


Sun jima suna tattaunawa akan yadda zasu tafiyar da komai,daga bisani wuraren karfe 2,Suka ɗunguma gaba dayansu zuwa wurin da incident ɗin ya afku,Sgr kamar yayi hauka lokacin daya yi arba da motar Junaid,Yaji mutuwar nan har cikin ranshi,daƙyar suka samu kowa ya dan daidaita natsuwarshi,Alwala su kayi gaba ɗayansu banda Armstrong da wasu da suka kasance ba musulmai ba,Anan sukayi mashi Sallah tare da burying ɗin tokarsa A gefen wata bishiya,bayan sun gama jana'izar,sojoji suka kawar da motarshi daga wurin,jikin kowa fa yayi mugun sanyi,Don suna kammala sallar jana'ixar Sgr ya zukunna gefen ƙabarin Junaid,tare da kwantar da kanshi asaman ƙabarin,Addu'o'e ya shiga jerowa abakinshi yana tottofa mashi,a ƙarshe yace"Allah ya jikanka Junaid,bazan ta6a yafewa kaina ba,idan har ban ɗauki fansa akan irin kisan wulakancin da akayi maka ba,Na ɗaurawa kaina alhakin mutuwarka,Saboda laifina ne Junaid da ban baka kariya ba,na tabka babban kuskuren da har duniya ta naɗe bazan ta6a mantawa dashi ba,"

   Kasa ɗagowa yayi daga kan  ƙabarinsa,

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




   Kasa ɗagowa yayi daga kan  ƙabarinsa,

  Marshal Omar ne ya ɗaura da cewa"In sha Allah junaid na aljanna,muna yi mashi kyakkyawan fata,Allah yasa ƙarshen wahalarshi kenan,"gaba daya basu ji daɗin irin yadda mutuwar junaid ta kasance ba,kamar wani mara gata,babu mahaifinshi akusa babu ƴan uwanshi,

  Ruƙo hannun Sgr major yayi,tare da janyoshi,jikinshi duk ya saki,daƙyar ya iya mikewa ya tsayar da kanshi akan ƙafafunshi,

  Sojojin dake kewaye da wurin sunyi su 50,Layi sukayi wani na bin wani,kowa yazo wurin ƙabarinsa sai ya tsaya ya tottafa mashi addu'a kafin ya wuce,Na bayan shi yazo shima yayi mashi addu'a a haka har suka kammala,ba tare da mutane sun samu damar tsayawa ganin abunda ke faruwa ba,dama kuma hanyar sam ba mutane sosae.

   Basu bar ƙabarin junaid a fili ba,saboda gudun kada mutane su dinga tattake wurin batare da saninsu ba,ko su zauna abakin bishiyar,waya suka sa suka kewaye bishiyar,


Sun jima a awurin cike da jimamin mutuwar junaid,kafin wani lokaci suka shige motocinsu suka tafi ba don sunso ba,Kuma duk da haka sai da Sgr ya sanya sojoji guda biyu suka tsaya a wurin,batare da uniform ajikinsu ba,


    *RIJF BABY JUNAID*


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 5:30 na marece,

Slowly motocinsu suka shiga cikin gidan,Bayan sunyi parking ɗinsu Major ya buɗe masu mota,don atare suka zauna shi da Sgr a motar Omar,kowa jiki babu ƙwari haka suka fito daga cikin Motar,kaitsaye suka nufi ƙopar shiga falon,


A lokacin hosana na zaune saman Sofa,duk ta takure kanta,tun da tafarka daga bacci take ta faman yin sintiri acikin gidan tana jiran dawowar Omar don ta faɗa mashi abunda haroon yayi mata,


Jin motsin shigowarsu yasa tayi saurin miƙewa jiki na rawa ta tunkareshi zata rungumeshi,

Da hannu yayi mata alamar karta matso kusa dashi,fuskarshi babu annuri,har cikin ranta bata ji daɗin abunda yayi mata ba,har gaishe dasu tayi amma babu wanda ya kulata,acikinsu,

  Upstairs suka wuce atare,kowa ya nufi part ɗinsa,komawa hosana tayi saman sofa ɗin tana kuka,abun ya ƙona mata rai,Yadda Omar ya dakatar da ita don karta ta6a shi,

  Faɗawa yayi saman gadonshi yayin da idanuwanshi ke fuskantar Ceiling,Fuskar Junaid ya dinga ganin tana yi mashi gizau,ji yake tamkar abunda ya faru mafarkine ba gaskiya ba,saboda wani sashe na zuciyarshi na raya mashi cewa Junaid yana raye bai mutu ba,Yayin da wani sashen na zuciyar tashi ke gasgata mashi mutuwar junaid,runtse idanuwanshi yayi Allah kaɗai yasan irin raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi daurewa kawai yake yi,ya jima a haka idonshi na kallon sama,kafin daga bisani ya miƙe tare da faɗawa toilet bayan ya rage kayan jikinshi,


Kwance yayi tsulundum acikin jacuzzi (kwamin wanka)wanda ke kewaye da glass,da niyyar yin wanka ya shiga toilet ɗin,Amma sai kasala ta baibayeshi ko yatsan shi ya gaza ɗagawa,abubuwa sunyi mashi yawa,tunda yake a rayuwarshi bai ta6a fuskantar mummunar rana irin wannan ba,da ace mutuwa hutu ce agareshi da ba abunda zai hana ya roƙi Allah akan ya ɗauki ranshi ya huta,Yaci alwashin saiya ga bayan waɗanda suka kashe junaid,Alƙawari ne ya ɗaukarwa kanshi,Ko bacci bazai ƙara yi ba,in har bai ɗaukarwa junaid FANSA ba,kamar yadda Sgr yaci Alwashin ɗaukar fansa haka shima Omar ya ɗauka,


Kasa jurewa yayi saboda kukan da hosana ke raira mashi ta la6e a ƙopar dakinshi batasan halin da yake ciki ba,

  "Hosana,"ya ambaci sunanta,muryarshi a kasalance,

  Cikin shessheƙar kuka tace"Na'am,"

  "Zonan,"

Hannu tasa ta tura ƙopar tare da shigewa ciki,Kwance ta same shi saman gadonshi,Ya baje daga shi sai short,kallo guda zakayiwa fuskarshi ka gane cewa yana acikin matsanancin tashin hankali,

  har Saman gadon hosana ta hau ta zauna tana kallonshi,lokaci guda ta dakata da yin kukan nata,Ganin dry tears asaman fuskarshi,nan fa hankalinta ya tashi sosai,

  "Ya omar,hawaye akan fuskarka?meke damunka ya Omar,Ban ta6a ganin hawayenka ba,Sae yau,"

  A hankali ya bude idanuwanshi da sukayi jawur dasu yana kallonta yace"Hosana,ki taimaka mun kaina kamar zai fashe,Ina cikin matsananciyar damuwa,Zuciyata raɗaɗi take yi mun,pray for me hosana kona samu sauƙi acikin zuciyata,

  Jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,hannayenta ta sanya tana kokarin janyo shi hakan yasa ya dan matso daura kanshi tayi saman laps ɗinta,Addu'o'i ta shiga karantowa tana tottafa mashi asaman fuskarshi,shafa sumar kanshi ta shiga yi,tana cewa"Ya Allah ga bawanka nan,kai kaɗai kasan meke damunshi,Ya Allah ka yaye mashi damuwarshi,Ka sanyaya mashi zuciyarshi,Alfarmar Annabi Muhammadu (S.A.W),

  Ba ƙaramin daɗin maganarta yaji ba,sosai ya gyara kwanciyarshi sama sama bacci ya fara ƙoƙarin daukarshi,

Yana jiyo muryarta tana tambayarshi Ko zaici abinci ta kawo mashi,

   Daƙyar ya iya amsa mata da cewa"A'a hosana,bana iya cin komai yanzu,"

  "Shikenan ya Omar ɗina,kayi baccinka kawai,zanci gaba da yi maka addu'a,har ka farka,"

   Shafa sumar kanshi taci gaba da yi,tamkar jinjiri haka ta dinga treating ɗinsa har bacci yayi awon gaba dashi,Yau hosana tayi mashi abunda bai ta6a tsammani ba,Ta bashi kyakkyawar kulawa kamar ba wannan mai ta6in hankalin ba,wani iko na Allah ta so sanar dashi damuwarta,amma tunda ta gane cewa baya a hayyacinshi,Sae kawai ta fasa sanar dashi.


*Tashin Hankali!"


Jin dirar motoci acikin gidan yasa shi yin firgit ya farka,tare da yunƙurawa ya miƙe zaune,Hosana ya gani kwance tana bacci,asaman gadon ya ɗauketa,

  Jiki na rawa ya saukko daga saman gadon ya samu jallabiya ya zura ma jikinshi ya bude ƙopar dakinshi da sauri ya nufi downstairs,Tunkan ya ƙarasa ya jiyo Muryar Abbansu yana ƙwalama Junaid kira,ko sallama baiyi ba,Burinshi kawai yayi tozali da junaid,

  "Hasbunallahu wani'e mal wakil"ya furta hakan tamkar zai fashe da kuka,

  Yana cikin wannan yanayin sai ga Sgr shima ya fito daga part ɗinsa,jikinshi sanye da jallabiya shima,kallon juna suka yi kowa fuskarshi ayamutse take,

   "Daga shigowarshi ko sallama baiyi ba sunan junaid kawai ya ambata,yanzu yaya zamuyi dashi'?omar ne yayi maganar tare da kallon Sgr dake tsaye a gefenshi,

   "Yanzu ya dawo yana buƙatar ya huta,yakamata muyi ƙoƙari wurin ganin mun daidaita natsuwarmu,if not za'a samu matsala ne,"


Shigowa cikin falon suka karasa yi,Abbansu ne sai Mommynsu,tare dasu twins,fawan gaba ɗaya matasan gidan sun dawo,hada kanal yousouf su irfan da sauransu,Banda gwaggon katsina suma sun shirya dawowa tare dasu Ammi,zasu zo daga baya,


Agajiye suke kowa ya samu wuri saman Sofa ya zauna,Abba kuwa jiki na rawa ya wuce upstairs,su Sgr najin takun takalminshi hankalinsu ya ƙara tashi,Yana tafiya yana ƙwalawa junaid kira,

  "Junaid!Junaid!where are you?Ur dad is back,Nayi missing ɗinka sosai...."

   

Bai ƙarasa maganar ba,ganinsu Omar atsaye,cirko cirko,ƙaƙaro murmushi suka yi gaba dayansu suka tunkareshi,Sgr ne ya fara yin hugging ɗinshi,Daddy I really missed you,Ya gajiyar tafiya?ya ƙarasa maganar tare da ɗagowa daga jikinshi,Bai amsa mashi gaisuwar tashi ba,yace"Yaushe ka dawo Abuja?ko kun dawo ne'?

   "A'a daddy,Wani uziri ne ya kawo ni,Amma zan koma kano ɗinne,"wani kallo da yaga Abbansu na binshi dashi yasa ya ɗan sha jinin jikinshi,

  "Abba sannu da dawowa,"Omar ne yayi maganar,wurga idanuwanshi yayi akan fuskar Omar,aɗan ruɗe yace"kunyi rashin lafiya ne?meke faruwa ne?naga fuskokinku duk sun kumbura,fuskar Rafayet tayi jawur da ita,kaima haka...."

  Da sauri Omar yace"Am...Abba..I know u are tired,kana buƙatar hutu,yakamata muje bedroom ɗin ka Inyi maka tausa,"

  Harara Abban ya ɗan watsa mashi tare da cewa"a ƙule nake dakai Omar,ina ta nemanka jiya,ka tashi ka kashe mun waya hmmmm..."yana kai ƙarshen maganar ya soma ƙoƙarin wuce wa ciki,Saboda tsabar ruɗu Sgr baisan sa'adda ya tarboshi da hannunshi,Zuba ma hannun nashi ido Abbansu yayi,fuskarshi ɗauke da mamaki yace"Rafayet,lafiyarka kuwa?cikina fa ka tarbe,"

  Zame hannunshi yayi tare da ɗan sosa ƙeyarshi yace"Am sorry Daddy,pls u need a rest,mu sauka down ka huta mana,ka kwaso gajiya,inaso na baka abinci kaci ka huta,Omar zaiyi maka massage ka ɗan ji daɗin jikinka,

  Cike da mamaki Abbansu ke kallonshi,"Rafayet!yau kaine da kanka kake zancen zaka bani abinci a baki na naci?Omar kuma zai yi mun tausa,sae kace wani ƙaramin yaro,"gyaɗa kanshi yayi tare da cewa"Naji toh,Amma saina fara zuwa ɗakin Junaid,idan nadawo sai mu je ɗakin nawa,"yana kai ƙarshen maganar ya wuce tare da nufar ɗakin Junaid yana ƙwala masa kira,

  Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,A hankali Abba ya tura ƙopar ɗakin junaid ya shiga daga ciki,Wayaam yaga babu kowa aciki,Bai kawo komai aransa ba,saboda ƙarar saukar ruwa dayaji a toilet,hakan yasa shi tunanin ko ya shiga wanka ne,ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa ya fito daga ɗakin,da niyar idan ya huta zai dawo wurinshi,don yau atare yake son su kwana dashi,


Koda suka yi arba da Abbansu yana nufosu sai kowannansu ya shiga ƴan kame kame,fargabarsu kada ace zai tambayesu ina Junaid ya ke,.  

   Tunkan ya ƙaraso wurinsu suka ji yace"Ashe ya shiga wanka ne,idan ya fito daga wankan pls ku sanar dashi cewa nadawo kuma inason ganinshi,a bedroom ɗina,"

  Atare suka haɗa baki wurin cewa"Toh Abba"


Saukowa down sukayi atare da abban yana gaba suna a bayanshi,Sae faman sauke ajiyar zuciya suke yi,


Lokacin da suka sauko down,Su kanal Yousouf na ganinsu kowa ya miƙe fuskar nan ɗauke da farin ciki,Yayin da su kuma kowannansu ya dabarbarce,

Daƙyar suke gaisawa da ƴan uwan nasu,kowa ya lura da yanayinsu shiru kawai su kayi,Su fawan sai tambayar Junaid suke yi,Yana ina?basu ganshi ba,amsa daya suke basu ta yana a cikin toilet yana wanka,Duk wanda yaje ɗakin Junaid yaji sautin saukar ruwa daga cikin toilet,sai yayi tunanin cewa wanka yake yi,Ashe fanfo ne Aka bari a kunne ba'a kashe ba,

   Daƙyar suka samu kowa ya haƙura da ganin junaid,Omar yace su wuce ɗakunansu kowa yaje ya huta,an kwaso gajiya,

  "Nifa ban yarda dasu babban yaya ba,Shi da ya Omar akwai wani abu da suke 6oye mana Allah,"Acewar Jahan,

A yayin da suke shiga bedroom ɗinsu,

  Ayaan yace"nikaina na lura da hakan,musamman faces ɗinsu,kamar sunsha kuka Allah,Gaskiya hankalina bazai kwanta ba,sai naga junaid,ni ban yarda wanka yake yi acikin toilet ba,"

  Jahan yace"mu bari mu huta,Zuwa dare sai muje ɗakin nashi,nasan lokacin idan ma wankan ne ya gama,"

  Ƙarasa shiga cikin ɗakin sukayi,kowa ya shiga rage kayan jikinshi,Jahan ne ya fara shiga waka,Ayaan ya zauna gefen gadon yana jiranshi ya fito shima ya shiga wankan,

   A can falo kuwa,Mommynsu ta tsare Sgr da Omar,Tasa su gaba tayi tana binsu da kallo one by one,dama bakowa Sgr yafi ji ba fa ce Mommynsu,tana da wuyar sha'ani,

  "Mommy,"Sgr ne ya ambaci sunanta,

bata amsa mashi sunan nata daya kira ba,sai cewa tayi"you didn't answer my question,It seems like you are hidding something for us!Rafayet where is junaid!kada kuyi mun ƙarya nasan ba halinku ba ne,just ku faɗamun Gaskiyar abunda ya faru,"

  Murya na rawa Omar yace“Am..mommy,Junaid fa yana a toilet yana wanka zai fito ne...m"daƙyar ya ƙarasa maganar ganin irin kallon da take yi mashi,kallon tuhuma,kallon ban yarda dakai ba 

"Wai taya za ku ce mun junaid yana wanka?Nifa ba ƙaramar yarinya bace,balle kuce zakuyi mun wayau,tun daga kan fuskarku na gane cewa akwai wani abu daya faru dashi...."

  Saussauta muryarta tayi,sannan taci gaba da magana"pls idan wani abu ne ya faru da Romeo ɗina ku sanar dani,i will accept it,"yadda tayi maganar yasa su kaji jikinsu ya ƙara mutuwa,

  "Am listening to u guys,ku faɗamun meya faru dashi ya mutu ko"?

  Gabansu ne ya faɗi rass!da sauri Sgr ya ruƙo hannunta muryarshi na kerma yace"Mommy dan Allah kiyi haƙuri,ki rufa mana asiri,I will explain to u mu shiga daga cikin bedroom ɗin..."

  "Rafayet,meyasa zaka sanar da ita"?Omar ne yayi maganar fuskarshi a yamutse,

  "To ya kakeso nayi Omar,Mommy bazata ta6a yarda ba,kwara kawai mu faɗa mata gaskiyar abunda ya faru,Ka wuce wurin Daddy,ni zanji da Mommy,'

  Ya ƙarasa maganar tare da jan hannunta,Suka wuce upstairs bedroom ɗinshi,

  Ajiyar zuciya Omar ya sauke,Ya jima atsaye yana tunanin Yadda zasu ƙare da Abbansu,tsoranshi kada farat ɗaya zuciyarshi ta buga idan yaji cewa Anyi garkuwa da junaid kamar yadda suka tsara,

  "Omar,lafiya kuwa,"firgit ya ɗanyi tare da kai idanuwanshi wurinta,Azmee ta nufo shi,Ganinshi a tsaye kamar akwai damuwa atattare dashi,

  Dakyar ya ƙaƙaro murmushin yaƙe yace"bakomai,"

    "Omar,dama inaso na tambayeka ne,Wai ina junaid ne?tun jiya da suka fita shi da jahad shiru har yau basu dawo ba,nashiga damuwa sosai akan rashin ganinsu,har cewa yayi idan suka je shan ice cream zaiyi min tsaraba," ta ƙarasa maganar tana kallonshi,

  "Aunty Azmee,bazan iya 6oye maki ba,Junaid da jahad anyi kidnapping ɗinsu...."jin wannan maganar yasa Azmee ta dafe ƙirjinta da ƙarfi,idanuwanta suka firfito waje,hankalinta yayi mugun tashi,

  "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"kusan sau biyar tana maimata kalmar,

   siraran hawaye ne suka soma saukowa saman cheeks ɗinta,ji tayi tamkar bazata iya ɗaga ƙafafunta ba,saboda nauyin da sukayi mata,

  "Junaid da jahad suna buƙatar addu'armu Azmee,"acewar Omar,

  Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Nashiga uku!Yanzu junaid da jahad aka ɗauke mana...."

Katse ta Omar yayi'pls Aunty azmee,ki daina ɗaga sautin muryarki,na faɗa maki ne don ki taimaka mana,Wurin kwantar da hankalin sauran mutanen gidan nan,Mun shiga damuwa sosai,saboda gudun halin da zasu shiga,musamman mahaifinmu...."

  Cikin shessheƙar kuka tace"Ya Allah ga bayinka nan!ka tsare manasu a duk inda suke,Ya Allah ka ku6utar dasu daga hannun azzaluman da suka yi garkuwa dasu,wannan wata irin masifa ce......"kuka ne yaci ƙarfinta,da gudun gaske ta juya tare da tunkarar kitchen,zama tayi ta dingi kuka kamar ranta zai fita,gani take yi kamar zasu rasa su ne,Ta ƙwallafa rai akan junaid,tana jinshi tamkar ɗan cikinta saboda ta shayar dashi,baiwar Allah,

  Jiki asanyaye Omar ya wuce bedroom ɗin Abbansu,tsaye ya same shi har ya zura kayan bacci ajikinshi,ta cikin mirror ya hango Omar,juyowa yayi fuskar shi ɗauke da murmushi yace"halan junaid ya fito daga wankan ne"?yayi tunanin abunda ya kawo shi ne,

  "Abba,me kake buƙata na kawo maka"ya tambaye shi ne don ya kawar mashi da tunanin Junaid aranshi 

Murmushi Abba yayi tare da cewa"Sannu Azmee,Yau kaine ka kar6i aikinta kenan"?

  Duk da halin daya ke ciki na fargaba sai da ya ɗan murmusa,jin abunda abban yace,

   "No,kawai inaso na baka kyakkyawar kulawa ne saboda nayi kewarka,ka fara faɗamun abunda kakeso sai in kawo maka,"

  Murmushi Abba ya ɗan yi kafin yace"shikenan,junaid nake son gani ka kawo mun shi,idan ma ya fara bacci ka ɗauko mun shi,ina jiranka,"ya ƙarasa maganar tare da samun wuri gefen gadonshi,yana kallon Omar da yayi mashi zuru da ido,

  "Omar,lafiya ka zubamin ido kana kallona'?

  "Babu komai Abba,bari na ɗauko maka junaid ɗin,"yayi maganar tare da juyawa yabar ɗakin,Zaman jiran dawowarshi Abba yayi,sai faman sakin murmushi yake yi,harya ƙosa Omar ya ɗauko mashi Baby Junaid ɗinshi,


A 6angaren Omar yana fita daga bedroom ɗin abban nasu,kaitsaye kitchen ya wuce,Anan ya samu azmee zaune saman kujera tana ta matsar kwalla,

"haba Aunty azmee,meyasa zakiyi mun haka?Addu'a yakamata kiyi masu akan Allah ya bayyanar mana dasu,kukan da kike yi bazai amfane su ba,"

  Zame hannuwanta tayi daga saman fuskarta,idanuwanta sunyi jawur dasu luhu luhu,

  "Omar,ba zaka gane bane,dole inyi kukan rashin su junaid,ko ka manta shakuwar dake tsakanina dashi ne'?

  Shiru omar yayi yana kallonta,Allah yaso bai sanar da ita gaskiyar abunda ya faru ba,da baisan abunda zai biyo baya ba daga gareta itama,

Lallashinta ya shiga yi har ya samu ta saukko,Tsayawa yayi ta shirya mashi dinner asaman tray,ya kar6a ya wuce ɗakin Abbansu,ita kuma ta shiga ɗaukar kayan abincin da ta shirya masu tana kaiwa dining,



Lokacin da Omar ya koma bedroom ɗin Abbansu,yana shiga ciki Abbansu yaga tray a hannunshi sai ya ɗaure fuskarshi tare da cewa"Nifa ba yunwa nace maka inaji ba,Junaid nace ka ɗauko mun,"

  Saman table omar ya ajiye tray din tare da samun wuri gefenshi ya zauna,ruƙo hannayenshi yayi tare da sassauta muryarshi

   "Abba pls,kaci abincin ka ƙoshi,idan ka kammala zamuyi magana dakai,"

  Shiru yayi yana kallonshi kamar mai nazarin wani abu yace"Shikenan zuba mun abincin naci,Allah yasa naji alkhairi,"

Serving ɗinshi Omar ya soma yi,sosai yaci abincin bayan ya gama da abincin,Omar ya tsiyaya mashi Lemu me sanyi a cup,yasha,

  "Yanzu ina sauraronka,wata maganace zamuyi,"

  "Abba ko zaka ɗan kwanta ne?ina ga kamar hakan zaifi,muna magana inayi maka tausa,"

  Abun ya daurewa Abbansu kai,gyara kwanciyarshi yayi saman gadon sannan yace"ina sauraronka toh,"

  Hawa saman gadon Omar yayi,A hankali ya fara yi mashi massage ɗin kafarsa,

   A tsanake ya soma magana"Abba dama game da junaid ne,nasan ka yarda dani sosai,kuma zaka fahimce ni ne,

  Tunda ya ambaci sunan Junaid,Abba ya miƙe daga zaune da sauri yana kallonshi

  daurewa Omar yayi tare da cigaba da cewa"mun shiga matsananciyar damuwa Abba,idan ka lura da fuskokinmu duk sun sauya saboda tsabar tashin hankalin da muke ciki...."dakatar dashi Abba yayi ta hanyar ɗaga mashi hannu,

   "Ka fito fili ka faɗamun ainihin abunda ke faruwa Omar,sai 6oye 6oye kake yi mun,dama ni tuni sai da raina ya bani cewa wani abu ya faru da junaid,dan Allah ka sanar dani!ina ɗana yake"?hankalinshi atashe yayi maganar,

  Cike da fargaba Omar ya ɗaura da cewa"Abba,junaid yana cikin ƙoshin lafiya,sai dai baya atare damu,Jiya bayan fitarsu shan ice cream tare da jahad,kidnappers su kayi garkuwa dasu,bana so ka tashi hankalinka Abba,Ni nayi maka alƙwarin zan dawo maka da ƴa'ƴanka,cikin ƙoshin lafiya batare da sun samu koda ƙwarzane ajikinsu ba....."duk wannan surutan da Omar keyi baisan cewa Abbansu ya jima da sumewa ba,tunda ya ambaci sunan kidnappers sunyi garkuwa dasu,Bai ƙara sanin inda kanshi yake ba,

  "Abba!"ya ambaci sunanshi,yayin da yake kallon fuskarshi,Hannu yasa tare da dafe goshinshi,Dama saida ranshi ya bashi cewar hakan zata iya faruwa,

  Idanuwanshi ne suka cuccuko da kwalla,kamar ya fasa ihu haka yake ji,ta ko'ina babu sauƙi,dirshan ya zauna saman gadon fuskarshi a yamutse,ya zuba ma Abban nasu ido yana kallonshi,


Adai dai Lokacin Sgr ya shigo bedroom ɗin tare da Mommynsu,tasha kuka duk da irin juriyarta,daƙyar ya samu ya shawo kanta,shima ɗin don yayi mata alƙwarin cewa zai dawo mata da ɗanta har gida ba tare da komai ya same shi ba,jin motsin shigowarsu yasa Omar waigawa yana kallonsu,har suka ƙarasa shigowa wurin gadon,Gefen gadon Sgr ya zauna,Mommy ta tsaya daga tsaye tana kallon Abba dake a zaune ido rufe,

  "Omar,ka faɗa mashi ne"!?ɗaga mashi kai Omar yayi alamar eh,Ya kuma cewa"ko ya samu bacci ne"?

  Girgiza kai yayi tare da cewa"a'a,taya zan faɗa mashi wannan tashin hankalin yayi bacci?Kaima ka sani,tun kafin ma na ƙarasa sanar dashi ya sume a zaune,Na rasa abun yi ne shiyasa nayi zugum ina kallonshi,

  Miƙewa Sgr yayi da sauri ya fuce daga ɗakin don ya ɗauko masu ruwan da za'a yayyafa mashi,

  "Mommy,dan Allah ku ƙara haƙuri akan 6atansu junaid,in sha Allah we will try our best don muga mun dawo dasu cikin gidan nan,"

Jinjina kai tayi "Na yarda daku Omar,Nidai burina ku dawo mun dasu cikin gidan nan,Na tambayi Son game da kidnappers ɗin ya sanar dani cewa,Sau ɗaya suka kira waya,Kunyi magana dasu kuma har sun baku Junaid kunyi magana dashi,Naso ace sun bar wata kafa da zatasa ayi tracking layinsu,Amma kashe yace mun Sun kira da hidden number ne,abunda nakeso naji shi ne,basu buƙaci adadin kuɗin da suke so ba?ni koma nawa ne zan bada a kar6ominsu,"

  Jikin Omar ba ƙaramin sanyi yayi ba,gwanin ban tausayi haka yake kallonta,Aransa yana ayyana irin tashin hankalin da zata shiga idan taji cewa,Junaid ya mutu ta hanyar take shi da mota,

  "Omar kayi shiru baka ce komai ba,"ta jifa mashi tambayar,tana kallonshi,

  Girgiza mata kai yayi"A'a Mommy,basu buƙaci komai ba yanzu,Sun sanar damu cewa,Zasu tuntu6emu idan buƙatar hakan ya taso,kuma sunyi warning ɗinmu,kada mu kuskura muyi gigin yin investigation akansu,if not zasu illatasu ne,shiyasa bamu yi wani yunƙuri ba ayanzu,Amma yanzu mu kanmu kiransu muke jira,muji nawa suke buƙata sai a tura masu,"ba don yaso ba haka ya dinga shirga mata ƙarya,kamar yayi kuka wai yau shine ke yin ƙarya,duk da yayi ba'ason ranshi ba,Dole ce tasa su yin hakan,

  Turo ƙopar Sgr yayi hannunshi ruƙe da bottle water,ƙarasawa yayi tare da buɗe murfi ya tarfa ruwan asaman tafin hannunshi,Sannan ya shafa fuskar Abban nasu,Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da ware idanuwanshi akansu yana kallonsu ɗaya bayan ɗaya,a hankali ya furta"Ina junaid"?

  Omar na ƙoƙarin buɗe baki yayi mashi jawabi,Alexandra ta katse mashi hanzarinshi da cewa"Ku barni dashi,dare yayi sosai yakamata kuje ku kwanta ku huta,kafin gobe,"ta fadi hakan ne don tasan cewa ba karamin tashin hankali suma suke ciki ba da ganin yanayin su,

    Saukowa daga saman gadon Omar yayi tare da ruƙo hannun Sgr yace"Mu tafi,"sallama su kayi mata tare da fucewa daga ɗakin,

Hawa saman gadon tayi suna fuskantar juna,tallabo fuskarshi tayi da hannayenta biyu,suka zuba ma juna ido,na wani lokaci kafin tace"Hubby,ka natsu ka saurare ni,Nasan zaka fahimce ni,Kuma kai musulmi ne!kayi imani da ƙaddara mai kyau ko mara kyau haka ne"?kamar wani ƙaramin yaro haka ta mayar dashi,

Nodding kai yayi mata alamar eh,

  Murmushi ta ɗan sakar mashi tare da cewa"haka nake son ji my hubby,"dakatawa ta ɗan yi da yin jawabin tana kallonshi,saboda ta kasa furta mashi abunda take so ta faɗa,farin ruwa ta gani ya kwanta acikin idanuwanshi,la66ansa na kerma yace"Pls tell me the truth,Meya faru ne?kowa ya sauya mun,Dama ni sai da raina ya bani cewa wani abu ya faru da baby junaid ɗina,"jikinshi har ya fara kakarwa kamar wanda sanyi ya kama,

   Hawaye ne suka ciko tab a idonta,

"Am sorry to say,Junaid yana cikin ƙoshin lafiya,Amma baya atare damu,Rafayet ya sanar dani cewa,since yesterday night around 8 suna kan hanyar dawowarsu gida,kidnappers suka ɗaukesu gaba ɗayansu,"

  Jin wannan maganar yasa hankalinshi yayi mugun tashi,wata irin zabura yayi yana ƙoƙarin saukowa daga saman gadon,Da sauri ta ruƙo rigar jikinshi"dan Allah ka natsu ka saurare ne...."

   Girgiza kai ya shiga yi yana faɗin"banga ta zama ba,Anyi garkuwa dasu junaid ɗina,Wlh bazata sa6u ba,duk inda junaid da jahad suke adawo mun dasu cikin daren nan in har anason zaman lafiya,wannan wani irin shashanci ne?har junaid ya kwana a hannun kidnappers tun jiya arasa wanda zai ƙwatosu daga hannunsu,Banga amfanin sojojin dana tara acikin gidan nan ba,Nikaina bani da amfani kenan!Kowa ma bai da amfani mun zama tamkar kwankwan ashana,tunda har bazamu iya ceto rayuwarsu ba,"idonshi ya rufe sai faman zazzaga masifa yakeyi,Ƙarasa saukowa yayi daga saman gadon,buguzun buguzun ya kama hanyar fita daga bedroom ɗin nashi,da sauri Alex tabi bayanshi,tana ambaton sunanshi

  Ko sauraronta baiyi ba,da alama ya zauce ne,

  "Yau ƙafata kafarsu junaid zamu dawo cikin gidan nan duk inda suke saina dawo dasu,abun ban haushi wai anyi garkuwa dasu junaid?sai kace ƴa'ƴan wani me siyar da kifi abakin titi,Ƴa'ƴana ne fa!Ni chief of army staff na Nigeria gaba ɗaya,banga amfanin matsayin da nake dashi ba Allah,tunda har za'a iya yin kidnapping ɗin ya'yana,wlh bazan yafewa kaina ba,in har bandawo da junaid cikin gidan nan ba,"ranshi amatukar 6ace yake yin maganar,jijiyoyin wuyanshi duk sun firfito waje,

  "Pls hubby Calm down ur mind,Ina zaka je ne?acikin daren nan!indai akansu junaid ne,na tabbata zasu dawo ne"

  Guntun tsoki yaja tare da cewa"baki da hankaline,da alama bakisan zafin haihuwa ba,Shiyasa kike faɗin hakan,"

  "Ni fa na haifeshi,taya zaka ce mun bansan zafin haihuwa ba?Ya kake so nayi ne?ka ƙi tsayawa nayi maka bayani,

  Su Marshal na zaune asaman sofa,kowa da abunda yake saƙawa aranshi,kwatsam suka jiyo muryoyinsu,nan fa suka miƙe suna kallonsu,

   Ganin Abbansu ya nufi hanyar fita daga falon ko takalma babu a ƙafarshi,da sauri suka sha gabanshi,

  Rufe ido yayi atsiwace yace"Ku matsa ku bani wuri,wlh Omar ka bani mamaki,ko ince kun bani mamaki,How many hours su junaid na a hannun kidnappers amma baku iya ƙwatomun shi ba,babu wani mataki da kuka ɗauka,to ni zanje in dawo da abuna,"yana magana huci na fitowa daga bakinshi,

   Ruƙo shi Omar yayi tare da fashewa da matsanancin kuka,Girgiza mashi kai ya soma yi batare da ya furta mashi komai,jikin Abbansu ba ƙaramin sanyi yayi ba,Cos ya manta when last yaga hawaye a fuskar Omar,tabbas abun na ci masu rai sosai,Mayar da idanuwanshi yayi kan Sgr,Hawaye ya gani kwance Luf acikin idanuwanshi,wanda tunda yake arayuwarshi bai ta6a ganin ruwan hawaye a idon Sgr ba,tun ma da aka haifeshi har suna expecting ko baida cikakkiyar lafiya ne,

   "Omar!kuka kake yi mun"?yayi maganar yayin da hawaye suka soma wanko fuskarshi,Kallon Sgr yayi tare da cewa"Kaima kukan zaka yi mun"?

  Duƙar da kanshi yayi ƙasa,gaba ɗaya jikin kowannansu yayi sanyi,

  "Abba,ka tausaya mana muna cikin matsananciyar damuwa na rashin Su junaid atare damu,Mun rasa yaya zamuyi,munyi tunanin zaka ƙarfafa mana guiwa wurin ganin mun ceto rayuwarsu,Amma sam kaƙi tsayawa kaji abunda muke son mu sanar dakai balle har musa ran zaka fahimce mu...."ya ƙarasa maganar tare da sanya tafin hannunshi yana share hawayen dake sauka a fuskarshi,

   "Abba,saboda rashin su junaid,ko bacci ba muyi ba,Yadda muka ga dare haka muka ga rana,Ga rafayet nan saboda shi,Ya baro kano ya dawo Abuja tunda sanyin safiya,dukanmu nan babu wanda ya iya kora koda ruwa ne ta maƙoshinsa,duk don saboda 6atansu junaid...."dakatawa ya ɗan yi da yin maganar yana kallon Abban nasu,da alama ya fara saukowa 

  "Kaine ka haifemu,kafi kowa sanin su wanene mu!me zamu iya da kuma wanda baza mu iya ba!Nasan ka yarda damu sosai,Idan har akwai wanda zai bada shaida akanmu kaine Abba!meyasa bazaka yi mana uziri ba?idan har bamu bi komai a hankali ba wurin ganin mun ceto rayuwarsu,Toh zamu rasa su ne gaba ɗayansu!"

  Juyawa Abba yayi ya soma tafiya cikin falon,Saman sofa ya zauna,ganin haka yasa suma suka dawo saman Sofa ɗin suka zauna suna fuskantarshi,Itama Mommy ta samu wuri daga gefen shi ta zauna,


Duk wannan abun dake faruwa akan idon ƙannensu,don tun lokacin da Abbansu ya fito yana sambatun nan,Kowannansu ya fito daga bedroom ɗinshi,Jikin kowannansu yayi mugun sanyi,jin cewa Anyi kidnapping ɗinsu Junaid,Abun ya ta6a masu zuciya sosai,


"Har tsawon wani lokaci,kuke so na baku ku dawo mun dasu junaid"?Acewar Abba,

  Shiru sukayi gabansu na faɗuwa,Omar ne yayi ƙoƙarin cewa"1 week"a hanzarce Sgr yace"Omar that's impossible,ka manta yarda mu kayi dasu ne?Sunyi mana alƙawarin cewa in dae aka yi masu yadda suke so zasu sakosu,Amma ba a tare ba,saboda suna ganin za'a gano su adau mataki, akwai yiyuwar su fara sauko junaid shi kaɗai acikin satin nan ko kuma su fara sakin Jahad,Ni ina ga kamar one month yayi,Kafin lokacin in sha Allah mun dawo dasu duka acikin gidan,

  Girgiza kai Abbansu ya ɗan yi tare da cewa"Har one month!su junaid basa atare damu?idan suka cutar dasu fa?

  "Abba sunyi mana alƙawarin cewa in har zamu biyasu yadda suke so,bazasu cutar mana dasu ba,"

  "Nawa suka buƙata"yayi tambayar yana kallon faces ɗinsu,

   "har yanzu dai su muke jira,sunce zasu kira su sanar damu,sannan sunce mu kwantar da hankalinmu,Bazasu ta6a cutar dasu ba,Zasu basu kyakkyawar kulawa,kuɗi kawai suke buƙata ba wani abu ba,"Omar ne ya kora mashi jawabin

  Cike da takaici Abba yace"just because of money,suka ɗauke mun ƴa'ƴana?Ae da sun sani sun nemi tallafi a wurinmu konawa ne zamu basu basai sun ɗauke mun su ba,"

   Miƙewa yayi sam babu kuzari ajikinshi,tafiya ya soma yi dakyar yake iya ɗaga ƙafarshi,har sai da yabar wurin Sofas ɗin,Sannan ya dakata da yin tafiyar,ya waiwayo tare da kallonsu,gaba ɗaya idanuwansu na akanshi,

  Magana ya soma yi masu babu wasa a fuskarshi"Omar!"

  "Na'am Abba"ya amsa mashi,

"Rafayet"shima ya amsa mashi"Na'am Daddy,"

   "Na yarda daku sosai,abu biyu nake tsammani daga wurinku,Na fako ku dawo mun dasu junaid,Cikin ƙoshin lafiya,Na biyu kuma ku kawo mun waɗannan gur6atattun mutanen da sukayi garkuwa dasu,Wallahi thumma tallahi idan har ku kasa yi mun waɗannan abubuwan dana lissafa maku,inaso ku sani Za ku rasa ni ne,NA HAR ABADA,daga yau zuwa 30 ga watan da zamu shiga,a kowace rana zan fara sa ran dawowarsu acikin gidan nan!kuma daga ranar ku fara ƙirgen ranakun da su kayi mun saura acikin duniyar nan


  *Tashin hankali!*

Mikewa Mommynsu tayi tare da kallonsu gwanin ban tausayi tace"Na yarda daku sosai,ku taimaki rayuwar mahaifinku,Zamu taya ku da Addu'a Har Allah yasa kuyi nasara akan kidnappers ɗin nan,"tana kai ƙarshen maganarta,tabi bayan abbansu,

  "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"wannan shi ne abunda ke fitowa daga bakunansu,basu ta6a ganin tashin hankali irin na wannan ranar ba,A tsaye kowannansu ya kwana,har sun fara regretting ɗin ƙaryar da suka shirya ma Abbansu,


Acikin waɗannan kwanakin,Komai ya hargitse masu,safe da marece dare da rana,kullum cikin Zullumi suke,Suna cikin tashin hankali,Duk sunbi sun firgice,kallo guda zaka yi masu ga gane cewar basa a hayyacinsu,Don gaba ɗayansu daga Omar ɗin har Sgr babu wanda baiyi rama ba ajikinsu,gidan ya zama tamkar maƙabarta,Babu wani sauran farin ciki daya rage masu,Saboda rashin junaid babu mai samun isasshen bacci acikinsu,Abinci ma har Azmee ta fara gajiya da girka masu saboda Asarar shi da akeyi,Yadda ta ajiye haka take zuwa ta same shi,duk rana ta Allah sai Abbansu ya tunasar dasu Adadin kwanakin daya rage masu na ƙwato su junaid a wurin kidnappers,yayin da suke cikin wannan tashin hankalin,Abusufyan na can suma ba kwanciyar hankali wanda hakan ya ɗauke hankalinshi gaba daya batare da ya fahimci halin da gidan suke ciki ba,Ciwon abu ya tashi gadan gadan,Kullum da daddare sai ta dinga kuka tana buge buge tana faɗin sunan sayyadi,hakan ba ƙaramin ruɗani ya sanyasu ba,har Sehrish ta fara zargin cewa,kodai yafara yi mata gizau ne?Anya ba wani abu ke faruwa ba?duk yadda taso Oummansu ta sanar da ita abunda take gani,Hakan ya faskara saboda bata da hankalin da zata iya fayyace mata komai,a ƙarshe dole sehrish ta koma ɗakinta da kwana,duk in haukan nata ya motsa da zarar ta fara raira mata karatun Alƙur'ani sai ta samu natsuwa,a haka suke samu tayi bacci,


A 6angaren Su Hayaam kuwa,ba ƙaramin daɗi suka ji ba,lokacin da Abra ta dawo abuja,Batare da tasha wahala ba,bayan An sallami Hayaam daga Asibiti gidan Amani suka koma,Zasu zauna na ɗan wani lokaci kafin su wuce Maiduguri,duk wannan budurin da sukeyi basu son abunda ke faruwa acan gidansu na maiduguri ba,Sun manta da mahaifiyarsu da suka baro kwance ba lafiya rai hannun Allah,


A 6angaren Aunty babba kuwa ba ƙaramin jiki taji ba,tun bayan da mai motar nan ya hankaɗe ta a Enugu,daƙyar aka samu wani bawan Allah ya ɗauketa a motarshi suka kaita asibiti,Taci baƙar wuya kamar bazata rayu ba,tsawon sati tana kwance a gadon asibiti batasan inda kanta yake ba,Komai ya ƙare mata ƙarƙaf,mutumin daya kawota asibitin tun da ya biya kuɗin da za'a yi mata aiki a ƙafarta da ta samu matsala,bai ƙara tako kafarshi yazo ba,Ga ciwo yaƙi ci yaƙi cinyewa,ta ɗuri ruwa,tayi suntum da ita,daga baya ta ru6e sai uban wari dake fitowa daga jikin ƙafar,Likitoci sunyi iya kar bakin ƙoƙarinsu wurin ganin sunyi mata magani,amma abun ya ci tura,da suka gaji gashi babu wani danginta a kusa,kuma babu kuɗin da zasu cigaba da kula da ita,A ƙarshe Suka sallame ta daga asibitin,Tashin hankali!ko ya  rayuwar Laila zata kasance"?

 


Yau Two Weeks kenan da mutuwar Junaid,Wanda ya kasance Wata biyu cuf da sati ɗaya da yin auren Sehrish Abusufyan da Rafayet salahuddeen,duk da muna sa ran kwanakin auren nasu zai ƙara tsayi saboda Sgr ya ɗaga tafiyarshi ta komawa U.s,Zuwa Next One Month,dalilin ɗaga tafiyar tashi saboda Investigation ɗin da sukeyi na ƙoƙarin gano waɗanda suka kashe Junaid,Ga kuma Abbansu daya zuba masu ido yana jiran su dawo mashi da ƴa'ƴanshi,bawan Allah ko bacci bai samu,duk ya rame ya fige,bai samun bacci da daddare saboda sallar daren da yake yi, haka zai zauna saman darduma yayi ta yi masu addu'a,Allah ya dawo mashi da ƴa'ƴanshi,ita kanta Mommynsu junaid tana cikin mawuyacin hali,cos ta fara zargin cewa ba Kidnapping ɗinsu akayi ba,there's something behind da suka 6oye masu,har sun fara fidda rai da dawowarsu,A ranar Litinin sai ga JAHAD ta dawo gidan da ƙafafunta,Murna a wurinsu kamar su haɗiyeta,duk da sun shiga damuwa ganin yadda ta rame ta fige,duk ta fita hayyacinta,ƙashin wuyanta duk ya firfito kamar zai fasa fatar wuyanta,Taji jiki sosai,Idanuwanta duk sun kumbura,duk yadda suka so jahad ta buɗe baki ta faɗa masu ina junaid yake,taƙi magana bakinta a rufe yake,sai dai kawai ta dinga binsu da ido,bakomai ya hanata yin magana ba,fa ce kukan dake cinta,muddin ta buɗe bakinta to zata fashe masu da kuka ne,kuma ta ɗaukarwa Su ya Omar alƙawarin bazata tona masu asiri ba nace wa junaid ya mutu,har sai lokacin da suka shirya sanar dasu,tunda ta dawo gidan nan,Ta zama salihar ƙarfi da yaji,magana saita zama dole sannan take yinta,ko ɗakinsu batasan fitowa daga ciki,tun hosana na lalla6ata don ta faɗa mata abunda ke damunta,saboda kullum sai ta farka ta sameta tsakar dare tana sallah hawaye na gangarowa akan fuskarta,Har tagaji da tambayarta ta ƙyaleta,


Kullum ne in zata kwanta da daddare sai ta ɗaukko wannan zanen fuskar junaid da tayi a cikin drawing book ɗinta,ta tasa shi gaba tayi ta kallo,Wani lokacin ta fashe da kuka wani lokacin kuma tayi murmushi,bakomai yafi tsaya mata araiba,kamar rana ta farko da ta fara haɗuwa dashi face to face,Yayi tsammanin Sehrish ce,ya ruƙo hannunta ya turata cikin motarshi,ya tasa ta gaba da wannan kyakkyawan murmushin nashi,jahad tayi kuka tamkar ranta zai fita,har ya bi jikinta,in har bata zubda kwallaba ita kanta bata jin daɗin jikinta,wani sa'in idan raɗaɗin yayi mata yawa ƙur'ani take ɗauka ta zauna tayi ta karantawa har ta samu sauƙi acikin zuciyarta,Sau dayawa Omar yakan kirata a garden su zauna yayi ta lallashinta,yana yi mata nasiha,hakan yasa ta fara samun sauƙin raɗaɗin da zuciyarta keyi mata,har ta fara sakewa da kowa acikin gidan,hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba,Yanzu saura dawowar Junaid suke jira shima Masu garkuwar su sako shi,😥rashin sani yafi dare duhu


*Boss Bature*


Kano State,


Wuraren ƙarfe 8 na dare,Sehrish ta fito daga cikin toilet,chest ɗinta ɗaure da towel,ta canza sosai,duk da babu kwanciyar hankali atare da ita,Ciwon Oummansu ba ƙaramin ɗaga mata hankali yake yi ba,harta fara murnar zasu koma gida,sae kuma abu ya dawo gadan gadan haukan take yi,wardrobe ta nufa tare da buɗewa,ta dauko kayan baccinta riga da wando ta zurasu ajikinta,bayan ta kammala sanya kayan,gaban mirror ta koma ta zauna tana kallon fuskarta acikin madubin,ta ƙara kyau da haske,mayukan da take amfani dasu ba ƙaramin gyara suke yi ma jikinta ba,tunani ta shiga yi yau saura satittika suka rage aurenta ya mutu da Sgr,ta ɗan damu da rashinsa a kusa da ita,kusan kullum ne saita tura mashi text message a wayarshi,Sometimes yana maido mata da reply,harma ya tambayi ya lafiyar Oummansu,hakan ba ƙaramin daɗi yake yi mata ba,

  Kiran wayane ya shigo,nan take wayarta ta soma ruri,jiki na rawa ta miƙe daga saman kujerar ta nufi inda ta ajiye wayar asaman pillow,hannu tasa ta ɗauki wayar tare da duba sunan mai kiran nata,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta ganin sunan Mommy Azeema ya bayyana akan screen ɗin wayar,Cike da zumuɗi ta ɗaga kiran,

   "Assalamu alaikum mommy"

On the other hand mommy Azeema tace"wa'alaikumus salam my Daughter hope kina lafiya,"

  Shiru Sehrish tayi batare da ta bata amsa ba,ƙasa kasa ta soma shessheƙar kuka,

    "Daughter,kuka kikeyi koh"?nan ma shiru bata amsa mata ba,

   "Kinyi missing ɗin mommynki ko?,

  Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Eh mommy,kin manta dani,ina cikin damuwa sosai,ta ko'ina ba sauƙi,dama kece kike kwantar mun da hankalina,gashi yanzu kona kira baki ɗagawa,"

  "Am sorry daughter,Nasan ban kyauta maki ba,Amma yanzu ki kwantar da hankalinki,In sha Allah this week zamu zo nan Abuja,Munyi waya da Abusufyan ya sanar dani cewa,Zaku dawo tare da Oummanku ko!

  sehrish tace"Eh,"

  "Naji daɗi sosai,Ban kira na tayaki murnar ganin Oummanku ba,Wlh na yi farin ciki sosai,har ina cewa gwaurancin Abusufyan ya ƙare tunda sanyin idaniyarshi ta dawo,"

  Murmushi sehrish ta saki,hajiya azeema taci gaba da cewa"Baki bani labarin rayuwarki da Sgr ba?ya ake ciki?ko har yanzu babu wani sauyi"?

   Komawa sehrish tayi gefen gadon ta zauna,A tsanake ta labarta mata irin zaman da sukayi dashi,"

  Hajiya azeema tace"Good,Koba komai ta wani 6angaren hankalinshi ya fara karkata akanki,Wannan ma mataki ne na nasara"

  Dakatawa tayi da yin maganar tana sauke ajiyar zuciya,kasa kunne sehrish tayi tana jiran jin me zatace mata,

  "Yaushe zaku dawo kano?kamata yayi ace kuna tare da juna,banji daɗin komawarshi Abuja ba,"

  "Gobe muka shirya komawa gida,Amma ciwon oumman mu sai ƙara gaba yake yi,bansani ba ko tafiyar na nan,ko an fasa,Daddy nake jira ya dawo na tambayeshi,"

  "Kisan yarda zakiyi Ku koma Abuja,if not duk wani shirin mu zai lalace ne,Ita kuma Oummanku,Allah ya bata  lafiya,zamu tayaku da addu'a,Zan yi magana da daddy ɗin naku gaskiya ƙwara adawo da ita nan Abuja,zata fi samun caring,ga kuma su hosana da jahad,idan tana ganinku ku uku atare sai inga kamar zata iya dawowa hayyacinta in a short time,"

 Sehrish ta Gamsu da bayaninta ita kanta tayi tunanin hakan,

  "Nagode sosae Mommy,Allah yabarmun ke,Har na kosa mu hadu,don nayi missing ɗinki sosai da sosai,"

  dariya hajiya azeema tayi tare da cewa"don't worry ur self in dai nice har sai kin gaji da gani na,Am coming back soon,Dani za'ayi yaƙin karshen nan,da makamaina zanzo,mu bazama a filin daga har sai mun cimma nasara,"cike da Zolaya tayi maganar,hakan ba ƙaramin dariya ya ba sehrish ba,hada dafe cikinta,taji daɗin kiran da Hajiya azeema tayi mata,Ta sanyata farin ciki sosai,Sun jima suna waya kafin daga bisani suka yi sallama,


Wurgi tayi da wayar saman mattress,fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi,tana cikin Nishaɗin nan ta soma jin faɗuwar gaba rass rass!tunani ta shiga yi ko mai yasa take jin faduwar gaba?kodai wani abu na faruwa ne,tana cikin wannan fargabar taji an kashe ƙwan falo,da farko bata damu ba,tun da ba ita kaɗai bace acikin gidan Akwai security guards zai iya yiwuwa ma Daddynsu ne ya dawo,dama ya sanar da ita cewa after isha' prayer zai wuce gidansu Maman sadeeq,


Ƙwala mashi kira ta soma yi don taji idan shi ne ya dawo,

  "Daddy!Daddy!Daddy Abusufyan"!shiru ba'a amsa mata ba,nan fa ta soma zargin kodai wani ne ya shigo masu,Amma ae akwai security a gidan,kasa jurewa tayi hakan yasa ta mike tsaye,ta tunkari ƙopar ɗakin,a hankali tasa hannu ta buɗe ƙopar ɗakin ta fara leƙawa,ko'ina duhu babu haske a falon,motsin takun takalmi ta fara ji,




🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾


  *_GYARA SHINE MACE_*


*_ZATA FASHE FA KARKU BARI AYI BABUKU ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI KUMA AKAN FARASHI MAI SAUK'I ,MAMAN YUSUF YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA ZAFAFAN KAYANTA MASU MATUKAR INGANCI_*

🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾🌻🌾


*_'Yar uwa shin ko kin San lokacin sanyi lokaci ne da yake dask'arar da ni'imar mace , yake yawan bushe gaban mace , sannan lokacin ne maza sukafi bukatar matansu , lokaci ne da kowane lafiyayyen namiji yakeson ya jishi ajikin matarshi a kowane lokaci , to ya kike gani idan har mijinki Yana son kasancewa Dake Haka kekuma ga ni'ima a bushe , 'yar uwa mace fa Saida gyara , ko kinada kyau to ki k'ara da wanka don ci gaba da kankanrowa kanki daraja da k'ima a idon Mai gida ,. Ki tuna duk son da namiji ke maki in har kinada matsala a wannan wajan to wlh akwai matsala don son da yake maki bazai Hana kurinka samun matsala dashi ba ,idan kuwa har Yana samun yadda yakeso wlh ko baya sonki to Ina tabbatar maki da a hankali wata Rana sai ya soki Kuma zakiga kowane lokaci Yana tattalinki da gudun abunda zai 'bata maki Rai , Mata a kula*_ maman yusuf likitar Mata 08133079957 


*Wannan dalilin ne yasa nazo maku da Kaya masu zafi kamar Haka*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻


Akwai ingantaccen maganin sanyi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata , kun dai San illar da sanyi yake da ita ku kula,


Akwai ingantaccen maganin nono hadin gargajiya na Sha Dana shafawa Mai taso da nono ya Kuma gyarashi Hadi da tsayuwarshi ,😍


Sai maganin hips Wanda zaisa hips dinki ya ciko kema ki shiga jerin Mata masu aji😍


Akwai maganin k'iba Wanda zai ciko da jikinki kiyi kiba Yar daidai Mai kyau wadda zata dace da yanayin jikin ki💃


Ina bada Hadi na mussaman ga yarinyar da ta rasa budurcinta sanadiyar fyade ko yaudarar d'a namiji ,Wanda insha Allah akayi amfani dasu to yarinya zata koma normal Wanda duk zata aura Ba zai iya Gane komai ,

Mmn Yusuf likitar Mata💃😍


Akwai hadin amarya Wanda zaisa ki ciko ki hade gam sannan su Baki ni'ima irin wadda akeso ingantaccen sirrin da zaisa ki Kara samun soyayyar mijinki cikin sauki💃💃💃


Akwai hadin sabon budurci da mukeyi ga wadda ta kasance bazawara hadine da ko haihuwarki nawa akayi maki shi Zaki koma tamkar budurwa Wanda ko Wanda Kika aura zaisha mamakinki Wanda hakan Kuma wata hanya ce ta kankanrowa kanki daraja da k'ima ne zawarawa ku matso karku Bari ayi babuku💃💃💃💃💃


Akwai hadin Mai jego , kunsani mace na rasa mafi yawa ni'imarta yayin haihuwa wata ma Zara karu ne to indai kikayi wannan hadin Ina tabbatar maki da cewa Zaki hade ciki da waje gabanki zai ciko sosai in karuwa kikayi K'arin zaizo ya hade tsaf sannan Zaki samu dawamammiyar Ni'ima


KADAN DAGA CIKI WASU KALOLIN👇🏻👇🏻


Kalolin gumba

Kalolin matsi

Kalolin gari

Kalolin tsumi


Zumar dabino

Zuma Mai rubutu

Zumar goron Tula

Zumar ridi


Dahuwar kaza

Dahuwar zabo

Dahuwar zuciya

Dahuwar ciccibi

Dahuwar tsoka Tara

Dahuwar Yan shila

Dahuwar kwai Mai rubutu


Turaren mallaka

Turaren Mara

Turaren tsugunno

Turaren k'irji

Shuumar humra

HATSABIBI turare

Hatsabibiyar humra


Matan gaske 

Maltinat Mata

Shayin Mata

Tsumin kankana

Sirrin tafin k'afa


Akwai sirrika na mallaka da hadin farinjini 

Akwai sirrin samun farinjini ga wadda ta rasa mijin aure ko wadda takeson samun farinjinin sana'a

Akwai hadin farinjini na matar aure 

Akwai kwallin mallaka 

Zoben mallaka

Set na Jigidar mallaka


*Yar uwa abubuwan fa da yawa sosai , Wanda in nace Zan tsaya bayyanasu anan wannan page din bazai Isa ba , Ina sokoto Ina aikawa kowane gari dake cikin Nigeria da Niger ,kwatano da Ghana , karku manta adade anayi sai gaskiya , ga Mai sayen d'ai d'ai ko masu siyan sari , ku tuntubeni ta wadan nan numbers👇🏻👇🏻👇🏻


 07069711327 or 08133079957 call or Whatsapp ,Ina maraba daku customers😍😍😍😍😍


Masu buk'atar ganin kalolin kayana to kuyi sarving wannan number 08133079957 sannan kuyi min magana Nima nayi sarving number ku ta hakanne zaku dinga ganin kayana da zarar na d'ora, ngd sosai taku maman yusuf likitar mata😊😊😊😊😊😊😊😊😊

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: tsoro ne ya kamata,Zuciyarta sai harbawa take yi da ƙarfi da ƙarfi,wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,Sam takasa Motsawa,tabbas wani ne ya shigo cikin gidan tunda harta Ambaci sunan Daddynsu bai amsa mata ba,A ƙopar ɗakin ta tsaya cak kamar an dasa mata Aya,Saboda duhu ta ko'ina bazata iya hangen meke wakana ba acikin falon,tunanin kiran Abusufyan tayi,da sauri ta juya hannunta na kerma tana ƙoƙarin tura ƙopar ɗakin ta shiga daga ciki,Ta jiyo ihun Oummansu dake a downstairs,A gigice Sehrish ta juya da gudun gaske ta nufi downstairs,cikin rashin sanin ina zata taka saboda duhu ƙafafunta suka harɗe daga saman benen gaba daya ta rubza mashi,mirginowa ta dinga yi daga saman benen har ta faɗo ƙasa ta ƙume goshinta,Sosai taji raɗaɗin buguwar da tayi amma a haka ta jure ta daddage ta mike,tana laluban hanyar zuwa ɗakin Oummansu cikin duhun,Sosai take jiyo sautin koke koken da Oummansu keyi,Duk tabi ta ruɗe ta rasa ina zata dosa,

  Da ƙarfi ta soma kwala mata kira"Oumma!Oumma!!"tamkar makoshinta zai 6allo waje,duhu ya hana ta gano kopar ɗakin,Bangon falon tabi ta dinga sanya tafin hannunta tana shasshafawa,da taimakon Koke koken da Oumman keyi ne ta samu ta ruƙo Handle ɗin kopar ɗakin,Da karfin ƙarfe ta sanya ƙafarta tare da Harba ƙopar ɗakin ta buɗe,Bata iya ganin komai ba saboda duhun da ɗakin yayi an kashe Hasken ɗakin kamar yadda aka kashe na Falo,

  Shafa bangon tayi dayake tasan inda Switch ɗin yake,Cikin sa'a ta kunno shi ƙitt Haske ya gauraye ko'ina na ɗakin,


Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu rasss!ƙwayar idonta tamkar zata faɗo ƙasa saboda Tashin hankalin da sukayi arba dashi,

  Ta ko'ina ya mamayeta,ƙokarin rabata da kayan jikinta yakeyi,babu kunya babu tsoron Allah,Wani irin kukan kura Sehrish tayi bata dira a ko'ina ba sai asaman gadon,A hargitse ta Cakumi Wuyan rigar jallabiyar dake ajikinshi,da iya ƙarfinta na ƙarshe tayi wurgi dashi gefe guda,Ya gangara ƙasan gadon,

  Fashewa tayi da matsanancin kuka,tana kallon Oummansu wadda tuni ta jima da sumewa asaman gadon,

  Jijjiga jikinta sehrish ta shiga  yi tana Ambaton sunanta,Dakatawa tayi da yin kukan tare da wurga ƙwayar idonta kan Mutumin wanda ke tsaye a bakin gadon,jallabiyace a jikinshi,kanshi kuwa Rawani ne,Ya sanya face mask a fuskarshi,"

  Huci kawai takeyi tana kallonshi,

Hannu yasa tare da zame takunkumin dake a fuskarshi,Mummunane sosai bai da kyau ko miskala zarratin,irin mutanen da kallo guda zakayi masu kaji ka tsanesu,Sehrish bazata ta6a mantawa da fuskar wannan fasiƙin mutumin ba,

  Ranta a matuƙar 6ace tace"Mugu azzalumi!dama sai da raina ya bani cewa kaine!Ashe har yanzu kana bibiyar rayuwarmu!Wai uban mi muka tsare maka ne!Meyasa bazaka fita arayuwarmu ba!,"

  Jinjina kai Ya sayyadi yayi yana kallonta batare da yace komai ba,sai da ta kammala balbaleshi da faɗa sannan yace"kin gama"?banza tayi bata tanka mashi ba,

  "Bansan wacece ke acikinsu ba,Amma fitsarar da kikayi mun a yanzu ya tabbatar mun dacewa rishi ce ke,Dama tun kina yarinya kangararra ce ke,balle kuma yanzu da kika samu ƴanci kika zama cikakkar budurwa,har kika samu bakin gayamun magana,Ban zo nan don inyi jayayya dake ba,Wurin uwarku nazo don ta bani haƙƙina na aure dake akanta....."

Tunkan ya ƙarasa maganar Sehrish ta Ambaci"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"dafe kanta tayi saboda jirin da take gani,Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata makoshinta,

  Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Amma baka da kunya!Tunda nake banta6a ganin ɗan akuya bunsuru ba,wawa jakki ba,kuma daƙiƙi irinka ba!Wai kai wani irin Dabbane....."A fusace Sayyadi ya daka mata tsawa tare da furta"Kalas!karki kuskura ki ƙara jifana da waɗannan munanan kalaman!Ki iya bakinki in ba so kike na keta maki rigar mutunci ba awurin nan!ƙaramar ƴar iska kawai,kin manta lokacin da kuke rayuwa a ƙarkashin ikona?idan kin manta toh bari na tuna maki,"

  Yayi maganar cike da sheƙiyanci yakai hannunshi tare da shafa gabanshi dake asandare yace"Ina fata kin tuna,"

  Waro ido waje sehrish tayi yayin da idanuwanta suka cicciko tab da ƙwalla ta furta"Nashiga uku!"

  Fashewa yayi da dariya kafin ya ɗaura da cewa"kin tuna lokacin da nake damƙar wuyanku in tasa ku gaba sai kun tsotsi gabana"?

  Innalillahi wa'inna ilahirraji'un!fashewa tayi da matsanancin kuka na tashin hankali,Tsabar raɗaɗin tunawa da wannan ƙazantar yasa ta fara yunƙurin yin amai ga ƙirjinta da yayi mata zafi sosai,

  Muryarta adisashe ta soma magana"Allah ya isa tsakaninmu dakai!Wlh Allah bazai ta6a barinka ba,Sai ya saka mana Cin zalin da kayi mana,in sha Allah tun agidan duniya zaka fara gir6ar abunda ka shuka,Ƙarshenka bazaiyi kyau ba Sayyadi,Sai kayi danasanin haihuwarka da Uwarka tayi acikin duniyar nan!Natsani ganin mummunar fuskarka fiye da yadda na tsani mutuwa,Munafuki,mugu azzalumi,fasiki,Sannan kuma matsoraci!tsabar bakin ciki ya hanaka sakat saboda ganin irin Canjin rayuwar da muka samu,Ni bansan wani tsautsayi bane yasa Oummanmu ta aureka ba,Nasan ba hakanan ka ƙyaleta ba,domin kuwa duk wata mace me hankali da tunani bazata auri dabba,daƙiƙi,bunsuru irinka ba,Jahilin addini jahilin rayuwa,Kana yin amfani da iliminka wurin cutar da rayuwar al'umma, idonta arufe take zazzaga mashi masifa,

  Goya hannayenshi yayi  asaman ƙirjinshi yana kallonta,maimakon yaji haushin kalaman da ta yada mashi,Sai ma yatsinci kanshi da jin sha'awarta,zuba mata kwartayen idanunwashi yayi yana bin jikinta da kallo batare data ankara ba,Kayan baccin jikinta shara shara suke,Subhanallah,

  Sautin dariyar da taji ne yasa ta dakata da yin masifar,ta buɗe idanuwanta da sukayi jawuur dasu,Zuba mashi ido tayi tana kallonshi ganin yana dariya,

  "Kin gama naki"?yayi maganar yana sakar mata wani shu'umin murmushi,

  Shiru tayi batace mashi komai ba,la66anta duk sun bushe sun ƙame,ga ƙishin ruwa da take ji,


"sai yanzu nake danasanin barinku da nayi araye!naso ace tun lokacin da kuke a hannuna na tattaraku gaba ɗaya na aika ku lahira,Amma Allah bai nufa ba,Duk yadda naso Sihiri na yayi tasiri akanku Amma hakan ya faskara,Na bibiyi rayuwarku tun lokacin da Mlm nura ya mayar daku wurin wata tsohuwa mai taurin kan tsiya......"

  Tunkan ya ƙarasa maganar Sehrish tace"hakan na nufin cewa,kaine kayi silar mutuwarta"?

  shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare dasa hannu yana gyara rawanin kanshi yace"ƙwarai kuwa!ni na kashe ta,saboda na nemi ta bani haɗin kai Wurin ganin na kawar daku,tayi mun gardama harda tofa mun kakin Majina ajikina,Wannan dalilin ne yasa nayi silar mutuwarta,duk da haka ban rabu daku ba,Bayan an kaiku Cell na tura inspector Esha donta tursasa maku akan ku amince Zaku amsa laifin ku kuka kashe ta,har kun amince sai kuma Ciwon Hosana ya tashi,Wanda hakan yasa Ƴan sanda suka kaiku Asibiti,Daga nan ne Allah ya haɗaku da Marshal Omar,har ya taimaki rayuwarku,Naji haushi sosai kamar na binne kaina lokacin,amma ba yadda na iya,Haka naci gaba da bibiyar rayuwarku,har lokacin da Omar yakai ku Kaduna gidan Yayanshi General Ishaq,Nan ma na biku don na kawar daku,babu wanda yasan duk wannan shirin nawa da nayi,Ni na tura matata wurin hafsat ɗiyar Laila,ta bata zunzurutun kuɗi har miliyan shidda donta Zubar mata daku,daga nan na halaka ku,hafsa ta kar6i kuɗin amma bata aiwatar da abunda ta sanyata ba,a ƙarshe ta buƙaci ta dawo mata da kuɗinta in ba haka ba zata yi ƙararsu........."

Duk cikin abunda ya sayyadi yake faɗa mata bakomai yafi ɗaga mata hankali ba,fa ce Mutuwar tsohuwa,Ashe dama shi ya kashe ta duk don saboda su?Sosai ta fashe da kuka tana kallonshi hawaye wasu na bin wasu sam ta kasa furta komai,

    Ko ajikinshi saima dariya da yake ta faman 6a66akawa kamar wani zautacce,

   "Meyasa?meyasa duk kayi wannan"A fadace tayi maganar,jijiyoyin wuyanta duk sun fito ruɗu ruɗu dasu,

   Tsagaitawa yayi da yin dariyar yace"ɗaukar fansa nake yi,ko ince mukeyi!Laifi akayi mana wanda bazamu ta6a yafewa ba,gaba ɗaya danginku a tafin hannunmu suke,duk wani motsi naku akan idonmu kuke yin shi,Nasan zaki yi mamaki,kuma zaki yi kokwanton ko ƙarya nake yi....."Hankali atashe sehrish take kallonshi,Ba ƙaramin Caza mata ƙwaƙwalwarta yayi ba,

  "Nazo nan ne,Don in kashe mahaifiyarku bawai don in biya bukatata da ita ba,Sai dai kuma ganinki da nayi yasa na canza ra'ayina akan hakan,Surar jikinki ta yi matukar tafiya dani,Yanzu haka da nake magana dake,tsuma kawai nakeyi,kin matukar tayar mun da sha'awata,tunda nake ma ni ban ta6a jin sha'awar mace ba,Sai da nayi tozali da kyakkyawar surar ƙirjinki,Nayi mamakin yadda kika Cika ta ko'ina,ba kamar yadda na sanki ba,Kai gaskiya Abusufyan ya iya raino,Naira ta zauna maki shiyasa kika canza,"

A ruɗe Sehrish take furta"Allahumma ajirni fil masibati wa'aklifni khairan minha,tsananin tsoro ne ya kamata,ganin ya sanya hannu yana ƙokarin tattare jallabiyar dake ajikinshi,Tashin hankali!

..girgiza kai ta shiga yi tana fadin"karka kuskura kace zaka kusanto ni,Ni matar aure ce,"a ruɗe tayi maganar tana ƙoƙarin saukkowa daga saman gadon'..

   "Oh ashe ke matar aure ce,wannan ae ba wani abu bane dan naci amfanin gonar wani,"

   Durowa tayi daga saman gadon tare da nufar ƙopar fita daga ɗakin,Aikuwa a zafafe Ya sayyadi ya biyo bayanta,kafin tayi wani yunkuri ya damƙi rigar baccin dake ajikinta,nan take rigar ta zame har izuwa mid back ɗinta,Fashewa ta kuma yi da matsanancin kuka tana ambaton Sunan Daddynsu,ƙoƙarin kwale mata rigar yakeyi gaba dayanta amma ta hana hakan,Ba zato ba tsammani taji yana goga mata abun gabanshi ta bayanta,Wa'iyazu billah,Daddagewa tayi da iya karfinta na ƙarshe,Ta kai mashi naushi a tsakiyar cikinshi,Amma wani abun mamaki ko gezau baiyi ba,Kamar ta naushi ƙarfe,kiciniyar ƙwace kanta ta shiga yi daga hannunshi,Ji take kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu saboda takaici,

  Saukar harshenshi taji asaman fatar bayanta,kamar wani maye haka ya dinga lashe shi,

  "Wayyo Allah na Oumma!na shiga ukku nabani na lalace!"cikin fitar hayyaci Sehrish ta samu hannunshi daya zagayo dashi ta gabanta,Ta daddage ta gartsa mashi cizo har saida ta fasa fatar hannunshi,raɗaɗin da yaji ne yasa shi yin saurin sakinta,A hanzarce ta sanya hannunta tana ƙoƙarin buɗe ƙopar ɗakin,Sayyadi ya taɗiyo ƙafarta gaba daya ta kife ƙasa,kanta ya bugu sosai,fashewa tayi da matsanancin kuka tana bugun floor ɗin da hannunta,Ta rasa ina zata tsoma ranta,jin motsinshi yasata yin saurin miƙewa zaune tana ja da baya,

  Cikin Shesshekar kuka take Ambaton sunan Daddynsu da sunan Oummansu don su kawo mata ɗauki,

  Hannayenshi ya sanya tare da tattaro jallabiyar jikinshi ya ɗage ta sama har izuwa saman cikinshi ya naɗe ta,tsikar jikinta ce ta fara tashi,ganin uban cunkoson gashin jikinshi mara kyan gani,hannu yasa ya kwale gajeran wandon nashi,Rasss taji mummunar faɗuwar gaba,

  Dariya ya dinga yi yana nuna mata abun nasa yayin da yake tunkararta tana ƙoƙarin ja da baya,

  Koke koken da sehrish keyi ne ya fara kai mata ziyara cikin kanta,lokaci guda Kwakwalwarta ta fara tariyo mata kukan ƴa'ƴanta yayin da suke ambaton Sunanta,Oumma Oumma aduk lokacin da suka shiga wani hali,Allah ne ya farfaɗo da ita,Hannu tasa tare da dafe kanta wani irin raɗaɗi ta dinga ji yanayi mata,tunkafin ta buɗe idanuwanta ta soma ambaton Sunayensu Sehrish Hosana Jahad,wani ihu da sehrish ta kurma ne yasa ta yin firgit ta mike zaune daga saman gadon,Zazzare idanuwanta tayi akan sayyadi daya duƙufa akan Sehrish,Ya sanya duka hannayenshi ya tallabo kanta yana ƙokarin Kafa bakinta agabanshi,Hasbunallah!

  Kukan kura abu tayi a fujajen ta diro daga saman gadon,a harzuƙe ta rarumi Side drawer ɗin gadon,gaba daya ta kinkimota ta ɗaga sama da gudun gaske,Bata sauketa a ko'ina ba sai akan sayyadi gaba ɗaya Ta rotsa mashi ita asaman kanshi,wani irin jiri ne ya ɗebe shi ya soma tangal tangal zai faɗi,Rawanin kanshi tuni ya yi tsalle ya fadi kasa,

  Tsabar raɗaɗin da yaji ne yasa shi sakin Wuyan sehrish,Jallabiyarshi ta sauko ƙasa daga naɗewar dayayi mata,Rawanin kanshi kuwa tuni ya wargaje aƙasa,wani irin jiri ya soma gani kafin ya dawo hayyacinshi,Ganin Abu yasa shi ɗaure fuskarshi tamau,idanuwannan sunyi jawur dasu babu ɗigon Imani akansu,Kallon kallo suka shiga yi,jinjina kanshi ya yi yana huci kamar wani mayunwacin zaki,gadan gadan ya tunkareta,gashin kanta ya damƙo tare da yin wurgi da ita,gaba ɗaya ta kife ƙasa,juyawa yayi ya koma kan Sehrish wadda ke yashe ƙasa a sume,naɗe jallabiyar jikinshi ya soma yi,zukunnawa yayi agabanta yana ƙoƙarin tallabo kanta,


Abu dake kwance a ƙasa,ta ɗaɗɗago da kanta,yayin da hawaye ke ta sharorowa akan fuskarta,karaf idanuwanta suka sauka akan Sirinjin Allurar da Likita yayi mata ɗazu da safe,Wani tunani ne yazo mata,matsawa tayi tare da miƙa hannunta,ta Damƙi sirinjin allurar,yunkurawa tayi ta miƙe,cikin sanɗa ta soma tafiya tana tunkararshi,motsin da ya ji abayanshi ne yasa yayi firgit,Juyowar nan da zaiyi don yaga me take ƙokarin yi mashi,Ba zato ba tsammani,Abu ta daddage ta burma mashi Allurar acikin ƙwayar idonshi,Zuruf ta nutse acikin ƙwayar idonshi,Wata irin ƙururuwa Sayyadi yayi,Gaba ɗaya yabi ya firgice ya gigice ya zauce,Wani irin raɗaɗin Azaba mara misaltuwa Yaji mai haɗe da zogi,Caccaka mashi allurar ta dinga yi,gaba daya ta tsiyaye mashi idanuwanshi duka biyun,sulalewa yayi kasa yana burgima,Wata irin ƙururuwa da ya soma yi gaba daya kwaratsin shi ya karaɗe ko'ina na cikin gidan,Abu ta shammace shi,ta naƙasa mashi idanuwanshi wanda ya kasance rauninsu ne,a ƙungiyarsu ta matsafa da zarar member ya rasa idonshi,duk wani sihiri na jikinshi zai rabu dashi ne,Ya dawo normal mutun kamar kowa,


Tsananin tsorone ya kama abu ganin yadda jikin ya sayyadi ke fitar da wani irin baƙin hayaki batare da wuta naci ajikinshi ba,kamar tsumma haka ya nannaɗe wuri guda,hannu tasa tare da toshe kunnuwanta,Saboda sautin kururuwar da yake yi tamkar  Ana buga ganga acikin kunnuwan nata haka take ji,sosai ta runtse idanuwanta,

Lokacin da ta buɗe su,Sai da ta tsorata,ya 6ace 6aat babu shi acikin ɗakin sai dai Tsummar jallabiyarshi tare da rawaninshi,da kuma sharba sharban Silifas ɗinshi,




*Boss Bature*



A hankali yake saukowa down stairs,jikinshi na sanye da Jeans tare da t.shirt fara,gaba ɗaya ya canza,komai nashi ya sauya,tamkar ba Sgr ba,kwata kwata babu annuri akan fuskarshi,ya ƙara haske sosai,ya kuma yi rama,


Jin takun tafiyarshi yasa suka ɗago suna kallonshi,Tsayawa yayi yana ƙare masu kallo one by One,Fuskarshi ɗauke da matsananciyar damuwa,kullum ne sai sun zauna Zaman jiran dawowar junaid,babu yadda baiyi dasu ba akan su daina hana idonsu bacci Amma sun ƙiya,koda zasu yi baccin to sai dai ya ɗaukesu anan falon,Yayin da suke zaune zaman jiran dawowar junaid,


Ƙarasa saukowa yayi daga Saman stairs ɗin Ya nufi wurinsu,tunkan ya isa yace'Bana hanaku zama anan ba"?

Shiru sukayi saboda basu da amsar da zasu bashi,

Fitowa azmee tayi daga kitchen ta tunkaro wurin da suke,ƙarasowa tayi tana faɗin"Yawwa Rafayet,Dan Allah kayi Masu magana,tun ɗazu nake fama dasu akan suci abinci amma sun ƙiya,narasa yadda zanyi dasu,

  Ɗaure fuska jahan yayi tare da cewa'Dan Allah abarmu muji da abunda ya Dame mu,Idan muna jin yunwa zamu taso ne muci,"

  Yana kai ƙarshen maganar Fawan yace"Ni wlh komai ya fita raina,Nasaba cin abinci tare da baby junaid ɗinmu,yanzu kuma babu shi,Taya ma zan iya Cin abinci?bayan bansan halin da junaid yake ciki ba,Shin yaci abinci ko bai ci ba,"ya ƙarasa maganar tamkar zai fashe da kuka,

   "Allah yasa basu cutar mana dashi ba,Junaid ya saba rayuwarshi acikin ƴan uwanshi,hakanan wasu mugaye marasa imani sun ɗauke mana shi,"Acewar Irfan,

  Guntun tsoki jabeer yaja kafin yace"Ni babban takaici na,Duk yawanmu nan,arasa wa za'ayi garkuwa dashi sai junaid,Saboda bakin Hali irin na mutanan nan,wlh duk ranar da sukayi kuskuren da Asirinsu ya tonu sai sun ɗanɗani kuɗarsu,"


Kasa kunne Sgr yayi yana sauraronsu,tsananin tausayinsu ne ya kamashi,Ita kanta azmee jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba jin maganganun da sukeyi,Banga laifinsu ba,dole ne suyi kukan rashin junaid,yaron ne akwai shiga rai,Ya damu da kowa,kowa nashi ne,

  "Wlh bazamu iya jure rashin junaid ba,Ya rafayet dan Allah idan sun ƙara kira,A sanar dasu cewa,Su dawo mana da junaid,Ni su ɗauke ni,In yaso ma su ruƙe ni na har abada,"Ayaan ne yayi maganar,yayin da yake share hawayenshi,

  "Yaya rafayet,dan Allah nima idan sun kira ace masu ga wani ƙarin ma,"khaleed ne yayi maganar idonshi arufe Kamar maijin bacci,

  "Wlh tun ranar da aka ɗauke mana junaid,ban ƙara yin wanka ba,na ƙuntata rayuwata ne saboda Nima in ɗanɗani irin raɗaɗin da junaid ke ji a hannun waɗancan Azzaluman mutanan"yana kai ƙarshen maganar ya sanya tafin hannunshi tare da rufe fuskarshi yana kuka,abun ya ta6a masu zuciyarsu sosai,


Juyawa azmee tayi da sauri ta koma kitchen saboda kukan daya ciyota,


Cike da takaici Jahan yace"wai sun ɗauke junaid saboda kuɗi..........



  

   








 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



Am sorry,



"Is Enough!"tsit su kayi basu ƙara cewa uffan ba,

  "Kafin nan da 3 minutes inaso inga kowa asaman dining chairs yana cin abinci"

Miƙewa suka yi ba don sun so ba suka nufi dining area,kowa yaja kujera ya zauna,wuri ya samu shima ya zauna,tare da ƙwalawa Azmee kira,


Fitowa tayi daga cikin kitchen ɗin fuskarta duk alamun hawaye,Serving ɗinsu ta shiga yi,daƙyar suke Cusa abincin abakinsu, 

"Kunsan Allah!kaf sai kun cinye abincin nan,its better ku saki jikinku,"


Loma suka soma yi,Suna ci hawaye na zuba,kowa da abunda yake ayyanawa aransa,

  "Babban yaya,kaifa?ba zaka ci ba?" Fawan ne yayi maganar,

Ɗaga mashi kai kawai yayi batare da yace ƙala ba,


Takun takalmi suka jiyo kamar ana tunkarosu,ɗagowa sukayi da idanuwansu suna kallon mai shigowar,Mommy ce jikinta sanye da Sleeping dress,ƙarasowa tayi ta samu wuri gefen Sgr ta zauna,

  Hada baki su kayi wurin gaisar da ita Mommy barka da dare,

  "Yawwa Sons,"ataƙaice ta amsa masu tare da kallon Fuskar Sgr dake a gefenta,

  "My son,har Yanzu ba zaka daina sa damuwa aranka ba?ina fa sane da irin yarda kake rayuwa acikin gidan nan yanzu,Ba abinci ba bacci taya zaka samu natsuwar yin investigation akan Kidnappers ɗin da Suka ɗauke mun Romeo ɗina"idanuwanta cike tab da hawaye ta karasa maganar,

  Calmly ya furta"Mommy,don't worry about that,Addu'arki kawai nake buƙata,"

  "Kullum haka kake ce mun,why should i not worry?addu'a dama inayi maka,Ni so nake inga kana cin abinci kuma kana bacci",


  Bai amsa mata ba sai ma fawan da yayi ma magana"Fawan,Call Jahad for me,"miƙewa fawan yayi jiki ba ƙwari ya nufi bedroom ɗinsu Sehrish,

mayar da hankalinshi yayi kan Mommy

  "She needs ur caring,tana cikin wani hali na buƙatar uwa atare da ita,Fawan zai kira maki ita,pls ki bata kyakkyawar kulawa,"yana kai ƙarshen maganar ya miƙe da sauri yabar dining ɗin,sam baison anayi mashi magana akan halin da yake ciki,

Girgiza kai kawai tayi,ita kanta jurewa kawai takeyi,


A bakin ƙopar ɗakinsu Fawan ya tsaya tare da sanya hannu yana kwankwasawa,

 "Wanene,"muryar hosana ce yaji ta amsa mashi,

 "Ya fawan ne,jahad ake kira,"

  bude mashi ƙopar Hosana tayi tare da ɗan leƙo da kanta tana kallonshi,

  "where is she"?

Nuna mashi cikin ɗakin tayi da hannunta,Jahad ya hango kwance saman Darduma,

  "Kamar bacci take yi ko"?

Jinjina mashi kai tayi"Eh,"

  "Ta ci abinci"

"A'a,bata ci komai ba,"

."Okey taso mun ita,"

Juyawa tayi ta koma cikin ɗakin zuƙunnawa tayi agaban jahad tare da sanya hannu tana bubbuga bayanta

  "Jahad!jahad!"mutsu mutsu ta fara yi kafin ta yunkura ta tashi zaune,ta rame sosai tun daga kan fuskarta zaka lura da hakan,idanuwanta sun ƙanƙance saboda kukan da take sha,

  "Hosana bana ce kada ki tashe ni ba,"

  "Yaya fawan ne ke kiranki ae,"ta ƙarasa maganar tare da miƙewa ta koma saman gadonsu,

 jiki ba ƙwari ta miƙe ta nufi ƙopar ɗakin,Fawan na ganinta ya ɗan saki fuskarshi,

 "Ya fawan,"ta ambaci sunanshi,

"Babban yaya ne yace in kira mashi ke,"

Hannunta ya ruƙo ya jata suka nufi dining area,

 Lokacin da suka ƙarasa dining area ɗin,kiranta Alex tayi"jahad,"Amsa mata tayi"na'am mommy,"da hannu Alex tayi mata nuni da tazo kusa da ita ta zauna,zagayawa tayi 6angaren da Alexandra take,taja kujera ta zauna,tana sauke ajiyar zuciya,

   "Ya jikin naki,"? jahad tace"Alhamdulillah da sauƙi,"

   "Good haka nake son ji,"

 Da kanta tayi serving ɗin jahad,ta shiga bata abincin abaki,dole Jahad ta saki ciki taci Abinci sosai,



 *Boss Bature*


Ajiyar zuciya ta soma saukewa tare da Ambaton"ALHAMDULILLAH"mayar da idanuwanta tayi kan Sehrish dake sume a ƙasa,da Sauri ta ƙarasa wurinta zama tayi daga gefenta sannan ta sanya hannunta tare da janyo Sehrish ta ɗaurata asaman cinyoyinta,lumshe idanuwanta tayi tare da buɗe su akan fuskar Sehrish,Slowly ta ɗaura tafin hannunta asaman fuskar Sehrish tana shafata,kafin ta yarfar da Sumar kanta gefe guda,tayi hakan ne don taga rubutun dake a bayan wuyanta,Wanda tun suna yara Maman Sadeeq ta bata shawarar tayi masu shaida,Sehrish ta sanya mata SB ma'anarshi Sehrish buzuwa,Hosana ma akwai nata rubutun wuyan HB haka ma jahad,kowaccensu tana da shi abayan wuyanta,

  "Ya Allah na gode maka,daka dawo dani cikin hayyacina,Adai dai lokacin da ƴata ke buƙatar taimako na,"tana magana hawaye ne shararowa akan fuskarta,waige waige ta soma yi tana kallon ɗakin da suke ciki,Allah sarki lokaci guda ta fashe da kuka Saboda ta gane ɗakinta ne na gidansu Abusufyan,Bazata ta6a mantawa da irin rayuwar farin cikin da tayi ba acikin gidan,Tunawa da mahaifinta Baba buzu mai gadi yasa ta ƙara sautin kukan nata,

  "Zainab!Zainabu abu,"haka yake ƙwala mata kira,idan yana nemanta,tayi matukar danasanin bijire mashi da tayi a lokacin da yake raye duk da ta auri za6inshi,bakowa tafi jin kunyar haɗuwa dashi ba,irin Abusufyan batasan da wani ido zata kalleshi ba,Ga kuma Hajiya Ameena,mutanen da suka yi mata halacci ta butulce masu,


Ruwan hawayen abu ne suka wanke mata fuskarta,wanda hakan yayi silar farfaɗowarta daga suman da tayi,Yunƙurin amai ta fara yi daga kwancen da take,da sauri abu ta ɗago da ita,nan take aman ya kwararo daga bakinta,tamkar ƴan hanjin cikinta zasu fito waje,hannu abu tasa tana ɗan bubbuga mata bayanta,Sosai ta dinga sharara aman anan ƙasa,ta galabaita sosai ga zazza6in da ya yi mata mugun kamu,

  Miƙewa abu tayi da sauri ta fito daga dakin ta shigo palour,fridge ta hango da sauri ta nufe shi,buɗewa tayi tare da zura hannu ta ɗaukko bottle water jiki na rawa ta koma cikin ɗakin,A gaban sehrish ta zuƙunna a lokacin ta kammala kwarara Aman,cire murfin robar tayi tare da tarba tafin hannunta ta debo ruwan tana zuba mata shi abakinta tana kuskurewa,bayan ta gama kuskure bakin Abu ta kafa mata robar ruwan abakinta,Sosai ta shiga kwankwadar ruwan tana sha,sai da ta ƙoshi sannan ta janye bakinta,Har lokacin Sehrish bata dawo hayyacinta ba,jikinta duk ya saki babu ƙwari,

    Ajiye robar ruwan abu tayi gefe tana kallon fuskarta,

  Gam ta runtse idanuwanta,tana faman ciccije la66anta,

  "RISHI"ta furta sunanta,

A hankali Sehrish ta ɗan ware idanuwanta akan fuskar abu,wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarta,ganin Oummansu agabanta,kuma da alama tadawo cikin Hayyacinta ne,

  "Oumma,"ta ambaci sunanta tare da fashewa da wani sabon kuka,

  Ita ma abun fashewa tayi da kuka,Cikin Shesshekar kuka take cewa"Laifina ne!komai ya faru arayuwarku ni ce sila,Ni naja maku...."

  "Oumma ba laifin ki bane,ki daina ɗaurawa kanki laifi,Allah ya rigada ya ƙaddara faruwar hakan"

  "Rishi bakisan irin raɗaɗin da nake ji acikin zuciyata ba,bansan tsawon lokacin dana ɗauka bana acikin hayyacina ba,bansan ya rayuwarku ta ƙare ba,Nasan dole kunsha Wahala"

  Sosai suke yin kukan babu mai lallashin wani acikinsu,

Sai da suka yi mai isarsu,Sannan suka tsagaita da yin kukan,

   "Ina Hosana take?ina Jahad?duk suna ina?meyasa kike zaune ke kadai acikin gidan nan?Babu kowa atare dake?

  ɗagowa Sehrish tayi daga kwancen da take saman ƙirjinta,cikin sanyin murya tace"Hosana da Jahad suna a Abuja wurin danginsu Daddy"

  Cike da Mamaki abu ta maimaita sunan Daddy,

  Sehrish tace"Eh,mahaifinmu nake nufi,Daddy Abusufyan atare muka zo kano,Tun da ya fita da marece bai dawo ba,kuma akwai security guards dake tsaron gidan,Amma bansan ya akai Ya sayyadi ya shigo ciki ba,"

  Tunda Sehrish ta ambaci sunan Abusufyan jikin abu ya kara yin sanyi lakwas,shiru tayi na wani lokaci kafin tace"Kina nufin Abusufyan yana atare daku"?

  ɗaga mata kai Sehrish tayi"Eh,"

Abun yayi matukar ɗaure mata kai,cike da mamaki tace"Taya akai kuka san cewa shi ne mahaifinku?Kuma ya akai kuka haɗu dashi"?har ya kai ku wurin danginshi"?daƙyar take magana saboda Ciwon kan da take ji yana ɗan takura mata,

  "Oumma,Labari ne mai dogon zango....,"kasa ƙarasa maganar tayi sakamakon tashin Zuciyar da take ji,

  "Sannu kinji,idan muka samu natsuwa sai ki sanar dani"

   ta ƙarasa maganar tare da ruƙo hannayen Sehrish Cikin nata,suka mike tsaye suna fuskantar junansu,haɗa ido sukayi lokaci guda suka sakarwa juna murmushi,

 "Kin girma sosai,komai naki ya canza mun,"duƙar da kai kasa sehrish tayi tana dariya,

  "Allah sarki hosana,Ashe da rabon zata rayu"?

  "Sai ma kin ganta Oumma,Zaki sha Mamaki Allah,saboda hosana duk tafi mu girman jiki,"

 wani irin farin ciki ne ya lullu6eta mara misaltuwa,


Sun jima suna tattaunawa atsakaninsu,kafin daga bisani Sehrish ta shiga toilet don tayi wanka,tunda ta rufo ƙopar toilet ɗin,ta sulale ƙasa jikin ƙofar tana kuka ƙasa ƙasa,Abunda ya sayyadi yayi mata ya tsaya mata aranta,yadda ya dinga goga mata Abunshi ajikinta,Da kuma harshenshi da ya sanya yana lasar mata bayanta Ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,runtse idanuwanta tayi sosai,wani irin ɗaci ta dinga ji acikin zuciyarta,lokaci guda ta fara jin ƙyanƙyamin jikinta,hada ƙaiƙayi miƙewa tayi ta soma tu6e kayan baccin dake ajikinta,


Lokacin da ta kammala wankan ta fito jikinta ɗaure da towel,bata samu kowa a ɗakin ba,Amma taga an gyara shi,komai ya koma yadda yake,hatta aman da tayi an kwashe shi da tarkacen Ya sayyadi,tasan cewa aikin Oummansu ne,


Jiki ba ƙwari ta wuce saman gado ta haye,tare jan bargo ta lullu6e jikinta,bakowa take jiran dawowarshi ba,fa ce Daddynsu,Tayi mamakin jimawarshi awaje,har wuraren 12,Allah yasa dai yana lafiya,


Kitchen ta shiga ta ɗauko Ashana,da sauri ta fito ta dawo harabar gidan,inda ta tattara Tsummokaran Ya sayyadi da ya bar masu,ba tare da taji komae ba ta Ƙyasta ashanar ta jefa ta asaman kayan nan take wuta ta soma ci ajikinsu,har sai da ta cinyesu abu na tsaye tana kallonsu,


Ajiyar Zuciya ta sauke tare da bin gidan da kallo,mutane ta hango a bakin gate ɗin gidan Sanye da kakin Sojoji,kowannansu a yashe ƙasa sai bacci sukeyi,Abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,ranta ne ya bata cewar Securities ne,Da alama Ya sayyadi ne yasa su yin baccin Dole,don ya samu hanyar shigowa cikin gidan,


Girgiza kai kawai tayi tare da komawa cikin falon,Bedroom ɗin ta shiga,tsayawa tayi abakin ƙopar ɗakin tana kallon Sehrish dake ƙumshe cikin bargo,jikinta sae kerma yake yi,

 Idasa shiga cikin ɗakin tayi har zuwa gefen gadon ta zauna,tare da Ambaton Sunanta"Sehrish,"

  Muryata na kerma tace"Na'am Oumma,"

   "Taya zan iya samun Daddynku?inaso nayi magana dashi,"

   "Ina da waya,nabarta a ɗaya daga cikin ɗakunan dake a upstairs,"

  Da sauri abu ta mike ta fuce daga ɗakin,Upstairs ta wuce,tana neman ɗakin da sehrish ta faɗa mata,Ɗaki ɗaya ta samu a buɗe,tun kafin ta shiga tajiyo ringing ɗin wayar tura ƙopar tayi ta shiga cikinsa,A saman gado ta samu wayar,hannu takai ta ɗauki wayar tare da duba screen ɗin

  "My Boss Man,"shi ne sunan daya bayyana akan Screen ɗin wayar,picking call ɗin abu tayi tare da kara wayar a kunnanta,batasan wanene ba kawai ranta ya bata cewar Abusufyan ne,tayi tunanin zai yi mata sallama sai taji shiru,

  Batare da ta kawo komai aranta ba,ta soma magana,

  "Assalamu Alaikum,Oummansu Sehrish ce ke magana,dan Allah kadawo gida akwai matsala,Sehrish tana cikin wani hali,yanzu haka bata jin daɗin jikinta,duk ta tsorata saboda abunda Ya sayyadi yayi mata,

  Sgr dake kwance asaman gadonshi,baisan lokacin da ya mike daga zaune ba,a kiɗime yace"What?meya faru da ita ne?Waye ya shigo"?

   Abu bata wayi muryarshi ba,ita dai kawai koma wanene so take akawo masu ɗauki ko dan saboda halin da Sehrish take ciki,

  "Ya sayyadi ne ya shigo cikin gidan,bamu san taya akai ya shigo ba,Ya so ya cutar da rayuwarta....."gaba daya abu ta kwashe dukkan abunda ya faru ta sanar dashi a ƙarshe tace"dan Allah idan ka tashi dawowa,Ka biya koda chemist ne asamo mata maganin Zazza6i,ga tashin zuciya da take ji,Tunkan takai ƙarshen maganar,Yayi rejecting Call ɗin,

  Hankalinshi yayi mugun mugun tashi,har wani jiri ya soma gani acikin idanuwanshi,a zafafe ya tunkari ƙopar fita daga bedroom ɗinshi,sai ga Marshal ya faɗo cikin ɗakin har karo suka kusan yi,

  "Bro whats happening?Where are going?"

  Zuciya ce kawai ke fusgarshi,

  "Omar,Airport zani je,"

Damko damtsen hannunshi Omar yayi ganin yana ƙokarin wuce shi ya tafi,

  "Haba Rafayet!Airport kuma at this time?Me zakayi acan "

  "Pls omar,leave alone,ka bani hanya in wuce,Zuciyana tafarfasa take yi,idan har ban kama wancan fasiƙin mutumin ba,hankalina bazai kwanta ba,"

  A ruɗe Marshal yace"Wai wa kake magana akai?ko ka gano waɗanda suka kashe junaid ne"?

  Girgiza kai yayi'A'a,ina magana akan wancan Bastard ɗin dake a Kano,Yau ya taka har gidan da Abusufyan yake..wai har...'kasa ƙarasa maganar yayi saboda raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi,

  Hankalin Omar ba karamin tashi yayi ba,tun kafin ma ya ƙarasa jin abunda ya faru ɗin,

  "Rafayet,pls Calm down ur mind,Kayi mun bayani yadda zan fahimta,'

  Mika mashi wayarshi yayi batare daya furta komai ba,

Kar6ar wayar Omar yayi, kaitsaye ya shiga call log nashi,

  Kiran da Sgr yayi ma sehrish ya fara gani,"Calling ɗin layin yayi,

A lokacin abu na acikin falo tana safa da marwa,jiran dawowar Abusufyan kawai takeyi,

  Kiran na shiga wayar,da sauri tayi picking tare da zabga sallama,

   "Am..sehrish,pls inason sanin meke faruwa anan ne,"?

  Abu tace"ba Sehrish bace,Oummansu ce,"

  Abun ya ɗan ɗaure mashi kai,jin tace Oummansu ce,a iya saninshi tana da ta6in Hankali,gaisar da ita ya fara yi cike da girmamawa tare da gabatar mata da kanshi a matsayin yayansu sehrish,abu ba ƙaramin daɗi taji ba,

  Bata 6oye mashi komai ba,kaf ta kwashe abunda tasan ya faru ta sanar dashi,"

  Jinjina kai Omar yayi,jikinshi har tsuma yake yi,daƙyar ya iya furta"Zan yi magana da Abusufyan ɗin,Ki kula da Sehrish ɗin kafin ya dawo gidan,"

  amsa mashi tayi da toh,daga bisani su kayi sallama,

  Zuba ma juna ido sukayi shi da Sgr,

"Bansan wani irin dabban mutun bane wannan,wai ma ina security ɗin dake tsaron gidan ne?aikin me sukeyi ne da har suka barshi Ya samu damar shiga gidan?shi kuma Uncle bansan ya akayi har yayi dare haka ba awaje,"Omar ne yayi maganar ranshi a matukar 6ace,

  "Last time ma,Ya ta6a yin irin hakan,Ya tafi ya barta ita kaɗai acikin gidan,"Acewar Sgr,

Omar yace"ba don Oummansu na a kusa ba,da bansan mezai biyo baya ba,Amma naji daɗin jarumtar da tayi wurin ceton sehrish ɗin,"

  Kar6ar wayar Sgr yayi daga hannunshi,Layin Abusufyan ya kira,

  Almost 3 times tana ringing ba'a ɗagawa,

  Sauke wayar yayi daga kan kunnanshi,

 Omar yace "Allah yasa dai lafiya,hankalina fa duk ya tashi,abunda za'ayi yanzu Kawai gobe da asussuba su dawo gida kawai,nasan kafin lokacin may be Abusufyan ɗin ya dawo,Zan cigaba da trying layinsa,"

  Dakyar ya samu ya lalla6a Sgr ya fasa zuwa airport ɗin,Amma fa abun ya tsaya Mashi aranshi,gefen gadonshi ya zauna,Omar ma ya zauna akusa dashi,

  "Omar,kodai mun aikata wani zunubi ne da yasa waɗannan abubuwan ke faruwa damu ne?daga wannan sai wannan!

  "Rafayet,ba laifin mu bane Laifin wasu ne aka ɗaura mana,ni tunda nake arayuwata ban ta6a fuskantar tashin hankali irin na waɗannan ranakun ba,kuma ban ta6a tunanin cewa rana irin Wannan zata zo mana ba,"

  "What's the solution now?time fa yana ƙure mana,Daddy ma harya fara karaya da dawowar junaid,ɗazu da safe da yazo bedroom ɗina,Tsare ni yayi akan in faɗa mashi gaskiya,Junaid zai dawo yaci gaba da sa rai,ko kuwa bazai dawo bane,A lokacin saina kasa buɗe baki inyi mashi magana,"Sgr ne yayi maganar 

  Omar yace"Wlh nayi regretting ɗin 6oye mashi ainihin abunda ya faru,Duk da munyi hakan ne don mu ceto rayuwarshi,Amma kuma fa mun tabka kuskure babba,Don kuwa duk ranar daya gano cewa Junaid ya mutu,wlh ya gama yarda damu har abada,zuciyarshi zata karaya ne,Inajin tsoron wannan ranar,Rafayet,kodai mu sanar dashi gaskiyar lamarin ne"?

  Shiru Sgr ya ɗan yi yana nazarin maganar tashi,girgiza kanshi ya ɗan yi tare da cewa"That's not the solution Omar,koda ace zai sani,yakasance time ɗin da muka kama waɗanda su kayi silar mutuwarshi,Mu gurfanar dasu agabanshi,before mu yanke masu hukunci akan idonshi,ina ganin kamar zaifi jin sauki acikin zuciyarshi,"

  Sun jima suna tattaunawa a tsakaninsu kafin daga bisani,Kowannansu ya ɗauro alwala,Suka daidai ta sahu tare da kabbara Sallah,


Ataƙaice 


Abusufyan bai tashi dawowa cikin gidan nan ba sai wuraren sallar asuba,Bawan Allah ashe Bayan ya baro gidan su Maman Sadeeq akan hanyar dawowarshi gida aka turo mashi da saƙo cikin wayarshi cewa za'a kashe Ƴarshi da ya bari acikin gidan,Hankalin shi yayi mugun tashi,Ya kure gudun motarshi,idonshi ya rufe saboda tashin hankalin dayake ciki,Baisan sa'adda ya buge wani Tsoho ba dake ƙoƙarin tsallaka titi,Tsohon yaji mummunan rauni dole ya tsaya don yaji bazai iya daukar alhakin guduwa yabarshi cikin mawuyacin halin da zai iya rasa ransa,mutane suka kama mashi tsohon yasa shi a motarshi suka wuce dashi asibiti,babu yadda ya iya,kamar ya fasa ihu haka yaji saboda tsabar baƙin ciki,duk da wani bangare na zuciyarshi na tunasar dashi akwae security guards a gidan,Bashi ya baro asibitin ba sai wuraren Sallar Asuba Ya dawo cikin gidan,Yayi mamakin ganin komai lafiya,Lokacin daya shiga ɗakin abu kwance ya samesu rungume Saman gadon ita da Sehrish suna ta sharar baccinsu,Hankalinshi ya kwanta sosai ganin babu abunda ya faru dasu,


Falo ya koma ya zauna saman sofa,jikinshi duk amace,Ringing ɗin wayarshi dayaji yasa shi zura hannu cikin aljihu ya ɗauko wayar tare da duba sunan mai kiran nashi,Marshal Omar ne,

  Picking call ɗin yayi tare da kara wayar a kunnanshi,

  "Omar me kake yi har yanzu bakayi bacci ba"?

  On the other hand Omar yace"Uncle,Ina ka shiga ne anata nemanka,"?

  Nan Abusufyan yake sanar dashi abunda ya faru dashi akan hanyar dawowarshi gidan,

   "Yanzu na dawo gidanma,Na same su cikin koshin lafiya suna ta bacci,"

  A nan Omar ya kwashe duk abunda Abu ta sanar dasu ya faɗa ma Abusufyan,A zabure ya miƙe tsaye jikinshi na rawa,

  "Pls Uncle,ka kwantar da hankalin ka,Tunda ba abunda ya faru dasu,Abunda ya kamata kawai ku dawo gida yau yau ɗin nan zamanku anan baida amfani,dama saboda ciwon Mahaifiyarsu ne Kuma ta samu lafiya,Yakamata ku dawo gida,Hankalinmu sai ya fi kwanciya,"

..jinjina kai kawai Abusufyan keyi sam ya kasa buɗe baki yayi magana,Allah kaɗai yasan raɗaɗin da yake ji acikin Zuciyarshi,dakyar ya iya buɗe baki yace"Shikenan Omar,yanzun nan zamu shirya,'

  "Allah ya dawo daku Lafiya,"

"Ameen"daga haka su kayi Sallama,

Komawa Bedroom ɗinsu yayi wuraren karfe 6 na asuba,da alama ko sallar asuba basu yi ba,sai sharar bacci sukeyi,

  Zagayawa yayi gefen da Sehrish take a kwance ya zauna tare da zuba mata ido yana kallonta,Yayin da hawaye ke sharara akan fuskarshi,tsananin tausayinta ne ya kamashi,baiji daɗin abunda ya faru ba,ta wani 6angaren kuma yaji sanyi aranshi da Allah ya tsare mashi ita,ga kuma Mahaifiyarsu da ta dawo cikin hayyacinta ta silar abunda ya faru,

  Shessheƙar kukan da Abusufyan keyi ne ya farkar da Sehrish,buɗe idanuwanta tayi masu ɗauke da bacci,Suna haɗa ido dashi tayi hanzarin mikewa daga zaune tana ambaton sunanshi"Daddy!yaushe ka dawo?meya faru kake kuka,"

  "Daughter,Am sorry!am really sorry,duk laifina ne dana tafi nabarki ke kaɗai acikin gidan,"

  "Daddy,bangane akan me kake magana ba?nifa babu abunda ya faru dani,"tayi hakan ne don ta 6oye mashi gudun karya sanya damuwa aranshi,batasan cewa ya riga daya ji ba,

  "Omar ya sanar dani duk abunda ya faru dangane da zuwan sayyadi cikin gidan nan,"

   Mamaki ta shiga yi taya akai Ya Omar yasan abunda ya faru  dasu?can kuma ta tuna da lokacin da Oummansu ta nemi yin magana da Abusufyan may be a wurinta yaji komai,

  "Dan Allah Daddy,kada kasa damuwa aran ka tunda ba abunda ya faru dani lafiyata kalau,Sai ma wani abun farin ciki da ya faru,Oummanmu ta dawo cikin hayyacinta,Sanadin zuwan ya sayyadi,Kuma ta lalata mashi idanuwanshi,karkaso kaga yarda ya dinga kururuwa yana ihu," Tayi maganar tana kwatanta mashi irin yarda Ya sayyadi yayi ihun,

  Hakan ba ƙaramin kwantar mashi da hankali yayi ba,dama tayi hakan ne don ta sanyaya mashi ranshi,

  ɗaure fuskarta ta ɗan yi ashagwa6e tace"Daddy banga kana farin ciki da abunda na sanar dakai ba"?

  Daƙyar ya ƙaƙaro murmushi akan fuskarshi yace"Ina farin ciki mana,Naji daɗi sosai,kawai dai  nadamu ne akan Halin da kika tsinci kanki a lokacin da bana nan,"

  ɗaure fuskarta tayi"Why Daddy,bana ce ka kwantar da hankalin ka ba?komai ya wuce,Yanzu lokacin farin ciki ne,Ga ka, Ga Ni,ga Oummanmu kuma,Bari na tashe ta daga bacci kuyi magana,"ta ƙarasa maganar tare da sanya hannu tana ɗan bubbuga kafadar Oummansu,

  Murmushi kawai Abusufyan ke saki yana kallonta,

  "Oumma!oumma!ki tashi ga Daddynmu nan ya dawo,"

  Kasa tashi abu tayi saboda kunyar Abusufyan da take ji,Ashe tun shigowarshi dakin ta farka,tana jinsu suna magana amma tayi likimo,


"Nasan cewa idonki biyu abu,bakison gani na ko"?Abusufyan ne yayi maganar ayayin da yake leƙen fuskarta,pillow ta sanya tare da rufe fuskarta dashi,

  Murmushi suka saki atare shi da Sehrish,

  "Inason magana dake,ki tashi daga zaune,"cike da jin kunyarshi ta cire pillow ɗin tare da tashi daga zaune suna fuskantar juna,Ta kasa ɗagowa su haɗa ido da Abusufyan,kunyarshi ta rufe ta,kamar tayi rami ta binne kanta,

      

   "ZAINAB"ya ambaci sunanta da wata irin kasalalliyar murya,

   daƙyar ta iya motsa lips ɗinta wurin amsa mashi,

   "Na'am,"

Murmushi ya saki tare da ɗaga hannunshi sama yana furta"Alhamdulillah!Alhamdulillah,Almost 3 times yana ambaton hakan,Cike da tsantsar farin ciki,

   Sai faman sauke ajiyar Zuciya take yi,matsawa yayi kusa da ita tare da sanya hannayenshi biyu ya tallabo fuskarta yana ƙare mata kallo,

  Siraran hawaye ne suka soma Zarya akan fuskarta masu ɗumin gaske,

   "Hawayen menene wannan"?

Cikin Shessheƙar kuka tace"Kayi haƙuri,ka yafe mun,Na gane kuskuren dana yi,Naji jiki Abusufyan,nayi dana sanin butulce maka da nayi,Haƙƙinka ne yake ta bibiyar rayuwata,Ni ce silar duk wani abu daya faru a rayuwarmu nida ƴa'ƴana...."ta ƙarasa maganar tare da fashewa da kuka,Hannu tasa ta zame hannayenshi daga saman fuskarta,kafin ta Sauko daga saman gadon ta zuƙunna saman guiwowinta agabanshi,tana ci gaba da yin kukan....

   "Tun da nake arayuwata,ban ta6a ganin mutun mai kyakkyawar Zuciya irin taka ba,duk irin girman laifin dana aikata maka,hakan baisa ka guje ni ba,Sai ma bibiyar rayuwata daka ci gaba dayi duk don kaga Ka taimake ni,Amma na kasa gane hakan,saboda tsabar baƙin kishin da nake dashi na yanke maka hukunci batare dana tsananta bincike ba......"

     Ruƙo hannunta Abusufyan yayi tare da ɗago da fuskarta yace"pls bana son muna tuna abunda ya wuce,Ni komai ya wuce a wurina Abu,tabbas naji zafin abunda kika yi mun Amma wlh banta6a ruƙe ki araina ba,kullum burina inga na taimaki rayuwarki saboda baki da kowa abu,Allah kaɗai gare ki,Sai kuma Ni dana haɗa zuri'a dake,Ba zanso rayuwarki ta wulaƙanta ba,ko ba don haka ba Ke amana ce agare Ni,"


Zuba masu ido Sehrish tayi tana kallonsu fuskarta ɗauke da Murmushi,tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,

  "Bansan da wasu kalmomi zanyi amfani ba wurin bayyana maka irin farin cikin da nake ciki ba,Abusufyan Allah kadai ne zai iya biyanka,",addu'oi ta shiga yi mashi yana amsa mata da ameen,Kafin daga bisani Ya nuna mata gefenshi ta miƙe ta zauna,

   "nasan kinyi kewar ƴa'ƴanki sosai,In sha Allah Yau ɗinnan zamu wuce Abuja,Zaki ga Hosana da Jahad,da kuma sauran Family ɗinmu,"


Fira sosai suka shiga yi,Anan ta samu labarin irin wuyar dasu sehrish suka sha bayan 6acewarta,da kuma yadda akai suka haɗu da dangin mahaifinsu da shi kanshi Abusufyan din har kawo yanzu da suke bata labarin,Abu tasha kuka sosai tsananin tausayinsu ne yakamata,ta wani 6angaren kuma tayi farin ciki sosai Da Allah ya nuna mata wannan ranar da ranta kuma da Lafiyarta,


Batare da 6ata lokaci ba Suka kammala shirinsu na komawa Abuja,A jere Motocinsu suka fita daga cikin gidan,Motar Abusufyan na atsakiyan motocin security ɗin gidan,Kaitsaye hotoro suka wuce domin yin sallama dasu Maman Sadeeq,

  Sunsha kuka sosai,musamman Maman sadeeq da Abu,rungume juna suka yi kamar karsu rabu,babu wanda bai zubda ƙwalla ba acikinsu,kafin su tafi sai da Abusufyan ya damƙa ma Malam Nura key din gidansu dake a nasarawa G.r.a,Ya mallaka masu shi duk da haka sai da ya ƙara masu da zunzurutun kuɗi har miliyan 10,yace ya dauki miliyan bakwai yaba Baban Umari cikon miliyan ukkun,don bai manta da gudunmawar da akace ya bada ba wurin neman abu,anan take ya rubuta ma Malam Nura cheque,Duk da haka bai ƙyalesu ba,Bayan haka kuma yayi masu albishir ɗin cewa tare dasu Za'ayi aikin hajjin bana,Wayyo Allah saboda tsabar farin ciki,kasa bude baki su kayi don suyi mashi godiya,Kuka kawai sukeyi,abun da basu ta6a tsammanin zasu samu a rayuwarsu ba,Yau gashi silar taimakon da sukayi Allah ya ɗaukaka rayuwarsu,

  Sehrish kuwa Dama tayi alƙawarin zata taimaka ma Sadeeq ya gyara keken shi,maimakon kuɗin gyaran keken sai Gashi ya samu kyautar danƙareriyar Motar Abusufyan gaba daya ya mallaka mashi ita,kusan zaucewa Sadeeq yayi saboda tsabar farin ciki,sun jima a wurinsu suna bankwana,kafin daga bisani Sukayi masu Sallama,Anyi rabuwar mutunci sai kuma in Allah ya haɗasu wurin shagalin bikin Ƴa'ƴan abu,


Ɗaya daga cikin motocin security ɗinsu suka shiga Gidan baya Abu da Sehrish,Abusufyan yana agaban motar,A jere Motocin suka kama hanyar fita daga unguwar,


Su Maman Sadeeq na tsaye a kopar gida ita da Mlm nura,tare da sadeeq sai bye bye suke yi masu da hannu,yayin da hawaye ke zuba a fuskar kowannansu,


Sehrish sai lekensu takeyi ta glass ɗin motar dake a zuge,har sai da suka 6ace ma ganinta tukunna ta hakuri da leken,Rayuwa kenan in akayi hakuri Komai mai wuce ne,


Hannu abu tasa tare da janyo Sehrish ta rungumota ajikinta,a lokacin har motocin sun haura saman titi,Sun miƙi hanyar barin garin da matsakaicin gudu,

   Da zarar ta ɗago da idonta ta kalli madubin motar,Fuskar Abusufyan take gani yana sakar mata murmushi,Sunnar da kanta ƙasa tayi tana ƴar dariya,

  Sehrish batasan wainar da suke toyawa ba,domin kuwa ta lumshe idanuwanta da alama bacci ya fara ɗaukarta,

  Sake ɗagowa abu tayi tare da kallon Mirror ɗin,suka ƙara haɗa ido dashi,

  Kashe mata ido ɗaya Abusufyan yayi,batasan lokacin da ta fashe da dariya ba cike da tsantsar farin ciki,

   Shima dariyar yayi,kusan minti 30 bata ƙara dagowa sun haɗa ido ba,saboda baccin da yayi awon gaba da ita,

  Wasa wasa shima bacci ya ɗauke shi,dama duk basu samu isasshen Bacci ba a adaren Jiya,


Wuraren ƙarfe 2 na rana suka ƙaraso Abuja,Slowly motocinsu suka shararo izuwa cikin gidan,tun da Hosana tajiyo sautin shigowar motoci da gudun gaske ta fito daga cikin falon don taga su wanene,


Bayan sunyi parking ɗin motocin,Abusufyan ya fito daga cikin motar,hosana na ganinshi ta ƙwala mashi kira"Daddy"!wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,da gudun gaske ta nufe shi tare da faɗawa jikinshi ta ƙankameshi sosai,tana dariya,

  "Hosana,"ya Ambaci sunanta tare da ɗago da ita daga jikinshi yana kallonta,fuskarshi ɗauke da murmushi,

  Ɗaure fuskarta ta ɗan yi ashagwa6e tace"Munyi fushi daddy,Sai yau zaku dawo"?

  Yana ƙokarin buɗe baki ya bata amsa,karaf idanuwanshi suka sauka akan Jahad wadda ta fito daga cikin falon tana tunkaro su,

Gabanshi ne ya faɗi rass!Ganin yadda kamanninta suka sauya tamkar ba ita ba,ta rame sosai ,tafiyar kanta ma daƙyar take yinta,

   Ƙarasawa tayi gabansu ta tsaya batare da tace komai ba,idanuwanta na kallon ƙasa,

  "Jahad!kinyi rashin lafiya ne"?ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

   "Zazza6i nayi sosae amma naji sauƙi yanzu,"

 Hannu yasa tare da janyota ya rungumeta ajikinshi,Kasa jurewa tayi aikuwa ta fashe mashi da kuka sosai,

  Hankalinshi ya ƙara tashi,

  "Jahad kukan menene"?

 Cikin shessheƙar kuka tace"bakomai Daddy,nayi kewarka sosai,"

  hannu yasa yana ɗan bubbuga bayanta yace"Am Sorry Daughter,pls ki daina kuka kada kisa nima na fara zubar da hawayen nawa,"

  Dakyar ta tsagaita da yin kuka ta ɗago da kanta daga jikinshi tace"Daddy,ina rishi take?ina kuma Oumman mu?Hosana ta sanar dani cewa an ganta,"

  Murmushi ya saki tare da sanya hannunshi ya ɗan kwankwasa glass ɗin motar,

  Buɗe murfin motar Abu tayi tare da fitowa daga cikin Motar,Zuba mata ido su kayi suna kallonta kamar yadda itama take kallonsu,

  Atare suka haɗa baki wurin ambaton sunanta"Oumma!"

  Murmushi ta ɗan sakar masu,tare da buɗe masu hannunwanta don su zo ta rungumesu,Matsawa suka yi tare da faɗawa saman jikinta,ta haɗasu duka ta rungume sosai,fashewa sukayi da matsanancin kuka kamar ransu zai fita,musamman jahad da take cikin wani hali na buƙatar kulawarsu,

  Itama abun kukan takeyi sosai,babu mai lallashin wani acikinsu,Fitowa Sehrish tayi daga cikin motar ta other side ɗin,jikinta a sanyaye ta zagayo ta wurin da suke,bayansu jahad ta fada ta rungumesu,abu ta haɗa da ita duka ta ƙanƙame abunta,


Tuni hawaye sun wanke fuskar Abusufyan,Yau burinshi Ya cika na ganin ya haɗa kan family ɗinshi,wannan rana ce da bazai ta6a mantawa ba arayuwarshi,,


Suna cikin wannan yanayin sai ga Abbansu junaid tare da Alexandra sun fito daga cikin gidan,tsayawa su kayi suna kallonsu fuskar kowannansu ɗauke da murmushi,

  "Bismilla,Ku ƙaraso daga ciki mana,"Abba ne yayi maganar tare da yi masu nuni da hannunshi,

  Kallonsu Abu yayi tare da yi masu gyaran murya yace"Koke koken sun isa haka,mu shiga daga ciki mana,"

  Raba jikinsu sukayi dana Oummansu,ta ruƙo hannun jahad da hosana acikin nata,Abusufyan kuma ya ruko hannun Sehrish wurinsu Abba dake atsaye,

  tunkan su ƙaraso Abba yace" masha Allah,Yau family ɗin Abusufyan ya haɗu wuri guda,Ga Uwar Ga uban Ga kuma ƴa'ƴansu,"ya ƙarasa maganar yana dariya,

Alex tace "U'r Highly welcome, Abusufyan's Family,Am glad to see guys "ta yi maganar tare da ƙarasawa ta rungumo Abu ajikinta,hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba,


Sun jima a waje suna gaisawa kafin daga bisani suka koma babban falon gidan,Kowa dake acikin gidan sai da ya hallara A falon,Abusufyan ya shiga gabatar ma abu kowa,Sun yi farin ciki sosai,duk da tashin hankalin da suke ciki hakan bai hanasu yin Murnar dawowar Uncle ɗinsu ba tare da Oummansu rishi,Abusufyan ya lura da yanayin fuskokinsu,abun ya ɗaure mashi kai,mutanen gidan duk sun rame sunyi duhu,bashi kaɗai ba hatta Sehrish ta ankara da canzawar da mutanen gidan su kayi,Sai faman wurga ido takeyi taga ko junaid zai fito amma shiru babu shi,Ranta ne ya bata cewar ko sun fita tare dasu Babban yaya ne tunda bata gansu ba acikin gidan,


Basu tashi sanin halin da Family ɗin suke ciki ba,Sai da suka huce gajiyarsu,tukunna Abba ya sanar da Abusufyan shima ɗin don ya matsa mashi ne akan son ganin junaid,Hankalin shi ba ƙaramin tashi yayi ba,jin anyi garkuwa dasu Junaid,baima son lokacin da ya rufe Abba da faɗa ba saboda ƙin sanar dashi da sukayi,Don me zasu 6oye mashi abunda ke faruwa acikin gidan,abun ya ƙona mashi rai,Har cikin ranshi baiji daɗin hakan ba,har ƙwalla saida ya zubar,


Yinin ranar Abu na tare da ƴan ukunta a bedroom ɗinsu,Sun sha firar yaushe rabo,har bacci ya ɗaukesu atare saman gadon,basu suka farka ba sai wuraren Sallar Magriba,


Bayan kowannansu yayo alwala Jahad ta shimfiɗa masu darduma suka jera atare da Oummansu,a tsanake sukayi sallar har suka kammala,basu tashi daga saman dardumar ba,ɗaga hannayensu suka yi sama suka shiga karanto addu'o'a abakunansu suna masu kara mika godiyar su ga Allah(S.W.A),


Allah Allah Sehrish take yi su kammala Sallar taja jahad gefe saboda ta tambayeta ina junaid yake sannan kuma ta bata Labarin Artabun da suka yi tsakaninsu da ya sayyadi,ita ma jahad ɗin a ƙagare take dasu ke6e ita da Sehrish,Don ta bata labarin mutuwar junaid,kota samu ta rage raɗaɗin dake acikin zuciyarta,bazata iya 6oyema Sehrish ba,duk da An gargaɗeta akan karta fadama kowa,


Basu suka samu lokacin kebewa da junansu ba,Sai bayan sallar Isha'e,kowa ya hallara a dining area,Suna cin abincin darensu,


Su biyu suka rage acikin bedroom ɗinsu,Zaune daga gefen gadonsu,kowa yayi tsit,na wani lokaci kafin Sehrish tace"Jahad,tun ɗazu nakeso na tambayeki game da canzawar dana ga mutanen gidan nan sunyi,kowa ya rame yayi duhu,musamman ke kamar kin yi ciwo,"

  Cikin sanyin murya Jahad tace"Labari ne mara daɗin ji Sehrish,Zan faɗa maki amma ina gudun na jefa ki cikin tashin hankali,"

  "Kada ki damu jahad,ki faɗamun koma menene,in sha Allah zan jure bazan tashi hankali na ba,"

    "Shikenan zan faɗa maki Amma kafin nan inaso ki yi mun alƙawarin cewa bazaki faɗa ma kowa ba"

..Sehrish tace"I promised you jahad,babu wanda zaiji abunda muka tattauna dake,"

  Shiru jahad ta ɗan yi yayin da take yin wasa da yatsun hannunta,

   "Ina sauraronki jahad,"ta faɗi hakan ne don a ƙagare take da ta ji abunda jahad zata sanar da ita,

  "Sehrish!munyi babban rashi,wanda ya raunata zukatanmu,"

..tunkan ta ƙarasa maganar sehrish taji gabanta ya faɗi rasss,

  Aruɗe tace"Jahad kada ki ce mun junaid ya mutu......!"

  Hawaye ne suka fara saukowa daga cikin idanun Jahad,bata 6oye mata komai ba game da mutuwar Junaid,Abun mamaki sai taga Sehrish na Zabga murmushi kamar wata zautacciya,

  Bata karaya ba,cigaba da magana tayi"Babu wanda yasan ainihin abunda ya faru,daga ni sai su ya Omar sai kuma Jami'an ƴan sandan da suke je wurin da kuma Sojojin dasu ya Omar suka je dasu,"

  Dakatawa tayi da yin maganar tare da kallon Sehrish,wadda ke ta sakin murmushi,

  Fashewa da kuka Jahad tayi tare da cewa"Sehrish meyasa kike yin murmushi?na faɗa maki ne don in rage raɗaɗin da nake ji acikin zuciyata,wlh da kinsan halin da muka shiga ni dasu Ya Omar da baki yi mana dariya ba,"tana kai ƙarshen maganar ta ƙara sautin kukan nata,

 Sai lokacin Sehrish ta tsagaita da yin dariyar,Sannan ta soma magana"Haba Jahad,taya zaki ce mun Junaid ya mutu farat ɗaya in yarda?bazan ƙaryata ki ba,mutuwa na akan kowa babu wanda yafi ƙarfinta,Amma ni dai ban yarda cewa junaid ya mutu ba,tunda banga gawarshi ba,"tuni hawaye sun cicciko acikin idanuwanta,

  Cikin Shesshekar kuka jahad tace"Taya za'ae kiga gawarshi!nace maki ko ƙashi ba'a samu ba daga sassan jikinshi,Saboda ya ruga da ya ƙone ƙurmus ya zama toka,"

  "Jahad ni ban yarda ba,Allah Junaid ɗinmu bai mutu ba,ki daina wahalar da kanki wurin faɗa mun,"

  Rai a6ace Jahad tace"Wlh dole ki yarda Sehrish!meyasa zakiyi mun haka!Maimakon ki tayani jimamin rashin shi amma shine kike ƙara jefa ni cikin damuwa,"

   Girgiza kai sehrish ta shiga yi tana faɗin'wlh bazan yarda ba,"tashin hankaline yasa Sehrish ta burkice mata,

  "Ko kin ƙi ko kin so dole ki yarda Sehrish,Junaid has gone forever,"

  Miƙewa Sehrish tayi jiki ba ƙwari ta nufi toilet,Shigewa ciki tayi tare da jan ƙopar ta rufe,

  Zuƙunnawa tayi ajikin ƙopar,sai lokacin ta fashe da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,

  "Allah sarki Junaid,Allah ya jiƙanka,bazan ta6a mantawa da halarcin da kayi mun ba,













 


  

  




  


   




   

   

 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





Zuƙunnawa tayi ajikin ƙopar,sai lokacin ta fashe da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,


  "Allah sarki Junaid,Allah ya jiƙanka,bazan ta6a mantawa da halarcin da kayi mun ba,Allah yasa ƙarshen wahalarka kenan"


Sai da tayi mai isarta,Sannan ta miƙe ta nufi basin,Fanfo ta kunna ta wanke fuskarta,bayan ta kashe shi ta fito daga toilet ɗin,Har lokacin Jahad na zaune tana matsar kwalla,

  Wuri sehrish ta samu gefenta,ta zauna yadda kasan ba ita bace tasha kuka acikin toilet ba,tayi hakan ne saboda batason jahad taga rauninta,hakan zaisa itama jahad ɗin ta ƙara shiga damuwa,

  "Jahad,kuka bashi ne magani ba,Allah ya jiƙanshi ya gafarta mashi,bazan iya misalta raɗaɗin dana ji acikin Zuciyata ba,Allah sarki junaid,Yayi mun abubuwan da bazan ta6a mantawa ba,"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar,yayin da take tariyo rayuwarsu ta baya ita da junaid,

   "Muna da kusanci da juna dani dashi tamkar abokai muke,ashe ɗan uwana ne shi," tana magana hawaye na zuba akan fuskarta,jurewa kawai take yi,Zuciyarta tayi mata nauyi sosai ga wani raɗaɗi da take ji,daga ta runtse idanuwanta fuskarshi kawai take gani,

  Sai lokacin Jahad ta tsagaita da yin kukan nata,kallon sehrish tayi da idanuwanta waɗanda suka yi jawur dasu sun ƙankance saboda yawan kuka,

  "Yaya rafayet da Ya Omar suna cikin tashin hankali Sehrish,baki ga yadda suka koma ba,Nafi jin tausayinsu akaina,ba don son ransu ba suka 6oye mutuwar junaid,sunyi hakan ne saboda su ceto rayuwar Abba daga rasa shi,sai gashi kuma abun ya fara damunsu,Yanzu kullum mutanen gidan nan suna sa ran dawowar junaid bansan ya zasu ƙare ba duk ranar da suka ji cewa junaid ya mutu ba garkuwa akayi dashi ba,"ƙarasa maganar tayi tare da sanya tafin hannunta saman fuskarta,ta sake fashewa da wani kukan,

  Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,abun ya ta6a mata zuciyarta sosai,

   "In sha Allah,Zamu tayasu da addu'a akan Allah ya kawo masu mafita,"Acewar sehrish,

  Sun jima suna jimamin mutuwar junaid,kafin daga bisani Jahad tace"Baki fadamun labarin rayuwarku a kano ba?Rashin kwanciyar hankaline ya hana in kiraku,Ni ban ma san inda na yarda wayata ba,"

     Nan sehrish ta labarta mata abunda ya faru zuwansu kano har zuwan ya sayyadi,"

   Murmushin takaici jahad ta saki kafin tace"Allah ya tsine ma la'anannan mutumin nan,Dama saida raina ya bani cewa shine ke bibiyar rayuwarmu,ta Allah ba tashi ba,ƙarshen shi ne yazo shiyasa yake bibiyar ajalinshi batare da ya sani ba....."

   "Jahad,Nifa ina zargin cewa su ne suka kashe Junaid,tabbaci ma nake dashi,tunda yace Family ɗinmu a tafin hannunsu yake,kuma duk motsin mu akan idonsu yake wannan ya tabbatar mun da cewa,Suna Atare damu,"

   Jinjina kai jahad tayi"Nima yanzu shi nake zargi,bayan shi kuma ina tunanin akwai wani mai take masa baya,ko kuma wanda yake take ma baya,Dole akwai wani a kusa damu,Lamarin ma ya fara bani tsoro Rishi,ɗan adam ba abun yarda bane,Ke dai kawai ki kalli mutum,"

 cike da takaici sehrish tace "Wlh ji nake da ina da halin da zan iya taimaka masu Babban yaya dana taimaka masu,Amma zamu tayasu da Addu'a dare da rana,That's the only solution......"


Turo ƙopar da akayi ne yasa suka dakata da yin maganar,atare suka ɗago don suga wanene

  Hosana ce atsaye sai faman lasar hannunta take yi,bakinta duk maikon abinci tace"Waiku ba zaku zo muci abinci ba"?

  A fusace Jahad ta warci pillow tare da wurga mata shi ya sauka akan fuskarta,

   "Sakarya kawai,Ci kaɗai kika sani,Ba za'aci abincin ba,sai kace bakisan Halin da ake ciki ba,"

    Harara hosana ta jefa mata,kafin tace"Ae bani na kar zoman ba,Rataya aka bani,"guntun tsoki taja tare da jan ƙopar ta fuce tana raira waƙa,

   Girgiza kai Sehrish tayi tare da cewa"Allah ya baki lafiya Hosana,"

  "Ameen,"jahad ta amsa a yayin da take gyara kwanciyarta saman gadon,




Wuraren ƙarfe Goma Sha biyu na dare,Kowa ya yi shirin kwanciya,A saman gadonsu Abu ta kwanta tare da Hosana da Jahad,Gadon yayi masu kaɗan su kwana su huɗu hakan yasa ta sanar dasu cewa zata wuce ɗakin Aunty Azmee ta kwana acan,fitowa tayi daga cikin dakinsu jikinta sanye da jallabiya,


Babu kowa A main palour ɗin,Da alama duk sunyi bacci koda basuyi bacci ba,to suna a bedrooms ɗinsu Ne,


Upstairs ta wuce Part ɗin Sgr,hannu tasa ta tura ƙopar tare da shigewa ciki,sai da gabanta ya faɗi ganin irin dattin da falonshi yayi,komai a hargitse,wannan ya ƙara tabbatar mata da cewar babu Lafiya,Mutun mai tsafta irin Sgr bazai bar part ɗinsa da dauɗa ba irin haka,


Ashe bata ga komai a falon ba,Sai da ta shiga bedroom ɗinshi,Tashin sense,tun A  ƙopar ɗakin ta fara cin karo da robobin lemun da ya sha yayi wurgi dasu a wurin,a hankali take tafiya izuwa cikin ɗakin,haɗaɗɗen gadon nan nashi ya canza kamani,Zanin gadon yayi uban squeezing,komai ya fita hayyacinshi,Pillow har a ƙasa anyi wurgi dashi,tausayinshi ne ya kamata,tuni hawaye sun fara saukowa saman kuncinta,gefen gadonshi ta zauna tana shessheƙar kuka sai da tayi mai isarta,Sannan ta mike tare da cire mayafin dake akanta ta  ɗaure ɗamara dashi,toilet ɗinshi ta fara shiga,yayi datti sosai,hada ƙura kamar ba mutun ke amfani da shi ba,batare da 6ata lokaci ba,within 30 minutes Sehrish ta gyara mashi ko'ina ya dawo fes dashi,taci baƙar wuya don ba ƙaramin aiki tasha ba,bayan ta kammala da toilet ta dawo bedroom ɗin ta gyara mashi,ta canza mashi bedsheet da blanket,komai tayi arranging ɗinshi,after ta gama da bedroom ɗin ta Koma falonshi,Nan ma ta gyara mashi shi,Ƴan share share ne,ƴan goge goge ne babu abunda ta bari,


A galabaice ta fito daga part ɗinshi lokacin da ta kammala gyaran,saukowa downstairs tayi tana tafiya kamar an zare mata lakar jikinta,kitchen ta wuce da niyyar ta ɗaura mashi girki duk da jahad ta sanar da ita cewa bai cika cin abinci ba,kuma bata da tabbacin zai dawo gidan ko bazai dawo ba,


Within 30 mins,ta kammala shirya mashi dinner ɗinshi,fitowa tayi daga kitchen ɗin ta koma bedroom ɗinsu,A hankali ta tura ƙopar ɗakin ta shiga ciki,

  Murmushi ta saki yayin da idanuwanta ke kallon Oummansu dake rungume da Jahad suna bacci,Hosana ma na manne da ita,ta rungumeta ta baya,

   "Allah sarki,Rayuwa kenan,ko kusa banta6a tunanin zanga wannan ranar ba,Ya Allah ka ƙara haɗa kan zuri'armu,"

  Na amsa mata da Ameeen,

Wall clock ta duba kusan ƙarfe 1:30 na dare,toilet ta wuce,within few mins,ta watso ruwa,


Fitowa tayi da ɗaurin gaba,Gaban dressing mirror ta zauna saman front chair ɗinshi,har lokacin Junaid na faɗo mata aranta,jin mutuwarshi take yi kamar ba a gaske ba,


Hannu takai jikin drawer chest na mirror ɗin gida na ƙarshe ta janyo shi,kayan da Aunty Azeema ta aiko mata dasu ne,a nan ta jerasu,tare da wasu daga ciki ta tafi kano na gyaran jiki,amma bata fara amfani da turarurrukan ba,

 

Ɗauko turaren tayi hadi da wasu haɗaɗɗun mayukan shafawa na jiki ta ajiyesu agaban madubin

  Ko'ina na jikinta tabi ta mulke shi da mayukan,bayan ta gama kuma ta feshe jikinta da turarurrukan,powder ta shafa a fuskarta,Sannan ta murza man baki mai ƙyalli asaman la66anta,Wow ta yi kyau ba kaɗan ba,kamar Aljana haka ta zauna tana kwalliya,ko tsoro bata ji ita kaɗai cikin daren nan,


Ta ƙwallafa rai akan son ganin Sgr,ta damu sosai akan rashin baccin da taji Ance baya yi,da kuma rashin cin abinci,Yafi kowa shiga damuwa akan rashin Junaid,


Miƙewa tayi tsaye tare da nufar wardrobe ɗinsu,buɗewa tayi tana laluben kayan baccin da zata sanya a jikinta,Night gown ta ɗauko red colour,tsayin rigar bazai wuce dai dai guiwarta ba,launinta kuma maroon colour ce,


Zura rigar tayi ajikinta,ta ɗauko mayafi ta yafa asaman kanta,komawa tayi gaban mirror ɗin,turarurrukan ta ƙara fesawa ajikinta,wani irin fragrance mai sanyaya zuciya jikinta ke fitarwa,


Zirga zirga ta soma yi acikin bedroom ɗin har ta fara fidda ran zasu dawo cikin gidan,Gaban window ta koma ta janyen labulen tare da zuge glass ɗin tana leƙen harabar gidan,


Gajiya tayi da tsayuwa ta koma daga gefen gadon ta zauna,gyangyaɗin bacci ta fara yi,a hankali ta ɗan kwanta a takure daga gefen gadon,in a short time bacci ya ɗauke ta,



Minti goma sha biyar da fara yin baccinta,Sai ga Motocinsu  sun shararo da gudun gaske cikin gidan,motarsu marshal Omar ce farko,Sai Motar Sgr dake biye da tasu,Da alama dai wani bincike suke yi wanda yasa har sukayi dare a waje,

 

Parking ɗin motocin suka yi,At same time Major da Armstrong suka fito tare da buɗe masu motar,


Atare suka fito kowannansu na sanye da army trouser,tare da Long sleeve shirt green colour,sallama suka yi masu Armstrong kafin suka Nufi ƙopar shiga Main palour ɗin,hannunsu ruke cikin na juna,Upstairs suka haye bayan sunyi sallama da junansu,kowa ya wuce part ɗinshi,


Tunkan ya shiga falon ya fara jin daddaɗan kamshin na kai mashi ziyara cikin hancinshi,Tura kopar yayi slowly ta buɗe,Shiga daga cikin falon yayi abun yayi matuƙar ɗaure mashi kai,Ganin an gyara mashi falonshi an canza mashi kamanni,ko'ina yayi fess,da farko yayi tunanin ko Azmee ce ta gyara mashi ɗakin,afterwards ya fara doubting ko Yarinyarshi ce ta dawo,Cos ya hana Azmee yi mashi aiki ko part ɗinshi ma bata Zuwa,ranshi ne ya bashi cewar Uncle ɗinsu ya dawo,


Walking slowly ya nufi bedroom ɗinshi,Lokacin da ya shiga cikin ɗakin nan ma yaga angyara mashi ɗakin,Har cikin ranshi yaji daɗi sosai,ƙarasawa ciki yayi tare da rage kayan jikinshi,Ya shiga toilet domin yayi wanka,cikin minti Goma sha biyar ya fito jikinshi sanye da bathrobe,hannunshi na ruqe da short towel fari yana tsane ruwan dake acikin sumar kanshi,bayan ya kammala ya koma gefen gadonshi ya Zauna,ya jima ahaka kafin ya gyara kwanciyarshi asaman gadon batare da ya cire Bathrobe ɗin ba ya sanya night dress ɗinshi, damuwa tayi mashi yawa,a kowace daƙiƙa gabanshi faɗuwa yake yi,saboda gudun da lokacin keyi,yau har ya rage saura 1 week da ƴan kwanaki su bayyanar da Junaid agaban Abbansu,

    _Ya Allah makes it easy for me_Ya furta hakan yayin da idanuwanshi ke kallon Ceiling,ya ƙura mashi ido fuskar junaid kawai yake gani tana yi mashi gizau,babu alamun bacci a idanuwanshi don kuwa tuni ya ƙaurace mashi,

     "Assalamu Alaikum,"kamar daga sama yaji muryarta acikin kunnanshi,Wurga eyeballs ɗinshi yayi akanta batare da ya ɗago daga kwancen da yake ba,tun daga ƙasa har sama yake bin ta da kallo,. 

      Tsaye take abakin ƙopar ɗakin,hannunta ruƙe da tray wanda ta shirya mashi dinner ɗinshi,

Amsa mata sallamar yayi tare da bata izinin shiga daga cikin ɗakin,

 Ƙarasawa cikin ɗakin tayi,asaman table ɗin gadonshi ta ajiye mashi tray ɗin,

  Lumshe idanuwanshi yayi,ƙamshin turarenta sai kai mashi attack yake yi,

Gaisar dashi tayi"Ya rafayet,how are u and how work" batare da ya buɗe idanuwanshi ba yace"Alhamdulillah,Am well,"iya abunda ya furta mata kenan,

 Jiki asanyaye ta juya zata bar ɗakin,bai tanka mata ba sai da takai bakin ƙopar fita daga ɗakin sannan taji yace"wannan food stuffs ɗin fa?wa kika ajiye mawa"?

   Dakyar ta iya bashi amsa da cewa"Kai na kawo mawa,". 

   "Okey,bana jin yunwa,Zo ki kwashe su,".

Sam bata ji daɗin jin hakan daga gare shi ba,at least koda ace yana cikin damuwa bai kamata ya yi mata haka ba,how many days basa atare almost 2 weeks,ko irin sannu da zuwa babu,tayi mashi uziri ne kawai saboda tasan halin da yake ciki,

komawa cikin ɗakin tayi idonta cike tab da ƙwalla,tasha wahalar girka mashi abinci don ta damu da halin da yake ciki,amma ya watsa mata ƙasa a ido,

Hannu tasa zata ɗauki tray ɗin kayan abinci,a hankali ya ɗan buɗe idanuwanshi ya saci kallon fuskarta,kallon ta ya shiga yi batare da ta sani ba,especially lips ɗinta dake matuƙar jan hankalinshi,tunawa yayi da halin da yake ciki,tabbas yana buƙatar natsuwa sosai,kuma yana jin cewa a wurinta ne kawai zai iya samun wannan natsuwar da kwanciyar hankali,harma da Lafiya,"Hold On!ya dakatar da ita da hannunshi a lokacin har ta juya zata tafi,

"ajiye mun,ki tsaya ki yi serving ɗina before ki tafi," juyawa tayi asanyaye tare da ajiye mashi tray ɗin asaman table,

  Yunƙurawa yayi ya tashi daga zaune,ya saukko da ƙafafunshi ƙasa,

  "Me zan zuba maka,"?

"Abunda kika san ya dace naci,"

A tsanake ta soma yin Serving ɗinshi,sosai ya ci abincin, yaushe rabon da ya sanya abincin kirki acikinshi har ya manta,sai da yaci ya ƙoshi,Sannan ya kalleta yace"faɗamun meya faru tsakanin ki da wannan bastard ɗin a Kano"?

  Gabanta ne ya faɗi rasss,mamakinta taya akai zancen yazo kunnanshiWayyo Allah!

  Girgiza kai ta ɗan yi "babu komai,babu abunda ya faru tsakanina dashi",

   "Ƙarya zaki yi mun"?rai a6ace yayi maganar tare da miƙewa tsaye,aikuwa a tsorace sehrish tace"wlh baiyi mun komai ba,ba ƙarya nake yi maka,bazan iya yi maka ƙarya ba,"

   Wani irin kallo taga yana yi mata,tarasa gane kallon menene,ganin yana ƙoƙarin zagayowa ta gabanta yasa ta soma ƙoƙarin ja da baya,

 Daga zarar ya matso saita ja da baya,a haka har suka ƙurewa bangon ɗakin,rumfa yayi mata da faffaɗan kirjinshi,lokaci guda ƙamshin turaren jikinta ya gama kashe mashi jiki,

 Da wata irin kasalalliyar murya,yace"tell me,me yayi maki?ya cutar dake?"

 Muryarta na kerma tace"A'a,bai yi mun komai ba,wlh dagaske nake,"

   "Its okey,"ya ambaci hakan tare da lumshe idanuwanshi,yayin da yake ci gaba da shakar kamshin turarenta,ganin ya rufe idanuwanshi yasa ta soma satar kallonshi,yayi haske sosai ga ramar da yayi,la66ansa sun ƙara cizawa sosai,

  Ganin yana ƙoƙarin buɗe idanuwan yasa tayi saurin kawar da nata idon,tun daga kan eye lashes ɗinta ya soma kallonta har izuwa saman hancinta,da kuma siraran la66anta,moving face ɗinshi yayi close to her face,tsinin hancinshi ya soma goga mata asaman hancinta,lokaci guda numfashinta ya fara canzawa,hannayenshi ya sanya tare da ruƙo waist ɗinta,sosai ya damƙi ƙugun,soft lips dinshi ya manna da nata a hankali ya zura tongue ɗinshi acikin bakinta,a gigice ya shiga kissing ɗinta kamar zai cinye mata la66anta,ƙanƙame juna sukayi kamar boss tace zata raba su,hannayenta gaba ɗaya suna acikin sumar kanshi tana hargitsa mashi ita,kasa jurewa yayi da tsayuwar,gaba ɗaya Ya sa6eta asaman shoulder ɗinshi,wurin switch ɗin ɗakin ya nufa ya kashe light ɗin,furniture ɗin dakin suka soma bada nasu hasken mai canza launi,ƙarasawa yayi saman gadon tare da sauketa,jikinshi har kerma yakeyi duk yabi ya susuce ya rasa tunaninshi,Rumfa ya yi mata ta ko'ina ya lullu6eta da ƙirjinshi,harshen shi ya mayar acikin bakinta,hot french kisses ya shiga bata,gaba ɗaya suka haukace ma juna,Dama bathrobe ce ajikinshi short ne kawai ya sanya daga ciki,zame mata rigar baccin jikinta ya soma yi da hannunshi,tun daga saman kafadarta ya sabule rigar har izuwa saman cikinta,Nan fa  hankalinshi ya ƙara tashi haikan,kamar sabon jinjiri haka ya kama boobs ɗinta yana sha,kamar zai cire mata nipples ɗinta,sosai ta ƙankameshi,daɗin da take ji ya hana taji raɗaɗin sucking ɗin da Sgr keyi mata,Tuni Zufa ta wanke masu jikinsu duk da sanyin A.c ɗin dake a ɗakin,wani irin gurnani Sgr keyi kamar mayunwacin zakin daya jima baici namun dawa ba,Cikin fitar hayyaci Sehrish ta zura hannayenta acikin short ɗin Sgr,tunda yaji hannunta ruƙe da Ak47 ɗinshi Ya ƙara haukacewa,a ruɗe ya shiga furta"Keep doing it Reesh,you're giving me fire, baisan lokacin da ya yayyage rigar jikinta ba gaba ɗaya yayi wurgi da rigar,damƙar pant ɗin jikinta yayi azafafe ya yage shi gida biyu,yayi wurgi dashi, idonshi ya rufe jikinshi sae kerma yakeyi He became uncontrollable,ya gama fita hayyacinshi,Zame short ɗin jikinshi yayi gaba daya ya cire shi,tashin hankali! Man at work,ƙoƙarin penetrating ɗinta yake da ƙarfin gaske bada wasa ba,Saboda baya acikin hayyacinshi,wata irin razananniyar kara Sehrish ta saki saboda raɗaɗin da taji har cikin tsakiyan kanta,a gigice ta tureshi ta Zabura ta mike jiki na 6ari ta nufi hanyar sauka daga gadon,Rukota yayi da ƙarfin gaske yayi wurgi da ita,a galabaice ta koma saman gadon,Fashewa tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,Ta tsorata sosai,gani take yi kamar mutuwa zatayi,ruƙo kafafuwanta yayi yana ƙokarin buɗesu,Ta ƙara burkice mashi,lokaci guda jikinshi ya saki wata irin kasala ta baibayeshi,da alama ya dawo cikin hayyacinshi,jiki amace ya mayar da short ɗinshi,saukkowa yayi daga saman gadon yana tafiya a wani irin yanayi Mara misaltuwa,toilet ya faɗa tare da turo ƙopar ya datse ta,

Within mins ya fito daga cikin toilet ɗin,a bakin ƙopar ya tsaya yana kallonta yayin da idanuwanshi ke rurrufewa,ƙarasawa yayi gaban gadon,tare da sanya hannunshi ya ɗauketa gaba daya ya aza asaman kafadarshi,Ya Wuce da ita cikin toilet ɗinshi,

Within 15 mins ya fito dauke da ita,irin ɗaukar da akeyiwa jarirai na hannu biyu ɗinnan,ya ɗaura mata towel a Chest ɗinta,mayar da ita yayi saman shoulder dinshi sannan ya sanya hannunshi tare da janye bedsheet ɗin ya nannaɗe shi,

A hankali ya kwantar da ita saman mattress ɗin,ɗaukar zanin gadon yayi ya tafi dashi izuwa laundry yayi datti,Wani sabon bedsheet ya ɗaukko ya shimfiɗa masu,bai kwanta ba sai da ya Sanya Sleeping dress ɗinshi white colour tukunna ya dawo saman gadon ya kwanta tare da janyota jikinshi yayi hugging ɗinta asaman wide chest ɗinshi,

 Gaba daya ya zura hannayenshi acikin towel yana shafa ƙirjinta,duk tana jin motsin hannayenshi ajikinta tayi likimo saboda kunyar shi da take ji,haɗe jikinsu yayi sosai,yadda duk wani motsi nata yake jinshi ajikinsa,ba zato ba tsammani bacci yayi awon gaba dasu,yaushe rabonshi da yayi bacci haka sati biyu kenan da ƴan kwanaki,Sai gashi yau a sanadin natsuwar da ya samu tare da Sehrish bacci ya ɗaukeshi batare daya ankare ba,

Tun daga kan yarda suke yin baccinsu zai tabbatar maka da cewa suna acikin yanayi mai daɗi,


*Boss Bature*


Can cikin dare wuraren sallar Asuba,ƙasa ƙasa ta dinga jin sambatun Sgr yana ambaton sunan junaid,yana faɗin remain two weeks ya rage mashi,Ya sanya damuwa aranshi ne shiyasa har yake yawan yin mafarki,ware idanuwanta tayi akan fuskarshi La66anshi sai kerma sukeyi,

Tafin hannunta ta sanya tare da shafa gefen fuskarshi,tsananin tausayinshi ne yakamata,taso ace tana da wata hanyar da zata iya taimaka mashi da ba abunda zai hana tayi hakan,

  Zame jikinta tayi daga jikinshi a hankali,ta saukko daga saman gadon,tana neman Night gown ɗinta,a can ƙasa ta hango rigar inda yayi wurgi da ita,ga kuma pant ɗinta da ya yaga mata shi biyu,

 Tsugunnawa tayi ta sanya hannu ta tattarasu,kafin ta miƙe da sauri ta fita daga bedroom din nashi,

  Cikin sanɗa take taka staircases ɗin,gudun kada wani ya fito yayi arba da ita a halin da take ciki,Daga ita sai Towel ajikinta,

Saukowa cikin palourn tayi babu kowa anan,gudu gudu sauri sauri ta wuce bedroom ɗinsu,Hannu tasa ta tura ƙopar sae da ta fara leƙawa taga basu farka daga bacci ba,Sannan ta kutsa kanta cikin ɗakin,toilet ta shiga da kayan jim kaɗan ta fito tare da nufar wardrobe ɗinsu,turkish dress ta ɗaukko riga da wando ta zura ajikinta,cikin sanɗa ta fito daga ɗakin ta wuce bedroom ɗin Azmee kamar yarda tayi dasu cewa acan zata kwana,

Turo ƙopar tayi ta shiga,a kwance ta samu azmee tana ta sharar baccinta hankali kwance hada minshari,lalla6awa Sehrish tayi cikin sanɗa ta nufi gadon tare da hayewa gefen azmee ta kwanta tare da jan bargo ta lullubesu,ajiyar zuciya ta shiga saukewa yayin da brain ɗinta ke tariyo mata abunda ya faru Tsakaninta da SGR,Namijin Duniya,bazata iya misalta irin halin da ta shiga ba,aduk lokacin da suke tare dashi,wata irin natsuwa take samu a wurinshi,

Junaid ne ya faɗo mata aranta,nan take kuma ta shiga tariyo memories ɗinsu lokacin da yana araye,tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,tana cikin wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita,


Lokacin da aka fara kiran sallar Asuba,azmee ta farka,har sai da ta tsorata da taga mutum kwance a gadonta,Ajiyar zuciya ta sauke lokacin da ta gane cewa ashe Sehrish ce,

 Hannu tasa tare da dan bubbugata"Sehrish!Sehrish!"

  Daƙyar Sehrish ta amsa mata"Na'am,"

 "Lokacin sallah yayi,ki tashi kiyi sallah,"

  "Toh"ta amsa mata batare da tayi yunkurin tashi ba,saukowa daga saman gadon Azmee tayi ta nufi toilet,

   Har Azmee ta kammala salla Sehrish bata motsa ba,bacci ne mai nauyi yake ɗawainiya da ita,

  Buɗe ɗakin Azmee tayi ta fuce tabar sehrish aciki,Sai da ta fara zuwa ɗakinsu Jahad ta kwankwasa masu ƙopa,taji alamun sun tashi,Sannan ta wuce kitchen,

 Tunda wuri ta fara shirye shiryen ɗaura girki,

 Sehrish kuwa sai da ta mula tasha iska kafin ta miƙe zaune,a hankali ta sauko daga saman gadon ta wuce toilet,bada jimawa ba tafito tana faman Yarfe hannunta,har lokacin akwai kasala atattare da ita,


Buɗe wardrobe ɗin Aunty Azmee tayi tana neman Hijabin da zata sanya tayi sallah,a gida na farko Cikin jerin hijabanta Sehrish takai hannu ta janyo wata maroon colour,Abayar ta gogu sosai ga ninkin da akayi mata,

Tana kammala janyo hijabin,Ba zato ba tsammani taji sautin faɗowar wani abu ƙasa kamar ƙarfe ƙarfe haka sautin ya bada,wurga eyeballs ɗinta tayi ƙasan tiles ɗin don taga menene,ƙura ido tayi tana kallon Diamond ring ɗin da ya faɗo ƙasa,A sukwane Sehrish ta tsugunna saman guiwowonta,tare da sanya hannunta ta ɗaukko zoben,Stone ɗin jikinshi sai faman ƙyalli yake yi,

 Kamar ta ta6a ganin zoben a hannun wani,zurfin tunani ta shiga yi tana ƙoƙarin gano inda ta ta6a ganin Zoben ko kuma hannun wanda ta ta6a gani,

Lokaci guda kanta ya ɗauki Caji,Almost 15 mins bata motsa ba,Jujjuya zoben take yi tana kallonshi,ta kasa tunawa amma tabbas ta ta6a ganinshi,

  Matso da zoben tayi saitin idanuwanta,Harafin da ke ajikin Dutsen Zoben ta ƙura wa ido,Harafin *J* ne,Duk yadda Sehrish taso ta gano a ina tasan zoben Sam ta kasa,miƙewa tayi hannunta ruke dashi,

  "Kodai in tambayi Aunty Azmee nawa ne farashinsa,Yayi mun kyau sosai,"ta ƙarasa maganar tare da tura zoben cikin wadrobe ɗin wurin da take tunanin tanan ciki ya faɗo,

 Darduma ta ɗauko ta shimfiɗa a ƙasa,A tsanake ta kabbara Sallah,Bayan ta kammala ta zauna saman dardumar tana Addu'a,

Hannayenta ta ɗaga sama"Ya Allah kaine gatan mu!Da kai kadai muka dogara!Ya Allah kana ganin halin da muke ciki,Ya Allah ka kawo mana ɗauki!

  "Ya Allah kaji ƙan Junaid,ka gafarta mashi kurakurenshi,Ya Allah Kasa can yafi mashi nan,Allah ka tonu asirin wadanda suka kashe shi....."sosai ta shiga yi ma junaid addu'a,bayan ta kammala sallar ta naɗe sallayar tare da hijabin da ta cire ta mayar dasu inda ta daukkosu ta ajiyesu,


Bude kopar tayi ta fuce daga cikin ɗakin,

Ɗakinsu ta koma,da sallama abakinta ta shiga cikin ɗakin,

  "Assalamu Alaikum"

"Wa'alaikum Salam,"muryar Oummansu ce ta Amsa mata,

 Murmushi ta saki tana kallonsu,gaba ɗaya suna zaune saman gadon sun zagaye juna da alama fira suke yi,

   Ƙarasawa cikin ɗakin tayi tare da samun wuri saman gadon ta zauna itama,

   "Oumma ina kwana,kin tashi lafiya,"murmushi abu ta sakar mata tare da cewa"lafiya qalou rishi,ina fata kin tashi cikin ƙoshin Lafiya"

   "Alhamdulillah Oumma,"

 Hosana tace"Yawwa rishi ƙwara da kika zo wlh,wai Oumma taƙi yarda cewa Ya Omar Saurayina ne shi zan aura,"

  Dariya Sehrish tayi tare da cewa"Amma baki da kunya Allah,Oumman kike faɗama cewa kina da saurayi,"?

  Zumbura baki hosana tayi a ɗan shagwa6e tace"ai ƙwara ni,saurayi gare ni,ke da ma kike da au.  "bata ƙarasa maganar ba,Sehrish ta buge mata baki,"shashasha karki kuskura ki faɗa wlh ranki zai 6aci ne,'

  A harzuƙe tace"Wlh sai an faɗa,"

Jahad tace"ki fada ɗin,Ni kuma in faɗawa ya Omar cewa baki respecting ɗinmu,"

  Tsuke baki Hosana tayi tana gatsina masu hanci,

  Ita dai Oummansu sai bin su takeyi da kallo,gwanin ban sha'awa,

  "Oumma,Jiya kinsha farfesun Aunty Azmee ko?ya kika ji ɗanɗanon girkinta,"Sehrish ce tayi maganar don ta kawar ma Hosana zancen da takeyi na son tona mata asiri,

  "Yayi daɗi sosai,ɗanɗanon girkin na musamman ne,Amma sai dai bansan wacece Azmeen ba,saboda banga fuskarta ba jiya da kyau,kodai itama Auntyn ku ce"?tayi maganar tana kallon fuskar Sehrish,

  Girgiza mata kai tayi alamar a'a,

  "Ba Auntyn mu bace,Amma kuma matsayin Auntynmu take,ta jima tana aiki acikin gidan nan,tana da mutunci sosai,zan haɗa ki da ita ku gaisa kuma kiyi Mata godiya,saboda ta bani kyakkyawar kulawa lokacin da nake cikin mawuyacin hali,"

  Fuskar Abu ɗauke da murmushi tace"Allah sarki,har naji ta kwantamin arai na,na kosa na ganta ma,"

  "Ae yanzu haka tana aiki a kitchen,bari muje mu tayata aiki idan muka haɗu wurin yin Breakfast zaki ganta ne,Sai ku gaisa,"

  Abu tace"To shikenan,Yanzu kuje ku tayata aiki ke da Hosana,Jahad ta zauna a wurina tunda bata da ƙoshin Lafiya,"

   Maƙe kafaɗa Hosana tayi"Ni bazanje wani kitchen ba,Ae ni ba ƴar aiki bace,"

  Dariya su kayi gaba ɗayansu,sehrish tace"Sha zamanki,Ni kaɗai na isa na tayata aikin har mu kammala,"ta ƙarasa maganar a yayin da take ƙoƙarin sauka daga saman gadon.


Fitowa tayi daga cikin ɗakin ta nufi kitchen,azmee ta samu acikin kitchen tana aikace aikacenta,

"Assalamu Alaikum,"sehrish ce tayi sallamar a yayin da take shiga daga cikin kitchen ɗin,

Juyowa azmee tayi fuskarta asake tace"Mutanen kano,An tashi lafiya'?

  "Lafiya lou Aunty azmee,Nayi missing ɗinki sosai,"

  Azmee tace"i missed u too,jiya naso mu haɗu dake,In tayaki murnar ganin Oummanku,Amma bansamu halin yin hakan ba,"

  "Nima jiya naso nazo ɗakinki mu gaisa Amma gajiya ta hana,"acewar Sehrish,

  "Ae na ganki da asuba,kinso ki tsoratar dani Allah,sam Ni banyi tsammanin akwai mutun a kwance  gefena ba,Ashe ke ce,"

  Dariya Sehrish ta ɗanyi kafin tace"Oh,aunty Azmee ashe kema kina da tsoro kamar ni,"

   "Ni ba mutun bace"ta ɗanyi maganar tana hararar sehrish 

   Murmushi kawai tayi batare da tace komai ba 

  Takowa azmee tayi izuwa kusa da ita,hannunta ta ruƙo cikinta 

  "Sehrish,kinji abunda ya faru ko"?

Cikin sanyin murya tace"Eh,jahad ta sanar dani komai,dangane da garkuwar da akayi dasu,nasha kuka sosai na gode wa Allah,Fatana shine Allah ya bayyanar da Junaid,"tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla,

   "Wlh aunty azmee na karaya sosai,jikina yayi mugun yin sanyi,Allah sarki Junaid,bawan Allah,Yaso ni sosai,Ya bani kyakkyawar kulawa,"

   Gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi,

"Sehrish akwai abunda na manta ban sanar dake ba,koda yake junaid ne Ya hana in faɗa maki tun lokacin bayaa yanzu tunda baya nan inaso na sanar dake,"

   "Menene aunty azmee"tayi maganar yayin da take kallonta,

   'A lokacin baya,farko farkon zuwanki gidan nan,Zaki iya tuna ranar da kikayi Ciwon ciki mai tsanani?har kika sanar dani cewa Aljani ne yazo maki a daren ranar"?

.shiru sehrish ta ɗanyi tana ƙoƙarin tunawa da ranar,Can tace"Na tuna,"

  Ajiyar zuciya azmee ta sauke kafin ta ɗaura da cewa"JUNAID NE ba Aljani ba!Sehrish shi ne ya taimake ki a wannan ranar,Ya sanar dani komai,kuma tun a lokacin yake ta ɗawainiya da sonki acikin zuciyarshi,"

  Fashewa sehrish tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,Cikin shessheƙar kuka tace"Dama junaid ne aunty azmee,Wayyo Allah na,Meyasa tuntuni baki sanar dani ba?meyasa aunty azmee!

  Hawaye ne ke shararowa akan fuskar Azmee,

  "Shiya ce karna faɗa maki Sehrish,saboda yana tsoron kiji haushinshi,Saboda ya gane cewa ke maca ce,After that,Sehrish junaid Shi ne ya siya maki wannan wayar taki ta farko,Tecno Camon 18,Wayarshi sabuwa ya mallaka maki ita,Bayan haka kuma Shi ne Silar da aka sanyaki Makarantar Boko,da kuɗinshi kuma,Wanda babban yayansu ya bashi don yayi Celebrating birthday ɗinshi,Amma ya fasa yin murnar ranar haihuwarshi Duk don saboda Ke!Na faɗa maki ne saboda in sauke nauyin dake akaina,"

Gaba ɗaya jikin Sehrish ya gama mutuwa,Kasa motsawa tayi daga tsayen da take,Ta ƙame kamar gunki,yayin da hawaye ke ta wanke mata fuskarta,masu ɗumi wasu nabin wasu,kamar wadda aka zarewa lakar jikinta,Ta rasa duk wani ƙarfi na jikinta,Abun da Ciwo acan ƙasan Zuciya,raɗaɗinshi yafi na zafin wuta,


Hannu tasa tare da dafe saitin Zuciyarta,ji take tamkar zata 6allo daga ƙirjinta,


Dafa shoulders ɗinta Azmee tayi tare da cewa"Sehrish!meya faru naga duk kin Canza?ban faɗa maki hakan ba don na tashi hankalinki,Na Sauke nauyin dake akaina ne,Junaid addu'armu yake buƙata Allah ya bayyanar dashi,Ni sai ma nake ji araina kamar bazai dawo ba,"

  Sai lokacin Sehrish taja dogon numfashi,daƙyar ta iya ɗaga ƙafarta tana tafiya,Ta fuce daga cikin kitchen ɗin,Har lokacin babu kowa a falon duk basu fito ba,kewar junaid duk ta baibayeta,tsananin sonshi ne ya kamata,komai ya fita ranta a yanzu junaid kawai take son gani a yanzu,Gashi ya tafi ya barta,Tafiya ta har ABADA,


  Garden ɗin gidan ta shiga,slowly take tafiya saman korayen Ciyayin dake aƙasan wurin,bakomai take tunawa ba,Fa ce irin rayuwar da sukayi da junaid,musamman ranar da suka fara haɗuwa a garden,Ranar da yazo zai bayyana mata kanshi amatsayin mutun na farko daya gane cewa ita maca ce,harya sanya hannu yana cire mata gashin bakinta,da kuma ranar da suka shirya zasu haɗu dashi a garden har yayi ta zaman jiranta bata fito ba,har dare Yayi akayi ta nemanshi acikin gida,

  Duk duniya bata da masoyi daya wuce junaid,kifa kanta tayi asaman table ɗin gabanta,Sosai ta fashe da kuka mai cin rai,taso ace tuntuni junaid ya bayyana mata soyayyarshi da babu abunda zai hana ta aure shi,

...tashin sense......



Mu haɗu on monday✍️


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 *ASLM GANI FA NA SAKE DANNOWA DA SABBIN KAYA MASU SABON SALO*💃🏻💃🏻💃🏻


*takuce mmn Yusuf Dr mata mai gyaran mata ciki da wake*💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻


Ina uwargida da Amarya ina masu shirin yin aure budare da zawarawa , ina masu son su zama taurari ✨🌟ababen alfaharin mazajensu , ina mata masu kishiyoyi da ake ci masu zarafi ake wulakantasu akan kishiyoyin su ina wacce keshan wulakancin namiji , ina matan da sukeson burge mazajensu da zallan ni'ima da dandano ??? Ina matan fake fama da rashin ni'ima , budewar gaba wadan da suka faru sanadin ciyon sanyi kokuma haihuwa , ko wadda Ke fama da k'arancin ni'ima da karancin sha'awa , ??  To saurara kiji✋🏻✋🏻✋🏻


Ko kinsan Maman Yusuf Dr mata kuwa ?? Hmmm akace in bakasan gari ba to ka saurari daka,💃🏻💃🏻

*Namu na dabanne kamar yadda salonmu yake daban ingantattun kaya ne da basuda wata illa ajiki sannan ba boka ba malam zaki mallaki mijinki da dandanonki sai yadda kikayi dashi*


Duk abunda kk so a bangaren kayan mata zaki samu hajiyata daga gyaran ciki harma Dana waje 


Munada ingantaccen maganin sanyi na maza Dana mata hakama maganin Basir 


Maganin nono Dana hips 

Maganin kiba dakuma maganin rage tumbi da kibar, 

Maganin gashi 

Maganin hawan jini

Maganin sugar


Sabulun wanka na gyaran jiki

Sabulun dilka na amare

Dilkar amare


Kwallin mallaka (daga ni sai kai)

Maltinar mata

Bobintan mata

Set na lalata gindin kiahiya

Set na ukku bala'i

Set na rantse bakida kishiya,


Kalolin gumba

Kalolin gari

Kalolin matsi

Kalolin sabulan tsarki

Zumar mata

Zumar ridi 

Zumar goron tula

Tsumin mallaka

Tsumin jaraba

Tsumin sabon budurci

Tsumin kankana

Tsumin tabaje

Tsumin makalemata 

Shayin mata 

Sirrikan mallaka

Dan goshi da mahadinshi 

Dan goshi na Mara

Kyallen al'ajabu

Rakumi da akala

Bita zai zai

Dahuwar kalolin kaza zabo zakara 

Dahuwar zuciya

Dahuwar ciccibi

Dahuwar zuciya

Dambun nama

Dahuwar yan shila

Yajin mata 

Yajin maza domin Karin karfi



*Hmmmmmm in nace sai na lissafamuku zafafan kayan nan sai in wuni ina typing shawara daya zan baki uwargida in har baki jaraba kayan mmn Yusuf ba to ki garzaya ki saya da kanki zakizo kina godiya , 😉😉😉😉😉😍 wadan da suka San ya kayan suke kuwa. Basa bukatar wani Karin bayani , 

Domin Neman Karin bayani kokuma ganin kayan da nake dasu Ku tuntubeni ta wannan number 07069711327 call or WhatsApp mmn Yusuf mai kayan mata🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰


Ina bada sari ina sokoto ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah , 

Don Allah in baki shirya siyaba to kibari sai kin shirya sai muyi magana🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 07069711327

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




💋💋💋





Kwance yake asaman doguwar sofa mai mazaunin mutun ukku,da alama bacci ne ya ɗauke shi,daga shi sai gajeran wando ajikinshi,


Sautin bugun ƙopar falon ne ya farkar dashi daga baccin da yake yi,tun kafin ya buɗe idanuwanshi yace"Who is Knocking!"

  From ouside the door yaji an ce"Afternoon sir!Kunyi bakuwa ne tana a waje tana jira,"

  "Ka sanar da ita cewa Matar gidan bata nan,"har lokacin bai buɗe idanuwanshi ba,


Jim kaɗan har ya koma baccin nashi,Yaji an sake kwankwasa ƙopar,rai a6ace yace"Sergeant!"

  "Am Sorry sir,matar ta nace akan tana son yin magana da matarka Laila,"

  Guntun tsoki General Ishaq yaja kafin yace"Let her Come in,"


"Okey,Sir,"


A ƙule yake dama sam ƙawayen Laila ba burgeshi suke yi ba,duk yawancinsu irinta ne,masu mugun hali,'


Kwankwasa kopar yaji anyi,muryarshi a kasalance yace"Who is knocking"

  "Hajiya Rabi'atu ce,ƙawar Laila,"har cikin dodon kunnanshi ya jiyo daddaɗar muryarta,sai gashi ya buɗe idanuwanshi,Saukowa yayi daga saman Sofa ɗin da sauri ya nufi bedroom ɗinshi dake a upstairs,Jim kaɗan yadawo jikinshi sanye da Jallabiya,


Hannu yasa tare da buɗe mata ƙopar,tun kafin ma ya kalleta,Wani irin daddaɗan ƙamshin turare mai ratsa sassan jiki da sanyaya zuciya ya daki hancinshi,from down ya soma kallonta,Highhills ne a ƙafarta,Jikinta kuma na sanye da Code lace milk colour riga bubuce ajikinta,ta aza mayafin asaman kafaɗarta,duka hannayenta da wuyanta na sanye da sarƙar gold,light make up ne akan fuskarta


Koda General Ishaq,ya yi arba da kyakkyawar fuskarta,farat ɗaya ya waye ta,

  da niyyar rashin mutunci ya buɗe ƙopar,Amma sai gashi yana sakar mata murmushi,A wayance yace"Hajjaju ko"?

  Mayar mashi da martanin murmusin tayi tare da ɗaga mashi kai alamar eh,

  "Ina fata ban takura maka ba,dama na shigo garin naku ne,Shi ne nace bari na leƙo mu gaisa da ƙawar tawa,nata trying layinta amma akashe I don't why,nashiga damuwa,"

  Matsa mata hanya Ishaq yayi"mu shiga daga ciki mana,sai muyi magana"

  "Toh"ta amsa mashi tare da bi ta gefenshi ta nufi cikin palourn,Shima yabi bayanta,Sai ƙara bin ta da kallo yake yi,from head to toe,wankan lace ɗin da ta ɗauka ba ƙaramin tafiya yayi dashi ba,musamman da ta kasance dirarrar mace,


Wuri ta samu saman 2 seater ta zauna,Ishaq ya zauna saman 3 seater,

A tsanake ta soma magana bayan sun gaisa"Am Lailan tana ciki ne"?

  "A'a,bata nan fa,bata sanar dake bane"?

  "No Bata sanar dani komai ba,ai na faɗa maka ina ta trying layinta a kashe,"magana takeyi tamkar bata son motsa la66anta,dama hajjaju anji wayewa,ishaq kuwa sai ƙara kalleta yake yi,

   "bazan 6oye maki ba,Zancen gaskiya mun rabu da laila,Ni banma son inda take ba ayanzu ha...."bai ƙarasa maganar ba ganin yadda ta zabura ta miƙe tsaye tana faɗin"ka rabu da laila"?

Murmushi Ishaq ya ɗan yi kafin yace"Calm down ur mind,koma ki zauna,"

  Muryarta tamkar zatayi kuka tace'haba Ishaq,taya zaka ce mun in zauna?zaman me zan yi kuma,bayan ka rabu da laila!amma gaskiya banji daɗin wannan maganar ba,"

  Zuba mata ido yayi yana kallonta,sai da ta kai ƙarshen maganarta,sannan yace"pls ki koma ki zauna,I will explain to you,"

  Fuskarta aɗaure ta koma ta zauna tare da cewa'wlh Ishaq ka bani mamaki,sam ni baka yi mun kama da irin mazan dake sakin matansu ba,meyasa zaka yiwa laila haka?idan ma laifi tayi maka,at least kodan saboda Hafsat ai bai kamata ka rabu da ita ba"

..shiru ya ɗan yi batare da yace komai ba,har sai da ta hasala,ta soma ƙoƙarin miƙewa"Ni zan wuce,dama saboda Laila nazo,tun da kayi mana tsiyar taku ta maza,banga amfanin zama na ba,"

  "Pls kada ki tafi,i will explain to u as i said,"Yanayin yadda ya furta maganar kamar akwai damuwa atattare dashi,hakan yasa ta gyara zamanta,tare da cewa"ina sauraronka,"

.."Ban cika son ina faɗin sirrikan matata ba,kuma bana ɗaya daga cikin mazajen da suke fallasa sirrin dake tsakaninsu da matayensu,so kamar yadda kika ce,banyi maki kama da mazajen da suke sakin matayensu ba,inaso ki ci gaba da yi mun wannan kyakkyawon zaton,Sam ni a tsari na babu sakin mace,kuma ke shaidace!kinsan wacece laila,kinsan halinta,bakowani namiji bane zai iya jure zama da mace irinta ba,amma haka ni na daure na rufe idona na zauna da ita,bayan duk irin Girman laifukan da take yi mun,Laila ta kaini maƙura ne,shiyasa har na zartar mata hukuncin saki........"Anan Ishaq ya kwashe dukkan Abunda ya faru tsakaninshi da laila game da irin Zaluncin da ta yiwa ƴa'ƴan Uncle ɗinshi ya sanar mata,

  Saboda tsabar tashin hankali,Hajjaju ta shiga zabga salati tana faɗi "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Dama su Sehrish ƴa'ƴan Abusufyan ne?"

  Cike da mamaki Ishaq yace"Dama kin sansu ne"?

  "Nasan su mana,Ae ni ce silar tura ita Sehrish din aikatau a anan gidanku,Ashe dama jininku ne su?Ya salaaam,"ta ƙarasa maganar tana dafe kanta da hannunta ɗaya,

  "Wlh Nayi danasanin rashin sanar dakai da ban yi ba,Nazo naga Hosana da Jahad,acikin gidan nan,tunda na kallesu dama nasan cewa suna cikin mawuyacin hali,bayin Allah,"

  "Dama kinsan da zamansu acikin gidan nan?kuma baki sanar damu ba?bayan kinsan halin ƙawartaki"?

  Idanuwanta cike tab da kwalla tace"Wlh banyi dabarar yin hakan ba,Amma ae komai ya wuce,kuma wlh nayi murna nayi farin ciki sosai da kasancewarsu ƴa'ƴan Abusufyan,in sha Allah idan na samu zuwa can abujan zanje na kai masu ziyara,"

Sun jima suna tattaunawa akan su Sehrish,bayan sun kammala firar tasu ne,Hajajju tace"Yanzu,mu dawo kan laila,"da sauri Ishaq ya katse ta da cewa"karfa kice zaki bani shawarar in mayar da ita,"

  Girgiza kai tayi"a'a ni na isa,kawai dai yakamata kayi zurfin tunani,banso ka yanke mata hukuncin saki ba,ka jima tare da laila,kodan albarkacin hafsat bai kamata ka rabu da ita,Ya kakeso rayuwar hafsat ta kasance babu uwa atare da ita"?tayi maganar tana kallonshi,

  "Hajjaju kenan!hafsat ba ƙaramar yarinya bace,ta mallaki hankalinta,ba zata yi maraicin uwa ba,zan iya sawa ayi mata transfer ta koma Abuja da aiki,in yaso sai ta zauna a wurinsu Abba,"

  

"Kai kuma fa?ba zakayi maraicin rashin mace atare dakai ba?nasan dole ka buƙaci kulawa,gashi gidan ma ko mai aiki babu,"tayi maganar tana ƙarewa gidan kallo,

  Wani ƙayataccen murmushi Ishaq ya saki,anzo wurin da ya fi so,

   Jingina bayanshi yayi ajikin sofa ɗin tare da cewa"kin faɗi gaskiya,ina buƙatar mace atare dani,musamman wadda ta iya ɗaukar wankan lace,ta iya kashe ɗaurin kallabi,Sai dai ina jin tsoran na sake yin aure,saboda matan ne basu da tabbas,"

   "Ba duka aka taru aka zama ɗaya ba,kada ka yanke hukunci akan abunda baka da masaniya akanshi,Dole akwai na gari kuma akwai na banza,shiyasa kafin mutun yayi aure yake da kyau ya tsananta bincike,Don ya sama ma ƴa'ƴanshi uwa ta gari,haka mu ma matan,"

  Sam bata kawo komai aranta ba,tana kai ƙarshen maganar ta ɗauki hand bag ɗinta tare da mikewa"Ni zan wuce,"bata jira amsarshi ba,ta nufi hanyar fita daga falon,

  Da sauri Ishaq ya miƙe tare da yin hazarin shan gabanta,ba arziki ta tsaya tana kallonshi,

   Marairaice mata fuska yayi"pls Kada kiyi mun haka mana,nasan kin fahimci abunda nake nufi,koda ban fito na bayyana maki ba,"ya ɗan daka da yin maganar yana jiran amsarta,

  "Sauri nake yi,dan Allah ka bani hanya na wuce,ae kasan alaƙata da laila,So bai kamata kayi mun wannan maganar ba,"

  "Ita laila ɗin ciki ɗaya kuka fito da ita ne"?yayi maganar tare da tamke fuskarshi,

  Girgiza kai tayi alamar a'a,

  "Ko akwai wani hadisi ko aya daya haramta wa namiji ya auri ƙawar matarshi"?

  Nan ma ta sake girgiza mashi kai"ko ɗaya babu,Amma ae ana barin halas ko dan kunya,Ishaq idan ma da wannan manufar kazo mun,Ni bazan iya aurenka ba gaskiya,ba wai don ka ta6a auren ƙawata bane,No kawai bana ra'ayin ƙara kasancewa da wani ɗa namiji ne,"

  "Koda ace ni ne"?yayi tambayar fuskarshi da alamun damuwa,shiru tayi bata tanka mashi ba,a qagare take ma daya bata hanya ta wuce,

    Cikin sanyin murya yaci gaba da cewa"Na jima da dakon sonki acikin zuciyata,Yanzu ne nasamu ƙwarin guiwar sanar dake,ko alokacin baya nayi kawaici ne kawai don saboda nasan bazaki amince da soyayyata ba,Saboda Ƙawanccan dake tsakaninki da laila,Amma yanzu babu Laila,meyasa zaki haramtawa kanki ƙara yin aure ne?nafa san komai agame da rayuwarki,lokacin da mijinki yayi hatsarin mota tare da ɗanki,hada ni cikin waɗanda suka halarci jana'izarsu,Nasan abun dole ya ta6a maki zuciya sosai,Amma Ya zakiyi?mutuwa ce kuma tana akan kowa...."

  Tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,cikin shessheƙar kuka tace"Dan Allah ka bani hanya na wuce"daƙyar sautin maganarta ke fita,

  "Zan baki hanya ki wuce,Amma kafin nan ki tsaya ki saurari maganata,kina buƙatar wanda zai maye maki gurbin mijinki,kuma ni ashirye nake dana zama madadinshi,zan baki kyakkyawar kulawa in har kika amince kika aure ni,ke kinsan wanene ni basai na faɗa maki ba,bazan yabi kaina ba,Amma nasan kinsan komai a wurin ƙawarki laila,kuma nima a wurinta nake jin labarinki,"

  Natsuwa tayi tana sauraran kalamanshi,yayin da take ta wasi wasi acikin zuciyarta,

  "Daga ni har ke,babu yaro acikinmu dukkanninmu mun mallaki hankalinmu,Ki amince kawai nasan ba zaki rasa manema ba,Ni late comer ne,Amma da shiri na nazo bada wasa ba,inaso na haɗa zuri'a dake,Yaronki da kika rasa,Zaki samu madadinshi atare dani....."bazata iya jure sauraron kalaman Ishaq ba,da sauri tabi ta gefenshi da gudu ta buɗe kopar falon ta fuce tana kuka,Ya fama mata tsohon ciwon daya daɗe acikin Zuciyarta,


Jiki asanyaye Ishaq ya koma saman sofa ya zauna tamkar ya fashe da kuka haka yake ji,bai yi tunanin zata ƙi amince mashi ba,gashi tunda yayi arba da ita ya rasa natsuwarshi,


   *Marshal Omar*


Abun ya ɗaure mashi kai!tunda ya shigo bedroom ɗinshi ya same shi kwance yana ta sharar bacci,Yaushe rabon daya ga Sgr yana bacci irin wannan,tun kafin mutuwar Junaid,wuri ya samu gefen gadon ya zauna yana ƙare mashi kallo,Har cikin ranshi ba ƙaramin daɗi yaji ba daya samu Sgr yana bacci,da alama tun da yadawo daga sallar Asuba yake kwance yana bacci,don bai cire jallabiyar jikinshi ba,


Zuba mashi ido omar yayi yana kallonshi,yayi hugging ɗin pillow sosai a ƙirjinshi,kasa tashin shi daga baccin Omar yayi,don bazai so ya katse shi ba tunda an samu baccin ya ɗaukeshi,don yafi kowa shiga matsananciyar damuwa akan rashin Junaid,da kuma Alƙawarin da sukayi ma mahaifinsu,


Motsi ya soma yi da la66ansa da alama mafarki yake yi,matsawa Omar yayi kusa dashi ya kasa kunne don yaji me yake cewa,Sambatu ne yake yi yana ambaton sunan Reesh,abun ya ɗaure mashi kai,instead yaji yana sambatu akan Halin da suke ciki kaman yadda yai tunani amma sai yaji yana ambaton sunan reesh,Wai ma sunan menene reesh ɗin nan?ya tambayi kanshi tare da kallon sama yana ƙokarin tunano inda yasan sunan,

  Sai da yayi zurfin tunani sannan ya gane cewa sunan Sehrish ne ya maida reesh,

  Ƙayataccen murmushi Omar ya saki,aranshi yace"shegen bisa na,Allah ya toni asirinka,Allah kadai yasan me ya aikata ma ƴar mutane jiya da har yake sambatu akanta,Haba no wonder!ba banza ba yake ta sharar bacci,mutumin da saboda tsabar tashin hankalin da muke ciki ko runtsawa baiyi amma yau gashi ya baje yayi ɗai dai saman gado yana ta bacci,"


Motsi Sgr ya fara yi alamar zai farka,slowly ya ɗan ware blue eyes ɗinshi ceiling ya fara kallo na wani lokaci,kafin ya wurga idonshi kan Omar daya ƙura mashi ido yana ta faman sakin murmushi,

  Muryarshi da alamun bacci bai ishe shi ba yace"Bro,yaushe ka shigo?

  "Ban jima da shigowa ba,nazo na taras da abun farin ciki,Na same ka kana ta sharar bacci,hankalinka kwance kamar kana cikin jirgi mai ya ƙare,"

  yatsina fuska Sgr yayi batare daya ce komai ba,

  "Ka gama shan ƙamshin naka,Nasan komai,babu abunda zaka 6oye mun,"cike da zolaya Omar yayi maganar,

  "What are u talking about"?Sgr ya tambaya fuska a ɗaure yana kallonshi,

   Murmushi Omar ya saki tare da kashe mashi ido ɗaya irin na ƴan duniyan nan,

   "Tell me,Wacece reesh da naji kana faɗi acikin baccinka"?

  A hasale Sgr yace"bansani ba,Omar yaushe ka fara sa ido,"

  Dariya Omar yayi tare da cewa"basa ido bane,its just a question pls ka faɗamun sunan wa naji kana faɗi acikin baccinka,"

  Harararshi Sgr yayi"I don't know,"

"Kada kayi tunanin zaka 6oye mun wani abu,saboda alamu sun bayyana ajikinka,"

  Jin haka yasa Sgr yayi saurin kai hannunshi saman short ɗin jikinshi,

  A ƙule ya furta"And then so what Omar!,Yau ka fara gani ne"?a fadace yake magana,dama ance wai da bori ake naɗe tabarmar kunya,

  Sosai Omar ya 6a66ake da dariya,daƙyar ya samu ya tsagaita da yin dariyar 

   "I know this is a normal thing,but akan ka ni ban saba gani ba,gaskiya in ma na ta6a gani to na yau dai na musamman ne fa,Kalli fa ka gani,Tayi tsaye ba ladabi ba biyayya....."kasa ƙarasa maganar yayi saboda dariyar da ta ciyoshi,Rai amatuƙar yace Sgr ya miƙe daga zaune tare da kai hannu ya warci pillow ya wurga ma Omar asaman fuskarshi,da sauri Omar ya ruƙo pillown ya janye shi daga fuskarshi yana yi mashi gwalo,

   "May be it needs a second round shiyasa taki relax,ɗan rainin hankali,kayi ta shan ƙamshi wai kai baka buƙatar mace a arayuwarka ko?Yanzun wannan menene? Yayi tambayar cike da tuhuma,

Sgr was speechless,Zuba mashi ido kawai yayi yana kallonshi without saying anything,

   Omar kuwa daɗin zolayar tashi yake ji,

   "Tell me the truth!meya faru jiya da daddare atsakaninka da ita"? cizon tausasan la66ansa ya shiga yi yayin da yake kallon Omar,kamar ya shaqe shi Haka yake ji,

   "Tunda bazaka faɗamun ba,Al'qur'an saina faɗama Uncle ince ka fara taushe mashi ɗiyarsa,ni ban ta6a ganin mara kunya irinka ba Allah,nan nan fa ka auri yarinyar nan don tayi maka aiki,ƴan share share da goge,Ashe muka maida shashashu,""


"Is enough Omar!kana so ka 6atamin raina ko?U know why i married her,yarjejeniyace akan zatayi mun aiki,so this is also part of her work," ya ƙarasa maganar tare da saukowa daga saman gadon yana faman hura hanci,

  Dariya sosai Omar keyi,hada kwantawa saman gadon Sgr ɗin,Yau da jan faɗa yazo,

   "Naji abunda kace,Amma pls kaga yarinya ce,Ya kamata ka dinga ɗan riritata,kana tarairayarta kamar new born baby,don nasan halinka Allah,kullum fuska a ɗaure,ita kanta bazata samu sakewa dakai ba,halan ma ƙarfi kake nuna mata?shiyasa har take baka"?

  Dakatawa Sgr yayi daga yin tafiyar da yakeyi,Omar ya ƙule shi a hasale ya juyo yana kallonshi........

  Ɗaga mashi gira ɗaya Omar yayi tare da cewa"what do u think if she becomes pregnant?kaga shikenan Abba zai samu little Junaid,hakan zai ɗebe mashi kewar Babynmu da muka rasa,"

  Har cikin zuciyarshi yaji maganar Omar,shi kanshi Omar da yayi maganar sai da yaji wani iri acikin zuciyarshi,

  Bai dai tanka mashi ba,ya shige cikin toilet tare da turo ƙopar ya rufe,


*Boss Bature*


A 6angaren Sehrish kuwa,bayan ta kammala shan kukan nata,Bacci ne ya ɗauke ta acikin garden ɗin yayin da take zaune asaman garden Chair ɗin,ta aza kanta asaman table ɗin gabanshi,


Kukan tsuntsayen dake shawagi a wurin ne ya farkar da ita,a hankali ta buɗe idanuwanta,tare da miƙewa zaune tana bin tsuntsayen da kallo,jikinta duk ya saki,kewar junaid duk ta baibayeta,daƙyar ta iya miƙewa tsaye ta juya tana tafiya iska na kaɗa sumar kanta,cikin gidan ta koma ta ƙopar da ta fito,ƙopar da idan ka shiga zata kaika direct corridor ɗin dakunansu,


Lokacin da ta ƙaraso bedroom ɗinsu,hannu tasa ta tura ƙopar ta shiga daga ciki,babu kowa da alama sun fita yin breakfast ne,


Rage kayan jikinta tayi,kafin ta shige cikin toilet don tayi wanka,almost 30 mins sannan ta fito daga ciki,jikinta sanye da white underwear ɗinta,gaban wadrobe ta nufa tare da sanya hannu ta buɗe tana neman kayan da zata sanya,


Wata gown ce ta ɗauko,Doguwa Red colour mai bazar net daga ƙasanta,daga sama kuma hannu ɗaya gareta siriri,rigar ta haɗu sosai,sanya rigar tayi ajikinta ta zauna mata sosai tabi shape ɗin jikinta,saukko da gashin kanta tayi ta sanya hannu ta barbazo dashi ya rufe bayanta,gaban mirror ta koma ta zauna da niyyar yin kwalliya amma sai ta shiga tunanin wai ma wa zatayi ma kwalliya?


Tana cikin wannan tunanin wayarta dake ajiye saman gadonsu ta soma ringing,miƙewa tayi jiki ba ƙwari ta ƙarasa tare da ɗaukar wayar,ta duba sunan mai kiran nata,Ajiyar zucia ta sauke tare da picking call ɗin ta kara wayar a kunnanta"Mommyna,kin tashi lafiya,"

  On the other hand Aunty azeema tace"Lafiya lou Daughter Alhamdulillah,Ya kike ya gida!ya jikin Oumman taku?Abba ya sanar dani cewa taji sauƙi,harma kun dawo gida,"

. "eh,jiya muka dawo,"

  "Allah sarki,to Allah ya ƙara mata lafiya,"

Ta amsa mata da Ameen,

  "Inason magana dake ne shiyasa na kira,"jin haka yasa Sehrish ta samu wuri gefen gadonsu ta zauna tare da wayar manne a kunnanta,

  "Mommy ina sauraronki,"

  Hajiya azeema tace"Yawwa,dama inaso naji ya tsakaninki da Rafayet?

  "Shiru sehrish tayi saboda kunyar da take ji,tuntuni taso ta fayyace mata abunda ya fara shiga tsakaninta da Sgr amma kunya ta hanata,

  "Kada kiji kunyar komai,ki ɗauke ni tamkar ƙawarki aminiyarki,inaso ki sanar dani komai,"Acewar hajiya azeema don ta ganota,kunyarta take ji shiyasa tayi shiru bata tanka mata ba,

  Cike da jin kunya Sehrish ta sanar da ita duk wani abu dake wakana atsakaninta dashi,

  Lokacin da ta kai ƙarshen maganar,tana jiyo sautin dariyar hajiya azeema ta cikin wayar,da alama abun ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,sai da tayi mai isarta sannan tace"amma Rafayet baida ta ido,in banda ma baturen mutun,ka auri yarinya don tayi maka aiki,kuma ka 6uge da neman biyan buƙatarka,'

  Sunnar dabkai Sehrish tayi,gani take yi kamar Mommy azeeman tana agabanta ne,

  "Am sorry fa,karki ji inata yi maki dariya,abunne ya sanya ni nishaɗi,kina ji na ko"?

  ɗaga kai sehrish tayi kamar tana agabanta"ina sauraronki Aunty,"

  "Yawwa inaso ki natsu ki saurare ni,nasan kina jin tsoron Sgr sosai,saboda yanayinsa,Yawan ɗaure fuska,rashin fara'a da sauransu,wannan tsoron shi nake so ki cire!

  Ɗan waro ido sehrish tayi hankalinta atashe tace"Aunty,taya zan daina jin shakkarshi"?

  "Na farko dai mutunne kamarki,ba aljani ba,dole sai kin cire kunya idan har kina so kija ra'ayinshi agare ki,har yanzu fa Sgr baisan so ba,sha'awarki kawai yake yi shiyasa ya fara kulaki,koda ace ma yana sonki bazai iya gane hakan ba,har sai kin koyar dashi,"

  "Amma Aunty taya zan iya koyar dashi soyayya"?muryarta sanyaye tayi maganar 

  "Yanzu Sgr ya fara sha'awarki,bazaiyi wasa dake ba,zaki ga canji atattare dashi,zai fara baki kulawa ta musamman kuma zai damu dake,ba don komai ba sai don saboda yasan cewa ta wurinki ne kawai zai samu natsuwa aduk lokacin da desire dinshi ta motsa,zai dinga tarairayarki ne yana baki kulawa sosae,ko tari kika yi zai tambayeki lafiya?Sanin cewa in fa baki da ƙoshin lafiya,abun zai shafe shi ne shiyasa zai dinga tambayarki da zarar yaga canji atattare dake,daga yanzu inaso ki lura dakyau ki gano wurin da yafi ra'ayin ta6awa ajikinki,saboda ta hakanne zaki gane lagwansa,sannan a duk lokacin da zaki je part ɗinshi,ki dinga ɗaukar wanka kuma kada ki dinga sanya manyan kaya irin atampa ko shadda wannan sai za'aje unguwa,ko cikin gida,ki dinga sanya kayan da zasu bayyana surar jikinki,Yadda zai dinga ganin komai Zahiran har ya gaza samun kwanciyar hankali,amma fa idan zaki sanya kalar wannan kayan ki tabbatar da kin sanya hijab ajikinki saboda akwai maza agidan,daga baya idan kinje part ɗinshi sai ki cire kina jina ko"?

  "Eh,"ta amsa mata,

"Yawwa,nasan dai basai na ƙara tunasar dake ba,game da tsafta duk kina yin wannan,Amma shagwa6a fa kin ta6a jaraba yi mashi...."tunkan ta ƙarasa maganar,Sehrish ta 6a66ake da dariya,

  Hajiya azeema tace"Allah kuwa,bafa wasa nake yi maki ba,shagwa6a tana ɗaya daga cikin abunda ke jan hankalin ɗa namiji zuwa ga mace,da kuma salon magana,da tafiya,da sauransu,"

  "Aunty azeema shagwa6a fa kika ce,babban yaya zan yiwa shagwa6a aikuwa da rabon insha Mari,"daƙyar ta ƙarasa maganar saboda dariyar data zo mata,

  Itama azeema dariyar take yi,sai da suka tsagaita da yin dariyar tukunna tace"Don kina jin tsoranshi ne shiyasa kike jin wani banbarakwai,ai ba wani abu bane,ko da yake kufa Majority ɗinku kunya ke hanaku nunawa miji soyayya,ba zaku iya sakin jiki ku nuna ma miji Soyayya ba,ga kuma girman kai,duk da nasan ke baki da wannam girman kan,kunyar dai ce kawai da kuma tsoro,'

  Murmushi kawai Sehrish keyi tana sauraronta,aranta kuwa tana aayyana abunda zai faru idan tayi kuskuren yi ma Sgr shagwa6a,

   "Ki ƙaddara cewa,Sgr jinjiri ne aka baki shi don ki kula da rayuwarshi,komai kece zaki koya mashi,kamar soyayya da bai iyaba zaki iya koya Mashi,duk abunda kika saba mashi,to shima ko bai iyaba zai fara kwatanta yi maki ne,"sosai Aunty azeema ta shiga koyar da ita,Yadda zata jawo hankalin Sgr,suna cikin magana ta wurga idonta kan Wall Clock,sam ta manta bata kai mashi breakfast ɗinshi ba,"

  Aruɗe tace"Aunty azeema,na manta ban kai mashi breakfast ɗinshi ba"

  "Okey,ki kwantar da hankalinki pls,Zamuyi Magana anjima,"

. sallama Su kayi da ita,jiki na rawa Sehrish ta koma gaban mirror,janbaki ta ɗauko red colour ta murza ma la66anta suka ciza sosai,turarenta ta ɗauka ta feshe jikinta dashi,

  Komawa tayi gaban wardrobe ta ɗauko babban mayafi ta lullu6e jikinta dashi tun daga saman kanta,


High heels ta sanya a ƙafarta launin rigar jikinta,ƙarasawa tayi tare da buɗe ƙopar ɗakin ta fito,tun kafin ta ƙarasa fitowa daga cikin corridor ɗin ta soma jin sautin ƙarar Cokula,alamar abinci suke ci,


Kamar karta fito haka ta dinga ji,batasan taya zata nufi part ɗinshi ba,ga mutane a dining area kuma dole ne in zata gifta sai sun ganta har ma su nemi jin ba'asin rashin fitowarta cin abincin,


Daƙyar ta ɗaure,ta nufi dining ɗin kaitsaye,tun kafin ta isa sautin takalmanta yaja hankalinsu,gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta

  "Daugher!dama idonki biyu?amma shi ne baki fito kin ci abinci ba"?Abusufyan ne yayi maganar,

  "Ni nayi tunanin ma ko bacci takeyi shiyasa banyi magana ba,"acewar Abba,wanda ya tasa plate ɗin abinci agabanshi sam ya kasa cin abinci,har yanzu kewar junaid ke ɗawainiya dashi,

  "Ina kwananku,"ta gaisar dasu cikin girmamawa atare suka amsa mata,

  Duka matasan gidan nan suka hallara,dogon table ɗin mai mazaunin mutun 12,anan Abbansu yake tare da Mommynsu,Fawan,Irfan, Jabeer,Khaleed,sai kanal Yousouf tare dasu Talal,Najeeb da twins,


Ɗayan table ɗin kuma mai mazaunin mutun 6,Oummansu ce tare da Abusufyan sai su Jahad da Hosana,idan ka kalli fuskokin matasan gidan sai sun baka tausayi,don kuwa kamar anyi masu dole don suci abinci,musamman fawan jujjuya cokalin hannunshi kawai yake yi,har yau ya hana kanshi jin daɗi duk don saboda Junaid,


"Samu wuri ki zauna mana"Mommynsu Junaid ce tayi mata magana ganin ta tsaya atsaye kiƙam,

  Sunkuyar da kanta ƙasa tayi,tana wasa da yatsun hannunta sam taƙi motsawa,

  "Ki zauna mana baki ji ana magana ba"Abusufyan ne ya tunasar da ita,

  Tafiya ta soma yi zata zagaya ta zauna,

  "Ina azmee take ne?naga yau tunda ta jera abinci,bata fito tayi serving ɗinmu ba kamar yadda ta saba,kodai bata lafiya ne"Abba ne yayi maganar cike da son jin ƙarin bayani daga wurinsu

Abusufyan yace"Nima tun ɗazu na lura bata a wurin nan,yakamata a dubo ta aji ko lafiya,"

"Bari naje na kirata,"Ko sauraron amsarsu batayi ba,dama so take ta gudu daga Dining area ɗin,

  Gudu gudu sauri sauri ta nufi corridor ɗin ɗakinsu,a ƙopar ɗakin azmee ta tsaya tare da sanya hannu ta kwankwasa ƙopar,kusan sau uku tana buga ƙopar,ana ƙarshe ne tajiyo muryar azmee daga cikin ɗakin tana tambayar wanene,

  "Sehrish ce Aunty azmee,su daddy ne ke nemanki,Sun ji shiru shi ne suka ce a kirawo ki,"

  "Okey,gani nan zuwa,bana jin daɗi ne,"

  Tsayawa sehrish tayi a bakin ƙopar ɗakin har saida azmee ta fito jikinta sanye da hijabi,

  "Aunty azmee ya jikin naki"?

Daƙyar ta iya buɗe baki"da sauki,ciwon kai ne,kuma nasha magani,"

  "Allah ya ƙaro sauki Aunty azmee,"ta ƙarasa maganar tare da ruko hannun azmee cikin nata,suka kama hanyar zuwa dining ɗin atare,


Lokacin da suka ƙaraso dining area ɗin,hankalin kowa ya dawo kansu,

"Oumma ga Aunty azmee nan,kallatta ki gani,itace muke baki labarinta jiya mai girka mana abinci"a wani slow abu ta wurga eyeballs ɗinta akan fuskar Azmee,karaf  idanuwansu suka shiga cikin na juna,Zumbur abu ta miƙe tsaye tana kallonta,kallon kamar nasanki,Itama Azmeen kallon Sani take yi mata,

  Ganin sun ƙurawa juna ido,babu mai magana acikinsu,yasa Abusufyan tanka masu"Ko kunsan juna ne"?

  Girgiza kai abu tayi"a'a gani nake yi kamar na santa ne,tayi mun kama da wata dana ta6a sani arayuwata,Amma bazan iya tunawa ba,

  "Aunty azmee kefa?kinsan Oumma ne"?Sehrish ce tayi mata tambayar,girgiza kai azmeen tayi"A'a nima dai kallon sani nake yi mata,kamar na ta6a sanin wata mai irin fuskarta,amma dai ba ita bace ba,sunyi kama ne"

  Murmushi sehrish ta ɗan saki tare da cewa,"tunda baku san juna ba,bari na gabatar da kowannanku,"

  "Aunty Azmee wannan itace Oummanmu,mahaifiyarmu,"

  Sannan ta nuna Azmee"Oumma ga Aunty azmeen da muke baki labarinta jiya,ba iya girki  kaɗai ta iya ba,tana da kyakkyawar zuciya,mutuniyar kirki ce ita,"

  Murmushi abu ta saki tare da miƙa ma azmee hannu suka gaisa da juna,kowa fuskarshi ɗauke da murmushi,


Ajiyar zuciya Sehrish ta sauke,ganin hankalin kowa ya koma kansu yasa tayi saurin lalla6awa ta wuce kitchen,shaf shaf ta shiga haɗa mashi breakfast ɗinshi,


"Sehrish ta faɗamun irin halarcin da kikayi mata,bansan da wasu kalmomi zanyi amfani dasu ba wurin gode maki,Allah ne kaɗai zai iya saka maki"

  Murmushi Azmee tayi"Ae duk yiwa kaine,na dauki sehrish tamkar ƴar cikina,"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar,ta mayar da idonta kan Abusufyan"ina tayaka murna sosai,Allah ya ƙara haɗa kan zuri'arku,"addu'o'i ta shiga yi masu suna amsa mata da Ameen,kafin daga bisani Abba yace"Samu wuri ki zauna,Ke ma Azmee daga yanzu bana so kina wannan tsayuwar,don yanzu kinfi ƙarfin ƴar aiki a wurinmu,pls kada kiyi mun musu kamar yadda kika saba,"

Murmushi Azmee tayi tare da samun wuri a table ɗinsu Abusufyan ta zauna,Abu ma ta zauna,a tsanake kowa yake cin  abincinshi,Abunda zai ɗaure maka kai,ya baka mamaki shine duk bayan ƴan mintina sai abu ta saci kallon Azmee,da alama dai tasanta ne,kuma tana ƙoƙarin tuna wurin da suka ta6a haɗuwa,itama Azmeen satar kallon nata take yi,kowa da abunda yake sakawa aranshi,

Fitowa tayi daga cikin kitchen ɗin hannunta ruƙe da ƙayataccen tray,hannu bibbiyu ta ruƙo shi,cikin sanɗa ta wuce upstairs,direct ta nufi part ɗin Sgr,a bakin ƙopar shiga falon ta tsaya sallama tayi jin shiru ba'a amsa mata ba,yasa ta wuce ciki izuwa bedroom ɗinshi,tana ƙoƙarin shiga,tajiyo maganganunsu shi da Omar,kasa kunne tayi tana sauraronsu,

  "Yanzu ya zamuyi?duk mun jefa kanmu cikin haɗari,idan har Abba yasan cewa ƙaryane ba kidnapping ɗin su Junaid akayi ba daga ranar zai ƙullace mu aranshi,kuma girmanmu zai faɗi agaban ƙannenmu ne,nayi regretting wlh,"Omar ne yayi maganar,a yayin da yake zaune gefen gadon,

  "Omar,nima ina danasanin yin hakan,na shiga damuwa sosai,bansan ya zamu yi ba,remain just one week and some days,daddy tare dasu fawan jiranmu kawai suke yi mu kawo masu Junaid"yayi maganar ne yayin da yake tsaye gaban mirror yana gyara jikinshi dake sanye da Bathrobe,ga danshi danshin ruwa da alama bai jima da fitowa wanka ba,

  Kowanne fuskarshi akwai tarin damuwa,abun ya tsaya masu aransu,

  Jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,

  "Assalamu alaikum,"jin muryarta yasa suka tsagaita da yin firartasu,

   "Who's there"Sgr ne yayi tambayar

  "Sehrish ce,breakfast ne na kawo maka"

  Murmushi Omar ya fara saki,yana kallonshi,harara Sgr ya ɗan wurga mashi,

  Miƙewa Omar din yayi"kar na takura maka,bari na baka wuri,idan Mun haɗu zamuyi magana,"bai tanka mashi ba,Ya nufi hanyar fita daga ɗakin,

  Sehrish na ganinshi tayi saurin gaisar dashi"Ina kwana ya Omar,"

  Fuskarshi ɗauka da fara'a ya amsa mata"Lafiya lou,ina fata kema haka".  

  "Ina lafiya,"daga haka ya matsa mata hanya ta wuce ciki,Shi kuma ya fuce daga ɗakin,


A hankali take tafiya ta cikin mirror yake ƙare mata kallo,A saman table ta ajiye mashi tray ɗin,sannan ta ɗan juya tare da kallon bayanshi,gaisar dashi tayi"Gm ya Rafayet,ka tashi lafiya,"shiru bai amsa mata ba,kamar bashi bane ya gama magana yanzu tare da Omar,


Juyawa tayi saɗaf saɗaf zata bar bedroom ɗin nashi,

  "Where are u going?kin kammala aikin ki ne?"

   "A'a,naga kamar kana shiri ne,Zan jira a falo,idan ka kammala zan shigo daga ciki in yi aikin,"

  A wani slow ya juyo tare da kallonta,adai dai lokacin itama ta waiwayo shi,

   Har sai da gabanta ya faɗi lokacin da idanuwansu suka haɗu cikin na juna,

  Da hannu yayi mata alamar ta dawo,kamar wadda aka zarewa laka,haka ta dawo daga ciki duk tasha jinin jikinta,ƙoƙarin gyara Mashi bedroom ɗin ta shiga yi,kamar daga sama taji ya cire mata mayafin jikinta,da sauri ta juya tana kallonshi

   "Taya zaki ji daɗin yi mun aiki da wannan abun a jikinki"?

  Shiru tayi batace komai ba,Sae ƴan kame kame takeyi,

   Jefa mata shi yayi asaman bayanta,"ki san inda zaki ajiye shi,"

  Ruƙo mayafin tayi tare da ɗaure ɗamararta dashi kamar yadda ta saba yi,mayar da hankalinta tayi wurin gyara mashi gadon,

  Cike da tsantsan sha'awarta yake bin jikinta da kallo,bai ta6a sanin kyawun launin ja ba sai da yayi arba da rigar jikin Sehrish wadda ta kasance Red colour,ga shi hannu ɗaya gareta,Soft skin ɗin bayanta mai matukar jan hankali sai fisgarshi takeyi izuwa gare ta,


Tana cikin gyaran taji motsinshi a bayanta,A firgice ta juya karaf suka haɗa idanu,Zazzare mashi kyawawan idanuwanta ta shiga yi,farare ƙyal dasu masu ɗauke da kwayar ido brown colour,ja da bayan da take ƙoƙarin yi ne yasa ta kusa faɗawa saman gadonshi saboda ta ƙure mashi,da sauri ya cafko Waist ɗinta da hannu ɗaya ya janyota izuwa jikinshi,gaba ɗaya yayi hugging ɗinta so tightly,ta ko'ina ƙamshin turarenta neman yi mashi illa yake yi yana ƙoƙarin Zautar dashi,natsuwa Sehrish tayi yayin da kanta ke kwance luff asaman faffaɗan ƙirjinshi,wannan daddaɗan ƙamshin turaren nashi ne ke dakar hancinta,Gaba ɗaya jikinta ya mace,

  Moving hands ɗinshi yayi tun daga kan Ass ɗinta ya tarboshi,ya jinjina girman hips ɗinta,slowly yayi sama da hannun zuwa cikin sumar kanta,sosai ya shiga murza gashin da yatsun hannunshi,tamkar yana yi mata susa haka ta dinga ji,ga wani irin daɗi mara misaltuwa,almost 5 mins ya rabata da jikinshi,Yayin da idanuwansu ke kallon cikin na juna kamar masu jin bacci,dawo da hannun nashi yayi saman Hips ɗinta tare da  pulling ɗinta ya haɗe gabansu sosai,Ji yake tamkar kawai ya aiwatar da abunda zuciyarshi ke raya mashi,but this is not the right time da yake son wannan abun ya kasance,

"Meyasa baki gaishe ni ba"?da wata irin kasalalliyar murya yayi maganar,

   Muryarta na kerma tace"wlh na gaishe da kai,tunda na shigo,"

   "Haka ake gaisuwa?"?

  Abun nashi ya fara ɗaure mata kai,

   Cigaba da magana yayi"Ni ba haka nake son ana gaishe dani ba,a kowani lokaci idan kika zo part ɗina,lemme teach u.."moving face ɗinshi yayi izuwa gefen fuskarta,Ya manna mata kiss,side by side na fuskarta,slowly ya dawo da sweet lips ɗinshi saman nata soft lips ɗin ya haɗesu wuri guda,kissing ɗinta ya fara yi,da niyyar ya koyar da ita yadda yake son ta dinga gaisar dashi,Boss man ɗin sai gashi ya fara Hawa kan Network,sosai ya matseta ajikinshi,A susuce ya shiga sucking lips ɗinta,Mayar mashi da martani ta shiga yi hakan yasa shi ƙara zaucewa,gaba daya ya sabeta izuwa saman gadonshi ya kwantar da ita,yabi kayansa ya turmushe,Zage zip ɗin rigarta ya fara yi,ƙankame hannunshi tayi saboda bata kaiga fita hayyacinta ba,kuma ta jiyo motsin mutun a falo,a rude yake faɗin"feed me pls,i really need it,"hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,ya zauce gashi wani yana tunkaro ɗakin,

   Girgiza mashi kai ta shiga yi tana faɗin"Akwai mutun a falo,bazan iya ba,"

   "I don't care,just feed me,ƙoƙarin sabule mata rigar jikinta yake yi,don ya samu yasha ko ya kore kishin ruwan da yake ji,don maƙoshin shi a bushe yake,

   "Rafayet"!muryar Abbansu ce ta karaɗe kunnuwansu,jiki na rawa Sehrish ta janye jikinta daga nashi,A hanzarce ta diro daga saman gadon ta faɗa bayan labule ta 6oye,tana faman sauke ajiyar zuciya,

  Kasa amsa mashi kiran nashi yayi numfashin shi na fita da wani irin huci huci,yayi Uban goho asaman gadon,Sumar kanshi duk ta rufe mashi fuskarshi,

  Shigowa cikin bedroom ɗin Abba yayi,yana kallonshi cike da mamaki yace"Rafayet baka da lafiya ne"?

  Daƙyar ya iya motsa lips ɗinshi"Am ok,"

  Ƙarasa shiga cikin ɗakin Abbansu yayi tare da samun wuri ya zauna daga gefen gadon yana ƙare mashi kallo,Yaƙi yadda ya ɗago da kanshi,gudun kada Abbansu ya gano shi,Don kallo guda zai yi mashi ya shaida cewa wani abu ke faruwa,ga janbakin sehrish daya 6ata mashi chest ɗinshi,

   "Rafayet,inason magana da kai game da Junaid,na kasa cin abinci ko isasshen bacci bana samu,Raina yana bani cewa kamar bazai dawo ba,idan har akwai abunda kuke 6oye mun kaida Omar dan Allah ku sanar dani,Don in fidda rai da dawowarshi,"

  Gyara bathrobe ɗin jikinshi yayi,ya ɗaure igiyoyin jikinta,sai da ya fara daidaita natsuwarshi sannan ya miƙe daga zaune ya zuro da ƙafafunshi ƙasa,kallon juna su kayi shi da Abbansu,hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,Ganin hawaye asaman fuskar Abbansu,

  "Daddy,don Allah kadaina zubar da hawayenka,before end of this month,in sha Allah daddy,zan sanar dakai komai,"

  "Har yaushe ne zaku cigaba da samun ran dawowarshi?Idan mutuwa yayi ku sanar dani mana,na fara zargin hakan acikin raina,da ace kidnapping ɗin Junaid akayi dagaske,Even one day bazaku bari yayi ba,batare da kun dawo dashi cikin gidan nan ba,Amma almost 3 Weeks Junaid baya a gidan nan?kullum ƙara samana ran dawowarshi kuke yi"miƙewa yayi daga tsaye jikinshi na kerma ya soma tafiya daƙyar yake iya tafiya,har sai da yakai bakin ƙopar sannan ya dakata da yin maganar ya juyo tare da kallonshi har lokacin bai motsa ba daga zaunen da yake,

   Cikin sanyin murya ya Ambaci sunanshi"RAFAYET"

"Na'am Abba,"ya furta hakan yayin da yake kallonshi,jikinshi ya gama yin sanyi,

  "In cigaba da sa ran dawowarshi ne?ko in fidda rai,"shiru Sgr yayi batare daya tanka mashi ba,Nazarin maganar shi ya shiga yi,muddin yace mashi ya fidda rai,to tabbas zai fahimci cewa Junaid ya mutu ne,

  Muryarshi tamkar zai fashe da kuka yace"Am really sorry Abba,dan Allah ka bani time,zan baka amsar tambayarka,Amma ba yanzu ba,akwai wani investigation da nakeyi,Zan sanar dakai komai,"

  Gyaɗa kanshi yayi tare da kama hanya ya fita daga cikin ɗakin,Yana juyo muryarshi yana fadin"Zan cigaba dasa rai,"

  Sun jefa kansu cikin tsaka mai wuya,kifa kanshi yayi A saman mattress ɗin,

  Sehrish dake la6e abayan curtains ɗin sai faman shessheƙar kuka takeyi,tausayinsu ne ya kamata,ta jima tana kuka abayan labulen kafin ta fito tana tafiya izuwa gefen da Sgr yake a kwance,

  Tsayawa tayi tana kallonshi,yatsun hannunshi sae kerma sukeyi kamar wanda sanyi ya kama,

  A hankali ta furta sunanshi"Ya Rafayet,"

  "Pls,Just Leave am not in the mood,"da gudun gaske Sehrish ta kama hanyar fita ɗakin tana kuka,bata ji zafin maganarshi ba,


Yinin ranar ko abinci Sgr baici ba,Yadda takai mashi kayan abinci haka ta kwaso su,bai ta6a koda Coffee ba,


After 5 days,bayan kwana biyar,wanda yayi dai dai da sati uku da kwana Biyu da rasuwar baby Junaid!!!!!saura kwana 5 ya rage masu su bayyanar da Junaid,komai ya gama hargitse masu babu wani sauran kwanciyar hankali da suke dashi,


Wuraren ƙarfe 9 na dare,Suna kwance a ɗakinsu,har lokacin Atare suke kwana da Oummansu,Har ɗaki aka ware mata haɗaɗɗen bedroom amma tace ita tafi son ta kwana tare da ƴa'ƴanta,Su uku ne saman gadon suna bacci,Oummansu tare dasu Hosana da Jahad,Sae faman sharar bacci suke yi,

  Sehrish kuwa sam ta gaza runtsawa,ta sanya damuwa sosai aranta,ta ɗaurawa kanta  nauyin alhakin Ƙaryar dasu Ya Omar su kayi ma Abbansu,

  Tana zaune saman sallaya bata jima da kammala yin nafilfilin dare ba,hannayenta ta ɗaga saman tana addu'a,yayin da hawaye ke shararowa akan fuskarta,kusan minti 30 Sehrish bata dakata da yin addu'ar ba,sai da tayi mai isarta aƙarshe ta fashe da matsanancin kuka,da sauri ta sanya tafin hannayenta saman fuskarta ta toshe bakinta gudun kada sautin kukanta ya tashi su Oummansu,

A saman dardumar ta kwanta,tana ci gaba da yin kukan,taso ace zata iya taimaka masu sai dai babu halin yin hakan,tafi damuwa da Sgr don tun ranar da Abbansu ya ƙara tunasar dashi akan Junaid,ita shaidace bai ƙara cin abinci ba,Sai dai lemu da yake sha,babu bacci a idanuwanshi,kullum babu lafiya ajikinshi,duk yabi ya hargitse,


A cikin wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita,

    _Sae da suka kammala hoton sannan ta lura da zoben diamond ɗin dake hannunshi,sae faman ƙyalli yake yi_

_Waro ido waje tayi alamar mamaki tace"wow junaid wannan fa,waya siya maka shi_

  _Mommy azeema ce ta bani shi,dama ɗazu na sanar dake cewa zan nuna maki gift din da takawo mun,to itace wannan_

  _Ya ƙarasa maganar yana nuna mata zoben da Wrist watch din_

  _Junaid sunyi kyau wlh,musamman daya kasance kaine ka sanyasu_

   _Thank u reesh,sunyi mun kyau amman idan ke kika sanyasu sae sun fi yi maki kyau,bari na ciro maki su ki sanya,nafison su kasance a hannunki_

  _cikin sauri tace mashi"no junaid that's impossible,Auntynku azeema ce ta baka shi,muddin ta neme shi a hannunka bata ganshi ba zata nemi jin ba'asin inda ka kai su,kuma ma in banda abun ka junaid wannan ae irin naku ne!kamar diamond ne fa,nida ko zoben azurfa ban ta6a sanyawa a hannu ba,balle diamond_


A firgice Sehrish ta farka daga baccin da ya dauketa,mafarkin da tayi yayi matukar ɗaure mata kai,Zurfin tunani ta shiga lokacin guda ta gane wannan zoben da Junaid ya ta6a nuna mata Shi ne tagani a ɗakin Aunty azmee kamanninsu ɗaya Sak!tabbas kuwa shi ne na Diamond wanda Aunty azeema ta siya mashi mai harafin *j*


Wata irin zufa ce ta shiga gangaro mata agafe da gefen fuskarta,tunani ta soma yi mai yakai zoben Junaid a dakin Aunty azmee?Yakai mata ajiya ne,?sam bata kawo komai aranta ba,Amma tunawa da tayi cewa junaid duk inda zaije zoben nan na ahannunshi wannan yasa ta fara kokonton wani abu,Zumbur ta miƙe daga saman sallayar ta nufi saman gadonsu,


Lalla6awa tayi ta haye saman gadon,saitin wurin da Jahad take a kwance,hannu tasa tana ɗan bubbugata yayin da take ambaton sunanta a Hankali don kada ta tashi Oummansu,

  "Jahad!jahad!"can cikin bacci jahad tajiyo muryarta,dakyar ta iya buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,ganin Sehrish yasa ta dan mike daga zaune"lafiya rishi?dama baki yi bacci ba?"

  "Jahad duk ba wannan ba,wata tambayace nakeso nayi maki,A ranar da kuka fita tare da Junaid shan ice cream shin kin kula akwai agogon diamond da ring a hannunshi ko babu"?

  'Meyasa kikayi mun wannan tambayar Sehrish!So kike ki tayarmun da hankalina?Kinsan fa banaso ana tunamun mutuwar Junaid,"tayi maganar hawaye na zuba akan fuskarta 

  Arude Sehrish tace"dan Allah ki sassauta muryarki Jahad,bana so kowa yaji,nasan baki so amma dan Allah ki yi hakuri ki amsa mun tambayata,"

  Shiru Jahad ta ɗan yi da alama ta shiga zurfin tunani,kusan minti 5 kafin tace"Kamar naso naga zoben a hannunshi,Amma bazan iya tunawa ba gaskiya"

  "Ko hoto baku ɗauka tare dashi ba"?

  Rai aɗan 6ace Jahad tace"haba Sehrish sai kace wata ƴar jarida,irin waɗannan tambayoyi haka?

  "Nidai ki amsa mun tambayata,"a kule tayi maganar,

  Ganin ranta ya 6aci yasa Jahad cewa"Am Sorry,munyi hoto da junaid,hada ma videos muka ɗauka,Amma wayar bata a hannuna,Tana a wurin Ya Omar....."tunkan takai ƙarshen maganar Sehrish ta fuce daga cikin ɗakin a fujajen.

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*





Abun ya ɗaurewa Jahad kai,irin wannan tambayoyi haka,Anya ba aljanu bane suka shige ta ba,


Babu kowa a babban falon,ko tsoro bata ji haka ta nufi Upstairs,gudu gudu sauri sauri take tattaka staircases ɗin,kaitsaye ta wuce bedroom ɗin Marshal Omar,sallama tayi jin anyi shiru ba'a amsa mata ba,Yasa ta fada cikin falon nashi,babu kowa a falon,da sauri ta nufi bedroom ɗinshi,a bakin kopar ta tsaya tare da Leƙawa cikin ɗakin nashi,A kwance ta same shi yana ta bacci,Ajiyar zuciya ta sauke,Cikin sanɗa ta shiga cikin ɗakin nashi,saɗaf saɗaf ta nufi side drawer dinshi dake a righ hand na gadon,Zuƙunnawa tayi agaban drawer chest din,Ta sanya hannu tana bubbuɗesu a hankali,tare da bincikawa ko zata ga wayar jahad,babu ita aciki,a hasale ta miƙe ta nufi wardrobe din kayan shi,gaba daya duk ta hargitsa kayan amma bata ga wayar ba,tsayawa tayi a tsanake ta shirya mashi kayanshi yadda suke,Bayan ta kammala jiki asanyaye ta nufi hanyar fita daga ɗakin dakatawa ta yi da yin tafiyar,Waiwayowa tayi tana kallon cikon ɗakin,tunani take yi kamar akwai wurin da bata duba ba,can ta tuna da Drawer ɗin dake ɗauke da mirror,da sauri ta juya izuwa gaban mirror ɗin,Janyo gida na farko tayi lokaci guda ta sauke ajiyar zuciya,ganin Wayar Jahad ajiye aciki,


Saukowa downstairs tayi,a main palour ɗin ta zauna saman Sofa tare da kunna wayar don akashe take,Allah yaso babu password a wayar,


Direct ta shiga Gallery ɗin wayar,videos ta gani tare da hotunan dasu Jahad sukayi tare da juna,A hanzarce ta shiga kunna videos ɗin ta ƙura ido tana kallonsu,

  Cikin motar Junaid shi da Jahad suka ɗauki video ɗin da take kallo,da hannu ɗaya yake ɗaukarsu video,yayin da dayan hannu ya rungumo jahad ajikinshi yana dariya,yana fadin"With My Juliet,My wife to be in sha Allah"

Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu rass!rass!a zabure ta miƙe tsaye tana kallon yatsun hannun Junaid dake sanye da diamond ring ɗinsa,ya Aza hannu saman sumar kan jahad Sosai Zoben ya fito mai ɗauke da harafin *J* sai ƙyalli yake yi


Abun yayi matukar ɗaure mata kai,a rude tace"Kai!junaid ya fita da zoben shi aranar!Ya akai zoben kuma ya koma ɗakin Aunty azmee?Taya akai hakan ta faru?Ta yaya zoben shi ya koma ɗakin Aunty azmee..?" tuni zufa ta wanke mata fuskarta,Still bata kawo komai aranta ba,


Jiki na rawa ta nufi bedroom ɗinsu,asaman side drawer ta ɗauki wayarta da ta ajiye,kafin ta ajiye wayar Jahad asaman drawer ɗin,


Gaban mirror ta koma ta zauna saman kujera,Layin Aunty Azeema ta kira,Cikin sa'a wayar ta soma Ringing,'natsuwa tayi tana jiran ta amsa kiran nata,jikinta sae kerma yakeyi,Allah Allah take yi acikin ranta ta samu Aunty azeema ta ɗaga kiran,

Almost 15 missed Calls hajiya Azeema bata ɗaga kiran ba,A ƙarshe dole ta haƙura da kiran nata,ba don taso ba,saboda akwai wani muhimman abu da take so ta tambayeta kuma a wurinta ne kaɗai zata iya samun amsoshin tambayoyin da take dasu,


Ajiye wayar tayi gaban mirror ɗin,Kafin ta miƙe tsaye tare da kai idanuwanta ta kalli wall clock ƙarfe 2 na dare,


Dafe kanta tayi saboda matsanancin ciwon kan da ya farmata lokaci guda,a sakamakon tunanin da take ta yi,Zuciyarta tayi nauyi sosai,ga kokwanton da take yi,ga fargabar da take ji,Abubuwa dak sun tarar mata,


Don bala'e a zaune ta kwana,batare da ta runtsa ba,sai wuraren sallar asuba bacci ya ɗauketa can cikin kunnanta taji ana ambaton Sunanta sehrish sehrish,a firgice ta farka,idanuwanta a zare,


Oummansu ta gani atsaye tana kallonta"Sehrish A zaune kika kwana?meyasa baki tafi ɗakin Auntyn taku ba"?

Muryarta da alamun bacci bai isheta ba tace"Oumma,bansan bacci ya ɗauke ni ba,"

   "Ki tashi kiyi sallah,Anata kira"ta ƙarasa maganar tare da wuce wa cikin toilet,


Miƙewa tayi dakyar take iya ɗaga ƙafarta saboda baccin da take ji,zuwa ta fara yi ta hau saman gadonsu ta tayar dasu Hosana suka farka tukunna ta sauko,bayan kowa yayi al'wala,Abu ta shimfiɗa masu Sallaya suka kabbara Sallah,a tsanake suke yin sallar,Bayan sun kammala sallar ne sun zauna kowa ya ɗaga hannunshi suna addu'a,Sehrish ta ɗan yi gyaran murya tare da cewa"Oumma,Jahad Hosana,dan Allah ku tayani da addu'a,Akan abunda nake yi,"


"Kada ki damu indai addu'a ce kin samu rishi,"acewar Oummansu,hosana tace"A nawa"?

  Harara Sehrish ta wurga mata batare da ta tanka mata ba,


Suna cikin yin addu'ar nan,Wayar Sehrish dake ajiye gaban mirror ta soma ruri,A zabure ta miƙe tare da nufar wayarta,

   "Kira kuma tunda Asuba?Wanene ke kiranki"?tsayawa tayi cak jin abunda oummansu tace,juyawa ta ɗan yi tare da kallonta,ɗan murmushi ta  sakar mata"ummm dama Ina tunani ko Aunty Azeema ce ke kira ne"

  "Okey,ki amsa kiran"da sauri Sehrish ta ƙarasa gaban dressing mirror ta dauki wayar tare da duba screen ɗin,Wani irin farin ciki ne ya lullu6eta ganin kiran Aunty Azeema,


Juyawa ta ɗan yi kamar mara gaskiya ta saci kallon Oummansu dake zaune saman darduma,Hosana harta fara hammar bacci sai cewa takeyi"Wai Oumma addu'ar bata isa haka ba?Dan allah mu koma mu kwanta,murmushi abu tayi tare da kallonta,

"kije ki kwanta mana,Wani ya ruƙe maki ƙafafunki,ibadarma baki iya yi da abinci ne duk mun yawanshi sai kin tada shi....."jahad ce tayi maganar tana harararta,

  Ganin hankalinsu ya koma kan Hosana yasa ta lalla6a ta fuce daga cikin ɗakin,Gudu gudu sauri sauri take tafiya,kaitsaye ta nufi hanyar nan da zata sadaka da wajen gidan,fitowa tayi ta nufi garden don batason kowa yaji ta,


A gefen wata bishiya ta tsaya,tare da duba Screen ɗin wayar missed call har 3 Aunty azeema tayi mata,Danna mata kira Sehrish tayi cikin sa'a Auny Azeema ta ɗaga kiran,


A hanzarce Sehrish ta kara wayar a kunnanta,tun kafin tayi magana Aunty Azeema tace"Sehrish lafiya kuwa?kin tashi hankalina,kawai ina farkawa yin sallar asuba sai naga missed calls ɗinki"


Muryar ta har shaƙewa takeyi saboda tsabar saurin tayi magana"Aunty azeema,babu abunda ke faruwa,lafiya lou nake,Dan Allah wasu tambayoyi ne nakeso nayi maki,Wani Assignment ne aka bamu a school,"


"Okey,Allah yasa nasani"

"Aunty azeema,Malamar da ta bamu assignment ɗin tana buƙatar muyi bincike akan wani accident daya faru ne,Sai mu sanar da ita amsar da muka samo,"


Natsuwa hajiya Azeema tayi tana sauraronta,

  "Saurayi ne da budurwa,suka shirya zuwa shan ice cream,to akan hanyar zuwansu,sai suka dakata agefen titi,ita budurwar ta tsallaka titin zata siya musu ice cream,ta bar saurayinta acikin motar,kwatsam sai ga wata truck ƙatuwa tabi ta kan motarsu,nan take kuma sai wuta ta kama ci da motar,kafin ƴan kwana kwana su ƙaraso wurin,Wutar taci ta cinye,ba'a samu komai ba daga sassan jikin saurayin,


Katseta Aunty azeema tayi"ita malamar taku me takeso ku gano mata ne,"


"Bari na kai maki ƙarshen labarin,shi saurayin ya zama toka,sai ƙarahunan motar aka samu,to abun mamaki kawai sai kuma ga Zobenshi na Diamond an tsince shi a hannun wani dattijo,zoben bai yi komai ba,sai ƙyalli yake yi kamar sabo,to shine take son kowa yayi nazarin labarin ya fada mata abunda yake hasashe"


Abun mamaki tana kai ƙarshen labarin sai taji Aunty azeema na dariya,bubbuga ƙafa Sehrish tayi kamar tana agabanta"Wayyo Allah mommy azeema,meyasa kike dariya,dan Allah ki taimaka ki bani amsar tambayata,"


Tsagaitawa tayi da yin dariyar,sannan tace"Abun mamaki abun Al'ajabi,kawai sai aka tsinci zoben diamond ɗin saurayin a hannun wani,bayan shi mamallakin Zoben ya ƙone ƙurmus,Gaskiya Sehrish ta baku Assignment me wuya,Amma fa ni abunda nake tunani,in har babban Diamond ne kamar irin wanda na ta6a siya ma Junaid,nasan kin ta6a ganinshi a hannunshi mai harafin J,"


  Muryarta har kerma takeyi wurin amsa mata"eh naganshi ahannunshi"

"Yawwa,so kin ga kalar wannan Diamond ɗin,In har wuta ta ta6a shi baiyin komai,Sai dai akwai wani abunda yake yi idan wutar ta haura mintuna tana ci ajikinshi,Stone ɗin jikinshi zaiyi duhu sosai,kuma ba hakan yana nufin ya mutu bane,Lafiyarshi ƙalau Amma fa wannan duhun da dutsen jikinshi yayi,A nigeria basu da chemical ɗin da zasu gogeshi,Sae dai anan dubai Companyn da nake siyayyar Diamonds ɗin a wurinsu ne kaɗai zasu iya goge wannan baƙin ya dawo yana ƙyalli"


"Amma Aunty Azeema me kike tunani game da Zoben da aka tsinta hannun wani dattijon?Wanda kuma ba'a gabanshi hatsarin ya faru ba,kuma shi saurayin da zoben ya shiga cikin motar Har ya haɗu da hatsarin"ta ƙarasa maganar tana jiran amsarta,don a ƙagare take,


Shiru Aunty azeema ta ɗanyi na wani lokaci da alama nazarin wani abu takeyi,

  "Naji kinyi shiru mommy,"

Sai lokacin ta ɗaura da maganarta"Gaskiya abu biyu ne nake tunani,Shi wannan dattijon suspect ne,Amma kuma in har dagaske shi matashin da zoben ya shiga cikin motar,dole abu biyu ne zai kasance!Kodai Shi saurayin ne yayi wurgi da zoben ya faɗo daga cikin motar ko kuma mamallakin Zoben Yana raye!!Yayi escape daga cikin motar shiyasa har aka samu Zobenshi kuma lafiyarshi ƙalau zoben babu alamun wuta ta ta6a shi,kinga kuwa Shima mai zoben bai mutu ba a hasashe na kenan,

  Gaban sehrish ne yayi wani irin mugun bugu,Hankalinta yayi matuƙar tashi,idanuwanta azazzare,jikinta har kerma yakeyi,

.."amma Aunty azeema,meyasa kike tunanin cewa mamallakin Zoben yana raye,"

  "Wlh sehrish ni ko a school ban ta6a cin karo da question mai sarƙaƙiya ba irin wannan tambayar da kikayi mun,Gaskiya nidai nafi kyautata Zaton Shi Mamallakin Zoben ya ku6uta daga cikin motar,Ai kince ita budurwar ta tsallaka titi ne,taje siya masu ice cream.

Katse mata hanzarinta sehrish tayi"Amma fa Aunty,ita budurwar koda ta tsallaka titi,Shi saurayin sai da ya kira sunanta,ta juya har yana ɗaga mata hannu ta cikin motar,"

  "Kinsan tazarar minti nawa ita budurwar ta ɗauka lokacin da mai ice cream ɗin yake zuba mata ice cream ɗin?

  Girgiza kai sehrish tayi kamar tana agabanta haka take gani"A'a bansani ba gaskiya,"

  "Idan har aka samu tazara koda na minti biyar ne,ita budurwar ta kawar da idonta daga kanshi,ta mayar da hankalinta wurin mai siyar da ice cream din,A wannan interval ɗin zai iya yiyuwa Ya ku6uta daga cikin motar,ko kuma an ɗaukeshi,Ni daga jin wannan labarin ma wlh duk shiri ne aka tsara don a caza maku brain ɗinku,kin sani sai surutu nakeyi ko breakfast banyi ba,"ta ƙarasa maganar da zolaya,

  Dariya Sehrish tayi tare da cewa"Am sorry Auntyna,thank u so much Aunty Azeemana,Kin taimake ni sosai,Yanzu na samu amsar da nakeso,"

  "Kada ki damu Daughter,duk lokacin da wani abu ya shige maki,ki sanar dani kawai a shirye nake dana baki shawara"

  Murmushi sehrish ta saki,har sunyi sallama zata kashe wayar da sauri hajiya azeema ta dakatar da ita "Wait!kince saurayin ya zama toka ko"?

  "Hakane,"ta amsa mata,

"Taya za'ace ko ƙashin jikinshi ba'a samu ba?wutar tayi more than one hour ne tana ci?ba kince an kira motar kwana kwana ba,"

   "A'a banda masaniya akan wannan amma zan tambaya,"

  "Okey,akwai wani incident daya ta6a faruwa, makamancin labarin da kika bani,almost 30 mins wutar naci A motarsu,ba'a kashe wutar ba,saboda babu wasu a kusa,Ko daga baya da mutane suka zo aka kashe wutar an samu wasu konannun 6angarori na jikinsu,duk da zai iya faruwa dagaske ae yasha faruwa ma,mutun ya ƙone ƙurmus sai tokarshi,ko indiyawa ma ai suke ƙona gawarsu su kuma ƙulle tokar in zasuyi jana'iza Amman kinga ai wutan tana daukar lokaci tana kona gawar,Amma nidai gaskiya a labarinki Ban yadda cewa Wannan mamallakin Zoben ya mutu ba!!Amsar da zaki ba malamar ku kenan!Ki sanar da ita duk wani bayani da nayi maki,Nasan zata baki mark sosai,"


Jiki asanyaye sehrish tace"in sha Allah Aunty azeema,Zan rubuta duk wani bayani da kika yi mun nagode sosai,"


Daga haka su kayi sallama,kamar jira takeyi ta katse kiran,jiki a mace ta zauna gefen bishir,Ta gaza yadda da abubuwan da kunnuwanta suka jiye mata,Dama kuma it will be very hard farat ɗaya ta fara suspecting ɗin Azmee,Bakomai yafi tsaya mata arai ba,fa ce waɗannan tambayoyin masu matuƙar wuyar amsuwa Junaid yana raye ko ya mutu?taya akai zoben Junaid yaje ɗakin Aunty Azmee?kodai zoben aljani ne yana da fiffike harya tashi sama ya fito daga cikin motar da fika fikinshi yazo ɗakin Aunty azmee?Sai lokacin ta soma tunanin wai ma wacece Aunty azmeen nan?tunda suke atare da ita,bata ta6a bata labarin danginta ba,kwata kwata bataso a tambayeta dangane da danginta,Sannan kuma tunda take da Aunty Azmee bata ta6a cewa zata je gano gida ba,Uwa uba kuma Aunty azmee bata ta6a gajiyawa dayi masu aiki ba,A ƙalla idan zata lissafa shekarun Junaid da akace ta shayar dashi tun yana jinjiri,Azmee tayi more than 20 years a gidan,


Zurfin tunani ta shiga yi,maganganun ya sayyadi ne suka shiga dawo mata acikin kanta,inda yake cewa kaf family dinsu a tafin hannunsu suke,Duk wani motsi nasu akan idanuwansu suke,Kenan Suna da ɗan leƙen asiri acikin gidan?Dolen doliya akwai wanda ke shirya wata maƙarƙashiya acikin gidan,Tunawa tayi da wannan malamin makarantar nasu Ya Mu'allim da ya ta6a bata ruwan addu'a ta sha saboda yawan bacci da take a aji,lokacinne kuma ta Manta dasu Hosana kwata kwata,Tabbas Akwai abunda akayi mata,still Sehrish bata fara zargin kowa ba kuma har lokacin bata sanyawa ranta cewa Aunty Azmee tana da sa hannu a Mutuwar Junaid ba,Tama fi zargin Haroon don yasha sanar da ita cewa Zai kashe farin cikin gidan,Duk da tana doubting akan kalamanshi,Saboda shi ɗan giya ne yawancin kalamansu suna faɗi ne ba don su aiwatar ba,koba don haka ba,tana ji aranta cewa Haroon bazai iya kashe junaid ba,


Sehrish bata bar wurin bishiyar nan ba,Har sai da ƙarfe 10 ta buga,kamar wadda tasha ƙwaya haka take tafiya,Ga wani matsanancin ciwon kai da ya rufar mata,Ta caza ƙwaƙwalwarta sosai,


Lokacin da ta shigo cikin gidan,ta ƙopar da ta fita,kaitsaye bedroom ɗinsu ta wuce,Tura ƙopar ɗakin tayi ta shiga,Oummansu ta samu zaune gefen gado tana shan Coffee,


Jin motsin shigowar sehrish ne yasa ta ɗago da idonta tana kallonta,

  "Ina kika je ne?har muka kammala yin breakfast baki dawo gida ba,"

  Daƙyar ta iya buɗe baki tace"na shiga garden ne shan iska,"gudun karta ƙara tambayarta yasa tayi saurin cewa"Oumma,Coffee kike sha"

  "Azmee ce ta kawo mun shi yanzun nan,"

  Murmushin yaƙe sehrish ta dan saki tare da samun wuri gefen oummansu ta zauna,

  "Ba zaki ci abinci bane"?cike da kulawa tayi mata maganar,

  "A'a,na ƙoshi bana jin yunwa sai zuwa anjima zanci,"

   Miƙa mata cup ɗin hannunta tayi"kar6i kisha,"batayi mata musu ba tasa hannu ta kar6i Cup din takai bakinta tana sha,kur6a uku tayi ta dakata da shan Coffee ɗin tare da kallon Oummansu,

  Ganin tana kallonta yasa tace"Lafiya,kike kallona?"

  Murmushi sehrish ta dan yi "babu komai oumma,kawai inaso na tambayeki wani abu ne,"

  "Ina sauraronki"

"Amm oumma,jiya naga kin ɗan razana da kika ga Azmee,kinsanta ne?

  "Kamar nasanta amma bazan iya tunawa ba,"

   "Dan Allah Oumma kiyi ƙoƙari ki tuna,"

  "Shikenan,idan na tuna zan sanar dake,"

  Ba ƙaramin daɗi taji ba,Miƙewa tayi da sauri ta nufi toilet,Shaf shaf tayi wanka,lokacin da ta fito bata samu Oumman tasu da ta batari a azaune ba,babu kowa a ɗakin,


Tunani ta shiga yi ko Sgr Yana acikin gidan?tanaso taje ta duba lafiyarshi amma tana fargabar a wani hali zata same shi,dan kwanakin nan sam baya buƙatar kowa atare dashi,


Wani haɗaɗɗen lace ta ɗauko Ash colour sai ƙyalli yakeyi,riga da skirt ne,Sanya kayan tayi a jikinta,sunyi mata cuf cuf sun bi shape ɗin jikinta,Ɗinkin ya fito da ita sosai,kashe ɗaurin kallabi tayi,bayan ta ɗaure gashin kanta da ribbom,Gaban mirror ta koma ta zauna ta fara yin make up,murza wanccan shafa wancan manna wancan,kamar Aljana haka ta koma tayi kyau Over,


Wayarta ta ɗauka,ranta ne ya bata cewar ta tura mashi text message,may be ya bata amsa,

  _Hi,Gm Ya Rafayet ina fata ka tashi cikin ƙoshin lafiya,bansani ba ko yau kana buƙatar wani abu in kawo maka_

  Almost 5 mins da tura mashi saƙon saiga reply ya maido mata"I need coffee,"

  Murmushi ta saki kamar bata da damuwa acikin ranta,Ajiye wayar tayi agaban mirror ɗin,ta fito daga cikin ɗakin,kaitsaye ta nufi kitchen,A babban falo ta samu mutanen gidan suna fira abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,ga Oummansu ga Alex gasu fawan ga kuma su Jahad,tare da Abusufyan,"mutun uku ne kaɗai basu Hallara ba,Sgr Omar da Abbansu junaid,


Basu jiyo takun takalminta ba,saɗaf saɗaf ta shiga kitchen,har sai da gabanta ya faɗi lokacin da ta ga azmee a cikin kitchen ɗin,Batayi tsammanin akwai mutun aciki ba,

  "Kin tsorata ni,"Azmee ce tayi maganar,A yayin da take tsaye gaban sink tana wanke kwanukan da sukayi amfani dasu,

  Murmushin yaƙe sehrish ta sakar mata 

  'Afuwan Aunty azmee,nikaina saida na tsorata dana gan ki,Banyi tunanin akwae mutun ba,Shiyasa banyi sallama ba,"

  "Irin wannan kyau haka Sehrish?lace ɗin nan ba ƙaramin kyau yayi maki ba,"tayi maganar fuskarta ɗauke da murmushi,

   Murmushi sehrish ta kuma saki"babban yaya zan kaiwa coffee,'

  "Allah sarki,kwana biyu na lura yana cikin matsananciyar damuwa shi da Omar,musamman Abba Allah ya kawo masu mafita,Allah ya bayyanar da Junaid,"damuwace ƙarara akan fuskar azmee da tayi maganar,

  "Nima na damu akan rashin Junaid aunty azmee,kowa ya shiga damuwa sosai,bawan Allah,junaid da baison komai ba sai kyautatawa,Amma dan rashin imani da tausayi aka samu wasu mugayen suka ɗauke shi,in sha Allah Nan bada jimawa ba asirinsu zai tonu,Sai sun gane kuskurensu,kuma sai sunyi danasanin abunda suka aikata"da biyu sehrish tayi maganar,don taga react ɗin da Azmee zatayi,

  "Am naji kince zaki kaiwa Sgr coffee ko?Yakamata ki hanzarta kai mashi,idan kin dawo inaso muyi gurasa atare,nasan mutanan gidan nan zasu ji daɗi sosai idan akayi gurasa,Don An jima ba'ayi masu ita ba kuma suna so,"

  Cike da mamaki sehrish ke kallonta,Maimakon ta bata amsa kan maganar da tayi mata,amma sai gashi ta Canza magana,

   "Shikenan Aunty Azmee,Bari na kaimashi,"

After some minutes ta fito hannunta ruƙe da Cofeen,


Sai da ta fara tsayawa ta gaisar da mutanen falon kowa nata yabon wankanta,kafin ta wuce upstairs,

Lokacin da ta shiga bedroom ɗinshi,a kwance ta same shi saman katafaren gadonshi kamar mai yin bacci alhalin nan kuwa idonshi biyu yadai lumshe idanuwanshi ne,


Ƙarasa shiga ciki tayi ta ajiye mashi cup din asaman table,Sannan anatse ta ambaci sunanshi"Ya Rafayet,ina kwana,"


Banza yayi bai amsa mata ba,tunani ta shiga yi kodai bacci yake yi ne?

  "Babban yaya,"ta ƙara kiran sunanshi nan ma yayi mata shiru,sai da ya mula yasha iska kafin ya ɗan buɗe idanuwanshi tare da kallon wurin da take a tsaye,duƙar da kanta ƙasa tayi tana wasa da yatsun hannunta,

   Da wannan sexy voice ɗin tashi ya furta"Au is that how i taught u to greet me"

  gabanta ne ya ɗan faɗi tunawa da irin gaisuwar da yakeso ta dinga yi mashi,tabɗijancan,wani irin kunyarshi take ji,

  "Am waiting within 3 mins"ya ƙarasa maganar tare da mayar da idanuwanshi ya rufesu,


Da sauri ta cire takalmanta kafin ta hau saman gadon,Sai da taje saitin inda yake kwance sannan ta tsaya tana tunanin taya Zata fara,ga lokaci na tafiya,don ma Allah Yasa ya rufe blue eyes ɗinshi,

    daidai lokacin da minti uku suka cika Cuf,a hanzarce ta ɗan ranƙwafa gefen fuskarshi,lips ɗinta na kerma ta manna mashi kiss,har sai da taji ajiyar zuciyarshi alamar yayi receiving ɗinshi,other side ɗinma ta Manna mashi kiss,Saura na baki,

  Zuba ma Sexy lips ɗinshi ido tayi tana kallonsu gwanin ban sha'awa yadda kasan na jinjiri haka suke,saboda kyau da softnesss dinsu,

  Ganin yana ƙoƙarin buɗe idanuwanshi ne yasa tayi saurin hada mouth ɗinsu wuri ɗaya,sam bai ta6a tsammanin zata iya yi mashi kiss ba,sosai take shan lips ɗinshi tun daga kan lower lip dinshi zuwa upper,baisan lokacin da ya ƙara ƙankameta ba ajikinshi,hannayenshi gaba ɗaya suna asaman Ass ɗinta,yayin da ita kuma hands ɗinta ke tallabe cikin sumar kanshi,gaba daya suka harɗe wuri guda kamar tip da tyre,da niyyar gaisuwa tayi mashi hakan kamar yarda ya umarce ta sai gashi ta zarce da sarrafashi,ƙaramar yarinya na neman Zautar dashi,sai da yayi dagaske sannan ya samu yayi control ɗin kanshi,a lokacin harya zuge zip ɗin rigarta,kwantar da fuskarshi ya yi asaman boobs ɗinta,hancinshi na gogarsu haka la66ansa,tana jin saukar numfashinshi dake fita da zafi zafi,jurewa kawai yake yi,Shi kaɗai yasan halin da yake shiga a duk time din da ya kasance tare da ita,

  Zagayo da hannunta tayi ta cikin sumar kanshi tana shafa mashi ita,nan fa ya ƙara narkewa a jikinta kamar jinjiri ajikin Babarsa,

   Bakomai ya faɗo mata aranta ba fa ce abunda Aunty azeema ta sanar da ita,Wato ta ɗaukeshi kamar jinjirin da aka bata rainonshi,komai ta koya mashi zai ɗauka ne harya fara kwatanta yi mata,

   Moving lips ɗinta tayi izuwa saitin kunnashi,Calmly ta furta sunanshi"Ya rafayet,"

   Ƙasa ƙasa taji ya amsa mata"yeah,"

  "Have you ever been in love"?ita kanta batasan ta furta mashi hakan ba,

   "I don't know anything about love,I only know how to hold a gun"

Sam batayi expecting ɗin zai bata amsa ba,

  Murmushi tayi sosai,kafin ta kuma cewa"Coffee ɗinka fa?Zai huce,"

   "I don't need it now,Am just enjoying being with u"daƙyar yake yin maganar saboda yanayin da yake jin kanshi,sehrish tsantsar farin ciki ne ya lullu6eta,kalamanshi sun ƙayatar da ita,

  Wasa wasa bacci yayi awon gaba dashi,dama kwanakin nan bai samu ya runtsa ba,Reesh da babynta,saura babyn baby mai zuwa,


Dayake itama bata samu enough sleep ba adaren jiya,sai gashi ta fara jin baccin,


Wayar Sgr dake ajiye saman side drawer ce ta soma ringing,firgit ta farka,tare da miƙa hannunta tana lalubar wayar,don batason tayi moving din da zaisa ya farka,


Daƙyar ta samu yatsun hannunta suka ruƙo wayar,janyota tayi izuwa saitin fuskarta,Wani kalar suna ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,Can dai na yarensu na sojoji,


Picking Call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta,

  Wata kakkausar murya ce ta soma ji acikin kunnanta,

  "Sir!kana magana da sergeant Lee ɗaya daga cikin sojojin da ka sanya Su tsare maka grave ɗin younger brother ɗinka Junaid,"

  Har saida gaban sehrish ya faɗi rass gashi ta kasa sanar dashi cewa ba Sgr ɗin bane,

   "Since yesterday night naso na kira wayarka bansamu halin yin hakan ba!abunda ke faruwa shi ne yau almost 1 week kenan,akwai wani matashin saurayi dake yawan yin zarya a titin nan,kullum yana zuwa ne cikin motarshi ƙirar Venza Ash colour,mun sanya mashi ido sosai,gaskiya Sir we are suspecting him,Zaryarshi tayi yawa,kuma bai tashi zuwa sai wuraren 10 na dare,kuma idan yazo wurin ƙabarin sai yayi parking ɗin motarshi ya fito daga ciki,Yayi ta zagaye wurin da grave ɗin yake,kamar yana neman wani abu......" 

  Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,batasan lokacin da tayi rejecting kiran ba,jikinta har kerma yake yi,mayar da wayar tayi saman drawer ɗin ta ajiyeta,


Lalla6awa tayi da sauri ta zame jikinta daga nashi,gyara zip ɗin rigarta tayi,kafin ta sauko daga saman gadon,Zuciyarta sai faman harbawa takeyi,tayi danasanin picking call ɗin,da bataji wannan tashin hankalin ba acikin kunnanta,


Fitowa falonshi tayi asaman sofa ta zauna jikinta nata kerma,tsananin tsoro ne ya kamata,tunani ta shiga yi wanene Yake yin zarya a wurin ƙabarin junaid?me yake kai shi?me yake nema a wurin!tuni kanta ya fara yi mata ciwo,dama akwai ciwon kan ya ɗan lafa ne,


Hawaye ne suka soma saukowa akan fuskarta,lamarin ya fara rikitar da ita,daga wannan sai wannan?wai duk waye ke shirya wannan Maƙarƙashiyar ne"?


Miƙewa tayi bayan ta share hawayenta,fitowa tayi daga cikin part ɗinsa ta sauko downstairs kitchen ta koma,A bakin ƙopar shiga kitchen ɗin ta tsaya tare da goya hannayenta akan ƙirjinta tana kallon Azmee dake gasa Gurasa a frying pan,

  Gaba ɗaya hankalinta bai atare da ita,

  "Sehrish,"Azmee ce ta ambaci sunanta a firgice takai idanuwanta kan Azmeen,

   "Tun ɗazu nake ta jiranki baki zo ba,har na fara gasa gurasar,ko zaki taimaka ki yanka mun vegetables din da zanyi amfani dasu?ga kuma ƙuli da za'a daka,"

  Tunda ta soma magana sehrish tayi kasaƙe tana kallonta,batare da tace uffan ba,abubuwa dak sun cunkushe mata kwalwarta,ta fara rasa tunaninta,ji take kamar ta tambayeta ya akai Zoben Junaid yaje ɗakinta amma ta kasa yin hakan,

   Dafa kafaɗunta Azmee tayi tare da ɗan girgiza jikinta"Wai baki ji ina magana bane"?

  Da sauri tace"Amm ummm yanka kuli ko zanyi"

  Dariya azmee tayi sosai jin abunda tace,

   "Kin ta6a ganin inda aka yanka ƙuli ne?Nifa Cabbage dasu tumatur nace ki yanka mun,Shi kulin daka shi za'ayi,already akwai shi,wai ko baki da lafiya ne?naji jikinki da zafi"tayi maganar tare da sanya hannunta agefen wuyan Sehrish,

   "Banajin daɗi Aunty azmee,ina buƙatar addu'arki,"tana magana kamar ta fashe da kuka,

   Janyota azmee tayi tare da rungumeta ajikinta,

  "Allah ya baki lafiya ƙanwata,in dai addu'ace zan cigaba da tayaki,kema kuma ki dage da yin addu'a akan Allah ya yaye maki abunda ke damunki"

   Lamo sehrish tayi ajikin azmee har yanzu bata fara zarginta ba,kuma bata kawo komai aranta ba,Tana jinta tamkar mahaifiyarta,Saboda irin kulawar da take bata,

   "Aunty azmee na gode sosai,Allah ya barmu tare"

."Ameen ameen,"ta ƙarasa maganar tare da ɗago sehrish daga jikinta,

   "Kije ki kwanta kawai kina buƙatar hutu ni zan ƙarasa yin gurasar"

   Girgiza kai Sehrish tayi"A'a ae da sauƙi ciwon,Inaso na tayaki aikin,Ae ba wani abu bane me wahala,"

  Batare da 6ata lokaci ba,Sehrish ta fiddo kayan da zasu yi amfani dasu,Cabbage ne tare da tomotoes,Albasa da sauransu,


Suna cikin yin aikin Sehrish ta soma ƙoƙarin bugun cikinta,

  "Aunty azmee,jiya da kika ga Oummanmu naga kin ɗan razana haka kamar kinsanta,"

   "Kallon sani nake yi mata,Amma gaskiya bansanta ba,Zai iya yiwuwa sunyi kama da wata wadda na ta6a sani ne,"

   "Okey,amma tunda nake dake Aunty azmee,baki ta6a bani labarin danginki ba,Gashi na kwaɗaitu da son jin Labarinki,inaso wata rana idan kin tashi kai musu ziyara mu tafi tare,"

  Shuru Azmee ta ɗan yi har lokacin tana tsaye agaban gas tana gasa gurasar,almost 15 mins bata ce komai ba,har sai da Sehrish ta ambaci sunanta"Aunty azmee,kin yi shiru,"

  Murmushi azmee tayi irin na gefen fuskar nan,

  "Sehrish tunda nake dake baki ta6a tambayar dangina ba sai yau,shiyasa ban ta6a baki labari ba nima,ina da wani hali ni,in har mutun bai tambayeni abu ba,to kuwa bazai ta6a ji ba abakina,Amma yanzu tunda kin tambaye ni,idan muka samu Free time zan baki tarihin rayuwata,"

  Daga haka suka mayar da hankalinsu akan aikin da suke yi,Bayan sun kammala yin gurasar a saman faffaɗan tray Suka jejjerata,uban ƙuli suka barbaza asamanta,sannan suka shanana mai asaman kulin,ko ina yaji,daga sama kuma sukayi mata ado da kayan lambun da sehrish ta yanka,


Fita azmee tayi daga kitchen ɗin tabar Sehrish kamar yadda sukayi ita zata raba masu gurasar,Ba ƙaramin daɗin gurasar nan suka ji ba,musamman matasan gidan har rububi suka dinga yi,kowa sai da ya yaba daɗin da tayi,


Wurarren ƙarfe biyu na rana,bayan ta kammala sallar azhar ta koma kitchen ta shirya ma Sgr tashi gurasar,A saman wani ƙayataccen plate mai faɗi,batasan ko yana ra'ayinta ba,ita dai kawai tayi niyar kai mashi ne,


Tana ƙoƙarin shiga falonshi suka ci karo da juna,ƙiris ya rage plate ɗin hannunta ya 6are da sauri ya tallabo mata shi,tun daga ƙasa ta soma kallonshi,T shirt ce a jikinshi Blue ta fito da hasken shi sosai,Sai trouser ɗinsa black colour,da alama sauri yake yi ya fita,

  Zuba ma juna ido sukayi batare da ƙyaftawa ba,

  "Ina yini,ka tashi lafiya"?

  Lumshe mata eyes ɗinshi yayi alamar yana lafiya batare daya furta mata ba,

..."menene wannan"yayi tambayar yana nuna plate ɗin hannunta,

  "Gurasa ce,kai na kawo mawa,"

  Yatsina fuskarshi ya ɗan yi,tare da cewa"Sauri nake yi zan fita,"jiki asanyaye ta juya zata koma da ita,

  "zonan"ya kirata,da sauri ta juya tana kallonshi,

   "Someone called my line,Ke kika ɗaga"?

  Zuru tayi mashi da idanuwa gudun kada yayi mata faɗa,

..a ɗan hasale yace"Am asking u!"

  A tsorace ta ɗaga mashi kai alamar eh'

  "Its okey,juyawa yayi tare da komawa ciki"

  Bin bayanshi tayi asaman Sofa ya zauna,Ta ajiye mashi gurasar saman table,cire mashi murfin da ta rufe plate ɗin tayi,

  

 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*







Saman Sofa ya zauna,Sehrish ta ƙaraso ta ajiye mashi plate ɗin saman table ɗin gabanshi,hannu tasa ta cire murfin da ta rufe gurasar dashi,ɗan ɗagowa tayi tare da satar kallonshi samun shi tayi ya jingina bayanshi a jikin kujerar,idanuwanshi a lumshe suke,gyaran Murya ta ɗan yi mashi"Ya rafayet,"slowly ya buɗe idanuwanshi akanta,nuna mashi gurasar tayi alamar yaci,


Muryarshi a kasalance yace"who asked u to pick the call?" gabanta ne ya fadi calmly tace"dama naga baka dade da yin bacci ba,don kar kiran ya tashe ka yasa na dauka don in fadi ma mai kiran bacci kake,to kuma sai naji banjin abunda ake cewa shine nai rejecting kiran,amman kayi hkr"ta karasa kanta a kasa,still yayi yana cigaba da kallonta can taji yace"Ni zanci da kaina?" dagowa tayi suka hada ido, saurin kawar da idanuwanta tayi saboda kunyarshi da take ji,musamman inta tuna abunda tayi mashi asaman shimfiɗarshi,


Daƙyar ta iya buɗe baki tace"zan iya baka idan kana so,"


Nuna mata gefenshi yayi ta zagayo ta zauna,ƙamshin turarenshi har cikin kanta,A yangance tasa hannu ta nannaɗo gurasar,tana ƙoƙarin kaiwa bakinshi idanuwansu suka haɗu wuri guda,kasa janye idanuwanshi yayi daga kallonta,wasu abubuwa sun ɗan fara ɗaure mashi kanshi,Ta canza mashi sosai ba kamar daba time ɗin da ko haɗa ido bata iyayi dashi amma yanzu takan ɗan kalleshi harma su haɗa ido,kuma jikinta ya daina wannan rawar da yake yi duk in tazo part ɗinshi,hakan na nufin ta rage jin tsoronshi?ko meyasa?ko dan saboda romancing ɗin da yake yi mata ne?


Ganin ta kasa tura mashi gurasar abaki yasa ya ruƙo hannunta tare da matso dashi saitin bakinshi ya tura gurasar ya ɗan 6alla yana Ci,yayin da idanuwanshi ke kallon fuskarta,ita kuwa tuni ta kawar da idanuwanta daga kallonshi da take yi,sai dai satar kallon mouth ɗinsa da take yi,yadda yake chewing ɗin gurasar,soft lips ɗinsa na motsi ba ƙaramin fisgarta yake yi ba,sun 6ata mintuna a wurin nan,har sai da ya kammala ci sannan Sehrish ta miƙe ta nufi fridge,Coke ta ɗauko mashi mai sanyi ya kora da shi,bayan ya kammala sha Ya nufi bedroom ɗinshi,bin bayanshi tayi don ta gyara mashi ɗakin,A tsaye ta same shi ya kara waya a kunnanshi yana magana,

  Shiga ciki tayi da sallama abakinta,kaitsaye ta fara gyara mashi bed ɗinshi,tana jin moving ɗinshi lokacin daya kammala yin wayar ya faɗa toilet,jim kaɗan ya fito yana gyara wrist watch ɗin hannunshi"Am leaving"Shi ne abunda taji yace,juyowa ta ɗan yi tare da kallonshi"when are u coming back"?daƙyar ta samu ta iya tambayarshi,tana ƙoƙarin yin practice ɗin abunda Azeema ta koya mata,

  Shi kanshi ya jinjina tambayar da tayi mashi,hakanan kawai dai yace"Zan kai 12 na dare,"

  Gyaɗa kai tayi tare da mayar da hankalinta kan Gadon da take gyarawa,tun kafin ma ya fita harta fara Missing ɗinshi,ga wani abu da ke yi mata yawo a kanta,Tana so ta sanar dashi about Junaid's ring da ta gani a cikin drawer ɗin Azmee amma ta kasa faɗa mashi,saboda bata ƙarasa investigation ɗinta ba,Amma taci alwashin muddin ta gano dasa hannun Azmee dumu dumu saita gaya mashi ne,'


tana cikin wannan zancen zucin unexpected taji yayi hugging ɗinta ta baya,gaba ɗaya ya saukar mata da kasala,hannayenshi ya zagayo ta saman stomach ɗinta,A hankali yake rubbing tsinin Hancinshi asaman fatar wuyanta,lumshe idanuwanshi yayi tamkar maijin bacci,bakomai yake yi mashi yawo acikin kanshi ba,fa ce zancen Marshal Na little Junaid,Still yana deciding din lokacin da ya dace ya aiwatar da hakan duk da yanzu baya cikin kwanciyar hankalinshi,wata irin kasala ce ta kama kowannansu ya jima ahaka kafin ya saketa,da sauri ya fuce daga Bedroom ɗin yana jiyo voice ɗinta tana yi mashi adawo Lafiya,


Fitarshi ke da wuya,Sehrish ta zauna gefen gadonshi tana tunanin ta yadda zata iya taimaka masu,remain 4 days Yanzu acikin waɗannan kwanakin Yakamata Su gano Abu biyu waɗanda suka kashe Junaid,ko kuma shi junaid ɗin if he'a still alive,Kamar yarda Aunty azeema take hasashe,abubuwa da yawa sun shige mata kanta,akwai buƙatar zuwanta ɗakin azmee domin ƙara yin bincike,Sai dai tana tsoran Azmee ta kamata,


Miƙewa tayi taci gaba da gyaran ɗakin,bedroom ta fara gyarawa,kafin ta shiga toilet ɗinshi nan ma ta gyara,dawowa palourn tayi tana Aiki tana sambatu kamar wata zautacciya,


Wuraren ƙarfe 4 na yamma,Amrish na kwance tana bacci saman katafaren gadonta,daga ita sai gajeran wando black colour,sai half vest wadda bata rufe cibinta ba,juyi ta soma yi alamun zata farka daga baccin,lokaci guda ta ware manyan idanuwanta tana kallon ceiling,ranta yayi matuƙar 6aci lokacin da ta tuna dalilin yin baccin nata,sam batasan ya ɗauketa ba,kuma tana zargin cewa maganin bacci aka bata,dama kwanakin nan duk in Mommynta zatayi baki saita ɗura mata ƙwayar da zata sata bacci,Yawanci acikin abunsha take sanya mata,miƙewa tayi daƙyar saboda kasalar da take ji,Saukowa tayi daga saman gadon tana miƙa tare da yin Hamma,toilet ta nufa zata shiga sai kuma ta fasa,Fitowa tayi daga cikin ɗakinsu ta nufi bedroom ɗin Mommynta,hannu tasa zata ruƙo handle ɗin ƙopar ɗakin don ta buɗe,Surutun da tajiyo daga cikin ɗakin yasa ta dakata,tare da kasa kunnanta tana sauraranta,

  "Wlh bazan ta6a ƙyalesu ba,Zasu yi galaba akanmu ne,ai kawai ku kashe shi,ku kashe shi kawai,ko ku cire mashi idanuwanshi,Uban kowa ya rasa,idan har ba zaku iya ɗaukar mataki ba,to ni zan ɗauka dakai na,"da alama waya take yi,yadda kasan yar daba,

  Hankali amatuƙar tashe,ta toshe bakinta da hannunta,gudun kada ta saki ihu,jikinta sai kerma yake yi,lalla6awa Amrish tayi cikin sanɗa ta koma bedroom ɗinta,agefen gado ta zauna,Yayin da zuciyarta ke ta bugawa,Dama ta jima tana zargin Momynta,

  "Amma mommy bata da Imani,sai cewa takeyi akashe akashe,kamar wata zararra,wlh nima bazan ƙyaleki ba mommy ki yi kisan kai ina gani,Zan cigaba da samaki ido ne batare da kinsani ba,kuma Allah muddin nagano cewa kashe ƴa'ƴan mutane kikeyi da kaina zan kaiki ƙara wurin hukuma su garƙameki,"tana magana tana cizon le6enta,


Turo ƙopar ɗakin nata akayi,da sauri ta baje saman gadon tana baccin ƙarya hada minshari,mommy ce ta shigo hannunta ruƙe da wayarta,


Zuba ma Amrish ido tayi tana kallonta,kafin ta Kanga wayar  a kunnanta

  "Har yanzu Bata farka daga baccin ba,Ni na bata maganin bacci,Wlh ta cika sa ido,ga bin ƙwaƙƙwafin tsiya,Har sa'insa take yi dani shiyasa nake bata maganin bacci"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar tana sauraron wanda suke yin wayar dashi,


"Ae ni na kwace wayar hannunta,Shiyasa ko ka kira bazaka same ta ba,idan ba haka ba zata iya zame mun matsala,"

  Kasa kunne Amrish tayi tana sauraronta,Aranta tace"Asirinki ya tonu mommy,yau naji da kunne na,wato ke kike bani maganin bacci ina sha,ko wa take faɗama cewa ina bacci hmmmm,ta ƙarasa zancen zucin tare da jan dogon numfashi irin na wanda yayi nisa a baccin nan,

  "Okey,Bazan barta da yunwa ba,Yanzu zan tashe ta taci abinci,Ae bazan ƙara wasa da lafiyarta ba,duk da bata da hankali,"

  Sallama sukayi da mutumin da take yin wayar dashi,zama tayi daga gefen gadon,a tsanake ta soma kiran sunanta

  "Amrish!Amrish!"kusan sau biyar tana ambaton sunanta,hada bubbuga ƙafarta,A hankali Amrish ta ɗan buɗe idanuwanta,muryarta a kasalance ta furta"Mommy,lafiya kike ƙwala mun kira"?

  "Tun ɗazu kike bacci,Ko sallah bakiyi ba halan?Ga la'asar ma na ƙoƙarin yi,ki tashi ga Abincinki can a dining kije ki ci,"

 miƙewa tayi daga zaune,tana yin hamma kafin ta wuce cikin toilet,koda zata rufo ƙopar saida ta ƙara leƙen Mommynta,kafin ta datse ƙopar,


*AMANI*


Zaune suke acikin falon gidan,Hayaam Da Abra na zaune saman 3 seater,Yayin da Amani ke zaune saman 2 seater,hayaam ce ta soma magana"Aunty Amani,mun yanke shawarar zamu koma gida gobe,bai kamata mu cigaba da zama anan ba muna ɗaura maku nauyinmu,kinyi mana abunda bazamu ta6a mantawa ba,"ta ƙarasa maganar yayin da idanuwanta ke acike tab da kwalla,

Ajiyar zuciya amani ta sauke tare da cewa"Shikenan,gaskiya yakamata ku koma kam kodan Saboda Mammy da Abra ta baro kwance tana jinya,Bamusan a wani hali take ciki ba ayanzu,'

  "Aunty laila fa'?Abra ce tayi tambayar,

  Hayaam tace"Ina ruwanmu da ita?tana raye kota mutu matsalarta ce,bata da amfani acikin rayuwarmu,"

  "Kada ki ce haka hayaam,itafa ƴar uwarkuce,duk da bata kyauta maku ba amma bai kamata kuyi watsi da ita ba,Yanzu dae bamu san awani hali take ciki ba,Amma mujira mu gani,indai Laila ce nasan zata dawo ne,sannan ina ƙara gargaɗinku akan irin rayuwar da kuka ɗaurawa kanku,musamman ke Abra,kinga dai irin abunda ya faru da hayaam kema kuma in baki kiyaye ba,zaki jefa rayuwarki cikin hatsari ne,mazan da kuke mu'amala dasu ɗaya daga cikinsu bazai iya aurenku ba,Idan ma ya aureku to bazai darajaku ba,sannan kullum zaku kasance cikin zargin juna,so wannan rayuwar ba mai 6ullewa bace,kuma ku mika dukkan al'amuranku wurin Allah,duk abunda yake rabonka ne kana zaune zai same ka,in ku ka ga baku samu abunda kuke so ba,to Allah bai kaddaro rabon ku bane...."sosai Amani tashiga yi masu nasiha jikinsu duk yayi sanyi,hada kuka,


Suna cikin tattaunawar nan,Amal ta faɗo cikin falon,hannunta ruƙe da wayar Amani,ƙarasowa tayi wurin da amanin take a zaune ta miƙa mata wayar"Yaya Abbas ne ya kira,"

Harararta Amani tayi"Dama wayata tana a hannunki,"?sunnar dakai ƙasa tayi tana dariya,

  "tare da Amal zamu tafi gobe'?acewar abra,tayi maganar tana kallon Amal ɗin

   Wani irin kallo Amal tayi mata,hada cizon la66a,dariya Amani tayi tare da cewa"Ba zaki bisu ba,kinga yanzu komai ya dai daita,ki amince kawai ki koma cikin ƴan uwanki da zama,

  A shagwa6e Amal ta bubbuga ƙafarta tare da ruqe qugunta"Nifa wlh bazan bisu ba,idan kin gaji da zamana ne a gidanki,nan bada jimawa ba,Yaya Jahan zai ɗauke ni,"

Gaba daya suka zuba mata ido suna kallonta cike da mamaki a fuskokinsu,banda Amani dama ita tasan tsakaninta da Jahan,

  Murmushi Amani ta saki tare da cewa"Nima wasa nake maki,Ae Amal ta gama zaman maiduguri in ba dai zuwa kai ziyara ba,daga Abuja sai ƙasar waje ko ba haka ba?'cike da zolaya tayi mata maganar,

Murmushi Amal tasaki,tare da juyawa da gudu tabar falon tana dariya

Tashin sense,jikinsu Abra ba ƙaramim sanyi yayi ba,duk irin burin da suke dashi na zama surukan Alexandra ya tashi abanza,Sai gashi Yarinyar da suka raina,Suke wulaƙantawa ita ke da rabon auran jinin Alexandra,Abun ba ƙaramin ta6a masu zuciya yayi ba,sunyi danasanin rayuwarsu,zuba masu ido Amani tayi tana kallonsu ganin yadda kowa tasha jinin jikinta,


*General Ishaq*


Fitowarshi kenan daga cikin toilet,Jikinshi sanye da jallabiya,tun yana acikin toilet yaji ringing ɗin wayarshi,ƙarasawa yayi tare da kai hannu ya ɗauki wayar,New number ce aka kirashi da ita,Bin kiran yayi kiran na shiga aka ɗaga wayar"Assalama Aleekum"muryar wani inyamurin mutunce,

  "Wa'alaikum salam,ko zan iya sanin dawa nake magana"?

On the other hand mutumin yace"Yalla6ai dama wani bawan Allah ne keson magana dakai,Shine yace in taimaka in kira mashi layinka,"

  "To bashi wayar,"tsayawa yayi yana jiran jin muryar mutumin da akace yana son magana dashi,

  Abun mamaki sai yaji kukan Laila Acikin wayar,ya cika kunnanshi,cikin shessheƙar kuka ta wanda ya galabaita ya jigata sosai ta soma magana"Abban hafsat ni ce laila,dan Allah akawo mun ɗauki,ina cikin mawuyacin hali,"

  Murmush Ishaq ya ɗanyi tare da cewa"Bangane wake magana ba?kodai wrong number ne aka kira"?

  Jin haka yasa ta ƙara sautin kukan nata"Ishaq kada kayi mun haka,Wlh ina cikin masifa,gani nan a Enugu yashe gefen bishiya,sai an bani sadaqa sannan nake samun abunda nake sawa acikina,Wlh Ishaq na tuba nabi Allah,Akawo mun agaji ƙafata ta lalace ta ru6e...."tana magana tana kuka,

  Handsfree  ya sanya don yaji daɗin sauraronta,Sai da takai ƙarshen maganarta sannan yace"the number you're trying to call is switch off,pls try again Later"yana kai ƙarshen maganar,yayi rejecting kiran yana dariya,ko kaɗan baiji tausayin kukanta ba,Don tafita aranshi kwata kwata,Yayi mamakin jin wai tana a Enugu ko ubanme yakaita enugu?ta6e le6enshi yayi tare da faɗin"I don't care Allah ya raka taki gona,nasamu na rabu da jangwamgwam,"

  Ƙarar shigowar message yaji,da sauri ya duba screen din wayar ya soma karanta saƙon

  _Ishaq ka taimaka ka ceci rayuwata,wlh ina cikin masifa,naga tashin hankalin da banta6a gani ba Ishaq,wayar ma aronta nayi a hannun wani inyamuri,kayi taimakon musulunci ishaq karka duba halina,dan Allah zakayi,ataimaka a dauko ni daga Enugu ko maiduguri ne a mayar dani in mutu acan_

  Guntun tsoki ishaq yaja,tare da yin deleting ɗin saƙon,a karshe ma blacklist ya tura number,yadda ko an kira baza a same shi,"

  Murmushi ya saki lokacin daya tuna da hajjaju,macen da yake burin aure,duk da taƙi amince mashi amma kullum saita kirashi ta tambayi lafiyarshi,Wannan ya tabbatar mashi da cewar tana sonshi,tunda ta damu dashi,sannu a hankali Zai samu yayi Wuff da ita ya kawota Cikin gidan shi,


*Boss Bature*


Yinin Ranar Sehrish da Ciwon kai Tayi shi saboda tsabar tunane tunanen da take yi,ta kasa tsaye ta kasa zaune,Har magani tasha amma kan yaƙi lafawa kamar ana kunna wuta acikin ƙoƙan kan nata,abun ya ɗaure mata kai yadda Azmee ta share zancen bata Labarinta,Har lokaci suka samu amma bata tada zancen ba,kuma ko tayi yunƙurin zata tuna mata sai tayi saurin Canza zancen,hakan ne yasa Sehrish ta fara accusing ɗinta,Ta sanya mata ido sosai duk wani motsinta akan idanuwan sehrish take yinsu,


Wuraren ƙarfe 9;30 na dare,gidan yayi tsit da alama wasu daga cikinsu sunyi bacci,Oummansu kaɗai ta rage a ɗakinsu,Zaune saman sallaya tana tasbihi,Yayin da su sehrish ke kwance saman gadon,hosana da jahad sunyi Bacci banda Sehrish wadda idonta biyu,ta kasa runtsawa,jira take yi Oummansu ta kammala Sallar ta dawo saman gadon ita kuma ta koma ɗakin Azmee,


Tana cikin Jan cazbahar nan wani abu ya faɗo mata aranta,abunda ta jima tana ƙoƙarin tunanawa,a hanzarce ta miƙe jiki na rawa ta tunkari gefen da sehrish take kwance saman gadon,Hannu tasa tana ɗan bubbuga kafaɗarta"Rishi!rishi!ko kinyi bacci ne,"yatsina fuskarta ta ɗan yi daƙyar ta iya huɗe idanuwanta,

  "Tambayar da kika yi mun game da wannan Auntyn taku Azmee,Na tuna inda nasanta.."tunkan takai ƙarshen Maganar,jiki na rawa Sehrish ta tashi daga zaune tana kallonta"Oumma a ina kika Santa?

  "Zan faɗa maki Sehrish amma fa karki kuskura ki sanar da ita cewa nasanta,tunda bansan da wata manufa take zaune acikin gidan nan ba,"

  "Bazam faɗamata ba Oumma"

Jinjina kai abu ta ɗanyi"Wannan matar da kike gani,Lokacin da na haifeku babu wanda yazo yi mun wankan jego,Sai daga baya Ya sayyadi yazo da ita amatsayin ƴar uwarshi da zata yi mun wankan jego...."

  Jin wannan maganar yasa hankalin Sehrish yayi mugun tashi,Saboda tsabar kiɗima gaba ɗaya idanuwanta suka firfito waje,Hannu tasa ta daki ƙirjinta"Ƴar uwar Ya sayyadi!"ta ambaci hakan a tsorace

  Abu ta lura da Yanayin da Sehrish ta shiga,bata dakata da yin maganar ba taci gaba da cewa"Wlh Sehrish matarcan da kike gani,Ba ƙaramar shu'uma bace!abun tsoroce ita,Dalilin dayasa nace maki haka,Lokacin da sayyadi yazo mun da ita don tayi mun wankan jego,Kamar kurma haka ta koma,duk in naso na bugi cikinta don ta sanar dani wani abu game da danginsu,Sae taƙi tanka mun,Nasan dai ta bani kyakkyawar kulawa a lokacin amma gaskiya ba abun yarda bace,saboda nayi mamaki dana ganta acikin gidan nan,Kuma sai surutu take yi kamar ba ita ba,Sa6anin a yadda nasanta lokacin da tazo gidanmu ko uffan bata cewa,daga um sai um um shine abunda ke fitowa daga bakinta,"

Hannu sehrish tasa tare da dafe kanta dake jujjuya mata,a hankali tashiga furta"Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un!Amma Azmee ta gama damu!indai abunda nake zargi ya tabbata to tabbas Azmee Itace Ƴar leƙen asirinsu dake fitar da surrukan gidan nan......"

Cike da mamaki abu ke sauraron kalamanta sae da takai ƙarshen maganarta Sannan tace"Meyasa kika ce haka?Dama kina zarginta ne?Amma naga kamar kuna zaman lafiya da ita,'

Hawaye na kwaranyowa akan furkarta ta shiga faɗin"Oumma,muna cikin tashin hankali in har ya kasance AZMEE itace take shirya maƙarƙashiya acikin gidan nan...."dafa kafadarta abu tayi"ki sanar dani abunda yasa kike zarginta inaso inji,ko Zan iya taimaka maku"

  Duk da tana cikin mawuyacin hali na firgici,haka ta zauna ta kwashe dukkan abunda ke wakana acikin gidan ta sanarwa Oummansu,abun mamaki tana kai ƙarshen maganar sai taga Abu na murmushi gami da girgiza kanta,

  "Oumma ko kin gano wani abu akanta ne?naga kina murmushi,"

  "Akwai wani abu da nakeso na sanar dake sehrish!Shi ɗan adam ba abun yadda bane,Bakomai zaisa kiyi kokwanto akan azmee ba fa ce Yardar da kukayi da ita,Ta ko'ina azmee ta gama daku,Ta siye zuciyoyinku ta hanyar kyautatawar da take yi maku,Shi mutun maison ɗaukar fansa,Zai iya yin 6adda kama ya shiga jikin maƙiyansa har na tsawon shekaru Yana yi masu bauta batare da gajiyawa ba,yayin da yake shirya masu maƙarkashiya batare da sun ankare ba,Har sai ranar da ya tarwatsa su gaba daya tukunna zai bayyana kanshi,Yanzu kinga gaba ɗaya ta gama sanin surrukanku......"dakatawa abu tayi da yin maganar,Ta jinjinawa azmee sosai,ta iya shirya tuggu

  "Gaskiya sehrish dole kiyi taka tsantsan,don wlh in har ya kasance zargin da muke yi ya zama gaskiya,To fa Azmee ba ƙaramar shu'uma bace,Kuma zata iya kashe duk wanda yayi gigin tona mata asiri,a yadda ta faro shirinta tsawon lokaci yanzu bazata bari wani Ya fallasa ta ba,"

  "Amma Oumma,nibansan ya zanyi ba,abubuwa sunyi mun yawa akaina,"tayi maganar damuwa ƙarara a kan fuskarta,

  Dafa kafaɗarta abu tayi"Ni dai shawarar da zan baki shi ne,Ki samu wani babba ki sanar dashi komai dangane da ita....."

  A ruɗe sehrish tace"Wazai yarda dani Oumma!idan har na faɗi cewa Azmee ƴar uwar sayyadi ce,kuma ina zarginta da mutuwar Junaid"

  "Tabbas kuwa babu wanda zai yarda dake a halin yanzu,a ƙarshe ma reshe zai iya juyewa da mujiya,Zata iya ɗaura maki laifin kinsan fa shi mugun mutun hatsari ne shi,balle su da suke da tsafi,duk da dai mu mun dogara da Allah ne,babu ja da baya Allah shi zai bamu kariya,"

  "Yanzu ya zanyi!inaso naci gaba da bincike akanta,Saboda inaso na tambayeta dangane da zoben Junaid dake a wurinta me yakai shi cikin kayanta,"

  "Nace maki karki kuskura ki ce zaki nuna cewa kinsan wani abu game da ita,in ba haka ba zatayi maki mummunar illane,Nidai shawarar da zan baki A yanzu ki damƙa binciken nan a hannun ɗaya daga cikin mutanen gidan nan,Zaifi ma ki sanar da Daddynku,Zan ma yi mashi magana,nasan zai yarda dani sosai'

Shikenan Oumma,Yanzu zan iya zuwa ɗakinta in kwanta"?

  "Me zai hana amma dai ina ƙara jan kunnanki akanta,karki kuskura ki tsananta bincike akanta,Don zata ganoki ne,"gyaɗa kai Sehrish tayi tare da saukowa daga saman gadon ta nufi hanyar fita daga ɗakin,ruƙo handle ɗin ƙopar tayi,bayan ta fita taja ƙopar ta rufe,gyara kwanciya Oummansu tayi saman gadon,ita kanta abun ya razanar da ita,Ta yadda akai har ƴar uwar sayyadi ke aiki acikin gidan,daƙyar bacci yayi awon gaba da ita,


Tafiya sehrish takeyi kamar wadda aka zarewa lakar jikinta,komai ya tsaya mata Cak,don abun ya girmi tunaninta,a ƙopar ɗakin Azmee ta tsaya gabanta na faɗuwa a hankali ta furta"La'ila ha illa anta subhaka inni kuntu minazzalimin,tana kai ƙarshen addu'ar ta tura ƙopar ta shiga daga ciki,abun mamaki bata samu kowa ba acikin ɗakin,Ranta ne ya bata cewar kodai ta shiga toilet ne,

A wauta irin na Sehrish,maimakon tabi abunda Oummansu ta sanar da ita,Sai ta soma tunanin Yin bincike acikin ɗakin don a qagare take da ta gano gaskiyar wacece AZMEE,


Agaban bedside drawer ɗinta ta zuƙunna jikinta na kerma,ta shiga bubbuɗe drawer chest ɗin,Yawanci duk tarkace ne na magunguna sai ƴan ƙulle ƙulle kamar na maganin Zafi,gida na ƙarshe ta bincika anan ne taga abun daya ɗaure mata kai,Ƙura ido tayi tana kallon Galleliyar wayar dake ajiye a wurin,Ƙirar i phone 13pro


Batasan lokacin da ta furta"Ya Allah!dama Aunty Azmee tana da waya?Amma meyasa ban ta6a ganin wayarta a hannunta ba,"ta ƙarasa maganar tare da zura hannunta ta ɗauki wayar,ta kunna power ɗinta,Nan take haske ya kawo,Gabanta ne ya faɗi Ganin Hoton dake ajikin Wallpaper ɗinta,bakowa bane face Fuskar HAROON,da ƴar ƙuruciyarshi,nan fa tashiga ruɗanin abun al'ajabin da take gani,Menene Alaƙarta da haroon da har ta ɗaura hotonshi a fuskar wayarta?dama ta jima tana zargin haroon ba mutumin kirki bane,kodai hadashi atare suke shirya maƙarƙashiyarsune?


Tana cikin wannan wasi wasin,kira ya shigo cikin wayar da baƙuwar lamba,kwata kwata babu sautin ringing an sanya wayar silent,Yadda ko an kira baza'aji ƙararta ba,


Sehrish da karanbani sai ta ɗaga kiran tare da kara wayar a kunnanta,

Shiru tayi tana jiran jin wanene zaiyi Magana,

Cikin harshen fulatanci taji ana magana,gashi ita bata iya yaren ba,Tunani ta shiga yi dama azmee bafullatana ce?dama ta ta6a ganin Zanen kalangu a gefen fuskarta,


  Tana cikin wannan zancen zucin tajiyo takun tafiyar mutun yana tunkaro ɗakin,Ba shakka Azmee ce,A tsananin tsorace Sehrish ta katse kiran,gashi wayar akwai password,babu yarda za'ae ta goge kiran da akayin,dole idan aka shiga Call log agane cewa An ɗaga kiran da akayi,

A matukar firgice Sehrish ta tura wayar acikin drawer ɗin,Duk tabi ta ruɗe ta rasa inda zata dosa,A ƙarshe ta faɗa toilet ta rufe,tana faman sauke ajiyar zuciya,jijiyoyin wuyanta duk sun fito saboda tsabar tsoro,Tayi danasanin ɗaga kiran wayar Azmee da tayi,


A hankali Azmee ta turo ƙopar ɗakin ta shigo,Jikinta sanye da baƙaƙen kaya,Jallabiya ce tare da mayafinta,kamar wadda taje anguwa,zama tayi daga gefen gadon,tare da kai Hannu jikin drawer ɗin ta ɗauko wayarta,dannata ta shiga yi,kafin ta danna call,


Sehrish dake la6e acikin toilet ɗin da alama mutumin da ya kira Sehrish ta ɗaga shi Azmee ta kira,Addu'a sehrish tashiga yi hannunta na kerma ido ya raina fata,tuni zufa ta wanke mata fuskarta,Ga fitsari daya matse,ta kasa tsugunnawa tayi futsarin gudun kada azmee taji ƙarar fitarshi,

  Ba ƙaramin haushi Sehrish taji ba lokacin da Azmee ta soma Magana Cikin harshen fulatanci,taso ace da yaren hausa tayi maganar don ta samu taji abunda zata ce,yanzu ta ƙara ƙarfafa zarginta akan Azmee,


*Boss Bature*


Around 10pm


Jami'an da Sgr ya sanya su tsare grave ɗin Junaid,sunyi 6adda kama yadda kasan ba Sojoji ba,kowannansu na sanye da Kaya namu na hausawa,riga da wando na yadi,ɗaya daga cikinsu yana zaune saman dogon benci yayin da ɗayan ke zuƙunne agaban bencin gefenshi kayan Shoe shiner ne,Yana goge ma na saman bencin Takalminshi,dayake akwai hasken street light,Bakomai suke jira ba fa ce wannan mai zuwa yana yin zarya a ƙabarin nasa,bisa Command ɗin da Sgr ya basu nasu sanya ido akanshi idan ya ƙaraso,Su sanar dashi yana so yaga ko wanene,Suna zaman jiran zuwanshi,Aikuwa cikin sa'a ƙarfe goma na bugawa,kamar yadda ya saba zuwa,Sai motar nan ƙirar Venza ta shararo da gudu izuwa titin,tunkan ya ƙaraso ɗaya daga cikin sojojin wanda ke zaune saman Bencin yace"Gashi nan!yakamata mu sanar da Sgr,tun kafin ya kufce mana"

  Wanda ke goge mashi takalmin yace"sai munyi taka tsantsan if not zai gudu ne,"


Koda ya ƙaraso wurin ƙabarin slowly yayi parking ɗin Motar a gefen titin batare daya fito ba,


A hankali Sergeant ɗinnan dake zaune saman bencin ya ɗauko wayarshi tamkar yana dannata,message ya turawa Sgr,bayan ya kammala tura saƙon Ya mayar da wayar cikin trouser ɗinshi,


Buɗe murfin motar yayi tare da saukowa daga cikinta,kamar yadda ya saba zuwa haka yau ma yazo,Ya sanya face mask a fuskarshi yayin da idanuwanshi ke sanye da glass baƙi,Jikinshi na sanye da Crazy jeans tare da T-Shirt purple,tafiya ya soma yi har izuwa gefen bishiyar nan inda aka kewaye ƙabarin Junaid,tsayawa yayi kamar mai neman wani abu,hada ruƙe qugu,kusan minti 5 kafin ya soma zagaye bishiyar yana jinjina kanshi,


Miƙewa ɗaya daga cikin Sojojin nan yayi,A hankali ya nufe shi batare daya ankara ba,koda matashin nan Ya lura da cewa wani na tunkaroshi,Aikuwa da gudun gaske yabar wurin bishiyar,Sojojin nan suka bishi a guje,duk yabi ya rude ko motarshi bai tsaya ɗauka ba,a rikice ya faɗa saman titin yana gudun ceton rai kamar zai tashi sama,da gudu suma suka bi bayanshi don karya kufce masu,yana gudu yana waiwayen bayanshi,Unfortunately Yana ƙoƙarin karya kwana,Adai dai Lokacin Motarsu Sgr ta shawo kwanar,Kwatsam ya faɗama motarsu ta bugeshi sosai,ya saki wata irin razananniyar ƙara tare da zamewa ya faɗi wanwar ƙasa,Ƙarasowa Sojojin suka yi suna faman sauke ajiyar zuciya,Ta kwana gidan sauƙi,


Fitowa Sgr yayi daga cikin motar,Armstrong ma ya fito,Atare sojojin suka sara mashi,Kafin ɗaya daga cikinsu ya nuna saurayin dake a kwance ƙasa yana bullayi"Sir,Wannan shi ne wannan matashin dake zarya a ƙabarin ƙaninka,rashin gaskiya yasa yana ganinmu ya zabura zai gudu",


Zuba mashi ido Sgr yayi yana bin shi da kallon ƙurulla,tun kafin ma Ya cire mashi face mask ɗin fuskarshi,Ya shaida shi,zuƙunnawa yayi saman guiwarshi ɗaya,tare da kai hannu Ya zame face mask ɗin saurayin tare da cire glass ɗin fuskarshi Yayi throwing dinshi saman titin,runtse idanuwanshi yayi jikinshi sae kerma yake yi,


A hankali Ya furta sunanshi"HAROON" kamar bashi ba,Ya rame,yayi baƙi,jin muryar Sgr yasa haroon ware manyan idanuwanshi masu kama dana mujiya,koda yayi tozali Da Sgr a hargitse Ya tashi daga zaune yana kallonshi yayin da yake faman zazzare ido,wata irin zufa ce ta soma tsastsafo mashi agefen fuskarshi,.  

  "Dama kaine"?cike da mamaki Sgr yayi tambayar,

  Shiru Haroon yayi bai tanka mashi ba,

  "Me kake yi a wurin grave ɗin Junaid"

  Daƙyar ya iya furta"ƙabarin junaid kuma?yayi maganar tamkar baisan akan me suke magana ba,

  ɗagowa Sgr yayi tare da kallon sojojin dake tsaye suna ta faman haki"Zaku iya komawa bakin aikinku,"juyawa su kayi da sauri suka bar wurin,

  "U will explain it don ubanka,I have been suspecting you for a while,Zuba maka ido nayi kawai inga ƙarshen gudun ruwanka,abunda ka aikata ne yasa ka gaza samun natsuwa acikin ranka That's why kazo kana zarya akan ƙabarinsa"?


Waro ido haroon yayi amatuƙar tsorace Yayi yunƙurin miƙewa ya gudu,damƙar ƙafarshi Sgr yayi hakan yasa ya gaza motsawa,

  "Amstrong,ɗaukarmun shi ka sanyamun shi acikin mota,"


Gadan gadan Amstrong ya tunkareshi,Yadda kasan ƙaramin Yaro haka ya ca6eshi asaman kafaɗarshi,Ya turashi cikin motar Sgr,Front seat suka shiga,Sgr da Amstrong Tada Motar yayi da gudun gaske ya fisgeta,

"Wai ina zaku kaini ne?Motata fa?kun barta a wurin"shiru su kayi mashi babu wanda ya tanka mashi,

  "Wlh kada kuce zaku ta6ani,Rafayet ku sauke ni in kama gabana!Ni bansan akan me kuke magana ba"Sai faman sambatu yake yi,zufa duk ta wanke jikinshi"

  Har Lokacin basu tanka mashi ba,ƙoƙarin buɗe motar yayi donya buɗe,amma yaji ƙopar adatse ta ko'ina babu hanyar da zai gudu,


Da gudun gaske motarsu ta shigo cikin gidan A lokacin Sehrish na la6e cikin toilet ɗin Azmee,Har cikin kunnanta tajiyo sautin Shigowar Motar Sgr,kamar ta fasa ihu haka take ji ga Azmee taƙi yin bacci bare ta lalla6a ta gudu,Sae dannar wayarta take yi,Yadda kasan tasan da zaman wani acikin ɗakin,


Window ta hango acikin toilet ɗin,Da gudu ta nufe ta,so take ta leƙa window ɗin don taga idan shi ne ya dawo dagaske,net ne ajikin tagar,kuma tagar tayi nesa,Tsawon sehrish bazai kai ta leƙa tagar ba,Lalla6awa tayi cikin sanɗa ta ɗauko bokiti,Ta kifa shi ajikin bangon,Sannan ta daddage ta haye saman bokitin cike da tsoran karya fashe bokitin,


Ƙura idanuwanta tayi tana leƙan wajen gidan daƙyar take hangen wurin da motar Sgr take,fitowa yayi daga cikin motar tare da zagayawa ya Shaƙo wuyan rigar haroon ya wurgo shi waje,gaba ɗaya ya kife ƙasa a susuce,Gabanta ne ya faɗi rass!lokacin da taga Ya damƙo rigar haroon,Tabbas ranta na bata cewar Sun kamoshi ne a matsayin me laifi!tsoranta kada Sgr yayi kuskuren raunata shi,wata'ƙil Sunji kalamanshi ne dayake cewa zai kashe Farin cikin mutanen gidan Shiyasa suke tuhumarshi,kamar ta bur6a tagar ta fito haka take ji,


Ɗaukarshi Sgr yayi asaman kafadarshi Ya wuce dashi cikin gidan Amstrong na biye da bayanshi,ɗakin horon nan nasu Ya shiga tare dashi,ɗakinda idan aka rufe ƙoparshi ko ihun mutun ba'aji,


Sauke shi yayi yana tangal tangal Zai faɗi ƙasa,Nuna mashi ɗaya daga cikin kujeru biyu dake kallon juna yace"Ave a seat,magana nakeso nayi dakai,"

  "Nifa bansan komai ba!meyasa ka shigo dani wurin nan"?

Wani irin kallo da Sgr ya wurga mashi yasa shi lalla6awa ya zauna,jikinshi nata kerma,kai cike da iskanci ga shegen tsoro 


Zama Sgr yayi suna fuskantar juna yayin da Amstrong ke atsaye yana kallonsu,


  Sai faman mazurai haroon keyi,irin na marasa gaskiyar nan,

  "Meyasa ka aikata hakan"?girgixa kai ya shiga"Ni wlh ban aikata komai ba,Nifa bansan komai ba,bansan akan me kake magana ba"

  Tsabar takaici ne yasa sgr ware yatsunshi Biyar ya kwasa mashi mari asaman fuskarshi,nan take le6enshi ya fashe,hannu yasa ya dafe kuncinshi saboda zafin daya ji,


"Ka faɗamun meyasa ka kashe junaid"?

    "Rafayet ba zaka ta6a jin komai ba,a abakina"Duk da halin da yake ciki hakan baihana shi gaya magana ba,

..rai amatuƙar 6ace,Sgr Ya damƙi kwalar rigashi da iya ƙarfinshi na ƙarshe ya daddaɗao da haroon a zafafe ya tunkari faskeken Madubin dake a aɗakin,Gaba ɗaya ya rotsa kanshi acikin glass ɗin,Wata irin gigitacciyar ƙara Haroon ya fasa yana fadin"Nashiga uku!Rafayet ka kashe ni!Na bani Na Lalace!!!.."kafin Haroon yayi wani yunƙurin kwace kanshi tuni Sgr ya ƙara Tarwatsa kanshi Acikin glass ɗin madubin,Nan take jini Ya soma tsastsafowa Asaman kanshi,Ya hada mashi Jini da Majina,Fitsari ya saki a wando ya shiga zubowa Zirrrrr yana kawarara Yaji bala'e,

  Naushin cikinshi sgr ya shiga yi gaba ɗaya,Duk In ya naushe shi sai Jini ya fito ta bakinshi,Ganin yana ƙoƙarin kashe shi yasa Amstrong Yin saurin dakatar dashi Ta hanyar ruƙo damtsen hannunshi"Allah ya huci zuci zuciyarka,Bai kamata ya mutu a yanzu ba,Still bamu samu bayanan da muke son samu a wurinshi ba,"

Ranshi amatuƙar 6ace yake magana"Kabarni in kashe wannan mugun mutumin Mara imani da tausayi!In har ban kashe shi ba,bazan samu kwanciyar hankali ba,Bazan cigaba da jure ganinshi yana yawo araye ba,

  Haroon dai tuni ya fita hayyacinshi sai faman ambaton Innallahi wa'inna ilaihirraji'un yake yi acikin bakinsa kamar wani musulmin ƙwarai,Jini duk ya wanke mashi fuskarsh,

  Daƙyar Amstrong ya samu ya shawo kanshi,Ya haƙura da zancen kashe haroon,Zuƙunnawa yayi agabanshi Yana kallonshi,Idanuwanshi tuni sun jima da juyewa,Yayi bleeding sosai,

  "Sir!ya rasa jini sosai,Yakamata Abashi Emergency treatment,don ya dawo cikin Hayyacinshi,idan yaso sai mu tuhu me shi daga Baya,

   Hannu Sgr yasa tare da kinkimar haroon ya wuce dashi medical Room ɗinsu,Ba don yaso ba haka ya shiga duba shi,Uban bandage ne akan goshinshi,duk ya cire mashi pieces na gilashin daya Sossoke shi,biji biji yake kallonsu


Zama daga gefen gadon Sgr yayi,yana kallonshi cike da jin tsanarshi acikin zuciyarshi,

  "Najima Ina samaka ido haroon,ban ta6a ɗaukar mataki akanka ba,saboda ina zargin cewa Ba yin kanka bane,Akwai wanda ke take maka baya kana aikata hakan!

  "Nazo nigeria ne saboda in ƙarfafa bincikena akanka,kafin na yanke maka hukunci,Na sanya maka ido sosai duk wani motsinka acikin garin nan ko ince acikin ƙasar nan a idona kake yinshi!!"

Haroon dai sai binshi da idanuwayake yi,sunyi jawur dasu ga raɗaɗin ciwon da yake ji,ga wani nishi da yake saki don ba ƙaramin jiki yaji ba,

  "Tun lokacin da ka sanyawa yarinyar can ido,Ka takura mata akan cewa ta amince ka kusanceta ko kuma Ka tona mata Asiri,Anyi haka ko ba'ayi ba"

  Waro ido waje haroon yayi Yana kallonshi,hankalinshi a matuƙar tashe,

  Cigaba da magana Sgr yayi"A kwai ranar dana sanya ta kawo mun injection inyiwa kaina,Saboda bata iya karanta hand writting ɗina,Sai kayi mata wayau da nufin zaka taimaketa,Shi ne ka bata allurar Maye ta kawomun,bisa rashin sani har nayiwa kaina"!

  Wani irin wahalallan Yawu haroon ya haɗiya,abun yayi mugu mugun ɗauke Mashi kai!Taya akai duk yasan da wannan?mutun sai kace Aljani

  Cigaba da magana sgr yayi"Bayan wannan,Kayi masu Twins barazana akan su baka 80million ko ka fallasa porn video wanda ka ɗauka a hotel room ɗinsu yayin da suke aikata Homo!Anyi haka ko ba'ayi ba'?

  Tashin Hankali,kasa buɗe baki Haroon yayi sai faman wurga idanuwa yake yi,

  "Kullum kalamanka sune zaka kashe farin cikin gidan na,kayi niyar kashe junaid sai kuma ka fasa saboda ƙaunar da yake nuna maka,Har so kayi ka shiga Jikinshi donka cutar dashi Amma ka gaza yin hakan saboda sonshi da kakeyi,Daga baya kuma Sai wani abu ya faru tsakaninka da Marshal Omar sakamakon marin da kayiwa Reesh,Shi da Uncle suka kwasa maka mari a lokaci ɗaya,bayan haka kuma Omar yayi maka bugun tsiya,wannan yasa ka dawo da wannan mummunan ƙudirin naka na son kashe Junaid....."tunkan yakai ƙarshen maganar Haroon daya gama razana yace"Duk ya akai kasan da wannan?kuma meyasa tun lokacin baka hukuntani ba?bayan kasancewa Ni maƙiyinku,Na tsaneku bana son farin cikinku,banda burin daya wuce inga na tarwatsa farin Cikinku,Kuma nayi nasara akanku tunda har na Kashe junaid,Ko yau nafaɗi na mutu na gama daku,


A fusace Amstrong ya zabura zai ɗauke shi daga saman gadon don ya rugurguzashi dasauri Sgr ya dakatar dashi"Ka barni dashi,Na ishe shi,"

  "Bansan wanene yake tunzuraka ba haroon,Amma inaji araina cewa Sanyaka akeyi kana yi,Laifin me muka aikata maka?da har muka cancanci hakan a wurinka?me junaid ya aikata maka da har kayi silar mutuwarshi?duk irin halarcin da akayi maka acikin gidan karasa dame zaka saka mana sai wannan?Da wani ido kake tunanin Abbanmu zai kalleka?Ya ta6a banbantamu dakai ne"?

  "Banbanci kuma na yaushe?babu mai sona acikin gidan nan,ba ku damu dani ba,bakusan halin da nake ciki ba,kowa kuna nuna mashi so da ƙauna acikin gidan nan,Ni kaɗaine kuka ware kamar wani bare,"yana magana yana kuka 

  "Nikaina bada son raina nayi silar mutuwar junaid ba,ɗacin raɗaɗin ƙuncin da kuke cusa munne yasa har nasa aka bi takanshi da mota,Yanzu bana jin tsoran kowa yaji cewa Na kashe junaid,Saboda nima so nake na mutu,tun ranar dana kashe Junaid na gaza samun kwanciyar hankali,duk wani mugun abu da nake aikatawa na daina duk don saboda shi,haƙƙinshi kaɗai ma bazai barni inyi rayuwa cikin salama ba,Duk ni najawa kaina wannan masifar da nake ciki........"sosai ya fashe da matsanancin kuka,gaba daya basu yarda da kalamanshi ba,Yana yin magana tamkar wanda yayi danasani,

  "Ka fadamun wanene yake baka Command kana aikata hakan?idan har ka faɗamun zan ƙyaleka kayi tafiyarka,"

  Girgiza kai Haroon ya shiga yi yayin da hawaye ke kwaranyowa daga cikin idanuwanshi"Wlh bazan iya faɗa maka ba!bazan iyaba,da ace zan iya dana fada maka,Amma bazan iya ba,"

  Jinjina kai Sgr yayi tare da miƙewa tsaye yana kallonshi"its okey,tunda baza ka faɗamun ba,Amstrong ɗaukarshi ka mayar dashi ɗakin horon nan,".  

  Fashewa haroon yayi da matsanancin kukan Yana ƙoƙarin dakatar da Amstrong akan karya ɗaukeshi,abun ba ƙaramin ɗaure masu kai Yayi ba,

  "Leave him,"Ya ambaci hakan tare da dakatar da amstrong daga ɗaukarshi,"

  Allura Sgr ya ɗauko,Aikuwa a firgice haroon ya shiga girgiza mashi Kai yana fadin"kada ka kashe ni dan Allah,kabarni da raina,inason Na nemi yafiya a wurin Abba kafin nabar duniya...."

  "Kasan daɗin ranka meyasa shi junaid ka kashe shi baka bari ya gana da iyayenshi ba?Haroon Rayuwarka bata da amfani"Turmushe shi Amstrong yayi,Sgr ya Caka mashi allurar a wuyanshi,lokaci guda jikinshi ya saki gaba ɗaya,Lokaci guda idanuwanshi suka kakkafe,daga bisani ya sanƙare babu numfashi,


Tashin Hankali!Haroon Zai rayu Koya mutu?Ya sehrish  ƙare acikin toilet ɗin Azmee ga futsari ya matse ta,Junaid Yana raye Koya Mutu?Am confused 


*Ga duk maison Abban sojoji ya tuntu6i Layina whatsapp message kawai banda call 08103884440*



 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*




Not edited



.Anan suka barshi saman gadon batare da sun kawar dashi ba,


Har zasu fita daga ɗakin sgr ya kalli Amstrong"Wayarshi nakeso ka ɗauko mun,Nasan dole akwai wasu mahimman bayanai da yake ajiyewa acikinta,"

Juyawa Amstrong yayi tare da nufar Haroon dake kwance magashiyan saman gadon,Hannu yasa cikin aljihun wandonshi Ya lalubo wayarshi tare da key ɗin Motarshi,dawowa yayi ya mika mashi su duka,hannu Yasa ya kar6esu daga hannun Amstrong,


Bayan sun fito daga ɗakin,Sgr Yayi Locking ɗin ƙopar,Sallama su kayi da Amstrong ya wuce upstairs part ɗinshi,


Gaba ɗaya ƙyanƙyamin jikinshi ya ke ji,blood ɗin Haroon daya fallasar mashi duk ya 6ata Shirt ɗin jikinshi,quickly yake taka staircases ɗin harya haura Sama,Lokacin daya ƙarasa Cikin Falonshi,yayi expecting ɗin zai sameta aciki,yaji daɗin ganin yadda ta gyara ko'ina gwanin ban sha'awa,kullum furniture ɗin ɗakin kamar sabbi suke komawa duk in suka sha gyara,


A hanzarce ya wuce cikin bedroom ɗinshi,


Ya zancen sehrish da take ƙumshe cikin toilet ɗin Azmee,Ta shiga matsanancin tashin hankali,ba laifi bane idan ta shiga toilet ɗin Azmee,matsalar da aka samu shine Wayar da tayi picking,in Azmee ta ganta zata gane cewa itace ta ɗaukar mata waya,



Jiki na rawa ta sauko daga saman bucket ɗin,Tasa hannu ta ɗago shi cikin sanɗa ta mayar dashi inda ta ɗauko shi,komawa tayi bakin ƙopar toilet ɗin ta tsaya,Duk tabi ta tsorata,fitsarin da take ta faman matsewa ne ya kufce mata nan take ya shiga fitowa Ziiir ta tsakankanin cinyoyinta,Runtse idanuwanta tayi sosai Cikin zuciyarta tana ambaton"Allahumma Ajirni filmasibati aklifni khairan minha'


Tana cikin wannan yanayin Kwatsam Ba zato ba tsammani tajiyo Muryar Azmee daga cikin ɗakin tana cewa"Sehrish idan kin gama la6e la6en naki,ki fito kizo ki kwanta dare nayi,"

  Gabanta ne taji yayi wani irin mugun bugu,Zuciyarta tamkar zata 6allo daga ƙirjinta,Idanuwanta sun Zazzaro waje kamar ƙwayar idon zata faɗo ƙasa

  Jin tayi shiru yasa Azmee ta ƙara ɗaga muryarta"ke fa nake Jira!"

Wani irin wahalallan Yawu ta haɗiya abakinta,Tashin Sense,kenan duk wannan la6e la6n da take yi Azmee tasan da zamanta acikin Toilet ɗinta How that Can be possible?Bayan batasan Lokacin da ta shiga cikinshi ba,Wannan ya ƙara firgitar da ita,

  "Ko saina Shigo cikin toilet ɗin nan"?

  Muryarta na kerma tace"A'a gani nan zuwa,"

  Tayi maganar tare da nufar tap ta kunna ruwa ya shiga kwararowa,Ɗebo ruwan tayi ta yayyafa shi a jikinta sosai Ta wanke fitsarin,'

Gabanta na faɗuwa ta nufo ƙopar,Yatsun hanunta na kerma ta buɗe ƙopar ta fito,

A bakin ƙopar toilet ɗin ta tsaya,kamar an dasa mata Aya,Idanuwanta na kallon ƙasa,


Juyowa Azmee tayi tare da kallonta,Sam babu wani sauyi akan fuskarta,Sai ma cewa tayi"Ya akai naga wandon jikinki a jiƙe"?

  La66anta na rawa tace"Fitsari ne ya matse ni,ina ƙoƙarin nayi shi ne ya zubo mun,Amma na wanke shi,"

  "Eyya,duk kin bi kin jiƙa jikinki,Sanyi zai iya kamaki,bari na ɗauko maki kaya ki sanya,"

  Da sauri Sehrish ta dakatar da ita"A'a aunty Azmee,Zan koma ɗakin mu ne,"

"Why"?tayi tambayar da ɗan mamaki akan fuskarta,

  "Ba'anan kike kwana ba"?

"Eh,Zan dawo akwai abunda zanyi acan"tana magana jikinta na kerma,

  Gyaɗa kai Azmee tayi"its Okey,Sai kin dawo,".

  Da sauri da sauri sehrish ta lalla6a ta nufi ƙopar fita daga ɗakin Harta ruƙo handle ɗin ƙopar zata buɗe,muryar azmee da katse mata hanzarinta"Take care of ur self"shi ne abunda taji tace mata,Ai ko waiwayonta bata yi ba,gudu gudu sauri sauri ta fito daga ɗakin Azmee,A haukace Ta faɗa bedroom ɗinsu,tana shiga ta fara jin ƙaiƙayi ajikinta,Hannu tasa tana sosa wuyanta,Abu kamar wasa bayanta ya ɗauka,cinyoyinta duk suka ɗauka ko'ina na jikinta,da gudun gaske ta faɗa cikin toilet,After some minutes ta fito ɗaure da towel,Ƙaiƙayin ya rage amma akwaishi kamar lafawa yayi,wadrobe taje ta buɗe tare da ɗauko Ƴar rigar bacci shara shara rigar haka take,Zura ta tayi ajikinta,har lokacin tana sosa jikinta,Burinta taje part ɗin Sgr don tasan Zai jirane ta kawo mashi coffee,turaren nan nata ta fesa ko mai bata tsaya shafawa,duk jikinta ba daɗi,


Slipper ta zura a kafarta,quickly ta nufi ƙopar ɗakin ta buɗe,Ta yafa mayafi akanta,Kitchen ta shiga shaf shaf within mins ta fito hannunta ɗauke da Cup of coffeee hada Fuits ta haɗo mashi,Don ya jima bai shasu ba,


Gadan gadan ta nufi cikin babban falon,tun tana tafiya ta soma jin wani irin kuka kuka Kamar na namun dawa,hakanan ta dake don bata kawo aranta ba,lokacin da ta ƙarasa Part ɗinshi,ta shiga falon da sallama bata same shi aciki ba,Bedroom dinshi ta shiga,Tana aza ƙafarta karaf idanuwanta suka sauka Akan Sgr wanda ke zaune Tsakiyar gadon jikinshi sanye da Sleeping dress ɗinshi,Yana daddana Laptop ɗinshi gaba daya ya mayar da hankalinshi akanta,gabanta ne ya faɗi Rass Lokacin da idanuwata suka fara nuna mata danƙara danƙaran kunamai A kewaye dashi suna ƙoƙarin Harbinshi,

Waro ido tayi waje tare da Sakin tray din dake hannunta,Ta fasa wata irin razananniyar ƙara wadda ta firgitar dashi,A hanzarce ya ɗago yana kallonta,Ta toshe kunnuwanta jikinta sae kerma yake yi,A ruɗe ta dinga nuna shimfiɗarshi tana fadin"Ya Rafayet Majici!kunama!zasu ɗalle ka gasu nan gasu nan Ya rafayet ka tashi....."Gaba daya gizan tsoranta sun tashi,To Fa,


Abun yayi matuƙar ɗaure mashi,Shi dai baiga komai ba,A wurinda yake zaune,Janye laptop ɗin yayi saman mattress ɗin,Gently ya sauko daga saman gadon ya tunkareta,Fashewa ta sake yi da uwar ƙara kamar maƙoshinta zai 6allo waje,Macijan nan ta gani tare da kunaman sun sauko daga saman gadon sun biyo Sgr suna ƙoƙarin sarin Kafarshi,

  Muryarta na kerma ta shiga fadin"Ka janye ƙafarka ya rafayet!gasu nan wlh gasu nan wurin ƙafarka zasu sare ka,Zasu cinye maka ƙafafunka....."

  Ƙarasawa yayi tare da ruƙo ƙafaɗunta,girgiza ta yayi"Hey!what's wrong with u?A ɗan tsawace yayi maganar,aikuwa nan take ta sume mashi Asaman wide chest dinshi ta faɗa,hannunshi yasa sosai yayi hunging ɗinta,Still abun ya bashi mamaki ya kuma ɗaure Mashi kai,wurga idanuwanshi yayi ƙasa saman tiles ɗin ɗakin mai kama da glass,Kayan marmarin da ta kawo mashi ne yashe a ƙasa sun tarwatse hatta cup ɗin Ya fashe,sigh yayi tare da mayar da idanuwanshi Kan sehrish dake sume a ƙirjinshi,bin fuskarta yayi da kallo,jiƙe take sharkaf da hawaye,la66anta duk sun bushe,tafin hannunshi ya sanya a saman kanta ya ɗan shafa sumar kwantacciyar sumarta,mayafinta tuni ya jima da sulalewa ƙasa,ɗaukarta Yayi gaba ɗaya saman kafaɗarshi Ya juya da ita izuwa wurin Katafaren gadonshi,Ya Kwantar da ita,kafin ya miƙa hannu ya dauke laptop ɗinshi Ya wuce da ita Palour don bai kammala aikinshi ba,


Almost 30 mins Yana zaune saman Sofa Yayin da yake daddana laptop ɗinshi,after Ya kammal aikin,Ya rufe ta,anan ya barta ya nufi fridge ya dauko Bottle water mai sanyi,walking slowly ya shiga bedroom ɗin,


Saman gadon Ya haye har izuwa saitin inda take akwance,emotionally yake kallon kyakkyawar fuskarta,expecially soft  lips ɗinta,tausasan gaske masu matuƙar fisgarshi,cire murfin bottle din yayi,ya tarfa ruwan a hannunshi,Ya yayyafa mata nan take ta soma sauke nauyayiyar Ajiyar zuciya,Ajiye robar yayi Saman side drawer ɗinshi,Still yayi yana kallonta,Yadda numfashinta ke fita duk in taja shi sai ƙirjinta yayi sama,da alama ta zarce da yin bacci ne,


Saukowa Yayi daga saman gadon sai da ya fara tsince Fruit ɗin da ta zubar mashi a ƙasa tare da cup ɗin data fasa duka ya tattarasu a cikin tray ɗin data zubo su, Ya kaisu palour,saman table ya ajiye plate ɗin,bayan ya ɗauki Laptop ɗinsa daya bari,bedoom ya koma bayan ya ajiye laptop ɗin,Ya ƙarasa wurin switch Ya kashe Hasken dakin,Nan take furniture ɗin suka fara haskaka ɗakin


Komawa yayi saman gadon Ya haye,tare da janyota zuwa ƙirjinshi,sosai yayi tighting ɗinta,yadda xaiji daɗin jin breath ɗinta,kamar ƴar jinjira haka sehrish ta koma a ƙirjinshi,zafin daya ji ajikinta ne ya tabbatar mashi da cewa Babu Lafiya atattare da ita,


*Boss Bature*


*AMRISH*


Sam ta kasa runtsawa sakamakon tattaunawar da taji Mommynta nayi na ɗazu da rana,Abun ya tsaya mata aranta,yayi matuƙar tayar mata da hankalinta,Kalmar akashe shi kawai take tariyowa acikin kanta,Shin wanene Mommynta ke bada Umarnin a kashe shi!!idan ma laifi yayi mata meyasa bazata haɗa shi da hukuma ba su ɗauki mataki akanshi,'Sai faman Juyi take yi asaman gadonta Sam ta gaza runtsawa,ƙwaƙwalwarta a cunkushe take


Dirar Motar da taji acikin gidansu ne yasa ta miƙe zaune,tana mai mamakin jin shigowar mota acikin gidan Adai dai irin wannan Lokacin,halan mommy ce ta fita,dama ta saba fitar dare,ta ambaci hakan acikin Ranta,Saukowa tayi daga saman gadon cikin sanɗa ta nufi hanyar fita daga ɗakinta,hannu tasa zata buɗe ƙopar taji an datseta,da ƙarfi ta dinga jan ƙopar amma ko motsi wannan batayi ba,hakan ya tabbatar mata da cewar,Mommynsu ce ta rufe ta da mukulli,


Ranta yayi mugun 6aci,kamar ta aza hannu akai ta fashe da kuka haka take ji,safa da marwa ta shiga yi acikin ɗakin,Can ta tuna da window ɗin ɗakin,Jiki na rawa ta ƙarasa gaban window ɗin,hannu tasa ta zuge glass ɗin a hankali don kada aji ƙarar buɗe ƙopar,Sai dai kash, bata iya hangen meke wakana acan down stairs,Motsin mutane ta dinga ji suna shigowa cikin gidan,Sosai ta kwallafa rai akan son ganin Su wanene ke shigowa Cikin gidan a irin wannan lokacin,tsabar haushin da taji kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu,ba don taso ba haka ta baro jikin window ɗin Ta koma Cikin ɗakin,Zuciyarta sae faman tafarfasa takeyi,


*RishRaf*


Wuraren ƙarfe 2 na dare,sunyi nisa acikin baccinsu,wannan ƙaiƙayin na jikinta ya fara takura mata,soshe soshe ta dinga yi tana karkarce fatar jikinta,A ƙarshe da raɗaɗin ya addabeta A zabure ta farka tare da miƙewa Zaune saman gadon nashi,


Har cikin kunnanshi sautin kukan sehrish ke kaimashi,A hankali ya ɗan buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci yana kallonta,lokaci guda ya miƙe zaune,Ya tasata gaba'meya yake damunki ne"yayi maganar muryarshi a kasalance,

Cikin shesheƙar kuka tace"ƙaiƙayi nake ji ajikina,ko'ina,"Ta takure kanta ajikin head board din gadon

  Moving yayi izuwa kusa da ita,sosai ya shiga jikinta,da niyar ya taimaka mata,Wurin sosa jikin nata kota samu relief,Zura hannyenshi yayi acikin rigar jikinta,nan take taji tsigar jikinta ta fara tashi,slowly ya fara shafa fatar laps ɗinta mai sul6in gaske,after ward ya gangara da hannunshi in between laps ɗinnata yana sosai mata wurin,Wani irin shock taji agigice ta ƙanƙameshi,gyara mata zama yayi ajikinshi,Ya buɗe ƙafafunta sukayi rouding waist ɗinshi,shessheƙar kukan da take yi ne ya fara disturbing ɗinshi,hakan yasa shi zura harshenshi cikin bakinta,Ya soma bata hot kissing a tsanake,ɗuff kake ji babu wannan kuka kukan da take yi,a wani irin yanayi mara misaltuwa yake shafa jikinta da sunan susa,natsuwa tayi tana recieving saƙonnin da Sgr ke aika mata a kowani sashe na jikinta,yayin da ita kuma hannuwanta ke acikin sumar kanshi,lokaci guda numfashin kowannansu ya canza,Yayin da bugun zuciyoyinsu ya ƙarfafa,moving yayi da hannayenshi waɗanda ke acikin rigarta ya zagayo dasu ta bayanta yana shasshafa bayanta,after 15 mins Ya cire tongue dinshi daga cikin bakinta,Haɗa tsinin hancinsu yayi guri guda,yayin da suka fara kallon junansu,idanuwan kowannan su ke lumshewa,ga yanayin ƙyallin hasken ɗakin da yake ƙara ƙayatar da abun,

Motsi taga yanayi da pink lips ɗinsa,da alama so yake ya furta wani abu amma ya kasa,

   yunƙurawa yayi tare da ita,suka faɗa saman lallausar mattress ɗin,kasa jurewa yayi nipple Ɗinta sai gogar mashi lips ɗinshi yake yi ta cikin rigarta,gaba ɗaya ya fara hawa kan Network,Cafka yakai ma nipple din da teeth dinsa har saida ta ɗanji zafi ta runtse idanuwanta sosai,tana cizon la66anta,tamkar jinjiri haka ya shiga sucking ɗinta tunkafin ya zame rigar,A ƙarshe ya ƙarasa zameta gaba daya har zuwa waist ɗinta sosai ya shiga jikinta,almost 20 mins kafin wani lokaci bacci yayi Awon gaba dasu,ƙankame da juna,yadda kasan Anta da Jini,


Wuraren Sallar asuba,Marshal na kwance saman gadonshi bai kaiga farkawa ba,Abbansu Ya faɗo cikin ɗakin a hargitse daga shi sai ƴar singlet da gajeran wando fari,bawan Allah duk ya rikice,tsufanshi ya fara bayyana sosai,hannunshi na ruƙe da wayarshi,

  Hawa saman gadon yayi yana bubbuga ƙafar Marshal tare da kwaɗa mashi kira"Omar!Omar!Omar?"


Can cikin kunnanshi ya dinga jin kiran Sunanshi da Abbansu ke yi,ba arziki ya farka,tunkan ya mike zaune yake kallon abbansu biji biji,kafin idanuwan nashi su washe,

"Abba lafiya"?yayi maganar muryarshi da kasala,

  Hawaye ya gani a kan fuskar abbansu,ya kasa buɗe baki yayi magana,sai dai wayarshi da yake miƙa mashi,

  Gaban marshal na faduwa yasa hannu ya kar6i wayar tare da kallon screen ɗin,Text message ne Aka turo da new number,wani irin jagwalgwalon rubutu ne acikin saƙon,

  "Abba bangane me aka rubuta a saƙon nan ba?wanene ya tura maka shi,wasu haruffa ne aka rubutasu ta yadda mutun bazai iya karanta abunda aka sanya ba,

  Cikin shesshekar kuka kamar ƙaramon yaro yace"Omar!nima bansan wanene ya tura mun saƙon nan ba,Amma inaji araina cewa JUNAID ne ya turo mun shi,Saboda yana buƙatar taimakona,'

  Shiru Omar yayi yana kallonshi,baisan ta yadda zai fahimtar dashi cewa Wannan sakon ba daga junaid bane,Taya wanda ya mutu zai turo saƙo?rashin sani ne yasa shi tunanin cewa Ɗanshi ne yayi mashi saƙon

  Lallashinshi ya soma yi"Abba dan Allah kayi haƙuri,babu abunda zai samu junaid ɗinka,wannan saƙon bana junaid bane wani ne can daban,zai iyayiyuwa ma cikin ƴa'ƴan Abokanan ka ne aka samu wani ya dauki wayar mahaifinshi ya tura maka wannan jagwalgwalon,

  Daƙyar ya ƙarasa maganar,jikinshi yayi mugun sanyi,Ya fara jin tsoran halin da suka jefa mahaifinsu,Duk ya rame yayi duhu,idanuwanshi sun faɗa,

  "Omar dan Allah ku dawomun da junaid,wlh bazan iya rayuwa batare dashi ba,na saba dashi tun yana jinjirinshi kullum a jikina yake kwana,abinci tare muke ci,Duk inda zaije ƙafata ƙafarshi,na saba dashi sosai,nafi son shi fiye da komai na rayuwata,dan Allah na roƙe ku,ku dawomun da junaid,"

  Tuni idanuwan marshal sun cicciko da ƙwalla,ji yake tamkar ya sanar dashi ainin abunda ya faru junaid,Don ya fidda rai da dawowarshi,Sai dai kash bazai iya ba,yana fargabar halin da Abban nasu zai shiga,Ya zama abun tausayi kamar ƙaramin yaro,haka ya tasa omar gaba yana yi mashi kuka,daƙyar ya samu ya shawo kanshi,harya samu ya Lafa da yin kukan yana faman sauke ajiyar zuciya

  "Abba lokacin sallah yayi,ka tashi mu tafi masallaci,daga nan sai muyi mashi addu'a,in sha Allah junaid zai kasance cikin ƙoshin lafiya,"

  Jikinshi na kerma ya sauko daga saman gadon yana tafiya ƙafafunshi.na hardewa kamar zai faɗi kasa,da sauri Omar ya sauko daga saman gadon yabi bayanshi,Don yayi mashi jagora ixuwa Bedroom ɗinshi,


Bayan ya raka abbansu ɗakinshi,Ya dawo bedroom dinshi da niyar yin Alwala,Toilet ya shiga after some minutes ya fito yana gyara agogonshi dake sanye a wuyan hannunshi,ƙarasawa yayi gefen gadonshi,ya ɗauki phone ɗinsa dake ajiye saman bedside drawer dinshi,

ƙarar shigowar message yaji ta cikin wayarshi,da Sauri yakai idanuwanshi kan screen ɗin wayar,buɗe message ɗin yayi don yaga menene,abun mamaki irin saƙon da aka turo ma abbansu ne,Wato wannan jagwalgwalon rubutun na haruffa da aka cakuɗesu,abun ya ɗaure mashi kai,amma bai kawo komai aranshi ba,fitowa yayi daga cikin ɗakin Ya nufi downstairs,tun akan benen ya dannawa Sgr kira,


Da ƙarfi kiran Ya shiga cikin wayar sgr dake ajiye gaban mirror ɗinshi,


Sehrish ce ta fara farkawa tana mutsu mutsun bude idanuwanta,zame jikinta tayi daga nashi,miƙewa tayi daga zaune tana faman sauke ajiyar zuciya yayin da take gyara zaman rigar jikinta,sai da ta samu natuwa sosai Sannan ta sanya hannunta Akan damtsen hannunshi,tana dan bubbuga shi a hankali

 Cikin sanyin murya ta soma ambaton sunanshi"Ya rafayet!Babban yaya"har cikin kanshi yake jin muryarta,daƙyar ya iya ware blue eyes ɗinshi akan fuskarta,

  Calmly tace"time ɗin salla yayi,"

Lumshe idanuwanshi ya ɗanyi,sam baccin bai ishe shi ba,sai da ya ƙara mintina kafin ya daure ya miƙe tare da saukowa daga saman gadon,Ya nufi wayarshi dake ta ringing,


Hannu yakai tare da daukar wayar,ya karata a kunnanshi tare da yin sallama 

On the other hand Marshal Omar yace"Ka sauko down zamu tafi masallaci,"

  "Okey,"ya amsa mashi tare da yin rejecting ɗin kiran,Yana ƙoƙarin mayar da wayar ya ajiye,idanuwanshi suka sauka akan message ɗin da aka turo mashi,kuma ta layinshi wanda ba kowa yasan shi dashi ba,Special ne Sai kana da mahimmanci a wurinshi sannan yake yin saving ɗin numbarka  a layin,

  Dangwala yatsanshi yayi akan Screen ɗin wayar,nan take saƙon ya sauko kasa ya buɗe,ƙura ido Sgr yayi yana kallon jagwalgwalon ruhutun da aka turo mashi,da baƙuwar number,ya ɗanyi mamakin ganin saƙon da aka turo mashi,tunani ya shiga yi kowanene da wannan shiriritar? Calling ɗin numbar yayi,nan take aka sanar dashi cewa Wayar a kashe take,Sae lokacin ya lura da lokacin da aka tura mashi sakon wuraren ƙarfe 3 na dare,bana yanzu bane,


Mayar da wayar yayi saman mirror ya ajiyeta,A hankali ya ɗan waiga tare da kallon sehrish,tuni ta jima da komawa bacci A zaune,


Toilet ya shiga,bayan ƴan mintuna ya fito tare da nufar closet ɗinshi,shiryawa yayi cikin jallabiya brown colour,gaban mirror ya koma ya feshe jikinshi da turare,tana cikin bacci taji an manna mata kiss a gefen fuskarta,da sauri ta buɗe idanuwanta don taga wanene,bata ga kowa ba,Amma ranta yana bata cewar Sgr ne Yayi mata Kiss ɗin,


Fitarshi ke da wuya,ta fara jin faɗuwar gaba,wani irin tsoro ne ya lullu6eta,motsi ta soma ji tamkar wani abu zai fito daga cikin toilet dinshi,Wani irin gurnani gurnani,da gudun gaske ta sauko daga saman gadonshi,a sukwane ta fito daga part ɗinshi ta sauko downstairs, alokacin har sun tafi masallaci,Tana ƙoƙarin giftawa ta falon muryar abusufyan ta katse mata hanzarinta

  "Daughter ina zuwa"?da sauri ta juya tare da kallonshi,yana a tsaye jikinshi sanye da jallabiya,fuskarshi na ɗauke da murmushi,Ajiyar zuciya ta sauke tare da ƙarasawa da niyar ta rungumoshi,nan take ya 6ace 6aat babu shi,

  Tashin hankali,Watsawa tayi a guje ta nufi bedroom ɗinsu,tana ƙarasawa jikin ƙopar ta sanya hannayenta duka biyun ta tura ƙopar ta shige,A lokacin Har sun Kammala sallarsu,Suna zaune saman darduma suna addu'a,

  Gaba daya suka ɗago suna kallonta,sae faman zazzare idanuwanta take yi,

  "Meya faru ne"?Oummansu ce tayi mata tambayar,ganin yadda ta faɗo dakin a fujajen babu shiri,

  Ƙarawa tayi wurinsu,gaba daya ta zube saman ƙafafunta,agaban oummansu,

Kallo ɗaya abu tayi mata,ta gane cewa akwai matsala,

  Hannu tasa ta janyota izuwa jikinta ta ɗan rungumeta,

  "Serish baki lafiya ne"?Jahad ce tayi tambayar,tana kallon sehrish ɗin dake manne jikin oummansu

  "Bana jin daɗin jikina ne,"muryarta ƙasa kasa tayi maganar,

  "Meya ke damunki ne"?ta kuma tambayarta,

  "Nikaina bansani ba,kawai bana jin daɗi"

Cike da tausayawa jahad take yi mata ya jiki,

  Hosana kuwa batasan ma wainar da ake toyawa ba,tana daga zaune gefen jahad tana gyangyaɗin bacci,dama daƙyar aka tashe ta don tayi sallah,

  Addu'o'i oummansu ta shiga yi tana tottofa mata asaman kanta,

 Dakatawa tayi da yin addu'ar,ta juya tare da kallon jahad dake a gefenta"Jahad hosana ku koma saman gado,"ta faɗi hakan ne don tasamu damar tambayar sehrish,

"To oumma," ta miƙe tare da ruko hannun hosana taja ta zuwa saman gadon,

  Ɗago da sehrish tayi daga jikinta,

"Faɗamun me yake damunki"?

  "Oumma na tabka kuskure,kin hanani na ƙara yin bincike akanta amma naqi ji,"

Cike da takaici abu tace"Hmmm ta kama ki ko"?

  ɗaga mata kai tayi alamar eh,daganan ta bata labarin abunda ya faru jiya a dakin Azmee,amma bata sanar da ita zuwanta Ɗakin Sgr ba,Don har yanzu batasan meke tsakaninta dashi ba,

  Rufe ta da faɗa abu tayi"meyasa bakin jin magana sehrish?kunnan ƙashi ko?Wannan matar da kike gani tafi ƙarfinki,Shiyasa nace ki damƙa binciken da kike yi a hannun wani,In ba haka ba zaki jama kanki ne"

  "Oumma nima bazan ƙara ba"ta faɗi hakan ne kawai ba don ta haƙura da bincikenta ba,Don tayi alƙawarin saita fallasa Azmee,Koda kuwa Zata Rasa Ranta ne,

"Tashi kije kiyi alwala"acewar oummansu,

Jiki asanyaye ta miƙe ta nufi cikin toilet ɗin,Bada jimawa ba ta fito tana faman yarfa hannunta,hijab ta ɗauko cikin wardrobe ta zura ajikinta,Sannan ta dawo saman dardumar ta kabbara salla,


Till Monday in sha Allah,


Ayi hkr da wannan,daƙyar na samu nayi shi,bana jin daɗi sai a slow,


*Ga duk mai buƙatar littafin Abban sojoji yayi mun magana kai tsaye ta layina,Amma fa whatsapp kawai banda kira,08103884440*


  



   







  






 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*







Cikin natsuwa ta kammala sallar,zama tayi saman dardumar ta ɗaga hannayenta sama tana addu'a,kafin ta ƙarasa yin addu'ar Abu ta miƙe daga kan dardumar,saman gadon ta koma daga gefe ta zauna tana jan casbaha,


Tana cikin yin Addu'ar ta tunano da wannan malamin nasu na makarantar Boko Ya Mu'allim,tabbas suna buƙatar taimakon malamai domin magance waɗannan miyagun mutanan,Shafa addu'ar tayi kafin ta miƙe tare da ɗaukar sallayar ta nannaɗe ta,Cire hijab ɗin jikinta tayi ta mayar dasu a wardrobe,


Komawa tayi gefen oummansu ta zauna,

"Oumma"ta ambaci sunanta,

"Na'am?ba zaki koma bacci bane"?

  "Zan koma,dama wata shawara nake nema a wurinki,me zai hana mu haɗa da malamai?su tayamu da addu'a,"

  Jinjina kai Oummansu ta ɗan yi"Kinyi tunani mai kyau,yakamata mu sanya manyan malamai aciki,domin kawar da waɗannan Azzaluman mutanan da suka addabi rayuwarmu,mu ma kuma mu dage da addu'a,Allah dai ya kawo mana ƙarshensu kowa ya huta,"

  "Ameen Oumma,"

Ta ambaci hakan tare da gyara kwanciyarta saman gadon ta kwanta,cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba da ita,dama jiya bata samu isasshen bacci ba,"



A 6angaren su Amrish kuwa,mommynta bata buɗe mata ƙopar ɗakinta ba,har sai wuraren ƙarfe takwas na safe,tana cikin taji mutsu mutsun za'a buɗe mata ƙopar,dama jiranta take yi,Saukowa tayi daga saman gadon ta tsaya ruƙe da qugunta tana jira a buɗe ƙopar,


Turo ƙopar Mommynta tayi hannunta ruƙe da key ɗin ɗakin,ganin Amrish tsaye a bakin ƙopar yasa ta ɗaure fuskarta"Lafiya kika wani ruƙe qugu kamar zaki dake ni"

  "Mommy yanzu abunda kika yi mun kin kyauta!kamar wata dabba dabbar ma akuya haka kika rufe ni a ɗaki batare da kinyi tunanin wani abu zai iya faruwa dani ba?meyasa Mommy?wai laifin me na aikata maki ne"?ƙarasa maganar tayi yayin da idanuwanta suka cicciko da ƙwalla,

  Ta6e baki mommyn tayi dama ba imani ta cika ba,

  "Rashin jinki ne yasa nake rufe ki a ɗaki,kin cika bin ƙwaƙƙwafin tsiya shegen sa ido,ga taurin kai,Ban isa na faɗa maki abu ki yi ba,da ace kina respecting ɗina as ur mother,da mun zauna lafiya,"

  "Shikenan Mommy in har wannan ne dalilin dayasa kike yi mun haka,Wlh zan daina......"

  Katse mata hanzarinta tayi"Zaki daina!ko kin daina,ban fahimceki ba"?

Da sauri Amrish tace"Na daina,"

  Jinjina kai Hajiya Sarat tayi"shikenan,Kin ga yanzu zamuyi zaman Lafiya dake,faɗamun me kikeso na kawo maki ki ci"?

  Yatsina fuska Amrish tayi still bata yarda da mommynta ba,

  "Duk abunda kikeso Mommy shi nake so,Yanzu dae dan Allah mommy wayata nakeso ki bani!pls mommy nayi missing ɗinta sosai,school friends ɗina duk nayi kewarsu,ina so nayi chatting dasu,"aɗan shagwa6e ta ƙarasa maganar,

  "Amrish!ni kaina bansan inda na jefa wayarki ba acikin gidan nan,Ranar kin 6ata mun raine,shiyasa Na ɗauketa,but in kinaso Zamu fita shopping atare daga nan saiki za6i wayar da kikeso,"

  Daƙyar Amrish ta ƙaƙaro murmushi akan fuskarta,

  "Shikenan mommy,Yanzu bari na shiga ciki nayi brush,"

  "Idan kin kammala brush din,Ki jira ni a dining,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta sauko Downstairs,"

  Komawa cikin ɗakin Amrish tayi,tsayawa ta ɗanyi ruƙe da qugu aranta tana faɗin"Matar nan bata da gaskiya,ko su waye suka shigo daren jiya?daga gani ba abun arziƙi suka aikata ba shiyasa suka garƙame ni acikin ɗakin kamar wani ɗan kuikuyo,"

  Ƙwafa tayi tare da nufar toilet,ta shiga ciki,

  After ta kammala,har wanka ta ɗanyi ta zura jeans da farar vest ajikinta,Saukowa downstairs tayi atsanake take tafiya,hannunta acikin aljihun wandonta irin nigogin nan,


Tana cikin tafiyar nan kwatsam taji ta taka wani abu a ƙafarta,da sauri ta ɗan ɗaga ƙafarta tare da kai idanuwanta kan abun,Wrist watch ce da alama yarda ta akayi a ƙasa,Zuƙunnawa tayi agaban agogon sai faman ƙyalli take yi da alama ta Diamond ce,

Hannu tasa ta ɗauki agogon tana jujjuyata,Aranta tana ayyana farashin agogon,Daga gani ba ƙaramin diamond bane,Don tunda ake siya mata Diamond ba'a ta6a siya mata mai ƙyalli kalar wannan ba,Agogon ta haɗu sosai,Tayi mata kyau,

  Murmushi ta saki tare cewa"Yanzu haka cikin baƙin jiya ne da suka shigo cikin gidan nan da daddare aka samu wani ya yarda ita ƙasa wanda baisan muhimmancin kuɗinshi ba,Ko kuma wanda bada guminshi aka siya agogon ba," 

Jin takun takalmin Mommynta Yasa tayi saurin,zura agogon acikin aljihun jeans ɗin jikinta

"Wlh bazan bari mommy taga wannan danƙareriyar agogon ba,Don ta burgeni da ita Zanyi Hotunan Birthday ɗina,Inyaso daga baya sai a mayarwa mai agogon kayanshi,"

  Ta ƙarasa zancen zucin tare da miƙewa ta wuce dining,Kujera taja ta zauna tana jiran ƙarasowar breakfast ɗinta,

  Shigowa area ɗin Hajiya Sarat tayi hannunta ruƙe da faffaɗan tray mai ɗauke da kayan kalacinsu,Saman table ɗin ta ajiye tray ɗin,

  Murmushi Amrish ta saki tare da yi mata sannu"

  "Yawwa Daughter,"ta amsa mata a yayin da take ɗaukar plate,warmer ta buɗe mai ɗauke da Chips ta soma zuba mata,bayan ta gama ta haɗa mata da kakkauran Tea,tare da slide bread wanda aka jerashi da wainar kwai,"

Nan fa suka hau cin abincin atare suna fira,abunda basu ta6a yi ba ita da amrish,


Wuraren ƙarfe 9,Sehrish ta farka daga bacci tana ta faman yin hamma wata irin matsiyaciyar Yunwa ce ta addabe ta,Saukowa tayi daga saman gadon babu kowa a ɗakin,duk sun fita yin breakfast,ita kaɗai ta rage,


Toilet ta shiga,shaf shaf tayi wanka after some minutes ta fito ɗaure da towel,gaban mirror ta zauna tana shafa mayukan jikinta,sai da ta kammala mulke ko'ina,Sannan ta ɗauki powder zata shafa,Kamar ance ta ɗago ta kalli mirror,kwatsam ba zato ba tsammani taga madubin ya koma mata tamkar tv,manya manyan bishiyoyi ta gani acikin daji ga wasu gwaggon burai gandara gandara masu uban gashi ajikinsu,Sae miƙo mata hannu suke yi ta cikin madubin suna kiran Sunanta"Sehrish kizo,Sehrish kizo"shi ne abunda suke faɗi


Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,Idanuwanta suka firfito waje tamkar ƙwayar idonta zata faɗo ƙasa sai kuma taga madubin ya koma lafiya lau,jikinta na kerma ta miƙe ta bar gaban madubin,Da sauri da sauri ta buɗe wadrobe ta ɗauko jallabiya ta zura ajikinta,Mayafin ma a hannu ta ruƙe shi,ko takalmi bata sanya a ƙafarta ba,Gudu gudu sauri sauri ta fito daga cikin ɗakin,


Lokacin da ta ƙaraso dining area din gaba ɗaya ta samu kowa zaune suna cin breakfast ɗinsu,tun daga kan Daddynsu Abusufyan,Oummansu da kuma su Hosana da Jahad,Ga Abba kuma tare da Mommynsu Alex,sai su twins da fawan kanal yousouf dasu Jabeer,Ganin Azmee tayi atsaye tana yin serving ɗinsu,Nan fa ta ƙara shan jinin jikinta,


Jiki asanyaye ta ƙarasa dining ɗin,hankalin kowa ya dawo kanta,

Fuskarta ɗauke da murmushi ta soma gaisar dasu"Abba ina kwana"

"Lafiya lou ƴan matan Abusufyan"murmushi ta ɗan saki tare da kallon Mommy"ina kwana mommy an tashi lafiya,

  "Lapiya lou Daughter,"

Komawa tayi kan Daddynsu"Ina kwana daddy kun tashi lafiya,"

Fuskarshi ɗauke da murmushi Ya amsa mata"lafiya lou daughter,An sha bacci ko"?

  Dariya sehrish ta ɗan yi tare da kallon Oummansu ta gaisar da ita,Sai da tabi kowa ta gaisar dashi,tana ƙoƙarin zama Abusufyan yace'baki ga Aunty Azmee bane?naga kamar baki gaisar da ita ba,"

  Jimm ta ɗanyi kafin ta wurga eye balls ɗinta kan fuskar Azmee dake tsaye,murmushi ta samu akan fuskarta,

Ba don taso ba hakanan ta daure ta gaisar da ita"ina kwana Aunty Azmee,"

"Lafiya lou Sehrish,Yanzun nan nake shirin zuwa na taso ki sai gashi ma kin fito"

  Baki asake Abu da sehrish ke kallonta,Ta ƙware wurin iya kisisina da munafurci,

  Banza sehrish tayi,batare da ta tanka mata ba,

  Zagayowa Azmee tayi wurinta tare da kai hannu ta ɗauki plate,Warmer ta buɗe mai ɗauke da farfesun Ƴan cikin shanu,Ta zuba ma Sehrish ta tura mata shi agabanta,

  Zuƙunnawa tayi daidai saitin kunnan sehrish cikin raɗa tace"Nasan zaki ji daɗin shan farfesun nan,"

  Tana kai ƙarshen maganar ta miƙe daga tsaye,kallon Oummansu tayi da ido tayi mata alamar ta kwantar da hankalinta,

Ajiyar zuciya ta ɗan sauke tare da zura yatsun hannunta cikin plate ɗin,A tsanake ta soma shan farfesun ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,


Sai da ta nutsa cikin shan farfesun ta dinga jin motsin wani abu a hannunta,duk in takai hannu zata ɗebo ƴan cikin sai taji suna kufce mata daga hannunta kamar abu mai rai,hakan yasa takai idanuwanta cikin plate ɗin,Tsutsotsi ta gani suna yawo acikin plate ɗin manya manya,A wani irin firgice Sehrish tayi wurgi da plate ɗin ta fasa Uwar ƙara,Nan take ta shiga kwarara Amai,

Gaba ɗaya hankalin Kowannansu Ya tashi haiƙam,Mikewa tsaye su kayi suna kallonta,kowa na tambayar Lafiya,Da ƙarfi take ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Wayyo Allah na,Na bani na lalace Daddy,Oumma ku taimake ni,Naci tsutsotsi acikin cikina,

Tana magana amai na zuba daga bakinta,duk ya 6ata gaban rigarta jaga jaga,duk tabi ta gigice ta rikice,Watsa wa tayi da gudun gaske tana kuka ta nufi bedroom ɗinsu,A guje Suka bi bayanta 

Toilet ta faɗa cikin fitar hayyaci ta nufi basin,Cigaba da kwarara aman tayi har saida takai ga babu abunda ke fitowa bakinta sai ɗigon jini ta ƙarar da koma da taci ko ruwa babu a cikinta,

  Soso ta ɗauko tare da detergent ta zazzaga shi abakinta,Adai dai lokacin suka ƙaraso ƙopar toilet ɗin,sunyi ƙoƙarin su tura ƙopar amma ƙopar ta datse sakamakon Bugata da sehrish tayi bayan ta shiga,Ƙwanƙwasa ƙopar suka shiga yi kowa na ambaton sunanta,

  'Sehrish!kizo ki buɗe mana ƙopa,kada ki Lahanta kanki fa,"muryar Oummansu ce keyi mata magana,tamkar zata fashe da kuka 

Abusufyan ma murya na kerma yace"Wai baza ki buɗe mana ƙopa ba?meyake damunki ne?Dan Allah Daughter ki fito kiyi mana bayani,"

Kwata kwata Sehrish bata jinsu domin kuwa ta jima da makancewa,Ta fita hayyacinta,abunda ta gani a plate ɗinta keta dawo mata cikin kanta,

  Tura soson tayi abakinta,Ta dinga gurzar bakin,har saida Le6enta suka faffashe jini ya soma zuba ta ko'ina abakinta,daga waje suka dinga jin Azababben kukan da Sehrish ke yi,na tashin hankali,

  Da gudun gaske Abusufyan yabar ɗakin kaitsaye ya nufi upstairs don ya sanar da Sgr,Suzo su 6alle ƙopar kada ta kashe kanta,


Lokacin da ya shiga Part dinshi ko sallama babu,faɗawa kawai yayi gudu gudu sauri sauri ya shiga bedroom ɗinshi,Sai faman haki yake yi,A kwance ya sameshi yana bacci jikinshi sanye da jallabiya,

  Tun kafin ma Ya ƙarasa wurin gadon ya shiga ƙwala mashi kira"Rafayet!Rafayet!!"

  Farkawa Sgr yayi lokaci guda ya wurga idanuwanshi masu ɗauke da bacci kan Abusufyan dake ta kwala mashi kira,

  "Uncle lafiya"?

"Ina fa lafiya!Ga sehrish can zata kashe kanta acikin toilet,bamu san meke damunta ba,sai ihu take tana kuka,Munyi munyi mu buɗe ƙopar ta datse ta,"

  Tunkafin Ma Abusufyan yakai ƙarshen maganarshi,Sgr ya sauko daga saman gadon,da wani irin sauri ya fito daga part ɗin,gudu gudu sauri sauri Ya nufi bedroom ɗinsu,Abusufyan kuwa bai baro Upstairs ɗin ba sai da ya wuce ɗakin Omar ya taso shi daga baccin don abun kowa ta shafa,


Lokacin da Sgr ya ƙaraso ɗakin abun ya tashi hankalinshi sosai,Tunda ya shigo corridor ɗin ɗakin Ya fara jin sautin kukan da sehrish keyi,Tamkar ana zare ranta daga jikinta,

  A sukwane ya faɗa cikin ɗakin,Ganinshi yasa suka matsa mashi daga wurin ƙopar,A zafafe ya daddage ya bangaji ƙopar da ƙafaɗarshi,Nan take ƙopar ta buɗe,Faɗawa cikin toilet ɗin yayi a lokacin Harta yanke jiki ta faɗi ƙasa,jinin da ya gani jaga jaga ajikin basin ɗin ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba,inda take kwance kasa ga soso nan a gefenta ga kuma ledar detergent ɗin da ta fasa,Bakinta yayi jaga jaga da jini fatar le6enta ta munana duk rauni,

  Jikinshi Yayi mugun sanyi,yaso ace tun lokacin da ta fara haukan suka sanar dashi,slowly ya zuƙunna agabanta,tare da kai hannu ya tallabo kanta,da hannu ɗaya,Ɗayan hannun kuma zura shi yayi cikin bakinta Ya buɗe shi,runtse idanuwanshi yayi yayin da zuciyarshi ke ta faman tafarfasa,harshenta gaba ɗaya ya faffashe,detergent ɗin yayi mata illa sosai,duk ya sale fatar harshen nata,Yaji raɗaɗin abun har cikin zuciyarshi,miƙewa yayi azafafe ya juya yana kallonsu dayake duk sun shigo cikin toilet ɗin,Oummansu sai kuka takeyi,Haka su Jahad da Hosana ma,

  "Tun yaushe ta fara wannan abun?meyasa ba'a sanar dashi ba!"a ruɗe yayi maganar 

  "Rafayet yanzu duk ba lokacin wannan bane dan Allah ka taimaka,kada mu rasata,"Abbansu Yayi maganar fuskarshi duk a hargitse


Juyawa yayi tare da sanya duka hannayenshi ya ɗaukota tare da ɗaurata saman kafadarshi,Ya fuce da ita daga ɗakin,A hanzarce Ya haura da ita Upstairs part ɗinshi,A saman gadonshi ya kwantar da ita,da sauri ya kuma saukowa down bayan ya ɗauki key Ya nufi medical Room ɗinsu,da kanshi Ya shiga duba Sehrish koda ta farfaɗo tana koke koke Allurar bacci yayi mata,



kowa ya shiga damuwa,abincin ma duk sun ƙoshi dashi,A ƙarshe saman Sofa kowa ya zauna cike da jimamin halin da Sehrish ta shiga,Abun ya ta6a masu zuciyarsu sosai,

Har lokacin abu bata daina kuka ba,Haka Jahad da Hosana ma 

  "Dan Allah ku kwantar da hankalinku,In sha Allah Sehrish zata samu lafiya,"acewar Kanal yousouf,

  "Kusan kashe kanta tayi fa,Omo ta zuba abakinta ta wanke da soso,Ni bansan meke damunta ba,Sae faman ambaton tsutsa takeyi ni banga komai ba a plate ɗin abincinta,"Abusufyan ne yayi maganar idanunshi cike tab da kwalla,

"Dole akwai wani abun dake damunta,ni tsorona ma kada ta Zauce"

  Abba da Mommy sai kwantar musu da hankali suke yi,

 

Hannun Abu sae kerma ya ke yi,acan ƙasan zuciyarta kuwa,tunanin yarda zata fallasa Azmee take yi don tasan cewa itace Silar Halin da Sehrish ke ciki,tayi jinkiri ne saboda bata jima da zuwa gidan ba,ba lallai bane su yarda da maganarta ba,


Miƙewa Tayi tare da kama hanyar zuwa kitchen,tana shiga ta samu Azmee tana gyara kitchen ɗin,hankalinta kwance,

"Meyasa kika yi mata haka"?ɗagowa Azmee tayi tare da kallon abu dake tsaye,lokaci guda ta saki murmushin gefen fuska tare da cewa"Bangane akan me kike magana ba"

  "Amma baki da Imani!munafuka mai fuska biyu,kina son ki cutar da ita ne saboda kina tsoran karta tona maki asiri,shiyasa kike ƙoƙarin kashe mun ita"tana magana hawaye na zuba akan fuskarta,,

  Girgiza kai azmee tayi"ko kusa ni bani da alaƙa da Abunda ya faru da Sehrish!kada kiyi mun ƙazafi,Ni bazan iya cutar da Sehrish ba,Saboda ina jinta tamkar ƴar cikina....."

Tunkan takai ƙarshen maganar a fusace abu tace"karki kuskura ki ƙara kwatanta sehrish da ƴar cikinki!mushirika kawai,muguwa kuma azzaluma!Makira!Ni bana jin tsoronki,Da Allah na dogara ba da wani tsubbace tsubbace ba irin naku,waɗanda suka jahilcewa addininsu,har yaushe ne zaku gane gaskiya ku daina aikata irin wannan mummunan zunubin da kuke aikatawa ne?Kuna ɗaukar kanku tamkar wasu shaggu saboda kawai kuna taƙama da tsafin da kuke dashi,In banda ma daƙiƙanci da jakkanci da jahilci irin naku,Kun manta cewa Allah shi ya halicce ku kuma a kowani lokaci zai iya ɗaukar ranku,Kuma zaku koma gareshi sannan ku gir6i abunda kuka shuka,akwai ranar da wannan sihirin da kuke taƙama dashi bazai ta6a amfanarku ba!tunda baku isa ko mutuwa ku hana kanku ba....."

Tunkan ta ƙarasa Maganar Azmee ta daka mata tsawa har sai da abu ta girgiza"Ya isa haka!ke baki isa ki ce zakiyi mun wa'azi ba!Idan ilimin addini kike taƙama dashi,ko ƙafata baki kama ba!ke kinsani basai na faɗa maki ba,Idan da naso tun lokacin dana zo gidanki yi maki wankan jego da tun lokacin Na murƙushe ki ke da ƴa'ƴan naki,Amma banyi hakan ba don baki acikin ainihin abun hari na,Idan har kika cika zaƙewa Wlh Zaki rasa Rayuwarki ne!Zanyi silar da zaki bar duniyar nan ne!

  "Raina ba ahannunki yake ba!A hannun Allah yake,Idan har kinga na mutu to lokacina ne yayi,kuma koda ace Na mutu ta silarki,inaso ki sani kema wata rana zaki zo inda nake ne,kuma zaki yi bayani ne,banza kawai,ina ilimin da kike taƙama dashi ne?ai dake da dabba duk ɗaya kuke dan wlh ƙwara dabba dake Azmee,ita haka Allah ya halicce ta,Amma ke fa?mutunce wadda ta sani ta take sanin,ko yau kika faɗi kika mutu kinsan makomarki,babu ruwan Allah da ilimin da kike dashi,in har bakiyi aiki dashi ba,Toh ya tashi abanza don azabar da za'ayi maki ranar gobe ƙiyama tafi azabar da za'ayiwa kafiri,"

  Lokaci guda Azmee ta juye tamkar ba ita ba,ta fito da ainihin suffarta ta mugaye marasa Imani,Idanuwanta sunyi jawur dasu wani kalar huci ke fita daga bakinta da hancinta,Kalaman Abu sun ƙona mata rai,Kamar ta shaƙo wuyanta haka take ji,

  "Ki fita ki bani wuri Zainab!tunkafin Nayi maki Illa"

  A harzuƙe abu tace"kiyi duk abunda kika ga dama Azmee,Wlh bazan ta6a karaya ba,koda kuwa zan rasa rayuwata saina tona maki asiri mushirika kawai,"abu nakai ƙarshen maganar,taja dogon tsoki ta juya a fusace tabar kitchen ɗin,


Komawa Azmee tayi saman ɗaya daga cikin kujerun dining na kitchen ɗin ta zauna,maganganun abu ta shiga tariyowa acikin kanta,tunda take a rayuwarta Wani ɗan adam bai ta6a fuskantarta ba,Ido cikin ido ya gaya mata baƙaƙen maganganu ba,in ba abu ba,Itace ta farko kuma ta ƙarshe don taci alwashin duk wanda yayi yunƙurin exposing ɗinta saita Kashe shi har LAHIRA,


Runtse idanuwanta tayi lokaci guda ta shiga tunanin Sehrish,sam bataso hakan ta faru da ita ba,ta ƙetare Iyakarta ne shiyasa Ta jefa ta a halin da take ciki,


Da sallama Omar ya shiga part din nashi,A lokacin Sgr yana ta Zarya acikin bedroom ɗin,lokaci bayan lokaci yakan juya ya kalli Sehrish dake kwance tana bacci,Ba ƙaramin jiki taji ba,don ma Allah Yasa ta samu emergency treatment a wurinshi,Da ba'a son me zai biyo baya ba,


Sam baiji sallamar da Omar yayi mashi ba,har saida ya Ambaci sunanshi"Rafayet"tukunna ya juyo tare da kallonshi,

  Ƙarasawa wurinshi Omar yayi tare da dafa kafadarshi,

  "Ya jikin nata"?

"tana samun sauƙi,nayi mata allurar bacci ne,in ba haka ba bazata daina firgitar da take yi ba,"

  Ajiyar Zuciya Omar ya sauke tare da cewa"Allah ya bata lafiya,amma meke damunta ne?

"I don't even know,jira nake ta farka,Don in tambayeta,nasan zata faɗamun meke damunta,me take gani ne da yake razanar da ita,"

  "Haka ya dace,ƴan uwanta na son ganinta,Zasu iya shigowa yanzu?"Omar yayi tambayar yana kallonshi,

  Girgiza mashi kai yayi alamar a'a,sannan yace"sai dai zuwa anjima idan taji sauƙi,"

  Omar yace"Okey,"harya juya zai fita ya kuma juyowa,

  "Ya maganar Haroon"?

Sgr yace"Still bai farfaɗo ba,Nasan zuwa anjima zai tashi,"

  Gyaɗa kai Omar yayi tare da juyawa ya fuce daga ɗakin,'

  


Wuraren Sallar Azhar gaba ɗaya suka tafi masallaci,Ya rage saura matan Acikin gidan,


Abu sam ta kasa samun natsuwa,gashi batasan ina aka kwantar da Sehrish ɗinba balle taje dubata,basu jima da kammala sallar Azhar ba,Abu ta mike tare da kallon Jahad"Inaso naga sehrish,gashi bansan inda aka kwantar da ita ba,

  Jahad tace"Tana a ɗakin Ya rafayet,nima inason na ganta,"ta ƙarasa maganar tare da miƙewa,hosana ma ta miƙe"Nima zanje ganin rishi ɗin,"


Kowannansu sanye da hijabi,Atare suka nufi upstairs,Da sallama suka shiga falon babu kowa,kaitsaye suka wuce bedroom ɗinshi,daga ciki suka shiga,gwanin ban tausayi haka suka tsaya cirko cirko abakin gadon suna kallonta,Tana bacci tana firgita,Numfashinta na fita daƙyar daƙyar,


Zama Oummansu Tayi daga gefen gadon Yayin da su Jahad ke atsaye,idanuwansu cike tab da kwalla,

  "Oumma wai meke damun rishi ne?duk tabi ta furgice ta fita hayyacinta,"

Hosana ce tayi maganar cikin shessheƙar kuka,

  Abu tace"ku tayata da Addu'a in sha Allah zata samu sauƙi ne,"

  Jahad tace"wlh dama ciwon ya dawo jikina,ita ta huta,Saboda taji jiki ba kaɗan ba,"

   Hannu abu tasa tare da shafa fuskar Sehrish,aikuwa kamar jira take yi taji an ta6ata nan ta fara sambatu da muryarta da bata fita sosae saboda ciwon cikin bakinta tana faɗin"ku kira mun shi,dan Allah ku kira shi,Ya mu'allim nake son gani,"lokaci guda kuma tadaina sambatun

  Kallon juna sukayi cike da mamaki,har suna haɗa baki wurin cewa"Ya mu'allim kuma?Wanene Shi"?

"Jiya tayi mun magana akanshi,Wai wani malaminsu ne Ya mu'allim,Ta sanar dani cewa Ya ta6a taimakonta,ko kunsanshi ne"?Tayi tambayar tana kallonsu jahad,

  "Ni ko sunan ma banta6a ji ba,"acewar hosana,

  Jahad tace"bazamu iya sanin malamin da take magana akai ba,tunda ba wurinmu ɗaya ba,"

  Addu'a suka shiga yi suna tattofa mata ajikinta,basu bar ɗakin ba sai wuraren sallar La'asar,Suka tafi banda hosana,tana zaune gefenta,ta kasa ta tsare sai rishi ɗinsu ta farka,


Bayan sallar La'asar,Abusufyan tare da Abba Suka shigo cikin ɗakin,a bakin gadon suka tsaya suna kallonta,A lokacin hosana ta fita daga ɗakin

"Banji daɗi abunda ya faru ba,Allah Ya bata lafiya,"cike da jimami Abba yayi maganar,

Abusufyan yace"tabbas akwai abunda ke damunta,tana faɗin abunda mu bamu gani ba,kuma a sanadin hakan ta kusa lahanta kanta,In har bamuyi kokarin gano abunda ke damunta ba,za'a iya samun matsala,"yana kai ƙarshen maganar Abba yace"in sha Allah hakan ma bazata faru ba,Yanzu dai ita muke jira ta farka sai muji daga bakinta,Tayi mana bayanin abunda ke damunta,"


Sunjima suna tattaunawa,Anan su kanal Yousouf da sauran matasan gidan suka same su,Kowa ya shigo ɗakin sai ya yi ma Abusufyan ya jikin Sehrish,daga bisani bayan Sgr Ya dawo ne suka ɗan basu wuri,Ya jima yana jiran farkawar Sehrish Amma babu alamun baccin nata zai ƙare,


Wuraren karfe 8 na dare,Sgr da Omar suka nufi Medical room ɗinsu Wurin Haroon,Lokacin da suka shiga a kwance suka same shi yana ta faman Jan numfashi,Idanuwanshi sunyi jawur dasu jikinshi sai kerma yake yi,


Tsayawa Sgr yayi tare da goya hannayenshi saman ƙirjinshi,Omar kuma wuri ya samu gefen gadon Ya zauna yayin da idanuwanshi ke akan Haroon

   "Ya jikin naka"?

Ba ƙaramin mamaki yayi ba,jin Omar yayi mashi ya jiki,yayi tsammanin da bugu zasu fara tambayarshi,

  Daƙyar ya iya buɗe baki Yace"babu sauƙi,Naji jiki sosai,Rafayet baiyi mun da sauƙi ba jiyan nan,dan Allah Ya Omar ka taimaka mun nasan kafi shi sauƙin kai,wlh ni babu ruwana kashe Junaid da nayi ma kuskure ne,Sharrin shaiɗanne,In fact ni bayin kaina bane....."a fusace Sgr Ya daka mashi tsawa"Idan ka kuskura ka sake ambaton shaiɗan a wurin nan saina Canza maka kamanni,akwai wani shaiɗanin daya wuce kaine"?

  Shiru yayi batare daya kuma cewa komai ba,Don bazai manta da lugudan wahalan daya shaba Adaren jiya,

A tsanake Omar ya soma magana"amsa ɗaya kawai nakeso a wurinka!Wanene yake baka Umarni?

  "Wlh bazan Iya faɗa maku ba,Ae ko ban sanar daku ba,in har rafayet zai iya sanin duk wani abu da nake aikatawa,Sanin wanda ke bani Umarni bazai gagare shi ba,Yasan Komai"

Haushi kamar ya shaqe shi haka yake ji,daƙyar ma yake magana saboda raɗaɗin ciwon da yake ji,Ga Yunwar da yake ji,ba don Omar ya hanashi Dukanshi ba,da ba abunda zai hana ya karairaya ƙasusuwan Jikinshi,ya tsani haroon kamar mutuwarshi,

  "Rafayet baisan komai ba,kai nakeso ka sanar dani!Haroon ka amsa mun tambayata,kai da Uban wanene kuke aika aika acikin gidan nan?"

Shiru haroon yayi,A hasale Sgr ya ɗaga Hannu zai mauje mashi kai,Omar yayi saurin ruƙoshi,"just leave him,Idan bai amsa mana ba,Wayar shi zata bamu amsa,"

  Basu bar ɗakin ba sai da suka ɗaure haroon jikin gadon sosai,Suka rufe bakinshi,Yarda baza aji Sambatun shi ba"

Datse ƙopar ɗakin Sgr Yayi,Sun jima suna tattaunawa da Omar kafin Ya wuce upstairs,Omar kuma ya nufi sashen su Abbansu,


Lokacin daya shiga bedroom ɗin,Still Sehrish bata farka ba,toilet Ya shiga,After some minutes ya fito sanye da bathrobe da alama wanka yayi,gaban mirror ɗinshi Ya tsaya yana kallon kanshi ta mirror,Abubuwa dayawa suna yi mashi yawo akanshi,yanzu baida burin daya wuce ya kawo ƙarshen maƙiyansu cikin kwanakin nan,da zarar ya gama dasu Zai fara tunanin komawa U.S,


Yana cikin zancen zucin nan,Ya fara Jin numfashin Sehrish dake fita da ƙarfi da ƙarfi,Da sauri Ya koma gefen gadon Ya zauna yana kallonta,A hankali ta soma ƙoƙarin buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,biji biji ta fara ganinshi,har sai da ta sanya hannunta saman fuskarta tana mutsustsuka idanuwan tukunna ta samu damar ganin shi da kyau,kwata kwata Jikinta babu ƙwari daƙyar ta samu ta miƙe zaune,Ciwo na yini ɗaya amma duk ta rame,idanuwanta duk sun faɗa,lips dinta sun dan kumbura,jikinta sai kerma yake Yi,


"How was ur body"?yayi tambayar Yana kallon Clavicle ɗinta,

Shuru bata bashi amsa ba,Sai dai zuba mashi ido da tayi tana kallonshi,Sake maimaita mata yayi"Ya jikin naki,"nan ma shiru bata bashi amsa ba,Cike da mamaki yace"Baki ji ina magana ba"

  Tunawa da ciwon bakinta ne yasa shi yin shiru,don yasan bazata iya magana ba sai a hankali,

  "If u can't talk to me,zaki iya yi mun alama ta yarda zan fahimci abunda ke damunki,"

Lumshe idanuwanta tayi tare da buɗesu a hankali

  "Are u hungry"?. 

Da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a,ba don taso ba,ita kaɗai tasan halin da take ciki,Ga matsiyaciyar yunwa tana ji amma fargabar abunda zata ƙara gani acikin abincinta take ji,

  Moving yayi kusa da ita,tare da sanya tafin hannunshi ya ruƙo kanta,A saman ƙirjinshi ya kwantar da ita,nan take taji natsuwa ta zo mata,hawaye ne suka soma zarya akan fuskarta,taso ace zata iya buɗe baki ta sanar dashi ainihin abunda ke damunta amma ta kasa,harshenta Ya raunata sosai,magana ma wuya take yi mata,

Shafa sumar kanta ya soma yi har izuwa tsakiyar bayanta,sosai ta manne mashi tana shaƙar kamshin jikinshi,

  "I really worried about it,pls Tell me what scared you?meyasa kike firgita"?

  Yayi maganar tare da mayar da hannunshi saitin zuciyarta dake ta bugawa da ƙarfi da ƙarfi,tunda ya aza hannun kuma sai heartbeat ɗin nata ya dai daita,

  Ƙanƙameshi tayi sosai,tana ji aranta kamar bazata rayu ba,tun da ta fara wannan ƴan gane ganen na tashin hankali,

  Waist ɗinta Ya ruƙo tare da Janyeta daga jikinshi,Miƙa hannunshi yayi gaban drawer chest,Ya curo biro tare da jotter,

  Miƙa mata yayi tasa hannu biyu ta kar6a

  "Ki rubutamun duk wani abu dake damunki anan,"

  Hannunta na kerma ta buɗe empty page ta soma rubutu,bayan ta kammala ta miƙa mashi jotter ɗin

  Hannu yasa ya kar6a yana karantawa

_Oumma tasan komai,Ka tambayeta zata faɗa maka abunda ke damuna_

Wannan shi ne abunda Sehrish ta rubuta mashi,


ɗagowa yayi tare da kallonta suka haɗa ido,hannu ya zura cikin front pocket ɗinsa Ya zaro wayarshi,Nan take ya kira Fawan ya sanar dashi cewa Ya kira Mashi Oummansu,


Miƙewa Yayi ya nufi cikin ɗakin,sai gashi ya dawo sanye da sleeping dress ɗinshi riga da wando Maroon colour,Gefen gadon Ya koma ya zauna yana jiran zuwan Abu,


Kusan 15 mins,Abu tayi sallama a ƙopar ɗakin,

  "Assalamu alaikum,"

"Wa'alaikum salam,"ya amsa mata tare da bata izinin shiga daga ciki,


Tana sanye da hijab ajikinta,Tunkan ta ƙarasa Sgr ya mike tare da janyo mata chair ɗin dake gaban dressing mirror ɗinshi ya ajiye mata ita,Tunda ta shigo ɗakin idonta ke akan Sehrish,Ba ƙaramin daɗi taji ba da sehrish ta farka,da alama jikin nata da sauki duk da akwai sauran ciwo atattare da ita,

  "Ya jikin naki"?tayi tambayar bayan ta zauna,shiru Sehrish bata ce uffan ba,Hakan yasa ta ɗan tashi hankalinta,

  "Kada ki damu,ba zata iya magana a yanzu ba,saboda raunin dake abakinta,

  Ajiyar zuciya abu ta sauke kafin tace"Allah ya baki lafiya,"

"Ameen"ya amsa mata amadadin Sehrish ɗin,don ita sai dai ta ɗaga kai,

  gaisar da ita Sgr yayi cikin girmamawa,ta amsa mashi fuskarta asake,

  "Inaso ki faɗamun meke damunta ne"?

  Buɗe baki abu tayi zata yi magana kenan taji anshaƙe mata maƙoshinta,runtse idanuwanta tayi tana ambaton Sunan Allah acikin Zuciyarta,

  "Be calm and answer me pls"Ya faɗi hakan ne don Ya lura tamkar bata a cikin natsuwarta,Sehrish kuwa hankalinta ya tashi ganin Oummansu ta kasa buɗe baki tayi magana,tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla,

  Wasu addu'oi abu ta shiga jerowa acikin bakinta,da ƙarfi da ƙarfi,bata daina ba har sai da Maƙoshinta Ya buɗe,nan take zufa ta wanke mata fuskarta,miƙewa Sgr yayi cikin sauri ya shiga palour,within secs ya dawo hannunshi ɗauke da bottle water,zama yayi tare da cire murfin ya miƙa ma Abu,hannu biyu tasa ta kar6a,kusan rabin ruwan ta shanye,janye robar tayi daga bakinta,har lokacin tana cigaba da karanto addu'o'in neman tsari a wurin ubangiji don ta gane cewa so ake a hanata magana,gashi ita kuma gwana ce wurin yin ibada, da kuma yin azkhar da sauransu,zaiyi wuya sihiri ya kama irinsu wani lokacin sai dai suci wahala,

 Lokacin da taji zata iya magana,da sauri ta soma bayyana mashi halin da sehrish ke ciki"tun jiya da ta shiga ɗakin Azmee bata ƙara samun natsuwa ba,ta sanar dani cewa tana ƴan gane gane,wasu abubuwa nayi mata gizau,kamar ɗazu da safe lokacin da muke cin abinci,Sehrish ta dinga sambatu tana faɗin tsutsotsi ne acikin plate ɗinta,har tayi wurgi da plate ɗin ta watsa da gudu ta shiga ɗaki,wannan ne silar data rikice ta shige toilet tana wanke bakinta da Omo da soso,kamar yarda ka gani....."

  Dakatawa ta ɗan yi da yin maganar tana faman sauke ajiyar zuciya,Sehrish sai murmushi take yi farin ciki kamar ta miƙe ta rungume Oummansu,

  Shiru Sgr yayi yana kallonta yayin da yake nazarin wani abu acikin brain dinshi,bakomai ya faɗo mashi arai ba face daren jiya da Sehrish tazo ɗakinshi ta tsorata harta yi wurgi da plate ɗin hannunta,tana fadin Ya rafayet maciji kunama zasu harbeka,anan ya gane cewa Bayan ta fito daga ɗakin Azmee ne ta shigo ɗakinshi,

Jinjina kanshi ya ɗan yi tare da cewa"Kina Zargin Azmee"?

  Da sauri abu ta ɗaga mashi kai Alamar eh,

  "Meyasa kike zarginta"?

 "Saboda na santa,lokacin dana  haifi su Sehrish,Itace Ƴar uwar  sayyadi wadda tazo yi mun wankan jego,"

  Tunkan takai ƙarshen maganar Sgr yace"Kenan ita ƴar uwar shi ce?",

  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,murmushin takaici Sgr ya saki,

Yana ƙoƙarin buɗe baki ya kuma tambayarta,Yaji Sehrish ta ruƙo hannunshi,da sauri yakai idonshi wurinta,

  Da hannu ta dinga yi mashi Alamar ya miƙo mata jotter dinnan zata yi rubutu,

  Hannu yasa ya dauki jotter ɗin tare da mika mata,dama biron na hannunta,

   Zane yaga tana yi maimakon rubutu bayan ta kammala ta mika mashi jotter ɗin,

  Hannu yasa ya kar6a tare da kallon abunda ta zana,Zobe ne ta zana,bai gane me take nufi ba,

  "Zan iya ganin me ta rubuta?"abu ce tayi tambayar,

  Miƙa mata jotter din 

Yayi tasa hannu ta kar6a,koda abu taga zanen sai ta tuna da binciken da Sehrish ke yi dangane da Junaid,dayake ta bata labarin mutuwarshi,baiwar Allah tana so tayi mashi maganar Junaid ɗin ta kasa,Gashi ita kuma abun ta manta bata sanar dashi ba,

  "Kin gane me take nufi"?

Jinjina kai abu tayi kafin ta ɗaura da bayani"Ta sanar dani komai daya faru dangane da mutuwar ƙaninku Junaid!"tunda sgr yaji ta ambaci junaid,hankalinshi gaba ɗaya ya koma kanta,

  "Akwai wata rana da ta shiga ɗakin Azmee,zatayi sallah tana ƙoƙarin ɗauko hijabi acikin wardrobe ɗin ita azmeen,Sai ga zoben ƙaninku na Diamond ya faɗo daga cikin wardrobe ɗin,A binciken da sehrish tayi ta gano cewa tare da zoben nan Shi Yaron ya fita aranar da al'amarin ya faru kuma abun mamaki Zoben nan nashi baiyi komai ba!babu alamar wuta taci shi!"

  Gaban Sgr ne ya faɗi rasss!ya ware idanuwanshi gaba ɗayansu,Abun ba ƙaramin girgiza shi Yayi ba,jikinshi har kerma yake yi,aruɗe yace"Taya akai Ita reesh ɗin tasan cewa tare da zoben Ya fita aranar'?

  "Ta hanyar hotunan da suka ɗauka tare da Junaid a wayar Jahad,"

  A hanzarce Sgr ya ɗauki wayarshi tare da dannawa Fawan kira,tana fara ringing ya ɗaga kiran,

  "Fawan Am sorry na takura ka ko"?

  On ther hand fawan yace"A'a babban Yaya,baka takuramin ba,"

  "Idan kana kusa,pls inaso ka kira mun Jahad,ka sanar da ita cewa tazo mun tare da wayarta da kuma wayar Sehrish ina buƙatar ganinsu,"

  "Toh babban Yaya"yana kai ƙarshen maganar ya ajiye wayar,zuciyarshi sai faman tafarfasa take yi,ita kanta daurewa kawai takeyi saboda maƙoshinta da ake ƙoƙarin shaƙewa ta dage sai ta faɗi gaskiya,koda kuwa Rai zaiyi halinsa,


 Bayan wasu mintuna,Jahad ta faɗo ɗakin da sallama a bakinta,jikinta sanye da dogon hijabi,yayin da hannunta ke ruƙe da wayarta da kuma wayar sehrish,

 Atare suka amsa mata sallamar,shiga cikin ɗakin tayi,gaba daya idanuwanta na akan Sehrish zaune tana ta murmushi,wani irin farin ciki ne ya lullu6e Jahad,

  "Sehrish Ya jikin naki?na damu sosai akan halin da kika shiga"

  "Jahad Rishi bazata iya magana ba a yanzu,ki tayata da addu'a,"acewar Oummansu,

 Jikin Jahad ba ƙaramin sanyi yayi ba,miƙa mashi wayoyin tayi,Yasa hannu ya kar6a,danna wayar Jahad ya shiga yi,direct ya shiga Gallery ɗinta,

  ɗagowa yayi tare da kallon Jahad"Ina hotunan da kukayi keda junaid aranar da kuka fita shan ice cream"?

  "Suna acikin Gallery ɗina,daga ka shiga zaka gansu,"

  "I did not see anything,ko kin gogesu ne"?

  Gaban abu ne ya faɗi rass,Ita kanta Sehrish saida hankalinta ya tashi,

  Jahad tace"Wlh ya rafayet ban gogesu ba suna acikin wayata,ko yanzu haka kafin nazo nan hotunan nake kallo"

  Miƙa mata wayar yayi"nuna mun su,"

  Bayan Jahad ta kar6i wayar,ta shiga neman pictures ɗin gaba ɗaya an goge mata su har vedios din daga cikin wayarta,

  Tamkar zata fashe da kuka,"Ya rafayet wlh an goge munsu,bansan ya akai ba,"

  "Wani ya amsa wayarki ne"?

 Girgiza kai tayi"a'a,duk yinin yau wayata tana a hannu na,"

  Mayar da idanuwanshi yayi kan abu"taya zan gane cewa,Junaid ya fita da zoben a hannunshi?ina yin amfani da shaida ne,kafin na yanke hukunci,"

 Gaba ɗaya sunyi shiru,jikin kowa yayi la'asar musamman Sehrish domin kuwa harta fara zubar da kwalla,Azmee tayi masu tsiya suna ƙoƙarin fallasa ta ita kuma ta hana hakan,Shi kuma Sgr bai yarda da sihiri ba,koda zasu fada mashi cewa tana amfani da sihiri zaiyi wuya ya yarda,

  Hannu Sehrish tasa tare da ta6o shi,juyawa Sgr yayi yana kallonta,Nuna mashi wayarta tayi da yatsanta alamar tana buƙatarta,

  Miƙa mata wayar yayi,tasa hannu ta kar6a,

  Tana kunna Power din wayar ta kawo haske,Sai ga text message Ya shigo ta layin AMRISH!

  Yaushe rabon da ta samu layin Amrish harta manta,kullum in ta kira kashe take samun wayar,Yanzu haka da ta kar6i wayar Amrish take so Ta tura ma saƙo akan ta nemo mata number Ya mu'allim ɗinsu,

  Shiga message ɗin tayi,ta ƙura ido tana kallon jagwalgwalon Rubutun da aka turo mata,Na haruffan da aka cakuɗesu,abun ya ɗaure mata kai!Nikaina Boss Ya ɗaure mun kai!





Duk maison Karanta Littafin Abban sojoji Yayi mun magana ta Layina amma whatsapp kawai banda kira 08103884440

  


  

  


  

  

  





  



  

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*










Ta jima tana kallon haruffan nan bata fahimci me aka rubuta a saƙon ba,layin Amrish ta kira nan take aka sanar da ita cewa wayar a kashe take!sam bata so haka ba,ɗagowa tayi tare da kallon Sgr dake magana da Oummansu,

  "Nagode sosai da bayanin da kika bani,duk da ban samu evidence ɗin da nake buƙata ba,but i wll try my best wurin ganin nayi investigation akanta,Zaku iya tafiya,"cikin girmamawa Yayi mata maganar,miƙewa Abu tayi"mun gode sosai Allah Ya taimaka,Ya baku sa'a..."sosai ta shiga yi masu Addu'a yana amsa mata da Ameen,"

  Ruƙo hannun Jahad tayi atare suka fuce daga ɗakin,Sae da suka fito palour sannan Oumma tace"Jahad ya akai ba'a ga hotunan a wayarki ba?ko kin gogesu ne batare da kin sani ba"?

  "Wlh Oumma ban gogesu ba,Nikaina abun ya ɗaure mun kai,"

  Jinjina kai Abu tayi"bakomai akwai Allah,Amma Sehrish ɗin fa?Anan zata kwana?ba ɗakin shi bane"?dama abun ya tsaya mata aranta shiyasa ta tambayeta,

  "Bedroom dinshi ne Oumma,kada ki damu mu tafi kawae,"


Bayan fitarsu ɗakin,Sgr ya mayar da hankalinshi kan Sehrish,har lokacin hannunta ruƙe da wayarta yayin da idanunta ke kallon Screen ɗin wayar,

"What are u looking at"jin muryarshi yasa ta ɗago da kyawawan idanuwanta tana kallon fuskarshi,

"If u need something pls lemme know"cike da kulawa yayi maganar,miƙewa tsaye yayi sai da ya fara ɗaukar Laptop ɗinshi sannan ya fita palour,Ji take kamar ta dakatar dashi,Saboda tsoran da take ji,


Yatsun hannunta na kerma Ta shiga danna wayar call log ta shiga ta kara dannawa Amrish kira,Nan take aka kara sanar da ita cewa Layin akashe yake,tamkar ta fasa ihu haka taji,runtse idanuwanta tayi tare da ɗan buɗesu kadan,yanke shawarar zuwa whatsapp group ɗinsu tayi Na Classmates ɗinta,Akwai kuma Na general wanda kowa ke aciki students ɗin da kuma malamansu ne aciki,A Group ɗin teachers kaɗaine zasu Iya tura saƙo banda students,tana fatan Allah yasa Ya Mu'allim yana acikin group ɗin,profile ta shiga daga ƙasa wurin da List ɗin Malaman dake group ɗin suke ta fara duba sunayensu tundaga kan Admins,Gasu nan sunayen birjik amma bata ga Numbar Ya mu'allim ba,Sai dai wasu numbobi da aka rubuta sunansu da harshen Larabci,shiru tayi tana tunanin kowanne ne aciki nashi,A ƙarshe dae duka numbobin masu ɗauke da rubutun Larabci ta turama Saƙon,bayan ta kammala rubuta saƙon ta ajiye wayar a saman bedside drawer,


Wuraren ƙarfe 2:30 na dare Lokacin masu bacci sunyi nisa a baccinsu,kamar yarda suka saba kwanciya a saman gadonsu su ukku,Hosana na a tsakiyarsu Abu na a ta 6angaren hannun dama inda yake fuskantar ƙopa,Jahad nata Can 6angaren hannun hagu,kwatsam Suna cikin Baccin nan,Abu ta soma jin wani irin gurnani gurnani asaman Gadonsu,a hankali ta buɗe idanuwanta tana ƙoƙarin ganin menene,har sai da gabanta ya faɗi rass,Wata Mummunar mage ce baƙa wulik mai Uban gashi ajikinta Hakoranta dogaye irin na Vam pires,Kafin abu tayi wani Yunƙuri Magen nan ta daddage ta kai Mata suka ta dira akan wuyan Abu,wasu Manyan ƙumbuna ta fiddo a hannunta tana ƙoƙarin Caccaka ma Abu akan fuskarta,A firgice Abu ta damƙi wuyan magen,Kokawa ta 6arke a tsakaninsu,duk yarda baƙar magen nan taso ta cutar da abu amma abun ya faskara,Domin kuwa Allah yaba Abu sa'a tunda ta damƙi wuyan magen nan ta dinga Jibgarta batare da jin shakkun wani abu ba,A jikin side drawer abu ta dinga buga kan magen nan bugu bana wasa ba,Har sai da magen ta fara kuka tana faman ambaton Miyau miyau,A faɗace Abu tace"Zaki ci ubanki ne,Baki ga komai ba,Nasan cewa ke ce Azmee,kika zo mun da suffar mage don ki kashe ni,Saboda kinga Asirinki na shirin Tonuwa ko?


Tunda abu ta ambaci hakan sai Magen nan ta bace 6aaat babu ita tamkar bata ta6a bayyana ba,ajiyar Zuciya abu ta sauke tana mai godiya ga Allah,daya bata nasara Akan Azmeee,

Saukowa tayi daga saman gadon,ba ƙaramin daɗi taji ba dasu Hosana basu farka ba,duk wannan badaƙalar da akayi suna ta shan baccinsu,


Toilet ta shiga,Bayan wasu mintuna ta fito ɗaure da alwala,Hijabi ta ɗauko tare da darduma ta shimfiɗa ta kabbara Sallah 



A 6angaren Sehrish kuwa kasa samun natsuwa tayi acikin ɗakin,har sai da Sgr ya shigo sannan hankalinta Ya kwanta,ruwa tace mashi zata sha don duk yadda taso kin sa wani abu a bakinta ta kasa yunwa take ji sosae,bayan ya kawo mata bottle water cike da zullumi ta kafa baki,sai da tasha kusan rabi sannan ta cire roban ta mika masa ya amsa ya rufe ya ajeta saman side drawer,saman gadon ya hau tare da janyota jikinshi ya rungumeta sosai har bacci ya ɗaukesu,


Wuraren Sallar Asuba da suka fita masallaci,Ya rage ita kaɗai acikin ɗakin,cikin bargo ta shige tana ta addu'a,tana jin motsin wasu abubuwa acikin kunnanta amma taƙi yarda ta buɗe bargon,Sai dai komai zai faru ya faru,


Lokacin da Sgr ya dawo daga masallaci,tare da fresh milk ɗin da ya ɗauko mata acikin Fridge ya shigo bedroom ɗin,abakin gadon ya tsaya yana kallonta ta cikin bargon sai kerma take yi kamar wadda sanyi ya kama,Saboda ita har A.c ɗin ɗakin ya kashe gaba ɗaya don ya lura tana da jin sanyi,


Zama yayi daga gefen gadon,Ya ajiye fresh milk ɗin asaman drawer sannan ya sanya hannunshi tare da yaye bargon jikinta,duka hannayenshi ya sanya wurin ɗaukkota ya ɗaurata asaman laps ɗinshi kamar wata jinjira,tunda taji ƙamshin turarenshi ta shaida cewa shine ya dawo,ba ƙaramin daɗi taji ba,kwantar da kanta yayi asaman ƙirjinshi,A hankali yake shafa sumar kanta yayin da idanuwanshi ke kallon long eyelashes ɗinta, ta rufe idanuwan sosai taƙi buɗesu,

"Ya jikin naki"?

"Da sauƙi,"ta amsa mashi daƙyar,bakin nata ya ɗan lafa,

  "Kina jin yunwa"?

jinjina mashi kai tayi alamar eh,

Dogon yatsan hannunshi ya zura mata abakinta,sai gashi ta buɗe Small mouth ɗin tare da kama yatsan hannun nashi,wani shock yaji da sauri ya zame yatsan don baiso ya shiga wani yanayi a wannan halin da take ciki na jinya,

  Fresh milk ɗin Ya ɗauko tare da cire murfin ya ɗan kafa mata robar abakinta,a hankali ta shiga shan madarar,natsuwa yayi yana kallonta shi kanshi mamakin yanda ya damu da ita sosai ya ke yi,Yadda take shan fresh milk ɗin ba ƙaramin sha'awa ta bashi ba,Sai da ta shanyeta tass,Sannan ya janye robar daga bakinta,

.."kin ƙoshi"?

  Ɗaga mashi kai tayi alamar eh,ba don ta ƙoshi ba,Amma taji sauƙin cikinta,

  "Zaki yi wanka,"?ɗaga mashi kai tayi alamar eh,Tayi tunanin zaice ta tashi ta tafi bedroom ɗinsu,Ba zato ba tsammani taji ya ɗauketa asaman kafadarshi Ya wuce da ita toilet,wata irin kunyace ta rufe ta,musamman Lokacin da ya cire rigar jikinta yayi mata naked,batasan meke wakana ba amman taji ya kwantar da ita cikin jacuzzi,da sunan wanka Sgr ya shiga da ita cikin kwamin amma sai da ya gama shafe jikinta da hannunshi,da sunan yana goga mata Sabulu,ga soap ɗin nashi wani irin ƙamshi tamkar turare haka sabulun yake,zuba mata ido yayi yana kallon fuskarta,ganin tana ƙoƙarin buɗe idanuwanta yasa shi yin saurin goga mata sabulu saman idanuwan,hakan yasa ta fasa buɗe idon,baison ta raina shi ne shiyasa yayi mata hakan,Wani irin ruwa ne mai ɗumi ga daɗi yayi mata amfani dashi,kamar karta fito daga cikin Jacuzzin nan hake ta dinga ji,



Bayan wasu mintuna Sgr ya fito ɗauke da Sehrish saman kafaɗarshi ya ɗaura mata towel,zaunar da ita yayi saman front chair ta gaban madubinshi,

  Saitin kunnanta ya duƙo a hankali yace"in shafa maki ne ko zaki iya shafawa,"?da sauri ta ɗaga mashi kai Alamar eh,

  "Okey,"ya miƙe tare da juyawa ya shige toilet ɗin don ya samu yayi wankan shima,Tana jin ya rufe ƙopa ta buɗe idanuwanta,Sae faman zabga uban murmushi takeyi,bata ta6a tunanin Sgr zai iya caring ɗin mace ba irin Yarda yayi mata a yau,Ko jinjira albarka,bakomai yafi burgeta ba fa ce Yarda yake ɗaukarta asaman kafadarshi,daɗi take ji sosai,Ajiyar zuciya ta ɗan sauke tare da kai hannu ta ɗauki ɗaya daga cikin body oils ɗinshi ta soma shafawa ajikinta,Bayan ta kammala ta feshe ko'ina da turarenshi ita ma yau ta ɗanɗana turaren Babban Yaya,Zasu yi ƙamshi iri ɗaya,


Miƙewa tayi daga saman kujerar ta nufi gadon tana ƙoƙarin ta gyara mashi,zanin gadon ta cire ta musanya da wani sabon da ta ɗauko ta jera pillows ɗin,Tana cikin gyaran nan tajiyo alamun motsin ƙopa tasan shine zai fito,A hanzarce ta haye saman gadon ta zauna tare da jingina bayanta ta kuma rufe idanuwanta saboda kunyarshi da take ji,Ya gama gane mata jiki saƙo da lungu,"


Sako fararen ƙafafunshi yayi masu sanye da slippers,A saman ƙaramin carpet ɗin dake bakin ƙopar toilet ya cire slippers ɗin,towel ya ɗaura asaman waist ɗinshi,Slowly ya ɗago da blue eyes ɗin shi yana kallon Sehrish,takawa yayi izuwa gaban dressing mirror ɗin ya tsaya don ya gyara jikinshi,satar kallonshi Sehrish ta dinga yi ta wutsiyar idonta,ba ƙaramin kyau yayi mata ba,ya saki kwantacciyar sumar kanshi ta baya,natsuwa tayi tana kallonshi,Ashe Sgr ya gane tana satar kallonshi,


Da gangan ya sanya hannunshi asaman ƙugunshi ya warware towel ɗin jikinshi,Aikuwa a ruɗe Sehrish ta kifa kanta saman pillow Jiki na kerma,duk a tunaninta babu short ajikinshi,Ƙayataccen murmushi Sgr ya saki,Shi kanshi baisan ya kubce mashi ba,razanar da tayi ne yaso bashi dariya,


ɗago da kanta tayi daga jikin pillow ɗin don ta saci kallonshi,karaf suka haɗa ido dashi,wani irin kallo taga yanayi mata,murmushi ta saki tare da mayar da fuskarta jikin pillow ɗin ta rufe,


Suna cikin wannan Yanayin na shauƙi Hosana ta kwala Sallama da ƙarfi,da sauri Sehrish taja bargon ta lullu6e kanta gaba ɗaya,Wucewa can cikin ɗakin yayi wurin closet ɗinshi,Jallabiya Ya zura ajikinshi kafin ya dawo ya zauna daga gefen gadon,


Jin Anyi shiru ba'a bata izinin shiga ba yasa tace"In shigo"?tayi tambayar tana leƙa kanta cikin ɗakin

  "Come in"ya bata permission din shiga,a tare da Jahad suka zo ɗakin tana la6e abayan Hosana,dama tun kafin su Shigo taja kunnan Hosana akan karta kuskura ta faɗa masu ɗaki batare da an basu izinin shiga ba,don tasan halinta,ɗan kaine da ita,


A tsanake suka shigo cikin ɗakin hannunsu ruƙe dana juna,

  "Yaya Rafayet ina kwana,kun tashi lafiya?Ya mai jiki"?

  "Alhamdulillah"bayan ya amsa masu ya miƙe tare da kallon Jahad a lokacin Hosana ta koma bakin gadon tana kallon Sehrish dake kudundune cikin bargo kamar mai bacci,

  "Ki ɗauko mata kayan da zata sanya ajikinta,"

  "Toh"ta ambaci hakan tare da juyawa ta nufi kopar fita daga ɗakin,fitowa palour yayi tare da samun wuri saman Sofa ya zauna,


"Rishi ya jiki?kinji sauƙi"?a hankali Sehrish ta ɗan zame bargon data lullu6e fuskarta dashi,kamar wadda ta tashi daga bacci haka tashiga mutsustsuka idanuwanta,kallon Hosana tayi daƙyar ta iya buɗe baki tace"da sauki,"

"Allah ya baki lafiya rishi,jiya fa ko bacci banyi ba saboda tunaninki...."murmushi kawai Sehrish tayi mata don tasan cewa ƙaryane,ba ƙaramin abu bane zai hana hosana yin bacci ba,

  Cigaba da magana Hosana tayi"nasha kuka Allah,Oumma tayi tayi dani akan in kwanta inyi bacci,Naƙiya nace nidai bazan iya bacci ba,har sai kin samu sauƙi,"ta ƙarasa maganar,hada ɗan kwa6e fuska,

  Murmushi Sehrish taci gaba da yi tana kallonta,

  Dawowa  Jahad tayi hannunta ruƙe da rigar da ta ɗauko ma Sehrish,turkey gown mara nauyi red colour mai maɗaurin igiya daga tsakiyarta,atare da mayafinta ta ɗaurosu asaman hannunta,Shigowa palourn ta yi da sallama abakinta,Amsa mata sallamar yayi kafin ta wuce bedroom ɗin,


Anan ta samu Hosana tana ta shirga mata ƙarya,da alama ba ƙaramin nishaɗi take sanyata ba,agaban gadon ta tsaya tare da kallon hosana"ki sauka down Oumma na kiranki zaku ci abinci ne An kammala shirya breakfast,"jin haka yasa Hosana ta juya da gudu ta fita daga bedroom ɗin,dama wayau Jahad tayi mata don tabar ɗakin ko Sehrish ta samu ta shirya,ta lura babu kaya ajikinta,


"Ya jikin naki My own sis,"fuskarta ɗauke da murmushi ta amsa mata da ƙyar"Am feeling better now,"

"Allah ya ƙaro lafiya,Ga wannan Ya rafayet ne yace in kawo maki,"tayi maganar tana miƙa mata kayan,yunkurawa tayi tare da miƙewa daga zaune takai hannu ta kar6i kayan,kafin ta sauko daga saman gadon,ɗaure da ɗan towel ɗinta,

"Bari na jiraki a palour,"da sauri Sehrish ta dakatar da ita"A'a,zan shiga daga cikin ɗakin na sanya kayan,Idan na kammala sai mu fita tare,"ba ƙaramar wahala take shaba idan zatayi magana,kamar ana tsaga bakinta haka take jin raɗaɗin,juya baya jahad tayi tana ƙarewa Bedroom ɗin kallo,a can ƙasan zuciyar kuwa tsabar farin ciki ne,Saboda ta gano wani abu game da Babban Yayansu,Da alama Ya fara faɗawa tarkon rishi ɗinsu,ashe da Rabon mafarkinta ya zama gaskiya,Wato na ganin Sehrish da ƙaton ciki ga kuma kwaɗayin Son Ganin Ƴa'ƴansu da take yi,lokaci guda kuma Yanayinta Ya canza,matsananciyar damuwa ta bayyana akan fuskarta,Bakomai Yasa ta shiga wannan Halin ba,Fa ce Masoyinta da ta tuna,tayi babban rashi wanda har ƙarshen rayuwarta bazata ta6a manta raɗaɗin rasa shi da tayi ba,a duk lokacin da suke waya dashi haka zai addabeta da tambaya wai Idan sunyi Aure A daren farko me zasuyi,duk in ta tuna wannan tambayar ta Junaid sai Murmushi Ya bayyana akan fuskarta,wasu siraran Hawayene suka soma saukowa saman cheeks ɗinta,


"Jahad,na shirya zamu iya tafiya,"jin muryar Sehrish yasa tayi saurin goge hawayenta,sannan ta juya tana kallonta,Ba ƙaramin kyau rigar tayi mata ba,kamar wanda zata gasar kyau,Hannunta na a ruqe da wayarta da ta ɗauko,

  "Masha Allah"tayi maganar tare da ruƙo hannun Sehrish tana murmushin dole,


Atare suka shigo cikin palourn,har zasu fita ta ɗan dakata tare da juyawa ta kalli Sgr dake zaune saman sofa,ya jinginar da bayanshi,yayin da ya lumshe idanuwanshi tamkar wanda Bacci bai ishe shi ba,

  Sakin hannun Jahad tayi"ina zuwa,"

Fita daga wajen palourn Jahad tayi tana jiran dawowarta,


   A hankali ta ƙarasa wurin sofan dayake zaune ta tsaya,Cikin sanyin murya ta soma magana"bansan da wasu kalmomi zanyi amfani dasu ba wurin yi maka godiya,saboda irin kyakkyawar kulawar daka bani,Thank You So much Ya Rafayet"tunda ta soma magana,Ya natsu yana sauraronta,daɗin voice ɗinta yake ji kamar kamar me ba kaman da take maganar a hankali,

  "Never mind,"yayi maganar batare da ya buɗe idanuwanshi ba,Juyawa Sehrish tayi da sauri ta nufi hanyar fita falon,Sai da ya tabbatar tabar wurin tukunna ya ɗan buɗe idanuwanshi tare da waigawa yana kallon bayanta,har sai da ta fuce daga falon,


A 6angarensu Hayaam da Abra waɗanda tun jiya suka bar Abuja,Abun da ya faru lokacin da suka isa unguwarsu,wuraren marece tunkafin Su shiga gidansu suka lura da yadda mutane ke kallonsu,tun daga nan suka sha jinin jikinsu,Har nunasu akeyi da hannu ana cewa gasu can sune ƴa'ƴanta,Sun dawo daga yawon biɗiɗin nasu,Wlh anyi asarar Rayuwa,wasu kuma na cewa,Ae laifin uwar tasu ne da bata basu tarbiya ba ita ta lalatasu,Lokacin da suka ƙarasa ƙopar gidansu,A buɗe suka samu gidan,Da sallama suka shiga sunyi tunanin za'a amsa masu amma sai suka ji shiru,gidan babu kowa,komai na gidan babu,An kwashe komai,hatta butoci da bokatai babu,Har kan fanfonsu an 6alleshi,


Nan fa hankalinsu yayi mugun tashi,Tun a tsakar gidan Abra ta saki trolley ɗin hannunta,da gudun gaske suka shiga cikin ɗakunan suna kwalawa Mammynsu kira,Mammy! Mammy!!gabansu ne ya faɗi ganin ɗakin mammynsu babu komai wayam hatta katifarta,yanke shawarar zuwa makwabtansu Suka yi donsu tambayi Ina mammynsu taje ne,


Suna zuwa zauren gidan suka fara jiyo hayaniyar mutane,kasa kunne suka yi suna sauraran Surutun mutanen da sukayi masu dandazo a ƙopar gidan,

"Kuna ina la'anannu!waɗanda basu son ciwon kansu ba,Ku fito muci ubanku inba haka ba Mu ƙona gidan da fetur,kun tafi kun barmu da bala'e acikin unguwa,Yau sai mun fanshe haushinmu akanku,Jinin ku ya halatta"

  Jin wannan yasa tsoro ya kamasu,da gudu suka Koma cikin gidan,A ɗaki suka datse ƙopa,Hankalinsu Yayi mugun tashi,Sun rasa gane zunubin da suka aikata har mutane ke neman bugunsu,Suna Cikin wannan halin ne suka ji anyi masu Sallama,muryar Limamin Unguwarsu ce,ƙin fitowa su kayi har saida suka ji yace"Kada kuji tsoron komai,ku fito inason magana daku ne,Naba mutanen anguwar haƙuri Sun tafi,"jin wannan maganar yasa suka buɗe ƙopar ɗakin suka fito,Bayin Allah kowacce jikinta sai kerma Yakeyi,hawaye sharkaf akan fuskarsu,


Nasiha yayi masu sosai,A ƙarshe ya sanar dasu laifin da suka aikata wanda yasa mutanan unguwar ke neman kashe su,Abunda Ya faru Bayan tafiyar Abra,tabar Mammynsu ita kaɗai kwance tana jinya ta kwana ta yini cikin mawuyacin hali a lokacinne makwabciyarta tsigai wadda suke zuwa yin gulma a kuma gidanta ne ake kulle Amal,ta shigo ta sameta a wannan halin da kyar ta taimaka mata alokacin tana ta sababi tana fadin ina ma amfanin haihuwar yara irin nata,uwarsu ba lpy sun haura kafa sun tafi gantali,a washe gari tsigai tafiya ta kamata dama bata cika zama ba,ta ba yaranta umarnin su rinka leka Mammy suna kai mata abinci ai tun ranar farko da suka taras da ita acikin kazanta basu sake komawa ba sai ma wayarta da suka sace don rashin tsoron Allah,sauran mutanen unguwar babu wanda yasan da mara Lafiya acikin gidan,kowa yazo gidan nasu Yayi sallama ba'a amsa mashi ba,Sai yayi tunanin cewa babu mutun a gidan,Basu tashi sanin abunda ke faruwa ba,Sai da azababben wari ya ishi mutanan unguwar kamar gunyar ƙwai ta fashe,aka rasa daga ina wannan warin ke fitowa,Mutane suka kasa samun natsuwa a ƙarshe da aka tsananta bincike Aka gano cewa wannan warin a gidansu ne,Matasan unguwar suka shiga cikin gidan suna bincikawa har suka samu gawar Mammy ta ru6e naman jikinta ya zagwanye,tsutsotsi duk sun mamaye jikinta suna ci,Wa'iyazubillah,lokacin da su hayaam suka ji wannan Mummunan labarin a wurin limamin nan,Anan take Abra ta sume,Hayaam kuwa har kusan Zaucewa Tayi,sunyi danasanin rayuwarsu fiye da tunanin mai tunani,Sun tsani kansu,sun muzanta a idon jama'a,A ranar basu kwana acikin gidansu ba,Saboda mutanan dake dakonsu,Malam Liman ya tafi dasu gidanshi,kafin komai Ya lafa😭

  

A lokacin daƙyar aka samu wasu bayin Allah da taimakon limamin nan suka kawar da gawarta,An yi mata jana'iza kenan da Sati guda,Wannan makwabciyar tasu Tsigai,Ta sanya matasa suka kwashe mata kayan gidan kaf saboda tana bin Mammy bashin kuɗi kafin ta mutu,dama kuma a wurinta suke cin bashi in zasu wurin boka.


Gani Ga wane Ya ishi wane jin tsoron Allah,ya Allah ka kare mu daga aikata aikin danasani,


A 6angaren Ishaq kuwa,Aunty babba ta addabe shi da kira da numbobin mutane,bata gajiya da aron waya tana yi mashi magiya akan Ya taimaki Rayuwarta,Abunda yasa Ishaq bai mayar da hankali akanta ba shine tasaba yi mashi ƙarya ba kamar in tana son ta samu kuɗi,wannan dalilinne yasa bai ɗauki maganarta Serious ba,a ƙarshe ma data isheshi da kira sai ya cire Sim ɗin wayar gaba ɗaya ya ajiye shi,Ya musanya da wani sabo,ɗaya daga cikin illar yin ƙarya kenan Gashi tajama kanta,Gaba ɗaya yanzu hankalinshi na akan Hajjaju,domin kuwa ta amince zata aureshi,Soyayyarsu Tayi ƙarfi har sun fara zancen Yin aure,


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 12 da rabi na rana,Amrish tana ta faman zarya acikin babban falon gidan,ranta a matuƙar 6ace,Ta cika tamkar zata fashe,tun safe ta ƙwallafa rai akan zasu fita a siya mata waya,Amma Mommy ta sa6a mata alƙawarinta,daga shiga ɗaki ta shirya ta fito bata ganta ba,ashe tabar gidan cikin motarta,Sae da ta bari ta ɗauki wankan lace ta sha uban make up tukunna tayi mata tsiya,Ta sha kuka harta gaji,fuskarta duk tayi jaga jaga da hawaye,tayi kukan harta gaji,a ƙarshe ta yanke shawarar zata nemo wayarta,Yau saita bincika ko'ina na gidan har sai Allah yasa ta gano wayarta,Upstairs ta fara hawa a buɗe ta samu ƙopar ɗakin Mommynta,Shiga ciki tayi tana ƙarewa ɗakin kallo,tunani ta shiga kota ina zata fara neman wayarta,bedroom ɗin ya haɗu sosai,Katafaren gado ne side by side ɗinshi kuma drawer ce,akwae faskekiyar wardrobe,ga tanƙameman Dressing mirror,da sauransu,hannu tasa ta cire kallabinta ta ɗaure shi a qugunta,drawer chest ta fara bubbuɗewa tana neman wayarta,sai da ta duba ko'ina duk ta hargitsa kayan bata ga wayarta ba,tuni ta haɗa gumi sai zufa ke tsastsafowa akan fuskarta,tsayawa tayi ruke da qugu tana faɗin"Wlh bazan haƙura ba,Duk inda kika 6oye mun wayata yau saina gano abuna,Ae ba ita ta siyamun wayar ba,Ya haroon ne ya siyamun,don haka dole a fiddo mun wayata,indai ana son Zaman lafiya"ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki ta nufi hanyar fita daga ɗakin,tana ƙoƙarin ruke handle ɗin ƙopar ta ɗan dakata yayin da kwalwarta ke tariyo mata wani abu kamar taso taga waya a saman gadon Mommynsu,

A waske ta juya tare da wurga idanuwanta kan Wayar dake ajiye asaman pillow,da farko tayi tunanin wayarta ce saboda iphone ce,Amma lokacin da ta ƙarasa gaban gadon ta ɗauki wayar sai taga ba wayarta bace,

  Cike da mamaki tace kodai Mommy ce ta siyamun sabuwar waya don tayi suprising ɗina'?

Jujjuya wayar ta shiga yi a hannunta,a kashe wayar take,

  Wuri ta samu gefen gadon ta zauna,ranta ne ya bata cewar ta kunna wayar ta gani,

  Danna power ɗin tayi nan take screen ɗin wayar ya kawo haske,Zama Amrish tayi tana jiran wayar ta kammala buɗewa,runtse idanuwanta ta ɗan yi kafin wayar ta buɗe,

  A hankali Amrish ta buɗe idanuwanta kan screen ɗin wayar,ƙura ido tayi tana kallon hoton wallpaper ɗin

Abun yayi mugun ɗaure mata kai!cike da mamaki tace"kai!Wannan ae hoton Yayan Sehrish ne,JUNAID ROMEO,wanda ke kawota makaranta!ya akai wayarshi tazo hannun Mommynmu,"miƙewa tsaye tayi tana ƙarewa hoton kallo,Fuskar nan ɗauke da wannan kyakkyawan murmushin nashi,tama rasa ina zata dosa,wani tunani zata yi,kwakwalwarta ta cunkushe,ita dai a iya saninta basu da alaƙa dasu Sehrish,Amma kuma ga wayar Yayan sehrish ɗin a gidansu,MEYA KAWO TA? tayi takaicin ganin wayar da face security dole sai da fuskar mamallakin wayar sannan za'a Iya buɗe ita,


Fitowa Amrish tayi daga cikin ɗakin Mommynsu hannunta ruke da wayar Junaid,Saukowa downstairs tayi a tsanake take taka staircases ɗin zuciyarta cike fal da mamaki,Zurfin tunani ta shiga bakomai ya faɗo mata aranta ba,fa ce Kalmar nan da Mommynta ke faɗi lokacin da tayi mata la6e a ƙopar ɗakinta,Wato akashe akashe shi kawai ko kuma a ƙwaƙule mashi idanuwanshi,tabbas kuwa ta fara zargin wani abu dangane da Mommynta,Akwai alamar Tambaya akanta babba ma kuwa,

  Gabanta ne ya faɗi lokacin da ta tuna da agogon Diamond ɗin da ta tsinta a tsakiyar falonsu,nan ta gane cewa iri ɗaya ce da agogon hannun Junaid da ta gani a hoton fuskar wayarshi,In har kuwa hakane kenan dole abu biyu zai kasance!


Ruƙe qugunta tayi da hannu ɗaya,tana ci gaba da zurfafa tunaninta 

  "Kodai su mommy sunyi kidnapping ɗinshi ne shiyasa suka shigo da agogonshi da wayarshi acikin gidan nan,ko kuma Sun shigo da Yayan Sehrish acikin gidanmu daren Jiya,dama kuma tajiyo dirar motoci agidan,Daga baya kuma taji shigowar mutane a falonsu,duk da bata samu damar ganin meke wakana ba,'


Kasa samun natsuwa Amrish tayi,gudu gudu sauri sauri ta fito daga cikin gidan ta nufi Baba mai gadin gidansu dake zaune saman benci,yana sauraran radio,tsohon har saida ya firgita da ganin Amrish kamar yar daba haka ta faɗo mashi,Ɗankwali ɗaure da qugunta,kitson shuku ne akanta,


"Lafiyar kuwa Amrishi?ko sallama babu"?baba mai gadi yayi tambayar yana kallonta,

  "Ina fa lafiya,dan Allah so nake na tambayeka!a daren jiya wasu baki sun shigo cikin gidan nan,Ka lura dasu"?

  Shiru tsohon yayi yana tunano abunda ya wakana a wannan lokacin,Hajiya taja kunnanshi akan cewa ya rufe idonshi Ya zama tamkar makaho,Sannan ya rufe kunnuwanshi Tamkar kurma,

  Tuna wannan yasa shi yin saurin cewa"Bansan komai ba,lokacin da suka shigo cikin gidan nan bacci ya ɗauke ni...."tunkan yakai ƙarshen maganar Amrish tace"mai ƙarya ɗan wuta,wlh kaji tsoron Allah baba mai gadi,Tsofe tsofe dakai zakayi mun ƙarya,in har dagaske bacci kakeyi to waye ya buɗe masu gate?dole kaji horn ɗin mota kuma dole ka farka,


A ruɗe baba mai gadi yace"kinga dan Allah ki rufa mun asiri ki bar wurin nan,Hajiya ta kusa dawowa idan ta ganki a bakin gate ɗinnan zata tuhumeni ne"

  "Wlh bazan bar wurin nan ba,ko ka faɗamun amsar tambayata,Ko kuma wlh in ƙala maka sharri wurin Mommy ince kana nemana,"

  A firgice Baba mai gadi Ya miƙe tsaye yana ambaton"Subhanallahi!Amrishi kina da hankali kuwa?kinsan me kike faɗa"?duk ya tsorata saboda yasan cewa jarababbiya ce,kamar uwarta,tsaf zata iya ƙala mashi sharri

  "Zan tafi baba mai gadi amma inaso ka sani,Wlh saina ƙala maka sharri,Kasan police station?kasan Gidan Yari"?tayi tambayar tana kallonshi

  Jin haka yasa shi ƙara firgita,Cikin lalama ya soma magana"zan faɗa maki gaskiya amma dan Allah Amrishi karki faɗama kowa,kada ki bari kowa yaji,"


"Naji bazan faɗa ma kowa ba,Nayi maka alkawari,"


  "Yawwa,wlh wasu danƙara danƙaran motoci ne suka shigo cikin gidan nan,Ina zaune ina sauraron radiyo ɗina naji hon dinsu,da azama na buɗe masu gate ɗin suka shigo a jere,bayan motocin nan sun tsaya,Hajiya ta fito daga motarta,ɗayar motar kuma wani gabjejen mutun ƙirar samudawa ya fito daga cikinta,Ya zagaya ya buɗe gidan bayan Motar,ina baki labari wani gabjejen ƙaton ƙirar adawa ne ya fito daga cikin Motar ashe su biyu ne,kwatsam!ingaya maki Sai naga ya sanya hannu ya ɗauko wani matashin yaro duk yaci wahalar rayuwa amma wlh baki ganshi ba,Kyakkyawan gaske fari tasss mai kwantacciyar Suma,kamar irin waɗannan indiyawan da nake gani a talabijin,Basamudan nan ya cuccuboshi saman kafadarshi Yaron kamar matacce baya motsi,ko'ina na jikinshi Ya raunata Amma fa yana numfashi don naga yatsun hannunshi na kerma........."

  Tashin hankali!,tunda baba mai gadi ya soma bata Labarin ta kasa kunne tana sauraronshi abun kamar a mafarki take jinshi,

  Sauke ajiyar zuciya baba mai gadi yayi kafin yaci gaba da cewa"kinsan Allah har ƙwalla saida na zubar saboda yaron nan,gwanin ban tausayi,Don Allah ko kin san Meyake damun Yaron nasan kin ganshi......"

  Hannun Amrish na kerma ta miƙa ma baba mai gadi wayar Junaid"duba ka gani shi ne wannan yaron"?

  Kar6ar wayar baba mai gadi yayi yana ƙarewa hoton Junaid kallo,

  "Gaskiya kamar shi wlh," cike da kokwanto Yayi maganar,Can kuma yace"tabbas ma shi ne,Ae daga ganin wannan hoton kafin ya fara shan wahala ne,jiya kuma dana ganshi Ya jigata sosai bawan Allah,dan Allah Amrish in kin shiga ciki,Kice ina yi mashi ya jiki,"

  A ruɗe tace"Baba mai gadi ae baya acikin gidan mu,jiya baka ga sun tafi dashi ba"?

   Girgiza kai Baba mai gadi yayi"basu fita dashi ba,Yana acikin gidan nan!bayan da suka shiga da yaron,ina zaune cike da jimami naga waɗannan Samudawan sun dawo batare dashi ba,kuma akan idona suka ja motarsu da gudu suka bar gidan nan......"yana kai ƙarshen Maganar Amrish ta kar6i wayar daga hannunshi,juyawa tayi da gudu ta nufi cikin gidan

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠 paid book


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*






Not edited👌




Lokacin da suka sauko downstairs,gaba ɗaya kowa Ya hallara akan dining suna Yin break fast,ƙarasawa Su kayi Bayan sun gaishe da kowannansu,Kowa saiyi Mata Ya jiki Yake yi,Taji daɗin yarda Suka nuna damuwa akanta,kusa da oummansu ta xauna,Jahad ma ta zauna a gefenta,a dai dai Lokacin Azmee ta dawo hannun ɗauke da wasu kayan abincin data ɗauko a kitchen,A saman table ɗin Ta ajiye tray ɗin,Atare Sehrish da Abu suka ɗago ido suna kallonta,fuskarta ta kumbura idanuwanta sunyi jawur kamar wadda tasha kuka,a gefen fuskarta hada gurjewa,fatar wurin ta tattare,Abu batayi mamaki ba,don kuwa ta gane cewa Itace ɗin tazo mata da suffar mage a daren jiya,Ga alamu nan Sun nuna,


Zagayawa tayi wurinsu Sehrish,plate biyu ta ɗauko ta zuzzuba masu abinci,tare da tura masu agabansu,Jahad ta hauci,Sehrish kuwa ƙin cin abincin tayi,Miƙewa Tayi daga saman chair ɗin,


  "Ina zaki je"?omamnsu ce tayi magana ganin ta miƙe,

  Daƙyar ta iya cewa"Kitchen zanje,"ta ƙarasa maganar tare da kama hanyar zuwa kitchen don ta shirya mashi breakfast ɗinshi,tun da ta fara jin sauƙin jikin nata,


Shaf shaf Ta shirya mashi asaman ƙayataccen tray,Ta wurinsu ta gifta cikin main palour,Upstairs Ta haye lokacin data ƙarasa part ɗin nashi tana ƙoƙarin Shiga,tajiyo muryoyinsu suna magana Shi da Omar,

  "The same fa irin message ɗin da aka turomin Ni da Abba,da farko da abba ya nuna mun saƙon nayi tsammanin ɗaya daga Cikin friends ɗinshi ne,Aka samu wani Yaron Ya ɗauki wayar mahaifinshi Ya rubuta jagwalgwalon,Amma daga baya dana ga saƙon sai abun Ya tsaya mun araina,kuma sai gashi kaima An tura maka,to wai wanene da wannan aikin"?Yayi tambar yana kallon Sgr,dake a gefenshi,

  "Am confused Omar,Nagaza fahimtar me aka rubuta ajikin message ɗin nan,abu 2 nake hasashe akan saƙon nan,kodai ƙaramin Yaro ne Ya rubutoshi,ko kuma wanda baya acikin hayyacinsa,Amma abunda yafi ɗaure mun kai shi ne,Taya akai wanda ya turo saƙon Ya samu special line ɗina,Wanda bakowa ne yasanni dashi ba,"ya kai ƙarshen maganar yayin da idanuwanshi ke akan Omar,


Kafin Omar yace wani abu,Sehrish Ta katsesu da sallama,Atare suka ɗago suna kallonta,

   Ƙarasawa tayi gaban table ɗin dake agabansu,ta sauke trayn asaman shi, kafin ta ɗan ɗago tare da kallon Marshal Omar,murmushi ta samu akan fuskarshi,

  'Ina kwana Ya omar,ka tashi lafiya,"

  "Lafiya Lou Sister,Ya jikin naki"?

  "Da sauki ya omar,"_

"Allah ya ƙara maki lafiya,"

"Ameen ngde,"ta amsa mashi,

Cike da Zolaya ya nuna kayan abincin data ajiye masu"Nawa ne ko nashi"?

  Duƙar dakai ta ɗanyi tana murmushi

"Naku ne,na kawo maku,"

"Kinsan da zuwana part ɗinshi ne,"?

  "A'a,"tayi maganar tare da satar kallon Sgr,Ya tsareta da blue eyes ɗinshi,duk saita shiga kame kanta,

   "Ya akai naga ka tsareta da ido?faɗamun menene sirrin kallon nan"yayi maganar yana ɗage mashi gira,da sauri Sehrish Ta juya ta kama hanyar fita ɗakin,

  "Kallon Ya isa haka,Its better ka kame kanka malam,saura ƴan satittika,Ka sakar mashi Ƴar shi,Ka koma U.s wurin Eva nasan har yanzu tana jiranka,"

Ɗaure fuska Sgr yayi"Omar bana son wannan joke ɗin,idan kaga nabar ƙasar nan,ƙafata ƙafarta,zan tafi tare da ita u.s don taci gaba da yi mun aiki acan,"

  Harararshi Omar yayi"Sannu ko?masu aikin dake garemu a U.s fa,Sallamarsu zaka yi ne"?

  "Aikinta daban nasu daban,"

"Kana nufin aikin gyara shimfiɗa"?dariya ce ta kufce ma omar,hakan ba ƙaramin hasala shi yayi ba,

  Ganin ya 6ata rai yasa shi cewa"Shikenan nadaina,yanzu dae bari nayi serving ɗinmu ko?nasan kana jin Yunwa,"

  Yayi maganar tare da kai hannu yana buɗe warmer,

  


Sehrish kuwa Bayan fitarta daga part ɗinshi,jiki asanyaye take tafiya,maganar da taji su Ya omar nayi akan saƙon nan ya tsaya mata aranta,Taya akai aka tura masu message iri ɗaya,Amma ita saƙon nata bada new number bane,ta layin Amrish ne,kuma a iya saninta Amrish bata da Number ɗinsu Ya omar,balle ace itace ke tura masu saƙon dagangan,to kodai ta yarda wayarta ne?wani yaron ya tsinta Yake tura masu saƙo,Can kuma ta tuna abunda Sgr yace da Special line ɗinshi aka tura mashi saƙon,Wanda ba kowa ne keda shi ba,


Ƙarasa Zancen zucin tayi a lokacin data sauko palour,bata koma dining ɗinba ta wuce bedroom ɗinsu tana zarya acikin ɗakin nasu,



*Amrish*


lokacin data juya izuwa cikin gidan A sukwane ta faɗa falon,da gudu ta nufi wani Corridor,Gidan Yana da girma sosai,tana da tabbacin cewa anan downstairs Suka rufe shi,haka ta dinga bin ɗakunan dake a gidan kaf tana bincikasu,Tasha wahala sosai,Ga uban gumi data haɗa,fuskarta sai naso take yi,A ƙarshe data gaji ta shiga ƙwala mashi kira ko Allah zaisa Yaji kiran nata Ya amsa mata,

  "Junaid!Junaid"tamkar maƙoshinta zai 6allo waje saboda yarda take 6are baki wurin kiran sunanshi,


A galabaice Amrish tayi ruku'e hannunta dafe da guiwowinta,Sae faman haki take yi,runtse idanuwanta tayi gam,yayin da take tariyo ɗakunan data bincika a ƙalla sun kai ɗaki takwas masu zaman banza wanda ba'a amfani dasu,zurfin tunani ta shiga,nan take wani abu ya faɗo mata aranta,Acan backyards ɗin gidan Akwai wani munafukin ɗaki,Wanda tun tana yarinya hajiya Sarat ta hanata shiga ɗakin,ko wurin ɗakin taje saita tsawatar mata,tunda take ita dai bata ta6a gani an buɗe ɗakin nan ba,Akan idanuwanta,Kamar an daina amfani dashi amma akwai wasu surruka da aka 6oye acikinsa,Shiyasa aka hanata zuwa,


Cike da ƙwarin guiwa Amrish Ta miƙe,ta juya tare da kutsawa Can ciki,Ta ƙopar baya ta fita,tsayawa Tayi tana kallon Girman ginin,A hankali ta aza idonta kan ƙopar ɗakin dake fuskantar backyard din,Wani ƙaton ƙwaɗo ta gani an garƙame ɗakin dashi,Wanda duk bala'enta bazata iya cire wannan makullin ba,tsabar baƙin ciki kamar ta haɗiyi zuciya a wurin nan,Gashi window ɗin ɗakin sunyi nesa can sama,matsawa tayi jikin ƙopar ta kanga kunnanta,hannu tasa tana ɗan kwankwasa ƙopar ko zata ji motsinshi,Amma shiru babu wani alamun akwai mutun,cike da takaici ta juya zata bar wurin kenan idonta ya hango mata ɗigon Jini a ƙasan wurin,har sai da ta dafe saitin zuciyarta saboda faɗuwar gaban da taji,wannan Yasa ta ƙara yarda cewa Akwai mutun a cikin ɗakin,tabbas Sun shiga dashi cikin ɗakin,da gudun gaske ta koma cikin gidan,akwai wani ɗaki dake jingine da wannan ɗakin dake a backyard ɗin Amma shi yana fuskartar Cikin gidan,ranta na bata cewar Zata Samu window ɗin ɗakin ta cikin ɗakin dake acikin gidan,cike da sa rai Amrish ta faɗo cikin gidan,gudu gudu sauri sauri Ta shiga ɗakin,kamar Store ne na ajiyar buhun hunan kayan abinci da jarkokin Mai,A jikin ƙopar store ɗin ta samu Key ɗin ɗakin,hannunta na kerma ta murza key ɗin ɗakin,kafin ta hankaɗe ƙopar ta shiga,Gabanta sai faɗuwa yake yi tsoranta kada Mommynta ta dawo,dan Wlh har kashe ta zata iyayi,Dama tasha faɗa mata cewa ita bata damuba don ta rasa ba,ba ɗigon Imani azuciyarta,Kamar arniya hake take,


Ajiyar zuciya ta sauke Lokacin data hango Window mai girman gaske Duk da akwai net ajikinta,Amma batayi nisa ba,in har ta taka wani abu zata Iya hangen abunda ke wakana acan ɗakin bayan gidan,Ga uban duhun da ke cikin ɗakin,Bazata Iya hango abunda ke aciki ba,da gudun gaske ta juya tabar store ɗin,kitchen ta nufa Ta ɗauko wuƙa lafiyayya,Kafin ta ƙarasa saman hannun kujera inda ta ajiye wayar junaid ta ɗauketa,dama ita waya koda security torch ligh na kawoka,Don haka ta kunna fitilar wayar,Ta nufi store ɗin a hanzarce,Rufe ƙopar tayi bayan ta shiga,gaban waɗannan jerin Jarkokin man ta nufa,da yake Allah yayi mata ƙarfi,ɗaukar jarkar Tayi tajata izuwa gaban window ɗin,Sannan Ta hau saman jarkar,Iya idanuwanta ne suka kai Wurin net ɗin tagar,


Wuƙar hannunta ta sanya,ta dinga caccakata jikin Ragar,nan take wurin ya lomatse,Gagara wuƙar ta shiga yi tana Yanka Ragar,har sai da ta cire Rabinta,Tukunna Ta saki wuƙar kasa,Haska wayar tayi tana leƙen ɗakin,Saboda tsabar duhun ɗakin fitilar wayar tayi mashi kaɗan,Amma a haka tadinga ƙura ido tana kallon abubuwan dake cikin ɗakin,Wato wasu tsofaffin makamaine aka ajiyesu acikin ɗakin,ga wasu tuluna kamar na ruwa,A jikin bangon ɗakin Ƙwaryoyi ne aka ratayasu,Samansu an rufesu da faifai,ta kasa ganinshi,har sai da ta fidda rai,tana ƙoƙarin janye wayar ta bar wurin,kawai ta hango ƙurar dake danƙare a ƙasan ɗakin tana motsi,nan take gabanta Ya faɗi Rass,lokaci guda ta gane cewa mutunne kwance ƙasan ɗakin,yayi buɗu buɗu da ƙura,nan take zuciyarta ta karaya batasan Lokacin da ta fashe da kuka ba,Don tana ji aranta cewa Shi ne,Batasan taya zata Iya taimakonshi ba,tunda alamun sun nuna cewa babu ƙwari a jikinshi,balle ya iya takowa wurin Window ɗin Ya biyo ta ciki,tunda tagar tana da girma,


Tana cikin wannan Yanayin,Hawaye shaba shaba akan fuskarta,karaf kunnuwanta Suka jiyo mata dirar Mota a cikin gidan,Zo kaga tashin hankali,A firgice ta duro daga saman jarkar,saboda tsabar ruɗi anan tabar wayar Junaid ƙasa, ta rarumi wuqar data wurgar,ta ruƙota a hannunta Da gudu ta rufe ɗakin,Ta nufi kitchen,ƙiris Ya rage ta shiga kitchen ɗin,Muryar Hajiya sarat ta katse mata hanzarinta

  "AMRISH"!a gigice Amrish Ta juya tana kallonta,Material ne ajikinta,Ta kashe ɗaurin kallabin nan na rashin mutunci,hannunta ruƙe da hand bag ɗinta,

  Wani irin fitsari ne ya matsi amrish,Sai faman haɗiyar yawu take yi,idanuwan nan wuri wuri dasu na mara gaskiya,

  "Naga kamar bakiyi farin ciki da dawowata ba ko"?

  Shiru bata amsa mata ba,

"Ko har yanzu fushin kike yi dani ne"?nan ma shiru Amrish bata Amsa mata ba 

  Sai lokacin Hajiya sarat ta lura da wuqar dake hannunta,cike da mamaki tace"Ke!me kikeyi da wuqa a hannunki?Ya akai naga hawaye sharkaf akan fuskarki?wai meke faruwa ne"?

  Ajiyar Zuciya Amrish ta sauke,Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Albasa nake yankawa a kitchen,ina girka abinci ne,saboda Yunwa nake ji,"ta ƙarasa maganar tana shafa cikinta,

Dariya Saratu Tayi"Manya Na girki,kinga yarda kika canza kamanni?Sai kace bada Gass kike girki ba?Yo wanna ae koda murhu kike girki baza ki yi irin wannan galabaitar ba,Fuskarki ta ca6e sosai kamar ma hada kwalliya kikayi ga janbaki nan dama dama har akan kumatunki"Tana magana tana dariya,

  Murmushin yaƙe Amrish tayi tareda sanya hannu tana goge zufar goshinta,Ba ƙaramin daɗi taji ba,Ganin bata Ganota ba,

  "Nasan ban kyauta maki ba,Nayi maki alƙawarin zamu fita shopping,Banji daɗi ba daughter,Wani emergency call ne aka yi mun Shiyasa na fita batare dana sanar maki ba,"

  "Kada ki damu mommy,Ni yanzu ma ta cikina nake yi,bari na shiga na ƙarasa Yanka Albasar,"

  "Okey,Zan shiga ciki na ɗan watsa ruwa,inaso na kwanta na huta,don wlh na gaji,Amma idan na tashi,Zuwa anjima kaɗan sai mu fita Shopping ɗin"

  "Toh mommy,A huta Lafiya,"daga haka ta shiga kitchen ɗin,Hajiya Sarat kuwa Upstairs ta wuce,


Ajiyar zuciya Amrish ta sauke,A dole ta ɗauko albasa ta shiga yayyankata,can kuma ta ajiye yankar albasar,ta soma zarya acikin kitchen ɗin tana tunanin Ta yadda za'ae Ta taimaki Junaid Ya koma wurin Iyayenshi,In ba haka ba kashe shi zasu yi,in ma basu kashe shi ba,Wannan daƙyar zai kai labari,


Tunanin kiran Sehrish Tayi a waya,Domin kuwa Ta haddace numberta,Babbar matsalar shi ne Babu wayar da zata Kirata,Wayar Junaid akwai security,duk ta gaza samun natsuwa,a ƙarshe ta ajiye yankar Albasar,ta fito daga kitchen ɗin ta nufi upstairs,A bakin ƙopar ɗakin mommy ta tsaya,tura ƙopar ɗakin tayi a hankali ta leƙa,bata same ta aciki ba,amma taji saukar ruwa alamar wanka Take yi,


Jiki na rawa ta shiga cikin ɗakin cike da fargabar karta kamata,handbag ɗinta ta buɗe anan ta samu wayoyinta guda biyu,ƙaramar nokia da kuma Infinix,duka ta haɗa wayoyin,Sannan ta ɗauki key ɗin ɗakin data gani saman side drawer,fitowa tayi daga cikin ɗakin,Ta garƙame Hajiya Saratu da mukulli,gudu gudu sauri sauri ta sauko downstairs,tana ƙoƙarin kunna ƙaramar wayar kenan,Infinix ɗin hannunta ta soma ringing,ƙura ido tayi tana kallon Sunan daya bayyana akan screen ɗin wayar,Daddyn Amrish,

  Maimaita sunan Tayi"daddyn Amrish!"da mamaki akan fuskarta,

"Dama amrish nada uba,"ta tambayi kanta sai kace ba ita bace Amrish ɗinba 

  Picking call ɗin tayi tare da kara wayar akan kunnanta,

   "Kina jina saratu,Wlh karki kuskura kibar yaron nan araye,Don na lura Yaya bazata ta6a bari A ɗauki fansa akanshi ba,Abunda nakeso dake shine,ki ƙwaƙule mashi idanuwanshi nasan zaki iya,Sannan ki binne mun shi da ranshi in bai mutu ba,"

  Wata irin zufa ce ta wanke mata fuskarta,Lokaci guda tsananin tsoro ya bayyana akan fuskarta,mutumin bai jira amsarta ba,Yaci gaba da magana duk a tunaninshi da Saratun Yake magana,

  "Banaso Ya wuce Yau araye,Kawai ki aiwatar da abunda nace maki,"a gigice Amrish tayi rejecting ɗin kiran,don bazata juri bata lokaci ba wurin sauraron munanan kalaman mutun daya kira wayar,Amma fa tajima tana nanata sunan da Mommynta tayi mashi saving a wayarta,wai daddyn Amrish,A rasa wa za'a sanya ma suna daddyn Amrish sai wannan Mugun,me kashe ƴa'ƴan mutane,


Dogon tsoki Taja,taso ace zata Iya buɗe infinix ɗin don tayi bincike akan wayar,Sae dai kash akwai security ajikin wayar,ƙaramar wayarce kaɗai babu security ajikinta,Call log ta shiga tare da dialling number ɗin Sehrish ta danna mata kira,Sai faman tsuma take yi,don ta qagara Sehrish ta ɗaga kiran ta sanar da ita cewa Yayanta na a gidansu,Suzo su dauke shi,


Almost 3 times Kiran nashiga,amma Sehrish bata ɗaga ba,sakamakon Wayarta dake a silent,tana cikin aljihun doguwar rigar Jikinta,

  A ruɗe amrish ta shiga faɗin"Nashiga Uku!Sehrish dan Allah ki ɗaga kiran!Ya zanyi in bata ɗaga ba,Yanzu idan suka kashe shi fa,Wayyo Allah na,"tana cikin wannan zullumin,


A can ɗakin Hajiya saratu kuwa,tana fitowa daga toilet,daga ita sai towel ɗaure a chest ɗinta,kaitsaye ta nufi handbag ɗinta donta ɗauki wayarta,tana zura hannu taji wayamm babu wayoyinta,Zazzage kayan cikin jakar tayi nan ma wayaam babu su dagaske dai an ɗauke mata wayoyinta,da farko tayi tunanin cewa ko a wurin meeting ɗin da taje ne aka dauke mata waya,Amma daga baya kuma sae ta tuna cewa tayi waya acikin mota lokacin da take shigowa cikin gidan,kodai Amrish ce ta ɗauke su!Nan take gabanta Ya faɗi rass,Sae lokacin ta tuna da wayar Junaid data bari asaman gadon,itama wayar babu ita,tun lokacin da tashigo ɗakin tayi noticing ɗin hakan amma bata kawo komai aranta ba,saboda ranta ya bata cewa ko ba anan ta ajiye wayar tashi ba,


A hargitse ta nufi ƙopar da dukkan ƙarfinta tasa hannu ta tura ƙopar,aikuwa taji an rufeta da mukulli,bubbuga ƙopar tashiga yi tana ƙwala mata kira

  "Amrish!Amrish!wlh karki kuskura kice zakiyi mun bincike acikin wayata!kizo ki buɗe ƙopa tunkafin in buɗeta dakaina,"

Ƴan hanjin cikinta ne suka kaɗa lokacin da tajiyo Muryar Mommynta,.  

  Tabbas in bata yi hanzarin kawar da junaid daga cikin ba,su duka biyun zasu iya rasa ransu,

  Duk da halin da take ciki hakan bai hanata mayar ma mommynta martani ba,.  

  "Wlh bazan buɗe ba mommy,Allah ya kamaki,Yau saina tona maki asiri,"

  Kamar ƴar dambe haka Hajiya saratu ta dinga bubbuga ƙopar,

  "Amrish wlh idan har kika kuskura kika tona mun asiri,Saina kashe shi acikin gidan nan,"ita duk a tunaninta Amrish a iya binciken wayarta ta tsaya batasan cewa ta gano inda suka 6oye shi ba,

  Ganin taƙi zuwa ta buɗe mata ƙopa yasa ta nufi cikin ɗakin tana neman ɗayan key ɗin ɗakin,Gaba ɗaya ta hargitsa ko'ina,

  Amrish kuwa yatsun hannunta na kerma Ta shiga ƙoƙarun rubuta ma Sehrish saƙo,Bayan ta tura mata text message ɗin,ta jefar da wayoyin saman Sofa,dabara ce ta fado mata,In har ta shiga ta cikin tagar dakin nan data cire ragarta,Zata Iya ƙoƙarin ku6utar dashi,


Da gudun gaske ta koma Store ɗin nan,Ta janyo jarkar man zuwa saitin tagar,ta haye samanta,hannuwanta ta sanya da dukka ƙarfinta ta ƙarasa yayyaga ragar jikin tagar,dama ta tsufa sosai daga taja saita kece,gaba ɗaya ta yakice ta,saukowa tayi daga saman jarkar ta dauko wayarshi da tayi wurgi da ita a ƙasa ɗakin,ta kunna torchlight ɗinta,Sannan ta koma saman jarkar,Da ƙarfin gaske ta kutsa kanta Cikin tagar,ba ƙaramar wahala tasha ba,Saboda girman jikinta don ma Allah yasa Tagar tana da girma,tana jin sauran ragar dake agefe da gefen tagar tana kartar jikinta amma haka ta jure,gaba ɗaya ta rubza cikin ɗakin,ta faɗo ƙasa timmm cikin ƙurar nan,duk ta 6ata mata fuska,A galabaice ta ɗago tare da sanya hannunta,Tana kakka6e ƙurar dake akan fuskarta,ɗago da wayar hannunta tayi tana haska ɗakin,Ga tsoro ga furgici,miƙewa tayi tana haska ƙasan ɗakin har Allah yasa ta gano inda yake kwance,numfashinshi na fita sama sama,zubewa tayi saman guiwowinta,Ta sanya dukkan hannayenta tare da ɗago dashi,yayi buɗu buɗu dashi,ƙurar duk ta rufe fuskarshi,har cikin hancinshi,baka iya ganin komai daga fatar jikinshi,fashewa amrish tayi da matsanancin kuka,kamar ranta zai fita,ya raunata sosai,Alamun sun nuna cewa yana akan hanyar gangara,daƙyar zai iya rayuwa,rungumeshi tayi ajikinta yayin da zuciyarta ke bugawa,Tunawa da Mommynta yasa Ta yunƙura tare da ɗaukarshi asaman kafaɗarta,Yayin da hannunta ke ruƙe da wayarshi,miƙewar da zatayi kenan hasken fitilar hannunta ya hasko mata Wayarta dake dadda6e da ƙura,bata bi ta kanta ba,don a halin yanzu tafi buƙatar Rayuwar Junaid,Ita dai koda gawarshi ce takai masu su ganshi,dole ta tagar ta fara turashi kamar tsumma haka ya faɗo ƙasan ɗakin,ita ma ta biyo ta window ɗin, a hanzarce ta ɗauke shi,saman kafadarta ta kama hanya,fitowa tayi daga cikin ɗakin ɗauke dashi,Ƙura duk ta buɗesu,musamman shi,kamar dodo haka ya koma,ya rame ya shanye ya bushe Ya ƙanjame bawan Allah


Adai dai Lokacin Hajiya saratu ta samu ɗayan mukullin ɗakin dake a cikin drawer chest,jinjina kai tayi tana huci tamkar zakanya haka ta Nufi  bakin ƙopar,Ta murza key ɗin.........


*Masu buƙatar karanta Abban Sojoji har zuwa Takun ƙarshe yayi mun magana Ta Layina whatsapp kawai 08103884440*


*Ayi hakuri da wannan*


⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫⭐💫

*_MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI_*


*DOMIN. DAWO DA MARTABAN NONONKI*


Shin ko kinsan nono yanada matukar muhimmanci a wajan mai gida ,? Shin ko kinsan babu abunda namiji yafiso yafi daukar hankalinahi kamar cikar k'irji , ? To nono shine babban Martaban mace a wajan mijinta , don babu namijin da zaiso mace mai yakunannen nono kamar silifas ,wannan yasa Nazo maku da sahihi kuma ingantaccen maganin nono Wanda bashida wata matsala hadin gargajiya ne , acikin lokaci kalilan zakisha mamakin yadda nononki zai ciko sosai Wanda wannan cikowar ita zata bashi damar da zai tashi sosai ta yadda kema zaki Shiga cikin jerin mata masu aji agaban mazajensu ........kedai hanzarta ki nemi mmn Yusuf mai kayan mata yar mutan sokoto zaki samu ingantattun kayan mata masu tafiyar da hankalin maigida.......don neman Karin bayani   07069711327 ......

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*









Har ta kusa Fita palourn ta tuna da wayar Mommyn nan Nokia,Sehrish zata iya kira Kuma in har tabar wayar za'a samu matsala,Juyawa tayi ɗauke dashi ta koma saman Sofa ɗin ta ɗauki nokia ɗin ga wayar Junaid duka ta haɗasu Sae faman nishi takeyi,tana ƙoƙarin kama Hanya ta fuce,Hajiya Sarat ta bude Ƙopar A fujajan ta fito,waro ido waje Amrish tayi a wani irin Firgice ta watsa da gudu tamkar ba mutun ta ɗauko a kafaɗarta ba,Lokacin Da Hajiya Sarat ta ankare da Junaid dake sa6e a kafaɗar Amrish,Wani irin kukan Kura tayi da dukkan ƙarfinta ta watso a guje irin gudun nan na fitar hayyaci,Cikin Rashin sa'a tana Sanya ƙafarta saman benen,Tamkar an ja ƙafarta gaba ɗaya ta burkice,a jirkice ta sulalo daga saman benen,kanta yayi Mugun buguwa,Qugunta kuwa sae dai muce Allah ya kyauta,


Amrish kuwa tsabar tsoro ko waiwaye batayi ba,lokacin data faɗo entry hall na gidan,Da gudu ta nufi gate,A lokacin baba mai gadi yana yin alwalar sallar Azhar da aka fara kira,Koda yayi arba da Su Amrish Baiyi tsammanin mutane bane,Wurgi yayi da butar hannunshi ya watsa da gudu zai shige ɗan ɗakinshi Ya ɗauko sandar shi,

  Daƙyar Amrish ta iya buɗe baki tace"Baba Mai gadi ni ce,Dan Allah kataimake ni,Ka tsaida mana Taxi mu kaishi asibiti kada ya mutu,"dakatawa baba mai gadi Yayi a sukwane ya juyo yana kallonta,Sae lokacin Ya gane ta,kuma ya gane yaron nan ne na jiya ta ɗauko,ganin zai 6ata mata lokaci yasa ta fashe da kuka tana faɗin"Baba mai gadi kashe mu zatayi,In har bamu bar gidan nan ba,"

  A hanzarce Baba mai gadi ya buɗe mata ƙopa suka fita,har zai tsaya ya tuna cewa Shine yaba Amrish Labarin Yaron,kenan shima Yana cikin hatsari,aikuwa da gudu ya bi bayan Amrish suka miƙi hanya suna neman Abun hawa,A ƙarshe daya ga ta jigata shi ya kar6i Junaid ya ɗaura shi a kafaɗarshi,Babban tashin hankalin tunda suka fito Unguwar babu kowa wayaam dama haka unguwannin ƴan gayun nan suke,Da ace irin geto ne da tuni jama'a sun agaza masu,ɗaiɗaikun mutanan dake wucewa duk wanda yayi arba dasu Amrish saiya watsa da gudu kamar sunga Aljanu,saboda ƙurar da ta 6ata masu jiki,


Da iya ƙarfinta Na ƙarshe ta daddage ta miƙe,ɗago kan da zatayi keda Wuya haƙorinta ɗaya ya 6allo jaga jaga da jini,qugunta ya ruƙe sosai,wani irin azababben raɗaɗi,daƙyar ta samu ta fara jan jiki a galabaice ta nufi wayarta dake ajiye saman sofa,jikinta sai tsuma yake yi,daƙyar ta iya cire password ɗin wayar,Call log ta shiga ta kira wani layi da akayi mashi saving da ƙare kukanka,Daƙyar take magana saboda ciwon bakinta,

  "Duk yarda za'ae karku bari yarinyar nan tabar cikin unguwar nan,Nasan zaiyi wuya su samu abun hawa,da ita da yaron Gawarsu kawai nakeso ku kawo mun...."tana magana tana goge zufar goshinta,ga wani irin huci dake fita abakinta,.  

  "Akwai ƙaramar nokia ɗita a hannunta,Zan tura maku Lambar wayar kuyi tracking ɗinta,"ta ƙarasa maganar tare da yin rejecting ɗin kiran,Gaba ɗaya Amrish ta ɗaure mata kai,saboda ta ɗauketa Shashasha,A irin rainon da tayi ma Amrish irin sangartattun nan ne,bata da wayau haka,Sai gashi yau ta bata mamaki,wai har tasan ma inda suka 6oye shi,koya akai duk tasan wannan?


Lokacin da Su Amrish suka haura saman titi,suna neman abun hawa,duk mai motar da suka tsaida sai yaƙi tsayawa,Baiwar Allah duk tabi ta ruɗe gashi sam taƙi tunanin yarda nokia ɗin Hajiya sarat data ɗauko,kuma ta hanyar bin diddigin layinne kaɗai za'a san Location ɗin da suke,


Suna cikin wannan tsayuwar,wata danƙareriyar mota ta shawo kwana da gudu,bata tsaya a ko'ina ba sai agabansu Amrish,mutuwar tsaye tayi lokacin,shi kanshi baba maigadi ya firgita da ganin motar,Jim kaɗan mamallakin Motar ya fito jikinshi sanye da fararen kaya hatta takalmanshi,Facemask ɗin fuskarshi Ya hana Amrish ta gane shi,


Yayi mamakin ganinsu cikin wannan halin,bai tsaya tambayarsu Lafiya ba Kawai ya buɗe masu bayan motar,badon ta yarda dashi ba hakanan dai kawai suka shiga cikin Motar tunda ba yarda zasu yi,a back seat na motar ta shiga baba mai gadi ya jinginar da junaid a tsakiya kafin shima ya shiga,Mai motar ya fusgi motar da gudu,a dai dai Lokacin motoci guda uku masu blank tunted ƙirar Range rover suka bi bayan motar shi,da wani irin mahaukacin gudu mutumin ke tuƙa motarshi,yarda kasan filin ƴar tseral haka motocin nan suke gudu asaman titi,


Amrish sai kuka takeyi tunda take a rayuwarta bata ta6a ganin tashin hankali ba irin na ranar,ba komai ya ƙara tsoratar da ita ba fa ce Harbin bindiga da taji a bayan motarsu,Ya salam!gashi hanyar da suka biyo babu ƴan sanda balle su samu taimako,


Ɗaya daga cikin Ƴan ta'addan da suka biyosu wanda ya buɗe murfin motar ya miƙe a tsaye hannunshi ruƙe da irin wannan bingidar mai fitar da bullet kamar bomb,kwakkwaran Saiti Yayi ma Motarsu,Yana sakin Bullet ɗin mai girman gaske nan take Ya hau saman motarsu Ya fashe gaba ɗaya Wuta ta kama ci a bayan boot ɗin Motar,Hakan yasa motar ta dakata da tafiya,ganin sun ci nasara akansu yasa suka tsayar da motocinsu,Suka diddiro daga cikinta kusan Su takwas ne,Ƙirar jikinsu gwanin ban tsoro,babu ɗigon imani akan fuskarsu,kowanne hannunshi ruƙe da manyan makamai,


Suna ƙarasowa gaban motar,ɗaya daga cikin samudawan nan ya damƙi murfin motar ya 6alleshi,hannu yakai tare da damƙo rigar mutumin dake acikin motar ya wurgoshi waje,basu tashi ankara ba,Sae da Mai tuƙin motar ya fito yana faman ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'una,Leƙa cikin motar sukayi Wayaam basu ga Amrish da yaron ba,Ashe Ba motarsu bace,Sunyi mistake Saboda mai wannan motar da suka kama iri ɗaya ce da motar da suka bi su Amrish,


Da sauri Suka koma cikin motocinsu,A guje suka ja motar,Sunbar bayin Allah da aikin neman taimakon kashe masu wutar motarsu,don ma Allah yasa babu wanda ya raunata acikinsu,



A 6angaren Su Amrish kuwa,mutumin dake tuƙa motarsu ne ya umarce ta data jefar da wayoyin hannunta gaba ɗayansu,nan take ta zuge glass ɗin motar ta wurgar dasu waje,Bayan ta jefar dasu sai ya Canza hanya da wani irin gudu yabar titin,Su kuma waɗannan miyagun da suka fara yin tracking ɗin Layin wayar Hajiya sarat na ƙaramar nokia ɗin da aka basu,Ta hanyar laptop ɗin dake a hannun wani kwararre acikinsu,Sae location ɗin ya dinga nuna masu hanyar da Amrish ta jefar da wayoyin,Nan fa suka miƙi hanyar cike da sa ran zasu kamasu,Lokacin da motarsu ƙare kukanka ta ƙarasa inda Location ɗin Ya basu,Sai suka tsayar da motocinsu,A zafafe suka fito suna waige waigen neman inda suka ajiye motarsu,Sai da suka gama shan wahalar nemansu a Area ɗin wurin abun takaici sai ga wayoyin sun tsinta yashe a ƙasa,Rai a matuƙar 6ace suka hanzarta komawa cikin motocinsu batare da sun ɗauki wayoyin ba,Nan fa suka ruɗe saboda hanyoyi ne guda uku,Ta hannun dama da kuma ta hannun hagu,Ga kuma wadda ta mike straight,To fa sun ruɗe a wannan lokacin,Basu san ta wace hanya su Amrish suka bi ba,A ƙarshe kawai suka raba motocinsu dama guda uku ne ɗaya tabi straight,ɗaya tabi Left ɗayar kuma tabi Right,Don sunsan Dole a ɗaya daga cikin hanyoyin suka bi,



*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 2 na rana,


Wayar Ishaq ta soma ringing,A lokacin dawowarshi kenan daga wurin aiki,Buɗe mashi mota sergeant Yayi Ya fito daga cikin motar hannunshi ruƙe da wayarshi,picking call ɗin Yayi tare da kara wayar a kunnanshi,


Fuskarshi ɗauke da murmushi ya soma magana"Mutanan Damaturu,Sai yau ake jinku"?

On the other hand Hafsat tace"Wlh Daddy fushi nake dakai,you forgot about me,"

  "Nima ae fushi nake dake,tunda na baro damaturu kin ƙara kirana ne?Ko irin Morning message ɗin nan babu ko,Yanzu da ace ban kiraki ba da shikenan bazaki neme ni ba,"ya ɗanyi maganar yana ɗaure fuska kamar tana agabanshi,

   "Shikenan na ɗauki laifin,Am so sorry,Amma daddy meyasa ka canza Layinka?in na kira wancen Mtn ɗin bana samun shi"

  "Kinga yanzu na dawo daga wurin aiki,Agajiye nake,bari na ɗan samu natsuwa I will call u later,"

A ɗan shagwa6e tace"dan Allah Daddy,idan ka huta kada ka manta ka kirani akwai maganar da nakeso nayi dakai,"

  "Toh,"ya amsa tare da kashe kiran Ya nufi cikin gidan aranshi yana faɗin"yanzu haka saboda Mommynta ne yasa ta kira ni,lokacin daya shiga gidan ya yi mamakin yarda aka gyara mashi ko'ina fess,murmushi ya dinga saki don ya san cewa aikin hajjaju ne,wani irin ƙamshi ke tashi acikin palourn,


Ga lafiyayyen abinci An jera mashi asaman dining,Dama da wata matsiyaciyar yunwa ya dawo,A hanzarce ya haura upstairs ya shige Bedroom ɗinshi,Bayan ya rage kayan jikinshi ya faɗa cikin toilet,Within mins Ya fito Ya kimtsa kanshi cikin jallabiya,Saukowa Downstairs Yayi kaitsaye ya nufi dining ya zauna,Da kanshi Yayi serving ɗin abincin ya zauna yana ci yana murmushi kamar wani zautacce,Sai da ya kammala cin abinci,tukunna ya koma saman Sofa ya zauna tare da aza ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya,


Wayarshi ya ɗauko ya lalubo Layin Hafsat ya danna mata kira,Kamar jira takeyi ta ɗaga kiran,

  "Daughter ina sauraronki!maganar menene kikeson Yi dani"?

"Daddy dan Allah ka taimaka,Nasan zaiyi wuya ka fahimceni,wlh Mommy tana cikin mawuyacin hali,Ta zama abun tausayi,ta kira ni da wani layi jiya tana kuka tana rokona cewa inyi maka magana ka yafe mata,Ta gane kuskurenta,Rayuwarta ta wulakanta Daddy a gefen bishiya take kwana zaune ba bacci,dare da rana a wurin nan take Yini......."

Tunkan Hafsat takai ƙarshen Maganarta,Ishaq ya katse ta"ke yanzu kin yarda da maganarta?Kodai kun haɗa baki ne da ita?

  Da sauri hafsat tace"Wlh daddy da gaske take,Ae nasa ta ɗauko mun video ɗinta,Wayarma fa aronta takeyi don ta kiramu,Zan tura maka video ɗin ta whatsapp yanzu,zaka shaida abunda nake faɗa maka,"

  Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"its okey,Am waiting for the video,"yana kai ƙarshen maganar ya katse kiran,Kafin Ya kunna wifi ɗinshi ya shiga whatsapp,Messages ne suka fara shigowa cikin wayar,can sai ga saƙon hafsat ya shigo,


Chat ɗinsu Ya shiga,Anan ya samu video ɗin data tura mashi,yatsanshi yasa ya ɗan ta6a video ɗin nan take Ya soma loading,ƙura ido Ishaq yayi akan Screen ɗin wayar yana kallon video ɗin,

   Bai ta6a tunanin zaiga laila a irin wannan ƙasƙantacciyar rayuwarba,a gefen bishiya take zaune,gefenta kwanon bara ne,ƙafarta ɗaya ta lalace babu kyan gani wani irin ruwa ke fita acikinta,Sae kuka takeyi tana magana

  "Don Allah Ishaq ka taimaki rayuwata,ba don halina ba,dan Allah da manzonsa zakayi,Nasan nina jefa kaina cikin wannan halin,Ku kalli irin wurin da nake rayuwa,kowa ƙyamar taimakona yake yi,babu mai son zuwa wurina saboda warin da nake yi,"_

  Saboda tsabar tashin hankali,Da sauri Ishaq ya kashe video ɗin tare da yin wurgi da wayar saman sofa ɗin,

Jingina bayanshi Yayi ajikin kujerar,tabbas Yaji tausayinta amma abunda ya ɗaure mashi kai shine taya akai taje Enugu!Uban me yakaita?don a iya saninshi bata da wata alaƙa da garin,Ya jima a haka kafin Ya ɗauki wayar Ya sake kiran Hafsat,

  Tana ɗaga kiran Yace"Naga video ɗin,wlh hafsat ba don zuciyar musulunci ba,babu abunda zaisa na taimaki Laila!ke bari in faɗa maki zan taimaketa ne kawai Saboda Allah!Taci albarkacinki hafsat!Zansa a ɗaukota akaita asibiti,Inyaso ko ƙafarce su cireta A maidata maiduguri,Amma ni bazan sake rayuwa da laila ba,"

  Fashewa hafsat Tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,daƙyar ta samu ta tsagaita da yin kukan tace"Nagode sosai Daddy,koma miye laifinta ne,ita taja ma kanta,naji daɗi sosai Daddy Am really proud of u,"

  "Yaushe zaki dawo gida!kinsan cewa hutun aikin da kika ɗauka ya qare ko"?

  "Eh daddy,Ina nan ina shirin dawowa amma yanzu gidan bazaiyi mun daɗi ba,nafison na zauna a wurinsu Abba,tunda ga ƴan uwana acikin gidan inyaso sai ka nema mun transfer na dawo aiki a Abuja,"

  "Idan kika koma Abuja,ni kuma fa?nikaɗai akeso inyi ta zama a kaduna "?

  A ɗan shagwa6e hafsat tace"idan zaka ƙara aure,Sai in dawo nan,"

Murmushi ya saki anzo dai dai inda yafi so,

  "Calm down ur mind,just ki dawo gida kawai,Cikin ƴan kwanakin nan Nima zanyi aure,"

  Yana jiyo sautin dariyarta,alamar taji daɗin maganarshi,sun jima suna waya kafin suka Yi sallama,


*Boss Bature*


*AMANI*


Tana kwance saman gadonta,Amal ta faɗo cikin ɗakin Hannunta ruƙe da wayarta,hawa saman gadon tayi har zuwa inda Amani ke kwance tana sharar bacci,Hannu tasa tana bubbuga ƙafarta,

  "Aunty Amani!ki tashi ana kira,"

Daƙyar ta iya buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,sun ɗanyi jawur dasu,rai a6ace ta kalleta"Bana hanaki tashi na daga bacci ba in aka kira ni"?

  Sunnar dakai Amal tayi"Am sorry,dama Aunty hayaam ce ta kira tana kuka......"hankali aɗan tashe Amani ta yunƙura tare da mikewa zaune tana faɗin"kuka kuma!Allah yasa lafiya,"ta ƙarasa maganar tare da kar6ar wayarta da Amal ke miƙo mata,

  Call log ta shiga,Anan taga kiran da hayaam tayi mata,

  Calling ɗin layin tayi,bayan Hayaam ta ɗaga kiran Amani ta kara wayar a kunnanta,tun kafin tayi sallama taji shessheƙar kukan Hayaam

  "Subhanallahi!wai meke faruwa ne?hayaam ki buɗe baki kiyi magana mana,"a ɗan ruɗe tayi maganar,

    "Kodai Wani ya rasu ne"?

Sai lokacin Hayaam ta soma magana"Aunty amani muna cikin masifa!munga rayuwa,rayuwarmu ta wulaƙanta a idon jama'a......"anan hayaam ta kwashe dukkan abunda Ya faru bayan komawarsu maiduguri ta sanar da ita,

  Saukowa Amani tayi daga saman gadon tana ambaton"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,.  

  "Allah yajiƙan Mammy,Allah ya gafarta mata zunubbanta,Amma banji daɗin irin mutuwar da tayi ba,ƙaddara ta riga fata,da kunsani tun farko baku barota ba, 

  Cikin shessheƙar kuka hayaam taci gaba da magana,

  "Munaji muna gani,zama gidanmu ya gagaremu,Mutane sun ɗaura mana karan tsana,Yanzu haka a gidan Malam limam muke,matanshi sun tsanemu,suyi ta tseguminmu suna zaginmu,Abinci basu bamu sai in liman yana acikin gidan,Abra ma sai addu'a domin kuwa ta fara samun ta6in hankali,sai sambatu takeyi tana faɗin duk ita taja,Itace tayi silar mutuwar Mammy...."kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da ya cuyota,

  Daƙyar Amani ta lallasheta"kuyi haƙuri ku rungumi ƙaddara,in sha Allah komai zai wuce,Yanzu nidai zanyi ƙoƙari wurin ganin na taimaka maku,Ko gidan ne a gyara maku shi,kafin Allah ya kawo maku mazajen aure,don kuwa yin auren shikaɗaine rufin asirinku,in ba haka ba mutane bazasu daina tsangwamarku ba,"

  (Wlh matsalar mutananmu kenan,idan mutun Ya aikata zunubi arayuwarshi yazo ya yi nadama ya shiryu,Sai su dinga tseguminshi suna ƙyamatarshi,Shi kanshi Allah daya halicce mu yana son bayinsa waɗanda suka Tuba daga aikata zunubi,Amma wasu mutanan da ruƙo,shiyasa wasu ko sun shiryun daga baya sai su koma ruwa saboda mutane,Wannan babban kuskure ne saboda mutane ka koma kana aikata barna,Makomarka zaka duba,In zaka tuba dan Allah zakayi,Dan kuma kanka,ba don mutun ba,a karshe ina mai jan hankalinmu da mu kiyaye harshenmu don zai iya jefamu  a halaka,aduk lokacin da wata mummunar kaddara ta fada ma wani muyi Addu'a mu nemi tsarin Allah kada mu rinka zundenshi don muma bamu fi karfin Allah ya jarabemu ba,Allah ubangiji ya rabamu da mummunan kaddara yasa mufi karfin zukatanmu,Amin )


Sosai Hayaam ta shiga yi mata godiya,kafin daga bisani Su kayi sallama,


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 6 na marece,Sehrish na kwance saman gadonsu abun duniya ya isheta,duk ta shiga damuwa saboda rashin samun kwakkwarar hujjar da zasu kama Azmee,tana cikin wannan zancen zucin taji an banko kopar ɗakin,A firgice takai idanuwanta kan mai shigowa,Jahad ce ta faɗo ɗakin fuskarta sharkaf da hawaye,a ruɗe Sehrish ta shiga tambayarta Lafiya,

  "Bakisan meke faruwa ba,Ga Abba can ya yanke jiki ya faɗi rai hannun Allah,"jin wannan maganar yasa Sehrish ta sauko daga saman gadon jikinta na kerma ta nufi hanyar fita ɗakin,atare da jahad suka fita,


Abunda ya faru,Alex na zaune gefen gado tana jiran fitowarshi daga toilet,tun da ya shiga shiru bai fito ba,tun tana sa ran fitowarshi harta fara tunanin ko lafiya kusan Awa ɗaya da rabi yana acikin toilet ɗin nan,Miƙewa tayi ta nufi toilet ɗin tasa hannu ta kwankwasa ƙopar"Abban Junaid!"ta kira sunanshi da ƙarfi,Shiru bai amsa mata ba,a ƙarshe dai ta yanke shawarar shiga ciki,tana tura ƙopa ta same shi kwance saman tiles,idanuwanshi sun jirkice,jikinshi sai kerma yake yi,Fasa ƙara Mommy tayi anan ta zube tana jijjigashi,Ganin cewa dagaske fa baya acikin hayyacinshi yasa ta miƙe da gudu ta fito daga ɗakin tana kuka,


A lokacin Abusufyan da abu suna zaune a main palour tare dasu Hosana da Jahad,Tun daga kan yarda ta faɗo falon Yasa su miƙewa suna tambayar lafiya,Kasa buɗe baki tayi sai dai nuna masu hanyar bedroom ɗinshi da tayi duk tabi ta ruɗe,da gudun gaske Abusufyan ya nufi ɗakin tare da abu,suna shiga ciki dama ƙopar toilet ɗin abuɗe Mommy tabarta,nan suka sameshi cikin mawuyacin hali,sunyi matuƙar girgiza,Cuccuboshi Abusufyan yayi ya fito dashi daga cikin toilet ɗin,Ya janyoshi zuwa saman gadon ya kwantar dashi,jiki na rawa Ya curo wayarshi saboda ruɗu daƙyar ya iya lalubo Layin Sgr ya danna mashi Kira,Sai daya bi kowannansu Ya sanar dashi halin da Mahaifinsu ke ciki,


A lokacin dasu Sehrish suka faɗo falon Ya yi dai dai da shigowar Omar da Sgr,da gudun gaske suka shigo kaitsaye suka nufi bedroom ɗin Abbansu,wucewarsu keda wuya Kanal yousouf ya faɗo falon da gudu shima Ya wuce part ɗin,gaba ɗaya sai da matasan gidan suka hallara a ɗakin,wasu tuni sun fara zubar da hawaye,tsoransu kada su rasa mahaifinsu a wannan halin da suke ciki,sae faman ambaton innalillahi wa'inna ilaihirraji'un suke yi,


Fawan dasu twins kuwa tuni sun fara kuka kamar wasu ƙananun yara,

  "Addu'a zakuyi mashi ba kuka ba,in sha Allah zai samu lafiya,"acewar Abusufyan shi kanshi dauriya kawai yake yi,don kada suga rauninshi,hakan zai ƙara tayar masu da hankali,

   yanke shawarar kaishi Asibiti suka yi,Sgr ne ya ɗauke shi asaman kafaɗarshi,Sauran suka bi bayanshi,

  Suna fitowa entry hall ɗin gidan,da gudun gaske armstrong ya buɗe mashi mota ya kwantar da Abbansu aciki,Sannan ya bude mashi front seat ya zauna,Jan motar yayi da gudun gaske motar Marshal tabi bayansu,Motocinsu Kanal yousouf suka rufa masu baya,hada Oummansu Sehrish aka tafi asibitin a motar fawan ta zauna tare da Jahad da Hosana,Mommynsu Junaid kuwa tana a motarsu Abusufyan sai lallashinta Yake yi,duk ta shiga damuwa alokacin motocinsu suka fita daga babban gate ɗin gidan,mutun uku aka bari a gidan Aunty Azmee dake kumshe a ɗakinta,Sae Haroon dake kulle a medical room dinsu,


Sehrish bata samu tabisu ba,daga komawa ta ɗauko mayafinta sai dai tajiyo tashin motocinsu,kamar tayi hauka lokacin da ta fito waje bata samu motar ɗaya daga cikinsu ba,anan ta zuƙunna gaban ƙopar palourn tana kuka,ga tsoron shiga gidan da takeyi,




Da wata irin jiniya motocinsu suka hau saman titi a jere,Lokacin da suka ƙaraso Katafaren Asibitin Sgr,Sai suka tsaida jiniyar,a hanzarce bayan sunyi parking ɗin motocin nasu,Sgr ya fito Ya ɗauki Abbansu,sauran ma suka fito gaba ɗaya suka wuce cikin asibitin,Zo kaga taron nurses da likitoci,Ai tunda suka ji isowar Sgr kuma suka ji cewa Mahaifinshi ne baida lafiya,nan fa sukayi dandazo domin duba lafiyarshi,


A wani katafaren ɗaki suka kwantar dashi,kusan likitoci shida ne akanshi daga cikinsu hada Doctor Emran,


Sgr baisamu shiga ba,saboda a halin da yake ciki a yanzu bazai iya duba Abbansu ba,yana cikin matsananciyar damuwa saboda yasan dalilin ciwon Abban nasu,dama yace su fara ƙirgen kwanakin mutuwarshi,in har basu dawo mashi da yaronshi ba,


A saman waiting seat suka zazzauna suna jiran tsammani,Omar da Sgr suna a tsaye,Kowa ka kalli fuskarshi gwanin ban tausayi,

  "I can't forgive my self,idan har Daddy ya mutu silar 6oye mashi mutuwar Junaid da mu kayi,"Ya ƙarasa maganar yayin da idanuwanshi suka cicciko tab da hawaye,

  Ruƙo hannunshi Omar yayi"bakai kaɗai ba Rafayet,nima bazan yafewa kaina ba,in har muka rasa shi,wlh i ave regretted already,Da mun sani tunfarko mun sanar dashi gaskiya kawae tunda dama gudun hakan yasa muka 6oye mashi,"gaba ɗaya duk sun sha jinin jikinsu,


"Dan Allah kukan ya isa haka,twins,fawan da irfan,in na sake jin shessheƙar kukan wani acikinku wlh zaku koma gida ne,"kanal yousouf ne keyi masu faɗa,.  

  "Sai kace ba musulmai ba!maimakon ku tayashi da addu'a amma kun dage sai kuka kukeyi,"ya ƙarasa maganar tare da jan guntun tsoki,idanuwanshi cike tab da kwalla,

  Abu kuwa sai faman lallashin Mommy takeyi,ganin yadda take ta shar6ar kuka,

  Abusufyan ne yace"don Allah Aunty kidaina,kina ƙara tayar masu da hankalinsu,keda yakamata ace kina lallashinsu,"hannu tasa tana share hawayen fuskarta,juriyarce bazata iya ba,ita kaɗai tasan yarda take ji acikin zuciyarta,


Fitowa Doctor emran yayi daga cikin ɗakin da aka kwantar da Abbansu,Aikuwa da sauri suka tunkareshi,kowa yana tambayar ya jikin nashi,

  "Ku kwantar da hankalinku,Yana samun sauƙi,Addu'ar ku kawai yake buƙata,"yakai ƙarshen maganar tare da aza idanuwanshi kansu Sgr da Marshal"ina son ganinku a office,"

  Tunda suka ji haka sai jikinsu ya ƙara yin lakwas,gaba Dr emran Yayi suka bi bayanshi,har izuwa Office ɗinshi,Wuri ya samu ya zauna,kafin suma suka zauna suna fuskantarshi,

  A tsanake ya soma yi masu bayani"nasan kunsan meke damun mahaifinku,damuwa ce akan rashin Junaid,Yanzu haka dana baro ɗakin,Sambatu yake yi yana ambaton sunan shi,"dakatawa ya ɗan yi da bayani yana kallonsu,jikinsu sai tsuma Yake yi,

  "Jinin shi ne ya hau sosae,Ga kuma Ciwon zuciya dake barazanar kamashi..."

  Tunkan emran yakai ƙarshen maganar,Omar ya dafe kai jikinshi na kerma,jikinsu Ya gama mutuwa,

  "Yanzu ya zamuyi kenan?menene solution"?Sgr ne yayi tambayar,

  "Akwai matsala fa,saboda ya ƙwallafa ranshi akan son yaron,Idan har ba ganinshi Yayi ba,tofa sai dai abishi da addu'a,"

  "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"miƙewa Sgr yayi da sauri ya fice daga Office ɗin,gaba ɗaya sun rasa inda zasu tsoma ransu suji daɗi,


Miƙewa Sehrish tayi daga zuƙunnan da take abakin ƙopar palourn,Hannu ta zura acikin aljihun rigarta,ta curo wayarta don ta kira Jahad taji Ya jikin Abban nasu,

  Tana kunna wayar,ta shiga Call log anan ta samu missed calls da baƙuwar number,har kusan sau 10 aka kira,Batasan number ɗin wanene ba,Har jaraba kiran Layin tayi wayar nata ringing ba'a ɗaga ba,

  Bayan kiran ya katse ne,ta lura da message ɗin da aka turo mata,Da sauri ta buɗe saƙon ta soma karanta shi kamar haka,

__Sehrish na kira layinki baki ɗaga ba,Amrish ce inason magana dake game da ɗan uwan nan naki,dan Allah idan kinga saƙon nan ki kira ni_

  Abun ya ɗaure mata kai,tunani ta shiga yi wani ɗan uwanta ne Amrish ke magana akai,sake kiran Layin tayi wayar ta dinga ringing amma ba'a ɗaga ba,

  Katse kiran tayi,tana ƙoƙarin juyawa ta koma cikin gidan kira ya shigo layinta da baƙuwar number,da sauri ta ɗaga kiran tare da kara wayar a kunnanta,tunkafin tayi sallama muryar Amrish ta katse mata hanzarinta,

  "Sehrish kina ina ne!ina ta kiran Layin wayarki amma baki ɗaga ba,magana ce akan Junaid na tura maki Address ta message,kibar komai kikeyi kizo ki same mu"tana kai ƙarshen maganar ta katse kiran,

  Wani irin faɗuwar gaba Sehrish taji,Abun ya matukar  ɗaure mata kai,musamman data ambaci sunan Junaid,

  

Hannunta na kerma ta shiga duba message ɗin da aka turo mata,kwatancen inda zata same su ne,


Tarasa ya zatayi,ita dai ba mota gareta ba,gashi babu wanda ya rage acikin gidan balle ya kaita,kama hanya tayi ta miƙi titin da zai sadaka da babban gate ɗin gidan,Sae faman zumbula sauri take yi,Sai da tasha wahalar zuwa babban gate ɗin,Sojojin dake tsaron gidan suka hanata fita,kamar ta fashe da kuka,


A dole ta shiga kiran layin matasan gidan,Duk wanda ta kira bai ɗagawa,har Abusufyan ta kira shima bai ɗaga kiran ba,

  

Sai da ƙyar ta samu Hosana ta ɗaga kiranta,da sauri ta kara wayar a kunnanta,

  "Hosana Ya jikin Abban"?

  "Nima bansani ba,Sun shiga dashi ciki,"

  "Dan Allah idan akwai wani kusa ki bashi wayar,"

  "To"ta amsa mata,jim kaɗan taji muryar Kanal yousouf,

  Sai da ta fara tambayarshi jikin Abban nasu,Ya sanar da ita cewa da sauki,tukunna tace"Gani nan zan fito gida an hanani,dan Allah ka taimaka kasa su barni na fita,nima asibitin zanzo,"

"Ki basu wayar,"Cire wayar tayi daga kunnanta ta miƙa ma ɗaya daga cikin sojojin,ya kar6a su kayi magana dashi sannan ya miƙa mata wayar,"Zaki iya tafiya,amma yace kada abarki ki fita ke kaɗai,don haka wani daga cikinmu zai ɗaukeki a mota ku fita,"

  Ba ƙaramin daɗi taji ba,dama ƙarfin hali ne kawai,ko kuɗin abun hawa bata dashi,


Anan ta tsaya,wani sergeant ya ɗauko mota ta buɗe ta shiga ciki ya tashi motar,saida suka hau saman titi sannan yace"Madam ina zuwa"?

  Karanto mashi Address ɗin wurin tayi kamar yadda Amrish ta rubuto mata a saƙon,


Wani private hospital ne suka shiga,sojan ya fito ya buɗe mata ƙopa ta fito daga ciki,a bakin ƙopar shiga ciki ta samu Amrish a tsaye hannunta ruƙe da waya,wani irin farin ciki ne ya lullu6e Sehrish da gudun gaske ta nufeta,rungume juna sukayi nan take Amrish ta fashe da kuka,

  Ɗago da ita Sehrish tayi tana tambayarta lafiya,

  "Amrish dama kina nan?layinki kona kira bana samu,meya sameki ne?me kike yi a asibitin nan ne"?

  Cikin shessheƙar kuka Amrish tace"mu shiga daga ciki ki gane ma idanuwanki,"

  Ta ƙarasa maganar tare da janyo hannun Sehrish suka shiga asibitin,A A&E aka kwantar dashi,a bakin ƙopar ɗakin Sukayi kici6us da Ya Mu'allim malamin da take ta nema,

  Cike da mamaki ta ambaci sunanshi"Ya mu'allim,"fuskarshi da alamun damuwa atare da ita,Ya amsa mata"Na'am,kina ta nemana ko"?

Jinjina mashi kai tayi alamar eh 

  "Naga saƙon da kika turomin,idan muka samu natsuwa zamuyi magana,Yanzu dai ga ɗan uwanki can kije ki duba jikinshi,"

  Gabanta ne ya faɗi rasss!,kawar da idanuwanta tayi daga kallon fuskar Ya mu'allim ta mayar da idanuwanta kan ƙopar ɗakin,mutun ta hango kwance an sanya mashi oxygen a hancinshi,yayin da hannunshi ke sanye da robar ƙarin jini,zuciyarta na harbawa a haka ta nufi cikin ɗakin,lokacin data ƙarasa gaban gadon tayi arba da fuskar Junaid,Sai ta yanke jiki ta faɗi a sume.......



Shigowa Cikin ɗakin Ya mu'allim yayi tare da Amrish,ruwan dake ajiye saman drawer din dake gefen gadon Ya ɗauka,Ya cire murfin ya tarfa ruwan a tafin hannunshi Ya watsa mata akan fuskarta,Nan take ta farfaɗo tana faman Sauke ajiyar zuciya,Yayin da take ambaton Sunan Junaid abakinta,Miƙawa tayi agaban gadon ta zube saman guiwowinta,kamar a mafarki haka take ganin Junaid,bazata Iya jurewa ba,fashewa tayi da matsanancin kuka yayin da take kallonshi,Dama sai da ranta ya bata cewa Junaid bai mutu ba,Yana araye,Ashe dagaske ne,tasha kuka ta gode ma Allah,Cikin shessheƙar kuka ta soma magana tana kallon Ya mu'alim da amrish dake a tsaye,

"Taya akai junaid daya mutu ya dawo?a ina kuka same shi,A iya saninmu junaid yayi hatsarin mota Ya ƙone ƙurmus"

  Jin wannan maganar yasa Ya mu'allim da Amrish suka kalli Junaid,har suna haɗa baki wurin cewa"Junaid Yayi hatsarin mota'?

  Jinjina kai Sehrish tayi"Babbar motace tabi takan Motarsu,Wuta ta kamaci,ba'a samu komai daga sassan jikinshi ba,wannan Shi ne abunda muka sani a game dashi....."tana kuka ta Zayyana masu Komai daya faru har 6oye mutuwar junaid dasu Marshal Su kayi,Da kuma Halin da abbansu ke ciki na rashinsa,.  

  Amrish tasha kuka hada majina,Shi kanshi Ya mu'allim jurewa kawai yake yi,rashin imanin Yayi yawa

  "In sha Allah komai Yazo ƙarshe,duk wanda keda sa hannu a wurin cutar da family ɗinku,Zai gane kuskurenshi,don wannan karan da shirina nazo,"Babu wasa a fuskarshi yayi maganar,

  "Dan Allah ku faɗamun ya akai kuka samu junaid"?tayi maganar yayin da take share hawayen fuskarta,

  Anan Amrish ta kwashe dukkan abunda Ya faru daga farko har ƙarshe


Miƙewa Sehrish tayi tana kuka,Ta rungume amrish tana Yi mata godiya,bawan Allah ashe shine Yake tura mana saƙo da layinki,muka kasa gane wanene,da yake ni ina da numberki,Shiyasa saƙon Ya bayyana da sunanki,nayi tunanin ko kin yada wayarki ne,Ashe junaid ne ya ɗauketa,Bawan Allah,wlh da ace zan iya mayar da ciwonshi jikina da nayi hakan,junaid bai ta6a shan wahala rayuwarba,Sae wannan karan da ƙaddara ta rutsa shi....."

  "Mu gode ma Allah junaid yana raye,duk yarda suka so su cutar dashi,basu ci nasara akanshi ba,domin kuwa junaid kainuwa ne dashen Allah,badai mutun ba,lokacin da muka kawo shi asibitin nan,jinin jikinshi Yayi ƙanƙanta,cikin sa'a likita ya gwada jinina,kuma aka dace yayi dai dai da nashi,gashi nan ana ƙara mashi,Amma yana bukatar jini sosai,"


 *ƙarin Bayani*


Abunda ya faru lokacin da Sehrish ta tura saƙonnin nan cike da saran Ya mu'allim zai gani,malaman da ta tura ma saƙon daga ciki akwai numbar Ya mu'alim,Yaga Saƙonta saƙonta sai kuma Aka kirashi a waya ana sanar dashi cewa ɗalibarsa na nemanshi,Sauran malaman data tura ma sakone suka sanar dashi,An turo masu saƙo ana nemanshi,Wannan dalilin ne yasa Ya mu'alimm Ya shirya zuwa gidan,tun lokacin baya ya ta6a zuwa gidan security guards ɗin gidan suka hanashi wuce wa,baisamu shiga ba a wannan lokacin,Sai yau daya samu saƙonnin nemanshi da sehrish keyi,Shi ne ya yanke shawarar Ya fara zuwa gidansu Amrish don tayi mashi jagora zuwa gidansu sehrish ɗin su tafi atare,Da yake ya ta6a zuwa gidansu Amrish lokacin da tayi jinya,kuma cikin sa'a ya zo adaidai lokacin da suke buƙatar taimako,Kunji yarda akai Allah ya hadasu dashi Har ya ɗauke su,


Saboda halin da Abban junaid ke ciki,Ya mu'allim Ya basu shawarar su ɗauki junaid su koma dashi Can Sgr hospital ɗin,Don A haɗashi da mahaifinshi in yaso sai acigaba da jinyarshi acan asibitin,Sai da suka tsaya Jinin ya ƙare sannan Likita ya sallamesu,Suka ɗauke shi a back seat ɗin motar Ya mu'alim Aka shigar da junaid,Sehrish ta shiga ta ruƙoshi ajikinta,bawan Allah ya zama tamkar lagwanin filita jikin sae kerma Yake yi sam baya acikin hayyacinshi,Mazaunin driver Ya mu'allim Ya shiga,Amrish ta zauna gefenshi,Ya tashi motar,a tsanake yake driving ɗinsu,Amrish sae faman zabga murmushi take yi,burinta Ya cika,junaid zai koma wurin ƴan uwanshi,Sehrish kuwa ba'a magana,Bakinta yaƙi rufuwa,Kamar wadda akayi ma Albishir da gidan Aljanna,Tsabar farin ciki ne kawai,Ta ƙankame junaid ajikinta kamar ta mayar dashi cikin cikinta,Saboda tsabar ƙaunar da take yi ma ɗan uwanta,A ranta tana ayyana irin farin cikin dasu Babban Yaya zasu yi idan suka ga junaid bai mutu ba,


Slowly motarsu ta ƙaraso cikin katafaren asibitin SGR................





*dakwai yiyuwar littafin Abban Sojoji yakai farkon march,Ba kamar yarda nace ba ƙarshen February,Amma idan kuna son ayi maku after 3 years,kuyi mun magana,sai mu katse shi,ra'ayinku nakeson ji,littafin yazo ƙarshe masu tunanin zai kai azumi,Aniyarku tabi ku😂*


*masu son karanta Littafin Abban Sojoji su tuntu6i layina,Message za'a tura mun ta whatsapp banda phone call*




  

 [3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*









Members na paid group ɗina Am really Sorry🙏masu cewa ko naje wurin za6e na gaji shiyasa banyi posting ba,Boss ko Voters card bata dashi🤣





Acan cikin asibitin kuwa,Suna cikin matsanancin tashin hankali,Jikin Abba Yayi tsauri sosai sam bai kar6ar treatment din da ake basa,Zuciyarshi tana barazanar bugawa,Kowa yayi zugudum cike da jimami suna jiran Tsammani,Sgr da Omar Sunfi kowa shiga matsananciyar damuwa,Saboda suna ganin sune silar Halin da Abbansu Yake ciki,


Tunda suka fito daga Office ɗin Doctor Emran,a tsaye suke sun jingina bayansu da wall,Sgr Ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi,zuciyarshi sai tafarfasa take yi,wani irin bugun zuciya yake ji,Omar kuwa idanuwanshi na kallon Ceiling,tsantsar damuwa ce akan fuskarshi,


Mommy tuni ta jima da kifa kanta saman cinyoyinta,tayi kukan harta gaji tayi shiru,Abu na zaune a gefenta,Yayin da Jahad ta kwantar da kanta saman kafadar Oummansu,idanuwanta a lumshe,Hosana na kwance saman cinyoyin Jahad,ta ɗan aza kanta saboda baccin da take ji,


Su fawan kuwa,Duk sun rufe idanuwansu yayin da kwalla ke zuba,Abusufyan dae Ya gaza samun natsuwa Sae faman safa da marya yake Yi a tsakanin Corridor ɗin dakin da Abban yake,


Dirar Motarsu Sehrish keda Wuya,Motar Sergeant ɗin daya ɗaukota daga gida ta faɗo asibitin dama Yana biye dasu,A bayan motarsu yai Parking ɗin tashi,Fitowa Sergeant ɗin Yayi,Sae ga Baba maigadi ya fito daga back seat na motar,Ashe lokacin da suka barshi acan asibitin,Masallaci Yaje don Yayi sallar azhar da bai samu yayi ba yana fitowa motarsu na fita shine sergeant ya taho da shi,


Wayar aljihunsa sai ringing take yi,sam hankalinshi baya a wurin,har sai da Abusufyan ya ambaci sunanshi"Rafayet ka ɗaga kiran mana,"

A kasalance Ya sanya hannu ya curo wayar,Abbas ne ke kiranshi,picking call din yayi tare da kara wayar a kunnanshi,akan rashin lafiyar Abbansu suke tattauna,


Kamar daga sama Sehrish ta faɗo wurin da suke bakinta ɗauke da sallama,jin muryarta yasa Jahad ta ɗago da kanta tana kallonta,kanal Yousouf ma ya ɗaura idonshi akanta,Haka Abusufyan da abu ma duk ita suke kallo,Sauran kuwa duk hankalinsu baya a wurinta,abun ya ɗaure masu kai ganin tana ta faman sakin Murmushi kamar wata zautacciya,

"Anya Sehrish tana da lafiya kuwa?sai kace batasan halin da muke ciki ba,Sai murmushi take ta saki kamar wata zararra,kodai Hosana batayi wannan haukan ba,"Jahad ce tayi maganar acikin zuciyarta,

  "Sehrish!waya kawo ki?dama bada ke muka zo ba"?Oummansu ce tayi mata tambayar,don ita bata lura ma babu ita ba,

"Daughter,"Abusufyan ya kira sunanta yayin da yake tunkaro wurinda take a tsaye,duk wannan abun dake faruwa Sgr bai ankara da ita ba,Saboda Ya juya bayanshi Yana waya da Abbas,

  A hankali ta soma magana"Bani kaɗai nazo ba"tana kai ƙarshen maganarta ta matsa gefe,Sae ga nurses guda biyu sun shigo da Junaid asaman gadon daukar marasa lafiya suna gunguroshi a wani irin Slow,


Ya mu'allim na a bayansu tare da Amrish da kuma Baba mai gadi,

Zuba ido Abusufyan yayi yana kallon fuskar mara lafiyan da suka ɗauko,Lokaci guda Ya ambaci sunanshi"JUNAID!!!"da tsantsan mamaki akan fuskarshi,Jin sunan Daya Ambata ne Yasa Su fawan suka ɗago da idanuwansu,Ai ko da sukayi Arba da Junaid kwance saman gadon,A wani irin firgice Suka mike suna ambaton Sunanshi Junaid! Junaid!!,Tuni Jahad ta ƙame a tsaye,gaba ɗaya ta rikice Sai faman zazzare idanuwanta take yi akan fuskarshi gani take Yi tamkar Mafarki ne ba gaske ba,Tsabar razanar da tayi ne Yasa ta Yanke jiki ta zube anan wurin,Gaba ɗaya sun miƙe tsaye cirko cirko agaban gadon,Surutun da suke yi ne Ya jawo hankalin Omar kansu,koda Yayi arba da Junaid nan take kirjinshi Yayi wani irin mugun bugu,Waro ido waje yayi yana ƙare mashi kallo a ruɗe ya ambaci sunanshi"JUNAID"!

Adai dai Lokacin Sgr Ya ɗan juyo a sukwane don Yaga meke wakana Yaji sunata ambaton Sunan junaid,baiyi tsammanin wani abu ba,Juyowarshi keda Wuya idanuwanshi Suka sauka direct kan gadon Da junid yake kwance,Saboda tsabar firgitar da yayi baisan Lokacin daya Saki wayar dake hannunshi ba,ta faɗo ƙasa,

Hannu yasa saman idanuwanshi Ya murzasu dakyau don Yaga in dagaske ne,A sukwane Ya kalli Marshal a lokacin shima Omar ya juya a hargitse suka haɗa ido,Just speechless sun gaza magana sai dai nuni da hannu,Sun zama kurmayen Ƙarfi da Yaji,Girgiza kai Sgr ya shiga yi,Alamar bai Yarda ba,

  "I can't believe it,Wannan bazai ta6a yiwuwa ba,Junaid Daya mutu Ya dawo,how can that be possible?Yaron daya ƙone a mota,dama ana mutuwa adawo ne....its just a dream...."acikin ranshi yake wannan Sambatun,Sae faman motsa la66ansa Yake yi amma ya kasa buɗe baki Yayi magana,sunyi matuƙar razana,Sun gigice da ganinshi,Duk da basu Yarda cewa shi bane,Ido kawai suke binshi dashi,


Su kuwa Sauran Matasan Sae murna Suke Yi baby Junaid ɗinsu Ya dawo,Duk da matsananciyar damuwar da suka Shiga na ganin halin da Junaid ɗin yake ciki,Tuni Fawan ya fashe da matsanancin kuka,haka su Irfan sun tasa shi gaba sai kuka sukeyi sun hana nurses ɗin su wuce dashi ciki,

Koke koken da suke Yi ne ya farkar da Alex,Dagowa tayi fuskarta sharkaf da hawaye,Ganinsu tsaitsaye cirko cirko Yasa ta miƙe tare da nufarsu tana Tambayar Lafiya,Matsa mata su kayi don ta ganshi dakyau,A sukwane Alex ta zube saman guiwowinta agabanshi Tana kallon fuskarshi,Yatsun hannunta Na kerma ta azasu asaman ramammar fuskarshi,

  Lokaci guda ta fashe da matsanancin kuka tana ambaton Sunan shi"Romeo ɗina ne ya koma haka"?rufe bakinta tayi da tafin hannunta tana cigaba da yin kuka,

  Ganin Suna 6ata Lokaci Yasa nurses ɗin suka nemi alfarmar su basu hanya su wuce dashi ciki,Gungurashi sukayi da sauri Abusufyan tare dasu Kanal Yousouf suka bi bayansu,Ɗakin da aka kwantar Da Abbansu nan suka nuna suna son a shigar dashi,Ko Allah zaisa adace Abba Ya dawo hayyacinshi,shiga ciki Su kayi dashi,anan gefe aka kwantar da Junaid,dandazo likitoci su Kayi acikin ɗakin domin duba Lafiyarshi,gwaje gwaje suka fara yi mashi,Yafi buƙatar blood ajikinshi fiye da Komai,tsabar so da ƙauna har kokawa su Fawan suke yi don a ɗebi jininsu,Kowa so Yake a sanya ma Junaid nashi,One by One aka dinga gwada Jininsu,A ƙarshe aka ɗibi jinin Fawan dana Ayaaan,kusan Leda huɗu za'a ƙara mashi,


Abun sai ya baka mamaki,Gaba ɗaya sun kasa samun natsuwa sae faman sintiri Suke Yi,da taimakon Oummansu Jahad  ta farfaɗo da matsanancin Ciwon kai,Still bata Yarda da abunda idanuwanta suka nuna mata ba,Asaman laps ɗin abu ta kwanta,wani irin zazza6i ne ya rufe ta,duk a tunaninta Fatalwarsa ce aka kawo masu,Mommyn Junaid kuwa tana bakin ƙopar ɗakin tsaye ita da Abusufyan,jikinta sae tsuma Yake Yi,ji take kamar ta faɗa ɗakin,


Ya Mu'allim yana a tsaye tare dasu Amrish,ba ƙaramin tausayi suka bashi ba,sam babu kwanciyar hankali atattare dasu,Tunda Allah yasa su kayi arba da Junaid,hankalinsu gabadaya ya koma akanshi,shiyasa basu nemi ƙarin bayani a wurinsu ba,Wuri Sehrish ta nuna masu suka zazzauna,kafin ta wuce izuwa wurinsu Marshal Omar dake a tsaye,Suna bin kowa da ido,Su da suka san Cewa Junaid Ya mutu,Abun ya matukar jijjigasu,


"Ya Omar,"firgit ya wurga idanuwanshi  akan fuskarta,A lokacin Shima Sgr Ya mayar da hankalinshi akanta,

  Da hannu Yake tambayarta taya akai hakan ta faru"?

  Murmushi ta ɗan saki,kafin ta soma magana a tsanake,

  "Nasan zaiyi wuya ku yarda,Amma tabbas Junaid ne,bai mutu ba,Lokacin da hatsarin motar nan ya faru,Junaid baya acikin motar,"a iya nan ta dakata,dan tasan brain ɗinsu a yanzu bazata Iya ɗaukar dogon bayani ba, 

  "Idan muka samu natsuwa zamu fahimtar daku komai,Atare da malamin makarantarmu,Da kuma ƙawata Amrish muka kawo shi,"tayi maganar tana nuna masu Ya mu'allim dake a zaune,

Sai Lokacin Sgr yaja dogon numfashi hadi da sauke nauyayyar Ajiyar Zuciya,runtse idanuwanshi Ya ɗanyi yana tariyo abunda Ya wakana a lokacin da suka je wurin da hatsarin motar ya faru,Tabbas sunyi kuskure da basu kwantar da hankali sun tsananta bincike ba,Shi kanshi Yajima yana ji aranshi cewa Kamar Junaid Yana araye,Koba don haka ba,Yayi mamakin Yadda akai ba'asamu ƙashi ko ɗaya ba na jikinshi,wata irin zufa ce ta wanke mashi fuskarshi,Ganin Yadda ta tsastsafo mashi akan fuskarshi ne Yasa Sehrish ta zame mayafinta,goge mashi zufar fuskarshi tayi,kafin ta mayar da mayafin akanta,

"Alhamdulillah,Junaid bai mutu ba,dama yana raye,Ya salaam!"Omar ne ya ambaci hakan fuskarshi ɗauke da wani irin murmushin farin ciki,

Doctor emran ne ya fito daga Medical room ɗin da aka kwantar dasu,Fuskarshi ɗauke da murmushi,kaitsaye wurinsu Sgr ya nufa yana dariya,Kallo Ya koma Sama,

  "Wonders shall neva end"!Ya ambaci hakan lokacin daya ƙarasa wurinsu,

  "Yau naga abun al'ajabin da banta6a gani ba,Dan Allah ku wayarmun da kaina!wanda ya mutu ne ya dawo ko kuwa ghost dinsa ce"?Yayi tambayar yana kallonsu,a lokacin Sgr ya ɗan buɗe idanuwanshi,Sun canza launi sosai,

  "Nikaina Abun Yayi mugun ɗaure mun kai wlh,Still ina doubting,Am confused Allah,ni dai idan ma mafarki nake yi kada ku tashe ni,Ku barni inta yin shi,"cike da tsantsar farin ciki Omar yayi maganar,hannunshi na dafe da saitin Zuciyarshi,No more tension

  Dafa kafaɗar Sgr Dr emran Yayi da hannunshi yana kallon fuskarshi,

  "Sgr fa kamar suman tsaye yayi,Ku tayani dubawa,"Dariya Sehrish tayi,Da alama farin cikine Ya hanashi yin magana,Ko ƙyafta idanuwanshi baiyi,Ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi ya shiga zurfin tunani sosai,hankalinshi Ya tafi wani wurin daban,


Wayarshi daya jefar ƙasa sai dai Sehrish ta ɗauketa,komawa Sehrish Tayi wurin Oummansu,wuri ta samu ta zauna tana kallon Jahad da ta kifa kanta saman laps ɗin Oummansu,

  Cikin sanyin murya ta Ambaci sunanta"Jahad"

"Na'am"ta amsa mata,batare da ta ɗago da kanta ba,'

  "Inason magana dake,"jin haka yasa ta ɗago da kanta,fuskarta duk a yamutse,idanuwanta sunyi jawur,

  "Sehrish amma dai ba gaskiya bane ko!nasan hakan bazai ta6a zama gaskiya ba,Junaid Ya mutu akan idona,Ni naji kukan shi acikin mota Lokacin da yake ƙonewa,Yau kuma sai gashi ya dawo da ranshi"?tayi tambayar a ruɗe,

  "Just believe it!Junaid bai mutu ba,Yana araye,ba lalle ne ki fahimce ni ba a yanzu,Amma tabbas Junaid muka shigo dashi,"_

  "Bazan ta6a yarda ba Sehrish,Sa dai ko me kama dashi ne kuka ɗauko,Amma Junaid dana sani baya acikin duniyar nan"tana kai ƙarshen maganar ta fashe da kuka tare da mayar da kanta saman laps ɗin Oummansu ta kwanta,Tsananin tausayinta ne Ya kamasu,

  "A yanzu ba lalle ne ta fahimce ki ba,Kada ki wahalar da kanki wurin yi mata bayani,"A cewar abu,da ta raba tsakaninsu,

  Gyaɗa kai Sehrish tayi tare da jingina bayanta jikin seat ɗin da suke,


Har time ɗin sallar Magrib ya shige basu ankara ba,Sae da Abusufyan ya tunasar dasu,daƙyar Ya tattarasu gaba ɗaya suka tafi masallaci,


Ya rage daga Alex dake tsaye a bakin ƙopar ɗakin,Sae Su Sehrish da Oummansu dake zaune saman waiting seat,Hosana dae tuni ta jima da yin nisa a baccinta,Duk wannan budurin da ake ita bata sani ba,anan Cikin asibitin ke akwai masallaci,Na mata dana maza,lokacin da suka tashi Yin sallar suna neman inda zasuyi wata Nurse ce ta yi masu jagora zuwa masallacin mata,Kowa sai da Yayi sallah banda Mommy da Hosana,Basu jima da yin magrib ba aka fara kiraye kirayen Sallar Isha'e,basu Baro masallacin ba sae da suka kammala Sallar Isha'en Sannan suka dawo,Ba ƙaramin natsuwa suka samu ba,


Dawowar su Sehrish da ƴan mintuna,ɗaya daga cikin likitocin dake dubasu Ya fito tare da basu izinin Shiga ciki,Alex ce ta fara Shiga,Oumma tare da su sehrish suka bi bayanta,gefen gadon ta zauna yayin da idanuwanta ke akan Junaid,sun canza mashi kayan jikinshi,Riga suka sanya mashi kamar uniform blue colour iya guiwarshi ta tsaya,hannunshi na sanye da kanula ana yi mashi ƙarin jini,Hancinshi na sanye da robar Oxygen,Sai jan numfashi Yake Yi da ƙarfi da ƙarfi,siraran hawaye ne suka sauko akan fuskarta,ruƙo yatsun hannunshi tayi acikin nata,


Jahad dai ta toge a bakin ƙopar ɗakin tana lekenshi,A tsorace take dashi gani take kamar fatalwarsa ce aka kawo masu,taƙi yarda cewa Shi ne Ya dawo,

  Matsawa Abu tayi zuwa gaban gadon ta samu wuri saman kujerar dake fuskantar gadon ta zauna,Addu'o'i ta soma karantowa tana tottofa mashi akan fuskarshi,hakan baƙaramin daɗi yayi ma Alexandra ba,

  Amrish dae na tsaye ta lullu6e kanta da kallabin lace dinta,hannunta na ruke dana Sehrish,gabanta sae faɗuwa yake yi,tana cikin mawuyacin hali,Duk ta tsani kanta,Gani take yi kamar in suka ji cewa Mahaifiyarta ce tayi ma Junaid haka zasu koreta ne,ko su fara ɗaukar fansa akanta,

  "Ki kwantar da hankalinki,ba abunda zai faru,nasan kina jin tsoro ne shiyasa kika tashi hankalinki,"Sehrish ce tayi maganar cikin sigar lallashi,don ta lura da yanayin da Amrish ɗin ke ciki,

  Ƙasa ƙasa suke magana,a tsakaninsu,

"Ji nake kamar in gudu,kafin kowa yaji labarin ainihin abunda Ya faru da Junaid,ni nasan cewa tawa ta ƙare,Ga kuma Mommy tana can tana nemana ta kashe ni"ta shiga damuwa sosai,batasan yanzu ina zata dosa ba,

'Kina tunanin cewa zamu barki ki tafi ne?duk irin ƙoƙarin da kikayi mana,indai kina fargaba ne akan Family ɗinmu,to ki kwantar da hankalinki,Suna da kyakkyawar Zuciya zasu fahimceki su kuma kar6eki hannu bubbiyu,In ma basu amshe ki ba,ni bazan bari Ki tafi ke kaɗai ba zan bi ki ne,"on a serious note,Sehrish tayi maganar,

Har cikin zuciyarta taji daɗin kalaman Sehrish kuma hankalinta ya kwanta,duk da akwai sauran fargaba,


"Assalamu Alaikum"Abusufyan Ne ya shigo fuskarshi ɗauke da Murmushi Hannunshi ruƙe dana Sgr,Omar na abayansu tare da Ya mu'allim,yayin dasu Fawan ke biye dasu,Kowa ka kalla tsantsan farin cikine bayyane akan fuskarshi,tsayawa su kayi agaban gadon cirko cirko suna kallon Junaid,Har lokacin Abbansu na kwance gefen Junaid,tunda akayi mashi allurar bacci bai farka ba,


Sai faman sauke ajiyar zuciya Omar da Sgr suke yi,sun jinjinawa lamarin,ƙaryar da suka shirya ta zama gaskiya,Ga ƙannensu sae murna Suke yi Junaid ya dawo,kidnappers sun sake shi,basu san dawan garin ba,

Da zarar Sgr ya haɗa ido da Omar saisu sakarwa juna murmushi,abun ba'a magana,shigowa ciki doctor Emran Yayi fuskar nan ɗauke da ƙayataccen murmushi,jerawa yayi tare dasu,yadda kasan sun Samu talabijin haka suka ƙurawa Junaid ido suna kallonshi,

Dr emran ne ya soma magana a tsanake,

  "In sha Allah,Zasu samu sauƙi,dama damuwarshi rashin Junaid ne,Yanzu gashi Allah ya dawo mana dashi"yana kai ƙarshen maganar,

  Ya mu'allim ya ɗaura da cewa"Yakamata mu nuna godiyarmu ga Allah subhanahu wata'ala,daya bayyanar mana shi,sannan muyi masu addu'a"

Atare suka ɗaga hannayensu sama,Ya mu'allim ya shiga yi masu addu'a suna amsa mashi da Ameen,sun ɗauki tsawon Lokaci kafin suka shafa Addu'ar,

  Suna zame hannayensu daga saman fuskokinsu,yatsun hannun Junaid suka fara motsi,Da ƙarfi Mommy ta ambaci sunan"Junaid"fuskarta ɗauke da murmushi,hankalin sauran ya dawo kanshi,

  Mutsu mutsu yaci gaba da yi,Jahad sai leƙenshi take yi daga tsayen da take abakin ƙopar,ita dai har yanzu bata yarda ba,

  Mutsu mutsun yaci gaba da yi,duk sun zuba ido suna kallonshi,la66ansa sae kerma suke yi,Slowly ya soma sambatu tun yanayi ƙasa ƙasa harya fara yi da ƙarfi Sunan Abbansu yake ambato,"Abba!Abba!"cikin fitar hayyaci ya soma kokarin ɗaga hannunshi zai cire Oxygen ɗin da aka sanya mashi,Da sauri Dr emran da Omar suka ƙarasa ta gefenshi tare da rurruƙe hannayenshi,hankalinsu gaba ɗaya ya tashi ganin yadda Junaid ke ta firgita,

  "Abba!Abba"daƙyar sautin ke fitowa daga bakinshi,tunda Ya Mu'allim yaji hakan,Sae ya basu shawarar Su matso da Junaid kusa da Abbansu,tunda akwai interval a tsakaninsu,da alama yana ji aranshi cewa mahaifinshi na a kusa dashi,Shiyasa yake ambaton sunanshi,

  Dubara su kayi a hankali suka janye Junaid zuwa gefen Abbanshi,Abun mamaki suna gyara mashi kwanciyarshi sae gashi yana kokarin lalubar jikin Abbansu,Abun yayi mugun ɗaure masu kai,Sam fa baya acikin hayyacinshi amma yaji aranshi Abbanshi na kusa dashi,daƙyar ya iya ɗaga hannunshi ya ɗaurashi akan fuskar Abbansu yana shafata,kuma wani abun mamaki idanuwanshi arufe suke gam,jikin ne kawai ke motsi,


Har saman wuyanshi Junaid yakai hannunshi zuwa saman ƙirjinshi,har lokacin bai daina ambaton sunanshi ba,ga la66anshi sae kerma  su ke yi,

  Murmushi kawai suke saki suna kallonshi,

"Gaskiya tunda nake banta6a ganin ƙauna tsakanin mahaifi da ɗansa ba,irinta mahaifinku da wannan ƙanin naku,"Dr emran ne yayi maganar,da mamaki akan fuskarshi,

  Sai lokacin Alex ta samu damar yin magana

  "Nikaina da nake mahaifiyarshi bana tunanin yanayi mun irin son da yake yiwa mahaifinshi,Koda yake dole yaso mahaifinshi akaina,shaƙuwarsu ta wuce tunaninmu,"

  Suna cikin yin maganar,Abbansu ya fara ƙoƙarin buɗe idanuwanshi,Wani irin nauyin bacci ne ya hanashi tun ɗazu ya farka,amma yana jin muryar Junaid acikin kanshi,sake ambaton sunanshi Junaid yayi da wata irin kasalalliyar murya,

  "Abba,"tunkafin Ya buɗe idanuwanshi ya soma kiran sunanshi"Junaid"gaba ɗaya suka matso kewaye da gadon suna murmushi,Yayin da idanuwansu ke akan Abbansu,

  Ruƙo hannun Junaid yayi acikin nashi,sosai har cikin ranshi Yaji dagaske Shi ɗinne,kokawa ya shiga yi da baccin dake ƙoƙarin hanashi buɗe idanuwanshi,

  Daƙyar ya ɗaure ya ware idanuwanshi,a wani slow ya wurga eye balls ɗinshi kan Junaid dake kwance agefenshi,Tunda ya ɗaura eyes ɗinshi akan fuskar Junaid ko ƙyaftawa baiyi kamar an dasa mashi aya,wani irin farin ciki ne ya lullu6eshi lokaci guda hawaye suka shiga wanke mashi fuskarshi,Muryarshi na kerma Ya ambaci sunanshi"Junaid!dagaske kaine a kusa dani,Junaid ɗina ne atare dani"?

  "Yaya hossein dagaske ne abunda kake gani,ga Junaid ɗinka nan,an dawo maka dashi"Abusufyan ne yayi maganar,

  Lumshe idanuwanshi yayi tare da sake buɗesu a hankali yana cigaba da kallon fuskarshi,Lokacin daya ankara da Jini da ake ƙara mashi aruɗe yace"Me ya same shi?Sun cutar mun dashi ko?duk sun canza mun Junaid ɗina kamar bashi ba,"

  "Abba,ka kwantar da hankalinka,Junaid yana samun sauƙi,"Omar ne yayi maganar cikin sigar lallashi,

   "Alhamdulillah Ya Allah daka dawo da farin cikana"ya ƙarasa maganar tare da dago da hannunshi zuwa cikin sumar kanshi,

  "Allah Ya baka lafiya Junaid ɗina,ka yafe mun duk laifina ne halin daka shiga,Bazan ƙara yin kuskuren da zan rasaka a kusa dani ba"yana magana hawaye naci gaba da sauka akan fuskarshi,


Jikinsu duk yayi sanyi,tsananin tausayinsu ne ya kamasu,


Wuraren ƙarfe 10 na dare,Abusufyan ya kwashe su Sehrish zuwa gida,Su biyar ya ɗauko hada Amrish da Oummansu,Ba don sun so ba ya ɗaukosu,lokacin da ya ƙaraso cikin gidan bayan yayi parking ɗin motar,Buɗe motar Oummansu sehrish tayi tare da fitowa waje,Bayan Abusufyan Ya fito ya zagaya ya buɗema su Sehrish,saukowa tayi daga cikin motar,Amrish ma ta sauko bayan ita sai Jahad,duk suka fito banda Hosana,ruƙo hannunta Yayi tare da ambaton sunanta,Daƙyar ta iya buɗe idanuwanta,

  "Ki fito ku wuce gida,Sae ki kwanta ki ƙarasa baccin naki,"A yamutse ta fito daga cikin motar,ruƙe hannunta Sehrish tayi ganin tana tangal tangal zata faɗi ƙasa,

  Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da kallonsu yace"Ku wuce ciki mana,Ni zan koma ne,zuwa gobe zamu dawo gida sai acigaba da jinyar tasu a gida,"

  Gyaɗa kai abu tayi tare da cewa"shikenan,Allah ya basu Allah,Amma Mommy fa?zata dawo itama"?

  "Sai zuwa gobe zamu dawo tare da ita,"ya ƙarasa maganar tare da kallon Jahad,

  "Banga kina farin ciki ba,ko bakiyi murna da ganin Masoyin naki bane"? Zuba mashi ido kawai tayi batare da tace komai ba,itafa har yanzu bata yarda Junaid bane,zaiyi wuya ta yarda inba an sanar da ita Yarda akai Ya tsira daga cikin motar nan ba,

  Sehrish na ƙoƙarin buɗe baki tayi mata magana,muryar AZMEE ta katsesu,

  "Sannunku da dawowa,"gaba ɗaya suka kai idanuwansu kanta,

  Jikinta na sanye da dogon hijabi,fuskarta da alamun damuwa,

  Ɗaure fuska Abu tayi,sam ta tsani ganin Azmee arayuwarta,

  Ƙarasowa tayi gaban motar da suke a tsaye,

  "Abusufyan Ya mai jikin?ɗazu naso na biyoku asibitin amma bansamu hali ba,Da yake tunda safe ina kwance ba lafiya,"tunda ta soma magana,Amrish ta ƙura mata ido tana yi mata kallon sani,kamar yarda amrish ke kallonta,itama haka take kallon Amrish ɗin,

  "Jikinshi da sauƙi,zuwa gobe zamu dawo gida,Ya jikin naki?naji kince bakya lafiya,"

  "Alhamdulillah,Naji sauƙi,Idan zaka koma asibitin akwai dinner dana kammala Yanzu,bari na shirya maka kayan abinci saika kai masu,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta wuce ciki,

  Abu ji take kamar ta hana Abusufyan ya kar6i abincin nan don bata yarda da ita ba,tsoranta kada ta sanya masu guba aciki,"

   Ganin sunƙi shiga gidan Yasa Abusufyan yi masu magana"Tsayuwar me kuke yi ne?ku wuce ciki mana,wanda zaiyi wanka yayi wanka,ku kwanta ku huta,"

   Sallama su kayi mashi,kafin suka nufi cikin gidan,Sehrish sae faman waiwayon Abusufyan take yi har sai da ya lura da kallon da take yi mashi,tsoro take ji Ya tafi ya barsu tare da Aunty Azmee cikin gidan,gashi babu kowa Su kaɗaine mata,

Bayan shigarsu da ƴan mintuna,Azmee ta fito hannunta ɗauke da food basket mai faɗi,A bayan boot ɗin motar ya shigar dashi,komawa ciki tayi jim kaɗan ta dawo da wasu kayan abincin ya lodasu bayan motarshi,Sallama sukayi dashi ta juya ta koma cikin gidan,


*Boss Bature*


Bayan Shigarsu gidan kaitsaye ɗakinsu suka wuce,bayan sun shiga Amrish ta buƙaci shiga toilet don tayi wanka jikinta yayi mata nauyi,bayan ta shiga wankan Sehrish ta ɗauko mata kayan da zata sanya idan ta fito daga wankan,asaman gadonsu ta ajiye mata kayan,

  "Oumma Yunwa nake ji,"Hosana ce tayi maganar tun lokacin da suka shiga dakin ta baje saman gado,Jahad na zaune gefen gadon tayi zugudum,

  Tunanin zuwa kitchen tayi don ta Shirya masu abinci,tana ƙoƙarin ruke handle ɗin ƙopar,Sai ga Azmee ta turo ƙopar ɗakin,

  "Na shirya maku abinci,nasan kuna jin yunwa,"

  Bata jira amsar da abu zata bata ba ta juya ta fuce daga dakin,Saukowa saman gadon hosana tayi jiki na rawa ta kama hanyar fita ɗakin,da sauri Abu ta ruko hannunta"Ina zaki je,"

  "Abinci zanci,"

  "Ba zaki ci shi ba,Ki bari in girka maku,"

  Kamar zata fashe da kuka tace"Nidai ki barni inje inci na Aunty Azmee tunda ta gama,"

  "Koma ki zauna,yanzu nima zan kammala girka maku,"

   "Kina tunanin cewa zan cutar daku ne?"Kwatsam taji muryar Azmee,turo ƙopar ɗakin tayi"Don me zaki hanata cin abinci na"?ranta a6ace tayi maganar,

  "Saboda ban yarda dake ba,bazan bari ƴa'ƴana suci abincinki ba,"

  "Hosana,koma ki zauna,"tayi maganar tare da nuna mata cikin dakin,

  Idanuwanta cike tab da kwalla ta juya zata koma,

   Miƙewa Jahad tayi tare da takawa zuwa bakin ƙopar ɗakin,

  "Oumma!Meya haɗaki da Aunty Azmee"?

  "Jahad babu komai,kawai banason Hosana taci abincinta ne,"

  "Amma meyasa oumma?kullum ita ke girka mana abinci muna ci,sai yau kuma Oumma"?tayi tambayar da damuwa akan fuskarta,

  Sehrish dae tana cikin ɗakin tana sauraronsu,

  "Bansan laifin da nayi ma Oummanku ba da har ta hanaku cin abinci na,Babu komai,Nidai ga abinci can wanda yaga dama yaje yaci,"takai ƙarshen maganar tare da juyawa tabar ɗakin,


  Guntun tsoki abu taja,kafin ta fuce daga ɗakin ta nufi kitchen,Don ta girka masu abincin da zasu ci,


Komawa Jahad tayi jiki asanyaye ta samu wuri gefen gadon ta zauna,yayin da zuciyarta ke ci gaba da tariyo mata fuskar Junaid,

  Hosana sae faman shessheƙar kuka take yi saboda an hanata cin abinci ga yunwa tana ji,


Fitowa Amrish tayi daga cikin toilet jikinta ɗaure da towel,

"Idan kin kammala shafa mai,ga kayanan na ɗauko maki,wanda zaki sanya"ta ƙarasa maganar tana nuna mata,kayan da ta ajiye mata saman gadon,

  Murmushi ta ɗan saki tare da cewa"Nagode sosai,"sai lokacin ta lura dasu Jahad,tun suna asibiti take taso tayi mata maganarsu amma tashin hankali ya hanata,Tayi mamakin kamaninsu koda yake wannan ya wuce kama,

  "Ƴan uwana ne su naga kina kallonsu,ƴan ukune mu,Ga Jahad can wadda ke zaune gefen gadon,Wannan mai kukan banzan kuma Sunanta Hosana,Sha takwas sha tara ce,ina fata kin gane,"ta ƙarasa maganar tana dariya,Wurgo mata harara Hosana tayi ba don tana jin yunwa ba da ba abunda zai hana takai mata bugu,


Murmushi Jahad tayi tare da cewa"kiyi haƙuri,tun a asibiti naso mu gaisa,bansamu dama ba saboda halin da muka shiga,Amma yanzu inayi maki barka da zuwa,"ta ƙarasa maganar tare da ƙokarin yin murmushin dole,

  "Nagode sosai da irin karramawar da kukayi mun,"hankalinta ya ƙara kwanciya,gaban dressing mirror ta zauna,ta dauki man shafawarsu ta soma shafama jikinta,bayan ta kammala,Sehrish ta miƙa mata Kayan baccin da ta dauko mata,hannu biyu tasa ta kar6a tana yi mata godiya,


Juya baya Sehrish tayi don tasamu damar sanya kayan,Ganin hosana na kallonta yasa Sehrish wurga mata harara tace"Lafiya kike kallonta?baki ga tana sanya kaya bane,"

Murguɗa baki Hosana tayi'Yo me zan kalla,Tana mace ina mace,Dama Namiji ne"

  Gaba ɗaya suka fashe da dariya,hatta Amrish ɗin,ba ƙaramin nishaɗi ta basu ba,

  Shaf shaf amrish ta zura kayan ajikinta ba ƙaramin kyau su kayi mata ba,white colour ne,

  "Nasan kina jin yunwa,Kiɗan ƙara haƙuri,ga Oummanmu can tana girka mana abinci,bari naje na tayata ma,"kama hanyar fita ɗakin tayi da sauri,

  Gefen gadonsu Amrish ta zauna,

"Yaushe zaki tafi gidanku"?

Baki asake Jahad ke kallon Hosana,

Shiru Amrish tayi bata tanka mata ba,saboda bata da amsar da zata bata,

"Nan zaki kwana ne"?ta kuma tambayarta,

  Rai a6ace Jahad tace"Ba'a sani ba dan uban mutun,Ina ruwanki da ita?ko saman kanki zata kwana ne?sai shegen ɗumi kamar aku,"

  Tsuke baki hosana tayi"nidai ba ubana ba,daga tambaya sai cibi ya zama ƙari?ƙari kuma ya zama ƙwababa"

Cike da takaici Jahad ta kalli Amrish"Am sorry pls,Wlh bata da hankali,Sai addu'a,Kuma hada ƙarin tana jin yunwa shiyasa take ta soki burutsun nan,"

Murmushi amrish ta ɗan saki tare da cewa"Bakomai,na fahimce ta,"


Lokacin da Sehrish ta shiga kitchen,Oumma ta samu tana ta faman zarya,Abincin da ta ɗaura masu take jira ya kammala dafuwa,

  "Oumma"jin muryar Sehrish yasa ta dakata da yin zaryar,Ta juya tare da kallonta,

  "Me kike dafa mana ne"?

Murmushi abu ta ɗan saki tare da cewa"jallof ɗin taliya na ɗaura tama kusa dafuwa,"

  Wucewa cikin kitchen ɗin Sehrish tayi,agaban gas ɗin ta tsaya,hannu tasa ta buɗe tukunyar ta leƙa ciki,

  Cike da mamaki tace"Oumma!amma dai yanzu kika zuba taliyar nan ko?naji kince ta kusa dafuwa amma kuma naga kamar yanzu kika zubata,"

  Jin haka yasa abu ta nufi wurin gas ɗin"kusan minti 15 fa da daurata,Ya isa ace ta kammala dafuwa yanzu"

  Leƙa tukunyar tayi,abun mamaki Taliyar tana nan yarda ta zubata,tamkar ba acikin ruwan zafi take ba,"

  Kallon juna su kayi at same time,abun ya ɗaure masu kai,

   "Oumma,ni a tunanina kawai mu haƙura muci abincin Aunty azmeen,

  Girgiza kai abu tayi"bazaiyiwu ba,Zanyi ƙoƙari naga taliyar nan ta dafu,"

  Wasa wasa taliya fa tayi kusan awa ɗaya bata dafu ba,

  Kodai gas ya qare ne,tayi tambayar tana leƙa ƙasan tukunyar wuta saici takeyi alamar akwai shi,

Jinjina kai tayi"wannan aikin Azmee ne,Wato don na hana ku ci abincinta,shine tayi mun haka,"

"Nima raina ya bani cewa itace,Kawai ki hakura Oumma,Dare yana kara yi ga Amrish tana jin yunwa sosai,"ba don taso ba,dole ta kashe gas cooker ɗin ta sauke girkin,


Komawa ɗakinsu Sehrish tayi,tana shiga ta sanar dasu cewa su fito suci abinci,


Jiki na rawa Hosana ta sauko daga saman gadon,Amrish ma ta mike tare da Jahad suka fito,Atare suka shiga dining area ɗin kowa ya zauna,Sehrish ce tayi serving ɗinsu,kowa ta zuba mashi a cikin plate ta tura masu agabansu,Sosai suka ci abincin,Ita dae bata ci ba Lemu kawai ta dinga sha,saboda gudun kada taga wani abu da zai tayar mata da hankali,don bazata manta da irin wahalar da tasha ba a jiya,


Wuraren ƙarfe goma sha biyu suka shirya kwanciya,A Bedroom ɗinsu Sehrish,Jahad da Oummansu tare dasu hosana suka kwanta,Amrish da Sehrish ɗakin Abusufyan suka wuce,A saman gadonshi suka kwanta tuni bacci ya ɗaukesu,Jahad dae ta kasa runtsawa tunanin Junaid ya hanata sakat,kokwanto take tayi acikin zuciyarta,ita dai a iya saninta in mutun ya mutu bai dawowa,Amma shi Junaid gashi ya dawo,Tabbas Tana ji aranta ba mutun bane fatalwarshi ce tazo a matsayinshi,


Acan ɗakin Abusufyan kuwa,Sehrish da Amrish tuni bacci yayi awon gaba dasu,can cikin dare wuraren ƙarfe ɗaya da rabi,Wayar dake cikin aljihun doguwar rigarta ta fara ringing,Sam ta manta da wayar Sgr da ta ɗauko acikin aljihunta,cikin magagin bacci ta zura hannu tare da curo wayar,picking call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta,

  "Who's on the line"?Jin Muryarshi yasa Sehrish ta wartsake daga baccin da take yi,miƙewa tayi daga zaune,

  "Ya Rafayet,"da wata irin kasalalliyar murya ta ambaci sunanshi,.  

  "Dama ke kika ɗauki wayar,"?

Jinjina kai tayi kamar tana agabanshi"eh,ni ce,na manta ban baka ita ba a asibiti"

  "Its okey,just keep it for me,"ta amsa mashi da toh,kafin tace"Ya jikin nasu"?

  "Da sauƙi,Zuwa gobe zamu dawo gida,Anan za'a cigaba da treating dinsu"yanayin muryarshi tayi sanyi sosai,

  Shiru suka ɗan yi na wani lokacin,

"Zan maida video call,"Jin yace haka ta janye wayar daga kunnanta,saukowa tayi daga saman gadon ta kunna hasken ɗakin kafin ta koma ta zauna saman gadon,

  Saita fuskarta tayi akan screen ɗin wayar a lokacin Ya canza kiran zuwa video Call,

  Kwance yake saman wani haɗaɗɗen gado kai kace ba cikin asibiti bane,daga shi sai dogon wando ya cire rigar jikinshi,Ya ɗan tada kanshi saman pillow,


Ƙura mashi ido tayi tana kallonshi kamar yarda shima yake kallonta,

  "Me kike yi har yanzu bakiyi bacci ba"?

  "Kaine ka tashe ni,Har na fara bacci,"

  "Okey,"shiru ya ɗan yi,gashi yana so suyi fira da ita,amma bai iya ba,ita kanta ta lura da hakan,sam bai iya surutu ba,

  "Meya hanaka bacci,"?daƙyar ta iya tambayarshi,.  

   Da buɗar bakinshi sai cewa yayi"not having u by my side" saboda tsabar mamakin maganarshi ta ɗan zaro ido tare da buɗe baki irin mamakin nan ya kamata jin yace wai rashinta a gefenshi,

  "Am so proud of you,"yayi maganar yana nunata da finger ɗinsa,A lokacin ji yake kamar ya janyota ta cikin wayar ya rungumeta,sai dai babu halin yin hakan,

  "When are u going back to U.S"?daƙyar ta iya tambayarshi,

  "Kin ƙosa na tafi ne"?

 Girgiza kai tayi"a'a,nasan cewa dole zaka tafi,that's why i asked u,'

  "Ko zaki bini ne"?

 Da sauri tace"A'a,"

 

 "You won't follow me?tell me why"?yayi maganar yayin da idanuwanshi ke lumshewa,


 "Bayan rabuwa zamuyi nan da wasu ƴan kwanaki,zaka sake ni,ka koma U.s,"

  Lokaci guda taga ya canza fuskarshi alamar baiji daɗin maganarta ba,

  "Its okey,take care of ur self,"yana kai ƙarshen maganar yayi rejecting ɗin kiran,Jiki asanyaye Sehrish ta ajiye wayar saman side drawer,


Gyara kwanciyarta tayi zuciyarta cike fal da tunanin maganganunsa,tai mamakin canzawar da yayi jin tace bazata bishi U.S ba,

  "I don't know why,but ni bazan bishi ba,koda ace ya buƙaci hakan tunda ba so na yake ba,yar aikinsa ya dauke ni,yanzu bani da burin daya wuce ya bani takardar sakina kawae in san matsayi na,tunda Aikina ya qare,"ta ƙarasa maganar tare da rufe idanuwanta,nan take bacci Yayi awon gaba da ita,



A 6angaren Hajiya sarat kuwa,Lokacin da kiran ƙare kukanka ya shigo wayarta cike da zumuɗi ta ɗaga kiran don taji ko sun samu nasarar kashe su Junaid din don ta gama sama ranta zasu yi nasara,

  Lokacin dasuka sanar da ita cewa sun rasa su,Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata makoshinta,Nan take Zuciyarta ta buga ta yanke jiki ta faɗi ƙasa wanwar.........."


Washe Garin ranar,Wuraren ƙarfe 7 na safe,Slowly motocinsu suka shararo da matsakaicin gudu izuwa cikin gidan,A jere motocin suka biyo layi,Bayan sunyi parking ɗinsu,Motar farko ta Sgr ce,a hanzarce Armstrong ya fito tare da zagayawa ya buɗe masu ƙopa,Fitowa Sgr yayi tare da zura hannuwanshi Ya ɗauko Junaid irin ɗaukar da akeyi jariri,


Motar bayansu ta marshal Omar ce,Major ne ya buɗe mashi ƙopar ya fito tare da zagayawa ya taimaka ma Abbansu wurin fitowa daga ciki,har yanzu da sauran jikinshi,Amma ya samu sauki dama ciwon na rashin Baby Junaid ne yanzu gashi Ya dawo,hankali ya kwanta No more tension,


Daga Motar Omar,Sae motar Kanal Yousouf,shi ya ɗauko Baba mai gadi na gidansu Amrish,


Motar fawan kuwa,Mommynsu ce aciki,Daga motarshi sai Motar Ya Mu'allim,Haka suka dinga fitowa daga cikin Motocin,gaba ɗaya suka ɗunguma izuwa cikin gidan,kaitsaye Sgr ya wuce da Junaid izuwa bedroom ɗin Abbansu,Omar na biye dashi Ya tallabo Abbansu saboda rashin ƙwarin jikinshi,


Asaman gadon Abbansu Sgr Ya kwantar da Junaid,Sannan Ya taimaka ma Abbansu Ya kwanta shima,Akwai Medicines dinsu da suka taho masu dashi,hada na asthma din Junaid tare da injections ɗin da za'a cigaba dayi mashi kafin Allah yasa ya dawo cikin Hayyacinshi,


"Yanzu duk wahalar da muke sha ashe Yaron nan yana araye"?Omar ne yayi maganar yana kallon Sgr,

  Kafin yaci gaba da cewa"Gaskiya duk wanda yayi silar jefa mu cikin wannan matsanancin tashin hankalin Sae ya ɗanɗani kudarshi,sai ya yi danasanin haihuwarshi da uwarshi tayi acikin duniyar nan,zanso nasan wanene wannan MASTER PLANNER ɗin"





   *Masu cewa Basu son littafin abban sojoji na kuɗi bane,Littafina na kuɗi ne,Book one ne kawai nayi shi kyauta,Amma 2 da 3 Na kuɗi ne,Dukansu 300 ne duk maiso yayi mun magana kaitsaye Amma message ta whatsapp 08103884440*

  

  

  


  

  


  





 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*






Kafin yaci gaba da cewa"Gaskiya duk wanda yayi silar jefa mu cikin wannan matsanancin tashin hankalin,Sae ya ɗanɗani kudarshi,sai yayi danasanin haihuwarshi da uwarshi tayi acikin duniyar nan,zanso nasan wanene wannan MASTER PLANNER ɗin"


Sannu da jiki suka ƙara Yi ma Abbansu kafin suka juya atare suka bar bedroom ɗin nashi,Matsawa Abba Yayi kusa da Junaid,Zuba mashi ido Yayi yana kallonshi cike da tsantsar so da ƙauna,Ji yake tamkar ya mayar dashi cikin cikinshi,tsananin tausayinshi ne ya kamashi,Rungumeshi yayi ajikinshi kamar jinjiri haka Ya koma,shafa sumar kanshi Abba Ya Soma yi a hankali har zuwa bayanshi,sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi,Jiya haka suka kwana a Asibiti manne da juna saboda firgitar da yake yi,kuma da zarar Abba ya janye jikinshi daga nashi sai ya dinga kiran sunanshi,har sai ya ji shi ajikinsa sannan yake rufe bakinshi,


Bayan fitarsu Sgr daga bedroom ɗin,direct suka wuce Babban Falon gidan Inda kowa Ya hallara Kamar yarda Ya Mu'allim Ya nemi alfarmar Yin magana dasu,A saman Sofa mai mazaunin mutun uku,Sgr tare da Marshal da kanal Yusuf,ɗayar Sofa ɗin itama mai 3 seat,dama 2 sofa sets ne a babban palourn,Ayyan da Jahan ne tare da Irfan suka zauna asamanta,Jabeer da khaleed suna a zaune saman sofa mai mazaunin mutun biyu,Alexandra tare da Fawan suna zaune a saman same Sofa,Abusufyan na tare da Ya' Mu'allim,gaba ɗayansu ne banda wanda suka kwana gidan,

  Gyaran Murya Ya Mu'allim yayi tare da cewa"Idan ba damuwa,ina buƙatar ganin sauran da basu hallara ba,"

Miƙewa Fawan yayi dama shine messenger,Duk in wani aike ya tashi jiki na rawa zaka ga Ya miƙe,


Bedroom ɗinsu Sehrish Ya nufa,A ƙopar ɗakin ya tsaya tare da kwankwasa ƙopar,Almost 3 times Yana buga ƙopar,Sae sharar bacci suke yi sun baje saman gado,da yake sun tara gajiya kuma basuyi bacci da wuri ba,

  Yana ƙoƙarin sake buga ƙopar yaji an buɗe ta,Tsayawa tayi ruƙe da qugu,fuskar nan a kumbure idanuwan sun ƙankance,Tunkafin yayi magana tace"Ya fawan wai lafiya irin wannan bugun ƙopar ɗakin haka,Sai kace zaka 6alle ƙopar,"

Sai da takai ƙarshen maganar,Ya wurga mata harara,don ya gane wacece acikinsu

"Rasa kunya 6eran tanka,aiko ni akayi,Ki shiga ciki ki sanar dasu cewa ana son ganin kowa a main palour,"

Murguɗa mashi baki tayi,har ya ɗaga hannu zai make bakin,Sae ga Abu na ƙoƙarin fitowa Jikinta sanye da hijabi,da sauri Ya kawar da hannun,

  "Ina kwana Aunty,"abu ta amsa mashi"Lafiya lou,fawan Ashe kun dawo,"

  "Eh,bamu jima da dawowa ba,dama An aiko ni ne don in kira ku,Ana son ganin kowa da kowa ne a babban falo,"

  "Allah yasa Lafiya,Bari na shiga ciki na tashi jahad,Yanzu zamu fito,"

  Ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta koma ciki,a lokacin Hosana ma ta shige ciki,

Ɗakin Azmee Ya nufa,Hannu yasa ya kwankwasa mata ƙopar ɗakin,bugun farko yajiyo muryarta tana magana daga cikin ɗakin

  "Wanene"?

"Fawan ne Aunty azmee,"

Jim kaɗan ta buɗe mashi ƙopar ɗakin,Jallabiya ce ajikinta ta yafa babban mayafi,Hannunta na ruƙe da Cazbaha,

  "Kun dawo kenan Ya jikin Abban naku,"

  "Jikinshi da sauƙi Alhamdulliah,"

"Allah Ya tashi kafaɗunshi"

"Ameen,Dama Akwai baƙi a palour,naga baki fito ba,Ko abunsha ne ataimaka a haɗo masu",

Jinjina kai tayi"badamuwa,gani nan zuwa,"tayi maganar tare da komawa cikin ɗakin,juyawa Fawan yayi a hanzarce Ya koma palourn,tare da samun wuri ya zauna,Shigarshi da minti Biyar,Abu ta fito tare da Jahad suka nufi palourn,Hosana kuma Oummansu ta aiketa Bedroom ɗin Abusufyan don ta kira su Sehrish,


A gefen Mommy,Oumma ta zauna,Jahad kuma A ƙasa ta zauna saman carpet,musayar gaisuwa suka shiga yi atsakaninsu,Bayan sun kammala gaisawa kowa Ya shiga natsuwarshi,

"Sun gama hallara ko akwai sauran wanda baya nan ne"?Ya Mu'allim Ya tambaya,don bayason wani yayi missing discussion ɗin da zasuyi,

"Akwai saura,Amma na aiki Hosana taje ta kirasu,"Abuce ta

 bashi amsa,Lokacin da Hosana ta kutsa kai ɗakin,A baje ta samu Sehrish da Amrish suna bacci,saman gadon ta hau tare da sanya hannunta tana bubbuga ƙafafunsu"Wai bazaku tashi ba!"shiru ba wadda ta motsa acikinsu,

  Bubbuga ƙafafun nasu ta kuma yi"wlh ko ku tashi,Ko in ɗebo ruwan sanyi in watsa maku,"jin wannan maganar yasa Sehrish ta buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,koda tayi arba da fuskar hosana nan take ta ɗaure fuskarta,A ƙule tace"Lafiya'?

"Nima bansani ba,Oumma ne tace na kira mata ku,Ana son ganinku a palour,"

Takai ƙarshen maganar tare da saukowa daga saman gadon ta fice daga ɗakin tana ƙara jaddada masu akan su fito,


Atare da Amrish suka fito daga ɗakin hannunsu ruƙe dana juna,tunkan su ƙaraso Sehrish ta hango Sgr dake gefen Kanal Yusuf ya lumshe idanuwanshi,kamar mai jin bacci,da alama Jiyan nan baiyi bacci ba,ko bai samu isasshen bacci ba,


Ƙarasawa Cikin palourn su kayi,A nan saman Carpet gefen Jahad suka zauna suma tare da lankwashe ƙafafuwansu,


Ɗagowa Ya Mu'allim yayi tare da binsu da kallo,kafin yace"Akwai saura ko su kenan"?

"na kira Aunty Azmee,Yanzu zata zo itama,"Fawan ne ya bashi amsa,Duk sun ƙagara suji abunda Ya Mu'allim ke son sanar dasu,


Saukowa Azmee tayi daga 3 steps na fitowa daga Corridor ɗin ɗakunansu,bata nufi falon kaitsaye ba,kitchen ta nufa,after few minutes ta fito hannunta ruƙe da faffaɗan tray saman shi glass cups ne,Wanda ta shirya masu abunsha ciki,


Jin takun takalmanta ne Ya jawo hankalinsu,tana ƙarasowa wurin sofas ɗin da suke zaune,Kamar ance ta ɗago karaf Suka haɗa ido da Ya Mu'allim,A gigice Azmee ta saki tray ɗin hannunta Wani irin sauti suka bada ji kake fass fass tatass Glass Cups ɗin suka faffashe,ganin haka yasa kowa Ya shiga tambayarta Lafiya,kasa buɗe baki tayi don tayi magana,gaba ɗaya duk tabi ta firgice ta rasa natsuwarta,Da gudu ta juya zata bar wurin Ya Mu'allim Ya daka mata tsawa"Karki kuskura kice zaki bar wurin nan,idan har kika ƙara ɗaga ƙafarki a wurin nan,Saina sa6a maki,"Cak ta tsaya lokaci guda wata irin Zufa ta shiga wanke mata fuskarta,

Abun ya ɗaure masu kai,har suna haɗa baki wurin tambayarshi A ina yasan Azmee?,

  Miƙewa tsaye Ya mu'allim yayi tare da nuna ta da yatsan hannunshi"Wannan itace Silar duk wani hali da kuka shiga acikin gidan nan!"

Saboda tsabar firgitar da su kayi gaba ɗaya suka miƙe suna kallonshi,

"Anya kasan me kake faɗa kuwa?Wannan fa Azmee ce,me aikin gidanmu,kusan Shekara Ashirin tana Yi mana aiki,"kanal Yusuf ne yayi maganar,


"Kodai tayi maka kama da wadda ka sani ne"?acewar Irfan,

A tsanake Ya mu'allim ya soma magana"Niko nasan Azmee farin sani!Ku ne baku santa ba,Wannan matar da kuke Gani,Mushirika ce ƴar qungiyar asiri",

Hankali A matuƙar tashe Suke kallonshi,Duk basu kaiga yarda da maganarshi ba,

Azmee kuwa tuni ta ɗaura hannu asaman kanta,Tunda Ya Mu'allim Ya fallasa cewa ƴar gungiyar asiri ce ita,tasan cewa Alƙadarinta ya karye!A ƙa'idar ƙungiyarsu daga inda wani Yasan sirrinka shikenan ƙarfin sihirinka zai naƙasa............"


"Kinji haushin rayuwarki!Muguwa azzaluma,dama Alƙawarine na ɗaukarwa kaina saina Tona maki asiri,koda kuwa zakiyi silar mutuwata ne,balle kuma ke baki isa ki kawar dani ba,"


Kallon kallo suka shiga yi atsakaninsu,Kowa yasha jinin Jikinshi,

Hankali atashe Mommy tace"Don Allah ka fahimtar damu,"


Cigaba da magana yayi"nasan ba lalle ne wasun ku su gane ni ba,Amma mahaifinku zai iya tuna fuskata,Ni ina ɗaya daga cikin malaman da aka ɗauko don su koyama Junaid karatu lokacin yana yaro,A lokacin Mahaifinku Ya faɗamun cewa duk malamin daya ɗauko don ya koya mashi karatu,tun arana ta farko idan Yazo bai ƙara dawowa,Abun Ya ɗaure mun kai,farkon haɗuwata dashi A masallaci ne,Ta dalilin  yabona da mutane keyi ne ya jawo hankalinshi akaina,harya jani gefe yake sanar dani game da ɗanshi da yake son indinga zuwa ina koya mashi karatu,


A ranar dana fara zuwa gidan nan koya ma junaid karatu,A garden muka zauna dashi in ban manta ba,Saman darduma ne muke zaune dashi,Idan inayi mashi karatu sai ya ƙura mun ido yana kallon bakina kamar yana fahimtar abunda nake cewa,Ashe kwata kwata bai ganewa ne,Abun ba ƙaramin ƙona mashi rai yake yi ba,a ƙarshe sai ya fashe mun da kuka yana cewa shi baiso ana zuwa yi mashi karatu tunda ba ganewa yake yi ba,Wahalar dashi muke Yi,naji tausayinshi sosai a wannan lokacin,Na kuma Yi mamakin yarda bai gane karatun al'qur'ani,sanin cewa Ƙaramin yaro yafi ɗaukar karatu a lokacin ƙuruciyarshi,Amma shi ko Bismillah wuyar faɗi take yi mashi,Idan na matsa mashi akan yayi karatu da zarar ya buɗe baki zai amsa karatun da nake biya mashi,kwatsam sai inga ya sanya hannu ya toshe kunnuwanshi,La66anshi na kerma,wani lokacin kuma sai inga yana ruƙe maƙoshinshi,tundaga nan na sanya ayar tambaya akanshi,bayan na koma gida,Yini nayi da tunanin Junaid,Saboda Yaron akwai shiga rai,Ya kwantamin araina sosai,a daren ranar,wuraren ƙarfe 1 na dare aka kira wayata Ana yi mun barazana akan karna kuskura na ƙara zuwa koya ma junaid karatu idan ba haka ba zan rasa raina ne,duk da haka ban daddara ba,A washe garin ranar na kuma dawowa koya mashi karatu hada ruwan Zam Zam na addu'a nazo mashi dashi don yasha,ruwan Addu'ar yana karya sihiri duk mun ƙarfinshi in akayi ma mutun in ba wani iko na Allah ba,Aranar nayi ƙoƙarin na bashi yasha ruwan addu'ar nan amma wani abun mamaki daga nayi yunƙurin kafa mashi ruwan a bakinshi don yasha Sai kawai inji an buge mun hannuna,tun daga nan na ƙara yarda cewa akwai sihirin ajikinshi,Sae na fara tunanin yin bincike akan Wanda ke  sarrafa kwakwalwarshi,domin in taimakeshi,Akwai wata rana Da Azmee ta kawoshi da hannunta,A ranar na gane cewa itace ke sarrafa shi,Allah yayi mun baiwar gane mutun mai sihiri da zarar mun hada ido,ta kalle ni na kalleta,Bayan tafiyarta nake tambayarshi Wacece ita,ko mahaifiyarshi ce?Sai ce mun yayi Eh,Mamansu ce,banyarda da maganarshi ba a lokacin saboda sam babu kamanceceniya a tsakaninsu,Hasken yaron ba irin nata bane,ko irin kama ta jini babu atsakaninsu,da na tsare shi da tambaya sai yake cemun mamanshi bata nan,kuma bata sonshi ta tafi tabarshi,Sai tausayinshi ya kamani,Bayan na koma gida na shiga zurfin tunani akanshi,Abunda ya tsayamun araina shine meyasa mahaifiyarshi ta tafi tabarshi?Wacece wannan matar dake sarrafa kwakwalwarshi,Meyasa take son juye mashi tunani don karya gane karatu,Na nace akan son sanin dalilinta na yin hakan,Gashi bansan wa zan tambaya ya bani amsa ba,matasan gidan kuma ba gwanayen son magana bane,Gasu sojoji in nace zan tambayesu ba dole su fahimce ni ba,Zasu yi mun wata mummunar fahimtar ne,akwai wata rana da muka haɗu da mahaifinku a lokacin na kammala Koya mashi karatun ranar,Shi kuma ya dawo daga wurin aiki,Na ƙarasa muka shiga gaisawa dashi har yake ce mun in shigo daga cikin gidan muci abinci atare,Dayake mutun ne shi mai son jama'a,baida girman kai ko kaɗan,Yana da kyakkyawar zuciya,Banyi niyyar shiga cikin gidan cin abinci ba,Amma tunawa da binciken da nakeso nayi saina Yanke shawarar binshi,


Lafiyayyen Abinci Azmee ta shirya mana tare dashi,a lokacin in ban manta ba,Hada waɗannan tagwayen guda biyu,ko gaishe ni basuyi ba lokacin,Dama tunda na kallesu nagane cewa suna da girman kai,wani kallon ƙaskanci suke yi mun,Amma wani abu dana hasko shine,Hasken fatarsu irin na Junaid ne,Sai na fara tunanin kodai cikin Iyayensu akwai jinsin turawa ne?Saboda ƙwayar idon ɗaya daga cikinsu,muna cikin cin abincin Sai naji ɗaya na tambayar Abbansu,na kasa kunne ina sauraronshi,

"Abba,har yanzu Mommy bazata dawo ba"?Sai Abbanku Yace"bana tunanin zata dawo da zama Nigeria,

Sai naji yaja dogon tsoki yana cewa"Gaskiya batayi mana adalci ba,kodan saboda Junaid yakamata ta dawo taci gaba da kula dashi,Ni bana so Azmee taci gaba da rainonshi....."bai kai ƙarshen maganarshi ba sai Abbanku yayi mashi tsawa,nan take yaja bakinshi yayi shiru,bayan mun kammala cin abincin,Na shirya tafiya mahaifinku yayi mun jagora a lokacin ko abun hawan kaina ban mallaka ba,A ƙafafuna nake yawo,ko in hau abun hawa,to a lokacin shima yana da wani uziri a waje,Sae yace mun in shiga motarshi su rage mun hanya,


Muka shiga motar atare,Driver ɗinshi Yaja motar muka fita,A cikin motar ne,na soma ƙoƙarin bugun cikinshi,

"Na lura kamar akwai damuwa akan fuskarka,"sai yayi ƙoƙarin 6oye damuwarshi yace mun bakomai,

Sai na canza maganar nace"Maganar Junaid Alhaji,Yau mahaifiyarshi data kawo mun shi daƙyar ya tsaya,Yana ta kuka sai ya bita,"Nayi mashi zancen junaid ne don na lura ba ƙaramin son Yaron yake yi ba,indai kanason kaga fara'arshi toh kayi mashi maganar Junaid,

  Nan yake ce mun ae ba mahaifiyarshi bace,Mommynshi bata a ƙasar tun lokacin da ta haifeshi tabar ƙasar,Wannan matar dana gani mai aikin gidan ce,Itace ta shayar dashi,sun shaƙu sosai,Ya saba da ita baison rabuwa da ita,iya haka ya tsaya mun da bayani,Bai faɗamun dalilin dayasa Mahaifiyarshi tabar ƙasar nan ba,batare data ƙarasa shayar dashi ba,Ni kuma a wannan lokacin na samu abunda nakeso,bayan sun sauke ni a gida,Yinin ranar da tunanin maganganun mahaifinku na kwana,Saboda yarda nasa ma raina junaid har mafarkinshi nake yi,Dana zauna nayi nazari sosai,Sai na hasasho wani abu game da Azmee,tabbas akwai wata mummunar manufa dayasa take zaune a gidan,In ba haka ba meyasa zata Juye mashi kwakwalwarshi?Saboda yaron yana da kaifin basira!he's genius,irin yaron nan ne masu wayon tsiya,Gifted Ne shi,ita kuma Azmee ita ke rainonshi dole zai iya kasancewa A ɗakinta yake kwana,koda yaushe yana manne da ita,duk wani surkulle da zatayi agabanshi take yi,Tanajin tsoron kada Ya tona mata asiri,that's the reason Why Ta toshe mashi kwakwalwarshi Ta yarda bazai Iya gane komai ba.........."


Gaba ɗaya hankalinsu Ya tashi haikam,Musamman Sgr da Mommyn Junaid,Jikinsu har tsuma Yake yi,Su kanal Yusuf kuwa sun shiga ruɗani sosai,Abun yafi ƙarfin tunaninsu,Har yanzu basu samu ƙwaƙƙwarar hujjar da suke son samu ba,Farat ɗaya bazasu fara Accusing ɗinta ba,


Azmee kuwa tuni ido ya raina fata,Jikinta sae kerma yake yi,Ta gaza buɗe baki tayi magana,binsu kawai takeyi da ido,


Cigaba da magana Ya mu'allim yayi"A lokacin sai tafiya ta kamani zuwa ƙasar Egypt,scholarship na samu don ƙaro ilimin addini acan,ba don naso ba haka na kwasa nabar ƙasar nan,cike da tunanin Junaid,Tsorona kada kafin in dawo Nigeria,Azmee tayi silar mutuwarshi,tunda ta fara zautar dashi,



bayan tafiyata ƙasar egypt,duk da bana a nigeria,ina samun Labarin halin da Junaid ke ciki,Duk in mukayi waya da mahaifinku yana sanar dani,Har na samu labarin ciwon Shi daya tashi har akayi mashi aiki a ƙirjinshi,Lokacin nashiga damuwa sosai,Saboda ni nasan cewa Junaid baida ciwon asthma,Lafiyayyen mutunne shi,Wannan ciwon asthma ɗin duk aikin Azmee ne,itace ta sanya mashi ita,duk don saboda kada yayi Lafiya,domin kuwa lafiyarshi zai iya jaza mata matsala,ta ko'ina ta hanashi sakat,ta mayar dashi tamkar soko,Yanayin wasu abubuwan irin na mata bayan shi namiji ne,kuma tundaga kan Iyayenshi da yayyenshi babu wani rago acikinsu balle ace ya ɗauko wani daga cikinsu ne,kuskuren da kukayi shine,Yarda da Azmee ta shayar dashi,Tabbas kun tafka babban kuskure na Yarda da ƴar aiki ta shayar maku da ƙaninku,Sauke ajiyar Zuciya Ya Mu'allim Yayi kafin ya ɗaura da cewa"Bayan wasu shekaru Allah yayi na dawo Nigeria,A lokacin bansan wani hali ahalinku suke ciki ba,Domin kuwa nadaina samun mahaifinku a waya sakamakon Rasa wayata da nayi wadda nake da saving ɗin Layinshi aciki,lokacin dana dawo mahaifinku Ya samu karin girma a wurin aiki,Na chief of army staffs,Hakan yasa gidanku Ya ƙara tsaro sosai kuma mahaifinku yayi wuyar gani,Har zuwa saida nayi amma Sojojin dake gadin gidan suka hanani shiga ciki,saboda banda shaidar da zasu Iya barina na wuce,kusan sau biyar ina zuwa amma bansamu shiga ciki ba,A ƙarshe na haƙura da zuwa gidan,


Ana haka,Na samu koyarwa,A makarantarsu wannan Yarinyar,Yayi maganar yana nuna Sehrish dake atsaye,

Kullum naje koya masu karatu sai inga yarinyar nan tana ta sharar bacci abunta,Sae kace ba karatu tazo ɗauka ba,Abun saiya ɗaure mun kaina har rannan na tanka sai yan ajin suka sanar dani haka take,duk in ana karatu sai tai ta bacci,jin haka yasa naje har seat ɗin da take zaune na tasheta daga bacci ta miƙe tana mutsuttsuka idanuwanta,Kallo guda nayi mata na gane cewar akwai matsala atattare da ita,Nace mata ta ɗago ta kalleni,Taƙi yarda mu haɗa ido,Ni kuma a lokacin inaso in gani idan akwai Jinnu ajikinta,Don naji ajikina cewa ba ita kaɗai bace,Dana tambayeta a wani gida take ne,Sae take sanar dani cewa ita Ƴar family ɗin SALAHUDDEEN HOSSEIN ce,Inajin hakan sai na gane cewa Ƴar uwar Junaid ce ita,tunda sunan mahaifinshi ne,kuma naga kamanninshi a fuskarta,


Tunda naji hakan sai na gane cewa Har lokacin Azmee na acikin Family ɗinku,Kuma ina tunanin itace ta shiga jikin Yarinyar tayi mata sihiri,ban tabbatar da zargina ba,Kawai na yanke shawarar in bata wannan ruwan addu'ar na zam zam,Ta hanyar ƙawarta Amrish gata nan a gefenta,Ita naba ruwan zam zam ɗin acikin robar ruwan donta ba Sehrish tasha,Har nace ta sanar da ita cewa idan bata sha ruwan ba,ƙusumbi zai fito mata abayanta ne,Nace haka ne don ta tsorata tasha ruwan,in ba haka ba nasan daƙyar ne tasha ruwan,To ni bansan tasha ruwan Addu'ar ba,ko bata sha ba......"ya dakata da maganar yana kallon Sehrish,hankali Ya koma kanta,. 

  Daƙyar ta iya buɗe baki tace"A'a bansha ba,Nazo dashi gida,Amma na neme shi na rasa,A lokacin nayi tunanin ko Junaid ne Ya ɗaukeshi saboda shikaɗai ne ke zuwa ɗakina,daga baya ban ƙara tada maganar ba,


Tunda ta soma magana Ayaan da Jahan ke kallon Juna,saboda sun gane cewa Wannan ruwan da suka sha ne,Har suka samu warakar Cutar dake damunsu,Na neman juna da suke yi,


Da sauri Ayaan yace"Ni na ɗauki Robar ruwan acikin fridge,bansan waya kaita ba,Amma nida Jahan ne muka sha ruwan.......'anan Ayaan ya kwashe duk abunda Ya faru ya sanar dasu,Bai 6oye masu komai ba game da homo sex ɗin da suke yi shi da Jahan,Saboda ƙwarin guiwar da suka samu ayanzu,

  "Yanzu haka robar ruwan,Tana a hannun Jahan,Shiya 6oyeta saboda muyi bincike akan wanda ya kawota cikin gidanmu,Ashe Sehrish ce ta shigo da ita,"

  Kallon Jahan Sgr yayi"inason ganin robar ruwan da kuka sha,"da sauri Jahan Ya nufi part ɗinsu,


Tashin hankalin da ba'a sama shi date,Gaba Ɗaya idanuwan ko wannansu na akan Azmee,Duk tasha Jinin jikinta,After some minutes Saiga Jahan ya dawo hannunshi ruƙe da bottle water ɗin,mai rubutun Larabci ajikinta,


Miƙa ma Sgr yayi,Bayan ya kar6i robar ya kalli Ya Mu'allim"Itace wannan"?

  Jinjina kai Ya mu'allim yayi,"ƙwarai kuwa itace wannan,idan kana jin harshen larabci ka karanta rubutun dake ajikinta,Zakaga Bayanin da take ɗauke dashi na karya sihiri,"

A fili Sgr ya karanto musu Larabcin dake rubuce a jikin robar,kafin Yayi masu translation ɗinshi,kowa Yaji a kunnanshi,


"Tun daga ranar da muka sha ruwan nida Jahan bamu ƙara neman junanmu ba,mun samu sauƙi,dama kullum cikin fargaba muke,Allah shikaɗai yasan irin raɗaɗin da muke ji acikin zuciyoyinmu,Saboda munsan cewa aikata homo babban zunubi ne wanda ubangijinmu Allah Ya haramta yinshi,Ga kuma tsoron hukuncin da za'a yanke mana idan aka kamamu muna yinshi,"idanuwanshi cike tab da kwalla Yayi maganar,


Tuni guiwowinsu sun sage,Zuciyoyinsu sun karaya sosai,

Cikin sanyin murya Kanal Yusuf Ya soma Yi mata magana"Aunty Azmee dagaske ne duk wannan Abun da malamin nan Ya faɗa akanki?Amsarki kawai muke son ji,"

"Amma in har dagaske ne,Azmee kin gama da mu,Kin cuce mu,kin zalunce mu,Laifin me muka aikata Maki?da har kika shigo cikin rayuwarmu,Tsawon Shekara ashirin kina yi mana aiki,"Acewar Jabeer,


  Ganin taƙi basu Amsa yasa Sgr Ya daka mata tsawa har saida ta firgita,

  "Zaki buɗe baki kiyi magana!ko kuwa saina sa kinyi"?


Maimakon ta bashi amsa,Saita rufe idanuwanta ta soma karanto wasu zantuttuka cikin wani harshe mara daɗin ji,Zuba mata ido sukayi suna kallonta,Watsa hannuwanta tayi saman iska tana kaɗasu,


Murmushin takaici Ya Mu'allim Ya saki tare da cewa"Kada ki wahalar da kanki AZMEE,Domin kuwa Allah Ya rigada ya kamaki,Sihirinki bazaiyi aiki ba A yanzu,"


Buɗe idanuwanta tayi akan fuskarsu,Duk a tunaninta tayi masu layar zana,Basu ganinta hakan yasa ta saki murmushi tare da juyawa zata kama hanyar fita daga falon,Wani irin kukan Kura Alexandra tayi tabi bayanta da gudu ta damƙo wuyan Jallabiyar jikinta da ƙarfin gaske ta wurgota,A sukwane goshinta Ya daki ƙasan tiles,bugu ta shiga kai mata,shaƙo wuyan rigarta tayi"Bazaki buɗe baki kiyi magana ba,"rai a matuƙar 6ace Alex ke magana,

  "Dama ni ban ta6a yarda dake ba AZMEE,I have been accusing you for a very long time,Nayi shiru ne saboda banda hujjar da zan kamaki,"

 Daƙyar Abusufyan yashawo kan Mommy ta rabu da ita,

  "Kodai kiyi mana jawabi da bakin ki ko kuma musa kiyi,"

  

 Motsi ta soma yi da la66anta,Yayin da idanuwanta ke kallon fuskokin kowannansu,lokacin da suka haɗa ido da Sehrish saita fashe da kuka,ita kanta sehrish ɗin hawaye ne sharkaf akan fuskarta,

 Hannu tasa tana goge jinin da Mommy ta fitar mata agefen bakinta,

  Lokaci guda idanuwanta suka canza sosai,Suka yi jawur tamkar garwashin wuta,


Duk wannan abun dake faruwa akan idanuwan Abbansu,Wanda ya jima da fitowa,Bawan Allah ya girgiza da jin abunda suke tattaunawa,ƙarasowa Yayi wurinsu daƙyar yake jan jikinshi saboda rashin ƙarfin jikin da babu,

 "Na kasa yarda da abunda kunnuwana suke jiye mun,Azmee dagaske kece kike son ɗaukar fansa akan ahalina?Laifin me suka yi maki?Me Junaid Yayi maki da kikeson kashe mun shi,Idan ma fansar ce zaki ɗauka meyasa ni baki kashe ni ba,Sai Ƴa'ƴana kawai"?fuskarshi ɗauke da matsananciyar damuwa yayi maganar,


Girgiza kai Azmee ta shiga yi kafin ta soma magana,

 "Da ace inason kashe ɗaya daga cikin ƴa'ƴanka,Wlh da yanzu na jima da shafe Babinku a doron duniyar nan!Dama nawa na samu?Meyasa ban sanya guba acikin abincin gidan nan kowa yaci mutu ba?Tabbas Dama nasan wannan ranar zata zo,Nikaina na jima ina jiranta,Banzo gidan nan don inyi maku aiki ba,Nazo ne don in ɗauki fansar kashe mun Iyayena da kukayi da kuma Mijina,Kun jima kuna cin zalin danginmu amma bamu ta6a ɗaukar mataki ba,Kun tarwatsa mana farin cikin Zuri'armu Yayin da ku Kuma kuke rayuwarku cikin Farin ciki....,


Wacece Azmee?


Azmee cikakkiyar bafullatana Ce ƴar jihar Gombe state,asali garinsu daga ruga ya fara kafin a hankali ya zama gari,A tsakanin family ɗinsu da family ɗin Salahuddeen basu Shiri,faɗansu tun kaka da kakanni ne,Dama tsakanin family ɗin soja da family ɗin Masu tada ƙayar baya a kasa basa jituwa,faɗan nasu ya fara tun daga kan kakanninsu,Kaka wanda sunan kakansu ne kuma dashi ake yi masu inkiya amatsayin sunan family ɗinsu,Kaka Mugun mutunne wanda ya gagari kowa hakan yasa al'ummar dake kewaye dashi Ke tsananin tsoronshi,Matsafin gaskene a wurinshi duk suka gado wani tsaface tsafacen da suke Yi,Sun kasance wasu irin mutane marasa buri a rayuwarsu,Mugunta kawai sukasa a gaba,Kuma abunda zai baka mamaki Suna da ilumin addinin musulunci,Da yawansu Mahaddatan Alqur'ani ne,Suna Yin iliminne ba don komai ba,Sai don su kawar da idanun mutane daga kansu,Don Tafiyar da rayuwarsu batare da jama'a sun zargesu ba,Kuma suna yin amfani dashi wurin Gudanar da sihirinsu,Dama ance in mutun ya 6ace ya 6ace kenan,Sae wani iko na Ubangiji,Sun tsunduma tsulundum wurin aikata shirka,Zubda jinin al'umma da kuma Yin amfani da Mutane wurin yin tsaface tsafacensu,A zamanin kaka,Salahudeen shi ne Ya kawo ƙarshen tawagarsu ta matsafa,Sunyi nasara akansu wurin ruguza ƙungiyarsu,Tundaga wannan lokacin Suka zama abokanan gaba,Salahuddeen Ya kafa dokar duk inda akaga ɗaya daga cikinsu yana yawo nan take A yanke mashi hukuncin kisa,Suma haka su kaka suka sanarwa jama'arsu da zarar sunga Jinin Salahudeen Su kashe shi,Kisan wulakanci,ya kasance suna farautar junansu,A lokacin da su salahudeen sukayi nasara akansu,Saida suka ƙarar da rabi da kwata na jama'arsu,Kuma a wannan lokacin suka kashe Kaka har lahira,sunyi tunanin sun gama dasu ashe akwai sauran runa akaba,Kaka ya mutu yabar ƴa'ƴanshi,Wanda bayan mutuwarshi,su kuma suka tada ƙungiyar,suka cigaba da aikata munanan laifuka acikin ƙasa,Nan fa su salahudeen suka bazama neman inda suke shirya maƙarƙashiyarsu,Babban danshi ne ya amshi mukamin mahaifinsu kaka,Sunanshi Ubaid Hatsabibine harya fi Ubanshi kaka,Su biyu kaka Ya haifa dashi da ƙaninshi Wanda suke Kira Uba,Dukkansu Mugayene Basu da Imani ko misƙala zarratin,Shan jini ya zama ruwan dare a wannan lokacin,cire sassan jikin ƴa'ƴan mutane abun ba'a magana,Sai dai kawai a tsinci gangar jikin mutun an cire wasu Organs na jikinshi,Abun Ya tashi hankalin Al'umma,Zama baiga su salahudeen ba,Nan fa suka Bazama neman waɗannan hatsabiban guda biyu,Ubaid da Uba,Yadda kasan aljanu haka suke,Baka ta6a ganinsu cikin jama'a,Sai Lokacin Sallah,Ubaid ma Shike jan Sallah a babban masallacin Yankinsu,Babban limaminsu ne,kuma babban Malamin addini ne,Baka ta6a gane halinshi inba gani kayi ya aikata agabanka ba,Fuska biyu ne shi,A fuska musa azuci fir'auna,a yadda mutane suka sanshi,Mutumin kirki ne,Mai tausayi ga son jama'a,Yafi kowa Iya kiran sunan Allah,Idan Ya hau mumbari zaiyi wa'azi sai ka sha mamakin yarda yake kuka Yana kira ga mutane su Koma ga Allah,shu'umin mutunne mai wuyar sha'ani,Ƴa'ƴanshi Biyu Gali shi ne  babban ɗanshi,Sai mai bi mashi mace ce Wadda suke kira da Saratu,Ƙanin mahaifinsu Uba shima Ƴa'ƴanshi Biyu,Babbar ƴarshi itace Azmee,Mai bi mata kuma Namiji ne,Wanda suke kira da Sayyad wato Ya sayyadi,


tundaga kan Iyayensu maza har matan Mugayen mutanene,Mushirikai,Tun daga kan kakanninsu ne abun Ya fara,Sai wanda Allah yaso acikin zuri'arsu yake zama na gari,kamar Azmee duk acikin ƴa'ƴansu itace bata ɗauko mugun hali ba irin na sauran,Hasalima batasan me iyayensu ke aikatawa ba,Mace ce mai tsananin son addini,Kamilar gaske,Tun tana da shekara goma sha Biyar a duniya ta haddace alqur'ani mai girma,Saratu kuwa ƴar wurin wan mahaifinsu jakkace,bata gane komai sai Iya mugunta,


Ana haka Azmee ta fara soyayya da wani bawan Allah,Wanda Ya ta6a taimakonta,akan hanyar dawowarta daga islamiyyar dare,Wasu ƴan iska suka biyota suna ƙoƙarin yi mata fyaɗe,A wannan lokacin wani matashin saurayi ƙakƙarfan gaske ya riƙesu sun kewayeta,Haɗa kawunansu yayi ya dinga bugu sai da yayi haɗa masu jini da majina,Sannan Yace ta sanya hijabinta suje ya rakata gidansu,A ƙopar gidansu yayi sallama da ita,Tunda ta koma gida ta kasa runtsawa saboda tunanin bawan Allahn nan daya taimaketa,tun adaren ranar ta kamu da tsananin sonshi,so bana wasa ba,


Saboda shi kullum sai taje islamiyar dare,tunda ta gane cewa hanyar dawowarshi ce,duk in suka haɗu saiya rakata har gidansu sai ya tsaya yaga shigarta kafin shima ya wuce gidansu,Soyayya mai ƙarfi ce ta shiga tsakaninsu,sam batasan asalinshi ba,Abu ɗaya kawai tasani akanshi yana da kyakkyawar Zuciya,


Tun tana 6oye ma Iyayenta soyayyarta dashi har suka fara lura da yadda Azmee ke yawan ambaton sunanshi Jabeer,ko bacci take yi sai ta dinga sambatu tana ambaton sunanshi,Sa6anin da in tana bacci karatun haddar da aka basu ne zaka ji tana biyawa a bakinta,


Da iyayensu maza suka gane cewa tana son wani bare ba danginsu ba,Sai suka gargaɗeta akan ta rabu dashi,In ba haka ba zata ja mashi ne,su sunfi son suyi mata auran zumunci dama kuma Family ɗin kaka basu auren bare,Yasu yasu ne,ita kuma ta tsani Wanda suke son su haɗa ta dashi,Ɗan wurin Ubaid ne yayan mahaifinta,Wato Ghali mugun mutunne kuma Arne ne shi,Sunan yana musulmi ne ko sallah baya yi,a lokacin taƙi jin maganarsu ta kangare,Aikuwa mahaifinta Uba yasa aka ɗauko mashi Jabeer,A wani kogon dutsi suka Rufe shi,Anan suke gana mashi azaba,duk don su raba ta dashi,kwana biyu da azmee bata sanya shi a idanuwanta,Ko abinci tadaina ci a ƙarshe ciwon zuciya yakusa kamata,ganin dagaske takeson Jabeer kuma zata Iya Kashe kanta akanshi gashi kuma Uba yafi Sonta cikin ƴa'ƴanshi,Sae ya yanke shawarar zai aura mata jabeer,ashe da wata mummunan manufa Ya amince zai aura mata shi,Saboda yayi bincike akanshi ya gano cewa Jinin Maƙiyansu ne,mutanan da suke hari,shi kanshi Jabeer ɗin baisan wanene shi ba,Yawo kawai yake yi acikin garinsu tun yana ƙarami ba'asan danginshi ba,Amma su dayake Shu'umaine da suka bi diddigi saida suka gano ainihin wanene shi............


Cikin lokaci ƙanƙani aka ɗaura auren Azmee da Jabeer,Aranar Hamma Gali kamar Ya haɗiyi zuciya Ya mutu,Ya tsaneshi kamar mutuwarshi,Saboda Shi ke son Azmee,duk da ba son Allah da Annabi yake yi mata ba,Yasha yin kokarin Keta haddinta amma Allah bai bashi iko ba,


Bayan sun ɗaura auren Azmee da jabeer,Mahaifinta da kanshi Ya basu kyautar gidan da zasu zauna,Saboda Jabeer baida komai,Talaka ne shi gaba da baya,


A ranar da aka kai Azmee gidan Jabeer wani  mummunan abu ya faru,lokacin da kowa yabar gidan Amarya Ya kasance su biyu ne acikin gidan,Bayan sunyi al'wala sun gabatar da sallah,jabeer ya ɗauketa zuwa saman gadonsu,sai da yafara karanta addu'ar saduwa da iyali kafin suka soma biyan buƙatar junansu,Ita dai a wannan lokacin tasan da jabeer suka kwanta,Amma a washe garin Ranar da ta farka cikin mawuyacin hali,Hamma gali ta gani kwance saman gadonta babu kaya ajikinshi,ta fasa wata irin gigitacciyar kara ta soma ƙoƙarin mayar da kayan jikinta,Da gudu ta shige bandaki tana kuka,Bata fito daga toilet ɗin ba har saida taji Muryar Jabeer yana ambaton sunanta,

Sannan ta fito tana kuka,A gefen gadonsu ta same shi zaune,Hawaye wasu na bin wasu akan fuskarshi,Jikinshi sai kerma yake yi,Zuƙunnawa tayi agabanshi tana kuka,

 Cikin shessheƙar kuka take tambayar meya faru dasu a daren jiya?ina ya tafi yabarta har Hamma Gali ya shigo cikin ɗakinsu,ta rikice ta rasa gane waye ya kusanceta a cikinsu,A lokacin Jabeer Ya amsa mata da cewa shine ya kusance ta,Bata yarda da kalamanshi ba,Hakan yasa ta soma tambayarshi Idan har dagaske shi ya kusanceta meyasa da ta farka da safe bata ganshi ba,Sai dai Hamma Gali ta gani kwance Saman gadonsu,Sannan meyasa yake kuka?"ganin halin da ta shiga ne yasa bai sanar da ita ainihin abunda ya faru ba,Shi dai A iya saninshi a daren jiya bashi kaɗai ya kusanceta ba,An gusar mashi da hankalinshi,Ya mike a wani irin yanayi yabar ɗakin bai ƙara sanin inda kanshi yake ba,A wannan lokacinne Gali ya shiga ya ƙarasa aikin,shi kanshi kokwanto Yake yi Anya Shine ya kawar da budurcinta ko kuwa Gali ne?kamar yarda tace Gali ta gani kwance saman gadonsu,Allah kaɗai yasan Ƙuncin da jabeer yaji acikin Zuciyarshi,Iya cuta dai an cutar dasu,Hakanan ya daure Ya rungumi matarshi suka ci gaba da rayuwa da ita,


Ana haka,Azmee ta fara ganin sauyi atattare da jabeer,Ya canza mata sosai,kwata kwata babu kwanciyar hankali atare dashi,Ko magana baisan yi,abinci ma baya ci,idan dare Yayi baya bacci sai dai ta farka ta same shi saman darduma Yana sallah yana kuka,Duk in ta tambayeshi meke damunshi sai yace mata,tayi ma mahaifinta magana,Yadaina yi mashi abunda baiso,Ta rasa gane me jabeer ke nufi,ita dai a iya saninta Mahaifinta mutumin kirki ne,babban malamine shi,ko maiyasa jabeer ke ƙorafi akanshi,duk yarda taso ya sanar da ita,ainihin abunda Iyayenta keyi mashi amma Yaƙi sanar da ita,tun tana tambayarshi har ta gaji ta ƙyaleshi,


Wata ɗaya da yin auransu,Azmee ta fara laulayin samun ciki,A lokacinne suka shiga ruɗani ita da jabeer,Ga ciki Ya bayyana ajikinta,Amma basu da tabbacin Cikin Shi ne kona Hamma Gali,A wannan time ɗin Jabeer Ya bata kyakkyawar kulawa,ya rage nuna damuwarshi,don kawai farin cikinta,


Ranar da Azmee bazata ta6a mantawa ba,Shine ranar da cikinta Ya shiga wata Tara ta fara nakuda,Dayake ƙa'idar family ɗin kaka in mace zata haihu,a gida suke kar6ar haihuwarta,



Cikin ɗakin mahaifiyarsu Dije aka shigar da ita saman gadon karfe,Su biyu ne akanta zasu kar6i haihuwarta,Hada matar wan mahaifinsu Ubaid,mahaifiyarsu Gali,Inno bata da mutunci matar nan,Halinta sak ƴa'ƴanta suka biyo,Duk acikin gidan suke,Dayake babban gidane na iyali,zumuɗinta akan jaririn da za'a haifa ne saboda gali ya sanar da ita cewa ɗanshi ne,



Azmee bata haihu ba Sae daren Ranar Allah yayi zata haifi santalelen ɗanta Namiji,Ko wanke jikin jaririn ba'a kaiga Yi ba,Kwatsam Ba zato ba tsammani Sojoji Su kayi masu dirar Mikiya,A fusace sojojin nan suka shigo,Kuma sunci sa'a Gaba ɗaya family ɗin sun taru a gidan suna jiran Haihuwar Azmee,Bisa umarnin Salahuddeen A lokacin shine shugaban sojoji na Nigeria,Umarni aka basu kai tsaye su kashe duk wanda suka Gani acikin Family house ɗinsu,amma banda mata da ƙananun Yara,Nan fa sojojin nan suka buɗe masu wuta,ta ko'ina sautin bindigu kake ji,Sunga tashin hankalin da basu ta6a gani ba,Anan Suka kashe ubaid da kuma Uba,Daga ciki hada iyayensu mata,domin sunyi ƙoƙarin Ɗauko makamai a cikin ɗakunansu da niyyar su taimaki Mazajensu,wannan ya tabbatar masu da cewa suma matan suna da sa hannu a aikata ta'addanci tunda har sunsan suyi harbi da bindiga,aikuwa suka kashesu gaba ɗayansu,A ranar an zubda jini kamar kamar mi,Daga cikin waɗanda tsautsayi Ya ritsa dasu,Hada Jabeer bawan Allah baiji ba bai gani ba,Suka kashe shi,A lokacin yazo duba jikin Azmee yaga in ta sauka lafiya,Shigowarshi keda Wuya,Sojojin suka harbeshi saitin zuciyarshi,Anan Ya yanke jiki ya faɗi matacce,



A ƙarshe mutun uku suka tsira,Azmee data 6oye a ƙarkashin gadon mahaifiyarsu,hannunta ruke da jaririnta, itama Saratu Ta tsira a wannan Lokacin,Sae kuma Gali tare da Ya sayyadi da basa acikin gidan abun Ya faru,


Azmee bata tashi sanin Jabeer ya rasu ba,Sae a washe garin ranar,ta fito daga ƙarkashin gadon hannunta ruƙe da jaririnta,jini duk ajikinshi domin ba'ayi mashi wanka ba,haka ta fito dashi rungume a hannunta,ta tsorata da ganin yadda sojoji suka wanke gidan da jinin Iyayenta,Tasha kuka kamar ranta zai fita,A lokacin Allah ne kawai Yayi zata rayu,A nan tsakar gidan taga gawar Jabeer yashe a ƙasa,ga gawawwakin Sauran Ƴan uwanta,nan take ta yanke jiki ta faɗi kasa a sume,jaririn hannunta ma Ya faɗi wanwar yana ta tsala kuka,


Bayan wasu kwanaki da yin wannan Tashin tashinar,Azmee ta farka a gadon asibiti,bayan ta shafe sati biyu kwance bata acikin hayyacinta,


Tasha kuka kamar ranta zai fita,ita sam bata damu da iyayenta da aka kashe mata ba,Mijinta tafi ji,shi da baisan komai ba,Bai aikata laifin komai ba,Amma an haɗa dashi an kashe,


 Hamma Ghali ne Ya kawo ta asibitin,Lokacin data farka tare da sayyadi da saratu tagani tsaye akanta,sune ke jinyarta tun daga wannan lokacin rayuwarsu ta tagayyara,mutane suka ƙyamace su,kowa gudunsu yake yi,saboda sanin Abunda iyayensu suka aikata,Idan suka biyo hanya har jifarsu akeyi da duwatsu ma,Dole suka daina shiga cikin jama'a,


Tundaga wannan Lokacinne,Hamma ghali Ya tunzurasu akan su ɗauki fansar kisan wulakancin da Family ɗin SALAHUDEEEN HOSSEIN suka Yi masu,Kunji silar shigar Azmee ƙungiyarsu,Wadda bayan Su salahuddeen sun ruguzata a karo na biyu,Ghali kuma Ya tada ƙungiyar ta hanyar wasu abokanan Iyayensu da suka rage ba'a kamasu ba,A lokacin ne kuma Salahuddeen yabar duniya,Saboda ɗaukar fansa Azmee ta jefa kanta cikin halaka,duk don saboda Mijinta da aka kashe,ko lokacin bataso shiga ƙungiyar ba,Hamma ghali ne Ya tunzurata sosai har saida ta amince Ta tsunduma tsulundum,Da ita da Ya Sayyadi da saratun dukkansu,Jinjirin da Azmee ta haifa ba kowa bane,Face Haroon shine ɗanta da take dashi ɗaya tilo,


Shiri na musamman sukayi domin ganin sun tarwatsa Family ɗin salahuddeen,Wannan yasa suka raba kansu,Ya sayyadi yabi Ta 6angaren Abusufyan dake zaune a kano,Da biyu ya shiga rayuwar abu saboda kawai Ya cimma burinshi na Ƙuntata rayuwar Abusufyan,Azmee kuma ta hanyar hajjaju ta biyo masu,Sai da tayi bincike sosai ta gano cewa hajjaju tana da kusanci sosai da mutanan gidan kuma itace ke kai masu ƴan aiki duk in suka buƙata,Wannan dalilin ne yasa taje har gidan hajjaju ta nemi da ta taimaka mata ta samo mata aiki a gidan Abban sojoji,

 Ganin yarda take roƙonta,Ga ƙaramin yaro yasa hajjaju ta tausaya mata,har dai ta amince zata sama mata aiki a gidan,kuma cikin sa'a Batare da ta sha wahala ba,ta samu aiki agidan duk da dama sai da tayi ma hakan shiri........"


  *Masu cewa Basu son littafin abban sojoji na kuɗi bane,Littafina na kuɗi ne,Book one ne kawai nayi shi kyauta,Amma 2 da 3 Na kuɗi ne,Dukansu 300 ne duk maiso yayi mun magana kaitsaye Amma message ta whatsapp 08103884440*

  

  




  *Masu cewa Basu son littafin abban sojoji na kuɗi bane,Littafina na kuɗi ne,Book one ne kawai nayi shi kyauta,Amma 2 da 3 Na kuɗi ne,Dukansu 300 ne duk maiso yayi mun magana kaitsaye Amma message ta whatsapp 08103884440*

  

 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*




_Ga masu karanbanin haɗa mun document,koda gigin wasa kada wanda ya kuskura Ya ƙara haɗamun document,kuma bazaku ta6a samun Complete document na takun ƙarshe ba,saboda ba yanzu zan haɗa shi ba koda na kammala littafin,Dole sai a wurina za'a same shi from page one to the end,if not babu wanda zai baku shi cikakken shi,Sannan Zan canza Lokacin posting_






Lokacin dana fara aiki acikin gidan nan,mahaifinku ya mayar dani tamkar ba ƴar aiki ba don alokacin ya tambayeni game da mahaifin yarona,na sanar dashi cewa ya rasu dalilin hadarin mota,daga haka kuma na kulle bakinshi don kar ya nemi jin wani bayani agame da dangina,Ya ɗauki Haroon ɗansa,Kuma Ya nuna yana so inbar mashi haroon ya kasance acikinku,baya son Ya taso a matsayin bare,Ba ƙaramin daɗi naji ba,Duk da mummunan ƙudirin da nake dashi,


Tsawon Lokaci da fara aikina cikin gidan nan,na fara shirya maku maƙarƙashiya,da niyyar tarwatsa farin cikin gidan nan,Amma silar kyautatawar da mahaifinku keyi mun da kuma wasu daga cikinku yasa na ɗan dakata,Akwai wani hadithi da manzon Allah (SAW)  yake cewa"Jubilatul ƙulubu ala hubbi man ahsana ilaiha,Wabugudi man Asa'a ilaiha,(An halicci zuciya da Son mai kyautata mata da kuma ƙin mai munana mata),Wannan kyautatawar da kuke Yi mun ita ta Jani har izuwa tsawon lokacin nan Batare dana Aiwatar da abunda ya kawoni cikinku ba,a lokacin banyi tsammanin zan faɗa tarkon son wani acikinku ba,Sai gashi na kamu da tsananin Son mahaifinku,Saboda yafi kowa kyautatamun,Ya yarda dani sosai Kuma ya damu dani akan kowa na cikin gidannan,Da yake ita zuciya ba ƙashi ne da ita ba,bansan lokacin dana afkawa Sonshi ba,sai kuma na fara kishi da Alexandra,don nasan cewa muddin tana acikin gidan bazan ta6a samun soyayyar mahaifinku ba,Wannan dalilinne Yasa nayi Amfani da sihirina wurin Ƙuntata mata,ta fara jin ƙunci acikin ranta,Zaman Nigeria ya gagareta,babu arziƙi ta tattara tabar ƙasar nan,batare da ta ƙarasa shayar da Junaid ba,ta barshi cikin tsummanshi yana ɗan jinjirinshi.......... "


Bata ƙarasa maganar ba,Sakamakon wani irin kukan Kura Da Mommy tayi takai mata damƙa a wuyanta,Muryarta adisashe take magana hawaye na zuba"Amma kin cutar dani Azmee,Kin cuci rayuwata,Da kuma rayuwar Junaid,Ashe kece silar dana tafi nabar mijina da ƴa'ƴana,I will neva forgive you....."kasa ƙarasa maganar tayi,nan take ta fashe da kuka,Daƙyar Abba ya samu ta saki wuyan Azmee,har tangal tangal tayi zata faɗi da sauri Jahan ya ruƙota,Ya taimaka mata ta zauna saman hannun kujera tana kuka"matar nan tajima tana cutar da rayuwarmu,Dama ance makashinka Yana tare dakai"Sosai take kuka,Ita kanta Azmeen kukan takeyi,Su Sehrish da Jahad dukkansu kuka sukeyi,Oummansu ma idanuwanta cike tab da kwalla,

Bayan ta tsagaita da yin kukan taci gaba da cewa"A lokacin mahaifinku Ya ɗauki Junaid ya bani shi don inci gaba da shayar dashi,babu yarda Hajiya azeema batayi ba akan Ya bata Junaid ta shayar dashi,Amma ya nuna cewa yafison na shayar dashi,Ba don komai ba Sae don baison Junaid Yayi nisa dashi,tunda ita a lagos take zaune,bayan ya damƙamun Amanar Junaid,naci gaba da shayar dashi,Allah shine shaidata,Inason Junaid sosai,Fiye da son da nake yi ma haroon,Sai na dinga ji kamar ni na haifeshi,har banso su Fawan suzo ɗaukarshi,gashi lokacin haushina suke Ji saboda ina ƴar aiki ƙasƙantacciya an bani Ƙaninsu ina shayarwa,ni kuwa daɗi na dinga Ji,Saboda ina tunanin ta hanyar Junaid zan samu soyayyar mahaifinku don tsakani da Allah nike sonshi hakan yasa banyi mashi wani sihiri ba wai don ya so ni,babu wanda yasan Inasonshi,Sae Laila matar Ishaq da yake ƙawatace duk da ba wani shiri nake da ita ba,Amma ina neman shawara awurinta,haka Hajjaju ma muna mutunci da ita,Dukkansu babu wanda yasan Ainihin wacece Ni,Duk irin son da nake yi ma Abbanku bai ta6a lura ba,Naso na sanar dashi amma ina tsoron Yace baiso na,bansan wani hali zanshiga ba,Lokacin da Junaid Ya fara tasawa,abunda Ya bani tsoro dashi irin wayon dake gare shi,Kullum agabanshi nake yin waya cikin harshen fulatanci,kwatsam wata rana,bayan na kammala waya,sai yake ce mun ae Yaji duk abunda nace,A lokacin na ɗauka da wasa yake yi don nasan baijin fulatanci,Sai cewa nayi toh ya faɗamun me nake cewa acikin wayar,ba zato ba tsammani Yaron nan Ya fassara mun maganganun da nayi acikin wayar,hankalina yayi mugun tashi,Ko makaranta ba'a sanyashi ba,na ruƙe shi ina tambayarshi a ina ya koyi harshen fulatanci,Sae ce mun yayi a wurina yaji ina yi,duk in zanyi waya,tunda naji haka saina tsorata dashi,tabbas wata rana zai iya tona mun asiri,tunda har ya iya yaren da nake yi wanda a waya kawai nake magana da harshen,Kawai na yanke shawarar In juye mashi tunaninshi ta yadda bazai ta6a fahimtar komai ba,Tun daga wannan lokacin Junaid Ya zama soko,Bai ɗaukar karatu ko mis'ƙala zarratin,Nasan na cuci Junaid,Da ace Yayi ilimi da ina da tabbacin cewa zai kasance ɗaya daga cikin ƴaran da duniya zatayi alfahari dasu saboda baiwarsu,A kwana a tashi,Rana ta farko dana fara Yin tozali da Rafayet,Bazan ta6a mantawa da wannan Lokacin ba,dawowarshi kenan daga U.S,Ya soma tambayar ina Babyn da Mommynsu ta bari,Su fawan ke sanar dashi cewa Yana a wurin mai aikinsu har suke bashi labarin cewa ni na shayar dashi,Ranshi yayi mugun 6aci Yasa su kirani,Na fito ɗauke da Junaid a hannuna,ya rufesu da faɗa don me za'a ba mai aiki ta shayar da ƙaninsu,sun tabbatar da tsaftar jikina ne,A karshe ya kar6e Junaid daga hannuna,Ya wuce dashi dakinshi,


Tunda na koma ɗaki,na kasa runtsawa saboda tunanin Rafayet,Kyawun fuskarshi dana surarshi suka ɗebeni har na Fara kamuwa da sonshi,Maimakon da yayi mun faɗa inji haushinshi,Sai ma sonshi da nake kara Yi,na kasa samun natsuwa kullum in naje kai mashi abinci,ban iya kawar da idanuwana daga kallonshi,shi kuwa bai ta6a ɗago da idonshi ya kalleni ba a wannan lokacin balle insa ran zan same shi........."dakatawa ta ɗanyi da yin maganar,Yayin da hawaye ke cigaba da wanke fuskarta,


Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,Kallon Sgr kawai take yi,Shi kanshi abun ya ɗaure mashi kai,bai ta6a sanin wannan zancen ba,Mommy kuwa wani irin kallo take binta dashi,


"Daƙyar na samu Sgr ya fara tanka mun in na gaishe shi,Ba ƙaramin daɗi nake ji ba idan na kai mashi abinci yaci,ni kaɗai nayita haukan soyayyata don shi baisan ma inayi ba,A kwana a tashi Ya koma U.s A ranar kamar nayi hauka,bayan tafiyarshi na soma tunanin Me ya kawoni gidan?Me nake jira da ban aiwatar da mummunan ƙudurin daya kawoni ba,Saboda jin daɗin da nake ciki,Na manta cewa ɗaukar fansa ta kawoni gidan,Komai na more rayuwa ina samu,Inci me kyau in sha me kyau in kwana a me kyau,ga Albashin da Abba ke bani harya zarce na wani likitan,ko lokacin bani albashina baiyi ba,Yana yawan dunƙulo kuɗi ya damƙa mun,Yace ga wannan in ina buƙatar wani abu,Insa driver yakaini kasuwa inyi siyayya,Wani irin daɗi nake ji,koba shi ba da yawan lokutta Yusuf Yana bani kuɗi hakanan kyauta yace mun ga wannan Inyi amfani dasu,Ganin irin ƙaunar da suke nuna mun saina fara tunanin kodai in janye batun ɗaukar fansar nan tawa,Tabbas a lokacin na fara tunanin yin tuba in koma Ga Allah,Amma sai Dangina suka taso ni gaba,Musamman Hamma Ghali barazana Ya soma yi mun akan kodai na aiwatar da abunda ya kawoni cikinku ko kuma zai ɗauki mataki akaina,na tsorata sosai,Saboda mugune shi,nasan shi sarai,kuma shine Shugaban ƙungiyarmu ta matsafa,komai nake Yi acikin gidan nan akan idonshi nake yi,Duk da bamu atare amma Yana da madubin tsafinshi wanda yake kallon duk wani motsina,Ba don naso ba haka naci gaba da bin umarninshi,A lokacin Haroon  na soma ƙoƙarin janyowa Jikina,Na nuna mashi cewa ku ba jininshi bane,Ya daina shige maku,Fansa muka zo ɗauka acikinku,Amma sai ya kangaremun,Yace shi bazai yarda a haɗa baki dashi ba,Wurin cutar daku ba,Saboda Abba yana sonshi,kuma Yanayi mashi duk abunda Yake so,Don haka inma naci gaba dayi mashi magana zai tona mun asiri ne,Jin wannan magana ta haroon Yasa na fara tunanin ta yadda zan juye mashi tunaninshi,Don na lura ɗabi'unsa da halayyarsa ba irin ta dangina bace,Duk da dama ina kokwanto akanshi,Banda tabbacin wanene mahaifinshi,Ganin yana nema yafi ƙarfina sai na sanar ma Hamma ghali abunda Haroon Yace,aikuwa tun daga wannan Lokacin da mukayi waya dashi,Ya sanar dani cewa In kawar dakaina akanshi zanga me zai biyo baya,tofa aikoda yace haka,cikin ƴan kwanaki ƙalilan Haroon ya canza,Ya zama mugun ƙarfi da yaji,Wata muguntar ma ba saina sanar dashi ba,dakanshi yake yi,Ga bin mata da bin maza,Shaye shaye duk wani aiki na shaiɗanci Haroon ya iyashi,nikaina banji daɗin Sauyawar Haroon ba,Iya Cuta dai Mun cutar dashi,Duk da bani bace silar jefa shi cikin halin da yake ciki ba,Amma ni mahaifiyarshi ce,dani akayi amfani wurin Canza mashi tunaninshi,su kuma Su twins Rashin kunyar da suke yi mun ne Yasa nayi masu turen shaiɗanin Aljanu ajikinsu,Waɗanda ke sanyasu suna Neman junansu wanda in har basuyi ba,Aljanun nan ke jibgarsu da bulala,........."sosai Azmee ta fashe da kuka,


Gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi,wasu ma gaza cigaba da tsayuwa suka yi dole suka zauna,


"About Junaid!Ke da Haroon Waye ya shirya Mutuwarshi"?Sgr ne yayi mata tambayar,

Daƙyar ta tsagaita da Yin kukan ta soma kora mashi bayani,

  "Haroon ne Ya shirya mutuwar Junaid,A lokacin Kun fusata shi sosai,dama a ƙule yake daku,saboda bambancin da kuke nuna mashi don ba ahankalinshi yake duk abubuwan da yakeyi ba,Duk da ni naso In kashe Junaid,ko dan in fanshe haushin kisan Mijina da akayi,Nasha Sanya Haroon ya kashe Junaid,Amma sai ya ce mun bazai Iya kashe shi ba,Junaid yana sonshi sosai,Kuma bai aikata mashi laifin da zai kasheshi ba,Har ce mun yakeyi zai iya kashe kowa acikin gidan nan koda kuwa Abbane,Amma banda Junaid,Ni gaskiya aranar bansan maiya ƙona mashi rai ba,Har ya bada Umarnin akashe mashi Junaid,



a ƙa'ida Miyagun dake yi mana aiki,basa Yanke hukunci in ba sun sanar dani ba,Dole sai in ni na basu umarni kaitsaye suke aiwatar da abu,Haroon ya basu Umarni su kashe Junaid su kuma Sun kirani a waya sun sanar dani cewa Haroon Ya basu Umarnin su kashe Junaid,Shin da sanina koba da sani na ba,"!nan take nace masu karsu kuskura su kashe shi,Su san yarda za'ae su ɗauke Junaid daga cikin motar sannan su ƙonata yarda kowa zaiyi tunanin ya mutu,Nayi hakanne saboda banaso Haroon yaji cewa Na hana su bi umarninshi don zai canja wata hanyarne,sannan Kuma Don Junaid Ya zame mun makamin da zan Yaƙe ku dashi,


Ƙarin bayani,


Lokacin da Jahad ta fita daga cikin motar ta tsallaka zata siya masu ice cream,Junaid Ya dinga ƙwala mata kira,Ta dinga juyowa tana kallonshi Yana yi mata bye bye,bayan mai ice cream ɗin ya sallami mutanan dake gabanshi,Yace ma Jahad madam guda nawa za'a baki,Ta juya ta bashi Amsa,A cikin wannan Lokacin kafin Jahad ta lalubo kuɗi acikin jakarta ta miƙa mashi,adai dai lokacin,waɗannan miyagun suka buɗe motar,kafin Junaid ya ankara suka shaƙa mashi cocaine a hancinshi gaba ɗaya ya fita hayyacinshi,janyoshi su kayi daga cikin motar da hanzari suka fitar dashi,wanda ya ɗauki Junaid a kafaɗarshi ya juya dashi ta baya inda suka ajiye motarsu ya tura shi aciki,Shi kuma ɗayan Ya jefa bomb acikin motar,Yana barin wurin,Gingimarin Motar nan Ta shararo da gudu,Dama already sun kira wayarshi yana akan layi suna sanar dashi cewa Babu Yaron acikin motar,Atsiyace Yabi takan motar Junaid Ya rugurguzata,Yana sauka ya antaya da gudun gaske,Nan take Bomb ɗin cikin motar Ya fashe,Dama sun ɗibar mashi adadin mintunan da zai tashi,To masu karatu Kunji yadda akai Junaid Ya tsira,Baya acikin motar lokacin da suka take motar,Ko lokacin da Jahad ke ihu tana kuka,Duk a kunnanshi bawan Allah,Yana acikin motarsu sun rufe shi,Sam baya acikin hayyacinshi sai faman shafa glass ɗin motar yake yi yana kallonta,A haka har suka tashi motar da gudu suka bar wurin bayan sun dauki vedion motar naci da wuta wanda suka tura ma haroon,


Yadda akai Sgr yasan game da abubuwan daya fadi ma haroon kuwa,dama tun farko,ya dawo Nigeria ne da niyyar yin bincike,don Mommynsa tasha fadi masa cewa akwae abubuwan dake faruwa ba daidai ba acikin gidan,kuma ta sanar dashi ita bata yarda da azmee ba,wannan dalilinne yasa yazo da shirinshi,a 6oye ya fara yin bincikenshi ba tare da kowa ya sani ba,ana haka kuma Mommynsu ta kirashi ta sanar dashi game da makudan kudin dasu twins suka bukata awurinta,ta tabbatar mashi akwae abunda yake faruwa dasu wanda suka 6oye don a yadda suka bukaci kudin sam hankalinsu ba'a kwance yake ba,gashi itama ta bukaci sai sun shirya tsakaninta da Junaid wanda tana ganin hakan ba mai yuwuwa bane cikin sauki,amman sai gashi sun aikata hakan duk don ta basu kudin,hakan yasa mata zarginsu,jin hakan yasa Sgr yin amfani da Surveillance Cameras wadanda yasa a wasu bangarori na gidan ba tare da kowa ya sani ba don bai barsu a bayyane ba wasu har a cikin chandeliers(fitilun sama) na parlon gidan aka sa,ta nan yake ganin duk abunda ke faruwa har lokacin dasu twins din suka kaima haroon kudin wanda daga baya yabi ya daukesu,koda ace asirin Azmee bai tonu ba ta hanyar ya Mu'allim ba,Sgr na gab da ganota,atakaice ma kusan ya gane bata da gaskia shiyasa ko lokacin da Abu ta sanar dashi dalilin ciwon Sehrish da kuma inda tasan Azmee yayi murmushin takaici,haka lokacin da Marshal Omar ke lallaba haroon akan ya sanar dasu wanda ke bashi umarni yace Sgr yasan komae,wannan kenan.


Azmee taci gaba da bayani "Tunkafin Afkuwar wannan Lamarin,Akwai sihiri ajikin Junaid,Wanda mukayi mashi turenshi,a duk daren duniya,dunƙulen jini na fita daga hancinshi batare da sanin kowa ba,Saboda bai sanar daku ba,bayan Faruwar Accident ɗin nan ni nasa aka killace mun Junaid,kuma na hana kowa Ya cutar mun dashi,Lokacin da kuka sanar cewa Junaid Anyi kidnapping dinshi,Nayi mamaki sosai,Yarda kuka tsara hakan bayan a iya saninku mutuwa Yayi,Sai kuma nayi tunanin cewa Kun 6oye mutuwar Junaid ne saboda mahaifinku gudun kada ku rasa shi,bakowa ya fara Zargina ba,Sae Sehrish da ta tsinci zoben Junaid a cikin wardrobe ɗina,tundaga nan ta fara sanya mun ido,ni kuma nayi kokarin rikitar da ita har ta fara ƴan gane gane..............."


Tunkan takai ƙarshen Maganar,Omar ya katse ta da cewa"Yanzu ina Junaid Yake,"?yayi tambayar tamkar baisan inda yake ba,

Shuru Azmee Ta ɗanyi kafin tace"daga bayan nan Nasa an kaishi gidan Hajiya saratu,Ɗiyar wan mahaifina wadda ke acikin garin nan,"..

  "Innalallahi wa'inna ilahirraji'un!!" Amrish ce ta ambaci hakan tare da ɗaura hannunta asaman kanta,Tana kuka,

Hankalin kowa Ya koma kanta,Muryarta na kerma ta nuna Azmee da hannunta tana faɗin"Dama ke kikasa aka kaishi gidanmu dan baƙin zalunci?Wacece ke?Ni bansan meya haɗani da ku ba,Wlh duk na tsani kaina,In har abunda nake zargi ya tabbata,wlh saina kashe kaina,"sosai ta fashe da kuka 


Tunda Azmee taji hakan nan ta gane cewa wani abu ya faru acan gidan,tabbas Junaid Ya ku6uta daga wurinsu,.

Gyaran murya Ya Mu'allim yayi,hankalinsu ya dawo kanshi,Anan Yake labarta masu duk abunda ya faru kamar yarda Amrish ta sanar dashi,Har zuwa kaishi asibiti da su kayi,


Yana kai ƙarshen maganar,Azeemi tace"Naji daɗi da Junaid ya dawo hannunku,Amrish ke bakowa bace face ɗiyar saratu matar ƙanina Ya Sayyadi,Da saratu dani ƴa'ƴan wa da kanine,Don haka ke jininmu ce gaba da baya,babu yarda zakiyi haka Allah Ya ƙaddaro maki,Ki gode ma Allah da baki ɗaukko irin mugayen ɗabi'un mahaifinki da mahaifiyarki ba wanda hakan ne ma yasa ba'a bayyana maki mahaifin naki ba,"


Waro ido waje Amrish tayi,idanuwanta sunyi jawur dasu,a fujajan ta watsa da gudu ta nufi Glass cups ɗin da suka faffashe a wurin,ta ɗauko ta daddage zata Caka shi a ƙahon zuciyarta da sauri Kanal Yusuf yayi hanzarin damƙar hannunta,ƙoƙarin kwacewa tadinga yi don ta Caka ma kanta,Amma ya hana hakan,Fisge glass ɗin yayi tare da jefar dashi ƙasa,Ya ruko kafaɗunta ya jinjigata"baki da hankali ne?Saboda me zaki kashe kanki?saboda Iyayenki sun kasance Gur6atattu!Laifinki ne?ko kin manta da ayar da Allah subhanahu wata Allah ke cewa"Yana fitar da mai rai daga matacce kuma yana fitar da matacce daga mai rai,kuma yana rayar da ƙasa a bayan mutuwarta,Kuma haka ake fitar daku,acikin suratul rum Ayata 20,Bayan ita akwai surar da tayi magana makamancin wannan acikin suratul Ahli'emran Aya ta 28,don haka ki kwantar da hankalinki,Ki rungumi ƙaddararki,Bakanki farau ba,Sau nawa cikakken malami ke haihuwar 6arawo ko kasurgumin dan fashi?Ba yadda Allah bai ikonshi,kuma bawai don baya sonku ba face don Ya jaraba imaninku,Sannan Laifin da iyayenki suka aikata bazai ta6a shafarki ba,ki gode ma Allah da baki ɗauko irin ɗabi'unsu ba,Ke tsarkakkiyace,Allah ya tsarkake ki daga faɗawa halaka.......'jikinta ba ƙaramin Sanyi yayi ba,Kalaman kanal Yusuf ba ƙaramin sanyaya mata zuciyarta su kayi ba,Har taji ta haƙura da kashe kanta da tace zata yi,Jiki asanyaye ta juya ta koma wurin Sehrish,rungumeta Sehrish tayi ajikinta,gaba ɗaya suka fashe da kuka maicin rai,dole Amrish taji ba daɗi,very heart touching ace iyayenka su dukansu gur6atattune kuma 6atattu,dayawa mutane zasu dinga yi maka wani mummunan kallo,Ya Allah kasa mu dace,



"Nasan bazaku ta6a yafe mun ba,Ku yanke mun duk hukuncin da ya dace dani,wlh zan kar6eshi hannu bibbiyu,Amma dan Allah ina neman wata alfarma ɗaya agare ku,"Azmee ce tayi maganar,yayin da kwalla ke cigaba da zubowa akan fuskarta,


Kasa kunne su kayi suna sauraronta,

"Dan Allah,Kada ku ta6a Haroon,Duk hukuncin da zaku yi mashi,Ni kuyi mun saboda ba laifin shi bane,tursasa mashi akayi,Bayan tafiyarku asibiti,Na same shi acikin mawuyacin hali ɗakin da kuka kwantar dashi,Na kwanceshi sannan na fitar dashi daga cikin gidan nan,Saboda gudun kada ku kashe shi nasan bazaku ƙyaleshi ba"


"Azmee kin bani mamaki,Kin karya mana zuciyoyinmu,Bakisan irin raɗaɗin da kika sanya mana acikin Zuciyoyinmu ba,Why Azmee?Duk don saboda daukar fansa Yasa kika shiga jikinmu!Ina iliminki ya tafi ne?Ke fa musulmace,bakiyi imani da ƙaddara bane?Meyasa Laifin wani zai shafe mu ?ballantana ma Ba wani abu akayi maku ba,Komai ya faru da family dinku laifinku ne,Saboda kun kashe ne shiyasa aka kashe naku,Da baku ta6a kowa ba,babu wanda zai ta6a naku,Kuskure ɗayane na kashe mijinki da akayi wanda shima don ya taka sahun 6arawo ne,Tsautsayine ya rutsa dashi....."daƙyar yake magana,sauke ajiyar zuciya yayi kafin yaci gaba da cewa"Almost 20 years Azmee kina tare damu ashe ba don Allah bane,Wlh tausayinki nake ji,Kin 6ata wayonki,kuma kinyi asarar Rayuwarki,Yanzu komai da kikayi ya tashi abanza,hatta ibadar da kikeyi itama ta tashi abanza,Idan yanzu kika faɗi kika mutu me zaki ce ma Allah?ya ƙarasa maganar yana kallonta,Sosai Azmee ta fashe da kuka kamar ranta zai fita 

  "Da ace kinyi hakuri,kin rungumi ƙaddara,Yaya kike tunanin Rayuwarki zata kasance?yadda kowa ke sonki,Kina da farin jini sosai,Ko abokanaina in suka zo gidan nan har santin girkinki suke yi,Kowa yabonki yake yi,Why Azmee?Kin ɗauki alhakin mutane dayawa,Kin cuce mu kin yaudare mu,kin kuma zalunce mu,Amma inaso ki sani,Wlh duk kanki kikayi mawa!"abun ya ƙona mashi rai sosai,

  "Ni wlh da tun farko kin sanar dani cewa kina sona,a yadda na yaba da kyawun halayanki a wannan lokacin,Da ba abunda zai hana in aure ki!"

  Ɗagowa tayi da idanuwanta waɗanda su kayi jawur dasu,tana kallon Abba dake magana,

 Rai a6ace Mommy tace"Ni bansan me kuke jira da ita ba,Banason ganin matar nan,Rayuwarta bata da amfani,ta mutu kowa ya huta,"


Gaba daya sun fusata,ganin suna ƙokarin zame belt ɗin wandonsu don su jibgeta,Abba yayi saurin dakatar dasu"Innallaha ma'assabirin!Kubarta da Allah Shiyasan yarda zaiyi da ita,ban amince ɗaya daga cikinku Ya ta6a lafiyar jikinta ba,Azmee bata kashe mun kowa ba,Iya cuta dai ta cutar damu,Ina neman alfarma a wurinku,daku miƙata wurin hukuma su yanke mata hukuncin daya dace da ita,Sannan kuma Ina umartarku da ku hanzarta Ruguza ƙungiyarsu,Da duk wani wanda ke cikinta,Kamar yarda kakanku salahudeen yayi,haka nakeso kuma Kuyi,Kada ku raga masu,banaso daya daga cikinsu Yasha,gawawwakinsu kawai nakeson Gani,"Yana kai ƙarshen maganar,Ya juya tare da barin wurin Ya koma bedroom ɗinshi,Idanuwanshi cike tab da kwalla,a ƙopar ɗakin ya tsaya yayin da idonshi ke akan Junaid dake kwance saman gadonshi Yana ta sharar bacci abunshi,Har cikin ranshi baiso Azmee Ta kasance haka ba,Koma miye ita taja ma kanta,Ya Allah kakare mu daga aikata Aikin dana Sani,


Bayan tafiyar Abba,Ya Mu'allim Yace"Shawarar da zan baku shine,Kuyi amfani da Azmee wurin kama sauran masu aikata laifin,saboda tasan komai,Tasan inda ƙungiyarsu take Inyaso daga bisani Sai a miƙata ga hukuma,zamu tayaku da Addu'a akan Allah ya baku nasara,"


Sosai sukayi ma Ya mu'allim Godiya,domin kuwa ya basu shawara mai kyau kuma Ya taimakesu,batare da 6ata Lokaci ba,suka tasa ƙeyar Azmee zuwa Ɗakin horonsu,Tambayoyi suka shiga jero mata,tana amsa masu,In tayi kuskuren yi masu taurin kai kuwa,zazzafan Mari take sha,Anan suka samu bayanin inda Ya sayyadi Yake,Ashe baya ƙasar tun Lokacin da abu ta kashe mashi idanuwanshi,Suka fiddashi ƙasar waje,Don a duba lafiyarshi,Da wayar Azmee sukayi amfani wurin gano Duk wani mugun abu da suke aikatawa,A ranar suka shirya tsaf cikin kakin Sojojinsu gaba dayansu domin fara yaƙar ƙungiyarsu,Manya manyan makamai suka ɗauka,Sai da Abba ya fara sanya masu Albarka,Yayi masu addu'a,Mommy ma tayi masu tare da sauran Mutanan gidan Kafin Su kayi masu sallama,A tare da Azmee suka tafi Asaman Helicopter kusan guda shida Ya ɗaga dasu,


Kasa samun natsuwa su Sehrish su kayi,kowa zullumin yake yi game da tafiyarsu Babban Yaya,wurine mai matukar haɗarin gaske acikin wani ƙurmamin daji,inda suka kafa ƙungiyarsu ta matsafa,kodai su kashe ko akashe su,Allah kaɗai yasan wanda zaiyi nasara,


Abu kamar wasa har goma sha ɗayan dare basu dawo ba,babu wani labari dangane dasu,Wayoyinsu kuma duk in aka kira bata shiga,Hakan Ya ƙara tayar masu da hankalinsu,shi kanshi Abba sai daga baya ya fara danasanin turasu,Mommy kuwa tuni ta fara zubda kwalla,tsoranta kada ta rasa Ƴa'ƴanta,


A 6angaren su Sehrish kuwa,Babu wanda ya runtsa acikinsu,kwana su kayi saman darduma sunayin sallah akan Allah ya basu nasara ya kuma dawo dasu Lafiya,abu kamar wasa Tsawon kwana biyu kenan su Sgr basu dawo ba,lamarin ya fara tsoratar dasu,Gashi ba'a samun Layinsu balle asan awani hali suke Ciki,


Sai adaren Rana ta biyu ne,Allah yayi suka dawo,Sunyi nasara sai dai sunyi babban rashi na mutun ɗaya acikinsu,Irfan Allah yayi mashi rasuwa,sunji mutuwar nan kamar kamar me,tare da gawarshi suka dawo,wasu daga cikinsu kuma sun raunata sosai,Dan Fawan Allah ne yayi zai rayu,Twins kuwa sun jigata sosai,kowa Yaji ajikinshi,Nasarorin da suka samu sune sun ruguza Ƙungiyar matsafan,sun lalata masu komai,Sun kuma kashe mutanan cikinta gaba ɗayansu,don sunyi masu zuwan bazata,kuma sunci sa'a  adai dai lokacin suna kan yin meeting ne,kowa Ya hallara,Hada shugaban nasu Ghali,Da taimakon Azmee suka kashe shi,Yanzu mutun ɗaya ya rage masu su kamashi Wato Ya Sayyadi,



A washe garin ranar akayi jana'izar Irfan,Abba Yafi kowa jin mutuwar nan,Abubuwa sunyi mashi yawa,Ga Junaid dake kwance yana jinya,Ga kuma fawan shima Yana ƙarkashin kulawar likitoci,


Bayan kammala Jana'izar Ifran,Batare da 6ata Lokaci ba,Sgr Ya tura Armstrong tare da wasu daga cikin sojojinshi,Suka hau jirgi zuwa ƙasar Malaysia,Don bala'e har asibitin da aka kwantar da Ya sayyadi suka Cafko shi,idanuwanshi Na manne da uban bandegi,da Alama aiki akayi mashi a wurin,Cikin jirgi suka sanyoshi,Sannan Suka dawo dashi Nigeria,har cikin gidan suka taso ƙeyarshi gaba,a garden ɗin gidan Sgr ya sanyasu suka Kwantar mashi dashi,kafin ya yanke mashi hukunci,Sai da Ya fara kiran Abusufyan tare dasu Jahad,da oummansu gaba ɗayansu suka hallara a garden ɗin,

Abusufyan yace"dama saida na faɗa maka,Wannan ranar zata zo,kuma gata Allah ya nuna mun da raina da lafiyata,Gani ga kuma Yaran daka zalunta,Ga kuma mahaifiyarsu,Kaji haushin rayuwarka Sayyad,A yau ƙarshenka yazo,tun a gidan duniya zaka fara ɗanɗani raɗaɗin azaba,kafin ka koma Ga Allah," gaba ɗaya yabi ya ruɗe,jikinshi sai kerma Yake yi,daga yayi ƙoƙarin buɗe baki zai basu haƙuri,Sai Sgr ya Kai mashi naushi a kuncinshi,duk saida Ya zubar mashi da haƙoran bakinshi,Jini jaga jaga A bakinshi,

 "Mugu azzalumi,Ni Ko kaɗan banji tausayinka ba,Allah yaji ƙanka don nasan cewa taka ta ƙare,Allah ya ƙara nauyin ƙasa,"Abuce tayi maganar,

  Jahad da sehrish basu ce komai ba,Hosana dai ce Ta tofa mashi Miyau Asaman fuskarshi,bayan sun gama gaya mashi magana,Sgr Yaba sehrish umarnin ta kawo mashi tafasasshen Mai,


Jiki na rawa ta juya ta koma cikin gidan,Oummansu dasu Jahad suka bi bayanta,Bada jimawa ba ta dawo hannunta ɗauke da ƙaramar tukunya,Tafasasshen mai ne aciki sai tartsatsi yake yi,

  Umarni yaba Su armstrong,Su cire wandon jikinshi,Ganin haka yasa Sehrish ta ajiye man,ta watsa da gudu ta koma cikin gida gabanta na faɗuwa,

  Bayan sun cire wandonshi,suka yi mashi zirr,sojoji guda biyu suka tale ƙafafunshi,Abun nan da yake takama dashi yana yi ma mutane iskanci dashi,Sgr ya ɗauki tafasasshen man nan ya kwarara mashi agabanshi gaba ɗaya,

 Wa'iyazubillahi!Wata irin kururuwa Ya sayyadi yayi,lokacin da gabanshi ke ƙonewa,wani irin raɗaɗin azaba Ya dinga ji,Gaba ɗaya ya zauce ya gigice Ya fita hayyacinshi,


Umarni Ya basu  Su ɗauke shi su kaishi can cikin ƙurmin daji,ko namun dawa sun samu abinci,A ƙarshe dae Ya sayyadi A cikin daji rayuwarshi ta ƙare,gawarshi A wulaƙance A ƙasƙance abun ba kyan gani,



Ita kuma Azmee Tare da Saratu,Jami'an ƴan sanda ne suka tafi dasu,Bayan an tattara hujjoji,Suka miƙasu Court domin Yin shari'a,A ƙarshe Aka yanke masu hukuncin zama gidan Yari,A ɗakin duhu na tsawon shekara 20,Sehrish tasha kuka,Saboda har lokacin tana son Azmee,Lokacin da aka kammala shari'ar za'a tafi dasu gidan Yari,Daƙyar aka rabasu,Sun rungume juna sosai suna kuka,ita da Sehrish,ita kam Amrish kin zuwa tayi wurin Mommynta balle ma ta rungumetan dama dakyar ta biyo su kotun,kowa baiji daɗin halin da Azmee ta jefa kanta ba,ba lalle ne lokacin da zasu fito ɗakin duhu ba,su dawo da idanuwansu ba,zaiyi wuya in basu makance ba,idan ma sun rayu kenan,'



Lokacin da Labarin mutuwar Irfan ta riski danginsu,Lokaci bai cika kwana biyu da rasuwa ba,Gidan Ya cika fam da masu zuwa yi masu jajen abunda Ya faru,Da kuma Yi masu gaisuwar rashin da suka yi,Mutane dayawa Sunyi mamakin jin cewa Azmee ce take ɗaukar fansa akan mutanan gidan,Sunyi Allah wadai da halinta,Tasha Zagi wurin jama'a don wasu da suna da halin da zasu ganta sai sun kasheta da bugu,Yanzu Alhamdulillah basu da wata sauran fargaba,NO MORE TENSION,


   Kowa yayi dakyau don kanshi,


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 6 na marece,A jere motoci suka dinga shararowa izuwa cikin gidan,dankara dankaran gaske,Bayan sunyi parking ɗin motocin,Mota ta farko,Wani sergent Ya fito tare da zagaya Ya buɗe gidan baya,A hankali ta sauko daga cikin motar,jikinta sanye da code lace fari,Bakowa bace face Hajiya Azeema,fuskarta ɗauke da murmushi,other side ɗin hafsat ce ta fito jikinta sanye da atampa,Ta ruƙo hand bag dinta,

  Motar bayansu,Ammi ce tare da Gwaggon katsina,Dr harriss ne yayi driving dinsu,Saude na a gefenshi,

Daga Motarsu kuma sai Motar MG Osman,Tare da Captain adam,basu kaɗai bane a motar,Akwai Ƴan matan da suka zo dasu kyawawan gaske daga Gani ƴan uwansu ne,

  Motar dake bayansu Motar Captain Najeeb ce,su biyu ne aciki shi da Talal autansu na biyu,


Babu wanda yasan a ranar zasu dawo,


A lokacin gaba ɗayansu sun hallara asaman dining suna Cin dinner ɗinsu,banda mutun biyu Omar da Sgr basu kaiga dawowa daga wurin aiki ba,They're busy for work ga prepation ɗin da suke yi Na Komawa U.S tafiya ta kankama,kowa ka kalli fuskarshi daurewa kawai suke yi akwai sauran jimami,Yanzu babu Azmee sai dai Abu dasu Jahad ke girka abincin gidan,



Sehrish ta zabga uban tagumi,Bakowa take tunani ba,face Aunty azmee,Duk in oummansu Nayi serving ɗinsu abinci,Sai ta dinga tunawa da ita,


Binsu da kallo ta soma yi ɗaya bayan ɗaya,tun daga kan mommy dake ta faman jujjuya cokali acikin abincin gabanta,Abba kuwa tunda ya zauna Bai ta6a komai ba,Lemu kawai yake tasha,

Su twins Da ɗan dama,Sun saki jikinsu suna cin abinci,Haka kanal yusif ma sosai yake Cin abincinshi,Irfan da jabeer still sai a hankali,Duk sun kasa sakewa saboda rashin Irfan da su kayi acikinsu,


Kallon Hosana tayi,Cinyar kaza ta ɗauko ta tura abakinta sai tauna take yi kamar akuya ta samu ciyawa,Murmushi sehrish ta ɗanyi tare da ɗan girgiza kanta,Mayar da idanuwanta tayi kan Amrish dake zaune daƙyar take tura abinci abakinta har yau ta kasa sakewa acikinsu,ɗagowa tayi suka haɗa ido Da sehrish atare suka sakarwa Juna murmushi,


  Miƙewa Jahad tayi,"Where are u going"?Abusufyan ne ya tambayeta ganin ta miƙe tsaye bata kammala cin abincin ba,

  Sunnar dakai ta ɗanyi kafin tace"Zanje na duba jikin junaid ne"

Murmushi ya saki,kafin yace"Je ki abunki,Allah yabar ƙauna,"


Kunyace ta rufe ta,daƙyar ta iya ɗaga ƙafarta,da sauri tabar wurin ta nufi bedroom ɗin abba,


Bayan tafiyar Jahad mommy ta mike"Zanje na duba jikin fawan,Inaso naji idan akwai abunda yake buƙata sai in kai mashi,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta kama hanyar bedroom ɗinshi,

Lokacin da jahad ta ƙarasa bedroom ɗin a ƙopar ɗakin ta tsaya,tare da sanya hannu ta ruke handle ɗin ƙopar,Slowly ta tura ƙopar ɗakin ta ɗan leƙa,har yanzu bawan Allah a kwance yake baisan inda kanshi yake ba,Da alama Ya samu bacci,kullum sai Ya mu'allim yazo duba shi,yanzu ya zama tamkar ɗan uwa agaresu,


A hankali take tafiya harta ƙarasa gefen gadon ta zauna,Zuba mashi ido tayi tana kallonshi,Yanzu bata da burin daya wuce taga junaid Ya dawo cikin hayyacinshi,Fargabarta kada Ya manta da soyayyarsu,


A hankali ta kwantar da kanta gefenshi,Allah ya baka Lafiya My Romeo,ta ambaci hakan tare da lumshe idanuwanta,Unexpect Taji Saukar hannunshi acikin Sumar kanta,A firgice ta ɗago da kanta tana kallon fuskarshi,slowly ya buɗe dara daran idanuwanshi farare ƙyal akan fuskarta,La66anta na kerma Ta ambaci Sunanshi JUNAID! da mamaki akan fuskarta,Binta da ido yayi yana kallonta,Matsawa tayi saitin fuskarshi,

  Cike da tsantsar farin ciki ta kuma ambaton sunanshi"Junaid"

  Lumshe mata idanuwanshi yayi tare da sake budesu akan fuskarta,Saboda tsabar farin Ciki,Da sauri ta sauko daga saman gadon ta watsa da gudu ta fito daga ɗakin,Jin takun takalmata yajanyo hankalinsu akanta,

  Tunkafin ta isa ta soma magana"Abba Junaid ya farka,Ya dawo cikin hayyacinshi,"Gaba ɗaya suka miƙe Fuskar kowannansu ɗauke da tsantsar farin Ciki suke kallonta,Adai dai Lokacin Gwaggon Katsina Ta dako masu Sallama da ƙarfin gaske tana fadin"Gafara dai,Mai wuri yazo Me tabarma ya naɗe,Masu Gidan sun dawo,"





*Masu cewa Basu son littafin abban sojoji na kuɗi bane,Littafina na kuɗi ne,Book one ne kawai nayi shi kyauta,Amma 2 da 3 Na kuɗi ne,Dukansu 300 ne duk maiso yayi mun magana kaitsaye Amma message ta whatsapp 08103884440*

 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋






𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤

𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠


*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*







Koda su kayi arba dasu Ammi wani irin farin ciki ne Ya lullu6esu,Watsawa Hosana tayi da gudun gaske tana faɗin"Ga gwaggo!Ga gwaggo!"Washe baki gwaggon katsina ta soma yi"Yawwa ya'yan abusufyan ɗina,Nayi kewarku sosai,"Rungumeta hosana tayi,Tana ta faman tikar dariya,Sehrish kuwa Tana yin arba da hajiya azeema,Da gudu ta nufeta,Murmushi Hajiya azeema ta saki tare da janyota jikinta,Ta rungumeta sosai tana shafa bayanta"I really missed u My daughter,Nasan kinyi kewata sosai,"

  ƙarasowa wurinsu Jahad tayi kaitsaye ta nufi Hafsat,wani irin farin cikine ya lullu6e hafsat ganin ta tunkarota fuskarta ɗauke da fara'a tayi tunanin har lokacin fushi suke yi da ita,Rungume juna sukayi sosai,

  "Wato kowa nashi ya sani ko?kun manta da kakarku,"Abba ne yayi maganar fuskarshi ɗauke da murmushi,Ya ƙarasa wurin Ammi,ta rumgume shi ajikinta,Wata nauyayyiyar ajiyar zuciya ya sauke,lokaci guda yaji idanuwanshi sun cicciko tab da kwalla,

  Shafa bayanshi Ammi tayi"Nasan ban kyauta maka ba,nayi nesa dakai a lokacin da kake buƙatar kulawata,Kayi haƙuri hossein Banji daɗin abubuwan da suka faruwa ba,abun ya ta6a zuciyoyinmu"Sosai ammi tashiga tausarshi,

  ƙarasowa Su Kanal yusif su kayi,Abusufyan ya rungume Dr harris,Yusif kuwa Wurin Captain adam Ya nufa rungume juna su kayi,Jabeer ya rungume Mg Osman,Kowannansu fuskarshi ɗauke da murmushi,


"Mu shiga daga ciki,Kun kwaso gajiya,"abba ne yayi maganar tare da ruƙo hannun Ammi,Suka nufi cikin Falon,

  "sassannunku da zuwa,Ya hanya Ya gajiyar tafiya,Ya kuka baro su"?acewar abusufyan

Hajiya azeema tace"Lafiyalou,duk suna gaisheku,"

Bayan ta ƙare maganar,Mg osman ya soma magana"ashe irfan Lokaci yayi,Allah yaji ƙanshi,Ya gafarta mashi zunubbanshi,Wlh naji mutuwarshi"yakai ƙarshen maganar tare da curo hanky daga aljihunshi Ya rufe fuskarshi,jikin kowa dake a wurin yayi sanyi,

  Talal tuni ya fara zubda kwalla"Abba ashe haka abu ya faru?munyi babban rashin na irfan acikinmu,Allah yasa ƙarshen wahalarshi kenan,Allah Yaji ƙanshi,"

"Ameen ameen,"daƙyar abba yake amsa masu saboda yanayin da suka jefa shi,Dama dauriya ce kawai yake yi,

  "Yaya hossein,Ya haƙurin rashin da mu kayi"?hajiya azeema ce tayi maganar yayin da take kallonshi,daƙyar ya iya amsa mata,Kowa dake a wurin sai da yayi masu gaisuwa,Hatta Ƴan matan da Ammi tazo dasu,

Shigowa palourn Abu tayi hannunta ruƙe da faffaɗan tray,Cups ne asama mai ɗauke da Lemu mai sanyi,sai da ta fara yi masu sannu da zuwa,kafin ta soma ƙoƙarin raba masu abunshan,.  

  Gyaran Murya abusufyan yayi mata,Da sauri takai idanuwanta kanshi,da ido yayi mata nuni da Ammi alamar ta fara miƙa mata,Murmushi tasaki kafin ta nufi sofa ɗin da ammi ke zaune tare da Abba,cikin girmamawa ta gaishe da ita"Sannunku da zuwa Ammi,Ya gajiyar tafiya,"

"Alhamdullillah,"tayi maganar tare da miƙa hannu ta kar6i cup din da abu ke miƙa mata,

  "Ince ko Mahaifiyar ƴan ukun nan ce"?tayi tambayar tana nuna su jahad dake zaune wurin gwaggon katsina,

  Abba ne ya bata amsa da cewa"Itace oummansu"

Murmushi ammi tayi tare da kallon abusufyan,A hanzarce ya kawar da kanshi gefe yana murmushi ƙasa ƙasa,

"Alhamdulillah Naji daɗi sosai,mun samu ƙaruwa acikin zuri'armu Allah ya ƙara hada kawunanmu,"atare suka amsa mata da ameen 

Kasa haƙuri Talal Yayi"Abba Ya jikin junaid da fawan?na kasa samun natsuwa,Burina in sanyasu acikin idanuwana na,"

  Tunkan yakai ƙarshen maganar Gwaggwon katsina tace"Allah sarki junaidu bawan Allah,An ji jaki,Amma Allah wadaran me hali irin na Azmee,Matar nan ta cuce mu,Munafuka mai zuciya irinta Kafiran farko,Yadda kasan A jahiliya period aka haife ta dama ni banyarda da ita ba,Shisshiginta yayi yawa,Sumumu kasau macijin sari ka noƙe.....Wannan matar tafi bomb bala'e,Wlh bazamu yafe mata ba,Allah ya ɗebe mata sauran albarkar dake......"bata ƙarasa maganarba,Abbba yayi hanzarin cewa"Gwaggo,Dan Allah adaina tuna abunda ya wuce,Azmee yanzu bata atare damu,Tana can prison tana kar6ar sakamakon abunda ta aikata,

  Tunkan yakai ƙarshen maganar tace"Haba hossein,Ai ni banso kuka kaita prison ba,So nayi ku kulleta acikin akurki irin na kaji har mu dawo,Wlh data yaba ma aya zaƙinta,Azmee bata kyauta mana ba,Kaga fa matar nan kamar tafi kowa tsoron Allah,Kullum Zaka ganta cikin zumbulelen hijabi kamar matar liman,Hannunta ruƙe da zungureran cazbi kamar duka kenan"cika da takaici tayi maganar,.  

  "Wlh ni dama banyarda da ita ba,shiyasa tun farko banso Yaya hossein Ya bata rainon junaid ba,ƙaddara ce kawai ta riga fata,babu yarda zamuyi,Allah Ya kyauta gaba,Yanzu sai musan dawa zamu yarda,"Azeema ce tayi maganar ranta a 6ace,

  "Ae azmee ta bamu mamaki,Ta koya mana hankali wlh,ɗan adam ba abun yarda bane,Mutun mugun icce ne,duk irin halarcin da akayi mata tarasa dame zata saka magana sai da wannan,"acewar abba,

  Gyaran Murya ammi tayi kafin ta soma magana a tsanake,

  "Kuskure ne tun farko an riga da an tabka,sai dai fatan Allah ya tsare gaba,bai kamata kuna tada maganartaba,tunda yanzu babu ita,amma duk da haka ina me ƙara jan hankalinku Akan ku daina saurin yarda da mutane,musamman bare a zamanin da muke ciki Na jikinka ma ana iya haɗa baki dashi a cutar dakai balle kuma wanda baku haɗa komai dashi ba,Iya cuta dai Azmee ta cutar damu,Amma mu gode ma Allah da bata kaiga yi mana illa ba,Don da taso da tuni ta jima da halaka wasu acikin gidan nan,Allah ne ya tsare mana ku,"bayan takai ƙarshen maganar,ta ɗan sauke ajiyar zuciya kafin taci gaba da cewa"Yanzu a wani Hali jikokina suke ciki?Fawan da junaid,Ya jikin nasu,"


"Alhamdulillah suna samun sauƙi sosai,Junaid yana kwance a bedroom ɗinta fawan kuma yana a dakinshi"miƙewa tayi tare da nufar ɗakin Talal ma Yabi bayanta,Gaba ɗayansu ma suka miƙe domin zuwa duba jikin nashi,Lokacin da suka shiga ɗakin,A zaune suka same shi,Ya sauko ƙafafunshi ƙasa,Da alama so yake yayi tafiya,jin an buɗe ƙopar ɗakin Yasa ya ɗago da manyan idanuwanshi yana kallonsu,

  Farin ciki ne Ya lullu6esu,Musamman Abba,jiki na rawa ya ƙarasa gefenshi ya zauna,rungumoshi yayi xuwa jikinshi,Yana shafa bayanshi,

"Alhamdulillah,Da alama Jikin nashi yayi sauƙi,ba kamar yarda aka bani labari ba,"acewar ammi fuskarta  ɗauke da murmushi,

  Zuƙunnawa Talal Yayi saitin fuskarshi"Junaid ɗan uwana,Ya jikin naka"?zuba mashi ido junaid yayi yana kallonshi batare da yace uffan ba,Yaƙi buɗe baki yayi magana,Sae dai kallonsu da yake yi ɗaya bayan ɗaya kamar baison su ba,

  "Allah yasa baiyi loosing memory ɗinshi ba,Naga ko magana ma ya gaza yi mana Sai dai yabi mu da ido,"acewar captain adam,

Osman yace"nima abunda nake tunani kenan,Junaid dana sani kullum fuskarshi ɗauke da murmushi kamar Gonar auduga"

  "Kada ku damu,Yanzu ya fara jin sauƙi,Nasan zuwa gobe zai warware in sha Allah,shikaɗai yasan me yake ji acikin zuciyarshi,"yayi maganar yayin da yake cigaba da shafa sumar kanshi,

  Kowa sai da yayi mashi yajiki,Kafin suka Yi mashi sallama suka koma Falon,basu jimawa da dawowa ba,Mommy ta fito hannunta ruƙe dana Fawan,Daga shi sai short ajikinshi,ba ƙaramin jiki yaji ba,Amma yanzu da sauƙi jikin nashi,

Tunkan su ƙaraso,Talal da najeeb suka miƙe,Da sauri suka ƙarasa Wurinshi,Suna yi mashi yaji,murmushi ya sakar masu"Alhamdulillah Am really glad to see you,nayi missing ɗinku sosai,"

  Rungumeshi su kayi,Kafin suka ruƙo hannunshi zuwa cikin falon,Saman Sofa suka zauna,Kowa ya soma Yi mashi Ya jiki,fuskarshi asake yake amsa masu,a tsaye mommy ta gaisa dasu,Kafin ta nufi kitchen donta shirya masu abunda zasu ci,Abu ta samu acikin kitchen ɗin tana shirya masu abinci,Taimaka mata tayi suka shirya abincin atare,



Abba kuwa still Yana a wurin babynsa ya ƙankameshi ajikinshi,ɗago da junaid yayi daga jikinshi,sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi

"Junaid Anya lafiya kuwa?Sai dai kabi kowa da ido kamar baka sanmu ba,dan Allah kayi mun magana,Kona ji sanyi acikin zuciyata,

Zuru yayi mashi sam yaƙi ya tanka mashi,Duk ya shiga damuwa,Jan kumatunshi yayi"Haba babyn abbansa,Ko murmushi ne to kayi mun,"

  Still bai tanka mashi ba,hakan ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba,

"Dan Allah junaid,ka kwantarmun da hankalina mana,duk na damu da rashinka,Nasan Nayi maka laifi amma dan Allah Kayi hakuri kaji My baby Boy,"hada ɗan murmushinshi yayi maganar,junaid kuwa sai binshi da ido yake yi,

  "Me kake son ci in kawo maka"?yayi tambayar yana shafa sumar kanshi,

Sai lokacin Junaid ya buɗe bakinshi,Yana nuna mashi teeth ɗinsa,Sunyi dauɗa sosai,

Murmushi Abba yayi"Saboda teeth ɗinka sunyi datti shine kaƙi yi mun magana,to menene aciki"sunnar da kansa ƙasa yayi,

  Ruko hannunshi Abba yayi tare da miƙar dashi tsaye,Toilet ya shiga dashi,A gaban sink suka tsaya,Brush ya ɗauko bayan ya matsa maclean asama,Yace"Ha bakinka inyi maka brush ɗin dakaina,"buɗe bakinshi yayi,Abba ya tura brush ɗin cikin mouth ɗinsa,a tsanake yake goge mashi hakoran,Yayin da idanuwansu ke kallon cikin na juna,

  Calmly Abba ya soma magana"Nasan sunyi hurting ɗinka sosai,But pls we should forget about the past,Komai ya wuce,babu wanda Allah baya jarabtarshi junaid,Ka gode ma Allah da basu yi maka illa sosai ba,Nasan ka shiga damuwa ne sosai saboda rashina dakuma ƴan uwanka,ka rayu atare da wasu mugaye marasa imani,Ka tsorata sosai,Shiyasa harka zauce,Amma Yanzu Alhamdullillah,Jiki yayi kyau,"ya ƙarasa maganar tare da kunna tap,zuƙunnowa junaid yayi,Abba ya tarfa hannunshi Ya ɗebo ruwan yana kuskure mashi bakinshi,Bayan ya kammala kuskure mashi bakin,Ya wanke mashi fuskarshi,Kamar wani ƙaramin yaro haka Yake treating dinsa,

   Hannunsu ruƙe dana juna suka fito daga cikin toilet ɗin,Zaunar dashi yayi gefen gadon,

  "Yanzu fadamun me kakeson Ci,"

Daƙyar ya iya cewa"Abbana,"

Murmushi abba ya saki tare dacewa"Na'am babyn abbansa,"murmushi gefen fuska junaid ya ɗan saki,

  "Repeat it pls,"

Sake ambaton sunanshi yayi kamar yarda ya buƙata"Abbana,"

  Hannu yasa tare da shafa gefen fuskarshi"Na'am sanyin idaniyata,tell me me zaka ci,in kawo maka,"

  Yana ƙoƙarin buɗe baki yayi magana Jahad ta turo ƙopar dakin,Sam batayi tsammanin Abba na aciki ba,da sauri ta juya zata koma,Abba yayi saurin dakatar da ita"Ina zuwa"?kunyace ta rufeta,Har takasa juyowa tayi magana,

    Murmushi abba ya saki tare da cewa"Yana jin yunwa ki kawo mashi abunda zaisa ma cikinsa,"

  "Toh abba,"ta amsa tare da buɗe ƙopar ta fuce,

  Mayar da idanuwanshi yayi kan fuskar junaid"Faɗamun har yanzu kana sonta insa a ɗaura maku aure,"

   Sunnar da kanshi ƙasa yayi batare daya tanka mashi ba,ya lura da canzawar da junaid yayi dama Ya mu'allim yace Ba lallai ne ya dawo yarda suka sonshi ba,tunda yanzu babu sihiri ajikinshi,Ya dawo Normal yadda Allah ya halicce shi,Wato Namijin gaske,

   Cike da zolaya abba yace"Oh ni junaid,Allah yasa ba irin rafayet bane,naga magana ma wuya take yi maka,Fuskarka kuma a ɗaure babu annuri,"

   Turo ƙopar jahad tayi hannunta ɗauke da tray ɗan madaidaci,Food stuffs ne ta dauko asaman shi,

  Mikewa Abba yayi"Yawwa My daughter,zoki zauna kusa dashi,ki taimaka mashi yaci abincin,Ni bari na koma wurinsu Ammi,"Ta amsa mashi da toh,Juyawa abba yayi yabar masu ɗakin,


  Tunda ta shigo junaid bai ɗago ya kalleta ba,tuni tasha jinin jikinta,Yadda kasan ba wannan junaid ɗin ba,mai yawan fara'a ga surutu kamar aku,


  Ajiye tray ɗin tayi saman table,ta janyoshi izuwa gabanshi,

  "Me zan zuba maka,"daƙyar ya iya buɗe bakinshi ya furta"Cornflakes nakeso,"

"Bari naje na haɗa maka,yanzu zan dawo,"cike da kulawa tayi maganar,A hanzarce ta fuce daga ɗakin,

  After some minutes,Ta dawo hannunta ɗauke da Cup ta sanya mashi spoon aciki,Gefenshi ta zauna tare da miƙa mashi cup ɗin,ganin yadda yatsun hannunshi ke kerma yasa tace"In baka abaki,"

  ɗaga mata kai yayi alamar Eh,ɗaukar cokalin tayi a tsanake ta soma ɗebo cornflakes ɗin tana tura mashi abaki yana sha,Natsuwa tayi tana kallon lips ɗinsa sunyi red sosai,yadda kasan na jinjiri,ba ƙaramin missing ɗinshi tayi ba,gashi yanzu ya sauya mata,ko son kallonta ma bayayi,balle aje ga magana,.  

   "Junaid"da wata irin kasalalliyar murya ta ambaci sunanshi,

  ɗago da idanuwanshi yayi akanta batare daya amsa mata ba,murmushi ta ɗan sakar mashi tare da cewa"Ashe da rabon zan sake sanyaka acikin idanuwana?nashiga tashin hankali sosai lokacin da motar nan ta danne motarka,duk a tunanina kana acikin motar,har zaucewa saida nayi,Allah ne yayi zan rayu a lokacin,mun shiga tashin hankali sosai,Nidasu Ya omar...."tunda ta fara zuba yake kallon bakinta,Labari ta soma bashi na abunda ya faru bayan mutuwarshi har zuwa bayyanarshi,hada ƴan hawayenta,

  "Da ace narasa ka a wannan lokacin bana tunanin zan iya son wani ɗa namiji,zan ƙare rayuwata ne batare dana auri kowa ba,"

  Sai da takai ƙarshen maganarta,Tukunna yace"WHO ARE YOU"?

Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu rass kakeji!Waro ido waje tayi a tsananin firgice take kallonshi,

  Hankalinta a matuƙar tashe tace"Junaid!Kana nufin baka sanni ba?i know u are just kidding me"

  "Pls who are you"?Ya kuma tambayarya again,

Abun yayi mugun ɗaure mata kai,

"Junaid nifa ce,Jahad ɗinka,Your juliet,"

  Girgiza kanshi yayi"Ni bansanki ba,Bansan wacece ke ba,kin zauna sai zuba kike yi mun kamar radio,"

Ya ƙarasa maganar tare da miƙewa Ya nufi cikin toilet ya shige,tare da jan kopar ya datse ta,


Fashewa tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,yana acikin toilet yana jiyo shessheƙar kukanta,A jikin ƙopar ya tsaya can kuma ya buɗe ƙopar yana leƙenta,daga zarar yaga tana ƙoƙarin juyowa sai ya garƙame ƙopar,in ta kawar dakai tana shessheƙar kuka sai ya buɗe yana cigaba da kallonta,miƙewa tayi da ƙyar ta buɗe ɗakin ta fuce,Ajiyar zuciya ya sauke tare da buɗe ƙopar ya fito,Saman gadon ya koma ya zauna,fuskarshi ɗauke da ƙayataccen murmushin side face,


Lokacin da jahad ta fito daga ɗakin Abban,A falo ta samu Ammi tare da matasan gidan dasu Abba da daddynsu,Sae nasiha take yi masu,tare da yi masu addu'a suna Amsa mata da Ameen,


Corridor ɗin ɗakinsu ta shige,a ƙopar ɗakin ta tsaya tare da sanya hannayenta biyu tana goge hawayenta,kafin ta tura ƙopar ɗakin ta shige daga ciki,a kwance ta samu hosana tana ta sharar bacci,Oummansu kuma tana a zaune gefen gadon hannunta ruƙe da qur'ani tana karantawa,jiki asanyaye Jahad ta ƙarasa saman gadon ta haye tare da rufe idanuwanta,Allah kaɗai yasan yarda take ji acikin zuciyarta,


*Boss Bature*


A 6angaren Sehrish kuwa,Yanzu sun koma kwana bedroom ɗin Azmee ita da Amrish,taso suyi magana da mommy azeema amma lokacin da taje ɗakin da ta sauke bacci ta samu tana yi,da alama ta gaji sosai,ba don taso ba,ta dawo ɗaki,Amrish ta samu a tsaye tana ta faman zarya ta kasa runtsawa,da alama tana zullumin wani abu,

  "Lafiyarki kuwa?Meyasa baki fita waje ba kun gaisa da ƴan uwanmu da suka dawo,"

  Fuskarta ɗauke da matsananciyar damu tace"Tsoron haɗuwa nake yi dasu,gani nake kamar in suka ganni zasu kore ni ne in suka ji ko ni wacece,"

  "Kina da matsala Amrish,nafa ce maki ki saki jikinki,Family ɗinmu ba kamar yarda kikayi tsammani bane,suna da mutunci sosai,kowa zai kar6eki hannu bibbiyu ne,"

  "Nidai kawai ina fargaba ne,"ta ƙarasa maganar tare da komawa gefen gadon ta zauna,

  Cigaba da magana tayi"Har yanzu ina jin raɗaɗin abunda dangina suka aikata,abun yana ƙonamun rai duk in na tuna,Ina jin kunya sosai,Yanzu bani da kowa,nikaɗai na rage acikinsu,Labarin rayuwata sam babu daɗin ji,Yanzu wata rana idan nayi aure na haihu ƴa'ƴana zasu tambayeni game da dangina me zance masu?Idan ma ban faɗa masu fa dole suji a wurin mutane,koda yake nasan ma babu wanda zai aure ni,bakowa ne zaiso ya haɗa zuri'a dani ba,saboda gudun kada ƴa'ƴanshi su taso gur6atattu....."daƙyar takai ƙarshen maganarta,hawaye sharkaf Akan fuskarta,

  Zama gefenta sehrish tayi tare da dafa kafadarta"in sha Allah hakan ma bazai ta6a faruwa ba Amrish!Ki manta da duk wani abu daya faru a rayuwarki,ki manta da wasu dangi dakike dasu,Family ɗina sun zama naki,Miji kuma in sha Allah kin samu,muda muke da Zaratan samari,Kika sani ko ɗaya daga cikinsu wani yayi Wuff dake..."duk da tasan ba abu bane maiyuyuwa ba sai da ta ɗanyi murmushi kalaman sehrish sun ɗan sanyaya mata zuciya,

  "Fadamun babu wanda ya kwanta maki rai acikinsu,Yanzun nan inje in sanarwa Abba,In aka tashi aurensu Ya omar a haɗa da naki"

  Murmushi amrish ta saki batare da tace komai ba 

  "Kinsan fa muna da gagarumin biki a cikin gidan nan,Abba yace kowa sai ya ɗaura mashi aure,Ran nan najisu suna tattaunawa da daddy,Kuma kinsan wani abun farin ciki,Yawancin matasan gidan nan duk basu kula ƴan mata,abba yace duk wanda bai da budurwa,Zai haɗashi da ɗaya daga cikin ƴa'ƴan abokanansa ne,ina saran kema Abba zai haɗaki da wani ne acikinsu,Ya kike gani idan Yaya yusif ya aure ki"?Tayi tambayar tana kallonta,Yau ta dage sai zuba takeyi mata,duk don saboda farin cikinta,

  Murmushi ta ɗan saki Still bata tanka mata ba,

  "Ko baki son shi"?

  Sai lokacin amrish ta tanka mata"idan ina sonshi,Shi yana sona ne?

  "Kuma fa haka ne,Ae ko bashi ba,akwai su Yaya fawan ga twins ga Yaya adam shima fa ya haɗu,"

  "Sehrish ni yanzu ba soyayya bace damuwata ba"tayi maganar a yayin da take gyara kwanciyarta saman gadon,

  "Are u missing someone"?

ɗaga mata gira tayi alamar eh,kafin tace"Bansan a wani hali ya haroon yake ciki ba,bawan Allah baida kowa mu kaɗai muke rage,Ni nasamu dangin da zan rayuwa cikinsu,Shi kuma fa?wazai kula da rayuwarshi?tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,

  Ita kanta Serish ta damu sosai akan Haroon,tun lokacin da suka ji cewa ba yin kanshi bane,

  Jinjina kai ta ɗanyi kafin tace"In sha Allah,zan yi iyakar bakin ƙoƙarina wurin ganin nayi magana da daddy akan su nemo shi,duk da ina fargabar in tunkareshi da maganar....."dakatawa ta ɗanyi da yin maganar,

  Kafin taci gaba da cewa"inaso na nemi alfarma a wurin Yaya rafayet,amma nasan daƙyar yayi mun"

  "Wata alfarma kenan"?Amrish tayi tambayar tana kallonta,

  "Hukuncin da aka yankewa Aunty azmee yayi tsauri sosai,a ɗakin duhu aka kaisu,zaiyi wuya suyi watanni idanuwansu basu raunata ba,sun ƙuntata sosai,zuciyarsu ma zata iya bugawa su mutu......"

  "Sehrish ashe baki da hankali?duk girman zunubin da suka aikata maku a haka har kike tunanin nema masu sassauci,Wlh karma ki fara,Ni hukuncin da akayi masu yayi mun kaɗan,So nayi da aka kaisu court nan take alƙali ya yanke masu hukuncin kisa ta hanyar rataya"rai a6ace take magana,Sehrish kuwa sakin baki tayi galala tana kallonta,Sai kace ba akan mahaifiyarta take magana ba,sai da takai ƙarshen maganarta sannan sehrish tace"Kece baki da hankali Amrish,Iyayenki fa nake nema ma sassauci,Bawai ina nufin su fito daga prison ba,Inaso ne a fito dasu daga wannan ɗakin duhun, sannan arage shekarun da aka sanya masu sunyi yawa,abunda nakeso ki gane shine,Basu kashe mana kowa ba,Zunubin da suka aikata tsakaninsu da Allah ne,Kuma Allah gafurin rahim ne"

  Wani irin kallo Amrish ke yi mata, a ƙarshe ma saita juya mata ƙeya,tasanya pillow ta tsoshe kunnuwanta,


  Dariya sehrish tayi tare da kai hannu ta dunguri kan Amrish"kar Allah yasa ki ji,"miƙewa tayi daga zaunan da take gefen gadon,ta nufi toilet ta shige,

  Shigarta keda wuya,Wayarta dake ajiye saman side drawer ta soma ringing,Amrish ce ta ɗauki wayar tare da duba mai kiran naga

  *My Boss Man*

 shine sunan da ta gani akan screen ɗin wayar,bata ɗaga kiran ba,harya katse,after one minute Text message ya shigo cikin wayar,Hannu tasa ta janyo message ɗin ya buɗe,ta soma karantawa,

  "Am on my way,"shine abunda ya rubuto mata,murmushi amrish tasaki,duk da batasan saƙon wanene ba,Amma tana da tabbacin cewa Yana da kusanci da sehrish sosai,"mayar da wayar tayi saman drawer ta ajiye,

"Ko meyasa take yawan yin wankan dare,Oho"tayi maganar tana murmushi,within mins bacci yayi awon gaba da ita,


Lokacin da Sehrish ta fito ɗaure da towel a ƙirjinta,wall clock ta fara kallo ƙarfe 12 na dare,Sgr ya sanar da ita cewa daga yau ya gama zuwa aiki,cos aikinshi Ya ƙare a nigeria,zuwa gobe za'a basu lambar yabo,Sannan za'a ƙara ma matasan gidan matsayi wurin aikinsu sakamon Namijin ƙoƙarin da sukayi wurin kawo ƙarshen miyagun da suka addabi ƙasar, 


Acikin month ɗin da muke ciki,Za'a ɗaura aurensu Omar kafin su wuce U.S,duk in ta tuna zai tafi wani iri take ji acikin zuciyarta,ba don taso ba,Amma taci alwashin bazata ta6a binshi U.S ba,kuma bazata ta6a neman ya tafi da ita ba,ko ta nemi soyayyarshi ba,ta lura ba sonta yake yi ba,yana yin amfani da itane don ya biya buƙatarshi kawai,in kuwa har hakane baisan darajarta ba,

  Jiki asanyaye ta zauna gaban mirror,tajima a haka kafin ta ɗauko handryer,Ta jonata ajikin socket,Nan take iska ta soma busowa buuuu da ƙarfin gaske,Busar da gashin kanta taci gaba da yi,Yanzu tsayin gashinta ya dawo fiye dana da,har waist ɗinta,Ga cikowar da yayi,daga gaban goshinta kuwa wani kwantaccen gashi ne wanda ya ƙarama fuskarta kyau,bayan ta kammala busar da gashin nata,ta shafe ko'ina na jikinta da waɗannan mayukan da aunty Azeema ta bata,Bayan ta kammala,Light make up tayi akan fuskarta,powder tasha fa,ta murza man baki,har wani ƙyalli lips ɗinta keyi,

  Miƙewa tayi daga gaban mirror ɗin ta koma wurin wadrobe ɗinsu,wata matsiyaciyar baby doll ta ɗauko,Shara shara wadda da ita da babu duk ɗaya ne,net ne kawai ajikin rigar,black color kana hangen komai muraran A bayyane,Iya guiwa rigar ta tsaya mata,komawa tayi gaban mirror ta ɗauki turarurrukan nan da hajiya azeema ta bata,tabi ko'ina ta feshe wani irin shu'umin ƙamshine ke fita daga jikinta,hatta Amrish dake bacci sai da turaren nan yakai mata karo,


Ribbom ta ɗauko,nan fa ta soma kiciniyar ɗaure sumar kanta,yayi yawa sosai gashin,sai tasha wahalar tattare sumar zata ɗaure,gashin Ya kubce mata,tuni ta fara haɗa gumi,tana cikin yin damben ɗaure gashin kanta,Tajiyo sautin shigowar motocinsu,


A jere suka shararo da gudu izuwa cikin gidan,Bayan sunyi parking ɗin Motocin Amstrong Ya buɗe murfin motar,Tare da zagayawa ya buɗe mashi,saukowa yayi daga cikin motar,Jikinshi na sanye da Army trouser,Light green Shirt,ta ɗame jikinshi sosai,Sumar kanshi kuwa ya ɗaureta a bayanshi,

  Fitowa Major yayi,Ya buɗe wa Marshal Motar ya fito,kaya kala ɗayane ajikinsu,

  "Sir,muna ƙara tayaku murna akan nasarorin da kuka samu,"Mojar ne yayi maganar,

  "Duk wata nasara da muka samu,Da taimakon Allah da kuma taimakonku,muna Alfahari daku,Kuma in sha Allah,Da zarar mun koma U.S Za'a ƙarama kowannanku Matsayi,then there's special gift da muka shirya maku,Bazata kawai zamuyi maku,"Omar ne yayi maganar fuskarshi ɗauke da murmushi,

  "Sir,Ni banason a ƙara mun matsayin aikina,Saboda banason na daina aiki a ƙarƙashinka,Na saba dakai sosai,kyautatawar da kake yi min yasa bana son rabuwa dakai,nafiso koda yaushe na kasance a ƙarƙashinka,"major nakai ƙarshen maganarshi,Amstrong ya ɗaura da cewa"Nikaina Sir banason muƙamin da za'a bani,indai zaisa nadaina aiki a ƙarƙashi Sgr ne"

ɗagowa Sgr yayi tare da kallonshi Ya ɗan jefe mashi harara,Dama Yaji ma yana son a ƙara mashi matsayi amma ya kafe akan shi bazai daina driving ɗinshi ba,Sun shaƙu sosai,tun suna 20years  a duniya Allah ya haɗa jininsu,Hasalima Laifi Amstrong yayi aka kamashi da nufin a hukunta,Sgr shine yasa aka sake shi,Sannan yasa Shi yi mashi alƙawarin bazai Ƙara aikata laifin ba,tundaga wannan lokacin Yayi ma Uncle Donald magana aka sama mashi Aiki ya fara kar6ar training,gashi yanzu ya mai dashi mutun,Babu abunda amstrong bai mallaka ba,Aure ne kawai baiyi ba,Shima ɗin saboda Sgr baiyi ba,Dashi Yake koyi Hatta gyaran gashin Sgr irinshi ne akan Amstrong,kamar yarda Amstrong yake da Sgr haka Major Yake da Omar,Abokan Juna ne na kut da kut,

  "Whether u like it or not,dole ku kar6i muƙamin da za'a baku,"ya ƙarasa kamar tare da ruƙo hannun Omar suka wuce cikin gidan,



Lokacin da suka shiga main palour babu kowa,Da alama mutanan gidan duk sunyi bacci,Hannunsu ruƙe dana juna suka haura upstairs daga bisani kowa Ya nufi part ɗinsa bayan sunyi sallama da juna,"


Agajiye ya faɗa bedroom ɗinshi,Ko'ina an gyara shi tsaf Sae ma wani daddaɗan ƙamshi dake tashi,tsaftar sehrish ba ƙaramin burgeshi take yi ba,Yana son mutun me tsafta da son ƙamshi,kasancewar shi ma'abocin Son ƙamshine shiyasa koda Yaushe zaka ji daddaɗan ƙamshi ajikinshi,


Ko takalman ƙafarshi bai kaiga cirewa ba,Ya faɗa saman gadon saboda wani irin bacci dake fisgarshi,adai dai wannan Lokacin Sehrish ta shigo palourn jikinta sanye da dogon hijabi mai hannu,Ta ruƙo tray,a ƙopar bedroom ɗinshi ta tsaya tare da yi mashi sallama,shiru bai amsa mata ba,


Sai da ta shiga cikin  bedroom ɗin tayi arba dashi baje saman gadon yana ta sharar bacci abunsa,cikin sanɗa ta ƙarasa gaban table ta sauke trayn hannunta,lalla6awa tayi zuwa saman gadon ta haye,Cire hijabin jikinta tayi tare da ajiye shi gefe ɗaya,ƙafarshi ta ruƙo ta soma kwance igiyoyin takalminshi,ƙasa ta ajiye shi kafin ta cire na ɗayan ƙafar shima ta sauke shi ƙasa,duk yana jin motsinta ƙasa ƙasa dayake baccin nashi baiyi nisa ba,Moving tayi zuwa saitin fuskarshi,Kwanciyar rubda ciki yayi ya danne hannunsa ɗaya,sehrish da karanbani sai ta fara ƙoƙarin curo hannunshi daya danne,da ƙarfi ta ruko hannun tana janyoshi shi,wani irin gumi ta haɗa kamar ba'a kunna A.c a ɗakin ba,daƙyar ta samu ta curo hannun aikuwa tana zare shi gaba ɗaya Sgr ya gangara zai faɗa ƙasan gadon,A gigice tabishi ta ruƙoshi sosai tana ƙoƙarin karkato dashi donya dawo daidai,Aikuwa gaba ɗaya ƙarfinshi ya rinjayeta,ɗungurugum daga ita harshi  suka ƙundumo ƙasa,ji kake timmmmmmmm,


Saboda buguwar da kanshi yayi har sai da ya furta"Assh,"a ruɗe sehrish ta ɗago da kanta tana kallon fuskarshi gaba ɗaya tana asaman jikinshi,Sai faman zazzare idanuwanta takeyi,cike da fargabar abunda zai biyo baya,almost 3 mins kafin ya soma ƙoƙarin buɗe blue eyes ɗinshi masu ɗauke da bacci har launinsu ya canza,biji biji ya fara ganin kafin su washe a kan fuskarsa,abun ya ɗaure mashi kai,ganin ya soma motsa lips ɗinsa alamar zaiyi magana,Saboda tsabar ruɗu batasan lokacin data sanya tafin hannunta asaman la66ansa ba,ta toshe mashi bakin don kar yayi mata faɗa,hakan da tayi ba ƙaramin mamaki ya bashi ba,ƙarfin hali,Tayi silar jefoshi ƙasa kanshi ya bugu sosai,Yanzu kuma ta hana shi yin magana don kar yayi mata faɗa,hada wani zare mashi ido duk don karya ce zai hukuntata,


Daddaɗan ƙamshin turarenta ne ya fara kai mashi karo,har wani shaƙewa yayi,Calmly yake bin kyakkyawar fuskarta da kallo,Man lips ɗin data shafa ba ƙaramin kyau yayi mashi ba,lumshe idanuwanshi ya ɗanyi slowly ya kuma buɗesu asaman wuyanta har izuwa ƙirjinta dake cike tab ga twins ɗin nan nata masu fusgarshi kaitsaye,sai lokacin ya lura da babydoll ɗin dake jikinta shara shara,hatta pant ɗinta yana kallonshi ta ciki,Ya jima yana bin surar jikinta da kallo kafin ya mayar da eyes ɗinshi kan Boobs ɗinta cos he needs it more than everything now,still bata buɗe mashi small mouth ɗinsa ba,Shi kuma ya kasa janyen hannunta daga saman bakinsa,Ƙamshin turarenta ya gama jefa cikin wani irin yanayi mara misaltuwa,kasala duk ta rufe shi,

 Jikinta sae kerma yake yi,tuni zufa ta wanke mata fuskarta,duk don saboda tsoron hukuncin da zaiyi mata, 


Muryarta na kerma ta soma magana"Am sorry ya Rafayet,wlh kuskure ne,ba da son raina ba,Nayi ƙoƙarin na gyara maka kwanciyarka ne,naga kayi rubda ciki,also ka danne hannunka zai iya hurting dinka shine nayi ƙoƙarin in cire hannun bansan ya akai ba,sai dai kawai naganmu mun faɗo ƙasa........"daƙyar ta ƙarasa maganar,ganin irin kallon da yake yi mata,tsit tayi tana faman mazurai,


Unexpected taji saukar hannayenshi asaman bayanta,ƙafafuwanshi ya aza asaman nata,ya danne su sosai,ta yarda bazata iya tsere mashi ba,a hankali  ya soma zare ribbom ɗin data ɗaure gashin kanta dashi,dama daƙyar ta samu ta ɗaureshi,Warware shi yayi nan take gashin ya tarwatse gaba ɗaya ya rufe fuskokinsu su,yayi mashi rumfa,wani irin ƙamshi ke fita daga jikin gashin mai daɗin gaske,sosai ya shiga shaƙar ƙamshin gashinta har wani lumshe idanuwanshi yake yi kamar mai jin bacci,Sehrish kuwa har lokacin taƙi janye tafin hannunta daga saman bakinsa,sucking ɗin fatar tafin hannun nata ya soma yi,tana jin motsin tongue dinsa,ba ƙaramar kasala ya jefata ba,


"Ya rafayet"ta ambaci sunanshi cikin sanyayyiyar muryarta,

  "Ka yafe mun?"sam ta manta cewa ta rufe mashi bakinshi babu halin ya bata amsa,shi kaɗai yasan yarda yake jinta acikin zuciyarshi,tana yunƙurin buɗe baki ta ƙara magana,Ba zato ba tsammani taji shigar hannunshi cikin pant ɗinta,a gigice ta saki bakinshi tana ƙoƙarin guduwa,tighting ɗinta yayi sosai ta hanyar danneta da yayi da ƙafafunshi tamkar ya ɗaureta da igiya,damƙo neck ɗinta yayi azafafe ya haɗa bakinsu wuri guda tamkar zai cinye mata lips ɗinta,Hot kissing ya shiga bata a haukace,duk tabi ta ruɗe,har time ɗin bai daina wasa da hannunshi cikin pant ɗinta ba,ƙoƙarin zaucewa takeyi ,da iya ƙarfinshi na ƙarshen ya ɗago da ita,gaba ɗaya ya dauketa izuwa saman katafaren gadonshi ya kwantar da ita,blacket ɗinsa ya janyo ya rufe su aciki,baka iya jin sauti komai sai sautin gurnanin da yake yi,kura ta samu nama,almost 30 mins kafin ya rabu da ita,ba don yaso ba,wani irin bacci ne ya ɗaukesu,rungume da juna,a ƙankame kamar wani yace zai rabasu,


Wuraren sallar asuba,ya farka daga bacci,tunkafin ya buɗe idanuwashi ya soma shafa gefenshi don yaji in tana a kusa dashi,bai sameta ba,sai dai pillow ya damƙo,kasala duk ta baibayeshi daƙyar ya iya miƙewa zaune,daga shi sae short ajikinshi,wurga eye balls ɗinshi yayi kan trouser ɗinshi daya cire saman gadon tare da Shirt dinsa

Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da zuro kafafunshi ƙasa,wata irin yunwace yake ji,kayan abincin data kawo mashi jiya duk sunyi sanyi,An sha romance an manta da ciki,

  Saukowa yayi daga saman gadon Ya faɗa toilet,Yaja kopa ya rufe,


After some minutes Ya fito jikinshi sanye da rigar wanka"bathrobe"hannunshi ruƙe da short towel yana tsane sumar kanshi,agaban mirror Ya tsaya yana gyara jikinshi,


Yana ƙoƙarin miƙa hannu ya ɗauki kwalbar turarensa,Unexpected Idanuwanshi suka sauka kan Farar paper ɗin dake ajiye gaban mirror ɗin tare da Biro,har sai da gabanshi ya faɗi duk da bai fahimci abunda suke nufi ba,Amma yana ji aranshi cewa Babu alkhairi a tattare da farar takardar daya gani,Slowly ya ɗaura yatsun hannunshi saman paper ɗin yana shafata,Yayin da yake ƙoƙarin yin nazari akan abunda Paper da biro ɗin ke nufi,


"Naga kana kallonta,Babu rubutu ajikinta,its just a paper amma kaine zaka yi rubutu akanta,divorce paper ce,Ta sehrish nakeso ka rubuta mata,"

  Gabanshi ne yayi wani irin mugun bugu,Ji kake rasss!A firgice ya juyo don yaga me wanene ke magana duk da ya shaida muryarshi,Uncle abusufyan ne,Tsaye abakin ƙopar ɗakin fuskarshi a ɗaure,Ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi,tashin sense,

Zuba mashi ido sgr yayi yana kallonshi batare daya ce komai ba,

  "Saboda halin da muka shiga,Yasa ban tanka maka ba,Amma yau Almost 5 months kenan da yin Auranka da Sehrish,Naji kana ta shirye shiryen komawa U.S,amma banji kana maganar zaka bata takardar sakinta ba,May be ka manta ne,So lemme remind u,Contract marriage ne a tsakaninku,munyi yarjeniya dakai akan zatayi maka aiki for 3 months before ka koma U.S,yanzu time yayi da zaka sake ta,tunda an samu kwanciyar hankali,Gashi kuma zaka koma ƙasarku,"

Tashin hankalin da ba'a samashi date,Wani irin kallo Sgr ke bin Uncle abusufyan dashi,

  

*An yanka ta tashi*



*ga masu buƙatar karanta littafin Abban sojoji from book one zuwa 3,Suyi mun magana kaitaye ta whatsapp 08103884440*

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*


*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*









Tashin hankalin da ba'a sa mashi date,Wani irin kallo Sgr ke bin Uncle abusufyan dashi,just speechless,Ya ƙame a tsaye ya kasa motsa lips ɗinsa,Sam ya manta da wata yarjejeniyar aure a tsakaninsu,kamar a mafarki haka yake ganin abun,

  "Rafayet!"ya ambaci sunanshi don ya lura hankalinshi baya atare dashi,firgigit Sgr yayi yana kallonshi Still bai tanka mashi ba,

  "Am talking to u!nasan kaji duk abunda nace,we don't ave time to waste,just to make it easy for you that's why na kawo maka Paper da biro,rubutu kawai ya rage maka,nasan within minutes zaka rubuta very simple"

  Gauran numfashi yaja da ƙarfi tare da runtse idanuwanshi,Da yake ba kunya ce ta ishe shi ba,Da buɗar bakinsa sai cewa yayi"Uncle,I changed my mind,I have already canceled the marriage contract,now I decided to go with her,"

  Zuba mashi ido abusufyan yayi,cike da Tsantsar mamaki Yake kallonshi,

  "Zan tafi da ita U.s taci gaba da yi mun aiki,"

  Harara abusufyan ya wurga mashi kafin yace"aiki fa kace?me ka ɗauke ta?idan ka manta bari na tuna maka!Sehrish ƴar cikina ce,your uncle's daughter ba house maid ba,Ni ban haifi ƴar aiki ba,"datakawa abusufyan ya ɗanyi da yin maganar yana fitar da huci,Yaji haushin maganar Sgr,Har yanzu bai daddara ba,Wato Still ƴar aiki ya ɗauketa,bai chanza ba yana nan kan bakanshi kenan,Yafi ƙarfin ya bata matsayin mata a wurinshi,daƙyar ya iya controlling  temper ɗinsa Ya ci gaba da magana"Amma rafayet baka da kunya!Har ni zaka kalli tsabar idona kace wai zaka tafi da ƴata U.s,kawai don taci gaba da yi maka aiki!ita Baiwarka ce?so kake ka ƙasƙantarmun da ƴata ne,Duk fa wani abu da kake taƙama dashi,Nima Allah ya hore mun koda bankaika ba,Also she's ur bloodline'yana kai ƙarshen maganar,Rai a6ace Sgr ya juya tare da kai hannu ya damƙi paper ɗin da Abusufyan ya kawo mashi,Yayi tearing ɗinta,into pieces,don ma yasan ba wai zai rubuta abinda akeso ya rubuta bane,


Abun yayi mugun ɗaure ma Uncle abusufyan kai,Shi komai sai ya nuna ƙarfin iko,Ya fi ƙarfin ya miƙa wuya ya roka abashi abunda yake so ta lalama ba,jinjina kai yayi tare da cewa"Ka yage takardar ko?Ko ka manta da agreement paper ɗin dake a wurina da kuma wurin Abbanku!?

  Gabansa ne yayi wani irin bugu mai sauti ji kake daram!!

  "Kuma akwai signature ɗinka jikin takardar,"

  Wata irin zufa ce ta soma tsatstsafo mashi,Sae kace ba yanzu ya fito daga wanka ba,

  Murmushin takaici abusfyan ya ɗanyi kafin yace"As from today!Sehrish bazata ƙara zuwa part ɗinka da sunan aiki ba,Also....."dakatawa ya ɗanyi da yin maganar yana duba wrist watch ɗin hannunsa,Lokaci yake kallo,

  "Before 24 hours,Ina jiran Takardar sakinta,Idan kaƙi kuma hmmm kasan me zai biyo baya,"yana kai ƙarshen maganarshi,Yayi ƙwafa tare da juyawa ya fuce daga ɗakin nashi,

  Wani irin jiri ne ya soma ɗibarshi,Ba arziƙi ya koma gefen gadonshi ya zauna tare da kifa kanshi saman guiwowinshi,

  "Innalallahi wa'inna Ilaihi raji'un"

  Wannan shine abunda yake ambato acikin Zuciyarshi,hankalinshi yayi mugun tashi,Taya zai Iya rayuwa batare da ita ba?Ta saba mashi da kanta,ta yadda bazai iya rayuwa batare da ita ba,bakomai yake tunawa ba face Romance ɗin da suka sha jiya,Yau rana ɗaya kawai ace za'a rabashi da ita,tabɗijan An taro match kuwa,Allah yasa sun tanadi filin bugata,


Kusan sau uku Marshal Omar yana kwaɗa  sallama amma shiru bai amsa mashi ba,sam hankalinshi baya atare dashi,

  "Rafayet"Ya ambaci sunanshi Yana shigowa cikin ɗakin,Firgit yayi tare da ɗago blue eyes ɗinsa,tamkar na wanda yasha Giya,fuskarshi tayi sharkaf da zufa,

  Zama gefenshi Omar yayi"bro lafiyarka kuwa?Zaman me kake yi,Muna ta jiranka,Time ɗin sallah yayi fa"

  Daƙyar ya iya buɗe baki yace"Omar,lokacin da zaka shigo kaga Uncle"?

  Jinjina kai omar yayi alamar eh,

"Ashe ba mafarki bane"Ya ambaci hakan acikin zuciyarshi,

  "What's wrong with u?ko wani abu ya shiga tsakaninka dashi ne"?

  girgiza kai yayi"bakomai,bari na shirya mu tafi,"yunƙurawa yayi tare da miƙewa tsaye,Daƙyar yake jan ƙafarshi,Direct ya nufi Closet ɗinshi,after some minute Ya dawo jikinshi sanye da Jallabiya,Omar ya tadda a tsaye hannunshi ruƙe da paper ɗin daya keta,Kallonshi yayi"Wannan fa?naga an yayyagata"

  Yatsina fuska yayi tare da cewa"Bakomai,mu tafi,"a jere suka fita,Shiru kawai Omar yayi amma tabbas yana ji aranshi cewa wani abu ya faru dashi,Jikinshi duk yayi sanyi,downstairs suka sauko anan suka haɗu da sauran matasan gidan suka ɗunguma izuwa masallaci,


A 6angaren Sehrish kuwa,Tunda ta gudo daga part ɗinsa,Bedroom ɗin Aunty azmee ta wuce,tana shiga ta samu amrish a tsaye saman darduma ta kabbara sallah,lalla6awa tayi cikin sanɗa ta shige toilet,don ta tsarkake jikinta,ta fito ɗaure da towel ta nufi wadrobe,Da yake duk ta kwaso kayanta,Doguwar riga ta zura ajikinta orange colour,mara nauyi ƴar ta shan iska,saman dardumar ta hau,A gefen Amrish ta kabbara sallah,bayan sun kammala Sallar,ko addu'a bata samu tayi ba,Saboda yanayin da take ciki,kasala duk ta baibayeta,Saman gadonsu ta koma ta haye,ta janyo bargo ta lullu6e har kanta,duk amrish na kallonta,ta fara sanya mata ido,in dare yayi  ta ɗau wanka,ta fuce daga ɗakin,tsakar dare ta dawo ko wurin asuba,Ta shiga toilet,Wani irin bacci ne ya ɗauketa mai daɗin gaske,hada minshari,


Bayan Amrish ta kammala Yin addu'ar da take yi,Komawa tayi gefen sehrish ta kwanta tana fuskantar ceilling,da alama tayi zurfin cikin tunani,


Tun wuraren ƙarfe 7 na safe,Mommy tare da Oumma suka shiga kitchen domin shirya breakfast ɗin gidan,basu jima da fara ƴan soye soye ba,Saude ta shigo kitchen ɗin tare da hajiya azeema,domin su tayasu aiki,hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba,Suna aiki suna fira,

  "Naji kuna ta fira banji kuna zancen gagarumin bikin da muke dashi ba,"Hajiya azeema ce tayi maganar,. 

mommy tace "Wai har mutun nawa za'a ɗaura ma aure ne?donni abbansu bai sanar dani ba,Amma yace mun in shirya tarbar surukai na,"

  Aunty azeema tace"Ni kaina bansan mutun nawa za'a shafa fatihar tasu ba,Amma ina da tabbacin cewa hada abusufyan acikinsu,"da gangan tayi maganar,cike da zolaya tana satar kallon Abu,

Wata irin kunyace ta rufe ta,har ta kasa tanka mata,

  "Ga kuma saude,Amaryar harrisun gwaggo,Kai gaskiya masha Allah zamu sha bikin da ba'a ta6a yin irinshi ba"abunka ga fulani ga kunya,da gudu saude ta fuce daga kitchen ɗin,

  Gaba ɗaya suka fashe da dariya,

"Tunda saude ta gudu bari in dawo kan Zainabu abu,tauraruwar dake haskaka zuciyar abusufyan,Gaskiya abu ki gode ma Allah,Abusfyan ba ƙaramin Sonki yake yi ba,Ae dole ma yaso ki,Tashin farko kika haifa mashi triplet kyawawan gaske," 

Murmushi kawai abu ke saki,da alama taji daɗin maganar Aunty azeema,

   Mayar da idanuwanta tayi kan mommy,

  "Auntynmu,Kinsan nifa bana 6oye 6oye,nasan su Ya hossein basu sanar dake ba,"

  Fuskar mommy ɗauke da murmushi tae"mekenan?

  "Nima fa bani da tabbaci nadaiji ƙishin ƙishin wai cikin ƴan ukunta za'a haɗa aurensu da biyu daga cikin zaratan samarin wurinki,Amma fa bansan wanne daga cikinsu ba,"da biyu Azeema tayi maganar don taga reaction ɗinta,

Shiru Alex ta ɗanyi jimmm batare da tace komai ba,har na tsawon mintuna,azeema ta kafe ta da ido,don tasan halinta,a lokacin baya tasha faɗin cewa Ƴa'ƴanta bazasu auri baƙar fata ba,ita kanta abu ta lura da sauyawar da tayi tunda akayi mata maganar,

  Lokaci guda,murmushi ya bayyana akan fuskarta,a tsanake ta soma magana"Zanfi kowa farin ciki,idan Zainab da abusufyan suka zama surukaina,Saboda na yaba da irin tarbiyar ƴa'ƴansu,suna da hankali sosai,ga girmama na gaba dasu,"

  Wani irin farin ciki ne ya lullu6e Aunty azeema,dama ita fargabarta karta basu matsala,

Abu kuwa taji daɗi sosai da irin yabon da Mommy tayi ma ƴa'ƴanta,

  Cigaba da magana mommy tayi"Dama fa junaid ya sanar dani tun kwanakin baya,duk da na ɗanji nauyi wlh,Ya nuna yana son aure,mukuma a ƙa'ida Yaro kamar junaid ko soyayya bai isa ya fara ba,nayi tsammanin sai ya kai shekera Talatin koda biyar haka kafin ya fara zancen aure,Amma sai gashi tun yana 19 years aure yake so......"da sauri aunty azeema tace"Wannan ae ba wani abu bane,Ya hossein fa,tun yana 20years yayi aurenshi na farko,duk dashi A lokacin ya mallaki komai na rayuwa,Shi kuma junaid sakamakon tauye mashi haƙkinshi da Azeemi tayi,baisamu damar yin karatu ba,Balle aje ga maganar aiki,Amma bai kamata mu damu akan wannan ba,Still junaid yana da sauran damar da zai gyara rayuwarshi,zai cigaba da zuwa makaranta,Sannan za'a sama mashi aikin yi,tunda alhmdllh Allah ya hore mana,"

  Murmushi mommy ta saki,Taji daɗin maganar azeema sosai,daga haka suka cigaba da yin firarsu suna aiki,cikin lokaci ƙanƙani suka kammala Girke girken nasu,a lokacin saude ta dawo kitchen ɗin,Atare da Oumma suka soma ɗaukar food stuffs ɗin suna kaiwa saman d-table,


Bayan sun kammala jerawa,Saude tabi ɗakunansu tana tashinsu,Don su hallara a fara ɗa'amin,


Turo ƙopar ɗakin ammi tayi,Zaune tasame ta gefen gadon hannunta ruke da ƙur'ani tana karanta,Idanuwanta na sanye da glass fari,

  Zuƙunnawa tayi cike da girmamawa ta gaishe da ita"Ammi ina kwana,kun tashi lafiya,Ya gajiyar tafiya,"

Murmushi ammi ta sakar mata"Lafiya lou,Gajiya tabi jiki,"

  Saude tace"An kammala shirya breakfast Anan zan kawo maki,".

  "A'a,nafison nafito naci atare da jikokina,"murmushi saude ta saki kafin ta miƙe tare da juyawa zata bar ɗakin,.  

  "Ji mana,"ammi ce ta katse mata hanzarinta,"juyowa tayi tana kallonta,.  .  

  "Amm..ince ko kinyi ma su Nafisa da khadija magana"?tana magana akan ƴan matan da suka zo dasu jiya

  "Ae daga ɗakinsu nake,Na same su suna shiryawa,"

  Jinjina kai tayi"Masha Allah,zaki iya tafiya,"

  Buɗe kopar tayi ta fuce izuwa ɗaki na gaba,


Jahad na kwance,since yesterday night bata runtsa ba,tashiga damuwa sosai akan junaid,hankalinta yaƙi kwanciya,tunda ya nuna baisanta ba,duk ta rasa natsuwarta,ita kaɗai Ce kwance saman gadon,Hosana na acikin toilet,


Kwankwasa ƙopar ɗakin akayi,Muryarta adisashe tace"Wanene"?

  Muryar Hafsat ta juyo daga waje,

  "Nice,"

saukowa tayi daga saman gadon taƙarasa tare da buɗe mata ƙopar,

  "Aunty hafsat"Tsaye take jikinta sanye da riga da wando,ta yafa mayafi akanta,

  "Jahad ce ko sehrish,"tayi tambayar ne don bata ganeta ba,

  "Jahad ce,Kin tashi lafiya?Ya gajiyar tafiya"?

  "Lafiyalou Alhamdullih"ta amsa mata tare da shugowa daga cikin ɗakin,

Gefen gadonsu ta zauna,kafin tace"Jahad inason magana dake,"jin haka yasa jahad ta koma gefenta ta zauna,ina sauraronki Aunty hafsat,

  Calmy ta soma magana"Game da abunda Mommyna tayi maku,Ina nema mata yafiya a wurinku,dan Nasan haƙƙinku ne ke bibiyarta,Jahad tana cikin mawuyacin hali,Yanzu haka maganar da nake yi maki,ƙafarta ta ru6e ta lalace,A sakamakon wani mai mota daya bugeta A enugu,Ni bansan ma meya kaita can ba"idanuwanta cike tab da kwalla tayi maganar,

  Hankali tashe jahad Tasoma ambaton'Innalallahi wa'inna ilaihirra'jin!"

  "Wlh jahad,ta zama abun tausayi,A gefen bishiya take kwana,dare da rana tana zaune a wurin,Kona abinci bata dashi sai in ansamu na Allah ya bata sadaqa,tukunna take samun abunda zata sama cikinta,"

  Jahad sarkin tausayi tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,


Hosana dake a la6e cikin toilet tana sauraronsu,Sai 6a66aka dariya takeyi hada dafe cikinta,Don bala'e ko kuskure bakinta batayi ba,yayi dama dama da kumfa,Hannunta ruƙe da brush,

  "Allah sarki aunty hafsat,wlh na tausaya mata baiwar Allah,Ni indan tani ce,Tuntuni na yafe mata,Amma meyasa ba ataimaka mata ba"?

   "Jahad bamusan komai game da tafiyarta enugu ba,wayarta ma ba'a samu,Ashe tun lokacin da mai motar ya bugeta,Anan ta rasa wayarta,Shiyasa bamusan halin da take ciki ba,Amma yanzu nayiwa daddy magana,Yanzu haka tana kwance gadon asibiti acan enugun,saboda lalacewar da ƙafar tayi baza a iya ɗaukota kaitsaye ba zuwa abuja,Dole acan za'a fara yi mata aiki,Za'a cire ƙafarne....."

  Tunkan hafsat takai ƙarshen maganarta,Hosana dake ƙumshe dariya acikin toilet,ta tuntsire da wata irin mahaukaciyar dariya,

"Waye acikin toilet?Naji kamar sautin dariya"

  Da sauri jahad tace"Bakowa aunty hafsat,Allah Ya bata lafiya,in sha Allah zata ji sauƙi,zamu tayata da addu'a,"

Hannu tasa tana share hawayen fuskarta,Kalaman jahad sun sanyaya mata zuciyarta,

  'Nagode sosai jahad,Yanzu saura hosana inaso na nema mata yafiyarta,"

  Jahad na ƙoƙarin buɗe baki tayi magana,hosana dake acikin toilet ta ɗaga murya tare da cewa"Wlh na yafe mata,tunda an gutsire kafar,Allah ya kyauta gaba,"

   Da sauri jahad ta daka mata tsawa"Hosana ya ishe ki haka,Wai meyasa baki iya magana ba,"

  Hafsat kuwa murya asanyaye tace"Nagode hosana,Ni banga laifinta ba,Ai ita taja ma kanta,"tana kai ƙarshen maganar,ta nufi hanyar fita daga dakin,bayan fitarta,hosana ta futo daga cikin toilet,bakinta washe,

Harara Jahad ta jefe mata"Wawuya kawai sullu6iya,Yanzu abunda kika faɗa ma Aunty hafsat ya dace"?

  Murguɗa mata baki Hosana tayi"Anje an faɗa,Allah shi ƙara in ma da ƙarin Ya ƙara,Uban dayasa ta kulle mu acikin store kamar wasu dabbobi,Wlh ni daɗi naji,wai agefen bishiya take kwana,har na hango ƙoƙwan bararta....."fashewa ta kuma yi da dariya hada dafe ciki,jahad dai bata tanka mata ba,ido kawai tabi ta dashi,cike da takaici,

Guntun tsoki taja"Ya omar dai baiyi dacen mata ba,"

   Harara hosana ta watsa mata kafin tace"eh ɗin ina ruwanki?A haka ya gani yana so,ɗan baƙin ciki sai dai ya mutu,Ni da ya Omar mutu ka raba takalmin kaza,"

    Girgiza kai kawai Tayi batare da ta kuma tanka mata ba,Komawa tayi gefen gadon ta zauna,

  

*Junaid Romeo*


Har cikin ɗaki,Mommy ta shigo mashi da breakfast ɗinshi,Jiya atare dashi suka kwana,dama tunda ya fara jinya a tsakiyarsu suke sanyashi,Yanzu kuma ya fara jin sauki,Ya fara tunanin komawa bedroom ɗinshi,


A kwance ta same shi idanuwanshi na fuskantar ceilling,yayin da hawaye yake gangarowa kan fuskarsa,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,

  "Junaid meke damunka ne"?tayi maganar a yayin da take ƙoƙarin zama gefenshi bayan ta ajiye mashi tray din kayan abinci saman table,

   Dakyar ya iya mikewa daga kwanciyar da yayi ya zaune,hannu tasa tana goge mashi hawayen dake akan fuskarshi

  "Pls tell me meyasa kake zubar da hawayenka"?ta tambaya cikin damuwa sosai,.  

  "Mommy,ina aunty azmee take"?

Ɗaure fuska Alex tayi"Junaid kar na sake ji,kayi mun zancenta,Yanzu azmee bata atare damu tana a prison,"

  Cikin shessheƙar kuka yace"Mommy aunty azmee tana a prison why?Meyasa za'a kaita can?nifa bata cutar dani ba....."rufe mashi baki mommy tayi da tafin hannunta"Shut up!ashe baka da hankali!duk irin cin zalun da tayi maka,amma kake faɗin bata cutar dakai ba?itace silar ciwon asthma ɗinka,sannan itace Ta mayar dakai soko ta hanaka ɗaukar karatu acikin brain ɗinka,A haka har kake cewa bata Cutar dakai ba"?shiru yayi baice komai ba,still hawaye basu daina zuba akan fuskarshi ba,

  'Why junaid?just because of azmee kake zubar da expensive tears ɗinka?kana so ka 6ata mun rai ko"?

  Girgiza kai yayi"Am sorry mommy,Bazan ƙara magana akanta ba,"cikin sanyin murya yayi maganar,

  Hugging ɗinshi tayi ajikinta"yawwa my baby boy,mu manta da abunda ya faru,Yakama ka mayar da hankalinka akan future ɗinka,yanzu dai bari na fara zuba maka abinci kaci ka koshi sai muyi magana mai mahimmanci akan rayuwarka,"

  Janye shi tayi daga jikinta,sannan ta soma yin serving dinshi,Ta tasa shi gaba Sai da yaci ya ƙoshi tukunna suka soma magana dashi,Akan karatunshi,


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 12 na rana,Gaba ɗaya matasan gidan suka shirya cikin kakinsu na sojoji,A jere motocinsu suka fita daga cikin gidan,babban taro su kayi a headquater ɗinsu,domin ƙarrama matasan gidan tare da ƙara masu Matsayin aikinsu,Farin ciki a wurin abbansu kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha,bakinshi Yaƙi rufuwa,ganin yadda ake ta yabon ƴa'ƴanshi,Manya manyan shuwagabanni na Armed forces suka halarci taron,na ƙasashe daban daban,



*SEHRISH*


Bata jima da fitowa daga wanka ba,Jikinta sanye da bathrobe,ta yarfo da gashin kanta ta gefen wuyanta,a takure ta samu amrish saman gadon,still taƙi sakin jikinta tayi rayuwarta kamar kowa,

  "Wai meke damunki ne"?

"Babu komai"ta bata amsa a taƙaice,

  "Idan kina jin kaɗaici ki fita waje mana,Ga ƴan uwa can suna ta fira a palour,"

"Bazan iya zuwa wurinsu ba,"

Tsananin tausayinta ya kamata,baiwar Allah duk ta tsani rayuwarta,ta takure kanta,

  "Zanyi magana da daddy,May be idan shi yayi maki magana zaki faɗa mashi damuwarki,"

  Da sauri tace"dan Allah kada kiyi mashi magana,wlh babu abunda ke damuna,rashin sabo ne nan da ɗan wani lokaci zan saba da kowa,"

  Gyaɗa kai sehrish tayi tare da samun wuri gaban mirror ta zauna,

  Zamanta keda wuya wayarta dake ajiye saman side drawer ta soma ringing,hannu amrish tasa ta ɗauki wayar,kafin ta sauko daga saman gadon ta miƙa mata,

  Kar6ar wayar Sehrish tayi tare da kallon screen ɗin,My Boss Man ne ke kiranta,

  Tayi mamakin ganin kiran Sgr,a wannan lokacin,picking call ɗin tayi tare da manna wayar a kunnanta,

  "Assalamu alaikum,"

Bai amsa mata sallamarta ba,Sai cewa yayi"what are u doing now"?

  "Yanzu na fito daga wanka,ina shiryawa"cikin sanyin murya ta bashi amsa,

  "Its okey,before na dawo,ki shirya mun kanki,"

cike da mamaki ta amsa mashi da"Toh " 

  Daga haka bai ƙara cewa komai ba,yayi rejecting kiran,tana ƙoƙarin ajiye wayar kiran Aunty azeema ya shigo wayar,murmushi ta saki dama tun jiya take ta son suyi magana da ita,

  Ɗaga kiran tayi tare da manna wayar akan kunnanta,tunkafin tayi sallama hajiya azeema tace"Daughter,ki sameni a ɗakina,inason magana dake,"

Cike da zumuɗi Sehrish ta amsa mata da toh auntyna Am on my way,


Bayan ta katse wayar ta miƙe,ta nufi wardrobe,dogon hijabi ta ɗauko ta zumbulashi ajikinta,ɗaukar wayarta dake ajiye saman mirror tayi,Amrish ta mika ma wayar"Ki yi amfani da ita,Zata ɗebe maki kewa kafin na dawo,zanje wurin auntyna ne,"

Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Nagode,Saikin dawo,"


Da sauri ta fuce daga ɗakin,gyara kwanciya amrish tayi saman gadon,Hannunta ruƙe da wayar Sehrish,comedy din cikin wayar ta fara kallo,tun tana murmushi har ta fara tiƙar dariya,tana cikin kallon videos din Kiran ya shigo wayar,Duba sunan Mai kiran wayar tayi,

  *Yaya Yusif*

A fili tace"yayanta ne ke kira,i won't pick it,idan ta dawo zan faɗa mata,"har kiran ya katse bata ɗaga ba,after one minute,wani kiran nashi ya sake shigowa wayar,

  Yanke shawarar ɗaga kiran tayi,A kunne ta manna wayar,Shiru tayi bata ce mashi komai ba,

  "Assalamu Alaikum,Sister ya kike"?

  Murmushi tasaki da yake ta ƙware wurin iya kwaikwayon muryar mutane sai cewa tayi"Lafiya lou yaya yusif,Ya kake"?

  "Ina lafiya,kinyi mamakin kira na ko"?

  "Eh,"ta amsa mashi,

"Na kira ne don na tambayeki,Yarinyar nan ƙawarki,i forgot her name,me irin sunanki,"

"Amrish"?tayi tambayar tana jiran jin amsarshi,

  "Yeah,ita nake Nufi,naga ban cika ganinta ba,ina fata dai babu abunda ke damunta ko"?

Wani irin farin ciki ne ya lullu6e amrish,ashe akwai wanda suka damu da ita acikin gidan,

  "Kinyi shiru baki ce komai ba"?

Da sauri tace"Lafiyarta qalou,Yanzu haka nabarta ɗaki tana bacci,"

  "Its okey,ki shafa mun kanta,idan ta tashi ki sanar da ita cewa,ina gaishe da ita,"

"Zanyi yadda kace in sha Allah,"

  "Good"Yana katse kiran,ta fashe da wata irin dariya,saboda tsabar farin ciki hada yin ƙundunbale ta wutsila gefe ɗaya,Kamar anyi mata Albishir da gidan Aljanna,


A 6angaren Sehrish kuwa,Lokacin da ta shiga ɗakin hajiya Azeema a zaune ta sameta gefen gadonta,bubu gown ce ajikinta ta material,ba ƙaramin kyau yayi mata ba,

   "My daughter,Zo ki zauna kusa dani,long time bamu haɗu ba,"

  "Aunty ai jiya saida nazo ɗakinki,Na sameki kina bacci,sai dai na haƙura na koma,"ta ƙarasa maganar tare da samun wuri ta zauna daga gefenta,Suna fuskantar juna,

  "Kinsan jiya mun kwaso gajiya,shiyasa ban samu na kiraki mun yi magana ba,Amma yanzu Alhamdullilah"

  Murmushi sehrish ta saki tare da sunnar da kanta kasa tana kallon yatsun hannunta,

  "Naga canji sosai attare dake,Kinyi haske kin ƙara kyau,ta ko'ina dai masha Allah,har na ƙosa naji labari me daɗi daga gare ki,"

  Kunyace ta rufe sehrish da sauri ta sanya tafin hannunta asaman fuskarta ta rufe,"

  dariya hajiya azeema tayi"kinfa san tsakanina dake babu kunya,Ba nace maki ki ɗauke ni tamkar ƙawarki ba"?tayi maganar tana kallonta fuskarta

  Daƙyar sehrish ta iya cewa"Eh,"

  "Yawwa,to cire hannunki yanzu,inaso ki faɗamun wani cigaba aka samu"?

  Daƙyar ta daure ta cije cike da jin kunya ta soma bayyana mata,duk wani abu dake a tsakaninta da SGR,

  Dariya sosai hajiya azeema tayi,bayan ta tsagaita da yin dariyar tace"Wonderful!My daughter u did a good job,you're so special tunda gashi kin fara Canza mana Sgr,Naji daɗin jin hakan sosai,"ajiyar zuciya ta ɗan sauke kafin ta cigaba da cewa"Yanzu ya ake ciki game da tafiyarshi U.S?Yace zai tafi dake ko kuwa baiyi maki magana akan hakan ba"?

   "Bani da masaniya akan wannan,bansani ba ko yana so ya tafi dani ko bayaso ya tafi dani,tunda baiyi mun magana akan hakan ba,Amma gaskiya aunty ko yace zai tafi dani ni bazan bishi ba,Saboda ba sona yake yi ba,bai ta6a furta mun kalmar so ba,"jiki asanyaye tayi maganar,

   "Kin faɗi gaskiya,Amma inaso ki sani,Shi so ba dole sai ta kalamin baki ake furta shi ba,kowa da kalar nashi salon Soyayyar,Rafayet Baison so ba,Idan har ya kasance akanki yafara jin shi,zaiyi matuƙar wuya ya iya gane hakan,bazance ki bi shi ba,kuma bazance kada ki bi shi ba,tunda Wuƙa da nama suna a hannun abusufyan,Dole sai idan Sgr Ya soke wannan yarjejeniyar dake a tsakaninku,Ya miƙa wuya,Ya kuma amince zai rayu dake a matsayin matarshi,Uwar ƴa'ƴanshi,Idan ba haka ba,Bana tunanin Abusufyan zai bari ya tafi dake,zai nemi ya sake ki ne,"

  Hankalin Sehrish ya ɗan tashi,don tasan halin Sgr,zai iya sakinta,tunda tasan ba sonta yake yi ba,A tunaninta kenan,.  

  "Yanzu mommy,Shikenan"

Jinjina kai hajiya azeema tayi,ƙwarai kuwa,bani da sauran shawarar da zan baki,Illa kawai mu zuba ido,muji me Abusufyan zaice,"

   Sun jima suna tattaunawa kafin daga bisani,Sehrish ta baro bedroom ɗin,har wani jiri take gani acikin idanuwanta,daƙyar ta lalla6a ta koma ɗakinsu,Lokacin Amrish ta shiga toilet,saman gado ta haye tare da jan bargo ta lullu6e kanta ciki,


Fitowa amrish tayi daga cikin toilet din,tayi ɗaurin gaba da towel,ganin sehrish cikin bargo yasa ta ɗanyi mata gyaran murya tare da cewa"kin dawo kenan"?

  "Eh"ta bata amsa atakaice,

"Okey,"ta ambaci hakan tare da wucewa gaban wardrobe ta buɗe ta dauko kayan da zata sanya,


Lokacin sallar magrib dakyar ta samu tayi sallah,ita kaɗai ta rage a ɗakin,Amrish ta ɗan fita waje,wurinsu Jahad,



Basu tashi dawowa cikin gidan ba,Sai wuraren ƙarfe 8 na dare,Gidan ya cika fam da manya manyan baƙi,ta ko'ina ka waiga Sojoji ne sanye cikin kakinsu,Wasu kuma Suna acikin shigarmu ta hausawa,Abun ya ƙayatar sosai,kowa na farin ciki banda mutun ɗaya SGR,domin kuwa yau ta kasance ranar baƙin ciki awurinshi,Fuskarshi kwata kwata babu annuri tunda suka fita har aka kammala taron,An karramashi shida Omar,Ga wani ƙarin  matsayin da za'a yi masu a U.S yana jiransu,Sauran matasan gidan kowanne da muƙamin da aka bashi,basu samun lokacin hutu ba,sai wuraren ƙarfe 10 lokacin Manyan bakin da suka zo,Duk sun tafi,Gidan ya rage sai mutanan cikinsu,Kowa Ya wuce bedroom ɗinshi domin hutawa,


*SGR*


Tun da ya shiga bedroom ɗinshi sai zarya yake yi,ya kasa samun natsuwa ko uniform ɗin jikinshi bai cire ba,Abbansu kawai yake jira Ya shigo cikin gidan suyi magana dashi,Sai kiran wayarshi yake yi,Amma bai ɗaga ba,atare dashi suka dawo,Amma bai shigo gidan ba,Yana a wurin abokinshi tafeeda a waje,komawa yayi gefen gadon ya zauna,kamar ance ya duba screen ɗin wayarshi,Sai ga text message na abusufyan,ƙin buɗe saƙon yayi don yasan cewa akan maganar sakin Sehrish ne,duk yabi ya tayar mashi da hankalinshi,duk yinin yau baisanya abinci acikinshi ba,Kamar me azumi,saboda tsabar tashin hankali,Zuciyarshi tare da agogo suke bugawa, awanni kaɗan suka rage mashi,shikaɗai yasan yadda yake ji acikin zuciyarshi,Yau da ƙishir ruwanta ya yini,yayi maraicin ganinta,duk a tunaninshi Uncle ne Ya dakatar da ita,


Yana cikin wannan mawuyacin halin,Omar Ya faɗo bedroom ɗin nashi jikinshi sanye da kaki,Yana ta faman ƙwala mashi kira"Rafayet!Rafayet"!

    Daƙyar ya iya amsa mashi"Na'am,"


Ajiyar zuciya ya ɗan sauke kafin yace"Wai meke damunka ne?tunda muka fita na lura dakai,fuskarka a ɗaure tamau,babu annuri,In wani abu ne ka faɗamun mana,May be i ave the solution of it,"

    Har lokacin bai motsa daga zaunan da yake ba,Gefen shi omar ya zauna tare da dafa kafaɗarsa,cikin lallami yake yi mashi magana"Pls my own bro,ka faɗamun mana,wlh duk na damu da halin da kake ciki,"

  Daƙyar ya samu Sgr Ya faɗa mashi abunda ya faru tsakaninshi da Abusufyan Da asuba,"

  Cike da takaici Omar yace"Ya salaam!Rafayet meke damunka ne wai?Wai meyasa komai saika nuna fin ƙarfi akanshi ne!don me zaka ce mashi haka?kana so ka tafi da ƴarshi ba don kana sonta a matsayin matarka ba,Sai don kanaso taci gaba da yi maka aiki kamar wata baiwa!?

  Runtse ido sgr yayi tare da cizon pink lips ɗinsa,

"Its okey Omar,Stop shouting at me,kana cika mun kunne na,"

Rai a6ace Omar ya miƙe tare da acewa "Oh haka ma zakace!Good,wlh baka ji jiki ba,Uncle yayi mun dai dai,"juyawa yayi a fusace har yakai baƙin ƙopar ya kuma juyowa tare da kallonshi,

  "Dole na fada maka gaskiya koda kuwa bakasan jinta,Rafayet ka kamu da Son Yarinyar nan!Kana tsananin sonta am advising u,tunkafin lokaci ya ƙure maka,Kayi hanzarin miƙa wuya,Idan kuma kace zaka sanya girman kai aciki,Wlh u will regret it,"yana kai ƙarshen maganarshi,ya fuce daga cikin ɗakin,bawan allah saboda yadda ya damu da sgr,a ƙopar falonshi ya tsaya sam ya kasa tafiya,tsananin tausayinshi ne ya kamashi,Sam baisan menene so ba,gashi yanzu zai fara shan wahalarshi,


Ya jima a haka kafin ya fito daga part ɗinsa,yana ƙoƙarin saukowa downstairs su kayi kici6us da Abbansu,da alama bene zai hau,shigowarshi kenan ko kakin jikinshi bai cire ba,

    "Yawwa abba,Inason magana dakai,"

  "Meya faru omar?Allah yasa dai Lafiya,Naga missed calls ɗin rafayet yana ta kirana,bansani ba saboda na sanya wayar silent"

  Ruƙo hannunshi Omar yayi,Suka koma upstairs din,a tsaye suka soma magana,

  "Abba,na samu rafayet cikin mawuyacin hali,dama duk yinin yau na lura dashi,ko abinci baici ba,Yanzu naje bedroom ɗinshi na tambayeshi meke damunshi,Shine yake sanar dani cewa Uncle abusufyan Ya nemi ya sakar mashi ƴarsa,"

  Murmushin takaici Abba yayi kafin yace"Wata amsa ya bashi"?

  "Yace shi bazai saketa ba,Ya soke yarjejeniyar auren,Maimakon yabi ta lalama,Sai cewa yayi wai zai tafi da ita U.s don taci gaba da yi mashi aiki,"

  Cike da takaici,Abba ya dafe goshinshi"Ni dama nasani wlh,shiyasa tunfarko nayi ƙoƙarin in karkato hankalinshi don ya soke yarjejeniyar,Amma ya nuna mun cewa baya buƙatarta,Da zarar wata uku sun cika zai sakar mashi ƴarshi,Yanzu gashi lokaci ya cika,Ni ba abunda zan iya yi mashi Omar,nasan na isa da abusufyan amma ban isa na hana shi yin iko da ƴarshi ba,"

"Yanzu abba,Babu wani solution?Ni so nake A soke wannan auren yarjejeniyar,A barshi yayi rayuwa da matarshi,"

  "Kasan Allah,in har rafayet bai miƙa wuya ba,Ni bazan ta6a tursasa ma abusufyan ba,Dole ya sauke jiji da kannan nashi,in har yana son yaci gaba da rayuwa da ita,Shi Yafi ƙarfin yayi biyayya ya samu abunda yakeso,Komai sai yace a dole saiya same shi,Ai bakomai ne ƙarfi da dukiya suke iya siya ma mutun ba,babban abun takaicin ma,Ya maida abusufyan tamkar tsaranshi,ko ba komai ,Shifa uncle dinsa ne,baya respecting dinshi yadda ya dace,"

  jinjina kai omar yayi'Shikenan Abba,Zanyi ƙoƙari wurin ganin na fahimtar dashi,wlh banaso a wahalar mun da ɗan uwana,irin rayuwar da aka saba mashi da itane,Shiyasa ya kasance haka,"

  Suna cikin maganar nan,suka jiyo takun takalmi,Alamar wani na tunkaraso,da sauri suka kai idanuwansu wurin,Bakowa bane face Abusufyan,Jikinshi na sanye da Jallabiya brown colour,ƙarasawa yayi tare da miƙa ma abba hannu suka gaisa,

  Fuskarshi asake yace"Sannu da dawowa Yayana nakaina,Yanzun nan Ayaan ke sanar dani cewa ka dawo gida,"

 "Eh wlh,ban jima da shigowa ba,Na nufo nan,wurin mutumin naka,"ya ƙarasa maganar da zolaya,

  ta6e baki Abusufyan yayi batare da yace komai ba,

 "Yanzu omar ke sanar dani abunda Ya faru atsakaninka da Sgr,Gaskiya banji daɗi ba,Rafayet bai kyauta ba,"

  Sai lokacin abusufyan ya soma magana"Allah yaya rafayet saiya gane kuskurenshi,A ƙule nake dashi,Wai har ni zai kalli tsabar idona yace wai Ya soke yarjejeniyar aurenshi da ita,Kuma zai tafi da ita u.s,don taci gaba dayi mashi aiki?wato shi yafi ƙarfin yace yana sonta a matsayin matarshi......."daƙyar yakai karshen maganar saboda ranshi yayi mugun 6aci,

  "Dan Allah uncle kayi haƙuri,Amma ......"tunkan Omar yakai ƙarshen maganar ya dakatar dashi"kada kace komai Omar,Ka barni da rafayet kawai,Ya raina ni,Har ni zan kai mashi paper don ya rubuta mata sakinta,Yasa hannu ya ɗauki paper ya kekketata akan idona,Baiso xaman lafiya ba Allah,"

  Tunda ya soma magana Abba ke kallonshi,Bai ta6a ganin abusufyan ya zuciya ba irin na yau,

  Yana kai ƙarshen maganarshi,bai jira wani daga cikinsu Ya ƙara magana ba,Ya wuce part ɗin Sgr,Don yaci alwashin saiya sakar mashi ƴarshi Ayau ɗin nan,da sauri Omar da Abba suka bi bayanshi,


A lokacin sgr ya miƙe yana ta faman yin zarya acikin bedroom ɗinshi,Ba zato ba tsammani Yaji sallamar abusufyan har sai da gabanshi Ya faɗi,Yana shigowa Abba da Omar suka faɗo ɗakin,

  "Rafayet!ina takardar dana ce ka rubuta mun"?

  Zuba mashi ido Sgr yayi batare dayace komai ba,a hankali ya sauke idanuwanshi daga kan abusufyan ya ɗaura su kan Abbansu,jikinshi ba ƙaramin sanyi yayi ba,ganin yadda Sgr ya koma,kamar wanda yayi zazza6i,

  Har lokacin bakinshi bai mutu ba,rai a6ace Ya soma magana,

  "I will never use my fingers to write her a divorce paper,sai dai duk abunda zai faru ya faru,"

  A hasale Abusufyan ya kalli abba"Kaji abunda yace ko"?

  Gaba ɗaya sun tashi hankalin abba,Ga gajiya daya kwaso,

  "Dan Allah mubi komai a hankali,Banaso kowa yaji wannan maganar,Zansa ya sake ta,ni dakaina,"

  Hankali atashe Sgr ke kallon Abbansu,

  "tun farko Auren nan Anyi shine bisa yarjejeniyar zaka sakar mashi ƴarshi,Bayan wata uku cuf,A tsakanin mu ukun nan mu kayi yarjejeniyar nan,Kuma akwai shaida a hannun kowannanmu,don haka baka da wani za6i daya wuce ka sakar mashi ƴarshi kamar yarda ya buƙata,"

  Girgiza kai sgr yayi"That's impossible,"Ya ambaci hakan tare da juya masu baya,

    "A matsayina na mahaifinka,Ina umartarka,daka rubuta mata takardar sakinta,Kamar yadda mahaifinta ya buƙata,Idan kuma ba haka ba,Zan yanke duk hukuncin dana ga ya dace,"

   A firgice ya juyo yana kallonshi,Muryarshi na kerma yace"Abb..ba"

  Fuska aɗaure abba yace"banason Jin komai daga gareka"

   Wata irin zufa ce ta soma tsatstsafowa ta gefen fuskarshi,hankali tashe yake kallon Omar,Da sauri Omar ya kawar da kanshi gefe,sam baiso hakan Ya faru ba,yaso ace Sgr Ya tausasa kalamanshi,Amma yaƙi fahimtar hakan,

   jikinshi har wani tsuma yake yi,gaba ɗaya sunso Sgr Ya miƙa wuya a wannan lokacin amma sai suka ji yace"Its Okey,Zan sake ta,Amma inaso a ƙara mun lokaci zuwa asuba,dakaina zan kawo takardar sakin nata,"

  Kallon juna sukayi,Cike da mamakin jin yayi amanna da sakin nata,

  Da sauri Omar yace"Pls,kada kuyi saurin yanke hukunci,yakamata muji ta bakin ita yarinyar,"

  Girgiza kai abusufyan yayi"babu buƙatar yin hakan,Na bashi nan da asuba,Ya kawo mun takardar sakinta,"Yana kaiwa ƙarshen maganarshi,Ya juya afusace yabar bedroom ɗin,Abba ma yabi bayanshi,

  Ya rage daga shi sai Omar,

  "Pls bro,kada kace zaka sake ta,Nasan kana sonta wlh zaka yima zuciyarka illa ne,naso ace ka miƙa wuya tun wuri....."

  A hasale sgr ya juyo idanuwanshi sun juye,tamkar bashi ba,da wata irin murya yace"Banason ganin kowa a tare da ni,"

  "Allah ya huci zuciyarka,"jiki asanyaye omar ya juya yabar mashi ɗakin,


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 12 na dare,tana zaune cikin duhu gefen gadonsu,sam batasan cewa sun dawo cikin gidan ba,saboda Baccin daya ɗauketa Mai nauyin gaske shiyasa har bata ji dirar motocinsu ba tun wurin ƙarfe goma da suka dawo,duk wannan budurin da akeyi ita bata sani ba,bata jima da farkawa ba,Amrish na kwance sai sharar baccinta takeyi hankali kwance,



Wata irin yunwa take ji,Sai faman lumshe idanuwanta takeyi don bacci bai isheta ba,gani tayi har sha biyu da rabi  basu dawo ba,hakan Yasa ta ɗan kwanta gefen gadon,cikin lokaci ƙanƙanin bacci yayi awon gaba da ita,


Kwatsam!ba zato ba tsammani kamar daga sama,Taji an banko ƙopar ɗakin da suke ciki,A firgice ta miƙe zaune don ganin wanene,bata iya tantance wanda ya shigo ɗakin ba saboda sun kashe hasken ɗakin,ko'ina duhu,a tsorace takai hannu tana ƙoƙarin lalubo Fitar saman drawer don ta kunnata,Sai dai kash kafin tayi wani yunƙuri,Gaba ɗaya,ɗungurugum taji an ɗauketa sama,Tana ƙoƙarin yin ihu aka toshe mata bakinta,

 

  

  *naso inyi weekend amma bazan samu halin yi ba,but in sha Allah zanyi hot pages masu tsayi,Ga duk mai buƙatar karanta Littafin Abban sojoji from Book one to 3,Ya yi mun saƙo ta whatsapp,08103884440*

  

  

  














  

 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*



*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*









A saman katafaren gadonshi yayi wurgi da ita,gaba ɗaya ta kife saman mattress ɗin,Yalwataccen gashin kanta ya tarwatse asaman bedsheet ɗin,tayi matuƙar tsorata duk da ta gane wanene ya ɗaukota sakamakon daddaɗan ƙamshin turaren nan nashi data shaƙa jikin Zanin gadonsa,Daƙyar ta samu ta ɗago da fuskarta tare da juyawa bakin ƙopar ɗakin don ta samu damar ganinshi,tuni ya fuce daga bedroom ɗin,Daga inda take tana jiyo sautin Ƙopar da yake rufewa ta palour ɗinsa,Abun yayi matuƙar ɗaure mata kai,batasan meyasa Ya ɗaukota daga ɗakinsu ba,Sannan kuma yazo yana rufe ƙopa,bata kai ƙarshen zancen zucin nata ba,Sai gashi kamar an jefoshi Ya faɗo cikin bedroom ɗin,hannu yasa tare da ruƙe ƙopar ɗakin ya garƙameta yadda ko sauti bazai fita ba,


Lokaci guda gabanta ya shiga faɗuwa,ganin yadda jikinshi keta tsuma,wata irin zufa ce ke tsassafo mashi ajikinshi,Ya jiƙe sharƙaf da gumi,sai faman huci yake yi,fuskarshi a ɗaure tamau babu annuri ko misƙala zarratin,Gaba ɗaya ma baya acikin hayyacinshi,muscles ɗinshi har kerma suke yi,


Muryarta na kerma ta ambaci sunanshi"Ya...Rafayet"bai amsa mata ba,Sae Ma ƙoƙarin Cire rigar jikinshi da yake yi,tu6e ta yayi tare da jefar da ita kasa,Wannan ƙirar ƙarfin tashi mai matuƙar tsoratarwa ta bayyana,breasts ɗinshi sai rawa suke yi kamar wanda zaiyi dambe,

  Hankali a matuƙar tashe tace"Am so sorry Ya rafayet,bacci ne ya ɗauke ni shiyasa ban kawo maka dinner ɗinka ba......."daƙyar ta ƙarasa maganar,duk tabi ta dabarbarce,

  Wani irin kallo yake bin ta dashi,Sexy blue eyes ɗin nan nashi yadda kasan na mashayin giya haka suka koma,

A zafafe Ya damƙi belt ɗin wandonshi,Ya fusgoshi tare da yin wurgi dashi ƙasa,Waro ido waje Sehrish tayi tana kallonshi,

   Gaba ɗaya ya cire kayan jikinshi Ya zama naked haihuwar uwarshi,A matuƙar razane Ta runtse idanuwanta,yayin da take ja da baya har ta ƙurewa head board ɗin gadon,ta taƙure kanta,la66anta na kerma Take Ambaton"Innalillahi wa'inna ilahirraji'un..."

  Gadan gadan Sgr Ya tunkari gadon Yadda kasan Mayunwacin Zaki haka ya farmaketa saman gadon nan,Hannu bibbiyu yasa ya damƙi gaban Night gown ɗin jikinta,tun daga sama har ƙasa ya direta,Gaba ɗaya ya fusge rigar daga jikinta yayi wurgi da ita can gefe guda,Damƙar bra ɗin jikinta ya kuma Yi ya 6an6arota daga jikinta,Duk yadda taso ta dakatar da shi amma hakan ya faskara,Wata irin damƙa da yayi ma Gashin kanta,Tsabar raɗaɗin da taji ne yasa ta fashe da matsanancin kuka,haɗa bakinsu yayi wuri guda,duk sai da ya faffasa mata bakinta wurin sucking lips ɗinta,tamkar zai cire mata harshenta,gaba ɗaya ya turmusheta ta ko'ina yayi mata rumfa da faffaɗan ƙirjinshi,tunda ya damƙi boobs ɗinta da hannunshi yake murzarsu tamkar zai tatsesu duka,Kuka sosai Sehrish ta shiga yi tana kai mashi bugu abayanshi saboda tsabar raɗaɗin da take ji,Kwata kwata baya jinta,Idanuwanshi sun makance,kunnuwanshi sun kurmance,Baya ji baya gani,Ganin yana ƙoƙarin Yi mata illane Yasa ta yi wani ƙwakkwaran Yunƙuri tayi wurgi dashi gefe guda,Da gudun gaske ta duro daga saman gadon,Cikin fitar hayyaci Sgr Ya biyota gaba ɗaya duk tabi ta ruɗe ta rasa ina zata dosa,Ya rufe ƙopar dakin,Cikin labule ta dinga shigewa tana kuka tana Ambaton Sunan Oumma da Daddy,A tsiyace Sgr ya dinga sanya hannunshi Yana tunbuƙe labulayen ɗakin gaba ɗaya sai daya ciresu duk inda ta shiga har Allah Ya bashi nasarar Cafko Qugunta,Wani irin ruƙo yayi mata tare da ɗaga ta Sama daga inda yake Yayi wurgi da ita agigice ta saki ƙara,Yaraf Ta faɗa saman gadon,Kamar wani bakure haka ya bita Ya danne ta,Ya soma ƙoƙarin penetrating ɗinta,da ƙarfi ya soma kokarin shigarta,wata irin kururuwa sehrish tayi,A galabaice la66anta na kerma take yi mashi magana"Ya Rafayet mutuwa zanyi,Bazan iya jurewa ba,kada ka kashe ni,Don Allah ya rafayet kada kayi mun horo ta wannan hanyar........"bata ƙarasa maganarba,Numfashinta ya soma Ƙoƙarin ɗaukewa,idanuwanta suka firfito waje tamkar ƙwayar idon zata faɗo ƙasa,wata irin zufa ce ta wanke mata fuskarta,cikin fitar hayyaci ta dinga kai mashi cizo da yakushi a saman kafaɗarshi har sai da ta fasa mashi fatar jikinshi ko gizau wannan baiyi ba,Aikinshi kawai yake yi duk ya haɗa uban gumi,

  Tun tana ambaton sunanshi "Ya rafayet mutuwa zanyi, bazan iya jurewa ba....",har muryarta ta fara disashewa,


Bai tashi ankara da 6arnar da yayi ba,Sai da idanuwanshi suka sauka kan Jinin dake malale saman bedsheet ɗinsu,Lokaci guda ya dawo cikin hayyacinshi,Gabanshi Yayi wani irin bugu,

  "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!!"


Yayi matuƙar razana da ganin irin aika aikar da yayi mata,babu tabbacin tana raye kota mutu,hankalinshi A matuƙar tashe Ya talla6o fuskarta,muryarshi na kerma ya soma ambaton sunanta"Reesh!Reesh!!pls wake up,"ko gizau wannan batayi ba,a gigice ya dinga jijjigata"reesh,reesh can u hear me..."

  Wani irin wahalallan yawu ya haɗiya,duk yabi ya dabarbarce,Durowa yayi daga saman gadon ya ɗauki short ɗinsa Ya zura ajikinshi,saboda tsabar ruɗu ya rasa ina zai dosa,daƙyar ya gane ƙopar fita daga bedroom ɗin,


  Fitowa yayi daga part ɗinsa,Saboda tsabar ruɗewa da yayi sam ya manta da yanayin da yake ciki,da gudun gaske Ya nufi part ɗin Marshal Omar,Yana shiga bedroom ɗinshi ya soma kwala mashi kira da karfin gaske"Omar!Omar!"


A firgice Omar ya farka daga bacci,daƙyar ya iya buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci,hannu yakai cikin duhu Ya lalubo bedside lamp Ya kunnata,Haskenta ya ɗan haskaka ɗakin,

  "Rafayet!"da mamaki a fuskarshi Ya ambaci sunan,Lokaci guda ya soma bin jikinshi da kallo,Short ɗinshi Yayi jaga jaga da jini,Ga Yakushin da Sehrish tayi mashi A kafadarshi,

  Hankali a matuƙar tashe Omar yace"Innalillahi'wa'inna ilahirraji'una!Nashiga Uku!Rafayet me kayi haka"!?yayi maganar a yayin da yake saukowa daga saman gadon ya ƙarasa gaban Sgr,sam ya kasa buɗe baki yayi magana,

  Murya na rawa Omar yace"Rafayet ka faɗamun me ka aikata?Meyasa nake ganin jini a jikin short ɗin jikinka?waye ya yakushe ka,Kayi faɗa da kura ne....."?

  So yake yayi magana amma Ya kasa motsa lips ɗinsa,fuskarshi cike da tsantsar damuwa,hawaye kwance acikin fararen idanuwanshi,

  Rai amatuƙar 6ace Omar yace"Can't You talk to me!Ka faɗamun mana!Jinin menene ajikin ka!meyasa nake ganin hawaye acikin idanuwanka,Allah yasa ba abunda nake zargi bane......."

  Sai lokacin Sgr ya iya buɗe bakinsa"Omar,I ave made a great mistake,Na kusance ta a lokacin da nake cikin fushi,Reesh bata numfashi......"tunkan yakai ƙarshen maganar Omar Ya kwatsa mashi tsawa Tare da nuna mashi hanyar fita daga ɗakin"Ka fuce kabarmin ɗakina!Lokacin da kayi aika aikar da kayi baka nemi shawarata ba,Don haka babu ruwana Rafayet,Wlh ban ta6a ganin mutun mai son zuciya ba irin taka,Mugu kawai,"

   Ganin ya toge yaƙi motsawa,Yasa Omar ya fusgi hannunshi,Har izuwa ƙopar ɗakinshi Ya futar dashi,Tare da jan ƙopar ɗakin Ya datse ta,


Komawa gefen gadonshi yayi,cike da takaici ya zauna,zuciyarshi har wani tafarfasa takeyi,bai ta6a jin haushin Sgr ba irin na yau,tuni idanuwanshi sun cicciko tab da ƙwalla,


Bai ta6a tunanin Omar zaiyi mashi irin wannan korar ba,A lokacin da yake buƙatar taimakonshi,har wani jiri ya dinga ɗibarshi,yana tangal tangal zai faɗi daƙyar ya dafe bango da tafin hannunshi,Hawayen dake kwance cikin idanuwanshi ne suka soma gangarowa masu zafin gaske,tuni sun wanke mashi fuskarshi sharkaf,Tashin Hankali,gaba ɗaya yaji ya tsani kanshi,bakomai yake tunowa ba face Yadda Sehrish ta dinga roƙanshi akan Yayi haƙuri amma ya rufe ido yayi mata kaca kaca batare daya tausaya mata ba,


Gabanshi ne yayi wani irin bugu,sakamakon Kiran Sallar Asuba da aka fara yi,A gigice ya fito daga part ɗin Omar,gudu gudu sauri sauri Ya fada part ɗinshi,toilet Ya shiga,After some minutes Ya fito jikinshi sharkaf da ruwa ya ɗauro towel,abaibai ya zura jallabiya ajikinshi,wuyanta ya karkace,Sam babu natsuwa ajikinshi,har ya nufo gadon sai kuma ya koma ya dauko wata T-shirt dinshi ya dawo ya zura ma Sehrish,Babban bargo ya ɗauko tare da nannaɗe Sehrish aciki ya ɗaukota asaman kafaɗarshi,Wayarshi dake ajiye saman mirror ya ɗauka,Hannunshi na kerma Ya shiga Call log,Armstrong Ya danna ma Kira,tana fara ringing Amstrong ya ɗaga kiran,

  "Armstrong pls Ka fito da mota immediately,Am coming right now,"

  Yana kai ƙarshen maganarshi,Yayi rejecting Call ɗin,tare da yin wurgi da wayar kasa,a gurguje ya fito bayan ya janyo ƙopar bedroom ɗin,Sam baiyi tunanin kawar da komai ba,haka yabar zanin gadon sharkaf da jini,


Saukowa yayi downstairs,a hanzarce Ya fuce daga palourn,A lokacin Armstrong ya fito masu da mota,Tunkan ya ƙarasa Ya buɗe mashi motar,Ya shige hannunshi ɗauke da sehrish cikin bargo,

  Hankalin armstrong ba ƙaramin tashi yayi ba,duk da baisan me Sgr ya ɗauko ba,Amma yasan cewa mutunne aka naɗe a bargo,Ya damu sosai akan halin daya ganshi,key yayi ma motar,tare da yin reverse ya karya kwana,A guje Ya miƙi shantalelen Titin gidan,


Ji yayi bazai iya barin Sgr cikin wani hali ba,A hanzarce Ya miƙe Ya fito daga part ɗinsa,Ya nufi part ɗin Sgr,Yana zuwa ƙopar ɗakin,Yasa hannu yana ƙwanƙwasawa,

  "Rafayet!Rafayet"Da ƙarfi yake ambaton sunanshi,

  "Ka fito inason magana dakai,"nan ma shiru ba'a tanka mashi ba,

A ƙarshe daya gaji da tsayuwa Yasa hannu ya tura ƙopar bedroom ɗin Ya shige ciki,

  A firgice ya ɗan ja da baya yana ambaton"Hasbunallahu'wa' ni'emal wakeel,"ya tsorata da ganin Jini malale saman bedsheet ɗin gadon,Yayi kaca kaca dashi,babu kyan gani,wurga idanuwanshi yayi kan Labulayen ɗakin da Sgr Ya cusgosu ƙasa,slowly ya ɗaura idanuwanshi kan Wandonshi daya cire,Ga kuma night gown ɗin sehrish daya yayyageta,Ga kuma pant ɗinta daya rabashi biyu,Komai a hargitse,


A ruɗe Yaci gaba da kwala mashi kira,duk a tunaninshi ko ya shiga da ita toilet ne. 

  "Rafayet!Rafayet!"tsit ba a amsa mashi ba,hakan ya tabbar mashi da cewa SGR ya gudu tare da ita daga gidan,


Jikinshi na kerma ya soma ƙoƙarin lalubo wayarshi cikin aljihun wandon baccin jikinshi,Yana ɗauko wayar ya kira layin sgr,Sai ga wayar shi dake yashe ƙasan tiles ta soma Ringing,


"Ya salaam"ya furta hakan tare da yin saurin juyawa,da gudun gaske Ya sauko down stairs,Kaitsaye ya nufi hanyar fita palour,A waje ya samu major yake tambayarshi game da Sgr,ko ya ga lokacin daya fita,yace mashi eh akan idonshi,Sgr ya fito ɗauke da bargo a kafadarshi da alama mutun ya ɗauko,


Jin haka yasa Omar ya bashi umarnin ɗauko masu mota,Da gudun gaske suka bi bayansu,Sai dai lokacin da suka fito tuni motar Sgr ta jima da 6acewa 6aat,yanke shawarar zuwa Asibitin shi sukayi,May be su ci sa'a in yakaita kenan,


Suna zuwa asibitin aka sanar dasu cewa Sgr baizo ba,A gefen titi Major yayi parking ɗin motar kamar yadda Omar ya bashi umarni,Kiran Layin Armstrong yayi,nan take kiran ya shiga sai ringing take yi amma ba'a ɗaga ba,sunyi ƙoƙarin yin tracking ɗin layin Armstrong,Sai dai kash Ya toshe duk wata hanya da za'a iya bin diddiginshi,


Hankalin Omar yayi matuƙar tashi,baiso ya kori Sgr ba a wannan lokacin da yazo cikin mawuyacin hali,babu yarda ya iya dole suka koma Gida da gudun gaske motar ta shiga,Major na yin parking ɗinta,Omar ya fito a hanzarce Ya nufi main palour ɗin,fargabarshi kada Uncle ko Abba wani yace zai shiga bedroom ɗin Sgr tabbas zasu ga tashin hankali,


Gudu gudu sauri sauri Ya haye upstairs,kaitsaye ya nufi part ɗin Sgr ya shiga bedroom ɗinshi,within minutes Ya kawar da duk wani abu daya 6aci da jininta,zama yayi sosai yayi ma ɗakin gyara,har palour duk inda jini ya zuba sai da ya gogeshi,bayan ya kammala Ya koma part ɗinshi,shaf shaf ya shiga toilet ya ɗauro Alwala,


Ɗaya bayan ɗayan Matasan gidan suka fara fitowa domin halartar Sallar Asuba,kamar yadda suka saba tafiya atare,Lokacin da Marshal Ya sauko down,Suna haɗa ido da Abusufyan da Abba sai da gabanshi ya faɗi,tunkafin wani daga cikinsu yayi yunƙurin yi mashi magana da sauri yace"Lokaci yana ƙurewa,"


Babu wanda ya lura babu Sgr sai Abba da Abusufyan,gudun kada lokacin sallah ya wuce su ne yasa basu tambayeshi ba,sun bari sai sun dawo daga masallacin,


Tunda ta farka take jin zuciyarta babu daɗi,gabanta sai faɗuwa yake yi,wurga idanuwanta tayi kan Hosana da Jahad ta samu kowannansu cikin ƙoshin Lafiya,hannu tasa tana ɗan bubbuga ƙafafunsu,

  "Hosana!Jahad!ku tashi lokacin salla yayi,"jahad ce ta fara farkawa,saukowa tayi daga saman gadon ta wuce cikin toilet,

  "Hosana ki tashi mana kullum saikin bani wahala,"tayi maganar tana ɗan bubbuga ƙafarta,

  Daƙyar ta samu hosana ta farka,miƙewa tayi zaune tana hamma tare da yin Miƙa,

  "Oumma wlh nayi wani mummunan mafarki acikin bacci na,"

  Kallonta abu tayi"wani irin mafarki,"

  "Oumma,rishi ɗinmu na gani acikin wani ƙurmun daji,tana ta tsala gudu kamar zata tashi sama,Ga zaki yana ta bin ta,Sai kuka take yi tana ta ambaton sunanki dana Daddy don ku taimaketa amma babu wanda yaje wurinta har sai da zakin nan Yaji mata ciwo......"tana kai ƙarshen maganar ta fashe da matsanancin kuka,abun ya ƙona mata rai,


Shiru abu tayi,yayin da idanuwanta ke kallon fuskar Hosana dake kuka,

  Fitowa Jahad tayi daga cikin toilet,

  "Meya sameta take kuka"?Tayi tambayar tana kallon Oummansu,

  Ajiyar zuciya abu ta ɗan sauke tare da cewa"wai mafarki tayi da Sehrish acikin daji tana ta gudu,Zaki ya biyo ta har ya ji mata rauni,Shine take kuka"abu nakai ƙarshen maganarta,

Jahad taja dogon tsoki mai sauti"Amma hosana ban ta6a ganin Hamago irinki ba,kawai daga yin mafarki sai ki fara yiwa mutane kuka Angaya maki mafarki gaskiyane,Ko yau kika fara yin mafarki ne"?

  Cikin shessheƙar tace"Wlh in nayi mafarki yana zama gaskiya,kin manta 6eran gidansu Maman sadeeq daya saci daddawar gidanmu yakaita raminshi dake a zauren gidansu,Bani nayi mafarki ba har na tona mashi asiri,Muka yi mashi bugun tsiya har ƙafarshi ta 6alle....."

  Basu san lokacin da suka fashe da dariya ba,gaba ɗayansu Jahad hada dafe cikinta,ɗaure fuska hosana tayi don ita dagaske tayi maganar ba don suyi mata dariya ba,Saukowa abu tayi daga saman gadon ta nufi toilet tana ta faman tiƙar dariya Sai da takai bakin ƙopar tukunna ta tsagaita da yin dariya ta shige ciki,

  Cike da zolaya Jahad tace"Da alama nan gaba malamar duba zaki koma Hosana,tunda harkin fara yin mafarki Yana zama gaskiya,dama akwai mafarkan da nakeso nima a fassara mun"

  Harara hosana Ta wurga mata,rai a6ace ta sauko daga saman gadon,Sleeping dress ne ajikinta riga da wando,Ganin ta nufi hanyar fita daga ɗakin yasa Jahad yin saurin dakatar da ita"Ke ina zuwa!Salla fa aka tasheki kiyi"

  A ƙule tace"Ina ruwanki,ni zanje in ga rishi ɗinmu ne,"

  "Kinsan Allah karki fita,zoki wuce kije kiyi sallah "

. ko sauraronta batayi ba,Ta buɗe ƙopar ɗakin ta fuce tana ƙunƙuni 


Ɗakin Azmee ta shiga,ko sallama babu,Amrish ta samu agaban wardrobe tana lalubo abayar da zatayi sallah,jin an turo ƙopar ɗakin yasa ta juyo don taga wanene,duk a tunaninta Sehrish ce,

   "Kin dawo kenan"

Turo baki hosana tayi"Ina rishi ɗinmu take?ita nake son gani,"sai da tayi magana sannan ta gane wacece

"Nima bansan inda taje ba,tun da na farka ban sanyata a idanuwana ba,"

  Guntun tsoki hosana taja,duk a tunnaninta,Amrish ƙarya take yi mata,

  Toilet Ta buɗe ta shiga tana neman Sehrish,Jim kaɗan ta fito daga toilet ɗin,Duk amrish na kallonta,Har ƙarƙashin gado ta leƙa bata ganta ba,a ƙarshe Tayi ƙwafa tare da bude ɗakin ta fuce,bedroom ɗinsu ta koma,A lokacin har Abu da Jahad sun kammala Sallah,toilet ta shiga shaf shaf ta ɗauro alwala,

Ta fito ta ɗauko hijabi a wardrobe ta jera dasu,



Bayan an kammala Sallar Asuban,suna dawowa gidan,Abusufyan bai nufi ko ina ba sai upstairs,tsabar sauri kamar zaiyi tuntu6e ya faɗi,Abba na biye da bayanshi,Omar ma yabi bayansu,kowannansu na sanye cikin jallabiya,


Yana shiga bedroom ɗinshi,Yaga wayaam babu kowa,yayi tunanin yana acikin toilet,wuri Ya samu gefen gadonshi Ya zauna yana jiran fitowarshi daga cikin toilet ɗin,Don ayita ta ƙare kowa ma ya huta,

A tsaye Abba ya tsaya Omar na agefenshi,Gabanshi sai faɗuwa yake yi,Sgr ya tafi ya barshi da zullumi,duk yabi yasha jinin jikinshi,

  "Omar me ya hana Rafayet zuwa masallaci"?Abusufyan ne ya jefo mashi tambayar,

  A ruɗe ya soma ƙoƙarin yin magana,En ena ta hana shi"am...um...'

  Cike da mamaki Abusufyan ke kallonshi don a iya saninshi Omar baya en inar magana,Amma sai gashi yau daga ƴar tambaya duk yabi ya dabarbace,

  Wurga idanuwanshi yayi kan Abbansu dake a gefenshi,Suna haɗa ido Omar yayi saurin sunnar da kanshi kasa,Dama ance Labarin zuciya a tambayi fuska,Tuni Abbansu Yayi hasashen wani abu acikin ranshi,kuma ga dukkan alamu Sgr baya acikin toilet ɗinshi,

  "Abusufyan"!ya ambaci sunanshi,

"Na'am yaya,"

"Ina tunanin bayan fitarmu masallaci Rafayet ya fita yin sallah shima,mu ƙara haƙuri mujira dawowarshi,"

  Girgiza kai Abusufyan yayi"ba inda zanje,ina nan ina jiran dawowarshi "

  "shikenan,Omar inason magana dakai," ya ƙarasa maganar tare da ruƙo hannun Omar,Suka fito falonshi,


  "Omar ka faɗa mun gaskiyar abunda ya faru,Ina SGR ya tafi"?cike da tuhuma yake kallonshi,

  A ruɗe Omar yace"Bansan Komai ba Abba,bani da masaniya akanshi,"

  "Hmmmm Omar kenan,Nifa mahaifinka ne,Har akwai abunda zaka iya 6oye mun?fuskarka kawai na kalla raina ya bani cewa wani abu ya faru kuma kana da masaniya akanshi,Shiyasa har kake in ina,"shuru Omar yayi batare daya ce komai ba,

  "Zuciyata har ta karaya,Dan Allah Omar ka faɗamun meya faru?Ina Sgr ya tafi tunda Asuba,"?ganin yadda Ya shiga damuwa sosai,Yasa Omar Ya soma bayyana mashi abunda Ya faru,tun daga kan zuwan da Sgr yayi bedroom ɗinshi,bai 6oye mashi komai ba kaf ya sanar dashi,

  "Innalillahi'wa' Inna ilahirraji'un!"


jiri ne ya soma ɗibarshi,Yayi tangal tangal zai faɗi,da sauri Omar ya ruƙoshi tare da taimaka mashi Ya zauna saman Sofa,Hankalinshi yayi mugun tashi,

  "Nashiga uku Omar,Ashe rafayet bai da hankali!Dama saboda ya aikata mata hakan Ya nemi da mu ƙara mashi lokaci....wlh in har ya kuskure yarinyar nan ta rasa ranta,shima sai na kashe shi,

  "Abba pls,ka rage muryarka,bansan ya zanyi ba,idan Uncle yaji wannan maganar,shiyasa tun jiya nayi ƙoƙarin in dakatar daku akan kubi komai asannu amma kuka ƙi saurarena...."tun kafin yakai ƙarshen maganarshi Abba ya katse mashi hanzarinshi da cewa"Amma Omar rafayet bai kyauta ma kanshi ba,Yayi tunanin idan yayi mata hakan zai zame mashi mafita,Gashi yanzu ya ƙara jefa kanshi cikin tashin hankali,Bansan wani irin bauɗaɗɗen mutun bane shi,Nikaina da nake mahaifinshi Yafi ƙarfina...."Idanuwanshi cike tab da kwalla yayi maganar,

  "Abba,kayi haƙuri da abunda zance,bai kamata kuna ganin laifin Rafayet ba,Irin rayuwar da aka saba mashi da itane,komai yake so shi yake samu,tunfarko kuskuren da aka tabka shine barinshi da kayi Uncle donald ya tafi dashi U.s,tun kafin ya mallaki hankalinshi,Kasan wanene Donald,Yayan Mommy ne,tarbiyar ɗan uwana kwata kwata ba irin tanan bace,ya taso ba a musulmi ba,kuma an damƙashi hannun wanda ba musulmi ba kuma bature,taya rayuwarshi bazata kasance haka ba?Abba kayi tunani,da ace kai da kanka kaba shi tarbiya ya taso a wurinka,Ya kake tunanin zai kasance? ......'ya ɗan dakata da yin maganar yana kallon Abbansu,wanda tuni hawaye sun wanke mashi fuskarshi,tsananin tausayinshi ne ya kamashi,

"Omar ka faɗi gaskiya,Laifina ne wlh,nayi danasani yafi a ƙirga,duk in na tuna cewa Sgr ba a hannuna ya taso ba,Na cutar da rayuwarshi banyi mashi adalci ba,banbari Ya taso a hannuna ba,a lokacin so ya rufe mun idanuna bani da burin daya wuce in faranta ma Alex rai,komai tace tana so gudun kada ranta ya 6aci yi mata shi nake yi,inaji ina gani Sgr ya taso ba'a musulmi ba,kullum in zaku tafi masallaci batare dashi ba,Allah kaɗai yasan irin raɗaɗin da nake ji acikin zuciyata,Donald yazo ya ƙwallafa rai akanshi,Alex tace in bar mashi shi ya tafi dashi can,wlh Omar bada son raina ba,Allah na gani inason Rafayet sosai,na amince ne don tayi mun alƙawarin zata ƙara haihuwa dani,kuma hada ƙarin don bana son ina ganinshi a matsayin wanda ba musulmi ba,shiyasa kawai na yanke shawarar Ƙwara yayi nesa dani,in banda ma rashin hankali irin nawa na ɗauki ƙaramin yaro naba wanda ban haɗa komai dashi ba,ƙanwarshi kawai nake aure,shi ba musulmi ba,Yanayin rayuwarsu da al'adarsu ba irin tamu ba,yanzu da ace rafayet ya mutu a wannan yanayin me zance ma Allah?Akan amanar daya bani!,ya makomarshi zata kasance Ya mutu a matsayin wanda ba musulmi ba,wlh na cuci rayuwarshi........'kasa ƙarasa maganar yayi saboda kukan daya ciyoshi,Tafin hannunshi yasa Ya rufe fuskarshi,shi kanshi Omar hawayen ne sharkaf akan fuskarshi,gefen Abba ya koma Ya zauna,tare da janyoshi jikinshi,Yana lallashinshi,

  "Ba don Allah yasa a wannan lokacin nayi tunanin haɗaka dashi ba,Har ka bisu U.s,kuma cikin sa'a ata dalilinka Ya musulunta,da bansan Ya rayuwarshi zata kasance ba,duk cikin ƴa'ƴana Rafayet ne ban yiwa adalci ba,Ya Allah ka yafe mun...."

  Lallashinshi Omar ya soma yi"Abba kayi haƙuri dan Allah,kadaina zubar da hawayenka,Yakamata muyi ƙoƙari wurin ganin mun nemo inda ya tafi da ita,bamusan a wani Hali suke ciki ba,naji takaici da ban taimaka mashi ba a lokacin da yazo wurina cikin mawuyacin hali,na rufe ido na kore shi da duk hakan bata faru ba,yasan cewa ni kaɗai zan iya fahimtarshi shiyasa yazo wurina,Sam baya acikin hayyacinshi amma haka yazo,Ni kuma maimakon in jashi ajikina in taimakeshin saina yi mashi tsawa nace ya fita ya bani wuri,


Duk wannan maganganun da suke yi akan kunnan Abusufyan dake tsaye abayan sofa ɗin da suke zaune,Kaf yaji abunda suke tattaunawa tun daga farko har ƙarshe,jikinshi yayi mugun sanyi,Hankalinshi  Yayi matuƙar tashi,Har wani jiri yake gani acikin idanuwanshi,


Ba zato ba tsammani suka ji muryarshi ta bayansu,

  "Rafayet ya kashe mun ƴata,"firgigit sukayi gaba ɗaya suka miƙe atare suna kallonshi,Fuskarshi sharkaf da hawaye,

  Aruɗe Abba yace"Abusufyan tun yaushe kake tsaye awurin nan"?

  Muryarshi adisashe ya basu Amsa"tun lokacin da kuka fara magana nake tsaye ina sauraronku....."dakatawa ya ɗan yi da yin maganar,cikin sanyin murya ta wanda ya karaya yaci gaba da magana

"Dan Allah ku faɗamun gaskiya,Sehrish tana raye kota mutu?Ina Rafayet yakai mun ita?Ni ko gawarta ce dan Allah ya maido mun,"

  Wannan maganar da yayi ta ƙarshe ba ƙaramin Kashe masu jiki tayi ba....

  "In sha Allah,Sehrish tana raye Uncle,a duk inda suke yanzu nasan Sgr yana akan gyara 6arnar da yayi mata ne,dan Allah ina ba kowa hakuri amadadin ɗan uwana,wlh duk wani hali da zamu shiga ayanzu bamu kama ƙafarshi ba,Ya tsorata sosai,tunda nake a rayuwata ban ta6a ganin Sgr cikin matsanancin tashin hankali ba irin na yau,nasan ya cutar da ita,Amma duk yayi wannan ne saboda son da yake yi mata,Yana tsoran ku rabashi da ita ne........

  "Omar,Kana goyon bayanshi ne?Ni ƴata ba mutun bace!Allah kaɗai yasan irin muguntar da yayi mata,Rafayet baida Imani baida tausayi,Wlh nayi danasanin aura mashi Sehrish!Kuma duk inda ya shiga acikin garin nan saina nemoshi,Ya dawo mun da ƴata,koda gawarta ce" duk yadda Omar yaso ya fahimtar dashi,Amma yaƙi sauraronshi,a zafafe ya nufi hanyar fita daga falon,Da sauri Abba yabi bayanshi tare da ruƙo hannunshi,idanuwanshi sun rufe rai a6ace yake magana"Ya Hossein ka sake ni,Wlh bazan ƙyale rafayet ba,har ni zai wulaƙanta ma ƴa?Allah hukuma ce zata rabani dashi,"ranshi a matuƙar 6ace yake magana,

  "Kada ka yanke hukunci cikin fushi,muzo muna danasani....."tunkan Abba yakai ƙarshen maganarshi,Abusufyan ya fusge hannunshi,A fusace Ya fuce daga part ɗin,

  Bai ta6a tunanin Abusufyan zaiyi mashi haka ba,ya 6ata mashi rai sosai,

"Abba,ni ina ganin me zai hana A sanarwa Ammi halin da ake ciki,wata'ƙila ta dakatar dashi,

  Girgiza kai Abba yayi"kabarshi kawai,Yadda zuciya ta ɗebeshi ɗin nan bazai saurari kowa ba,Sam baya cikin hayyacinshi,Ni tsorona ma kada yace zai yi driving a irin wannan yanayin da yake ciki,"


Hannu Omar ya tura cikin trouser pocket dinsa Ya zaro wayarshi,Layin Abusufyan ya dinga kira,Wayar nata ringing amma yaƙi ɗagawa,

  "Dama kadaina wahalar kiranshi,don bazai saurareka ba,Ni yanzu babban tashin hankalina bansan a wani hali suke ciki ba,Omar ba yadda za'ae asan Location dinshi"?

  "Abba wayarfa tana a bedroom ɗinshi ya barta,Sannan nayi kokarin kiran Armstrong yaƙi picking,kuma ya toshe duk wata hanya da za'a yin tracking layinsa,'

  "Ina kake tunanin ya tafi da ita"?

  Shuru Omar ya ɗanyi yana kokarin yin tunani akan inda Sgr zai tafi da ita,

  "Da farko nayi tunanin asibitinshi ya tafi da ita don ya dubata,Amma munje har can nida Major bamu same shi ba,nidai inaji araina cewa Suna acikin garin nan,Sgr bai gudu da ita ba,nafi tunanin ya 6oyeta a wani wurine saboda gudun kada Abusufyan yaga 6arnar da yayi mata,Amma Ina da tabbacin cewa zaiyi ƙoƙarin Yi mata aikine da kanshi,"

  Jinjina kai Abba ya ɗan yi,tare da cewa"Dan Allah Omar,kuyi ƙoƙari wurin ganin kun gano mana inda yake,Zan cigaba da kiran Layin Abusufyan,har Allah yasa ya ɗaga,"


Amsa mashi yayi da toh Abba,A hanzarce Ya fuce daga part ɗin,Abba yajima zaune asaman sofa yana ta faman kiran Abusufyan Amma yaƙi ɗaga kiran,A ƙarshe ma sai ya kashe wayar gaba ɗaya,hakan ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba,jiki asanyaye ya fito daga part ɗinshi,Ya sauko downstairs,bedroom ɗinshi Ya shiga,Mommy ya samu zaune gefen gadon,hannunta ruƙe da Cup,Tana ba Junaid magungunanshi yana sha,jin motsinshi yasa suka kai idanuwansu wurinshi,

  "Abba,"Junaid ne ya ambaci sunanshi,

Mommy tace"Ina ka shiga ne?Tunda kuka tafi masallaci ban ganka ba"

  Daƙyar ya iya buɗe baki yace"wani abune ya tsayar dani,"tunkafin ta ƙara tambayarshi,yayi saurin cewa"Junaid ya jikin naka"?

  "Alhamdulillah Abba,Am feeling better,Nayi missing dinka sosai,jiya kace zaka tashe ni mu tafi masallaci sallar Asuba atare,"

  "Am Sorry,Na manta ne,Amma gobe in sha Allah,Zamu fara zuwa masallaci dakai,tunda naga jikin naka ya murmure,"Ya ƙarasa maganar,yana kakaro murmushin dole,Mommy dai ta kafe shi da ido,Don ta lura akwai damuwa atattare dashi,Ga hawaye nan bushe kan fuskarshi,toilet ya shige yaja ƙopa ya rufe,a Gaban sink ya tsaya fuskarshi duk ta yamutse,Ya damu sosai akan son sanin Halin Da Sehrish take ciki,Allah yasa tana raye bata mutu ba,baisan ina zai tsoma ranshi ba,


"Abban Junaid"!mommy ce ta kira shi,daga cikin ɗakin,Da sauri Ya kunna fanfo ya wanke fuskarshi sosai,Kafin Ya nufi ƙopar ya fito daga cikin toilet ɗin,


A tsaye ya sameta,tana jiranshi,

 "Inason magana dakai,"tayi maganar batare data jira amsarshi ba,Ta ruƙo hannunshi suka ja gefe guda,

  "Wani abu ya faru ne?naga canji akan fuskarka,"

  "Babu komai,bana jin daɗi ne kawai,ki tayani da Addu'a,"

  "Ni banyarda ba,inaji araina wani abu ya faru,kawai ka sanar dani,"

   Shiru yayi yana wasi wasi acikin ranshi,kodai ya faɗa mata gaskiyar abunda ya faru,wata'kil ta taimaka mashi,ta wani 6angaren kuma yana jin fargabar ya sanar da ita cewa,SGR yana da Aure,baisan ya zata ɗauki abun ba,

  "Ka tsareni da ido,Ka faɗamun mana,meke faruwa ne"

  Juyawa ya ɗan yi tare da kallon Junaid,Sam hankalinshi baya a wurinsu,Ya lullu6e kanshi cikin bargo,

  Mayar da idanuwanshi yayi kanta"Zan faɗa maki,Amma ba yanzu ba,"

  Ruƙo rigarshi tayi"kodai ka faɗamun abunda ke damunka ko kuma wlh duk inda zaka je saina bika,"

 Gyaɗa kai yayi"shikenan zan faɗa maki,Amma dan Allah inaso ki fahimce ni........."natsuwa tayi tana sauraronshi,gaba ɗaya ya kwashe duk abunda ya faru tun daga kan auren Sgr da Sehrish da sukayi a 6oye har izuwa aika aikan da yayi mata yau,Don ance za'a rabashi da ita,Yayi tsammanin Mommy zata Balbaleshi da masifa,musamman da yaga ta kafe shi da blue eyes ɗinta,batare data ƙyafta ba,


"kiyi haƙuri dan Allah,nasan nayi maki laifi da ban sanar dake ba,na damune sosai akan halinshi,Shiyasa na ɗauki shawarar abokina akan inyi mashi aure ko zai canza,wannan dalilin ne yasa mukayi amfani da wannan damar muka shirya hakan tsakanina da Abusufyan"muryarshi asanyaye ya ƙarasa maganar,yana kallonta,


Jinjina kai ta ɗan yi kafin tace"banji zafin auren da kayi mashi batare da sanina ba,Amma naji haushin Tursasa mashi da kuka yi akan ya saketa,Meyasa?Gashi yanzu kun jefa rayuwar yarinyar cikin hatsari,U made a mistake ku dukanku,U know him better than any other person, tunda ya nuna yana son tafiya da ita dat means yana sonta ne,tunda kasan yana da masu yi mashi aiki,,"ranta a6ace tayi maganar,


"Wlh nayi danasani sosai,laifin da rafayet yayi shine dabai miƙa wuya ba,Ya nuna cewa yana son ya tafi da ita don taci gaba da yi mashi aiki,maimakon Ya amince zai tafi da ita amatsayin matarshi,wannan maganar tashi ce ta harzuƙa Abusufyan harya tursasa mashi,Ni na goyi bayan Abusufyan ne,Saboda kafiyar da rafayet ya nuna,babu yarda banyi dashi ba akan Ya soke yarjejeniyar,amma yaƙiya,duk da dama bamu aura mashi ita da sunan yarjejiniya ba,tun tana yarinya Abusufyan ya bashi ita,........."dakatawa yayi da yin maganar yana sauke ajiyar zuciya,

  Jinjina kai Mommy tayi kafin ta soma magana"Yanzu menene solution?Gashi babu wanda yasan inda ya tafi da ita,balle asan wani hali suke ciki,Babban tashin hankalinma idan Mahaifiyar yarinyar nan tasan cewa bata acikin gidan nan,Dole ta damu sosai,"_

  "Ke zaki taimaka mun,kafin Allah yasa mu gano inda suke,kisan yarda zakiyi wurin kawar mata da tunaninta akanta,"

  "Shikenan,Zanyi hakan,Amma pls kuyi kokari kafin rana ta faɗi asan inda suke,Sannan yakamata a bincika ɗaya daga cikin guest house ɗinmu,Zai iya zuwa can"_

  Hugging ɗinta yayi don ba ƙaramin kwantar mashi da hankali tayi ba,

  "Nagode sosai da shawarar da kika bani"ya ƙarasa maganar,tare da kama hanyar fita daga dakin,

  "Allah yasa aje asa'a,"_

 Ya amsa mata da Ameen kafin ya fuce,


Ta jima atsaye cike da zullumin abunda zai biyo baya,bata ji daɗin abunda Sgr yayi ba,tashiga damuwa sosai akan halin da Sehrish take ciki,fatanta Allah yasa yarinyar bata mutu ba,


Fucewa tayi daga cikin ɗakin,Ta nufi kitchen,Oumma tasamu tare da Hajiya azeema da Saude suna shirya abincin karin kumallonsu,kamar yadda suka yi jiya,Suna aiki suna fira,tunda tashiga kitchen ɗin,idanuwanta na akan Abu dake tsaye agaban Gas cooker tana motsa Farfesun da ta ɗaura,

  Hajiya azeema ce ta lura da ita"Ina kwana Aunty,kin tashi lafiya,"daƙyar Mommy ta ƙaƙaro murmushin dole,

  "Lafiya lou,sassanunku da aiki,Tun ɗazu naso na shigo kitchen ɗin,na tsaya wurin Junaid ne,"

  Juyowa abu tayi suka haɗa ido da Mommy,murmushi tasakar mata,cikin girmamawa abu ta gaisar da ita,mayar mata da martanin murmushin tayi tare da amsa mata gaisuwar,Saude ma ta gaishe da ita,

  Cike da zolaya,Mommy tace"Amaryar harrisun gwaggo,yau naga hada make up akan fuskarki,Shi kikayi ma kwalliya,"Cike da jin kunya,Saude ta ajiye wuƙar da take yanka kayan lambu da ita,Ta sanya tafin hannunta akan fuskarta,dariya su kayi gaba ɗayansu,

  "Kamar wata me kunya,Ae gwaggo ta sanar dani komai,abar kaza cikin gashinta dai kar a fige,"ta ƙarasa maganar da zolaya,

  A shagwa6e Saude tace"dan Allah Aunty azeema kidaina yarda da maganar Gwaggo....."bata ƙarasa maganar nan ba,Gwaggon katsina ta faɗo cikin kitchen ɗin,Jikinta sanye da waɗannan kayan baccin nata na gado ƴan ƙasar turƙiya,Duk sunyi squeezing sun cukuikuye,kanta ko kallabi babu duk hurhura,ta ƙwama glass baƙi kato akan fuskarta,

  Tsayawa tayi tare da ruƙe qugu tana kallonsu ɗaya bayan ɗaya,kafin tace"Waye ke kiran sunana?Wato ina can ina bacci ana nan ana yi mun munshari,"

  Ƙumshe dariya sukayi gaba ɗayansu,dabsauri hajiya Azeema ta nuna Saude"Kin ganta nan itace ke kiranki,"

 Uwar harara gwaggo ta watsa ma saude"Munafuki dai baiji daɗin rayuwarshi ba,Ae naji abunda tace,Wato adaina yarda da maganata,Ni ga mahaukaciya ko?Wlh saude kiji tsoran Allah,A haka kikeso In bari Harrisu ya aureki?kina yi mun rashin kunya?Allah ya kiyaye,Ae sai dai ki koma rigarku ki samu irinsu jauro ki aura badai harrisuna ba,"tayi maganar tana murguɗa mata baki,

  "Gwaggo nifa ba haka nake nufi ba,dan Allah kiyi haƙuri idan na 6ata maki rai,

  Guntun tsoki taja,kafin ta mayar da idanuwanta kan Abu,Lokaci guda ta soma washe baki"Ina ƴa'ƴan Abusufyan ɗina suke?yau har mafarkinsu nayi,"

  Murmushi abu tayi"Gwaggo suna nan cikin ƙoshin lafiya,"

  "Madallah,bari naje na dubosu,dan Allah ashirya masu lafiyayyen abinci,suci su ƙoshi,"

 Hankalin Mommy ne ya tashi,Gudun kada gwaggo taje ta taras babu ɗaya daga cikinsu,Da sauri ta dakatar da ita,

  "Gwaggo,ki tsaya mana,ga farfesu ya sauka,Yakamata ki ɗanɗana girkin Amaryar Abusufyan ɗinki,"

  A sukwane ta juyo fuskar nan ɗauke da murmushi"dagaske abusufyan zaiyi aure"?

 "Eh mana,Za'a maida aurenshi da zainabu abu,kinga nan bada jimawa ba zaki samu wasu ƴa'ƴan na Abusufyan,"

  Wani irin farin cikine ya lullu6e gwaggo,Hada sanya hannu ta dafe saitin zuciyarta,

  "Wlh bakiji daɗin da naji ba,Wayyo Allahna,Ranar dana daɗe ina jira gashi zata zo,Zainabu abu zata koma ɗakin Abusufyan,Ga harrisu shima zai angwance,dole inyi rawa," ta ƙarasa maganar tana kwaso shoki da hannuwanta,Gaba ɗaya suka fashe da dariya,


A 6angarensu Hayaam,Sun fuskanci matsanancin tashin hankali A gidan malam liman,Duk sun rame sun kode saboda yunwa,Ga tsangwamarsu da akeyi,aikin gidan gaba ɗaya ya dawo kansu,sune wanke wanke,Sune shara hatta dabbobin gidan suke wanke garkensu,duk yawan mutanan gidan Suke girka masu abinci,a ƙalla yana da ƴa'ƴa kusan talatin,Ga matanshi huɗu,Sun tsanesu sun addabi rayuwarsu,Wata rana kwatsam sai ga mahaifinsu Ya dawo Abie,Ya zama cikakken mutun,Yanzu babu asirin mammy ajikinshi,tun lokacin da Amal ta bashi waɗannan kuɗin ta gudu wurin Amani,Shima Ya gudu zuwa kano wurin wani Abokinshi,Acan ya fara ta6a kasuwanci,Labarin mutuwar mammy ne ya riskeshi acan ta hanyar wani ɗan uwanshi da suka haɗu dashi a nan kano ya sanar dashi komai daya faru ya kuma bashi shawarar ya dawo ya rungumi ƴa'ƴanshi,tunvkafin ya rasasu,


Wannan dalilin ne yasa Abie yayi tattaki zuwa Maiduguri,Lokacin da yayi arba dasu Abra,Hankalinshi ya tashi sosai,A ranar ya kwashe su zuwa gidansu,sunyi kuka sosai sun nemi yafiyarshi,Yace masu komai ya wuce tunda sun shiryu,sati ɗaya suka yi a gida,Ya tattara su gaba ɗaya ya tafi dasu kano,Saboda zama maiduguri bazaiyiwu ba,mutane sun addabi rayuwarsu,Ko ƙopar gida ba damar su leƙa sai ahau zaginsu ana nunasu da yatsa,


Gidan haya ya fara kama masu,Sai kuma ga Kuɗi Amani ta turo masu ta account ɗin hayaam kusan miliyan ɗaya da rabi,dama yana da wasu kuɗi hannunshi na gidansu daya saida kafin su baro,kuɗi suka cika 3 million Ya sama masu gida irin na masu rufin asiri,Ya siya masu,Ba ƙaramin daɗi suka ji ba,Yanzu basu da sauran damuwa,rayuwarsu ta canza sosai,Har makarantar islamiyya abie ya sanyasu,wannan kenan,





*Very Soon Littafi zai ƙare sai dai kawai kuji nace Alhamdulillah,Ga azumi  yana zuwa Allah yasa muna da rabon ganin watan ramadan👌Ga duk mai buƙatar littafin Abban sojoji yayi mun magana kai tsaye ta layina,Amma fa whatsapp kawai banda kira,08103884440*




 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*



*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




_Double page ne,Saboda jiya da bana jin daɗi bansamu nayi ba,that's why na hada maku pages biyu💋_



Lokacin da Abusufyan ya fita a fusace ya shiga motarshi yayi mata key da gudun gaske ya fusgeta,shi kanshi baisan ina zai dosa ba,A ƙarshe gefen bishiya yayi parking ɗin motar Ya kifa kanshi jikin steering,tuni hawaye sun wanke mashi fuskarshi,Bai ta6a tunanin Sgr zaiyi mashi haka ba,duk irin yadda yake treating ɗinsu,tun suna yara yake hawa jirgi daga Turkey zuwa U.s don kawai ya gansu,saboda ƙaunar da yake yi masu shi da Omar Amma sai gashi yau Sgr Yayi mashi abunda bazai ta6a mantawa ba,Tsananin damuwa ne akan fuskarshi,zuciyarshi sai tafarfasa take yi,Zufa tuni ta wanke mashi fuskarshi,cikin shessheƙar kuka Ya furta"Why Rafayet!why!ban ta6a tunanin haka kake ba"lumshe idanuwanshi yayi,Anan Ya yini gefen bishiyar,


Duk ta damu saboda rashin ganin Sehrish ga wayarta dake ajiye saman side drawer tun safe,tun tana zarya acikin bedroom ɗin harta fara tunanin Zuwa nemanta,hijab ta zura ajikinta ta buɗe ƙopar ɗakin ta fito,miƙar hanya tayi tana tafiya,Adai dai ƙopar bedroom ɗinsu ta tsaya,Hannu tasa tayi knocking ɗin ƙopar,


Jahad ce ta buɗe mata ƙopar,jikinta na sanye da pakistan wando Burgujeje pink da Riga fara mai dogon hannu,daga ƙasan rigar anyi mata adon stones,Ta yafa mayafin a ƙafada,Yayin da ta saki sumar kanta,


Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Amrish"ta ƙarasa maganar tare da yin hugging ɗinta,Suka rungume juna,bayan sun kammala gaisawa Amrish ta soma tambayarta

  "dama ina neman Sehrish ne,tun asuba dana farka banganta ba,bansani ba ko tazo wurinku ne,ko ta fita daga gidan," 

  Gaban jahad ne ya ɗan faɗi don ita kanta duk yinin ranar bata sanya Sehrish a idanuwanta ba,

  "Gaskiya bansan inda taje ba,nima duk yau banganta ba,Amma abunda za'ayi bari na bincika cikin gidan may be ko tana wurin Aunty azeema ne,"

  Juyawa Amrish tayi,da sauri jahad ta ce"Ki shiga mana,Ga Hosana can tana kallon drama,". 

  Murmushi ta ɗan saki tare da gyaɗa kai tace"okey,"Matsa mata hanya Jahad tayi ita kuma ta shige ɗakin,A kwance ta samu Hosana ta baje saman gadon,Ga laptop agabanta ta ƙura ido tana kallo,wuri ta samu daga gefe ta zauna,

  "Hosana,ya kike,"

Juyowa hosana tayi fuskar nan a yamutse tace"Lahiya,"ta mayar da idanuwanta kan laptop din,zama sosai Amrish tayi suka cigaba da yin kallon atare,




Tana ƙoƙarin fitowa daga Toilet,tajiyo Muryar Mommy tana sallama,Ƙarasa fitowa Hajiya Azeema tayi jikinta sanye da bubu ta atampa ,fuskarta ɗauke da murmushi ta amsa mata"Wa'alaikum salam,Aunty ki shigo daga ciki mana,"

  turo ƙopar mommy tayi jikinta na sanye da jallabiya fara,babu mayafi akanta,sam babu kwanciyar hankali atattare da ita,ganin fuskarta a hargitse yasa Hajiya azeema tace"Aunty Lafiya naga kamar akwai damuwa a fuskarki,"

  Mommy tace"Ina fa lafiya,Rafayet yayi aika aika,yabarmu da zullumi,"tayi maganar yayin da take zama daga gefen gadon nata,

  "Me Rafayet yayi"?

"Hmmmm,ɗazu Abban Junaid ke sanar dani,Nasan kinsan da auren sirrin da su kayi mashi ko"?

  jinjina kai hajiya azeema tayi"Eh,nasani,"

  "Oh ashe kema kinsani,Ni aka mayar shashasha,babu wanda ya sanar dani,"

  Murmushi hajiya azeema ta ɗan yi"Naso in sanar dake Aunty,Kawai ina fargabar yadda zaki ɗauki abunne,"

  Ta6e baki Alex ta ɗan yi,

"Amma meya faru ne"?

Nan Mommy ta kwashe duk abunda Abba ya sanar da ita,tun daga farko har ƙarshe ta sanar da ita,..

Hannu Hajiya Azeema ta ɗaura akai,Hankalinta amatukar tashe take ambaton"Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un!Nashiga uku!"duk tabi ta ruɗe,

Cike da takaici Mommy taci gaba dacewa"Wlh tun safe ake ta faman nemanshi ba'a ganshi ba,Ni yanzu babban tashin hankalina shine a wani hali yarinyar take ciki!Ina Rafayet ya kaita!Tana raye kota mutu"?.

Tuni idanuwan hajiya azeema sun cicciko tab da kwalla,bakinta ya mutu,Jikinta yayi sanyi,

  "Amma rafayet bai kyauta mana ba Allah,duk da nasan yayi ne saboda son da yake yi mata,Yaji tsoran su rabashi da ita ne amma....."tunkan takai ƙarshen maganarta,Mommy ta katse mata hanzarinta"aini banso Suka tursasa mashi akan ya saketa ba,Wannan shine kuskuren da suka aikata,Babu wanda baisan halin Rafayet ba acikinsu,tunda ya nuna yana son ya tafi da ita,to tabbas Yana sonta ne,Ni nasan wanene rafayet,Wlh da ace baison yarinyar nan,ko kallo bata ishe shi,balle har ya aureta,Amma tunda yayi accepting aurenta as a contract wlh yana sonta ne,So bana wasa ba,that's the reason why yaƙi sakinta,Shima kuma da laifinshi,komai sai yace zai nuna ƙarfi,Ai akwai abunda ƙarfi ko dukiya basa iya siyawa mutun,duk da ana siyan soyayya da kuɗi,Amma bakowace zuciya bace zaka iya mallakarta cikin sauƙi ba,kuma hada ƙarin shi bai ta6a soyayyaba,balle yasan yarda zai baiyanata,"


Jinjina kai Hajiya Azeema tayi"Allah sarki Sehrish,wlh na tausaya mata baiwar Allah,banji daɗin abunda ya faru ba,Yanzu ya zamuyi?wlh duk na ƙagu da insan a wani hali take,Ga Abusufyan ma,Naji kince Ya fita ba'a san inda yake ba,"ta ƙarasa maganar tana kallon Mommy,Duk sun shiga damuwa,

  "Tun ɗazu suka fita nemansu,Amma har yanzu shiru babu wani labari,yanzu sai dai muyi ta jiran tsammani"acewar Mommy,



Kafin Hajiya azeema ta ƙara cewa wani abu,Jahad ta kwankwaso ƙopar dakin,

  "Wanene"

"Ni ce Aunty azeema,"kallon juna sukayi ita da Mommy kafin tace"Shigo daga ciki,"

Da sallama abakinta ta shiga ɗakin,cikin girmamawa Jahad ta gaishe su,Suka amsa mata,

  "Ina neman sehrish ne,Na bincika ko'ina banganta ba,Nayi tunanin ko tazo wurinki ne," 

  Jin wannan maganar yasa hankalinsu ya tashi,shiru su kayi na wani lokaci batare da sun amsa mata ba, 

  ƙoƙarin juyawa tayi zata bar ɗakin,Da sauri Mommy tace"Zonan,Jahad ce ko Hosana?"

Cikin sanyin murya tace"Jahad ce,". 

  Azeema tace"Baki bambantasu ne,Ae wannan duk tafisu natsuwa,Hosana kuma tafi su jiki,har ƴan kumatu gareta,kuma ita sam bata da natsuwa,ta cika ƙiriniya,"

Murmushi Mommy tayi tare da cewa"masha Allah,Juliet ɗin Junaid ce kenan,ae ko jiya sai da yayi mun maganarta,"

cike da mamaki Jahad ta ɗanyi murmushi,jin tace Junaid yayi mata maganarta,bayan ita ko son kallonta baiyi,

  "Amma Oummanku tasan cewa Sehrish bata nan"?hajiya azeema ce tayi mata tambayar,

  Girgiza kai tayi"a'a bata sani ba,Nima Yanzu nake ji wurin Amrish,tace tun da safe bata ganta ba,"

  Jinjina kai hajiya azeema ta ɗanyi kafin tace"Shikenan,koda ace Oummanku ta tambayeki game da sehrish,ki sanar da ita cewa Sun fita ita da babban yayanku,zasu dawo in sha Allah,"

  "Shikenan,zan sanar da ita hakan,"


Gyaran murya Mommy tayi mata,ɗagowa Jahad tayi cike da jin kunyarta take kallonta,

  "Munyi magana da Junaid,Na bashi shawara akan yazo wurinki kuyi magana,nasan zaki taimaka mashi sosai,"

  Ƙayataccen murmushi Jahad,ta saki daƙyar ta iya cewa"in sha Allah Mommy,"tana kai ƙarshen maganar ta fuce da sauri,murmushi suka saki gaba ɗayansu,daga bisani kuma suka cigaba da tattaunawarsu,


A 6angarensu Omar kuwa,Yinin ranar suna wajen neman Sgr,duk wani wuri da suke tunanin zasu same shi sunje basu gansu ba,lamarin ya fara bashi tsoro,


Har wuraren ƙarfe Goma na dare babu wani Labari me daɗi,duk sun shiga matsananciyar damuwa,ga Abusufyan yaƙi dawowa cikin gidan,Abu kuwa tunda Jahad ta sanar da ita cewa Sehrish sun fita tare da babban yayansu,bata wani sanya damuwa aranta ba,don tasan cewa duk inda take tana cikin ƙoshin lafiya,Tun da ba ita kaɗai bace,duk da ta ɗan damu ganin har goma tayi Basu dawo ba,


Damuwace ta ishi Abba,A ƙarshe ya yanke shawarar sanarma Ammi halin da suke ciki,wata'ƙil ta taimaka wurin shawo masu kan Abusufyan,A lokacin tana kishingiɗe saman gadonta,Abba yayi sallama daga waje,Amsa mashi sallamar tayi,A nutse ya tura ƙopar ɗakin ya shiga,cike da girmamawa ya samu wuri daga ƙasa ya zauna tare da lanƙwashe kafafunshi,cikin sanyin murya ya gaisar da ita,miƙewa daga zaune ammi tayi yayin da idanuwanta ke akan fuskarshi,tayi mamakin ganin jirwayen hawaye,

  Hankali aɗan tashe tace"Hossein!Lafiyarka kuwa?Hawayen menene akan fuskarka"kamar jira yakeyi tayi magana,nan take ya fashe mata da kuka kamar ƙaramin yaro,duk tabi ta ruɗe,

  "Ka faɗamun meya faru ne?Ka tasani gaba kana yi mun kuka,idan wani abu ke damunka bazaka fadamun ba!"

  Cikin shessheƙar kuka ya soma magana"Abubuwa ne sunyi mun yawa ammi,daga wannan sai wannan na rasa yadda zanyi da rayuwata"

  "Ka natsu ka sanar dani meke damunka,"daƙyar ya samu ya tsagaita da yin kukan,a tsanake ya kwashe duk abunda ya faru ya sanar da ita,


Jinjina kai ammi tayi yayin da idanuwanta ke akanshi sai da yakai ƙarshen maganarshi tukunna tace"Gaskiya banji daɗin wannan abun da kuka aikata ba,nayi masu auren yarjejeniya batare da kun sanar dani ba,sam bakuyi tunani ba wlh,Haba hossein da hankalinka da tunaninka...."ta ɗan dakata da yin maganar tana kallonshi,sosai hawaye ke zuba akan fuskarshi,

  "Dama dole kuga ba daidai ba,kuskure ne tun farko kun riga da kun tabka,Ni yanzu bansan ya zanyi ba,tunda baku yi shawara dani ba lokacin da kuka shirya yi masu auren,bani da abunda zan iyayi maku.... "Tunkan takai ƙarshen maganar,Abba ya zukunna agabanta ya ruƙe hannayenta,"Duk duniya bani da mai sharemun hawayena in bake ba,Dan Allah ki taimaka mun Ammina,ni kaɗai nasan irin raɗaɗin da nake ji acikin zuciyata"

  Jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,tafin hannunta ta sanya tana share mashi hawayenshi,

  "Shikenan,kadaina kukan ya isa haka,idan ba so kake nima in fara kukan ba,"

  Da sauri yace"nadaina ammina,bazan ƙara ba,"

  Jinjina kai ta ɗanyi kafin tace"abun da ciwo,banji daɗin abunda Rafayet ya aikata ba,Yanzu in mahaifiyar yarinyar nan taji ya kuke tunanin zata ɗauki abun?sam bakuyi tunani ba,Shi kuma Abusufyan baikyauta ba abunda yayi maka,Zai dawo ya same ni ne,Sannan inaso ka kwantar da hankalinka,ni nasan cewa duk inda rafayet yake a halin yanzu yana tare da yarinyar,koba komai ita ƴar uwarshice,Jinin dake yawo ajikinta shike yawo ajikinshi,zai bata kyakkyawar kulawa,tunfarko kuskuren da kukayi na tursasa mashi akan ya saketa shine duk yajawo wannan abun,da ace kun bi a hankali da duk baza azo ana danasani ba,"ta ƙarasa maganar tare da nuna mashi gefenta alamar yazo ya zauna,


Miƙewa Abba yayi tare da komawa gefen ammi ya zauna,kwantar da kanshi yayi asaman kafaɗarta,Wani irin ciwon kaine ke damunshi,


"Kayi hakuri da duk abunda ya faru,banason kana sanya damuwa aranka,in sha Allah komai zai tafi daidai,zan tayaku da addu'a akan Allah Ya bayyanar dasu"sosai ammi tashiga tausarshi,tana kwantar mashi da hankali,

  "Ka kwanta ka huta,zanyi kokarin jaraba kiran layinshi,"

  "To ammi,"ya amsa mata,kafin ya gyara kwanciyarshi A saman gadonta,


Miƙewa ammi tayi gaban drawer taje tare da kai hannu ta ɗauki wayarta,Layin Abusufyan ta kira,Cikin sa'a wayar ta soma ringing,yana ɗaga kiran ta kara wayar a kunnanta tunkafin yayi magana tayi saurin cewa"Duk inda kake kadawo gida yanzun nan,ina son ganinka aɗakina,Umarni nake baka,"tana kai ƙarshen maganarta batare da ta jira amsarshi ba,Ta katse kiran,


Safa da marwa ta shiga yi aɗakin tana jiran zuwanshi,kusan minti goma sha biyar da yin wayar,Motar Abusufyan ta kunno kai cikin gidan,bayan yayi parking ɗinta ya fito jiki babu ƙwari ya nufi cikin gidan,Yana shiga babban falon gidan Ya taras da mutanan gidan,bai bi takan kowa ba Ya wuce ɗakin Ammi,da sallama abakinshi Ya shiga ɗakin,


Tunda ya shigo ammi ta kafe shi da ido tana kallonshi,yaji jiki ba ƙadan ba,

  Daƙyar ya iya gaisar da ita"ina yini ammi,"bata amsa mashi ba,Sai nuna mashi wuri tayi saman sofa ɗin dake dakin,Ya zauna yana faman sauke ajiyar zuciya,sai daga baya ya lura da Abba dake kwance ya rufe idanuwanshi,

  "Meya haɗaka da ɗan uwanka'?tayi tambayar tamkar batasan komai ba dangane da abunda ya faru,a ruɗe yace"Wani abu yace nayi mashi"?

  "Kafi kowa sani ae,meyasa Abusufyan kafiye son zuciya ne?Sam baka da kara duk irin halaccin da hossein yayi ma ƴa'ƴanka tunkafin yasan cewa jininka ne su,abunda kayi mashi sam bai dace ba,kuma abunda Rafayet Ya aikata ma ƴar wurinka,Ni banga laifinshi ba,Nafi ganin laifinku ku da kuka shirya auren yarjejeniyar,In har kayi niyyar bashi auran ƴarka don me zaka tursasa mashi akan ya saketa?Gashi yanzu kun jefa rayuwar yarinyar cikin hatsari.....'tunkan takai ƙarshen maganar,Abusufyan yace"Dama nasani,ba sona kikeyi ba,Shiyasa har kike goya mashi ba,yanzu duk girman laifin da rafayet ya aikata baki ga laifinshi ba,Saboda shi jinin Hossein ne,dama can kinfi sonshi ae......'

Bai ƙarasa maganarba,Sakamakon tsawar da Abba ya daka mashi,a lokacin ya miƙe daga zaune ya sauko da kafarshi ƙasan gadon,

  "Dama abunda kake tunani kenan!?Meyasa Abusufyan?Wlh idan ka biyewa zuciyarka Zata kaika ta baroka ne,dani dakai duk abu ɗaya ne awurin ammi,baikamata ka furta mata haka ba,ni a tunani na ƴa'ƴana naka ne,Ƴa'ƴanka nawa ne,Ban ta6a tunanin ina da bambanci dakai ba,wlh nafika jin raɗaɗin abunda Rafayet ya aikatama Sehrish,Yinin yau ko ruwa bansa abakina ba saboda damuwar halin da suke ciki...."hawaye ne suka wanke mashi fuskarshi,

  Maganganun Abusufyan sunyi matuƙar ƙona mashi rai,musamman ammi,tayi mamakin yarda harya iya furta mashi hakan,Son ƴa'ƴa ya rufe mashi ido har yake ganin tamkar ba'ayi mashi adalci,

  "Ammi dan Allah ki ƙyaleshi kada kice komai,kibarshi kawai ya tafi,Abusufyan yanzu baya acikin hayyacinshi,komai ya fito bakinshi zai iya faɗa mana,"

 Ranta a6ace tace "Banji daɗin kalamanka ba Abusufyan,ban ta6a tunanin zaka iya furta mun haka ba,kada ka manta dakai dashi dukanku ni na haifeku,kuma banta6a nuna banbanci atsakaninku ba,Abu ɗaya danasani shine Hossein yafika sauƙin kai,Zan iya cewa duk cikinku babu wanda yakaishi haƙuri,yana yi mun biyayya sosai,aduk lokacin dana shiga wani hali hossein shi nake fara gani,yana faranta mun rai sosai ba kamar kai ba.....'daƙyar takai karshen maganar,idanuwanta sun cika tab da kwalla,hankalin Abusufyan ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin ammi na shirin zubar da hawayenta kanshi,sai ma lokacin ya farga don baisan ya furta mata maganar  ba,ranshi ne ya 6aci sosai,idanuwanshi sun rufe,


Saukowa yayi daga saman kujerar,Ya zuƙunna saman guiwowinshi agabanta,

Cikin sanyin murya ya soma magana"dan Allah ammi kiyi haƙuri,banaso nayi silar da hawayenki zasu fita,hakan zai ƙara jefa rayuwata cikin matsala,na tuba bazan ƙara ba,Komai kikeso wlh shi zanyi,yaya hossein...."ya ambaci sunanshi tare da mayar da idanuwanshi kanshi"Kayi haƙuri da abunda nace yayana nakaina,nasan kalamaina sun 6ata maka rai,zuciyata ce sam batayi mun daɗi,Nafi kowa sanin yadda kakeson Jini na..."duk yabi ya ruɗe,

    "Ka tashi ka koma ka zauna,inason magana daku,"miƙewa yayi jiki na rawa ya koma saman kujerar ya zauna,gwanin ban tausayi ammi ke kallonsu,

  "Kada ku bari son ya'ya yayi silar da zaku raba kanku,bana fatan hakan ya faru,Ban goyi bayan abunda Rafayet Ya aikata ma ƴar wurinka ba,Kuma ban goyi bayan kowannanku ba,dakai dashi,duk abunda ya faru Laifinku ne,Tunda ku kuka haɗa aurennasu,Sannan kuma kuka soma ƙoƙarin tursasa mashi akan ya sake ta,wanda silar hakan ne yasa shi Rafayet ɗin yayi mata aika aikar da yayi,maimakon daya nuna yana son Ya tafi da ita ku ƙyaleshi yayi rayuwarshi da matarshi,amma sai kuka matsa lamba akan ya saketa bacin kuma kunfi kowa sanin halinshi,Wannan shine kuskuren da kuka aikata......"

  Shiru ta ɗanyi tana kallon kowannansu,gaba ɗaya sun natsu suna sauraronta,cigaba da magana tayi"Abusufyan amadadin Rafayet ina mai baka haƙuri,tabbas ya cutar da ƴar wurinka,Abunda yayi sam bai kyauta ba bai sa hankali ba,Amma inaso ka sani,Duk yayi wannan ne saboda tsananin son da yake yi mata,Yana gudun ku rabashi da ita ne shiyasa ya yanke shawara ya aiwatar da hakan,A tunanin shi in yayi mata hakan ba zaku iya raba shi da ita ba,Sai dai kash ya tabka babban kuskure,Ya kusanceta a lokacin da yake cikin fushi,shi kanshi yanzu nasan yayi danasanin abunda ya aikata mata fiye da tunaninku,kuma duk yacce kuka kaiga jin ɗacin abunda ya aikata mata wlh baku kaishi ba,Yafi ku jin raɗaɗin abunda yayi mata acikin zuciyarshi,da ace da son ranshi yayi mata wlh bazai gudu da ita ba,Anan zai bar maku ita,Ya tafi yabar kasar,Ya zakuyi dashi?tayi tambayar tana kallonsu,duk jikinsu yayi sanyi,

  "Duk inda yake yanzu nasan cewa yana tare da ita,Kuma zai gyara 6arnar da yayi ne,Sannan inaso ku kwantar da hankalinku,in sha Allah zasu bayyana ne,kuma kudaina tunanin cewa ko ta rasa ranta ne,tana araye bi'iznillah,kuma zata ji sauƙi ta dawo kamar yadda take ada"sosai ammi tayi masu nasiha,duk ta kashe masu jikinsu,

  A ƙarshe tace"idan har Allah yasa Rafayet ya dawo da yarinyar nan,zan zaunar dasu agaban kowa zan tambayi ra'ayinsu,idan har duka suka amince zasu rayu da junansu,To bana so wani daga cikin ku ya ƙara tada maganar saki,Idan kuma har ita jikar tawa ta nuna cewa batason shi,Zanyi adalci atsakaninsu in raba auransu,'


Ajiyar zuciya kowannansu ya sauke,Abusufyan yace"In sha Allah,nima bazan ƙara tursasa mashi akan ya sake ta ba,"

Abba kuma yace"Duk hukuncin da kika yanke masu dai dai ne,mungode sosai da irin nasihar da kikayi mana,kuma in sha Allah,ba zaki ƙara jin kanmu ba,"

  "Allah yayi maku Albarka,Allah ya ƙara hada kan zuri'armu,"

Atare suka amsa mata da Ameen,

"Amma ammi,bansan ya zanyi da zainab ba"acewar Abusufyan 

  "Kada ka damu,idan ta tambayeka akan Yarinyar,ka sanar da ita komai game da auran yarinyar,amma bance ka faɗa mata ainihin abunda ya faru ba game da abunda rafayet ya aikata mata,Idan kace mata Mijinta ya tafi da ita,Bazata damu ba,"

  Jinjina kai yayi"shikenan nagode sosai,Zan sanar da ita hakan,

    "Yanzu yakamata mu mayar da hankali wurin neman inda ya tafi da ita,",'

  "Zamuyi kokarin yin hakan,Yanzu haka Omar tun safe suke gararin nemansu acikin garin nan,Amma har yanzu shiru bamu ji daga gare shi ba,"Abba ne yayi magar,

  "Allah ya taimaka,zasu bayyana ne nasan zai dawo da ita ne"daga haka ta basu iznin tafiya,Miƙewa sukayi atare har sun kusa fita daga ɗakin,Ammi ta kuma kiran Abusufyan Dakatawa yayi tare da juyowa ya dawo wurinta,

  Dafa kafadarshi tayi"game da abunda ka yiwa yayanka,Ya tsaya mashi arai,yaji zafin abun har hawaye saida ya zubar akanka,sam banji daɗi ba daka buge mashi hannunshi don yana ƙoƙarin dakatar dakai,kafi kowa sanin yadda Hossein ke tsananin sonka,yafi kowa son ganin farin cikinka,Bai kamata kayi silar shigarshi cikin damuwa ba,Idan kukayi hakuri komai mai wucewa ne,Wata rana sai dai muji ana ɗaura auren jikokinku,".  

  Murmushi Abusufyan yayi,cike da jin kunya ya sunnar dakanshi ƙasa,

  'Koda yake naji ƙishin ƙishin wurin azeema cewa kanaso ka maida auranku da Zainab,dagaske ne'?

  Hannu yasa tare da shafa ƙeyarshi,

Murmushi ammi tasaki"Allah yasa ina da rabon sake ganin wasu Ƴa'ƴan na Abusufyan,"ƙasa kasa ya amsa mata da Amin,

  Hannu tasa ta ɗan bugi kafaɗarshi"rasa kunya,wayace maka ana amsawa,da ace yayanka ne,Cikin zuciyarshi zai amsa mun,"dariya sosai Abusufyan yayi,

   ɗaure fuska ammi tayi"Nama tuna fushi nake dakai,Ni banji daɗin maganar da kayi ba,nacewa wai nafison Yayanka akanka,kasan irin yadda nake jinka acikin zuciyata"?tayi tambayar tana kallonshi,duk tana yin wannan ne don ta faranta mashi ranshi,ko hankalinshi ya kwanta yadaina sanya damuwa aranshi,

  "Kiyi hakuri mommyna,bazan ƙara ba,nima nace ne kawai,ba don ina nufin haka ba,bana jin daɗin zuciyata ne shiyasa harna furta hakan batare dana tauna maganarba,"

  Shafa sumar kanshi tayi"Allah yayi maka albarka,dan Allah ka sanyaya zuciyarka,Allah ya baka hakuri da juriyar cinye wannan jarabawar,'

  "Ameen ameen Ammina,"rungumeta yayi sosai ajikinshi,Yaji daɗin kalamanta,Daga bisani yayi mata sallama Ya futo daga ɗakin,


Yana kokarin shiga bedroom ɗinshi,Muryar Abu ta katse mashi hanzarinshi,

  "Abban Jahad,"har sai da gabanshi ya fadi,A sukwane ya juyo yana kallonta,

  Jikinta na sanye da hijabi dogo,

Murmushin yaƙe yayi mata tare da cewa"Na'am Oummu Sehrish,"

  Murmushi itama ta sakar mashi,

Matsawa tayi kusa dashi"shiru har yanzu,Yayan sehrish bai dawo da ita ba ko"?tayi tambayar fuskarta ɗauke da matsananciyar damuwa,

  "Waya faɗa maki haka"

"Jahad ce ta sanar dani ɗazu,To naji shiru har yanzu basu dawo ba,duk nashiga damuwa,Gashi tabar wayarta agida,inason nasan a wani hali take ciki,"

  Bai bata amsa ba,sai da ya fara buɗe dakin ya nuna mata hanya"Mu shiga daga ciki,inason magana dake,"

Shiga ciki abu tayi yabi bayanta,Gefen gadonshi ya nuna mata"ki zauna,"

  Girgiza kai tayi"a'a,muyi maganar daga tsaye,inaso in koma ɗakine,

  "Ki kwantar da hankalinki,Ƴarki ko ince ƴarmu tana cikin ƙoshin Lafiya,Tana atare da yayanta kamar yadda Jahad ta sanar dake,

  Aruɗe abu tace"Dare fa yayi sosai,duk inda suka je ya isa ace yanzu sunyi tunanin dawowa gida,"

  "Shiyasa nace ki zauna muyi magana,akwai abunda nakeso in sanar dake,"jin haka yasa abu ta samu wuri ta zauna,tana kallonshi,daga can gefenta ya zauna suna fuskantar juna,

  "Nayi maki laifi bansanar dake ba,"

Cike da mamaki tace"Laifi kuma,na me kenan,"?

Daƙyar ya daure yace"naso na sanar dake amma halin da muka shiga a kwanakin baya yasa ban samu lokaci munyi magana dake ba",

Kasa kunne abu tayi tana sauraronshi,har ta ƙosa ya gaya mata,

  "Ina sauraronka,Ka sanar dani kawai,"

  "Sehrish tana da aure,"

Gabanta ne ya faɗi rass,A ruɗe ta maimaita abunda yace"Sehrish tana da aure?tun yaushe"?

  "Ina tunanin ya wuce wata hutu da yin aurenta,Ita da babban yayansu,Nasan kin gane shi,"

Abun yayi matuƙar bata mamaki,sai lokacin ta tuna da ranar nan da sehrish tayi jinya har ta kwana ɗakinshi,abun ya tsaya mata aranta ashe mijinta ne shi,zurfin tunani ta shiga,Abusufyan kuwa zuba mata ido yayi yana kallonta cike da fargabar amsar da zata bashi,

  Can yaga ta ɗan saki murmushin gefen fuska,

  "Ashe ina da suruki bansani ba,shine ba'a sanar dani bako"?tayi maganar tana harararshi,

  Ba ƙaramin daɗi abusufyan yaji ba,duk da halin da yake ciki,

  "am sorry,nasan nayi laifi amma yanzu na goge laifina tunda na sanar dake komai,"

"Hakane,naji dadi sosai,saboda na yaba da kyawun halinshi,Yana girmamani sosai"

  Kallonta kawai Abusufyan yake yi,acikin ranshi yace"da ace kinsan meya aikata ma ƴarki,da yanzu ba wannan zancen ake yi ba"a fili kuma yace"Ae abun alfahari ne shi,Mutumin kirki,yana da kyakkyawar zuciya,"

  "Yanzu kenan shiya tafi da ita,amma baka faɗamun inda suka je ba,kuma yaushe zasu dawo,"ba don yaso ba,Ya shiga shirga mata ƙarya,

  "Sun tafi kaduna ne,wani aiki ne yakai shi,Shine ya tafi da ita,Amma bai sanar dani lokacin da zasu dawo ba,"

  Jinjina kai Abu tayi"Allah ya dawo dasu lafiya,Har hankalina ya kwanta yanzu,Dama Hosana ta addabeni da tambayar ina Rishi ɗinsu take ne,Kaga yanzu na samu amsar da zan fada mata idan ta ƙara tambayata,"ta ƙarasa maganar tare da mikewa tsaye,

  Tashi yayi shima"mu je na rakaki ɗakin,Inaso na gansu,"

  "Kunya nake jifa,idan wani yaganmu atare fa?Kuma yanzu nasan sunyi bacci ma,"

  "Koda sunyi bacci nidai inason ganinsu,"duk yadda taso ta hanashi bin ta sai da yabita,Lokacin da suka shiga ɗakin A kwance ya samu jahad da hosana suna ta sharar bacci,tamkar ya fashe da kuka haka yaji,Saboda tunawa da halin da ƴar uwarsu take ciki,Yasan tana cikin mawuyacin hali,da ace sunsan halin da take ciki da baza suyi wannan baccin ba,Allah sarki,


Ya jima aɗakin yana kallonsu,Kafin yayi ma abu sallama Ya koma ɗakinshi,


Aranar kowa yayi bacci banda waɗannan mutanan,Abba,Abusufyan,Omar,Da duk wanda Yaji abunda ya faru da Sehrish,Baccinsu ragagge ne,sun shiga damuwa sosai,


*Boss Bature*


Tun da sanyin safiyar,Wayar Mommy dake ajiye saman side drawer ta soma Ringing,can cikin bacci ta dinga jin ringing ɗin wayar,daƙyar ta iya buɗe idanuwanta saboda baccin da ke fusgarta,Mikewa tayi daga zaune,batasamu Abba acikin ɗakin ba tun da suka fita sallar asuba shida Junaid bai kaiga dawowa ba,


Hannu takai tare da ɗaukar wayar,ta duba sunan mai kiran nata,Dr Harriet ce,ɗaya daga cikin aminnanta wanda ke zaune a Nigeria,tayi mamakin ganin kiranta a irin wannan lokacin,don sun jima basu yi waya ba,


Picking call ɗin tayi kafin ta kara wayar a kunnanta,Cikin harshen spanish suka soma magana 

  "Ina fata ban katse maki baccinki ba,"?

  "Kusan haka,ina fata kina cikin ƙoshin lafiya"?

  Lafiya lou,kwana dayawa kin manta dani,Miji daɗi ko?Zaman Nigeria ya kar6eki,shiyasa har kika manta da mutane "acewar Dr harriet tayi maganar muryarta da sautin dariya,

  "Me yafi raina,Ga mijina Ga ƴa'ƴana atare dani,bani da sauran damuwa,"ta ƙarasa maganar fuskarta ɗauke da murmushi,

  "Shiyasa kika manta dani kenan,Wai yaushe kika dawo Nigeria ne,baki sanar dani ba,nifa duk tunani na kina America ne ashe kin dawo daga yajin da kikayi,"

  Dariya Mommy ta ɗanyi kafin tace"Najima da dawowa,naso na sanar dake,mun shiga cikin wani hali ne na rayuwa,Amma yanzu Alhamdulillah,In na samu time zanzo,"

  "Oh sai ma kin samu time tukunna zaki zo,gaskiya ban yarda ba kizo kawai yanzu,Inason ganinki,Immediately pls,Wani taimako zakiyi mun,"

  Cike da mamaki tace"To fa!Wani irin taimako kenan"?

  "Kedai kawai kizo pls,I will be waiting for u,rashin zuwanki zai iya haddasa mun matsala,"tana kai ƙarshen maganarta,bata jira amsar da Mommy zata bata ba,Da sauri ta kashe kiran,

  Abun ya ɗaurewa Mommy kai,bata yi niyyar zuwa ba,amma yanayin yadda harriet tayi maganarne yasa ta mike da sauri ta shiga toilet,Shaf shaf Ta fito daga wanka,ta zura doguwar riga ajikinta,Ta ɗauki mayafi ta yafa akanta,


  Handbag ɗinta ta ɗauko,Sai da ta fara tura wayar cikin jakar,tukunna ta fito daga bedroom ɗin,bata samu kowa a babban falon ba,kaitsaye ta nufi hanyar fita daga falon da sauri da sauri,


  Da gudun gaske motarsu ta fuce daga cikin gidan,Wani sergeant ne ke yin driving ɗinta,Kaitsaye suka nufi estate ɗin da harriet take zaune,bayan yayi parking ɗin motar,ya fito tare da zagayawa ya buɗe mata mota ta fito daga ciki,


Da sauri ta nufi ƙopar da zata sadaka da cikin gidan,A bakin ƙopar ta tsaya tare da sanya hannunta taja door bell ɗin ƙopar,Yayi sauti,,


Ko minti ɗaya batayi ba a tsaye,taji an buɗe ƙopar,babbar mace ce fara tass baturiyar asali,a shekaru zata haura arba'in,tana da jiki,Ƙwayar idonta green colour ce,jikinta na sanye da riga da wando sun tsuke jikinta sosai dakyar take motsi acikinsu,Gashin kanta Ja ne sosai,Ta ɗaureshi da ribbom. 

  Lokaci guda suka sakarwa juna murmushi,

  "You're highly welcome,Am really glad to see u,"Ta ƙarasa maganar,Tare da rungume mommy ajikinta,

   "I really missed u,Bamu kyautawa juna ba tsawon lokaci babu wanda ya nemi wani acikinmu sai kace ba abokan juna ba,"Mommy ce tayi maganar bayan sun raba jikinsu,

  Ruƙo hannunta Harriet tayi tajata izuwa cikin gidan"lets get in",

  Katafaren palour ne ya haɗu sosai,yaji komai na buƙata acikinsa,

  Nuna mata wuri harriet tayi"have a seat,".  

  Girgiza kai Mommy tayi"Nifa hankalina ba akwance yake ba,kince kinason gani na,ki fara faɗamun menene kafin in zauna "

  Murmushi harriet tayi"Jiya nayi baƙo,Na ban mamaki kuwa,"

  Zuba mata ido mommy tayi,

"Idan kinason ganin kowanene,mu shiga ciki,"tayi maganar tana yi mata nuni da upstairs,


  Gaba tayi mommy tabi bayanta har suka hau saman stairs ɗin,A ƙopar wani bedroom Harriet ta tsaya"Go in,"

  Sallama mommy tayi tare da sanya hannu ta tura ƙopar ɗakin ta shiga daga ciki,Ya haɗu bedroom ɗin sosai,Aljannar duniya ce,


Slowly mommy ta sauke idanuwanta saman katafaren gadon,Mutun ta gani kwance saman gadon,lullu6e da white bedsheet,ba'a rufe fuskarba,Amma daga inda take bazata iya tantance fuskar wanene ba,kuma daga gani patient ne,Hannun mara lafiyar hada kanula ajiki,da alama Jini aka ƙara mashi,Ga kuma allurorin dake ajiye tare da magunguna gefen side drawer ɗin,


"Ki ƙarasa ciki mana,"harriet ce tayi mata maganar,tana ƙoƙarin ɗaga ƙafarta ta shiga daga ciki,Taji an buɗe kopar toilet ɗin ɗakin,da sauri takai idanuwanta akan mai fitowar,bakowa bane face SGR daga shi sai short ajikinshi,Rass yaji gabanshi ya faɗi lokacin da yayi arba da Mommynsu,Zuba mashi ido Tayi ƙuri tana kallonshi,mamaki ƙarara akan fuskarta,


Duk yasha jinin jikinshi,a ruɗe ya juya zai koma cikin toilet ɗin,Tayi saurin dakatar dashi"Rafayet!"a sukwane ya juyo,duk ya sauya tamkar bashi ba,Jiya zuwa yau har ƴar rama yayi,

  A hankali ya ambaci sunanta"Mommy"juyawa ta kuma yi tana kallon Sehrish dake kwance saman gadon sai da taga Sgr sannan ta gane cewa itace,

    "So u are here?meyasa baka sanar damu ba,gaba ɗaya ka tashi hankalinmu rafayet,Duk mun damu akan son sanin halin da kuke ciki'

  "Mommy,I ave no choice,Nasan babu wanda zai saurareni awannan lokacin shiyasa kawai na yanke shawarar in baro gidan da ita,Omar ma ya juyamun baya,"cikin sanyin murya yayi maganar,kana kallon fuskarshi zaka gane cewa Ba ƙaramin kuka yayi ba,idanuwan duk sun kumbura suntum,hatta la66ansa,Ga Sahun yakushin Sehrish nan a asaman kafaɗarshi da kuma damtsen hannunshi,duk da anyi dressing ɗin ciwukan '

   Shigowa ciki Harriet tayi tana kallon kowannansu,kafin ta soma magana"Jiya da suba Alexander ya kirani a waya ya sanar dani cewa Yana da patient zai kawota private hospital ɗina,Sai na bashi shawarar cewa Ya kawota gidana,tunda dama aikina ne,kuma dayawa masu irin matsalarta a cikin gidana nake dubasu,Gaskiya Yarinyar tasha baƙar wahala sosai,don nayi mamaki data kasance araye bata mutu ba,don ma Allah yasa munyi mata aiki cikin gaggawa batare da 6ata lokaci ba,Amma taji jiki sosai,ta zubda jini,don kusan leda biyu na Jini muka ƙara mata,Alex ne ya bata jininshi aka sanya mata,ni tun da nake duba patient irinta banta6a zubda kwallata ba,Sai akanta Mun sha kuka,daga ni harshi,yarinyar ce ga ƙananun shekaru......."cikin harshen spanish take maganar idanuwanta cike tab da kwalla,Mommy kuwa tuni ta fashe da kuka,dakyar ta iya matsawa gefen gadon da Sehrish take kwance ta sanya hannu ta yaye bedsheet din,Riga ce ajikinta blue colour dai dai guiwarta rigar ta tsaya,duk jikinta ya bushe,kamar matacciya haka take yin bacci,


Yatsun hannunta na kerma ta ɗaurasu asaman fuskar sehrish,tsananin tausayinta ne ya kamata,Juyawa tayi wurin da Sgr yake tsaye ya duƙar da kanshi kasa,duk jikinshi yayi sanyi,Ya karaya sosai,

  "Rafayet yanzu ka kyauta abunda ka aikata mata"?idanuwanta jawur take kallonshi,

  "What i neva expect from u,kai da kanka kake hukunta masu aikata laifi makamancin wannan amma yau kaida kanka kayiwa ƴar uwarka ta jininka,Why rafayet?ko laifi tayi maka ta cancanci wannan hukuncin?balle kuma batayi maka laifin komai ba!saboda kawai sun 6ata maka rai sai ka huce haushinka akanta?Yanzu kalli halin da ka jefata!Ka ƙiyasta irin raɗaɗin azabar da take ji a lokacin da kake kusantarta da kuma wannan lokacin da take halin jinya......'


Tuni idanuwanshi sun cicciko tab da kwalla,Sam ya kasa ɗagowa su haɗa ido da ita,

  "Pls Alex,bai kamata muna tuna abunda ya wuce ba,Wannan abu ya riga daya faru,Sai dai kawai mubi ta da addu'a,Allah ya kawo mata sauki,very soon zata wartsake,"

   Cike da takaici Mommy tace"don bakisan Halin da iyayen yarinyar nan suke ciki bane,sun damu sosai akan rashin ƴarsu,ni banma san me zance masu ba idan suka ganta,"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar tana share hawayen dake zarya akan fuskarta,

  "Baikamata asanar dasu ba,Don ta yanzu,Gaskiya in suka ganta a halin da take ciki yanzu zasu shiga matsananciyar damuwa,saboda har yanzu bata dawo cikin hayyacinta ba,da zarar ta farka sai ta dinga sambatu akan abunda Alex yayi mata,"

  Ajiyar zuciya mommy ta ɗan sauke before tace"What's the solution now?zata kai tsawon wani lokaci kafin ta dawo hayyacinta,"

  "Koda wani lokaci zata iya dawowa cikin hayyacinta,Yanzu ma baccin nan da kikaga tanayi munyi mata allurar bacci ne,abunda za'ae yanzu shine kada ki sanar da kowa inda suke,Har sai ta dawo cikin hayyacinta,zan sanar dake,Sai asan yadda za'ae a mayar da ita can gidan taci gaba da jinya,ina ga kamar hakan zaifi,"

Mommy tace"Hakan yayi,thank u so much Harriet,bansan da wasu kalmomi zanyi amfani wurin gode maki ba,kin taimakemu sosai,Yanzu zan koma gida kada su nemi ni,"ta ƙarasa maganar tare da mikewa tsaye,

  Rungume juna suka kumayi ita da harriet kafin Ta mayar da idanuwanta kan Sgr,

  Tausayinshi ne ya kamata,a hankali ta furta sunanshi"Rafayet"

  ɗagowa yayi da idanuwanshi ya kalleta,

  "Don't u need me"?

Yana jin haka jiki asanyaye ya nufeta,sosai ta rungumeshi ajikinta,

"Mommy i need ur prayer,am in serious dilemma,bani da wani sauran kwanciyar hankali daya rage mun,Mommy i ave regretted wlh,Nasan Uncle da Daddy fushi suke dani"

   Cikin sigar lallashi ta sanya hannunta abayanshi tana ɗan bubbugashi tace"Allah ya bata lafiya,nasan zaka bata kyakkyawar kulawa,dan Allah rafayet ka rage wannan zafin zuciyar naka,baida amfani,ni nasan cewa kana son yarinyar nan,ka mika wuya kawai ka nuna masu cewa kana sonta,Zaka tafi da ita a matsayin matarka,Shine fa 

kawai abunda suke buƙata a wurinka,simple and short amma ka kasa yi masu,har sai da ka illata masu yarinya,


Sun jima suna magana dashi,Kafin tayi masu sallama ta fuce daga gidan,


*Boss Bature*


Tun bayan da Mommy ta koma gidan bata sanarwa kowa game da inda rafayet yake ba,kamar yadda suka tsara,duk da tashiga damuwa sosai akan halin da Abusufyan yake ciki,Shi da Omar da kuma Abba,ko abincin kirki basu ci,Bacci kuwa tuni ya ƙauracewa idanuwansu saboda damuwa,Yanzu kowa na cikin gidan Ya gane cewa Mutun biyu basa nan,Sgr da Sehrish,Amma mommy bata bari sun gano wani abu ba,Da zarar sun soma tambayarsu sai ta sanar dasu cewa Sunyi tafiya ita da Sgr,wannan dalilin ne yasa basu tashi hankalinsu sosai ba,,yau a ƙalla kusan 2 weeks kenan babu su babu alamarsu,


Wuraren ƙarfe 1:30 na dare,Sgr na rungume da ita ajikinshi,dayake shi yake kula da ita,koda yaushe yana manne da ita,tamkar jinjira haka yake riritata,jikinta yayi sauƙi sosai sai dai abunda ba'a rasa ba,Saboda har yanzu bata ida dawowa hayyacinta ba,can cikin bacci ya dinga jin sambatunta"Ya rafayet bazan iya jurewa ba,mutuwa zanyi,Wayyo Allah na,Daddy kazo ka taimaki rayuwata,Ya rafayet baisona,Kashe ni yake so yayi,ƙoƙarin ƙwace jikinta take yi daga nashi,Da sauri ya zura hannunshi ya ta6o bedside lamp ya kunnata,Haske ya ɗan kawo,


Slowly ya mayar da idanuwanshi kan fuskarta,har sai da gabanshi ya faɗi ganin yadda ta zazzare idanuwanta,suna haɗa ido dashi,A gigice ta soma ƙoƙarin zame kanta daga ruƙon da yayi mata,

  

  Yunƙurawa yayi tare da miƙewa zaune Ya taimaka mata ta zauna,Ya sanya mata pillow daga bayanta,

  "Are u feeling hungry?"yayi tambayar yana kallonta,shiru bata bashi amsa ba,Sai dai kallon da take binshi dashi,Saukowa yayi daga saman gadon Ya nufi fridge ɗin ɗakin Ya ɗauko mata fresh milk mai sanyi,tare da ruwa,


Hawa saman gadon yayi dab da ita suna fuskantar juna,buɗe murfin robar yayi tare da kafa mata ita saitin bakinta,Buɗe baki tayi sosai tasha madarar,kusan duka ta shanye,Magungunanta ya soma bata tana sha,har ta kammala,


  Sai faman lumshe idanuwanta takeyi da alama baccin bai isheta ba,

  Nuna mata fuskarshi yayi"Look at my face,Kin gane  ni kuwa,"

  A hankali ta ware kyawawan idanuwanta akan fuskarshi,ta jima tana kallonshi batare data tanka mashi ba,hannu yasa tare da janyota jikinshi,ya zaunar da ita saman laps ɗinshi,ya kasance kanta yana asaman ƙirjinshi,a hankali ya ɗaura hannunshi asaman sumar kanta,shafa sumar kan nata yaci gaba dayi,kafin ya duƙo da fuskarshi zuwa gefen tata,tsinin hancinshi yana gogar fatar wuyanta,

  Calmly ya soma magana"I made a mistake,but I still have time to correct it,idan nace kiyi haƙuri nasan nacuce ki.......'ya ɗan dakata da yin maganar,baisan ko tana fahimtarshi ba,

  "Amma ashirye nake dana kar6i koma wani irin hukuncine daga gareki,"cikin sanyin murya ya ƙarasa maganar,shi kaɗai yasan yadda yake ji acikin zuciyarshi,still bata nuna mashi wata alama da zata nuna cewa tana acikin hayyacinta,tunda ta kwantar da kanta saman wide chest ɗinshi,bata ƙara motsawa ba,ta lumshe idanuwanta, 

  "Reesh,"ya kuma ambaton sunanta,bata amsa mashi ba,sai dai motsin hannunta dayaji abayanshi,dayake ta zagayo dasu,

  "Can't u talk to me?i know you're hearing me,"

  Tabbas kuwa tana jinshi,duk abunda yake cewa kaf acikin kunnanta,domin kuwa ta dawo hayyacinta,a ƙule take dashi,don taci alwashin sai yabata takardar sakinta,bazata ta6a cigaba da rayuwa dashi ba,ta tsorata da irin rashin imanin daya gwada mata,Yanzu ta daina kallonshi a matsayin mutun Dodo ya koma mata,a zaunan da suke bacci ya ɗauketa,shima ya fara gyangyaɗi,A hankali ya kwantar da ita,kafin ya kwanta tare da janyota ya ƙanƙameta jikinshi,


A washe garin ranar wuraren ƙarfe 7 na safe,Dr harriet ta kira Mommy awaya take sanar da ita game da cigaban da akasamu na Lafiyar Sehrish,ba ƙaramin daɗi taji ba,suna cikin yin wayar nan,tajiyo knocking daga waje,Da sauri tayi rejecting kiran,Ta juya bakin ƙopar ɗakin ta buɗe,

  Omar ta gani atsaye,duk ya rame kamarshi ya aikata laifin,

  "Ina kwana Mommy,".

  "Lafiya lou,"ta amsa mashi fuskarta asake,

   "Mommy still Rafayet bai tuntu6eki ba"?

  Shiru tayi tana tunanin kodai ta faɗa mashi inda suke,ganin yadda ya shiga damuwa over,

  "Omar,i won't hide it for u,Nasan inda rafayet yake,bansanar ma kowa bane saboda gudun halin da ƴan uwanta zasu shiga idan suka ganta a halin da take ciki na jinya,"

  Tunda ta fara magana Omar,Ya zuba mata ido yana kallonta Ya rasa me zaiyi farin ciki ko baƙin ciki,Duk irin halin da suke ciki na neman Sgr ashe ta sani?

  Daƙyar ya iya buɗe baki yace"A ina suke mommy,"

  "Banaso kowa ya sani Omar,nafiso saita samu sauƙi sosai,Yadda hankalin Abusufyan zai kwanta,"

  Jinjina kai yayi"bazan fada masu ba,"

  "Yana gidan Dr harriet,Nasan kasanta,"

  Tunkafin takai ƙarshen Maganar,Omar yayi hanzarin juyawa a gaggauce Ya fuce daga cikin gidan,Mota ya shiga,Major yajasu da gudun gaske zuwa gidan,dan bazai manta kwatancen gidan ba,tunda sun ta6a zuwa a lokacin baya,


Yana yin parking ɗin motar,tunkafin Major ya zagayo ya buɗe mashi ƙopa,Yasa hannu ya ture murfin motar,kaitsaye ya nufi cikin gidan,A buɗe ya samu ƙopar da zata sadaka da palourn gidan,ko sallama baiyi ba ya faɗa cikin gidan,A saman dining ya taras da Harriet tare da twins ɗinta matasan ƴan mata su biyu suna yin breakfast,Tana ganin shi ta soma sakin murmushi,

  "Omar yau kaine a gidana,"bai amsa mata tambayarta ba,Sai cewa yayi"Ina Rafayet yake,"?jim ta ɗanyi tana kallonshi Sam babu natsuwa atattare dashi,dama tayi mamakin ganinshi,

  Nuna mashi upstairs tayi"Suna acan sama,"ko kwatancen ɗakin bai tsaya tayi mashi ba,Da gudun gaske ya haye stairs ɗin,cikin sa'a ya gano ɗakin,Yana turo ƙopar Ya samu Sehrish zaune ta jingina kanta jikin headboard na gadon,Duk atakure take,


"Sister,"ya ambaci sunanta da wata irin kasalalliyar murya,

  Firgigit sehrish ta ware idanuwanta akanshi,tana ganinshi wani irin farin ciki ya lullu6eta,"Ya Omar",Da sauri ya ƙarasa gefen gadon ya zauna,Zuba mata ido yayi yana kallon Canzawar da tayi,Ta rame sosai takuma yi haske,


"Ya jikin naki"?bata amsa mashi ba,saboda kukan daya ciyota,Sosai ta fashe mashi da kuka,ruƙo hannayenshi tayi"Ya Omar dan Allah ka tafi dani gida,Wlh banjin daɗin zama anan,nafison na ganni cikin ƴan uwana"

  Tsananin tausayinta ne ya kamashi,tuni hawaye sun wanke mashi fuskarshi,

   "Ya Omar wlh ka tafi dani gida tunkafin Ya rafayet Ya fito,don bazai ta6a bari ka tafi dani ba,Ni kuma natsani zama a gidan nan,duk a ƙuntace nake babu daɗi,"

   "Yana ina rafayet ɗin"?

  "Ya shiga wanka"

  Jinjina kanshi ya ɗanyi,kafin yace"Zaki iya tafiya,"

  Girgiza kai tayi"a'a bazan iyaba",don tasan in dae da kafafunta zata taka to kuwa har sgr ya fito ya gansu,

  Batare da 6ata Lokaci ba Omar ya ɗauketa saman kafadarshi ya sauko downstairs da ita,Dr harriet na ganinshi da ita,Hankalinta ya tashi aruɗe ta tare shi tana faɗin"Omar where are u going with her?Rafayet ne ya baka izni?Ko alex ce tace kazo ka ɗauketa,

  Tunkafin Omar yayi magana Sehrish tace"Ya Omar kada ka saurareta,wlh in ka barni acikin gidan nan Poison zansha in mutu,"yana jin haka ya ƙara harzuka,

  Ko kallon Harriet baiyi ba Ya fuce daga falon,Major ya bude mashi mota ya shigar da sehrish yana cewa"nasan idan ya fito yaji cewa Mun tafi da ita,dole ya dawo gida,"


Da gudun gaske Motar major ta fuce daga cikin gidan,Sehrish sai faman sauke ajiyar zuciya take yi,baiwar Allah daga ita sai wannan rigar mai kama da uniform,Ƴan ƙafafuwan ko takalma babu,Kanta ko mayafi babu sai dai gashin kanta dake a cukurkuɗe,duk ta ƙosa taga Mahaifiyarta da mahaifinta,da kuma ƴan uwanta,Rafayet ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,ya ƙumsa mata baƙin cikin da bazata ta6a mantawa ba,Ya sanya mata ƙiyayyarsa acikin zuciyarta,


A hankali Major Ya shigar da motar ta cikin babban gate ɗin gidan,Bayan yayi parking ɗinta,Ya fito da sauri Ya buɗe mashi Mota,Saukowa marshal yayi tare da zura hannayenshi Ya kinkimo Sehrish asaman kafaɗarshi,

  "Thank u Major"Yana ambaton hakan ya wuce da ita cikin gidan,A lokacin  babu kowa a palour sai dai mutanan dake kitchen suna shirya breakfast,Yana yin sallama hankalinsu Ya dawo kan Omar dayake suna hangenshi daga inda yake,Koda abu tayi arba da matashiyar dake kwance asaman kafaɗarshi,nan take taji aranta cewa Sehrish ce,Da gudun gaske ta fito daga kitchen ɗin,Hajiya azeema tare da Mommy suka biyo bayanta,Ai koda Mommy taganshi ɗauke da sehrish sai da gabanta Ya faɗi,Har warning tayi mashi akan kar ya sanarwa kowa inda ta suke,Sai gashi ɗungurugum Ya ɗauko ta,

 

Aruɗe abu take kallonta"Sehrish ce?Meya faru da ita"?tayi tambayar tana ƙare mata kallo,har lokacin bai sauketa daga kan faɗarshi ba,

  Hajiya azeema kuwa Alhamdulillah ta soma faɗi,fuskarta ɗauke da murmushi,duk da ta damuwa sosai ganin yadda ta rame,

  "Dan Allah ku faɗamun meya faru da ita,Meyasa nake ganinta haka?kamar bata da lafiya,"

  Omar na ƙoƙarin Yin Magana,Sehrish Tace"Oumma,Lafiyata qalou,Yaya Omar ka kaini ɗaki inaso inga ƴan uwana,"

   Wucewa bedroom ɗinsu yayi,da sauri suka bi bayanshi,jikin abu duk yayi sanyi,koba a fada mata ba tasan cewa babu lafiya atattare da ita,tunda har bazata iya tafiya da ƙafafuwanta ba,Suna ƙarasowa kopar ɗakin,Oumma ta buɗe mashi Ya shiga da ita,A lokacin Jahad na zaune gefen gadon Tana karatun al'qur'ani,Hosana kuma ta kabbara sallah,Don bata samu yin sallar a lokacinta ba,


A firgice Jahad ta miƙe tana kallon Ya Omar dake ɗauke da Sehrish,da ƙarfi ta ambaci sunanta Sehrish!Ae Hosana najin an kira sunan Sehrish Ta katse sallar da take yi dama tunda suka shigo take ƴan waige waige,A hankali Omar ya zaunar da ita samam gadon,Ya sanya mata pillow a bayanta,ɗaya bayan ɗaya take bin fuskokinsu da kallo kamar yadda suma suke binta da kallon ƙurulla,Hosana sai tsalle take yi tana ambaton sunanta saboda murna,


Fashewa Sehrish tayi da matsanancin kuka,Da sauri ta sanya tafin hannunta asaman fuskarta,tsananin tausayinta ne ya kamasu,da sauri Oumma ta zauna gefen gadon"Sehrish meya faru dake ne?na damu sosai akan rashin ganinki,Har Abusufyan na tambaya yake sanar dani cewa kunyi tafiya keda babban yayanku,"kasa buɗe baki sehrish tayi,saboda ƙululun baƙin cikin da ya tokare mata makoshinta,A duk lokacin data tuna abunda Sgr yayi mata,

  Zuƙunnowa Hajiya azeema tayi saitin fuskarta"Pls stop crying,Wlh nashiga damuwa sosai akan rashinki,banji daɗin abunda ya faru ba,Amma kiyi haƙuri haka Allah ya ƙaddara maki,Yanzu dai ki sassauta kukan nan naki,kodan saboda mahaifiyarki zata shiga damuwa sosai"tayi maganar ne ta yadda abu bazata iya jiyota ba,

  "Koda sun tambayeki meyake damunki,Kice baki da lafiya zazza6ine ya kamaki,"cikin shessheƙar kuka Sehrish ta ɗaga mata kai alamar zatayi yadda tace,Miƙewa Hajiya azeema ta yi,Jahad ta zauna saman side drawer na gadon tana tambayarta Lafiya,

  Cikin shessheƙar kuka tace"Bani da lafiya ne,Amma jikin da sauƙi,kawai nayi kewarku ne sosai,"

 Kallonta kawai Jahad take yi ba don ta yadda da abunda tace ba,

  "Tana buƙatar hutu,Bai kamata mu takura mata da tambayoyi ba,idan ta huta sai muyi magana da ita,"acewar Hajiya Azeema,daga haka babu wanda ya ƙara tambayarta,

  Matsawa abu tayi kusa da ita,ta sanya hannunta ta rungumota jikinta,wani irin zafi dama kullum cikin zazza6in take,

  "Allah ya baki lafiya Sehrish,"

 "Ameen Oumma,"_


Mommy kuwa bayan fitar Omar da sauri tabi bayanshi,

  "Why omar meyasa zaka ɗaukota?haka mukayi dakai"?

  Juyawo yayi fuskarshi sam babu annuri acikinta,.  

  "Haba mommy,don me zan barta acan?An ƙuntata rayuwar yarinyar nan sosai,Na farko an cutar da ita,na biyu kuma an kaita wani wuri inda batasan kowa ba,Hakanan ya rabata da kowa nata,lokacin dana je kuka ta dinga yi mun tana ruƙe hannuwana akan in tafi da ita gida kota kashe kanta,Shiyasa na yanke shawarar ɗaukota,Tunda jikin nata da sauƙi,"

  "Shikenan Omar,Nima nayi tunanin a dawo da ita gidan,Kawai ina fargabar halin da Zasu shiga ne idan suka ganta,"

  "Kada ki damu Mommy,rashin ganinta a kusa dasu shiya fi haɗari,Amma in tana atare dasu,To da sauƙi,ita kanta tafi son cikin ƴan uwanta,"

   Jinjina kai Mommy tayi"Wannan haka yake,nagode sosai Omar,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa Ta nufi kitchen,shi kuma Ya wuce ɗakin Abusufyan,Hannu yasa yana kwankwasa kopar,A lokacin Abusufyan yana ta faman zarya cikin ɗakin,Damuwa duk ta isheshi,jin knocking ɗin ƙopar yasa shi yin hanzarin juyawa yaje ya buɗe mashi,

  Tunda yaga fuskar Omar awashe ranshi ya bashi cewa Akwai labari me daɗi,. 

  Muryarshi na kerma yace"Omar,An gano inda suke,".  

  Fuskar Omar ɗauke da murmushi yace"yanzu haka Sehrish tana aɗakinsu,"tunkan yakai ƙarshen maganar Abusufyan Ya fuce da sauri har yana tuntu6e,


Suna zaune saman gadon sun zagayeta,Sai gashi Ya banko ƙopar dakin Yana ambaton sunanta"Sehrish!"yadda kasan makoshinshi zai 6allo,

  "Daddy,"ta amsa mashi fuskarta ɗauke da murmushi,Wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarshi,Da sauri ya ƙarasa suka matsa mashi,Ya hau saman gadon Ya rungumota jikinshi,Wata irin nauyayyiyar ajiyar zuciya Ya sauke,Wasu irin zafafan hawaye ne suka wanke mashi fuskarshi,

  "Daughter,Am sorry for everything,i ave regretted already,duk nine silar halin da kika tsinci kanki,"sosai yayi tighting ɗinta ajikinshi,tamkar zai mayar da ita cikin cikinshi,

  tamkar raɗa haka yake yi mata maganar don kar suji abunda yake cewa,tunda bakowa yasan ainihin abunda ya faru da ita ba,

  Cikin shessheƙar tace"Daddy kamar Bazan rayu ba,Nasha wahala,Lokacin mutuwa nane kawai baiyi ba,'

  "Nasani,wlh naji ajikina Daughter,danasan hakan zata faru da ban tursasa mashi akan ya sakeki ba,da duk hakan bata faru ba,"Sai lokacin Sehrish ta gane dalilin dayasa Sgr yayi mata hakan,

  Janyeta yayi daga jikinshi,tare da sanya hannunshi asaman fuskarta yana share mata hawayenta yace"Ina babban yayan naku?nayi tunanin atare dashi zaku dawo,'

  Girgiza kai ta ɗan yi"A'a,Sai zuwa anjima zai dawo,Ya Omar ne ya kawo ni,Na matsa mashi ne akan inaso na dawo gida," sunyi pretending ne don kada Oummansu ta gano gaskiyar abunda Ya faru da ita,

  "Allah ya baki Lafiya Daughter,"

 "Ameen daddy,"

  Turo kopar ɗakin akayi,Mommy ce ta shigo hannunta ruke da plate mai ɗauke da farfesun nama,da zafi zafinshi sai ƙamshi yake yi,


  Ƙarasowa ciki tayi fuskarta a ɗan sake tace"Ya jikin naki,"

  Batare da sehrish ta kalleta ba ta amsata"da sauki Mommy,"

  Miƙa ma Abu plate ɗin tayi"Ga wannan nasan zata buƙace shi,Akwai tea dana haɗa mata,bari naje na ɗauko mata shi,"

  Hannu bibbiyu Oumma tasa ta kar6i plate ɗin"Mun gode sosai,"

  "Kada ki damu,duk yiwa kaine"takai ƙarshen maganar,tare da juyawa a hanzarce tabar bedroom ɗin,Abusufyan ya lura da sehrish,tunda Mommy ta shigo bata kalli fuskarta ba,tayi hakanne saboda ta tsani ganin fuskar Sgr,Ita kuma Mommy dashi take kama shiyasa taƙi kallonta,

   Shafa fuskarta yayi"Daughter,"murmushi ta ɗan saki batare data ɗago da idanuwanta ba,Sun cika tab da kwalla,

  Juyawa yayi tare da kallon Abu dake tsaye hannunta ruƙe da plate,. 

  Kar6ar plate ɗin yayi daga hannunta,

  Ruƙo hannun Oumma Mommy azeema tayi"mu koma kitchen munbar Aiki acan,In sha Allah zata samu sauƙi,"atare suka fuce daga ɗakin,

  Ya rage daga Abusufyan Sai Hosana da Jahad dake kewaye da ita,

   jim kaɗan Mommy ta dawo hannunta ɗauke da Cup wanda ta haɗa mata Kakkauran tea acikinsa,

  Asaman side drawer ta ajiye mata Cup ɗin,

    Kafin ta juya tabar dakin,

 "Rishi wai ina kika shiga ne?Kin tafi kin barmu da tunani,"Hosana ce tayi maganar fuskarta a yamutse,

  Jahad tace"Dan Allah kibarta ta huta,Ba kiga bata da lafiya ba,Sannu Sehrish Allah ya baki Lafiya,muryarta ƙasa ƙasa ta amsa mata da Ameen,

  Abusufyan da kanshi Ya zauna yana bata farfesun abakinta,Cike da kulawa,ba ƙaramin daɗinshi taji ba,sosai tasha,kusan duka ta shanye duk da hosana ta tsoma masu hannu,Ta dinga ɗaukar naman tana turawa abakinta wai ae itama bata ci ba,


Bayan ta kammala Ya ajiye plate ɗin Ya dauki cup of tea ɗin da mommy ta ajiye mata,A baki ya kafa mata shi,Sosai ta shiga kur6arshi abakinta,

  "Amma nima ka bani tea ɗin abaki"?

Hosana ce tayi maganar,tana tura mashi bakinta,Hakan ba ƙaramin dariya yaso ya basu ba,murmushi sehrish ta ɗan saki tana kallonta,

   "Daddy ka bata tasha,"

Cike da zolaya Abusufyan yace"Na mara lafiya ne,Hosana kiyi hakuri wannan na sehrish ne,bata baki tausayi ba Kalli fa ki gani duk ta rame,"

  A shagwa6e Hosana ta langwa6ar da kanta,tasa hannu tana nuna mashi ƙashin wuyanta,

  "Daddy ae nima banda Lafiya,Kalli ka gani,"

  Kallon wuyanta yayi acike yake babu wani ƙashin daya leƙo,

  Harara Jahad ta ɗan watsa mata"Saboda kofin tea zaki jama kanki ciwo,Tirr da wannan halin naki,Shegen Ci kamar gara"

  Guntun tsoki Hosana taja"eh ɗin ina ruwanki,Ƴar shigar shugula,ba'a kasa dake ba,kin tsomo mana baki,".

  Dariya sosai Abusufyan yayi yana kallonsu,ita kanta Sehrish murmushi ne kwance akan fuskarta,Hankalinta Ya kwanta sosai,gata ga iyayenta ga kuma ƴan uwanta,


Kwankwasa ƙopar ɗakin akayi,Abusufyan yace"Wanene"?

 "Nice Amrish,"

 "Okey shigo daga ciki,"turo ƙopar ɗakin tayi,jikinta sanye da hijabi dai dai guiwa,Waro ido waje tayi ganin Sehrish 

  Da ƙarfi ta ambaci sunanta"SEHRISH"

  Wani irin farin ciki ne ya lullu6ete,har ta manta da abusufyan dake zaune,Da gudu ta ƙarasa gefen gadon,Ta haura sama ta rungumota ajikinta,

  "Sehrish ina kika shiga ne?ina ta nemanki?Oumma tace mun kunyi tafiya keda Babban yayanku,"

  Fuskar Sehrish ɗauke da murmushi tace"Am sorry Amrish,Nayi laifi ban sanar dake ba,Tafiyarce ban shirya mata ba,ni kaina bansan da ita ba,"

  ɗagowa amrish tayi daga jikinta ta sanya tafin hannayenta ta tallabo fuskar Sehrish"Duk kin rame,Baki lafiya ne "

  "Zazza6i nake yi,"

  Gyaran murya Abusufyan yayi mata,Da sauri Amrish ta sauko daga saman gadon ta zuƙunna tana gaishe shi"Ina kwana daddy,An tashi lafiya,Ya mai jiki,"

 Murmushi Abusufyan ya sakar mata tare da cewa"Lafiya Lou,yaushe rabon dana sanyaki acikin idanuwana,bakyason zuwa kina gaishe ni ko"?

  Sunnar dakai ƙasa tayi cike da jin kunyarshi tace"A'a,inason zuwa,"

  "Baki ɗaukeni a matsayin mahaifinki bane"?

  Da sauri tace"Na ɗauke ka,"

  "To meyasa bakya sakin jiki dani ne"?

  Shiru tayi batace Komai ba,

  "Daga yanzu inaso ki saki jikinki dani,Dake dasu Sehrish duk ɗaya kuke a wurina,duk wani abu da kike buƙata na rayuwa,ki sanar dani ni kuma zanyi maki shi,"

  "Nagode sosai Daddy,"ta ambaci hakan tare da miƙewa,

  "Sehrish wayarki na ɗaki,bari na ɗauko maki ita,"

  Da sauri ta juya ta fuce daga ɗakin,Kallonta Abusufyan yayi,

  "U need a rest,ki kwanta ki huta,Zuwa anjima zan sake zuwa dubaki,Yanzu hankalina ya kwanta,ashe da rabon yau inyi bacci hada minshari don tunda kuka tafi wlh ban runtsawa sai dae bacci 6arawo ya dan dauke ni Daughter,"

  Murmushi ta ɗan saki,mikewa yayi tare da kallonsu Jahad yace"Ku kulamun da ita pls,"

  Atare suka amsa mashi da toh,kafin ya bude kopar ɗakin ya fuce,


Baijima da fita ba,Amrish ta shigo ɗakin hannunta ruƙe da wayar Sehrish,zama gefen gadon tayi tare da miƙa mata wayar,hannu tasa ta kar6i wayar,

   "Ya jikin naki"?

 "Am feeling better now,nayi missing dinku sosai,"

  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Nima nayi missing ɗinki sosai,Kullum saina tambayi Oumma yaushe zaki dawo,"

  "Allah sarki,nagode sosai da nuna damuwarku akaina,"


Bayan fitar Abusufyan kaitsaye ya nufi ɗakin Ammi,A lokacin khadija da nafeesat suna acikin ɗakinta,Suna tattaunawa game da bikin da za'ayi,


Da sallama ya shiga ɗakin,atare suka amsa mashi,da sauri suka soma gaisar dashi,fuskarshi asake ya amsa masu,Suna zaune ƙasa sun lankwashe kafafunsu,Ammi kuma na zaune gefen gadonta,

  Agabanta ya zuƙunna"Ina kwana Ammi,kun tashi lafiya,"

  "Lafiya lou,Autana,Ina fata kaima haka,"

 "Alhamdulillah"ya amsa mata,

  "Da alama yau akwai labari me daɗi akan fuskarka,murmushi ya saki tare dacewa"Ammi Sehrish ta dawo,Yanzu haka daga ɗakinsu nake,"

  "Masha Allah,Kai amma naji daɗi sosai wlh,Amma waye ya kawota?

  "Omar ne ya ɗaukota,"

  "Amma ya lafiyar jikin nata"

  "Da sauki ammi,"

Miƙewa tayi hannunta ruƙe da sandarta,kallonsu Nafisat tayi"yanzu zan dawo,Zanje na duba jikin jikata ne,"

  Mikewa sukayi atare"Muma zamu je ammi,"

  Murmushi tasaki"shikenan bismilla,"Abusufyan Ya shiga gaba suka bi bayanshi,har zuwa ɗakin Su Sehrish,

Ba ƙaramin farin ciki ammi tayi ba,Ganin yadda sehrish take ta faman sakin murmushi,tashi Amrish tayi daga gefen gadon,Ammi ta sauna suna fuskantar juna ita da sehrish,

 Atare suka haɗa baki suna gaishe da ita,Bayan ta amsa masu tace"Ya jikin naki"?

  "Naji sauki,"

Jinjina kai ammi tayi"Alhamdulillah mun godewa Allah,Haka mukeso,"Takai ƙarshen maganar tare da kallonsu Khadija dake atsaye,Ga ƴar uwarku nan,ɗaya daga cikin ƴan ukun Abusufyan ne,Bata da lafiya ne,"


Har suna hada baki wurin yi mata Ya jiki,fuskarta asake ta amsa masu,kafin ta soma gabatar masu dasu,

 "Jikokin modibbo ne,Ƴa'ƴan ƙanwar Mahaifiyarsu Omar,sannan kuma nan bada jimawa ba,Zasu zama surukan Abba,ta 6angaren Adam Da Osman"


Farin ciki ne ya lullu6esu,Ammi taci gaba da cewa"su kuma waɗannan zasu bi sahunku suma,Wato zasu Zama surukan Abba,Ga Sehrish nan Amaryar Babban Yayansu,ɗan wurin Fatima," tunda ammi ta ambaci hakan ran Sehrish ya 6aci sosai,tuni ta ɗaure fuskarta,Sam babu wanda ya lura da ita,

  "Bayan ita kuma Sai Jahad,Amaryar shalelen Abba wato Junaid,"da sauri jahad Ta kife kanta saman katifar saboda kunya,

  "Ita kuma wannan,Mai hankalin cikinsu,Amaryar Omar ce in sha Allah,"

  Fashewa Hosana tayi da dariya,kowa najin kunya banda ita,

  "Inason nayi magana da ita, ku ɗan bamu wuri,"


Amsa mata suka yi da toh,Gaba ɗaya suka fuce daga dakin,A waje suka tsaya suna fira atsakaninsu,Amrish dai tayi shiru saboda ita batasan matsayarta ba,Amma taso ace hada ita za'a ɗaurama aure,Itama ta zama ɗaya daga cikin amaren gidan,


 Bayan fitarsu Ammi ta zauna tayi mata nasiha sosai,ta kuma nuna mata 6acin ranta akan abunda Sgr yayi mata,A ƙarshe ta ruƙe hannayenta"Bazanso abunda zai cutar dake ba,Dama jiran dawowarki nake yi,Saboda inaso inji ra'ayinki game dashi,Kina son Cigaba da rayuwa dashi,Ko kuwa A'a,"

  kamar jira takeyi da sauri tace"Banaso ammi,dan Allah ku rabani dashi,wlh bazan iya rayuwa dashi ba,Ni dai kawai asanyashi Ya sake ni,"hada hawayenta,

  Shiru ammi ta ɗan yi tana kallonta,Kafin tace"Amma fa yana sonki sosai,Wanda silar hakan ne yajawo har ya aikata maki hakan,Saboda anyi ƙoƙarin rabashi dake,"

  Cikin shessheƙar tace"Nidai bana sonshi ammi,wlh yafita araina,"

  Ajiyar zuciya ammi ta sauke,

  "Shikenan,In sha Allah zan shiga tsakaninki dashi"


WANNAN KENAN!


*masu yi mun ya jiki nagode sosai da irin kulawarku,kuma in sha Allah kamar yadda nace very soon zan kammala maku littafi in Allah ya yarda,koda ba lafiya indai yatsun hannuna na motsi zan daure inyi ne,Don in gama akan lokaci,kafin watan ramadan,*Ga mai buƙatar karanta Littafin Abban Sojoji from Book one to 3,Yayi mun magana ta whatsapp 08103884440*

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*



*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





Story And written By


 *Hafsat Bature*





Not edited




Ammi ta jima zaune a wurinta,kafin daga bisani tayi mata sallama ta fita,A hankali ta gyara kwanciyarta samam gadon,lumshe idanuwanta tayi yayin da kwakwalwarta ke tariyo mata abunda ya faru lokacin Da Sgr Ya farmaketa,wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshinta,a irin kallon da take yi mashi yanzu Mara tausayi mara Imani,sanna kuma ba sonta yake yi ba, Jikinta yake so,shiyasa yake yi mata komai da mugunta don yaga yaƙarar da ita,kafin Ya koma U.s,tunda yasan rabasu Za'ayi,


Yinin ranar tana kwance samn gadon,Anan Abba ya same ta,Yayi mata ya jiki,da kuma ban haƙurin abunda Sgr yayi mata,taji daɗin yadda Abba Ya nuna 6acin ranshi,kuma yace duk abunda takeso Yanzu shi za'ayi,bayan fitar Abba,Su jahad da Amrish suka dawo cikin ɗakin,Yanzu kowa Ya Zuba Ido Yana jira dawowar SGR,


Wuraren Ƙarfe shida na mare ce,Omar Ya fito daga cikin toilet,Jikin shi sanye da Jallabiya,Yana ƙoƙarin Zama gefen Gadon,Wayar shi dake ajiye gaban mirror ta soma ringing,miƙewa Yayi izuwa gaban madubin ya tsaya,Hannu yasa ya ɗauki wayar,Ya duba me kiran nash,A hankali Ya furta Sunanshi"Rafayet,"kafin ya ɗaga kiran tare da manna wayar a kunnashi,

Tunkafin yayi magana,Sgr ya ambaci sunanshi"Omar,"cikin sanyin murya,tamkar bata shi ba,

  Ajiyar zuciya Omar ya sauke"Rafayet,Meyasa ka tafi ka barni?Nasan ban kyauta maka ba,dana barka a wannan yanayin,Amma banji daɗin tafiyar da kayi ba,"

  "Bani da za6ine Omar,bansan ya zanyi ba,banyi tunanin zaka ɗaga kira na ba,Saboda kowa fushi yake yi dani,"

  "Dole suyi fushi dakai,abunda kayi sam bai dace ba rafayet,duk in na tuna cewa ɗan uwanane ya aikata hakan sai inji ɗaci araina,why Rafayet?

  "Omar,I ave regretted,i hate my self,ban kyautawa kowa ba,Zan ba kowa hakuri,In yi nesa da kowa,"

  Waɗannan kalaman na Sgr ba ƙaramin ta6a mashi zuciya su kayi ba,tuni Ya karaya,

  "Am Sorry Nayi maka laifi na ɗauko Sehrish batare da saninka ba,"

  "Don't worry about that,Nima nayi niyar na dawo da ita gida,just ina fargabar abunda zai biyo bayane,"

  "Rafayet,ka dawo gida kawai,Ka nemi afwar Abba da uncle,nasan zasu sauko ne,".  . 

  "Its Okey,Zan dawo,amma sai zuwa sha biyu na dare".  . 

  "Shikenan,i will be waiting for u,Ko bacci bazan bari ya ɗaukeni ba,har sai naga ɗan uwana,Nayi hugging ɗinsa ajikina,"

  Sun jima suna waya da juna,Kafin daga bisani su kayi sallama,yana ajiye wayar gaban mirror,Hosana ta bango ƙopar ɗakin nashi,cak ya tsaya yana kallonta ta cikin madubi,doguwar rigace ajikinta mai baza daga ƙasa,babu mayafi akanta,da alama gayu akayi mashi,ta sauko da Curly hair ɗinta,An shafa jan baki ja,


A tsiyace ta toge tare da ruƙe qugunta"Ya Omar,"

  A sukwane Ya juyo yana kallonta,from head to toe,Ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,cikin sanyin Murya ya ambaci sunanta"Hosana,"

  Murguɗa mashi baki tayi,Yace"To fa!Halan wani laifin nayi,"

  Ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

  Ashagwa6e tace"Ya Omar wai dagaske idan aka ɗaura mana aure bada ni zaka tafi U.s ba,Wai a gida zaka barni,"?

  "Wurin wa kika ji hakan"?

Bubbuga ƙafarta tayi"Nidai ka amsa mun tambayata,"

Jinjina kanshi yayi tare dacewa"Eh,Anan zan barki,amma zan dinga zuwa duk ƙarshen.....  ..'

Bai ƙarasa maganar ba saboda wani kallo da yaga tana jifarshi dashi,kallon baka isa ba,

  "Ya omar ae wlh baka isa ba,Ko kana so ko ba kaso,Dole ne duk in da zaka tafi mu tafi tare,Ƙafata ƙafarka,Nida kai mutu karaba takalmin kaza,"ta ƙarasa maganar tana jefarshi da harara,

"Oh,a haka zan tafi dake can?Kina murguɗa mun baki,Sai kace wani tsaranki,Nifa in kika takuramin Allah,Zan fasa auren ne,"

Turo baki tayi"Yo he me?Ka fasa,Kai kasani wlh ya omar,Maza rubibina suke yi saboda kyau na,Don ma dai kawai ina sonka yasa nake kulaka,"

  Ƙumshe dariya yayi acikin bakinsa,don baisan tayi tunanin ko wasa yake yi mata,juya mata baya yayi batare daya ƙara tanka mata ba,


Yayi tunanin zata fita daga ɗakinne Amma sai yaga ta tattare bazar rigarta,ta haye saman gadonshi can tsakiyarshi ta baje tana kallon ceilling,

  Girgiza kai yayi"Oh ni Omar na ɗebo ruwan dafa kaina,"Yayi maganar acikin zuciyarshi,


"Ya Omar"ta ambaci sunanshi yayin da idanuwanta ke kallon ceilling kamar me nazarin wani abu,

  "Na'am,"ya amsa mata,


"Ya Omar,idan aka ɗaura auren kai kana America,Ni ina a nigeria,To wai taya za'ae in samu Ciki,"

  Rass Yaji gabanshi Ya faɗi,A firgice ya juyo yana kallonta,Hankalinta kwance tayi mashi tambayar,Abun ya ɗaure mashi kai,mamaki ne ya kamashi,

  "Ke!Waya faɗa maki cewa dole sai muna atare zaki samu ciki,"?

  "Yo oho,Nidai nasani ae,Ko kaza sai da zakara take samun cici,Kaga kenan,Nima sai kana tare dani zan....."bata ƙarasa maganar ba,da gudun gaske ta turo daga saman gadon ta nufi hanyar fita,A hanzarce ya damƙo hannunta,Ya juyo da ita,a jikin bangon yayi mata rumfa,sai faman zazzare mashi manyan idanuwanta takeyi,

  "Saboda rashin gaskiya,daga ganin na nufoki,kika watsa da gudu ko"?

   Runtse idanuwanta tayi"Ya omar,wai menene haka,kalli yadda ka takure,"

  "So nake ki faɗamun,Wayake koya maki waɗannan maganganun da kike gaya min,ko kunyata bakya ji"

Turo baki tayi"Babu kowa,"

  Sam bai yarda da ita ba,A matsayinta name ta6in hankali baya tunanin zata Iya sanin wannan,Sai dai ko gaya mata akeyi ko kuma tana kallon a wayarta,

  "Kiji tsoron Allah,ki faɗamun gaskiya,taya akai kikasan cewa dole sai muna atare da juna zaki samu ciki"

  A ƙule tace"Nifa babu kowa,"

Jinjina kanshi yayi"where's ur phone"?

  "Tana a ɗakinmu,"

"Ok,je ki ɗaukomin ita"


"Toh,"ta amsa mashi tare da juyawa da gudu taje ɗakinsu ta dauko wayar ta dawo bedroom ɗinshi Ta miƙa mashi"Gata,"

  "Cire pass word din"

Ashagwa6e tace"Sunanka ne,"

Ta6e baki ya ɗanyi,Acikin Zuciyarshi kuwa ba ƙaramin daɗi yaji ba,

  Yana rubuta sunanshi Omar,Nan take pass word ɗin Ya cire,

   Bincike yashiga yi mata acikin wayar,Gallery ya fara shiga kaf ya duba videos ɗin dake a wurin,baiga abunda yake zargi ba,ita kuwa sai faman sakin murmushi takeyi,

  ɗagowa yayi suka haɗa ido da ita"Kin gogesu ko"?

 "`Wai me kake magana akai Ya omar,"

Moving yayi kusa da ita,lalla6ata ya shiga yi"Pls My hosana,Ki fadamun gaskiya,Bazan maki komai ba,A ina kike sanin abubuwan da kike faɗamun,"?

    Kafin ta bashi amsa,aka kwankwaso ƙopar ɗakin,

  "Omar,zoka buɗe mun ƙopa,"muryar abbansu ce,da sauri ya saki hosana,ya ƙarasa bakin ƙopar ya bude mashi,

  "Abba,"omar ya kira sunanshi,

"Kunyi waya da rafayet"?fuskarshi da alamun damuwa yayi maganar,

Omar yace"eh,munyi magana dashi,"

  "Dan Allah omar,kasan yadda za'ae ya dawo gida,"

  Murmushi Omar ya ɗan saki kafin yace"Abba,kana missing dinshi ne ko,"

"Omar bazaka gane ba,inaso ya dawo ne,"tun da ya shigo bai lura da hosana ba,don tuni ta la6e bayan labule,kamar wata mara gaskiya,

  "In sha Allah zai dawo abba,Yace mun around 12 na dare zai shigo gidan,"

Ajiyar zuciya abba ya sauke tare da cewa"Allah ya kawoshi lafiya,Naga an fara kiran Magrib,Ka hanzarta shiryawa mu tafi masallaci,"

  Amsa mashi yayi da toh,Bayan fitar abba,Shaf shaf Ya shiga toilet Ya ɗauro alwala,Kafin Ya fito tuni hosana ta bar ɗakin,Dama haushinshi take ji ya tsareta da tambayoyi kamar wata ƙaramar yarinya,acewarta


Wuraren ƙarfe 10 na dare,Wayar jahad ta soma ringing,a lokacin har Bacci Ya fara ɗaukarta,Tana kwance gefen Sehrish,Hosana dake bayanta tuni bacci yayi awon gaba da ita,Oummansu kuwa na zaune saman darduma tana karatun qur'ani,


A saman mattress ɗin ta ajiye wayar,Bayan ta ɗauketa ta duba mai kiranta Sunan Fawan ne ya bayyana akan screen ɗin wayar tayi matuƙar yin mamakin ganin kiranshi,


Picking call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta,

  "Assalamu Alaikum"

On the other hand,Fawan ya amsa mata"Wa'alaikum Salam,Ya kike"?

  "Lafiyalou,"

"Sorry fa,bansani ba ko na tashe ki daga bacci,naji muryarki kamar kin fara ko"?

Murmushi ta ɗanyi kamar tana agabanshi"Hakane na fara amma banyi nisa ba,"

  "Dama junaid ne,ke son magana dake,ya bi ya ishe ni ya hanani sakat,Kinsan yanzu babu waya a hannunshi,Ina fa bacci sai gashi har bedroom ɗina,wai in kira mashi juliet dinshi,Sai kace baisan hanyar zuciya ɗakinku ba"

Wani irin farin ciki ne Ya lullu6e Jahad,a hanzarce ta miƙe daga zaune,

   "Gashi ku gaisa"jim kaɗan taji muryar junaid,

  "My juliet,"batasan lokacin da ta saki murmushi ba,

  "Na'am My romeo,Dama kana tunawa dani,"?

   "Yeah,ae bakison zuwa duba jikina,shiyasa nake fushi dake,"

  "Kaine ka juyamun baya,tun rana ta farko da nazo wurinka,Ka nuna tamkar baka sanni ba,abun ya tsayamun araina,rana ta biyu dana zo,kaƙi kallona,rana ta uku dana zo,Kana yin tozali ka rufe idanuwanka,kamar kaga wani mugun abu,"

   Sai da takai ƙarshen maganarta,Sannan yace"Am sorry,just forget about it,I really missed u,In ba damuwa inason ganinki yanzu,"

  Da sauri ta kalli agogon bangon dakin

  "Ƙarfe goma fa?Kuma oumma na kallona bansan ko zata barni in fito ba,"

  "Idan ta tambayeki,Ki sanar da ita cewa,Mijinki ne ke kira,Ae an biya sadaki,"

Jin wannan maganar yasa jahad ta fashe da dariya,Har oummansu dake karatun qur'ani saman darduma sai da ta ɗago ta kalleta,

  "still baka canza ba,kana nan a romeo ɗin dana sanka,"

  "Of course,I will be waiting for u pls,"yana kai ƙarshen maganarshi yayi rejecting ɗin kiran,

  Ajiye wayar tayi,A hankali ta sauko da ƙafafunta ƙasa,Jikinta na sanye cikin night gown pink colour,ta ɗaure gashin kanta da ribbom,

  Sai da ta miƙe tsaye sannan ta soma tunanin abunda zata ce ma Oumma,

  Gaban wadrobe taje ta bude ta lalubo hijab Ash colour ta zura ajikinta,saɗaf saɗaf Ta nufi hanyar fita,jin Oummansu Ta janyo doguwar aya,tasan bazata katse taba,balle tayi mata magana,da sauri ta buɗe ƙopar ɗakin ta fuce, babban falon ta nufa tana ta ƴan waige waige,duk ta ƙosa tayi tozali dashi,


A hankali Yake saukowa downstairs,Jikinshi na sanye cikin sleeping dress dinshi,riga da wando,Yayi haske sosai,Ga wani irin kyau daya ƙara,kwantacciyar sumar kanshi tayi tsayi sosai,Saboda bata samu aski ba,Gashin ya fara taruwa,


Hannayenshi duka biyun na acikin trouser pocket dinsa,A hankali ya ƙarasa saukowa cikin palourn,Kaitsaye ya nufe ba,kasa janye idanuwanta tayi daga kallonshi,Sai da ya ƙaraso kusa da ita,Suna fuskantar Juna,tun daga ƙasa har sama yake kallonta,lokaci guda suka sakarwa juna ƙayataccen murmushi,dimples din kowannansu Ya lotsa,zunzurutun kyau abun ba'a magana,

  Miƙa mata hannunshi yayi,ta zura nata asaman nashi,Ya ruƙe hannun sosai acikin nashi,wani irin daddaɗan ƙamshi ke fita daga jikinshi,

  "Mommy tace mun zaka zo wurina muyi shawara ko"?

  "Eh hakane,tace daga yanzu in zanyi shawara dake yakamata nayi,"

  Ba ƙaramin daɗin maganar nan taji ba,

  "Tunani me kyau,Banaso wani ya ganmu anan,Kunya nake ji,"

  "Zan jiraki a bakin swimming pool,Ki kawo mana Coffee,Yadda zamu ji daɗin tattaunawa,"

  Zaro ido ta ɗanyi"Dare fa yayi har 10,ko baka duba agogo bane,"

  "I know,ae ba jimawa zamuyi ba,Just 30 mins,"

"Shikenan yanzu xan zo,"takai ƙarashen maganar tare da juyawa da sauri ta nufi kitchen,

  Fitowa daga falon yayi kaitsaye Ya wuce bakin pool din,A ɗaya daga cikin ƙayatatun kujerun dake a wurin Ya xauma yana jiran zuwanta,wata irin iske ce mai daɗin gaske take kaɗawa a wurin,


Badajimawa ba,Jahad ta dawo hannunta ɗauke da Cup guda biyu ta ajiyesu saman table din gabanshi,Kafin ta zauna itama,sunji daɗin yanayin sosai suna shan Coffee dinsu suna fira,Tsawon 30 minutse kafin Suka bar wurin Kowa ya koma ɗakinshi,


Wuraren ƙarfe Goma Sha biyu na dare,Motar Sgr ta shararo da gudun gaske izuwa cikin gidan,Bayan Amstrong yayi parking ɗinta Ya fito tare da zagayawa Ya buɗe mashi mota,A hankali Ya zuro ƙafarshi ɗaya kafin Ya ƙarasa fitowa waje,


Jikinshi na sanye da jallabiyar nan daya fita da ita a lokacin da ya ɗauki Sehrish,hannunshi na ruƙe da leda fara mai ɗauke da sunan asibitin Dr harriet,Sallama yayi ma Amstrong kafin Ya nufi cikin gidan,Baisamu kowa a palourn ba,kaitsaye ya nufi upstairs,A hanzarce Ya fada part ɗinshi,A rufe ya samu ƙopar palourn,Hannu yasa ya turata,Sannan ya shiga daga ciki,ko'ina fess an gyara mashi,Sa6anin yadda ya tafi tabarshi,Bedroom ɗinshi ya shiga nan ma ya tarass An gyarashi,yayi mamaki sosai,bai ta6a tunanin za'a samu wanda zai kawar da ƙazantar da ya bari saman gadon ba,Ajiyar zuciya ya sauke,Kafin ya ƙarasa ciki,toilet Ya shiga,After Some minutes Ya fito daga wanka,Jikinshi sanye cikin bathrobe,A gaban mirror ya tsaya yana kallon fuskarshi,Bakomai yake fargababa,face haɗuwarshi da Abbansu,Da kuma Uncle abusufyan,yayi danasani sosai,Baisan da wani ido zasu kalleshi ba,zama yayi  saman front chair din madubin,Ya zabga tagumi da hannu ɗaya,ya damu sosai akan son sanin wani hali Sehrish take ciki,taci abinci ko bata ci ba,ga allurorinta da bai kammala yi mata ba,hada medicine dinta,Duk yau batasha ba,


Yana cikin wannan zancen zucin,Omar ya faɗo ɗakin nashi,ta cikin mirror ya hangoshi,farin cikine Ya lullu6eshi,Da sauri ya miƙe tare da juyawa ya nufeshi,Hankalin Omar ya ɗan tashi ganin yadda Sgr ya canza,Yayi rama,ya kuma yi haske sosai,kamar ka ta6a jini ya fito,yana ƙarasowa suka rungume juna sosai,kamar zasu haɗiye kawunansu,

  "Nayi missing dinka sosai,ɗan uwana nakaina,"Omar ne yayi maganar,Yayin da hannunshi ke abayan rafayet yana dan bubbugashi,

   Tun da ya kwantar da kanshi a kafadar Omar,Jikinshi yayi sanyi sosai,Hawaye suka cicciko tab a idanuwanshi,sam ya kasa buɗe baki yayi magana,Shi kaɗai yasan halin da yake ciki,

  Ɗago dashi Omar yayi"Rafayet"ya ambaci sunanshi tare da kai hannunshi saman fuskarshi,

  "Ka rame sosai,Duk ka canza,Kodai atare kukayi jinyar,"?

  "I don't ave peace of mind,ina cikin matsanancin tashin hankali Omar,na damu sosai,bansan ya zanyi ba,"

Lallashinshi Omar yayi tare da janyo shi suka zauna gefen gadonshi,Sosai ya shiga yi mashi nasiha akan abunda ya aikata,a ƙarshe yace"Tun wuri Rafayet,Kaje ka samu abba da uncle abusufyan,ka nemi yafiyarsu,Sannan ka sanar dasu cewa Kana son matarka,Kuma zaka tafi da ita u.s ba amatsayin mai aiki ba,idan har kayi wannan shikenan zaka zauna Lafiya,Nima kuma zan samu kwanciyar hankali,"

  Muryarshi asanyaye yace"Shikenan,zanyi hakan amma nasan zaiyi wuya uncle ya yafe mun,"

  "Zai yafe maka,ka jaraba yin hakan,Yanzu ka tashi ka shirya ka fara zuwa wurin Abba,Nasan baiyi bacci ba,"

  Amsa mashi yayi da toh,duk tausayinshi ya kama Omar,Miƙewa Omar yayi tare da kallonshi"Ka kulamun da kanka,Duk yarda ku kayi dasu saika sanarmun "

   Har yakai bakin ƙopar Sgr ya dakatar dashi"Na manta,Akwai injection din Sehrish tare da medicine ɗinta,Dana zo dasu,"


"Tana kwance a ɗakin oummansu,"ya ƙarasa maganar tare da fucewa daga ɗakin,


Shaf shaf Ya kammala shiryawa cikin Sleeping dress dinshi,White colour masu ɗigon baƙi,Bayan ya feshe jikinshi da turare Ya sauko down stairs,Direct Ya nufi ɗakin abbansu,A ƙopar ɗakin ya tsaya cike da zullumi,almost 5 mins yana a tsaye bai motsa ba,Ya kasa sanya hannunshi balle ya kwankwasa ƙopar,


Ji yayi bazai iya haɗa ido da abbansu ba,jiki asanyaye ya juya zai bar ƙopar ɗakin,Ba zato ba tsammi sai ga abbansu,A tsaye Ashe Yaji ma a bayanshi yana kallonshi,bai jima da shigowa ciki ba,gabanshi ne Ya faɗi rass,Da sauri ya duƙar da kanshi kasa,duk yabi ya dabarbarce,

  "Ka dawo kenan"?daƙyar ya iya buɗe baki yace"Eh,"

   "Banyi tunanin zaka ji kunyar haɗa ido dani ba,"yayi maganar yana kallon fuskarshi,shiru Sgr baice komai ba 

"Munga takardar saki mun gode,"yana kai ƙarshen maganar,Ya soma ƙoƙarin bi ta gefen Shi zai wuce ya shiga ciki,Da sauri Sgr ya ruƙo hannunshi,Rai a6ace abba yace"Ka sakarmun hannuna tunkafin ranka ya 6aci,Mara mutunci kawai,wlh rafayet ka bani kunya,ban ta6a tunanin zaka yi mun haka na,Kana ɗaya daga cikin ƴa'ƴana waɗanda nake alfahari dasu,Amma sai gashi Ka watsa mun ƙasa a ido,"tuni hawaye sun wanke mashi fuskarshi,hankalin Sgr ba ƙaramin tashi yayi ba,

  Muryashi na kerma Ya ambaci sunanshi'Abba,"

  "Ni ba abbanka bane,ban haifi ɗa irinka ba,Tunda ban isa na sanyaka abu kayi mun ba,"jin wannan maganar yasa hawayen dake kwance cikin idanuwanshi suka soma gangarowa saman fuskarshi,Gaba ɗaya Ya tafi Zai zube saman guiwowinshi,da sauri Abba ya ruƙoshi"kada ka kuskura ka zukunnamun,Saboda bakayi a lokacin daya dace ba,"

  "Am sorry abba,Nasan nayi kuskure,kuma nayi danasani,pls abba,kada kayi fushi dani,"


Zuciyar abba ta karaya sosai,daurewa kawai yake yi,ba don son ranshi yake furta mashi kalaman bakinshi ba,

   "Idan har kanaso,In shirya dakai,Kaje ka fara neman Yafiyar abusufyan,Sannan ka dawo wurina,"Yana kai ƙarshen maganar,Ya buɗe ɗakin Ya shige,


Ya jima a tsaye batare da ya motsa ba,Daƙyar ya iya jan ƙafarshi Ya doshi ɗakin abusufyan,A ƙopar ɗakin ya tsaya cike da zullumi,yafi jin shakkar tunkararshi akan kowa,hannu yasa yayi knocking ɗin ƙopar,Kusan sau uku yana kwankwasawa amma ba'a buɗe mashi ba,tunanin tura ƙopar yayi sai gashi ta buɗe,Da sallama abakinshi ya shiga ɗakin,Hasken bedside lamp ne ya haskaka mashi gadon abusufyan,Yana akwance yayi nisa acikin baccinshi,Was wasi ya tsaya yi acikin zuciyarshi Ya tafi koya tsaya,in har abusufyan bai yafe mashi ba,Abba ma bazai yafe mashi ba,Taya zai samu kwanciyar hankali?mahaifinshi na fushi dashi,


Kasa tafiya yayi,wuri ya samu gefen gadon uncle ya zauna,batare daya tayar dashi ba,Don yaci alwashin bazai ta6a tafiya ba,koda kuwa zai kwana a dakinne har sai Uncle ya yafe mashi,har wuraren ƙarfe 1:30 na dare yana zaune babu alamun bacci atattare dashi,Yayin da abusufyan keta sharar baccinshi,


Daya gaji da zamanne ya kwantar da kanshi gefen saman gadon,har bacci yayi awon gaba dashi,Lokacin da aka fara kiraye kirayen sallar asuba,Wayar abusufyan dake ajiye saman side drawer ta soma ringing,da ƙarfi kiran ya shigo,har cikin kunnanshi yajiyo sautin,A hankali ya ɗan buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci don bai ishe shi ba,daga kwancen da yake ya wurga idanuwanshi kan Agogon bangon ɗakin,Lokacin sallar asuba yayi,dama sai da ya kawo hakan aranshi,don kuwa bamai kiranshi a wannan lokacin in ba abba ba,domin ya tashe shi sallar asuba,sam bai lura da mutun a gefenshi ba,daƙyar ya samu ya miƙe yana yin hamma,tare da yin miƙa,kafin ya sauke hannunshi ne karaf idanuwanshi suka sauka akan Sgr dake kwance yana ta sharar bacci,Gabanshi ba ƙaramin faɗuwa yayi ba,don baiyi tsammanin ganin mutun adakinsa ba,kuma farat ɗaya bai waye shi ba,don har sai daya ɗan raza,Cike da mamaki yake binshi da kallo,Abun yayi mugu mugun ɗaure mashi kai. 

   "Rafayet"!ya ambaci sunanshi da ƙarfi,hannu yasa ya ɗan bubbugi kafadarshi,nan fa ya fara sambatu yana faɗin"Am sorry uncle,ka yafe mun,bazan ƙara ba,Nasan nayi kuskure amma ba'a son raina ba uncle i ave realized my mistake,a shirye nake dana kar6i koma wani irin hukuncine daga gare ka........"duk cikin bacci Sgr yake wannan sambatun batare daya sani ba,hada hawaye akan fuskarshi,tsananin tausayinshi ne ya kama abusufyan,ya lura da irin ramar da yayi,sam babu natsuwa atattare dashi,dama sai da ammi ta sanar dasu cewa duk irin raɗaɗin da zasuji na abunda ya aikata,Basu kaishi ba,don saiya fi su jin jiki,tuni idanuwan abusufyan sun cicciko tab da kwalla,


Slowly yakai hannunshi saman  sumar kanshi,bai ta6a tunanin Sgr zai iya sauke girman kanshi ba,Yazo neman yafiya a wurinshi,sai gashi da kanshi ya bashi mamaki,Allah kadai yasan tun lokacin dayazo ɗakin yana jiranshi ya farka,


Bubbuga kafaɗarshi yayi tare da ambaton sunanshi"Rafayet!Rafayet"!a firgice Sgr ya farka,yana faman zare blue eyes ɗinshi,Koda su kayi ido biyu da Uncle abusufyan da sauri ya sunnar da kanshi ƙansa,cike da jin kunyarshi,

  "Tun yaushe kazo ne"?

Cikin sanyin murya yace"Tun wuraren ƙarfe sha biyu da rabi,nazo na same ka kana bacci,".

  "Meyasa baka tashe ni ba"?

 "Saboda Banaso na takura maka ne,"daƙyar yake magana,saboda nauyinshi da yake ji,

  Yaƙi yarda su hada ido,Baisan yaushe Sgr ya fara jin kunya ba,Tabbas Ya fara ganin Canji atare dashi,'

  "Kanason magana dani ne"?yayi tambayar yana kallon fuskarshi,.  

  ɗaga mashi kai yayi alamar eh 

 "Okey,Ina sauraronka,"yayi maganar tare da matsowa Ya sauko da ƙafafunshi kasa,Kafin Ya mayar da hankalinshi kan Sgr,

   "Uncle,"ya ambaci sunanshi,tare da saukowa daga saman gadon,Ya tsugunna agabanshi,abun mamaki abun al'ajabi,Kamar a mafarki haka abusufyan ke kallon lamarin,Yau Sgr ya sauke girman kan nan nashi,Ya zuƙunna agabanshi,Lallai yau babba rana ce agareshi,


   Ruƙo hannunshi yayi acikin nashi,Calmly Ya soma magana"Pls uncle,Kaina bisa wuya na,ka yafe mun,Nasan nayi hurting dinka sosai,wlh na gane kuskurena.........'tun da ya fara magana,bai bari sun haɗa ido da abusufyan ba,shi kuwa ya kafe shi da ido yana kallonshi,

    "Ka yanke mun duk wani hukunci daya dace dani wlh i will accept it,amma dan Allah uncle,kada ku rabani da ita,bazan iya jure rashinta ba,atare dani,na saba da ita sosai......'tunkan yakai karshen maganar,Abusufyan ya katse mashi hanzarinshi dacewa"Zaka tafi da ita a matsayin mai aiki ko kuwa"?

  Da sauri yace"A'a,Zan tafi da ita,A matsayin matata,in har kun amince mun,"


   Murmushin gefen fuska abusufyan ya ɗan saki,batare daya bari Sgr ya gani ba,ci gaba da magana abusufyan yayi"Naji daɗi daka gane kuskurenka,Dama ni can ban ruƙe ka araina ba kawai banji daɗin abunda ka aikata mata ba,Amma bbu komai,komai ya wuce Allah ma muna yi mashi laifi ya yafe mana balle mu ƴan adam,Don haka na yafe maka rafayet,Allah ya yafe mana gaba ɗaya,Sannan bazan ƙara shiga tsakaninka da matarka ba,Yanzu ya rage tsakaninku da Ammi ne,tace zata yi adalci atsakaninku idan har ku duka kun amince da junanku toh,idan kuma har ɗaya daga cikinku ya musa,to zata raba aurenku ne,"

  Cikin sanyin murya yace"bansan da wasu kalmomin zanyi amfani wurin gode maka ba uncle......"

  "Kada ka samu damuwa,komai ya wuce,Allah ya baku zaman lafiya kaida matarka......."daga haka Abusufyan ya zarce dayi mashi nasiha,duk ya kashe mashi jikinshi,fuskarshi ɗauke da murmushin nasara ya futo daga ɗakin Abusufyan ya nufi bedroom ɗin abbansu,knocking ɗin ƙopar yayi,

  "Wanene"?Muryar abbansu ce,

 "Ni ne abba,"

Buɗe kopar abba yayi jikinshi sanye da jallabiya da alama shirin zuwa masallaci yayi,

  Tunkafin yayi magana abba ya ruga shi cewa"kaje wurin abusufyan ɗin"?

  "Eh,daga can nake,"nan ya kwashe duk abunda suka tattauna a tsakaninsu ya sanar dashi,farin ciki ne ya lullu6e abba,har baisa lokacin daya rungumo Sgr  ajikinshi ba,

   "Allah yayi maka albarka My son,"

 "Ameen abbana,"

  "Nima na yafe maka,"

  Har cikin ranshi ba ƙaramin sanyi yaji ba,

  Bayan ya raba jikinshi daga nashi,Ya ruƙo hannunshi zuwa cikin ɗakin"mu shiga daga ciki,in bakayi alwala ba,kayi sai mu tafi masallaci,'

  Ba ƙaramin daɗi sgr yaji ba,Mommynsu na kwance tana bacci lullu6e da bargo,toilet ɗin ɗakin ya shiga,Abba ya tsaya a tsaye yana jiran fitowarshi,After some minutes Ya fito,

  Suna hada ido da babansu Ya sakar mashi murmushi,mayar mashi da martanin murmushi yayi tare da cewa"inaso zan canza kayan jikina"

 Shikenan,Zan jiraka a palour,Daga nan ka tashi su Omar,su fito mu tafi masallaci,"

  Amsa mashi yayi da toh,kafin ya futo daga dakin,Jiki na rawa ya haura upstairs bai nufi ko'ina ba sai bedroom ɗin Omar,tunkafin ya shiga ya soma kwala mashi kira,

  "Omar,Omar,"a firgice Omar ya farka,tare da miƙewa zaune yana tambayarshi lafiya,fadawa saman gadon Sgr yayi tare da rungumeshi ajikinshi,Yana dariya,

  Tun da yaga haka,Ya gane cewa Sun yafe mashi 

  "Omar ka tayani murna,Uncle da abba sun yafe mun,kuma yace bazai ƙara shiga tsakanina da reesh ba,Ya amince na tafi da ita,"

 Omar yayi farin ciki sosai,Amma kuma akwai sauran rina akaba,idan su sun amince mashi,Itafa Yarinyar!!!


Shafa bayanshi Omar yayi"Am so happy rafayet,ashe da rabon asha shagalin bikina tare dana ka,Kafin mu wuce U.s,tare da matayenmu,Alhamdulillah My dream will come true,


Zuciyar kowannansu a wanke take da tsantsar farin ciki mara misaltuwa,

  "Amma wani hanzari ba gudu ba,jiya kaje wurin Sehrish kuwa?naji kayi magana akan maganinta"?

  "Bansamu naje ba,amma idan muka dawo daga masallaci,Zan je na duba Lafiyarta,"

  "Hakan ma yayi,bari na je nayi alwala sai mu wuce masallaci"acewar Omar,yakai ƙarshen maganar tare da saukowa daga saman gadon,Toilet ya shiga Sgr kuma Ya wuce part ɗinsa,don ya canza Kayan jikinshi,


Batare da 6ata lokaci ba suka hallara gaba dayansu matasan gidan a babban falon gida,atare suka wuce masallaci,


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 8 na safe a lokacin Su oumma sun hallara a kitchen suna shirya breakfast ɗin gidan tare dasu Mommy,da hajiya azeema,


A wannan lokacin ne Sgr ya shirya tsaf cikin fararen suit,wankan ya hau dashi sosai,fitowa yayi daga part dinsa Ya nufi corridor din dakinsu Sehrish,a baƙin ƙopar ɗakin ya tsaya,tare da sanya hannunshi yayi knocking din ƙopar ɗakin,

  Daga ciki yaji ance"Wai wanene"shiru bai tanka ba,Ya sake kwankwasa kopar,Da ƙarfi yaji a bude ƙopar,a ruɗe ta sanya hannu abakinta,ido ya raina fata,sam batayi tsamanin Baban yayansu bane,

  "Yaya rafayet,ashe kaine,wlh nayi tunanin wanine daban"abun ma dariya yaso ya bashi,

   "Rishi kake nema"?tunkafin ya bata amsa taci gaba da cewa"In ma oumma kake nema,tana a kitchen,Jahad kuma ta tafi wurin aunty hafsaf,Ni kaɗaice nake jinyar sehrish,baiwar Allah wlh saita baka tausayi,duk ta rame,duk taji ciwo abakinta,abinci ma daƙyar take iya ci ......'

 Surutunne ya ishe shi"its Okey,Zan wuce,"matsa mashi hanya tayi ya nufi cikin ɗakin,

  "Tayi breakfast"?yayi tambayar yayin da idanuwanshi ke akan sehrish dake kwance magashiyyan tana bacci,

  "Inafa,bataci komai ba tun jiya da daddy yabata farfesu tasha,tare da ɗan tea bata ƙara cin komai ba,koda daddare sai da oumma ta bata abinci ta amayar dashi duka......'

   Surutun Hosana ba ƙaramin mamaki yake bashi ba,Amsa kaɗan yake buƙata amma sai zuba takeyi mashi kamar radiyon da bata da saiti ,lallai Omar zaiyi fama,

  "Its okey,Kije ki amso mata breakfast ɗinta  yanzu ina jiranki "

  "Toh,"ta amsa tare da fucewa daga cikin dakin 


Xama yayi daga gefen gadon ,ya zuba mata waɗannan sexy eyes ɗin nashi yana kallonta,tsananin tausayinta ne ya kamashi, hannu yasa ya zame bargon data lullu6e half body dinta dashi,Still blue gown ɗin nan ce ajikinta,bata canza kayan jikinta ba,ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,har baiso ya ƙyafta idanuwanshi daga kan fuskarta, hannu yakai saman side drawer inda ya ajiye ledar allurorin nata tare da magungunanta,shaf shaf Ya ɗura ruwan allurar acikin syringe,so yake ya tayar da ita daga baccin amma ya kasa,Saboda baison Ya katse mata shi,don ya lura da yadda take yinshi cikin kwanciyar hankali,


Ajiye injection ɗin yayi sama drawer din,slowly yakai hannu yana ƙoƙarin shafa wuyanta,Hosana ta banko ƙopar ɗakin hannunta ɗauke da tray,A firgice Sehrish ta farka,Tana kokarin mikewa zaune,duk ta rikice,har yanzu bata daina jin fargababa,

  "Reesh are u okey,"?jin muryarshi yasa ta mayar da eye balls ɗinta akanshi,koda suka haɗa ido lokaci guda Ta ɗaure fuskarta tamau babu annuri ko misƙala zarratin,janye idanuwanta tayi daga kan fuskarshi,hankalinshi ya ɗan tashi da ganin irin kallon da tayi mashi mai cike da tsantsar tsana,kuma wani abu daya ɗaure mashi kai lokacin da suka haɗa ido,Sai yaga tana gyara wuyan rigarta,saboda ƙirjinta daya fito sosai,kamar taga wani wanda ba muharraminta ba,Tashin sense,


Miƙa mashi tray ɗin hosana tayi"Gashi Ya rafayet,Mommy ce ta haɗa mata breakfast ɗin ,"

  "Okey,"ya ambaci hakan tare da sanya hannu ya kar6i tray din,ɗan madaidaici,ya daurashi akan lap ɗinshi daya haura saman gadon,

  Juyawa hosana tayi da gudu tabar dakin saboda taje taci abincinta,

   "How was your body?hosana ta sanar dani cewa jiya baki ci isasshen abinci ba,haka ne"?

  Rai a6ace tace"eh,saboda bana jin yunwa,"

   Ajiyar zuciya ya ɗan sauke kafin yace"okey,Yanzu ya kamata kici,ko don saboda maganinki da zaki sha,"

  Bata tanka mashi ba,ta sauko daga saman gadon dakyar take iya taka ƙafarta,toilet ta shige,yana jiyo nishinta daga inda yake zaune,wahala take sha ba ƙadan ba,idan zatayi fitsari,sai data wanke fuskarta ta kuskure bakinta,Tukunna tafito daga toilet ɗin,ta koma saman gadon ta zauna,batare data kalleshi ba,

  cup ɗin dake ɗauke da Tea ya soma kokarin kwafa mata a bakinta da nufin ya bata da kanshi,da sauri tasa hannu ta kar6e kofin,Tasa abaki tana sha,abun ya bashi mamaki,kaf ta shanye tea din, 

 "Bari na baki abaki....naga hannunki na kerma "

  A ƙule tace"Zanci dakaina,"bata jira ya ƙara magana ba,ta sanya hannu ta bude plate tana cin abincin da kanta,natsuwa yayi yana kallonta,yadda take moving lips ɗinta wurin taunar abuncin ba ƙaramin yanayi take jefa shi ba,bawan Allah ya kafe ta da ido yana kallonta,a tsiyace take cin abinci,kafin ta haɗiye wani ta tura wani abakinta,Har ce mata yayi taci a hankali karta shaƙe,Amma ko sauraronshi batayi ba,Ita burinta ya tashi ya tafi shiyasa take sauri ta gama cin abincin yayi mata allurar koya tafi ya bata wuri,


Bayan ta kammala cin abincin ,ta miƙa mashi hannun sai kace ba ita bace wannan me tsoron Allurar ba,Yau dai yaga abubuwan ban mamaki atattare da ita,ajiye tray ɗin yayi,Kafin ya ɗauko sirinjin allurar,ya tsira mata a cikin jijiyar hannunta,Tsabar raɗaɗi yasa ta runtse idanuwanta,tana fidda sauti"Wash Allahna,"Lumshe idanuwanshi yayi a yayin da yake kallonta,A hankali ya zame allurar daga hannun, ya ajiyeta,Magungunan ya shiga miƙa mata,ta dinga turasu abaki tana korasu da ruwan dake hannunta acikin kofi,


 Bayan ta kammala shan magungunan Ya tattarasu ya mayar acikin ledar,ya ɗauke sirinjin  allurar da sauran tarkacen Ya mike ya nufi dustbin ya zuba su aciki,

Komawa yayi gefen gadon ya zauna yana kallonta,har lokacin babu annuri akan fuskarta,So yake ya bata hakuri akan abunda yayi mata ba,data ga ya ƙura mata ido,Sai ta rufe idanuwanta tamkar maiyin bacci,ba zato ba tsammani taji saukar kiss ɗinshi a saman neck ɗinta A harzuke ta buɗe idanuwanta,tamkar zata rufeshi da fada,Amma sai ta kasa,


Yana ƙoƙarin buɗe baki yayi magana,Wayarshi dake ajiye cikin trouser pocket dinshi ta soma ringing,da sauri ya lalubo wayar tare da cirota Ya duba mai kiran nashi,

  Abbansu ne,picking call ɗin yayi kafin ya kara wayar a kunnanshi,tunkafin yayi sallama,Muryar abba ta katse mashi hanzarinshi,

  "Kana ina ne"?

  Kallon sehrish ya ɗanyi,ta kawar da idonta gefe,

 "Nazo duba jikin reesh ne,"

 Abba yace"Okey,Dama ammi ce ke son ganinku"

  Hakanan Yaji gabanshi ya faɗi rass,





(ga duk mai buƙatar Littafin Abban Sojoji from book one to 3,Yayi mun magana,Sannan idan mutun nada tambaya dangane da littafin nan shima yayi mun magana,Saboda masu yaɗa  jita jita,Da kuma mahassadan dake kokarin 6ata mun suna,its better mutun ya tunkareni idan ma tambaya gareshi,Su kuma munafukan dake kokarin  shiga gonata Allah Ya basu sa'a,tamkar taki suke agare ni)

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*



*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*









Tunkafin ma yaji dalilin kiran Na Ammi har ya fara jin fargaba,duk da baya tunanin Sehrish zata bashi matsala,Ajiyar Zuciya ya ɗan sauke Still Eyes dinshi na akan fuskarta,


Yana kokarin sanar da ita kiran da Ammi ke yi masu,Mommy Azeema ta shigo cikin ɗakin da sallama abakinta,"Assalamu alaikum",


Har suna haɗa baki wurin Amsa mata sallamar"Wa'alaikum Salaam,"tunda ta shigo idanuwanta na akan Sgr daya tsare Sehrish da ido,


Gyaran murya ta ɗanyi"Rafayet Ya mai jikin"?

  Daƙyar ya iya amsa mata"jiki Alhamdulillah,fatan kun Tashi lafiya,"

  "Lafiya lou,"kafin ta mayar da idanuwanta kan Sehrish"Ya jikin naki Daughter"?

  Cikin sanyin murya tace"da sauƙi Mommy,"

  "Allah ya ƙaro sauƙi,"

"Ameen,"ta amsa mata,


Miƙewa Tsaye Sgr yayi a tsanake Ya soma magana"Ammi nason ganinmu yanzu,"

  Hajiya azeema tace"Eh dama Daga can nake,nazo ne don in taimaka mata mu tafi,Sai kuma na same ku atare,"

  "Okey,"ya ambaci hakan tare da kama hanyar fita daga ɗakin,


Daƙyar sehrish ta sauko daga saman gadon,Da taimakon Hajiya Azeema ta canza rigar jikinta zuwa jallabiya baƙa,Ta yafa mata gyale,Yadda kasan balarabiya saboda hasken da tayi,


Dafa Hajiya azeema tayi itama ta tallabota don ta samu damar yin tafiya,Fitowa suka yi daga ɗakin,kaitsaye suka Nufi bedroom ɗin Ammi,Lokacin da suka Shiga,sun tarar da Abba da Abusufyan Zaune gefen gadon Ammi,Mommy na zaune saman Sofa tare da Sgr duk ya kame kanshi,Yayin da Ammi ke zaune Saman Kujerar gaban Madubin ɗakin ta juyo da ita,Yadda zata samu damar ganin kowannansu,


Ganin sun shigo Yasa Mommy ta mike ta koma gefen Abba ta zauna,da hannu ta nuna ma Sehrish gefen Sgr,Ba don taso ba,ta zauna kusa dashi,ƙamshin turarenshi duk ya cika mata hancinta,a hannun Sofa ɗin Hajiya Azeema ta zauna ta 6angaren Sehrish,cike da girmamawa Sehrish ta soma gaishe dasu,Fuskar kowannansu asake suke Amsa mata gaisuwarta,haɗi da yi mata Ya jiki,daƙyar take amsa masu da sauƙi,daga haka Ta duƙar da kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannunta,sai da kowa ya natsuwa,tukunna Ammi ta soma magana atsanake,

  "Muyi ma Annabi salati" gaba daya suka amsa da Sallallahu alaihi wasallam,bayan sun gama Ammi taci gaba"Alhamdullilah,Naji daɗin ganin kowannanku,ko ban faɗi ba nasan kunsan dalilin kiran naku da nayi,dafarko dai kuskure ne anriga da an yishi,tun daga kan iyayenku da suka yanke shawarar yi maku aure batare da sunyi shawara dani ba...."dakatawa ta ɗanyi da yin maganar tana mayar da numfashi,kafin ta ɗaura da cewa"kamar yarda nace zanyi adalci atsakaninku,in har kun amince zaku cigaba da zama da junanku to falillahil Hamdu,ba wanda zai raba ku,In kuma ɗaya daga cikinku Ya nuna baya ra'ayin auren to za'a rabashi,'


Hankalin Sgr ba ƙaramin tashi yayi ba,don har saida ya ɗago ya kalli Ammi dake kora jawabi,hakanan ya dinga jin zuciyarshi na bugawa,


"Amma kafin In fara jin ra'ayoyinku,zan yi maku wata ƴar nasiha,"kowa ya kasa kunne yana sauraronta,sosai tayi masu nasiha akan Kuskuren da kowannansu Yayi,tun daga kan Abusufyan da Abba da suka haɗa auran har izuwa kan tursasa mashi akan Ya saketan da sukayi,Sgr ma tayi mashi faɗa sosai Akan abunda ya aikata,jikin kowannansu Yayi sanyi sosai,


Bayan ta kammala Yi masu nasihar Ta kalli Sgr tace"Inaso naji ra'ayinka game da yarinyar nan,Shin kana ra'ayin cigaba da zama da ita amatsayin matarka ko kuwa.... ?"


Jim ya ɗan yi kafin ya jinjina kanshi tare cewa"zan cigaba da zama da ita a matsayin matata,"Sehrish tayi mamakin amsar da ya bayar,kuma bilhakki dagaske yayi maganar,On a serious matter,

  Nunata Ammi tayi da sandar hannunta"Saura ke,Shin kin amince zaki cigaba da rayuwa dashi A matsayin mijinki......?"gaba ɗaya ido ya dawo kan Sehrish ana jiran jin amsarta,musamman Sgr duk da bai ɗago ya kalleta ba,Amma a ƙagare yake da yaji amsarta,haka hajiya azeema ma duk ta ƙosa taji amsar da Sehrish zata bayar,itama Mommy idonta na akan Sehrish,


Jin tayi shiru Yasa Abusufyan Ya tanka mata"Daughter amsarki muke son ji,"


A ruɗe tace"Ni banason shi,bazan cigaba da rayuwa dashi ba,Dan Allah a rabani dashi,"


A firgice Sgr ya ɗago yana kallon fuskarta,tashin hankali,Ko a mafarki bai ta6a tunanin Sehrish zata iya furta waɗannan kalaman ba,


Ita kanta Hajiya Azeema sai da gabanta Ya faɗi jin amsar da sehrish ta bayar,Babu wanda ya tsammaci hakan daga gareta,


Daƙyar Sgr ya iya daurewa Ya cije Ya soma magana cikin sanyin murya ta wanda ya karaya"Idan har akan laifin da nayi maki ne,inaso ki sani ba'a son raina nayi maki hakan ba,kuma ina baki hakuri akan hakan,'


Girgiza kai ta shiga tana fadin"Dan Allah Ammi a rabani dashi,Ya rafayet bai ta6a sona ba,yana so yaci gaba da zama dani ne saboda wata manufa tashi,ya fadi hakan ne saboda Yaci gaba da ƙasƙantar dani a matsayin ƴar aikinshi ba matarshi ba......'


Jikinshi har tsuma yake yi,ba don Allah yasa Manyanshi na akusa ba,da ba abunda zai hana ya ham6are bakinta,just speechless Yama rasa me zaice!!


Ƙasa ƙasa da murya Hajiya Azeema ta soma yi mata magana"Ki shiga natsuwarki,sannan ki gyara kalamanki,ban hanaki ki faɗi ra'ayinki ba,Amma ina guje maki kizo kiyi abunda zakiyi danasani,"


Mommy kuwa cewa tayi"har yanzu yarinyar nan bata dawo hayyacinta ba,tundaga kan yarda take magana babu natsuwa atare da ita,nasan ta faɗi hakan ne saboda Abunda Rafayet yayi mata,"


Shidai Abusufyan bai tanka masu ba,sam baiji dadin abunda Sehrish tace ba,Saboda yanzu kowa Shi zai zarga,za'ayi tunanin koshi ya tunzurata ne,Kamar kuwa ya sani tunda Sehrish ta fara surutannan idanuwan Abba na akanshi,Kallon tuhuma kawai yake yi mashi,


Duk wannan abun dake wakana Akan Kunnan Omar,wanda bai jima da shigowa ba,Yana atsaye Ya goya hannayenshi Asaman kirjinshi,Hankinshi ba ƙaramin tashi yayi ba jin abunda Sehrish take faɗi,dama sai da yakawo hakan aranshi,ta tsorata ne sosai,gani take kamar in taci gaba da rayuwa dashi zai kasheta ne wata rana,


"Sure i know initially nayi accepting aurenta don tayi mun aiki,ko wannan lokacin banyi don na ƙasƙantar da ita ba,kuma na amince da aurenta ne,don ina ra'ayin zama da ita,Ba amatsayin contract ba"tuni idanuwanshi sun cicciko tab da kwalla,duk ya muzanta a idanuwansu,tun da yake arayuwarshi bai ta6a tunanin wata ƴa' mace zata Iya rejecting dinshi ba,abun Ya girgiza shi fiye da tunanin me tunani don tuni zazza6i Ya rufar mashi,duk da Sanyin A.c ɗin dake shawagi a ɗakin,Hakan bai hanashi Yin zufa ba,fuskarshi sharkaf take tamkar an watsa mashi ruwa,kowa Ya lura da Yanayin da Sgr ya shiga,


"Ni shaida ne Ammi,wlh Rafayet Yana sonta sosai,da ace baisonta ko aurenta bazai kar6a ba,kuma abunda ya faru atsakaninsu tsautsayine,ba don son ranshi yayi mata hakan ba"Marshal Omar ne yayi maganar,duk ya shiga damuwa,Sehrish naso ta 6allo masu aiki,


"Ki fadamun me nayi Maki da har kike guduna?Na ta6a cutar dake ne hakanan,bayan wannan abunda ya faru"?yayi maganar muryarshi tamkar zai fashe da kuka,yayin da idanuwanshi ke akan fuskarta,kwata kwata babu annuri akan fuskar Sehrish,ta canza tamkar ba ita ba,


"Idan har akwai abunda nake yi maki,wanda bakyaso ki fadamun zan daina,"cikin lalama yake lallashinta,


Ammi dai ta kasa kunne tana sauraron kowannansu,tana jira su gama,Ta zartar da hukuncin daya dace,


Fashewa Sehrish tayi da matsanancin kuka,tamkar ranta zai fita,cikin shessheƙar kuka take cewa"Don Allah A sanya ya sake ni,shi dakanshi yace duk hukuncin dana yanke mashi zai kar6a hannu bibbiyu don haka inaso Ya bani takardar Sakina,kuma bayan aurenmu saida ya bani damar cewar Zan iya kula duk wanda nakeso koda Namiji ne shi bai damu ba,don haka Ni Ina da wanda nakeso Yanzu haka ......... ."

  Gaban Sgr ne Ya faɗi rasss!lokaci guda yabi ya susuce ya dabarbarce,jikinshi sai kerma yakeyi,Zuciyarshi sai faman tafarfasa take yi,Ya harzuƙa sosai but he's trying to control his anger,don ta fara wuce gona da iri,


Kowa na wurin sai da yayi mamakin kalaman sehrish basu ta6a tsammanin zata iya furta su ba,gaba ɗaya ammi ta karancesu tsaf,


Gyaran Murya ta ɗanyi,hankalinsu ya dawo kanta,yayin da idanuwanta ke akan Sehrish dake ta faman matsar kwalla,

  "Share hawayenki,kukan ya isa haka!Ae dama nace zanyi maku adalci atsakaninku,To ki kwantar da hankalinki,"jin wannan maganar yasa Sehrish taji hankalinta ya kwanta,


  "Amma inaso ki natsu kiyi tunani kafin ki yanke hukunci,don na lura kina acikin fushi sosai,kada kiyi irin kuskuren da iyayenku suka yi na tursasa mashi akan Ya sake ki,wanda silar hakan ne yasa shi rafayet din Ya huce akanki,daga baya akazo ana danasani,to banaso kiyi danasani daga baya jikata,Tabbas Rafayet bai kyauta maki ba,amma inaso ki sani saboda son da yake yi maki ne duk yajawo hakan,saboda bayaso a rabashi dake,yayi tunanin hakan shi zaisa abarmashi ke sai dai kash Yayi abu cikin fushi,kuma daga baya yazo yana danasani,sannan kuma karki manta da kanshi ya gyara 6arnar da yayi maki,wanda da ace da mugunta yayi maki zai tafi ya barki ne,Kiyi rai ko ki mutu,Amma saboda yasan bai kyauta ba,Ya tsaya har sai daya ga kin samu Lafiya,Ina faɗa maki wannan ne ba don ina goyan bayanshi ba,Sai don ina guje maki yin danasani,musamman idan ya kasance kinason Shi tun fil,azal,"Ajiyar zuciya ammi ta ɗan sauke bayan takai ƙarshen maganarta,ɗaya bayan ɗaya take kallon fuskokinsu,ɗakin yayi tsit baka jin komai sai shessheƙar kukan Sehrish,


Cigaba da magana tayi a tsanake"zan tambayeki a karo na ƙarshe,Amma inaso Ki fara yin tunani kafin ki bani Amsa,kinaji ko"?


Cikin shessheƙar kuka tace"Eh ammi,"

Ita kanta ammin bason rabasu takeyi ba,don ta fahimci akwai soyayya mai ƙarfi atsakaninsu,daƙyar ta iya buɗe baki tace"Har yanzu kina akan bakanki na son rabuwa dashi"?cike da fargaba ammi tayi maganar,ba ita ba hatta su Mommy,kowa hankalinshi ya tashi,Sgr kuwa tuni Ya karaya,ya rufe fuskarshi da tafin hannunshi,


Cike da kwarin guiwa tace"Eh,Nidai arabani dashi,"yadda kasan Ya shako wuyanta haka yake ji,takaishi ƙarshe,tuni ciwon kai ya farmasa,


Duk yadda Abusufyan yaso ta ɗago su hada ido don ya dakatar da ita,Amma yarinyar nan ta kafe,taki kallon kowa daga cikinsu,


Jinjina kai ammi tayi"Shikenan,rafayet ina fata kaji abunda tace!tana buƙatar ka sake ta,"Yadda kasan tayi magana da bango haka Sgr yayi masu shiru,baice uffan ba,domin kuwa baya acikin hayyacinsa,Sama sama yake jinsu,


"Amma kuma wani hanzari ba gudu ba,"ammi ce tayi maganar tana kallon Sehrish,

  "Har yanzu da sauran jikinki kuma shine likitan dake dubaki,ni aganina,me zai hana ki bari kiji sauƙi sosai sai ya sake ki?Ni nayi maki alƙawarin da zarar kinji sauƙi zansa ya sake ki,"

Tunda Ammi taso ma magana,Abba ya fara sakin murmushin gefen fuska,don ya gane wayau ammi takeso tayi mata,don tasan kafin lokacin zaiyi wuya in bata sauko daga fushin da take yi dashi ba,

  "Ki amince Sehrish,kinga baki da lafiya kuma shi kaɗaine zai iya dubaki acikin gidan nan,shi yasan kan abun,kuma kinga da igiyar auran nan kawai zai iya yin hakan,"Hajiya Azeema ce ke yi mata raɗa acikin kunnanta,shiru sehrish tayi da alama tana yanke shawara da zuciyarta ne,ita aganinta za'a iya ɗauko wani likitan yaci gaba da dubata ba dole sai shi ba,tana kokarin bude baki tayi magana Hajiya azeema tayi saurin cewa"Ta amince,"

  Ammi tace"Nafiso naji ta bakinta,"

  Nauyin Hajiya azeema da take ji ne yasa tace"Na amince,"saboda bata son ta ƙaryatata," dama da biyu Hajiya Azeema tayi mata hakan,don tasan Sehrish bazata Iya musawa ba,in har tasa baki,"


  Ajiyar Zuciya kowannansu ya sauke,har Lokacin Sgr bai ɗago ya kallesu ba,


"Shikenan magana ta ƙare,Zamu zuba ido har Allah ya baki Lafiya,daga nan ni kuma zan Kar6ar maki takardar sakinki,"tana kai ƙarshen maganar,Tace ma azeema"Ki taimaka mata,ta koma ɗaki,"

  "To ammi,"ta amsa tare da ruko sehrish ta miƙe daƙyar,suka fuce daga dakin,


Bayan fitarsu ammi taci gaba da magana"kar kuga laifinta,tana cikin wani hali ne wanda dama karshe hakance zata faru,anma ci sa'a da ta dawo hayyacinta don mafi akasarin wadanda irin hakan ya faru dasu sukan fita hayyacinsu tsawon lokaci wasu ma ta6in hankaline ke samunsu,yayin da wasu kuma daga haka sai su fara tsoron maza....." dan dakatawa tayi sakamakon shigowa da Hajiya Azeema tayi,ta koma kan hannun kujeran data tashi ta zauna,


Ammin ta dasa"kamar ita dae,na tabbatar bata rasa son shi kawae abunda yayi mata ne yasa take tsoron cigaba da zama dashi",

   "Tabbas Ammi tana son shi wllh don ni shaida ce baki na da nata munyi maganar lokacin da aka daura masu Auren,wanda hakanne ma yasa lokacin da ta gano dalilin da yasa ya auretan ba don yana sonta bane don tayi masa aikine yasa ta shiga wani hali har ta kulle kanta acikin Toilet"Hajiya Azeema ce tayi maganar,gaba daya suka shiga jinjina kai,

Kallon Sgr Ammi tayi wanda har lokacin tafin hannunshi na rufe da fuskarshi,sai dae duk abunda suke fada yana jinsu,


"Rafayet",Ammi ta kira sunanshi,a hankali ya zame tafin hannunshi ya kalleta, blue eyes dinshi sun canja launi don ba karamin sarawa kanshi ke mashi ba,

"Matarka tana son ka tunda ga tabbaci nan daga Azeema,muma kuma ba son rabuwarku muke ba,don haka inason kayi amfani da wannan damar dana samar maka wurin ganin ka shawo kanta daga dokin zuciyar da ta hau,kaima kuma inason na kara jan hankalinka,ba komae ne karfi ke samarwa Mutun ba,wani abun in kace zaka sa mashi karfi to kuwa zaka rasa shine gaba daya kamar dae aurenka yanzu,inason kabi komae a hankali in sha Allah komae zai zama daidai,sannan wannan bakar zuciyar dole sai ka rinka yin yaki da ita,ka rinka neman tsari daga wurin Allah akan ya rabaka da sharrinta don in dae zaka rinka yanke hukunci cikin fushi to wllh ka dinga yin dana sani kenan,A duk lokacin da wani abu ya 6ata ma rae kayi kokarin ganin ka daidaita natsuwarka kafin ka yanke hukunci,Yadda kake yin nasara Akan aikinka haka nikeson ka rinka yin nasara akan zuciyarka aduk lokacin da ta taso maka kaji?" dan jinjina mata kae yayi,

Cike da zolaya ta juya ta kalli su Abba tace"Yakamata a siyo mashi buta ya rinka yin alwala da ita,yana rage sauran ruwan yana sha ya daina yi a famfo ko Allah ya sanyaya mashi ita"gaba daya sukae Murmushi,shi dai still yayi bai tanka ba,


"Ko akwae mai magana?" gaba daya suka ce a'a,kallon Marshal Omar tayi"sai ka rufe mana da Addu'a"gaba daya suka daga hannu harda Mommy,Omar ya shiga jero Addu'oi daga bisani suka shafa.


Daga haka Ammi ta basu Iznin Tafiya,


ƙoƙarin miƙewa Sgr yayi wani irin  Jiri ne ya soma ƙoƙarin kwasarshi,da sauri Omar ya ruƙe shi,ya taimaka mashi har suka fita daga ɗakin,


A bedroom ɗinshi Omar ya shigar dashi,Kaitsaye ya faɗa yaraaaf saman gadon,jiki babu kwari,yadda kasan baya numfashi,hawa saman gadon Omar yayi,Yasa hannu ya cire mashi rigar jikinshi,ganin yadda zufa ke tsastsafowa daga jikinshi,


"Bro,Are u not feeling well"?yayi tambayar yana kallonshi,ya runtse idanuwanshi sai faman Cizon pink lip ɗinsa yake yi,daƙyar ya iyacewa"Omar,zuciyata babu daɗi,yarinyar can ta 6ata mun rai,wai har ni zatace bataso?bata ra'ayin zama dani?wacece ita?mata nawa suke neman wannan damar a wurina"?......daƙyar sautin muryarshi 

 ke fita,da wani irin hucin zafin zazza6in jikinshi,


murmushin gefen fuska Omar ya saki,wato har yanzu rafayet bai gane cewa Ya afka tarkon so ba,babban takaicinshi Yadda Sehrish ta furta bata ra'ayinshi agaban kowa,ba ƙaramin ƙona mashi rai tayi ba,


"Am sorry bro,just forget about her,idan ka shareta zata dawo maka ne"

  A hasale yace"tafita daga cikin zuciyata mana,"

  Ƙiris ya rage Omar ya fashe da dariya,Aranshi yace"Kaine ka sanyata acikin zuciyarka malam,"

   Miƙewa yayi daga kwancen da yake,Ya sauko ƙafafunshi ƙasa,sumar kanshi duk ta rufe mashi gefe da gefen fuskarshi,

    "Zan shiga toilet,pls before na fito,ina bukatar magani ciwon kai,"yana kai ƙarshen maganar,ya sauko daga saman gadon Ya nufi toilet ya shige,kafin ya fito Omar ya ajiye mashi medicine ɗin asaman side drawer tare robar ruwa,


Sehrish kuwa,bayan mommy azeema takaita ɗakinsu,Saman gadon ta haye fuskarta sharkaf da hawaye,taso ace Sgr ya sake ta,don yanzu batason duk wani abu da zai alaƙantata dashi,ta wani 6angaren kuma taji daɗin hukuncin da Ammi ta yanke,koba komai tayi mata alƙawarin zata amsar mata takardar sakinta,


Tana cikin yin wannan zancen zucin nata,Hajiya azeema ta turo ƙopar ɗakin fuskarta ɗauke da matsananciyar damuwa,xama tayi daga gefen gadon cikin sanyin murya ta soma magana"Why sehrish?Don me zaki nemi ya baki takardar sakinki!Ba kina sonshi ba"?

  cikin shessheƙar tace"Yanzu bana sonshi aunty azeema,bana iya rayuwa dashi,Nidai kawai nafison arabani dashi,"

  "Indan kan abunda yayi maki ne yasa kika yanke shawarar rabuwa dashi,to kuwa zaki tabka kuskure,Domin kuwa Kina sonshi,Kuma shima ba ason ranshi yayi maki haka ba,Kuma ga dukkan alamu ba ƙaramin so yake yi maki ba,wanda silar hakan yasa shi yi maki haka duk don kada araba shi dake....."dakatawa ta ɗanyi da yin maganar 

  "Aunty azeema,wlh baya sona,bani yakeso ba,kema kinsani yana yin amfani dani ne kawai don biyan buƙatarshi,Sannan don naci gaba dayi mashi aiki,ba amatasayin matarshi ba,tunda nake dashi bai ta6a furta mun kalmarso ba,"tana magana hawaye na wanke fuskarta,

  Shiru azeema tayi tana kallonta,Lamarin Ya fara bata tsoro,don dagaske sehrish take yin maganarta 

Cikin sigar lallashi tace"Haba sehrish,duk irin wahalar dana sha wurin ganin na gyara tsakaninki da Sgr saboda in taimaka maki ki samu soyayyarshi,amma shine kike ƙoƙarin lalata mana shirinmu why pls"?cike da takaici tayi maganar,

"Am sorry aunty azeema kada ranki ya 6aci,Wlh yanzu bana sonshi,Ko son kallon fuskarshi ma banayi,"

  Jinjina kai Hajiya azeema tayi"Shikenan,tunda kin nuna baki sonshi,bazan tursasa maki ba,"shiru suka ɗanyi na wani lokacin kafin tace"inaso zanyi wanka,jikina duk yayi mun tsami,"

    "Okey,Yakamata ki dage da yin sit bath,ko kin dawo daidai,naga tafiya ma daƙyar kike yinta,kuma bazan fasa gyaraki ba,kamar yadda nayi niyya,zan ɗaura daga inda na tsaya ne,sannan cikin kayan dana kawo maki akwai wasu sabulai na nan,zasu taimaka maki sosai,idan har kika dage da yin amfani dasu"


"Shikenan,nagode sosai,"saukowa tayi daga saman gadon,a hankali take tafiya,Azeema na binta da kallo harta shige cikin toilet,Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta miƙe ta fuce daga ɗakin,


After some minutes,sehrish ta fito jikinta ɗaure da towel fari,gaban mirror ta zauna,ta jima tana kallon kanta,ta cikin mirror batare data motsa ba,ita kanta ta lura da sauyawar da tayi,kodan saboda jinyar da tayi ne yasa tayi haske sosai,Amma tafi tunanin Jinin Sgr ne da aka ƙara mata, yasa tayi haske,Anata shirmen,hannu tasa tana shafa ƙashin wuyanta daya fito,Ba ƙaramin kyau yayi mata ba,almost 15 mins,Tana zaune,kafin daga bisani ta mike,Ta koma gaban wadrobe ta budeta,doguwar riga ta ɗauko mara nauyi red colour ta zurata ajikinta,Lalla6awa tayi ta koma saman gadon,idanuwanta cike tab da ƙwalla tarasa meke yi mata daɗi,


Yinin ranar daga ita harshi babu wanda yaci abinci,saboda yanayin da suka tsinci kansu,ita tana kukan arabata dashi,Yayin dashi kuma yake neman mafita kafin lokaci ya qure mashi,Saboda tsabar farga duk in agogo ta buga sai gabanshi ya faɗi,saboda lokacine ke tafiya......'acikin bargonshi ya yini kiran sallane kawai ke fito dashi,kamar yadda itama Take ƙumshe acikin bargonta,Kiran sallah ne kawai ke tayar da ita,


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 8:30 na dare sehrish na ƙumshe cikin bargo,ita kaɗai ta rage acikin ɗakin,Su jahad da oummansu sun fita wurinsu Mommy dake zaune suna fira a babban palourn gidan,tare da gwaggon katsina dasu hafsat,duk sun hallara a palourn,Hada wasu daga cikin matasan gidan,Gwanin ban sha'awa,


Turo ƙopar ɗakin akayi,Duk a tunaninta Sgr ne yazo dubata,tuni ranta ya 6aci,jin muryar hajiya azeema ne yasa ta leƙo daga cikin bargon,

  "Ya jikin naki"?

"Da sauƙi,"ta amsa mata a yayin da take kokarin mikewa daga zaune,ta sauko ƙafafunta kasa,

"Me zai hana ki koma ɗakin azmee da yin jinyar?nan kamar zaki takura ne,"

  Girgiza kai sehrish tayi"A'a,nafi jin daɗin zama anan,"

  "Gaskiya ni ban goyi bayan ki zauna anan ba,can sai kin  fi sakewa,Yanzu haka ma daga can ɗakin nake,Na gyara maki shi,ki taso in taimaka maki ki koma can,kinga nan yayi maki kaɗan,kuma dama can kike kwana ae "

  Ba don taso ba,tace"toh,"

Miƙewa tayi hajiya azeema ta taimaka mata,suka fito daga ɗakin takaita ɗakin azmee,Lokacin da suka shiga cikin ɗakin,An gyara ko'ina tsaf sai ƙamshi ke tashi acikinshi,ita kanta ba ƙaramin kyau ɗakin yayi mata ba,"


Kaitsaye saman gadon ta hau ta kwanta,tana faman sauke ajiyar zuciya,

  'Bari na kawo maki dinner ɗinki nasan kina jin yunwa,"

  "Aunty kona ci,Amayar dashi nake yi,bakomai ke zama cikin cikina ba,bana jin daɗin abincin ma,"ta ƙarasa maganar,tare da jan bargo ta lullu6e rabin jikinta,

  "Kada ki damu,ba wani abu mai nauyi zan haɗo maki ba,in sha Allah,ba zaki amayar ba,".  

  "Toh,"iya amsar data bata kenan,

Bayan Aunty azeema ta fita daga ɗakin abakin ƙopar ɗakin ta tsaya,Hannu tasa cikin aljihun rigar jikinta ta ciro wayarta,


Call log ta shiga,ta danna ma layin Marshal Kira,Tana fara ringing ya ɗaga awayar,

  "Omar,ina rafayet din?Yakamata yazo ya dubata,yanzu haka na dawo da ita ɗakin azmeen,inaga kamar zasu fi sakewa anan,"

  On the other hand Omar yace"Yanzu zanyi mashi magana,nagode ssai,"

Daga haka su kayi sallama,Ta nufi kitchen,


After some minutes harta fara jin bacci,hajiya azema ta turo kopar ɗakin hannunta ɗauke da tray,Wanda ta shirya mata dinner ɗinta,a saman table ta ajiye mata shi,tare da janyoshi izuwa gaban gadon,

  "Ki daure ki ci,Zaki ji sauƙin jikinki,"

  Yunƙuwa sehrish tayi daƙyar ta miƙe zaune,ta sauko da ƙafafunta ƙasa,

   Wayar hajiya azeema ce ta soma ringing,Da sauri tace"ina zuwa,ki fara ci kafin in dawo,"tana kai karshen maganar tayi saurin fucewa daga ɗakin,


Ajiyar zuciya sehrish ta sauke,a hankali ta kai hannu ta ɗauki kofin tea mai zafi,takai bakinta tana kur6arshi a hankali,ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,tana cikin Shan tea ɗinnan,Taji an turo ƙopar ɗakin,Afirgice ta ɗago don taga wanene koda sukayi arba da Sgr,Nan take ta saki kofin hannunta,Ya faɗi ƙasa,ruwan tea ɗin data rage ya zube,


Abakin ƙopar ya tsaya yana kallonta,yayin da ya goya hannunshi asaman ƙirjinshi,wani irin daddaɗan ƙamshine ke fitowa daga jikinshi,Yana sanye cikin Sleeping dress dinshi,blue colour, hasken shi ya fito ssai,ya ɗaure sumar kanshi ta baya,Kyau Iya kyau,


Duk da taji tsoranshi,amma bata bari ya gane hakan ba,tuni ta ɗaure fuska,tare da kawar da idanuwanta gefe guda,


Slowly ya ƙarasa cikin ɗakin tare da samun wuri gefen gadon ya zauna a kusa da ita,gaba ɗaya ƙamshin turarenshi ya cika mata hancinta,sam bata so zuwanshi ba,yayi tunanin zata gaishe shi amma ko kallo wannan bai isheta ba,

  "Ya jikin naki,"?

daƙyar ta iya amsa mashi"da sauki,"

  Shiru su ka ɗanyi wani lokaci,bakomai yake tunawa ba,face maganar dasuka tattauna da Omar,

    "Laifin me na aikata maki da har kike son na sake ki"!

    Wannan tambayar da yayi mata ba ƙaramin 6ata mata rai yayi ba,wato baima son laifin da yayi mata ba,Saboda shi bai ɗauki abun serious ba,

  "Ko don saboda abunda ya shiga tsakanina dake ne"?

  Girgiza mashi kai tayi Alamar a'a,


Ya kuma cewa"I won't hurt you anymore,i promised u"

 Ko uffan bata ƙara ce mashi ba,ranshi ya 6aci sosai,hakanan ya daure yaci gaba da magana,

   "Its Okey,just calm down ur mind,da zarar kinji sauƙi,zanyi maki yadda kikeso,Hakan yayi maki"?.

  ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

Hannu yakai tare da ɗaukar cup din data jefar,Ya haɗa mata wani tea din Ya miƙa mata,

  Hannu tasa ta kar6a,har lokacin bata ɗaura idanuwanta akanshi ba,

  Sosai tashiga shan tea din,don ba ƙaramar yunwa take ji ba,

  Abunda zai baka mamaki da kanshi,Ya shiga yin serving ɗinta,bayan ta kammala shan tea ɗin,Ya zuba mata farfesu acikin plate mai zafin gaske,yaso ya bata abaki amma sai ta nuna cewa zata Iyaci da kanta,natsuwa yayi yana kallonta,Daƙyar take ɗaukar Naman  tana turawa acikin bakinta,Jurewa kawai yake yi,amma shi kaɗai yasan yadda yake ji acikin zuciyarshi,baisan ya zaiyi ya shawo kanta ba,gashi Omar ya gargaɗeshi akan ya guji 6acin ranta,kuma aduk lokacin da yake tare da ita,ya manta da matsayinshi na Suregon general,


Ganin ya sanya hannunshi acikin plate ɗinne,yasa ta dakata da shan farfesun,batare data ɗago ta kalleshi ba,sai ma cire hannunta da tayi,Har ya harzuƙa zai daka mata tsawa,Sai ya tuna sharuɗɗan da Omar ya bashi,a hankali ya furta Ya salaam,

  Sai da ya cire hannunshi daga cikin plate ɗin tukunna ta mayar da nata hannun taci gaba ci,'abun ya ɗaure mashi kai,Kuma ya kasa yi mata komai,,

   Turo ƙopar ɗakin hajiya azeema tayi fuskarta ɗauke da murmushi,hannunta na ruƙe da ledar magungunan sehrish,Asaman bedside drawer ta ajiye mashi ledar,"kafin ta juya ta nufi ƙopar fita daga ɗakin,A lokacin Amrish na ƙoƙarin shigowa ɗakin,su kayi kici6us da Aunty azeema,da sauri Amrish ta gaishe da ita,

  Fuskarta ɗauke da murmushi ta amsa mata,

  "Lafiyalou,amrish har an gama firar"?

  "A'a,bacci nake jine,"

  Ruƙo hannunta hajiya azeema tayi,"mu tafi ɗakina ki kwanta,"batare da tayi mata musu ba,tabita suka nufi ɗakinta 


Bayan sehrish ta kammala cin abincin,ya bata magungunanta,kafin ta gyara kwanciyarta saman gadon,Sai faman hura hanci takeyi,ita duk atakure take jinta,saboda kallon Da sgr keyi mata,ta kosa ya tafi yabar mata ɗakin,a ƙarshe data lura daɗin kallonta yake ji,Sai ta janyo bargo ta lullu6e jikinta duka hada fuskarta,


Kusan minti 5 ta soma tunanin koya tafi ko yana nan oho,Hannu tasa a hankali ta ɗan zame bargon ta leƙo don taga idan ya tafi,Abun mamaki saita same shi zaune yana cin sauran abincin data rage,ta6e baki tayi kafin ta koma cikin bargon,tayi mamaki sosai,Ko meyasa yake cin kingin abincinta Ohom masa,


Bawan Allah,Duk yinin ranar baici abinci ba,saboda damuwar daya shiga,Shiyasa yake cin sauran abincin data rage,ko zai samu sauƙi acikin zuciyarshi,don ba ƙaramin ƙona mashi rai tayi ba,Bayan ya kammala cin abincin,Ya kora da ruwa mai sanyi,ita duk a tunaninta zai tafi ne idan ya kammala cin abincin,amma har wurin ƙarfe goma sha biyu na dare,Yana zaune gefen gadon,Ya kasa motsawa,ya saba da ita koda yaushe a irin wannan lokacin suna manne da junansu,ko yaje ɗakinshi bazai iya runtsawa ba,Kwarama ya zauna yana kallonta nannaɗe cikin bargo,zaifi samun natsuwa,



Boss Bature✍️



_Ina rokon Allah Ya bani Ikon Kammala Littafin Nan cikin sati mai zuwa I need ur prayers,ga duk mai buƙatar karanta Littafin abban Sojoji from book one two 3 ya tuntu6i ne,Amma ta whatsapp za'ayi mun magana 08103884440_







  




  

  


 

[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💖💖💖💖

💖💖💖

💖💖

💖 *ABBAN SOJOJI* 💖

                                 💖💖

                            💖💖💖

                       💖💖💖💖


```The father Of Soldiers```



          *🔥TAKUN ƘARSHE🔥*


Story 

       &  

       Written 

                   by 

      *_Hafsat Bature_*


          ~(Boss Lady)~




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




Dedicated to my beloved sisters. 😍   




Proud Of My First Novel💋


_Warning banyarda wani yayi amfani da wani sashe na littafina ba, kada a ta6amin komai na littafina,Sannan kar a kuskura a haɗamun document,Ga mai buƙatar karanta Littafin Abban Sojoji from Book one to 3 yayi mun magana ta whatsapp 08103884440_





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*






Baccine ya fara ɗaukarshi,a hankali ya ƙarasa hawa saman gadon ya kwanta gefenta,duk bata sani ba,saboda baccin da yayi awon gaba da ita,bai jima da kwanciya ba,bacci ya ɗaukeshi,can cikin bacci ta dinga jin numfashinshi asaman neck ɗinta,mutsu mutsu ta soma yi zata buɗe idanuwanta,ta ko'ina taji tamkar an ɗaureta,gaba ɗaya sumar kanshi ta lullu6e idanuwanta,ƙoƙarin raba jikinta ta soma yi da nashi,kiciniyar data rinqayi ne tana kokarin janyeshi,Yasa shi farkawa,shi kanshi baisan ya akai suka haɗe da juna ba,sun manne sosai,gaba ɗaya ta shige ƙirjinshi,hannunshi na dafe da ita,


Fashewa tayi da matsanancin kuka,na takaicin haɗa jiki da sukayi,ga baƙin cikin hannunshi daya sanya abayanta,ta kasa janyewa,saboda nauyi,ta haɗa uban gumi akan fuskarta,


Daƙyar ya iya buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci,ɗago da kanshi yayi,ya kasance tsinin hancinshi na gogar forehead ɗinta,janye hannuwanshi yayi daga saman bayanta,karaf idanuwanshi suka sauka akan surar jikinta,rigar ta cukuikuye ta nannaɗe,Fararen cinyoyinta sun fito waje,daga sama rigar ta zame,har ta sauko under boobs ɗinta,fatar jikinta har wani salƙi take yi saboda kyau,


Kasa janye idanuwanshi yayi daga kan jikinta,Sam bata lura ba,tana ta shessheƙar kuka,hawaye sun wanke fuskar sae kace ta haɗa jiki da wanda ba muharraminta ba,


Lokacin data buɗe idanuwanta sosai,taga yadda ya zuba mata ido batare da ƙyaftawa ba,a hanzarce Ta soma bin jikinta da kallo,ranta yayi mugun 6aci duk a tunaninta shiya yaye mata rigar,don ya biya buƙatarshi,jikinta har kyarma yake yi wurin sanya hannu ta janyo rigar ta mayar da hannunta,taja can ƙasan ya rufe ƙafafun,


Shi dai baice mata komai ba,zuba mata ido kawai yayi yana kallonta,

  Cikin shessheƙar tace"Dama abunda kakeso kenan,ina jinya ma ba zaka ƙyaleni ba,"

  Aruɗe Sgr ke kallonta don bai fahinci inda zancen nata ya dosa ba,wani irin kallon tsana take jifarshi dashi,Saukowa tayi daga saman gadon,da gudu ta fuce daga ɗakin tana kuka,


Runtse idanuwanshi yayi tuni sun cicciko tab da kwalla,ta harzuƙashi sosai ranshi ya 6aci,sai daga baya ya gane me take nufi,hannu yasa ya daki mattress din,Zuciyarshi sai tafarfasa take yi,


Cusa hannunshi yayi acikin sumar kanshi yana cakuɗata,har lokacin bai buɗe idanuwanshi ba,sai faman cizon le6ensa yake yi,har sai da ya fasa shi,


Almost 15 mins,kafin ya sauko daga saman gadon ya nufi hayar fita daga ɗakin,Lokacin daya fita,Bai sameta ba,tuni ta shige bedroom ɗinsu,ta faɗa cikin toilet ta rufo ƙopar,wani irin ƙululun baƙin cikine ya tsaya mata aranta,aduk lokacin da ta tuna cewa Sgr ba sonta yake yi ba,Jikinta yake so,shiyasa har ya gaza hakura ta samu sauƙi yazo yana neman ƙara yi mata illa,hakan yasa ta ƙara jin tsanarshi acikin zuciyarta,a jikin ƙopar ta zuƙunna tana shessheƙar kuka,


Jiki a sanyaye Sgr ya wuce upstairs,kaitsaye yana shiga bedroom ɗinshi,Ya zube ƙasa saman guwowinsa,Ya kwantar da kanshi agefen gadon,Batare daya hau saman gadon ba,wani irin raɗaɗi yake ji acikin zuciyarshi,yayi mamakin dabai iya tsawatar mata ba,lokacin da take gaya mashi maganar nan ba,Ƴar ƙaramar yarinya tana shirin Zautar dashi,ta ko'ina ta gama dashi,ta kanainaye dukkan wani sashe na zuciyarshi,


Acikin wannan yanayin Omar ya same shi,yazo tashin shi sallar asuba,hankalinshi ba ƙaramin tashi yayi ba,A sukwane ya tsaya a ƙopar ɗakin yana kallonshi,still Yana zuƙunne saman guiwowinsa,ya kifa kanshi saman gadon daga gefe,sumar kanshi duk ta rufe kanshi,


A hankali Omar ya ƙarasa cikin ɗakin,zugunnawa yayi agefen Sgr,cikin sanyin murya ya ambaci sunanshi"Rafayet,"shiru bai amsa mashi ba,hannu yasa ya ɗan bubbugi shoulder ɗinshi,Sai lokacin Sgr ya amsa mashi"na'am,"

  Xama Omar yayi tare da janyoshi zuwa jikinshi,a saman kafadarshi Sgr ya ɗaura kanshi,

  "Meya faru ne"?

Shiru bai amsa mashi ba,

  "Plss tell me what's wrong with u?Meya hanaka bacci?meyasa kayi kneeling?

  Dogon numfashi yaja kafin yace"Omar,she's trying to kill me,bansan me na mata ba,ta tsani koda kallo na,Why zata yi mun haka?sai da ta bari ta saba mun da kanta sannan zatayi mun Illa"

  Tsananin tausayinshi ne ya kama Omar,don ba ƙaramin jiki yake ji ba,tun daga kan yarda yake magana,nunfashinshi na fita da huci....'

  "Pls rafayet,just be strong,har yanzu fa ita matarka ce,Mallakinka,so bai kamata kana sanya damuwa ba akanta,"

  "Omar,ba zaka gane bane....'

Shafa Sumar kanshi Omar yayi"Ka kwantar da hankalinka,zanyi magana da ita,"

  Daƙyar ya samu ya lalla6a Sgr,ya shiga toilet ya ɗauro alwala ya dawo ya shirya cikin jallabiya,jikinshi duk ba daɗi,tare da Omar suka tafi masallaci,


Bata fito daga cikin toilet din ba,Sai da tayi alwala,tukunna ta fito tana faman ɗan gyasa ƙafa,Still bata daina zubar da hawayenta ba,

  "Sehrish!"oummansu ce ta ambaci sunanta,firgit tayi tare dakai idanuwanta kan oummansu tana kallonta,zaune take saman gadon bata jima da farkawa ba,

  "Lafiyarki kuwa?yaushe kika shigo ɗakin?a ina kika kwana ne"?

  Cikin sanyin murya tace"daga ɗakin aunty azmee nake,acan na kwana,"

  "Ya jikin naki"?tayi tambayar a yayinda take saukowa daga saman gadon,Ta nufi inda sehrish take a tsaye,"da sauƙi Oumma,"rungumota abu tayi ajikinta,

  "Allah ya baki lafiya rishi ɗina,na damu sosai akan halin da kike ciki,"

  Sosai sehrish ta ƙankameta"Oumma,dan Allah ki tayani da addu'a,Akan Allah ya yaye mun damuwata,"

  "Wata irin damuwace wannan?ko zan iya sani"?shiru tayi tana tunanun amsar da zata bata,

  Jin haka yasa abu ta gane cewa bataso ta faɗa mata ne,

  "Shikenan,Zan tayaki da addu'a,kema kuma ki dage da yin addu'ar,"ta ƙarasa maganar tare da sanya hannu ta raba sehrish daga jikinta,suka dan zauna gefen gadon,

  Zuba mata ido abu tayi tana kallonta,maganar da abusufyan ya sanar da ita take tariyowa acikin kanta na cewa Sehrish tana da aure,taso suyi maganar da ita,Amma ta kasa,ta zuba mata idone har zuwa lokacin da Sehrish ɗin taso ta sani,don ta lura 6oye mata take yi,

  "Kinsan wani abu"?

Girgiza kai sehrish tayi"A'a"

Murmushi abu ta ɗan saki kafin tace"Lokacin da mahaifinku ya nuna yana sona nayi matuƙar yin mamaki sosai,Saboda ni bakowa bace,mata dayawa suna sonshi,Suna rubibinshi kamar suyi hauka,Kuma abunda zai baki mamaki waɗannan matan dake sonshi,Sunfi ni komai,gasu ƴa'ƴanmasu kuɗi ni kuma ƴar maigadi,Amma a haka Ya nace ya like yace dole saini,Ni kuma saboda kafiyata da taurin kai irin nawa,Sai zuciyata ta dinga saƙa mun cewa yana mu'amala da mata don kawai ina ganinshi atare dasu shiyasa na fara zarginshi,ashe bansani ba nayi kuskure,sau dayawa muna samun dama a rayuwarmu sai muyi watsi da ita,kuma sai daga baya muzo muna danasani,Na yanke ma mahaifinku hukunci batare dana tabbatar da abunda nake zargi akanshi ba,wanda silar hakan na jefa rayuwata cikin haɗari........"dakatawa abu tayi tuni hawaye sun soma sauka daga kan fuskarta,Sehrish kuwa tunda Oummansu ta soma maganar nan,ta natsu tana sauraronta,

  "Ba'ason yankewa mutun hukunci cikin sauri,batare da an tabbatar da abunda ake zargi akanshi ba,Akwai buƙatar yin bincike sosai,hanyoyi dayawa da zaka iya jaraba mutun kafin ka yanke mashi hukunci,Wanda ni banyi tunanin yin hakan ba,A wannan lokacin,kawai idona ya rufe saboda kishi,nayi wasa da damar da nake da ita,Sai gashi nazo ina danasani mara amfani....."kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya ciyota,Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,Sai ta dinga jin maganar oummansu tamkar da ita take yinta,wasu siraran hawayene suka soma sauka akan fuskarta,

  "Ita dama sau ɗaya take zuwa ma mutun,da ace a wannan lokacin nayi amfani da damar da nake da ita,da ban jefa rayuwata cikin hatsari ba,da kuma rayuwar ƴa'ƴana,sai gashi ata dalilin hakan Har gidan mahaukata aka kaini,ni nasan bankyauta ma rayuwata ba,Mutanan da su kayi mun halacci na butulce masu,mutumin dayasoni ya qaunace ni,duk da matsayina na ƴar maigadi,hakan baisa ya ƙyamace ni ba,wlh danasani bata da amfani......"

  Cikin shessheƙar kuka Sehrish tace"dan Allah Oumma kidaina tuna abunda ya wuce,banason ina ganin hawayenki,"

  Girgiza kai abu ta ɗanyi kafin tace"indaina tuna abunda ya wuce?baƙya tunanin wannan zai zama darasi ga ƴan baya?waɗanda Allah yaba ma dama irin tawa suke ƙoƙarin yin watsi da ita....."

  Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,gani take kamar oummansu tana yi mata gargaɗine a fakaice,duk da tasan batasan abunda ke wakana ba,Amma tasha jinin jikinta,

  "Don me ake bamu tarihin Annabawa da waɗanda suka zo kafin mu?Ba don muji daɗinshi ba kawai face don muyi koyi da kyawawan dabi'unsu da halayansu,mu kuma ɗauki darussan rayuwa acikinsu,"

  Ajiyar zuciya sehrish ta sauke,tare da sanya tafin hannunta asaman fuskar oummansu tana share mata hawayenta,

  "Hakane oumma,kin faɗi gaskiya,"

Murmushi abu tayi"banaso kuma kuyi irin kuskuren da nayi,shiyasanya nake faɗa maki wannan,"ta ƙarasa maganar tare da wuce wa ta gefen Sehrish ta nufi toilet tana faɗin"Ki tada su hosana da jahad,su tashi suyi sallah,"

  "To oumma,"abu na shiga toilet,hakanan tadinga jin gabanta na faɗuwa,kalaman oummasu sunyi matuƙar ta6a mata zuciyarta,hankalinta ya tashi ba kaɗan ba,kokwanto ta shiga yi Akan Sgr,Gaba ɗaya ta rikita kwakwalwarta,tayi zurfi acikin tunaninta Muryar Jahad ta katse ta"My Own sis!"firgit tayi tare da juyawa tana kallon Jahad,dake ƙoƙarin miƙewa zaune,

  "Lafiya naganki zaune kamar kina acikin damuwa"?

  Da sauri tace"babu komai,Oummace tace na tashe ku daga bacci lokacin sallah yayi,"

  "Ya jikin naki"?

"Jiki Alhamdulillah,"

Murmushi jahad ta ɗan saki tana satar kallonta,

  "Na nemeki banganki ba,"

"Ina ɗakin aunty azmee ne,"

  Jinjina kai jahad ta ɗanyi"dama saida raina ya bani cewa kina acan,naso nazo,amma dare yayi sosai ga bacci daya fi ƙarfina,"

  Kafin sehrish tace wani abun,Oummansu ta fito daga cikin toilet,fuskarta da hannunta duk lemar ruwan alwalan da tayi,


"Xaman me kuke yi ne"?tayi tambayar tana kallonsu,miƙewa sehrish tayi,Jahad kuma ta sanya hannu tare da janye bargon jikin hosana,kafin ta ɗan bubbuga hannunta"Get up hosana,Time ɗin sallah yayi,wai bazaki tashi ba "


Rai a6ace hosana ta buɗe idanuwanta a ƙule take kallon Jahad,kamar ta shaqota,

  "Oummace tace atasheki,"

Zumburo baki tayi batare data ce komai ba,ta tsani atada ta daga bacci,


Batare da 6ata Lokaci ba,kowannasu yayi alwala,suka zumbula hijabai ajikinsu tare da kabbara sallah,


*Boss Bature*


Bayan dawowarsu daga masallaci,abusufyan tare da dr harris suka nufi ɗakinshi,kamar yadda ya nemi yin magana dashi,daga gefen gadon suka zaune suna fuskantar juna,

  "Naji kace kana son magana dani,menene"?

  Murmushi abusufyan ya saki batare dayace komai ba,.  

  Harris yace"Hmmm na ganoka,halan kana son yi mun magana akan zainabu abu ne?Ae gwaggo ta faɗamun cewa zaka mayar da matarka,nace ashe da rabon gaurancin abusufyan ya ƙare......"cike da zolaya yayi maganar,

  Dariya abusufyan yayi"hmmm,ae gwaggo ta sanar dani cewa,kaima zaka angwance da saudatu,wlh naji daɗi sosai yarinyar akwai hankali,"

   "Ni fa da farko nayi tunanin gwaggo zata hanani auranta,kasan basu jituwa ita da saudat,yadda kasan Tom and jerry haka suke acikin gida"harris ne yayi maganar yana dariya,

Abusufyan yace"Allah sarki gwaggo,inata so in tambayeka game da rashin lafiyarta,Ana samun cigaba ko kuwa har yanzu sai a hankali,Duk da naga lafiyalou muke magana da ita....  "

Tunkafin yakai ƙarshen maganarshi Harris yace"Gwaggo fa ta samu lafiya,.

  Cike da mamaki abusufyan yace"Kai haba"?

  "Wlh kuwa,Lafiyarta qalou,garass take kallon kowa,Babu wani ta6in hankali atare da ita,Ae gwaggonku Allah ya bata Lafiya,ita da kanta take faɗamun cewa taji sauƙi,tana cikin hankalinta,"

  Wani irin farin cikine Ya lullu6e Abusufyan,har baisan lokacin daya mike cike da zumuɗi ba,yana kokarin kama hanyar barin dakin don yaje ɗakin gwaggonsu,

  Ruko jallabiyar jikinshi Harris yayi"ina zuwa?ba kace zamuyi magana ba"?

  "Ba zaka gane ba,inaso naganta ne,ka taso mu tafi acan sai muyi maganar atare,"


Fuskar harris ɗauke da murmushi ya mike suka fita ɗakin a tare,


A ƙopar ɗakin gwaggon katsina suka tsaya,abusufyan ne ya kwankwasa ƙopar dakin,kusan sau uku yana kwankwasawa, kafin suka ji tace"Wanene"

  Har suna haɗa baki wurin cewa"Mune,"


Buɗe ƙopar ɗakin gwaggon katsina tayi,jikinta na sanye da riga da zane na jar atampa,ta kifa ɗaurin ɗan kwali akanta,koda tayi arba da abusufyan sai tasaki murmushi,


   Cike da tsantsar farin ciki Abusufyan yace"Gwaggo wai dagaske kin samu lafiya"?


Kallon Harris tayi"bana ce kada ka sanar dakowa ba"?jin haka yasa abusufyan ya rungumeta yana dariya,

  "Alhamdullillah Ya Allah,I can't hide my happiness gwaggo,"

  Shafa bayanshi tayi"Abusufyan ɗina,kaga yadda Allah ke ikonsa ko?Rana ɗaya kawai na farka batare da haukan nan da nake fama dashi ba,Allah ya yaye mun,"idanuwanta cike tab da kwalla tayi maganar,janye jikinshi yayi daga nata,

  Ruƙo hannunta yayi suka shiga daga cikin ɗakin,harris yabi bayansu sai faman sakin murmushi yake yi,saman kujera Harris ya zauna,Abusufyan da gwaggo suka zauna gefen gadon,har lokacin hannunshi na rike dana gwaggo,salati suka fara yiwa Annabi muhammad(S.A.W),kafin daga bisani,Gwaggo tace"Allah yasa inji wani cikinku ya faɗi ma wani cewa naji sauki,Yasin saiyaji ajikinshi,"


Fashewa sukayi da dariya gaba ɗayansu,harris yace"Saboda me bakiso asani mommyna?wannan fa abun farin cikine,"

  Girgiza kai tayi"A'a,banaso na canza daga yadda nake,inajin daɗin barkwancin da nake yi,Ina sanya mutane nishaɗi,Nima kuma ina samun nishaɗi,koda ace zasu sani ba yanzu ba,Ku bari sai bayan an ɗaura auran kowannanku,"

  Abusufyan yace"Duk yadda kikeso haka za'ayi gwaggonmu,babu wanda zaiji wannan maganar,amma fa zan sanarwa abu,don kuwa tana son yin magana dake sosai,"

  Ƙayataccen murmushi gwaggwon katsina ta saki"Shikenan,ka sanar da ita,Don nima inason magana da abu sosai amma bayan ita,banaso kowa ya sani,"

  Bayan sun ɗanyi shiru na wani lokaci,kowa fuskarshi ɗauke da tsantsar farin ciki,


"Gwaggo,dama akwai maganar da nakeson nayi dake,dana yanke shawarar inyi maganar da harris,amma tunda naga kinji sauki zaifi kyau muyi maganar nan atare,"a tsanake yayi maganar,.  .

   Mayar da hankali tayi akanshi"Ina sauraronka,

   "Dama game da gidan nan ne dake a kano nasarawa g.r.a,nayi laifi ban sanar dake ba,tunda na amshi key din a wurin harris,lokacin da muka je kano,neman abu,mun zauna a gidan,Da zamu dawo kuma sai na mallaka ma Malam nura shi,da niyar idan nadawo muka haɗu zamuyi magana inyaso ko siyarmun da gidanne sai ayi,tunda ba mallakina bane,Gadon Harris ne......."

  Tunkan ya kai ƙarshen maganar dr harris yace"Da ace nasan wannan maganar zakayi wlh da ban 6ata Lokacina wurin sauraronta ba,Haba abusufyan menene aciki don kayi kyauta da gidanmu,Mutanan daka ba wannan gidan sunyi mana halaccin da bazamu ta6a mantawa ba,sun taimaki rayuwar ƴa'ƴanmu,kuma sune silar da aka agano inda Zainab take,Ni inaga kamar kanason nuna banbancine atsakanina dakai........"ranshi a6ace yake maganar,


Murmushi kawai abusufyan yayi yayin da yake kallonshi,Ya harzuka sosai,dama saida ranshi ya bashi cewar hakan zata biyo baya,

   "Allah ya huci zuciyarka,ɗan uwana nakaina,Nima badon naso nayi maganar ba,Sai don in sauke nauyin dake akaina,don nasan cewa gidan ba gadona bane,Naka ne,kuma nayi kyauta dashi,batare dana nemi iznin ɗaya daga cikinku ba"

   "Abusufyan kenan,Ni dariya ma ka bani,musamman daka ce inyaso ko kuɗine ayi mashi ka biya,Nace sannu ko"?gwaggoce tayi maganar tana hararanshi,

  Sunnar dakai ƙasa yayi yana dariya,cike da jin kunyarta,

  Ta6e baki ta ɗanyi kafin tace"Akwai takardun gonakina dake a wurin dankama,guda uku,Na Mallaka masu ita,idan mun koma za'a ɗauki takardun nan a damƙa masu a hannu"


Tunda ta soma magana,Abusfyan ke kallonta,Tsabar farin ciki bakinshi yaƙi rufuwa don murna,


Tana kai ƙarshen maganarta,Dr harris yace"Nima kuma,Na ɗauki nauyin karatun ɗansu sadeeq,tun daga secondry har ya kammala Jami'a,a duk inda yakeso koda ba'a nan kasar ba,sannan mahaifiyar yaron,zan bata miliyan biyar,taja jari dasu,"


Daɗi kamar zai kashe abusufyan,baisan lokacin daya rungume gwaggo ba"nagode sosai da irin ƙaunar da kuke nuna mun da kuma jinina,Allah yabar zumunci atsakaninmu daga nan har gidan Aljanna....."sosai abusufyan ya shiga yi masu godiya,duk da sun hanashi,sun jima a ɗakin gwaggon katsina suna fira,har sai da gwaggo ta shigo ta sanar dasu cewa an shirya masu breakfast tukunna,Suka baro ɗakin a tare da gwaggo


*Hafsat*


Tunkafin ta fito daga cikin toilet tajiyo muryoyinsu Khadija da Nafisat suna fira,la6ewa abakin ƙopar toilet ɗin tayi tana sauraronsu,

  "Nifa abunda yafi bani mamaki,Dana ji Ammi tace,Itace wadda Hamma  rafayet zai aura,abun ya girgizani,Nace ashe yana kula mata"?khadija ce tayi maganar,

  Nafisat tace"Ae bake kaɗaiba,nikaina abun ya bani mamaki,Mutumin nan fa lokacin dayazo damaturu,duk kyawun ƴan matan family ɗinmu,ko kallo wannan basu ishe shi ba,balle aje ga magana,Gaskiya yarinyar nan Allah ya bata,Ƴar baiwace ita,jinin nasarace,Wlh da ace nice ita,Yadda yake da farin jinin nan,Sau da ƙafa zanbi shi,ko musu bazan yi mashi ba,"

  Hafsat dake yi masu la6e,sae faman tiƙar dariya take yi,

  "kinga kullum sainaje gaishe shi,ko Allah zaisa mu haɗa ido dashi in samu shiga,Amma ɗan ta halikin nan gaisuwarma daƙyar yake amsa mun,"acewar khadija,cike da takaici tayi maganar,

  Nafisat tace"Yo ba dole yayi rowar muryarshi ba,in yana magana yadda kikasan ana busa sarewa don daɗinta...  "


Surutunne ya ishi hafsat,Hannu tasa ta buɗe kopar ta fito,Suna ganinta da sauri suka rufe bakunansu,Gaba ɗaya suna xaune saman gadon,sun lankwashe kafafuwasu,Zaman cin tuwo sukayi,

Girgiza kai hafsat tayi"Allah ya shiryeku,Shiyasa dayawa mata suke rasa mijin aure,Saboda Ruwan ido,Yanzu duk kyawun Hamma adam da Osman baiyi maku ba,saboda haɗama ko"?

  Ƙumshe dariya sukayi,batare da Sun tanka mata ba,

    Jin ringing ɗin wayarta ne yasa tayi sauri juyawa ta nufi mirror hannu tasa ta ɗauki wayar,My daddy,Shine sunan daya bayyana akan screen ɗin wayar,picking call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta,

   "Assalamu alaikum,Daddy,"

On the other hand Ishaq yace"Wa'alaiki salam daughter,Ya kike Ya hutu"?

  "Lafiya lau Alhamdullilah,"tayi maganar,a yayin da take zama saman kujerar dake gaban madubin,

   "Shiru baki dawo ba,ko kin manta da aikin ki ne"?

  "A'a daddy Gobe insha Allah xan dawo,naji daɗin zaman gidanne cikin ƴan uwana,"

  "Kada ki damu,yanzu dai goben ki dawo gida,tunda nan bada jimawa ba,zamuzo bikinsu Omar tare,Hada ma Auntynki "

  Murmushi hafsat ta saki"Shikenan zan dawo goben"

  "In kuma kina da wanda kikeso,ki fadamun kinga sai a haɗa auranki danasu Jahad,ayi a wuce wurin,"

    Aɗan shagwa6e tace"Ae bani da saurayi yanzu,nadaina kula kowa "_

Ishaq yace"Zanyiwa daddy magana,Ya sama maki Miji,sai a haɗa auranku,"

   Bubbuga ƙafafunta tayi kamar tana agabanshi"ni banason auran haɗi Allah,nafison in auri wanda ke sona nima nakeson shi,"

  "Allah ya baki Miji na gari daughter,I will keep praying for u,"

  "Ameen daddyna nakaina,"

  Shiru suka ɗanyi na wani lokaci,Kafin yace"Ya jikin Mommyn naki"?

  "Da sauƙi,Ae jiya munyi waya da ita,ta kirani da layin ɗaya daga cikin likitocin dake kula da ita,tama faɗamun cikin satin nan za'a sallameta,"

  "Jiki yayi kyau kenan,To Allah ya ƙara mata Lafiya,".  

  "Ameen daddy,mungode ssai,Allah ya saka da alheri,"

  Sun jima suna waya,kafin su kayi sallama,Ta kira Layin Hayaam......'

  Tana fara ringing Hayaam ta ɗaga kiran,bayan sun gaisa Hafsat tace"Aunty hayaam,tunda safe nake ta kiran Layinki tana ta ringing baki ɗaga ba,"


"Na sanya wayar silent ne,dayake naje makaranta ne,"

  "Dama inaso na sanar dake cewa,Mommy na nan zata dawo gida,An kusa sallamarta,"

  Muryar hayaam da alamun farin ciki tattare da ita tace"Alhamdulullah,Amma naji daɗi sosai,nayi farin ciki,Ya mutanan gidan?

  "Suna nan cikin ƙoshin Lafiya,Ae zakuzo bikinsu yaya Omar ko,"_

  Shiru hayaam ta ɗanyi kafin tace"Anya!"

  "Dan Allah aunty hayaam kuzo,Gagarumin biki za'ayi,Kuma hada fa Amal ma,Kodan ita yakamata kuzo,tunda ƴar uwarku ce,"

  "Allah ya bamu ikon zuwan,"

  "Ameen,in sha Allah ma zakuzo,"


Sun jima suna waya kafin daga bisani,Sukayi sallama,

  

*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe shida na marece,Ya mu'allim yazo gidan domin duba jikin junaid,tun bayan da yayi parking ɗin motarshi,adai dai lokacin Kanal Yusif da Abba suke ƙoƙarin fitowa daga entry din falon,Suka yi arba dashi,Yana sanye cikin shigar nan tashi ta Larabawa,sai ƙamshi ke tashi daga jikinshi,fuskar kowannansu ɗauke da murmushi,

  Mika mashi hannu abba yayi suka gaisa tare da rungume juna,"Nayi farin ciki sosai da zuwanka,Dama junaid ya addabe ni da tambayarka,Har cewa yake yi shi dai ayi mashi kwatancen gidanka Yaje ku gaisa"yayi maganarne bayan sun raba jikinsu,

  "Allah sarki,junaid Ya jikin nashi,wlh nima nayi kewarshi sosai,Shiyasa na gaza hakura,"Ya kai ƙarshen maganar,tare da miƙawa Kanal yusif hannu suka gaisa"sannu zuwa,ya gida ya aiki,"

  "Alhamdulillah,Yusif Ya mai jiki"!yayi tambayar yana kallonshi,

  Yusif yace"mai jiki da sauƙi,Yana nan yanzu ba inda bai zuwa da ƙafafunshi,don da ace yana da mota da ba abunda xai hana ka ganshi ƙopar gidanka,"

  Dariya suka saki gaba ɗayansu,Abba yace"bismillah mu shiga daga ciki,"


Atare suka nufi falon Ya mu'allim na a tsakiyarsu,lokacin da suka ƙarasa cikin babban falon,mutun uku suka samu zaune suna fira,Major general osman tare da Adam da Najeeb,miƙewa sukayi ganin abbansu,Gaishe dashi suka yi kafin suka miƙa ma Ya mu'allim hannu ɗaya baya ɗaya ya gaisa dasu,daga bisani kowannasu Ya zauna suka ci gaba da firarsu


Hannu abba yasa cikin aljihun wandon jikinshi ya lulubo wayarshi,Mommy ta dannawa kira,tana fara ringin mommy ta ɗaga kiran,

   "Kina ina ne"?

 "Na shiga wurin azeema ne,"

  "Okey,Ya mu'allim ne yazo,muna buƙatar abunsha,"

  Amsa mashi tayi da toh"Gani nan zuwa,"daga haka yayi rejecting kiran,tare da mayar da hankalinshi kan Ya mu'allim

   "Yakamata ka gayyace mu zuwa gidanka,tunda mun zama ɗaya,ko ba haka ba"?yayi tambayar yana kallon su Yusif,

  "Hakane daddy,abunda na lura dashi,baya son sakewa acikin gidan nan,kuma kullum zaizo shikaɗai yake zuwa,banda ya'yanshi,"acewar yusif,

  Murmushi ya mu'allim ya ɗanyi kafin yace"Bani da ya'ya,"

  Abba yace"Karfa kace mun baka da aure"?

  Dariya yayi batare daya ce komai ba,Osman yace"Haba ya za ace baida aure,Yadda yake malamin nan kyau ace yana da mata huɗu cuf,Ya cike sunnah kenan,"

  Sunnar dakai ƙasa ya mu'allim yayi yayin da yake wasa da key ɗin motarshi,

  Abba yace"Kayi shiru bakace komai ba?

  Najeeb yace"duk kunsa yaji kunya,kunsan fa bakowa keso ayi mashi maganar iyali ba,musamman idan ya kasance baidasu,"

  Jin wannan maganar yasa Ya mu'allim ya ɗan ɗago tare da kallon Captain najeeb da yayi maganar,domin kuwa ya canko dai dai,

   "Ae ni tun rana ta farko dana fara ganinshi,raina ya bani cewa,duk irinmu ne,"adam ne yayi maganar,fuskarshi dauke da murmushi,


 Abba yace"wai dagaske ne?kaima irinsu ne"?

  Daƙyar Ya mu'allim ya iya amsa mashi"hakane abba,"

  Tafa hannu abba ya shiga yi yana Faɗin"Subhanallahi!An shiga uku!haba Ya mu'alim,Ni duk a tunani na ka cike sunnah,ashe ko ɗaya baka ajiye ba,"


  Murmushi kawai Ya mu'allim keyi batare daya ce uffan ba,Saboda kunyar abba da yake yi,

  "To dai ga junaid ɗinka nan,In sha Allahu cikin sati mai zuwa zai angwance,"

  Cike da mamaki Ya mu'allim yace"junaid zaiyi aure"?

  Jinjina kai abba yayi"ƙwarai kuwa,Ae bashi kaɗai ba,Suna dayawa,kusan dukansu zan aurar a lokaci ɗaya,Ina fata kaima kafin lokacin zaka fiddo da mata inyi maka aure,"

  Murmushi kawai ya mu'allim yayi,


Fitowa mommy tayi daga cikin kitchen hannunta ɗauke da tray,wanda ta shirya masu abunsha mai sanyi acikin glass cup,hada snacks ta haɗo masu,


Adai dai Lokacin hafsat ta nufe wurinta,jikinta na sanye da arab gown white colour ta yafa mayafi akanta,

  "Mommy,"da sauri takai idanuwanta kan hafsat data ambaci sunanta,

   Fuskarta asake tace"Hafsat,ina zuwa haka"?

  "Ba ko'ina,nagaji da zama cikin ɗakine,Shine nace bari na fito in ɗan zagaye gidan,"

   Kafin mommy ta kuma cewa wani abu,hafsat ta nuna tray ɗin hannunta"Wannan fa"?

  "Abbane yazo da baƙo,wannan malamin dake duba junaid,shine ya buƙaci in shirya masu drinks,"

  "Bari nakai masu,"

 Ba ƙarami daɗi mommy taji ba,Miƙa mata tray ɗin tayi,ta sanya hannu biyu ta kar6a,kafin ta wuce cikin palourn,Mommy kuma ta juya zuwa ɗakinta,


"Assalamu Alaikum"cikin sanyin murya tayi masu sallamar,gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta,cikin girmamawa ta shiga gaishe dasu,fuska asake suke amsa mata,

  Abba ta fara mika mawa ya ɗauki kofin ɗaya,

  "Ga ya mu'allim nan ki miƙa masa,"juyawa tayi wurin Ya mu'allim ta miƙa mashi cup ɗin,a hankali ya sanya hannunshi ya ɗauki cup ɗin,har zata juya taji yace"kina mace kike shafa turare har haka"?ƙasa ƙasa yayi maganar

  Gabanta ne ya faɗi rass,dama sai da ranta ya bata cewar zaiyi wuya in bai tanka mata ba,saboda tasan halin malaman nan,kuskure kaɗan sai sunyiwa mutun wa'azi akanshi,'ƙasa ƙasa da murya tace"Za'a gyara,'bata jira amsar da zai bata ba,tayi saurin yin gaba wurin Su osman ta miƙa masu,


Murmushi abba ya ɗan saki bayan ya kur6i lemun yace"Nasan bakasanta ba,Jikata ce,sunanta hafsat,"

  Murmushi Ya mu'allim ya ɗan saki kafin yace"Masha Allah,"

  Abba da ɗumi sai cewa yayi"itama bata da aure kamar kai,sai dai bansani ba,ko tana da saurayi,"

 A sukwane hafsat ta juyo tana kallon Abba,hankalinshi kwance yake magana,

     Ƙumshe dariya kanal yusif yayi ganin yadda hafsat ta gumtse fuska,taji ana ƙoƙarin yin tallatarta,da sauri ta juya tabar wurin,sai da tayi nisa,takaici ya isheta,juyowa ta kuma yi don ta kalli Ya mu'allim,karaf suka haɗa ido dashi,watsa mashi harara tayi,duk don saboda yayi complain akan turarenta,abun ya bashi mamaki,hakan da tayi kuma ba ƙaramin burgeshi tayi ba,har yayi tunanin yin magana da abba akanta,idan sun ke6e,


Bayan ya kammala shan lemun,Abba yayi mashi jagora zuwa bedroom ɗin junaid,Lokacin da suka shiga zaune suka same shi,tare da Talal suna kallo acikin laptop ɗinshi,


Cike da zolaya ya mu'allim yace"kaida zan sameka kana karatun qur'ani,sai in sameka kana kallon drama?haka mu kayi dakai"?


Saukowa junaid yayi daga saman gadon ya ƙarasa da sauri ya rungumeshi,ba ƙaramin daɗi Ya mu'allim yaji ba,ganin yadda junaid ya samu lafiya sosai,har ƙiba yayi sa6anin da,

Shafa sumar kanshi yayi"Masha Allah,jiki yayi kyau junaid,Naji daɗi sosai,Allah ya Albarkanci rayuwarka,"Abban ya amsa mashi da Ameen

  Ɗagowa junaid yayi fuskarshi ɗauke da murmushi yace"I really missed u,meyasa bakazo ba,2 days banganka ba,"ya ɗanyi maganar shagwa6e

  Waro ido abbansu yayi ganin junaid na shagwa6a,

  "La haula masalli ila!Junaid me nake gani haka?Dama har yanzu akwai sauran shagwa6ar"?

  Dariya ya mu'allim yayi"A jininshi take,shiya sanya har yanzu bata rabu dashi ba,kuma hada ƙarin autane shi,dole yayi shagwa6a,"

  Abba yace"amma yaci ace ya daina,Nan fa da wani lokaci zai zama ango,"jin wannan maganar yasa junaid,Jin kunya da sauri ya koma saman gadonsu,Ya janyo pillow ya kifa kanshi asama yana dariya,Talal ma dake a gefenshi dariyar yake yi,


 "Yana da kunya sosai,"acewar Ya mu'allim,

 Abba yace"hmmmmm abar kaza cikin gashinta dai,kar atona,"


Dariya sosai su kayi,Sun jima a wurin Junaid sai da aka fara kiran Sallar magrib tukunna,suka fuce atare,


*Sehrish*


A hankali ta turo ƙopar toilet ɗin,jikinta sanye cikin bathrobe fara ƙyal,ta ɗaure igiyar rigar,wani irin ƙamshine ke fita daga jikinta,kamar wadda tayi wanka da ruwan turare,lallausar suman kanta tayi mata rumfa a bayanta,mai yawan gaske,jiƙe take lemar ruwa,tun bayan sallar Azhar,ta dawo ɗakin Azmee,gudun kada hajiya azeema taga tabaro shi,


Gaban mirror ta zauna,zugudum bakomai keyi mata yawo aranta ba,face maganganun da oummansu ta faɗa mata,sun tsaya mata aranta,

  A hankali ta furta"Ya rafayet sona  yake yi,ko jikina yake so?taya za'ae na gane haka?,tana tsoran tayi irin kuskuren da Oummansu tayi,Nayin watsi da damarta,


Hand dryer ta fara ɗaukowa,ta jona ajikin socket,busar da gashin kanta tayi,bayan ta kammala ta kashe ta,jikinta ta soma gyarawa,ko'ina ta shafe shi da mai,


Turo ƙopar ɗakin Hajiya azeema tayi da sallama abakinta ta shigo,Sehrish ta amsa mata,fuskarta adan sake ta amsa mata,

  'Ina yini aunty azeema,"

"Lafiya Lou daughter,Ya jikin naki"?

  "Alhamdulillah,ina samun sauƙi sosai,"

   "Naga gashin kanki,Yayi tsayi sosai,ga yawa,yakamata ku shirya in kaiku wurin Saloon dake da ƴan uwanki,amma fa idan kinji sauki,"_

  "Ae nama ji sauƙi,warwarewa kawai zan ƙarasa yi,"

  Hararar wasa Azeema tayi mata"A haka din,kina ɗan gyasa ƙafa shine kinji sauki?

  Dariya sehrish ta ɗanyi"bari nayi maki make up,"acewar hajiya azeema,

  Ba don taso ba,Saboda yanzu bata buƙatar yin kwalliya,tunda wanda take yi dominshi,Rabuwa zasuyi,

   Within mins hajiya azeema tayi mata make up,fuskar ta fito sosai,jan bakin data shafa mata red ne mai ƙyalli ajikinshi,daga sama ta shafa mata lip gloss,fuskar ta lindu da foundation mai kyan gaske,ga eye brows ɗinta natural amma ta ƙara mata da brown eye pencil,

  "Masha Allah my daughter,Allah yayi maki kyau,ki godewa Allah,Son kowa ƙin wanda Ya rasa,"

  Murmushi sehrish ta ɗan saki,

"Bari na ɗauko maki,kayan da zaki sanya,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta nufi wardrobe ɗin kayanta,

  Can ta hango wata Atampa,Golden glitter,Brown Colour,Riga da skirt ne,ɗinkin ya haɗu over,

  Juyawa tayi tare da kallon Sehrish"Har na hangoki acikin wannan,"

  "Sunyi kyau sosai,Amma dare yayi,koda na sanyasu,zan cirene in na tashi kwanciya,"

  "Duk da haka,ki sanyasu,in yaso daga baya kin cire,"

  Gyaɗa kai tayi"shikenan,"ta ambaci hakan tare da mikewa,taje ta kar6i atampar daga hannunta,

"Bari naje,na kawo maki dinner dinki,"tayi maganar tare da nufar hanyar fita daga dakin,Harta ruƙe handle ɗin kopar ta juyo ta kalli sehrish"Munyi magana da Amrish,tace tana so taje gidansu ta kwaso kayanta,bansani ba kota fada maki"

  "Bata faɗamun ba,"

"Okey,in Allah yakaimu,Zuwa gobe zanyiwa wani magana cikin  matasan gidan nan,yakaita gidan ta dauko kayanta,"

  "Allah yakaimu Lafiya,"

  "Ameen"ta amsa mata tare da juya ta fuce daga ɗakin,


Shaf shaf ta shiga zura kayan ajikinta,sun zauna mata sosai sunbi dirin jikinta,bata ɗaura ɗankwalin ba,don bata iyaba,zama tayi gaban mirror ɗin tana jiran dawowar,Hajiya azeema don ta ɗaura mata shi,


After some minutes hajiya azeema,ta shigo hannunta dauke da tray mai fadi,Asamanshi food stuff ne,Saman table ta sauke tray ɗin,kafin ta nufo Sehrish,

  "Banta6a ganin budurwar da atampa keyi mata kyau ba irinki,yadda kasan donke companyn suka ƙerata,"fashewa sehrish tayi da dariya,don ba ƙaramin nishaɗi ta sanyata ba,


Bayan ta kammala ɗaura mata ɗan kwalin,style me kyau,tace"Aikina ya qare,ga abincinki can kije ki zauna ki ci,"

  "Nagode sosai,"tana kai karshen maganarta,ta fuce daga dakin,


Murmushi sehrish ta ɗan saki tana kallon kanta ta cikin madubin,miƙewa tayi daga gaban madubin ta dawo gefen gadon ta zauna,sae ƙamshi ke tashi ajikinta,


Tsaf Ya kammala Shiryawa cikin shadda Ash colour,wa'iyazubillah,kyau iya kyau,a tsaye yake gaban mirror yana gyara agogon diamond ɗin hannunshi,


Omar dake zaune gefen gadonshi sai faman sakin murmushi yake yi,yayin da yake kallonshi,

  "Kasan Allah duk macen data mallake ka ba ƙaramar me sa'a bace,cos you're expensive,komai naka Extraordinary ne,wlh mace koda Ilminta koda kyanta koda arzikinta sai da rabonta,"Sai faman zuzutashi Omar yake yi,Shidai baice mashi uffan ba,a hankali yakai hannu tare da ɗaukar turaren nan nashi,Yabi ko'ina na jikinshi ya feshe,

  "just ka bayyana mata irin son da kake yi mata,ka ƙaddara cewa yau zaka fara dating......"

  Slowly ya juya gefe tare da kallon Omar"how can i do that"?

  "Ni zan koya maka,"

Girgiza kai yayi,Omar  kasan ban iya soyayya ba,'

  Matsalarka kenan,tunda baka iyaba ka bari in koya mata,natsuwa sgr yayi yana sauraronshi

  "Kece sanyin idaniyata,bana iya runtsawa in bakya a kusa dani....."

  Kwata kwata Sgr baya fahimtar abunda Omar ke koya mashi,

  "Na lura baka fahimtata,Zamuyi amfani da bluetooth,zaka manna shi a kunnanka,Idan kaje wurinta,zan dinga karanto maka,kai kuma kana faɗa mata,haka yayi"?

  Ɗaga mashi kai yayi"yeah,i can try it,

 

[3/19, 2:58 PM] +234 810 388 4440: _💋The father Of Soldiers💋_



          *🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



Story 

       &  

       Written 

                   by 

      *_Boss Bature_*


          




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




Dedicated to my beloved sisters. 😍   




Proud Of My First Novel💋


_Warning banyarda wani yayi amfani da wani sashe na littafina ba, kada a ta6amin komai na littafina,Sannan kar a kuskura a haɗamun document,Ga mai buƙatar karanta Littafin Abban Sojoji from Book one to 3 yayi mun magana ta whatsapp 08103884440_




Canza ra'ayi yayi"Omar,bana buƙatar using the bluetooth Just komai ya dace ka sanar da ni,"

Murmushi Omar ya ɗan saki don yasan cewa Sgr zai iya,A nan ya shiga kwatanta mashi yadda zai bayyanar da Soyayyarshi,bayan Ya Kammala Sgr yace"thanks,sai nadawo,"yakai ƙarshen maganar tare da juyawa ya nufi hanyar fita ɗakin,Yana jiyo muryar Omar Yana faɗin"Wish u all the best,"


A lokacin Sehrish tana zaune ta tasa abincin da Aunty Azeema ta haɗa mata sai ci take yi,bayan ta kammala ta yagi tissue tana goge bakinta,A dai dai wannan Lokacin taji an turo ƙopar ɗakin,dakatawa tayi tana jiran ganin mai shigowar,Natsuwa tayi tana shaƙar daddaɗan kamshin turaren dake kai ma hancinta ziyara,tunkafin ma Ya shigo ƙamshin jikinshi ya gauraye ɗakin saƙo da lugu,


A hankali ya sako ƙafarshi kafin ya ƙarasa shigowa ciki,Har sai da gabanta ya faɗi rass,Saboda razana da tayi da kyawun da Sgr yayi,Kayan hausawa ba ƙaramin kyau suke yi mashi ba,yadda kasan danshi kamfanin shadda suke ƙerata,cikakkiyar surar jikin nan nashi ta ƙara fito da kyan shaddar,

Tunda ya ɗaura idanuwanshi akanta,gaba ɗaya wankanta ya tafi da imaninshi,natsuwa yayi yana kallonta,from head to toe,Atampar jikinta ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,Ya kasa kawar da idanuwanshi kamar yadda itama take Kallonshi,


Sallama yayi mata cikin sanyin Murya ta amsa mashi,kafin ya ƙarasa shiga ciki,gefen gadon ya zauna dab da ita,tuni kasala ta fara baibaye kowannansu,


Almost 15 mins,tsit kake ji ba wanda yace uffan acikinsu,Ajiyar Zuciya ya ɗan sauke kafin Ya soma magana, 

  "Ya jikinki?"A hankali tace"da sauki" jinjina kai yayi yana cigaba da kallonta,hakan yasa ta Sunkuyar da kanta tana kallon hannuwanta,


"Reesh,nasan nayi maki laifi wanda yasa kika juyamun baya,But Why can't u forgive me?komai ya wuce mana,Idan har bana ƙaunarki serious bazan kulaki ba,kuma abunda ya faru,duk don saboda ƙaunar da nake yi maki ne,Naji fargabar su rabani dake,I thought yi maki hakan da nayi will be the solution,sai dai nayi mistake na kusantarki a lokacin da nake cikin fushi,wanda duk Iyayenmu ne suka jawo hakan,"ya ɗan dakata da yin maganar Yana mayar da numfashi,jin yayi shiru yasa ta dago,yayin da idanuwansu ke kallon cikin na Juna,

  "Ina neman alfarma a wurinki,For the Last time,ki bani dama,zan gyara kuskure na,Zan canza maki kamar yarda kikeso,"

  Jikinta ya ɗanyi sanyi da jin kalamansa,Amma still tana kokwanto akanshi,gani take kamar Sgr bazai ta6a sonta don Allah ba,sai don ya mayar da ita abun biyan buƙatarshi kamar yadda ya saba yi mata,Zurfin tunani ta shiga,ba zato ba tsammani,taji ya ruko hannuwanta Acikin nashi,sosai ya ruƙe hannun yana shafa lallausar fatar hannun,a hankali ya fara matsawa yana niyyar rumgumeta....

  "Reesh,I've Fallen for you......   "Tunkan yakai ƙarshen Maganar,Rai a matuƙar 6ace Sehrish Ta ƙwace hannunta daga nashi tare da yin wurgi da hannunsa ta dan ja baya,Abunda bai ta6a tsammani ba,Waro idanuwanshi yayi waje yana kallonta,

  A fusace take magana"Wlh ba sona kake yi ba don Allah,Ni nasani don kawai biyan buƙatarka yasa kake so naci gaba da kasancewa dakai,idan har dagaske kana sona,Meyasa tuntuni baka sanar dasu cewa kana sona ka maida ni matarka ba,kuma tun farko kayi accepting aurena don kawai naci gaba da yi maka Aiki,Saboda kafi ƙarfin kayi soyayya dani,bankai matsayin da zan zama Matarka.....     "Kasa ƙarasa Maganar tayi sakamakon gigitacciyar tsawar da Sgr ya daka mata,A firgice ta zazzare idanuwanta tana kallonshi,tuni idanuwanshi sun Canza launi sosai,Ranshi yayi Mugun 6aci,Zuciyarshi ta hasala,har ya ɗaga yatsu biyar cuf zai wanka mata mari,Ta fashe da matsanancin kuka,Ta dinga ja da baya har ta ƙurewa kan gadon,ta runtse idanuwanta sosai,'


Yarfar da hannun gefe yayi,wani irin raɗaɗi yake ji acikin zuciyarshi,tuni idanuwanshi sun cicciko tab da ƙwalla,takaicin Duniya ya ishe shi,ƙaramar yarinya kamar wannan ce take gaya mashi Magana,gudun kada ya karya ƙasusuwan jikinta ne Yasa yayi saurin miƙewa da saurin gaske har yana tuntu6e ya fuce daga ɗakin,A makance yake tafiya Allah yaso babu kowa a babban falon,A zafafe ya nufi twin stairs ɗin Ya haye,yana taka staircases ɗin wasu Zafafan hawaye suka wanke mashi fuskarshi masu ɗumin gaske,har wani zazza6i yake ji ajikinshi,Sehrish ta hasala shi sosai,


Yana shiga Bedroom Yasa hannu Ya tu6e rigar jikinshi yayi wurgi da ita ƙasa,A haukace Yakai hannu Ya damƙi bedsheet din gadon Ya yayeshi tare da Jefar dashi gefe guda,Dunƙule hannunshi Yayi da ƙarfin gaske Ya naushi Dressing Mirror ɗinshi,gaba ɗaya madubin ya farfashe ya zube,hatta hannunshi sai da glass din ya faffasashi,jini ya shiga tsastsafowa,raɗaɗin da yake ji a hannunshi bai kai raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi ba,lokacin da Sehrish ke faɗa mashi wannan maganganun,Biji biji ya fara gani acikin idanuwanshi,Jiri ya soma ɗaukarshi,tangal tangal yayi zai faɗi,kaitsaye ya faɗa saman gadonshi,numfashin shi na fita da wani irin huci,ga wani matsanancin ciwon kai daya farmasa,



Wuraren ƙarfe 12 na dare,Omar ya faɗo part ɗinsa,fuskarshi ɗauke da Murmushi,Yazo cike da sa ran sunyi nasara,Tun a palour Yake ƙwala mashi kira"Bro!bro!"shiru ba Amsa,har yayi tunanin ko bai kaiga dawowa bane,Acikin ransa har yana cewa"Yanzu haka yana can manne da ita suna shan Soyayya,"ya ƙarasa zancen zucin yana kokarin juyawa kwatsam Idanuwanshui suka sauka akan Agogon Diamond ɗin Sgr,dake yashe a ƙasan tiles,

  Har sai da gabanshi ya faɗi,don yasan cewa ba ƙaramin abu bane zaisa Sgr ya yarda watch dinsa ba,zuƙunnawa Omar yayi tare dakai hannu ya ɗauki wrist watch ɗin,A fili Ya ambaci Sunanshi Rafayet,Da gudun gaske Omar Ya faɗa bedroom ɗinshi,A kwance ya samu Sgr tamkar baya numfashi,hankalinshi yayi Mugun tashi,A sukwane ya haye saman gadon saitin fuskar Sgr,hannu yasa yana shafa fuskarshi"Rafayet meya faru dakai?Meyasa kayi hakan?duk ka hargitsa ɗakin ka fasa glass,"ɗago da kanshi yayi tare da ɗaurashi saman laps ɗinshi,Omar sarkin tausayi tuni idanuwanshi sun cicciko tab da ƙwalla,

  Muryarshi na kerma yace"Dan Allah Rafayet ka fadamun meya faru da kaine?nashiga damuwa sosai pls....."tuni hawayen fuskarshi sun soma sauka saman fuskar Sgr,


Sai lokacin Sgr Ya yunƙura tare da miƙewa daga zaune,yana faman fitar da huci,

  "Omar,Reesh batasona,She hates me completely,i can see dat in her eyes,danasan zata ci mutuncina haka da banje ba,nafi ƙarfin wulaƙancin mace,Saboda Allah ya jarabce ni da son ta shiyasa har take ƙoƙarin gaya mun magana".....Ya ɗan dakata da yin maganar,Omar ya kasa kunne yana sauraronshi,.

  "tana tunanin cewa Jikinta nakeso!Me take dashi?Mata nawa ne suka sha kawomin kansu wanda suka fita komai don kawai nayi lalata dasu,Amma banta6a kula ɗaya daga cikinsu ba,sai ita da Allah ya bata dama?

Jinjina kanshi ya ɗanyi kafin yaci gaba da cewa"As a Surgeon General,I stoop too low don kawai inason cigaba da rayuwa da ita,wata ƴar ƙarama da ita,if not love dat's  Crazy me zanyi da ita.........."tuni hawaye sun wanke mashi fuskarshi,

  "Itace mutun na farko da ta fara sani zubar da ruwan hawayena,"

  Jikin Omar ba ƙaramin sanyi yayi ba,Hannu Yasa tare da janyoshi jikinshi lallashinshi ya shiga yi,Yana tausarshi, 

  

"Omar,dama kadaina Wahalar da kanka,Na yanke shawarar gobe zan tafi U.s,"

  "Dan Allah Rafayet mubi komai a sannu,Ni nasan cewa tana sonka,zata sauko ne,amma tafiya U.s will not be a Solution,"

  "Na riga na yanke shawara Omar,i will distance Myself from her,nasan hakan zai sa nasamu kwanciyar hankali in na daina ganinta,So Zan tafi kawai first thing tomorrow Morning",

  Shiru Omar yayi,don kuwa yasan Sgr bazai canza ra'ayinshi na tafiya ba,

"Shikenan,bazan hanaka tafiya ba,bari na taimaka maka,Hannunka yana bleeding,"

  Girgiza kai yayi"a'a,kabarshi kawai,"yana faɗin hakan ya sauko daga saman gadon Ya nufi toilet ɗinsa Ya shige,


Saukowa Omar yayi daga saman gadon,Ranshi ya 6aci sosai baiji daɗin abunda Sehrish ta yiwa Sgr ba,bai ta6a tunanin zata Iya furta mashi waɗannan kalaman ba,


Gyara mashi Bedroom ɗin ya tsaya yi,Sai da ya kwashe glass ɗin daya zube duka ya kawar da komai,kafin Ya sauko Downstairs Ya nufi Medical Room ɗinsu,P.A box ya ɗauko Kafin Ya koma up part ɗin Sgr,Ya ajiye mashi asaman gadonshi don yayi dressing ɗin hannunshi,


Bayan Omar ya fito a hanzarce ya nufi ɗakin Azmee,A lokacin Sehrish tana ƙumshe cikin bargo,tajiyo bugun ƙopar ɗakin,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,duk a tunaninta Sgr ne ya dawo,gabanta sai faɗuwa yake yi,ƙin buɗe ƙopar tayi Har sai da Omar ya ɗaga Murya tare da cewa"Sister Omar ne,Zo ki buɗe mun ƙopa,"

  Cire blanket ɗin tayi cike da fargaba ta ƙarasa gaban door din tasa hannu ta buɗe mashi,tunda take bata ta6a ganin Omar cikin 6acin rai irin na yau ba,jikinshi har wani jijjiga yake yi,sam babu annuri akan fuskarshi,

  Muryarta na kerma ta ambaci sunanshi"yay...ya Omar,"

  Shiga cikin ɗakin yayi bayan ya sanya hannu ya garƙame kopar,

  A fusace Ya damƙi kafaɗunta tare da jijjigata yace"Ke!Ashe baki da hankali bansani ba?Anya kuwa kinsan ciwon kanki?kin bani kunya kin kuma bani mamaki,Ki rasa abun wulakantawa Sai Sgr?tsaran wasanki ne?dan Kin samu Allah ya mallaka maki shi shine har kike kokarin banzatar dashi?Idan saboda laifin da yayi maki ne baya baki hakuri ba!shine bazaki hakura ba!........"fashewa tayi da wani irin matsanancin kuka,


   "Don me zaki ce wai jikinki yake so?ke kinsan adadin matan dake bibiyar rayuwarshi don kawai su samu shiga awurinshi koda da sunan lalatane bada aureba,Sai ke don Allah ya jarabceshi da Sonki,ni shaidane Akan Sgr,wlh da ace baisonki bazai ta6a sha'awar ta6a jikinki ba,don yana sonki ne yasa har yake yi maki hakan,shi baturen mutun ne shiyasa yake nuna maki so ta hakan........"dakatawa ya ɗanyi da yin maganar yana mayar da numfashi,zufa duk ta wanke mashi fuskarshi,Sehrish kuwa sai faman shessheƙar kuka take yi,


Sassauto da Muryarshi yayi kafin yaci gaba da cewa"Yanzu hankalinki ya kwanta,kin kaishi ƙarshe,Gobe zai koma U.s,duk don saboda abunda kikayi mashi,Kuma inaso ki sani da zarar ya ɗaga ƙafarshi yabar ƙasar nan,Akwai mata dayawa dake jiranshi,daga Cikinsu akwai Eva his Uncle's Daughter,dawowarshi kawai take jira don a ɗaura masu aure...tun suna yara take sonshi,ba abunda bata mallaka ba da duk wani ɗa Namiji zai buƙata a wurin ƴa mace..,......"

  Tunda ya soma maganar tafiyar Sgr U.s da kuma Maganar Eva,hankalin Sehrish yayi mugun tashi,duk tabi ta ruɗe ta susuce,

   "Sgr baya kula mace don bashi da ra'ayin yin aure,kuma shi ba ɗan iska bane bai ta6a kusantar zina ba balle har ya aikata ta,baisan menene so ba,baisan kuma ya akeyin shi ba,Amma wannan karon Akanki Yasan menene So,ya kuma san daɗin mace,Kinga kuwa da zarar yabar ƙasar nan Ya koma can,zai amince da Auranta ne,kodan ya nema ma kanshi mafita,ke kuma zakiyi dana sani ne,domin kuwa duk macen data samu miji kamar Sgr tayi watsi dashi wlh sai tayi danasani na har Abada,"


Fashewa ta kuma yi da wani sabon kukan tamkar ranta zai fita,Sam ta kasa buɗe baki tayi magana,


"Ya Sauke duk wani girman kai nashi,Ya ajiye matsayinshi duk don saboda ke ɗinnan,Don Ya samu soyayyarki,da kanshi ya nemi da in koya mashi soyayya saboda yana son ya faranta maki,Yana kuma son ki gane cewa ba jikinki yake so ba,Zuciyarki yake so,kuma kinyi kuskure da iliminki da hankalinka,kika bari Mijinki yake kwana da baƙin cikinki acikin zuciyarshi!?"


Rass taji gabanta Ya faɗi,girgiza kai Omar yayi,tare da juyawa rai a6ace ya nufi hanyar fita daga ɗakin har ya ruke handle ɗin ƙopar ya kuma juyowa ya kalleta,

  "Ina ƙara tunasar dake,Gobe da Safe zai tafi,shawara ta rage taki,wlh don kina ƴar uwata ne yasa na zauna ina yi maki wannan gargaɗin,Saboda ina sonki dashi,Kuma kema kina sonshi,wannan damarkice ta ƙarshe kiyi tunani kafin nan da safe,nabarki lafiya,"


Yana kai ƙarshen Maganarshi,Ya buɗe kopar ya fuce waje,


Tashin hankali,Wani irin zazza6ine Ya lullu6eta,hawaye ta ko'ina saman fuskarta,wani irin tuƙuƙin baƙin ciki take ji acan ƙasan zuciyarta,sunan Eva ya tsaya mata aranta,saboda ta ta6a jin sunyi magana akanta a lokacin baya shi da Omar,har yake cewa in ma akwai Macen da ya dace ta mallake shi,to itace,


  A hankali ta soma ambaton"Innalillahi wa'inna ilahirraji'un,"


Maganganun Oummansu ta shiga tariyowa acikin kanta,daƙyar ta iya lalla6awa ta haye saman gadon ta kwanta,sosai tashiga raira kuka kamar jinjira jikinta sai kerma yake yi,Wani irin kishine ya rufeta,cikin shesshekar kuka take faɗin"Ya Rafayet zai tafi U.s ya barni,zai je ya aureta,"nutsar da fuskarta tayi jikin pillow tana ta raira kuka,


A daren Ranar Mutun biyu basu runtsa ba,Waɗanda zuciyoyinsu ke cikin halin ha'ula'e,kamar yadda Sgr ya kwana kwance saman gadonshi cikin mawuyacin hali,Haka itama Sehrish ta kwana da tunanin abu biyu,kalaman Oummansu da kuma kalaman Marshal Omar sun tsaya mata aranta,shi kanshi Omar ɗin bai samu isasshen bacci ba,saboda damuwar daya shiga duk akan Ɗan Uwanshi,


Wuraren Sallar Asuba Sehrish tana a kwance kamar matacciya,jikinta duk ya saki,ga zazza6in da take fama dashi tare da matsanancin ciwon kai,daƙyar ta samu ta sauko daga saman gadon ta shiga toilet,agaban Sink ta tsaya tana kallon kanta cikin Mirror,fuskarta tayi jaga jaga da hawaye hada majina,jan bakin data shafa duk ya 6ata fuskar,duk ta harmutsa gashin kanta,tasha kuka sosai,lips ɗinta duk sun kumbura,hancinta yayi jawur dashi saboda matsar daya sha,tajima acikin Toilet ɗin kafin ta samu tayi alwala,


Lalla6awa tayi ta fito daga toilet ɗin ta tunkari wardrobe ɗin kayanta,hijab ta ɗauko tare da darduma ta shimfiɗata,daƙyar ta samu ta tattara natsuwarta kafin ta kabbara sallah,bayan ta kammala Sallar ta zauna tare da ɗaga hannuwanta,tana Addu'a hawaye na shararowa akan face ɗinta,jikinta duk yayi sanyi,A saman dardumar bacci ya ɗauketa,


Baccin bai kaiga yin nisa ba aka soma kwankwasa ƙopar ɗakin,kwan kwan,can cikin bacci take jin bugun ƙopar,firgigit ta farka,zufa sharkaf akan fuskarta tamkar an watsa mata ruwa,bakomai bane ya fado mata aranta ba fa ce Maganar Omar na cewa Yau Sgr zai koma U.s,A hargitse ta miƙe tare da nufar ƙopar tasa hannu ta bude,Amrish ce a tsaye jikinta sanye da hijabi,ganin Sehrish cikin damuwa yasa tace"Meya faru ne?baki da lafiya ne?a ruɗe tayi tambayar,


Sehrish bata tsaya jin amsarta ba,duk hankalinta ya tashi,ta gefen Amrish tabi da gudun gaske ta nufi babban falon gidan,babu kowa duk basu tashi daga bacci ba,Upstairs ta haye har tana tuntu6e wurin taka matattakalar,Idanuwanta sun makance tana tsoran ta rasashi,a fujajen ta faɗa part ɗinsa,shigarta falon keda wuya,Sai ga Sgr Ya turo trolley a hannunshi,Ya kammala shirin shi tsaf zai tafi Airport,Jikinshi nasanye cikin jeans da T-shirt,fuskarshi sam babu annuri akanta,ga hannunshi daya jima rauni,


Cikin sanyin Murya ta ambaci sunanshi"Ya Rafayet,"ɗagowa yayi da idanuwanshi akan fuskarta,ita kanta ta tsorata da ganin launin idanuwanshi,Sun yi jawur dasu gwanin ban tsoro,tsantsar 6acin raine acikinsu,bai amsa kiran sunanshi da tayi ba,tamkar ma baisan da zuwanta ba,janyo trolley ɗinshi yayi kaitsaye ya nufi hanyar fita daga falon inda take a tsaye,tayi tunanin zai kula ta,amma ko kallo bata ishe shi ba,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,tuni hawaye sun wanke fuskarta,Yana ƙoƙarin bi ta gefenta ya wuce,a hanzarce tayi saurin sanya hannu ta ruko damtsen hannunshi,

  Muryarta na kerma tace"Ya Rafayet,idan ka tafi ni kuma fa?ya kakeso nayi da rayuwata"?


Runtse idanuwanshi yayi"ki sakarmun hannuna,tunkafin ranki ya 6aci,"A kausashe yayi maganar,


"Na yarda kayi mun duk wani hukunci da ya dace dani Saboda bani da hankali,amma dan Allah kada ka tafi ka barni," 

  Tana kai ƙarshen maganar,ta faɗa saman faffaɗan kirjinshi ta rungumeshi sosai tare da fashewa da matsanancin kuka,har cikin zuciyarshi yake jin kukan nata,

   "Ya rafayet am sorry,bazan ƙara ba,"cikin shessheƙar kuka tayi maganar,lokaci guda kuma ta ɗauke ɗuff,a hankali ya buɗe idanuwanshi tare da sauke su akanta,tayi tighting ɗinshi sosai,kamar ance za'a ƙwace mata shi,

Nauyayyiyar ajiyar zuciya ya shiga saukewa,wani irin sanyine ya ratsa zuciyarshi,sakin trolley ɗin hannunshi yayi tare da ruƙota,ya ɗago da kanta daga jikinshi,da alama ta sume,fuskar nan tayi jaga jaga da hawaye,ta jigata sosai,jikinta yayi zafi sosai,tsantsar sonta da ƙaunarta ne acikin zuciyarshi,kamar ya haɗiyeta cikin cikinshi haka yake ji,

  Gaba ɗaya ya sa6eta saman kafaɗarshi,ya juya da ita zuwa bedroom dinshi,a saman katafaren gadonshi ya sauketa,ya gyara mata kwanciyarta,ya kasance tana fuskantar ceilling,hijabin jikinta ya cire mata,ganin yadda take zufa,a gefe ya ajiye hijabin,ya sauko daga saman gadon ya fita palour,within minute ya dawo hannunshi ɗauke da bottle water mai sanyi,gefen gadon ya zauna bayan ya buɗe murfin ya tarfa ruwan a hannunshi ya yayyafa mata shi asaman fuskarta,nan take taja dogon numfashi haɗi da sauke ajiyar zuciya ajere,tunkafin ta buɗe idanuwanta,ta soma sambatu"ya rafayet kada ka tafi ka barni,bazan iya rayuwa batare dakai ba,'


  Ajiye bottle din yayi saman drawer,kafin ya hau saman gadon gaba ɗaya,a dai dai saitin fuskarta yakai tashi fuskar,zuba mata ido yayi yana kallon yadda take ta sambatu

  "Reesh!You know you love me, but why kike wahalar dani"?he said calmly,jin muryarshi yasa ta buɗe idanuwanta,sunyi luhu luhu cike tab da ƙwalla,

   A hankali take kallonshi,yayin da shima yake kallonta,batare da kyaftawar ido ba,tamkar zasu haɗiyi junansu,saboda tsabar so,

   Ganin tana ƙoƙarin sake fashewa da kuka,yasa shi yin saurin toshe mata bakinta,da tafin hannunshi"its ok,u don't ave to cry,tunda gani a kusa dake,"

  Lumshe idanuwanta tayi tare da sake buɗesu akan fuskarshi,zame hannunshi yayi daga kan fuskarta,

"Ya rafayet,Am really sorry,pls don't leave me,i can't survive without you,"

Kalamanta ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya sukeyi ba,

  "why reesh?kin tada mun hankalina,ko bacci bana iyayi just because of you,kin fusata ni sosai,kin sanyani zubar da hawayena,'

  Girgiza mashi kai tayi"Bazan ƙara ba,"

  "Kin yarda cewa inasonki?ba jikinki nakeso ba?kuma kin amince zaki rayu dani a matsayin Mijinki Uban ƴa'ƴanki"?

  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,

Kafin tace"na aminta dakai,Na yarda da irin son da kake yi mun,kuma ina namen yafiyarka,akan misunderstanding din da muka samu,ban kyauta maka ba,its all my fault,nice ƙarama koba haka ba,kai ɗan uwana,Yayana kuma Mijina,nice a ƙasa dakai,amma ban duba hakan ba......"

  Bata kai ƙarshen maganar ba,ya dakatar da ita,ta hanyar sanya yatsanshi ɗaya asaman lips ɗinta,

   "Komai ya wuce a wurin,nima ina neman yafiyarki akan laifin da nayi maki,"

  Kallonshi kawai take yi,ba ƙaramin mamaki Sgr ya bata,ta ƙara yarda da irin son da yake yi mata,ya canza mata ba kamar da ba,

  "Nima komai ya wuce A wurina,amma pls,ka fasa tafiya U.s din,idan ma zaka tafi ƙafata ƙafarka,don bazan bari na rasaka ba,"

  Ƙayataccen murmushin gefen fuska Sgr ya sakar mata,gaba ɗaya ya tafi da tunaninta,natsuwa tayi tana kallon kyakkyawan murmushinshi,ƙurawa juna ido sukayi wani irin kallon so suke jefawa junansu,


A wannan yanayin na shauƙi,Marshal Omar ya faɗo bedroom ɗin,Yazo da niyar ya lallashi Sgr akan ya fasa tafiyarshi,tun a palour yaci karo da trolley an ajiyeshi,yana zuwa bakin ƙopar ɗakin,ba zato ba tsammani ya hango  romeo da juliet,abun ya bashi mamaki,Yadda ya samesu,manne da juna,sun ƙurawa juna ido,kamar zasu cinye junansu,Ƙayataccen murmushi marshal Omar ya saki,yadda kasan wani zautacce,Su suke yin soyayyar amma yafi su jin daɗinta,a hankali Ya furta Alhamdulillah Ya Allah,Na gode maka daka cikama ɗan uwana burinshi,Nima Ya Allah ka cikamin burina na ganin na mallaki hosana,A matsayin matata,Uwar ƴa'ƴana,Ya Allah ka dawwamar da farin ciki acikin zukatanmu,Ya Allah ka ƙara haɗa kan masoyan nan,ka albarkance da  samun zuri'a ɗayyiba,


Bai bari sun ganshi ba,juyawa yayi da sauri yabar part ɗin,A ƙopar palourn Ya tsaya tare da zura hannu cikin aljihun wandonshi,Ya zaro wayarshi,Layin hajiya azeema ya dannawa kira,sae faman sakin murmushi yake yi,kamar wanda Akayiwa Albishir da gidan Aljanna,yafi kowa farin cikin wannan ranar,


A lokacin da kiran Omar ya shiga,Hajiya azeema na kwance bata farka daga baccin asuba ɗin data koma ba,ringing ɗin wayartane Ya tayar da ita,hannu takai saman side drawer ta ɗauki wayar,ganin sunan daya bayyana akan screen ɗin wayarna yasa ta cewa"to fa,Omar ne ke kira tunda safe,to Allah yasa muji alkahiri,

  Ta ambaci hakan tare da ɗaga kiran nashi,ta manna wayar a kunnanta,

  Gaisawa suka fara yi kafin tace"Ya Andace ko kuwa har yanzu ba canji"?

  Muryarshi da alamun farin ciki atattare da ita,Yace"Congratulation Mommy azeema,munyi winning,"tunkafin Ya karasa maganar tace"Alhamdulillah Ya Allah,'ta ambaci hakan yayin da take miƙewa zaune,

  "Omar shaƙa mun naji,wlh aƙagare nake,Meya faru,sun shirya,Sehrish ta janye maganar sakin,"

  Dariya omar yayi sosai,jin yadda take ta jero mashi tambayoyi,

  "Aunty ae yanzu haka daga part dinsa nake,Na same su manne da juna,maganar saki ta ƙare,Zama na har abada,"daga haka  Omar ya kwashe duk abunda ya faru tundaga daren jiya har zuwa yau da safe daya same su,Ya sanar da ita,

  Saboda tsabar farin ciki,Saukowa tayi daga saman gadon hannunta manne da wayar,Ta shiga yin rawa,tsantsar farin cikine akan fuskarta,

  "Mommy,suna buƙatar wasu abubuwa da zasu ƙara danƙon soyayyarsu,amma kafin nan,Yanzu dai suna buƙatar lafiyayyen breakfast,don jiya ɗan uwana baici komai ba,"

  Murmushi hajiya azeema tasaki kafin tace"in sha Allah,Yanzu zan tafi kitchen don in shirya masu,"

  "Yawwa aunty,mun gode sosai,sai munzo yin godiya nida rafayet,"

  "Haba dai,ae duk yiwa kaine,kada ka wani damu kanka,Amma ya tsakaninka da hosana?Ba tada matsala"?

  Omar yace"Nikaɗai zan iya da hosana,Bata da matsala,"

  Jinjina kai tayi"shikenan omar,duk da haka zan dage damtse wurin ganin na koya mata abubuwan da suka dace,"

  "Thank so much auntynmu,mai son ganin farin cikinmu,"

  Murmushi ta saki"yanzu bari naje na shirya masu breakfast din"

   Daga haka su kayi sallama dashi,Ajiyar zuciya ta sauke fuskarta ɗauke da murmushi ta ajiya wayar sama drawer,


A hanzarce ta nufi hanyar fita daga ɗakin,tana kokarin buɗe ƙopar ɗakin,Amrish ta turo ƙopar,jikinta sanye da jallabiya black colour ta yafa mayafi akanta,

  "Amrish har kin shirya kenan"?

Ɗaga mata kai tayi"eh mommy,"

  'Meya faru naga fuskarki kamar da alamun damuwa attare da ita,"

  Cike da damuwa amrish tace"ɗazu da zan shiga ɗaki,naci karo da sehrish,fuskarta sharkaf da hawaye,wlh na shiga damu sosai,bansan inda ta dosa ba,har tambayarta nayi ko bata da lafiya,Amma bata tanka mun ba,sai dai kawai naga ta watsa da gudu..."

  Hannu hajiya azeema tasanya tare da shafa gefen fuskarta"Calm down ur mind,A halin Yanzu sehrish tafi ki ƙoshin Lafiya,tana cikin farin ciki,babu abunda ke damunta,don haka kema ki kwantar da hankalinki,"

Ajiyar zuciya amrish ta sauke,haɗi da yin murmushi,

  "Muje waje,bari nayiwa wani magana acikinsu sai ya kaiki gidan,"

  Ta ƙarasa yin maganar,tare da yin gaba,Amrish tabi bayanta,

  Suna saukowa Babban Falon,Sai ga kanal Yusif ya fito daga part ɗinsu sai faman sauri yake yi,jikinshi sanye cikin shadda brown colour,wani irin ƙamshine ke fita ajikinshi,

  "Yawwa yusif"hajiya azeema ce ta kwala mashi kira,A hanzarce ya juyo 6angaren da suke,ganin hajiya azeema yasa shi sakin murmushi,da sauri ya tunkari wurinta,yana ƙarasawa ya soma gaisar da ita"Ina kwana Auntynmu,An tashi Lafiya,"

  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Lafiyalou,Alhamdulilla,Ina zaka je naga kana ta faman zumbula sauri,"

  "Inaso zanje dubo jikin abokina ne,An farmakesu ne wurin aiki da aka turasu,yanzu haka yana asibitin yaya rafayet,acan aka kwantar dashi,

  "Allah sarki,bawan Allah,Allah ya bashi Lafiya,"acewar hajiya azeema,

  Kallon Amrish yayi,ta sunnar da kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannunta,

  "Wannan fa,ina zuwa"?

Da sauri tace"Ina kwana yaya yusif,"

  "Lafiya lou,"cike da jin kunyarshi amrish ta amsa mashi,

"Tana so zataje kwaso kayanta ne a gidansu,ni nace ta shirya zanyiwa wani magana yakaita gidan,"

"Ba damuwa,Zan sauketa,in yaso saina wuce asibitin,kafin ta kammala kwasar kayan,sai na dawo na ɗauketa,"

Wani irin farin cikine ya lullu6e amrish,

  Godiya hajiya azeema tayi mashi"nagode ssai,Sai kun dawo,"

  Gaba yayi amrish tabi bayanshi,bayan sun fita,Yace ta tsaya ya dauko motarshi,Jim kaɗan sai gashi yayi driving ɗin motar,har zuwa inda take a tsaye,buɗe motar amrish tayi kafin ta shiga daga ciki,yana a diver seat tana a gefen shi,karya kwana yayi,kafin ya fisgi motar da gudun gaske ya fuce dasu,


Lokacin da suka hau titin a tsanake yake yin driving ɗin,har suka isa unguwarsu,adai dai ƙopar gidansu Amrish yayi parking ɗin motar,juyawa ya ɗanyi gefen da take ya saci kallonta,tare da cewa

  "Zan dawo na ɗauke ki,nan da 30 minutes,ina fata bazaki gaji da jirana ba,"

  Murmushi ta ɗan saki tare da kallonshi,suka haɗa idonsu dashi,tayi mamakin irin sanyin kyan dake gareshi,mai matuƙar jan hankali,musamman kwantaccen sajen gefen fuskarshi,

  "Nagode sosai,Ya yusif,sai ka dawo,a gaishe mun da mara lafiyan,"

  Mayar mata da martanin murmushi yayi"ki kulamun da kanki,"

  "Kaima haka,"tana ambaton hakan ta buɗe motar ta fuce,


A buɗe ta samu ƙopar dake jikin gate ɗin gidan,hannu tasa ta tura ƙopar ta shiga daga ciki bakinta ɗauke da sallama,murmushi ta saki lokacin da tayi arba da baba mai gadi,zaune saman tabarma,Ga tray agabanshi mai ɗauke da soyayyun kaji,Ga kayan marmari,Ga kuma lemu acikin cup  hada kankara acikinsa,duniya tayi kyau,

  "Assalamu akaikum,"jin muryarta yasa baba mai gadi yin hanzarin kai idanuwanshi kanta,washe baki ya soma yi,ya miƙe ya nufeta"Allah sarki Amrishi,yau kece da kanki,ashe ba rabon in rigaki zuwa,don yanzun nan nake cewa da zarar na kammala yin karin kumallona,naba furannin can ruwa,Zan shirya inzo har gidanku in duba ki,"

  Zuƙunnawa amrish tayi tare da gaisar dashi,ba ƙaramin daɗi yaji ba,shi kanshi ya lura da irin sauyawar da tayi,don da lokacin bayane ko kallo bai ishe taba,balle har ta gaishe dashi,"

  Bayan sun kammala gaisawa,tace"dama,nazo kwasar kayan sawata ne,"

  "Oh to,bari na ɗauko maki key ɗin,"yakai ƙarshen maganar,tare da juyawa ya nufi cikin ɗakinsa,jim kaɗan ya dawo hannunshi,ruke da key ya miƙa mata,tasa hannu buyi ta kar6a kafin ta wuce cikin gidan,


Komawa baba mai gadi yayi saman tabarmar ya zauna,sae faman washe baki yake yi,duk murnar ganin amrish,A fili yace"Mutanan kirki,gashi har zun canza yarinyar nan,Kai Allah dai ya saka masu da mafificin Alkhairinsa,nima ata dalilin Yaron nan da muka taimaka,Sunyi mun alheri,mahaifinsu ya dunƙulo kuɗi har dubu ɗari shida ya damƙa mun,gashi yanzu inata Cin kaji,"sai faman sambatu yake yi,


Amrish kuwa bayan ta shiga gidan,bedroom ɗinta ta shige,ta kwashi kayanta acikin trolley,hada agogon diamond ɗin junaid ta haɗo don ta mayar mashi da abunshi,a falo ta zauna tana jiran dawowar kanal Yusif,har kitchen ta shiga ta dafa indomie ta zubota acikin plate ta zauna saman Sofa,tana ci tana tunanin Kanal Yusuf,


*Boss Bature*


Bayan tafiyar Amrish da kanal Yusif,juyawa hajiya azeema tayi izuwa kitchen,Anan ta samu abu tare da Mommy da saude suna girke girken breakfast ɗin gidan,gaisawa suka fara yi,kafin ta shiga shirya masu lafiyayyen abinci,mutun biyu ta shirya mawa,Na Omar da kuma Na Sgr,Har ɗaki taje ta kira hosana don takai mashi abinci,a lokacin suna kwance saman gadonsu,ita da jahad,Hajiya azeema tazo mata da maganar,hada bata shawarar tayi mashi kwalliya,ta sanya kaya masu kyau,dama kamar jira take yi,cike da zumuɗi ta sauko daga saman gadon ta faɗa toilet don tayi wanka,komawa kitchen hajiya azeema tayi ta ɗauki na Sgr da sehrish Ta nufi Uptairs dashi,


Lokacin da hosana ta fito daga toilet,ɗaure da towel a chest ɗinta,Jahad na zaune saman gadon ta manna wayarta akan kunnata,Da alama da junaid suke waya,akan idonta hosana,Ta zauna gaban mirror tana kwalliya,kamar aljana haka ta koma,amma tayi kyau ba laifi,matsalarta bata iya shafa janbaki ba,dam6arashi takeyi,bayan ta kammala kwalliyar,Ta shirya kanta cikin riga da skirt na lace milk colour,ganin tana ta kiciniyar ɗaura ɗan kwali ta kasa,hakan yasa jahad tayi rejecting ɗin wayar,ta sauko daga saman gadon ta nufeta,Da taimakon jahad, Hosana ta ɗaura kallabin,ta kuma gyara mata makeup ɗinta,asaman kafaɗarta ta yafa mayafinta,juyowa tayi tare da kallon Jahad tace"idan naje kai mashi abincin ya zance mashi"?

  Murmushi jahad ta saki tare da cewa"bangane me kike nufi ba?ko kina nufin kalaman soyayya,"

  "Eh su nake nufi,"

Dariya jahad ta ɗanyi kafin tace"yanzu lokaci ya qure,ki bari idan kika dawo sai in koya maki,"

  Girgiza kai hosana tayi"a'a wlh,nidai ki rubutamun ko a paper ne,in naje sai in dinga karanto mashi,"

  Fashewa jahad ta kuma yi da dariya,daƙyar ta tsagaita da yin dariyar tace"Its okey,amma karki bari yaga takardar,ki 6oyeta,"ta amsa mata da toh,

A paper jahad ta rubuta mata kalaman soyayyan,sai murna take yi,ninke takardar tayi,a cikin bra ɗinta,ta soke takardar,da gudu ta fuce daga ɗakin,


Murmushi jahad ta saki tana girgiza kai tace"Yau ya omar zaisha kallo,don nasan saiya ganota,"


Toilet ta shiga,after some minutes ta fito ɗaure da towel,jikinta duk lemar ruwa da alama wanka tayi,hannunta na ruƙe da short towel tana goge sumar kanta,


Kwankwasa ƙopar ɗakin akayi,batare da tambayar wanene ba,tace"Come in,"duk a tunaninta oummansu ce,


A hankali ya turo ƙopar ɗakin,jikinshi sanye da Jallabiya,batare da jahad ta juyo ta kalleshi ba,tace"Oumma,kin gamu da hosana kuwa?Yanzun nan ta gama kwalliya wai zataje kaima Ya Omar abinci,ba don na gyara mata janbakin data shafa ba,da shi kanshi ya Omar ɗin sai ya razana.....'sai surutu take yi,


Murmushi kawai junaid ke saki,Ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi,sai kallonta yake yi,koda taji oumman tasu bata tanka mata ba,Sam bata kawo komai arantaba,


Cikin sanɗa junaid yake tafiya harya ƙarasa bayan jahad ya tsaya,ƙamshin turarenshi ne ya dakar mata hancinta,lumshe idanuwanta tayi tare da sake buɗesu a hankali tace"hmmmm ina nake jin ƙamshin turare mai daɗi kamar na baby junaid ɗina,

  Kwantar da kanshi yayi saman kafaɗarta,aikuwa a firgice ta zabura zata gudu,yayi hanzarin ƙanƙameta sosai,cikin sanyin murya ya furta sunan da yake kiranta dashi"My juliet,its me ur Romeo,"

  A ruɗe tace"Junaid kayi hauka ne,Yaushe ka shigo cikin ɗakin?yanzu idan wani ya shigo ya ganmu a haka fa?ko kaya ban sanya ajikina ba,daga ni sai towel,"

  A shagwa6e junaid yace"meyasa kikayi rejecting call ɗina,batare da iznina ba?

  ɗaure fuskarta ta ɗanyi kafin tace"Am Sorry my romeo bazan ƙara yin hakan ba,but pls ka tafi kada wani ya shigo ya same mu a haka,"

  Maimakon ya tafi saiya ƙara ƙanƙameta sosai,yana shaƙar ƙamshin jikinta"Kamar nayi bacci Allah,kina jin abunda nake ji kuwa"?shiru tayi batare da tace mashi komai ba,Gaba ɗaya ya kashe mata jikinta,

  Daƙyar ta iya buɗe baki tace"Babyna,pls ka tafi,idan na kammala shiryawa,zanzo na same ka,'

  ashagwa6e junaid yace"i won't go anywhere,an fa biya sadaki,ki bari kawai na taimaka maki ki sanya kayan,tun yanzu mu fara practicing kafin a shafa fatihar auranmu,A sanyamun ke a ɗakina.......'

  Baikai ƙarshen maganarshi ba,Oummansu ta turo ƙopar ɗakin da ƙarfi,bakinta ɗauke da sallama,aikuwa a guje daga junaid ɗin har jahad,suka faɗa cikin toilet,tare jan ƙopar suka rufe,Tashin hankali,Tsoro yasa jahad tabi junaid toilet,Komai zai biyo baya,Ga Oumma ta shigo ɗakin..........'


*Boss Bature*

[3/19, 2:58 PM] +234 810 388 4440: Tsayawa abu tayi cike da mamaki take kallon ƙopar toilet din,don taji lokacin da aka banko ƙopar da ƙarfi aka rufeta,bata kawo komai aranta ba,tuni sun kammala breakfast din,jikinta ne baiyi mata daɗi,shine tashigo ɗakin  don tayi wanka kota jin daɗin jikin nata,


Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba,duk tabi ta ruɗe baiwar Allah,junaid kuwa,koda suka faɗa toilet ɗin,wata irin zufa ce ke kartowa a kan fuskar kowannansu,sun ƙurawa juna ido,

  Muryarshi na kerma Yace"Jahad,dan Allah ki taimaka,ki fiddani daga cikin toilet ɗin nan,wlh idan oummanku ta ganmu atare zata sa a fasa bani auranki ne,"

  Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Ya kakeso inyi junaid!duk laifinka ne,nayi maka magiya akan ka tafi amma kaƙi tafiya,yanzu duk wanda ya ganmu cikin toilet atare a irin wannan yanayin me kake tunanin zaiyi tsammani"?

  Tayi tambayar tana kallonshi,fuskarshi duk a hargitse,sai faman cizon yatsanshi yake yi,

  "Jahad na shiga ukuna,Wayyo Allah.....'

Bai kai ƙarshen maganar ba,ta sanya tafin hannunta,ta toshe mashi bakinshi,

  Cikin raɗa tace"Kayi shiru,kada agane cewa akwai mutun a toilet ɗin,"

  Shiru su kayi,yayin da suka ƙurawa junansu ido,lumshe idanuwanta ta ɗanyi batare data buɗesu ba,ba zato ba tsammani,taji ya faɗa mata,sosai ya qanqameta,hankalinta ya ƙara tashi,aruɗe ta shiga faɗin"junaid wai menene haka?wlh zanyi ihu kowa yaji muna acikin toilet ɗin nan,"

  "Jahad tsoro nake ji,dan Allah ki barni a haka,bazan ta6aki ba,"yana magana yana ƙara matseta ajikinshi,tarasa yaya zatayi dashi,ga Oumma acikin ɗakin,

  Batayi aune ba,taji yana goga lips ɗinshi saitin nipple dinta,kokarin kamawa yakeyi,A firgice jahad ta soma kiciniyar kwace shi,yaƙi sakinta,Ya ƙanƙameta yana faɗin"Wai menene haka jahad,so kika asirin mun ya tonu,

  A ƙule tace"bana son iskanci junaid,bazaka iya hakuri a ɗaura auran ba,"

  Da buɗar bakinsa sai cewa yayi"ae an biya sadaki,tun yanzu mu fara practicing," haushine ya isheta,saboda ƙarya yake yi,ba'a biya sadaki ba,Yana fakewa da hakan don ya samu tadinga yi mashi biyayya,

  Gartsa mashi cizo tayi asaman kafaɗarshi,abunka ga shagwa6a66en,Ya fasa ƙara tare da faɗin"Wayyo Allahna,Ta cije ni,"a gigice Jahad ta toshe mashi bakinta,ta janyoshi ta rungume don ta samu yayi shiru,


Abu dake acikin ɗakin,Abun ya ɗaure mata kai,domin kuwa tajiyo muryar mutun acikin toilet ɗin,bakin ƙopar ta nufa,ta ɗan tsaya tare da sanya hannu ta ƙwanƙwasa ƙopar"akwai mutun"

Gabansu ne ya faɗi,tuni ido ya raina fata,

"Junaid mun shiga uku,"tayi maganar,idanuwanta cike ta da kwalla 

  "Wai bakowa ne"?oumma ta ƙarayin tambayar,junaid yayi shiru ya lafe a ƙirjinta,jikinshi sai kerma yake yi ga tsoro ga iskanci cike dakai,

  Muryarshi na kerma yace"Jahad,kice mata kece,"

Jin haka yasa jahad ta ɗanyi gyaran murya,

  Ajiyar zuciya abu ta sauke tare da cewa"Lafiya naji kina ihu"?tayi maganar don ta gane wacece,

  Ƙasa ƙasa da murya jahad tace"Lafiyalou oumma,na sanya ruwan zafine,ban surka dakyau ba,"

  Jinjina kai abu tayi"ki ƙara surkashi mana,"

  "To oumma,"


Juyawa abu tayi maimakon ta fita daga ɗakin,Sai ta zauna gefen gadonsu,Tana jiran jahad ta fito itama ta shiga toilet ɗin tayi wanka 

  Hannu tasa ta 6an6are junaid daga jikinta,hannu yasa tare da dafe cikinshi,ya ɗan ɗago da dara daran idanuwanshi yana kallonta,zuba mashi ido tayi tana kallonshi,

  Kamar wani ɗan iska,Ya kashe mata ido ɗaya,tare da zuro harshen shi yana lasar gefen le6ensa,

  Abun ya bata haushi,jarabar junaid tafi ƙarfinta,ita duk a tunaninta yayi hankali tunda an rabashi da sihirin jikinshi ashe dama can tunfil azal,Ɗan iskan kanshi ne,

  Harara ta wurga mashi,tare da cewa"Wlh zan fasa auren,"

Bubbuga ƙafarshi ya ɗanyi,Ashagwaye yace"wlh da nayi maki lalata,kinga dole ki amince ayi auran,"

  Har sai da gabanta ya faɗi jin abunda yace,hankali atashe take kallonshi"nashiga uku junaid'

 

  Lamarin shi ya fara bata tsoro,ƙura ido tayi tana kallonshi,jiki asanyaye tace"Junaid,kana shaye shaye,"

  Girgiza kai yayi"wlh ko taba ban ta6a sha ba,"

  

Abu dake zaune gefen gadon tana jiran fitowar jahad,kunnuwanta suna jiyo mata ƙusƙus acikin toilet din,

  "Jahad,surutun me nake ji acikin toilet ɗin nan,ke da waye"?

  Aruɗe tace"babu kowa oumma,"jinjina kai abu tayi"kiyi sauri ki fito inaso in shiga,"

  Rass taji gabanta ya faɗi,amarairaice ta kalli junaid"Ya zamuyi,"

  "Nima kaina bansani ba jahad,pls ki nema mana mafita,"

  Shiru su kayi na wani lokaci,can taga yana nannaɗe jallabiyar jikinshi,tayi tunanin wata dabara zaiyi hada saurin cewa"Junaid,ka gano mana mafita ne"

  Batare daya kalleta ba,yace"fitsarine ya matse ni.....'

Tunkan yakai ƙarshen maganar,tayi hanzarin buge hannunshi"ashe baka da hankali,agabana zakayi,"

  "To sai me,wlh ya matse ni,in ba so kike inyi a wando ba,"zuba mashi ido tayi tana kallon ikon Allah,

  Ganin yana kokarin xame short ɗin ya curo abunshi yasa tace"Nashiga uku"!da ƙarfi tayi maganar,Abu dake zaune a ɗakin a firgice ta mike ta nufi toilet ɗin tana faman kwala mata kira"Jahad lafiyarki kuwa?wai me ke farune?tun ɗazu nake ta jin surutu acikin toilet ɗin nan,Zaman me kikeyi ne,Ya isa ace kin fito,"

  Hankali atashe Jahad tace"Babu komai oumma,Yanzu zan fito,kan famfo ne ya lalace,ruwa duk ya fallatsarmin,Shiyasa kika ji ina  magana,Yanzu zan gyara shi,ba wuya,"

Jinjina kai abu tayi"ok ina jiranki,"komawa tayi gefen gadon ta zauna tana jiran fitowarta,


  "Dan Allah junaid,kada kayi fitsarin nan,"a ƙule yace"ji wani ikon Allah,Nace dole saikin kalleni ne,ki juya baya mana,wlh sai nayi,"da sauri ta juya mashi baya,ta kifa kanta da bango,tana jin sautin fitar fitsarinshi,abun ya bata mamaki,kwata kwata junaid baida kunya,bata ta6a tunanin haka yake ba,tabbas zata sha wahala a hannunshi,don ba ƙaramin jarababbe bane,


Kwankwasa ƙopar ɗakin akayi,da sauri abu ta miƙe ta nufi ƙopar tana tambayar wanene,daga waje akace"Mommyn junaid ce,"hannu tasa ta buɗe mata ƙopar fuskarta ɗauke da murmushi,gaisawa suka fara yi kafin mommy tace"bansani ba ko Azeema ta sanar maki game da tafiyarmu dubai,"

  Girgiza kai abu tayi'a'a bata sanar dani komai ba,"

  Mommy tace"Inaji ta mantane,Dama zamuje haɗo lefen yaran nan ne,shine muka yanke shawarar zuwa can don muyi masu siyayya,amma kafin nan zamu fara zuwa kasuwa mu fara sayen wasu kayan anan,"

  Murmushi xainab ta saki"masha Allah,naji daɗi sosai,Allah yakaimu lafiya,"

  "Ameen ameen,"har mommy ta juya ta kuma cewa"oh na mata,Ya jikin Sehrish?tun a kitchen naso na tambayeki,Nayi tunanin ma idan nazo nan,zan sameta,"

  "A'a,suna a ɗayan ɗakin,Nima yanzu nake tunanin zuwa na duba jikinta,Ya jikin fawan?


  Mommy tace"da sauƙi sosai,Yanzu bai cika son fitowa waje ba,kullum yana ƙunshe a ɗakinshi,

   A ƙarshe abu tabi mommy suka tafi duba jikin sehrish,dana Fawan,'

  


Su jahad dake ƙumshe cikin toilet suna jin fitarsu,a hanzarce suka buɗe toilet ɗin,cikin sanɗa junaid ya lalla6a ya fuce daga ɗakin,Cikin sa'a bai ci karo da kowa ba,


Ajiyar zuciya jahad ta sauke,shaf shaf ta ɗauko kaya cikin wardrobe ta zura ajikinta,


*Boss Bature* 


*Reeshraf*


Sannu a hankali bacci ya ɗaukesu,rungume da juna,tamkar zai mayar da ita cikin cikinshi,a Lokacin da Mommy azeema tazo part din nashi,sallama ta fara yi shiru ba'a amsa mata ba,ranta ya bata cewa ko suna a cikin bedroom ne,Shiga cikin palourn tayi babu kowa,kaitsaye ta nufi wurin sofas ɗin,A saman table ta sauke masu trayn,yanke shawarar zuwa tadasu tayi,can kuma tayi tunanin yiwa omar magana,Ya kira shi a waya,don ya sanar mashi an kawo masu breakfast,


Sun yi nisa acikin baccinsu,wayar Sgr dake ajiye saman side drawer ta soma ringing,a hankali ya buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci don bai ishe shi ba,akan fuskar sehrish ya saukesu,zuba mata ido yayi yana kallonta,sosai ta shige mashi,ta ƙanƙameshi,sai jan numfashi take yi,lumshe idanuwanshi yayi tare dakai hannu ya shafa sumar kanta,kafin ya manna mata kiss asaman forehead ɗinta,

  "I love u.....'ya furta ƙasa ƙasa da muryarshi,har kiran yayi rejecting wani kiran Ya kuma shigowa,Hannu ya miƙa saman drawer ɗin ya ɗauki wayar,tare da duba sunan mai kiran nashi,Omar ne,picking call ɗin yayi tare da kara wayar a kunnashi,

  "How are u my own bro,"

Muryarshi a kasalance yace"Am ok,ya kake?

  "Lafiya lou,jiya banji ya kuka ƙare da mutuniyar taka ba,"

Murmushi sgr ya saki,ɗayan hannunshi na acikin sumar sehrish yana wasa da ita yace"nasan duk kai ka shirya wannan,bansan da wasu kalmomi zanyi amfani ba wurin gode maka,

  Omar yace"ae ba komai,duk yiwa kaine,"

  "Tana tare dani,na samu kwanciyar hankali,yanzu haka ma kiran wayarka ne ya tashe ni,"

  Cike da zolaya Omar yace"Ya maganar tafiya U.s ɗin?ɗazu nazo part ɗinka,na samu trolley ɗinka ajiye,"

   "Ka fara ko"?

Dariya omar yayi"Nifa nayi tunanin yanzu haka jirginka ya sauka los angeles,"

   dariya Sgr ya ɗanyi,kafin yace"don't worry ur self,tunda na samu abunda nakeso,Very soon zamu tafi,"

  "Kada na takura maka,naga jiya bakaci abincin kirki ba,Ga break fast nan a palour an ajiye maku,kaida Babynka,"

  Ƙayataccen murmushi sgr ya saki tare da cewa"thank u Omar,"

  "Aunty azeema yakamata kayiwa godiya,duk ita ta shirya wannan,"acewar Omar,

  "Okey,zanje na same ta,"ya ambaci hakan yayin da hannunshi ke asaman wuyan sehrish,yana shafa shi,laushin skin ɗinta ba ƙaramin fusgarshi yake yi ba,

  "Sai anjima,but karka manta,kuyi feeding ɗin juna,hakan yana ƙara danƙon soyayya,"ya ƙarasa maganar muryarshi da alamun dariya yayi rejecting kiran,"yaji daɗin shawarar Omar sosai,don kuwa yana cikin tsarinshi,

  Ajiye wayar yayi saman drawer ɗin,a hankali ya matsar da fuskarshi saitin fuskar sehrish,saitin kunnanta yakai bakinsa,cikin raɗa ya ambaci sunanta"Reesh,can u hear me"?

  Shiru bata  Motsa ba,hannunshi ya sanya yana ɗan shafa bayanta,yaci gaba da ambaton sunanta cikin raɗa,har sai da Sehrish ta fara mutsu mutsu zata farka,tukunna ya janye kanshi daga saitin nata,

Biji biji ta fara ganinshi lokacin da take ƙoƙarin buɗe idanuwanta,ya tasa ta gaba yana kallonta,lips ɗinta duk sun bushe,still akwai jirwayen hawaye akan fuskarta,

   A hankali ta ambaci sunan shi"Ya rafayet,are u with me,"

  Shafa gefen fuskarta yayi"My wife,am sorry nayi disturbing dinki ko?na katse maki bacci"?

  Lumshe idanuwanta ta ɗanyi sun marairaice,

  "I know you're feeling hungry,that's why na tashe ki,"ya ƙarasa maganar,tare da kai hannu ya shafi cikinta,

  A hankali ta furta"Ina jin yunwa sosai,amma nafi buƙatar yin wanka,jikina duk babu daɗi,"yadda take magana tana ɗan yamutsa fuskarta,ba ƙaramin yanayi take jefashi ba,daurewa kawai yake yi,

  Miƙewa sukayi zaune saman gadon ganin tana ƙoƙarin ɗaukar hijab ɗinta yasa shi yin saurin cewa"Ba anan zaki yi ba"?

  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,ɗaure fuskarshi ya ɗanyi alamar baiji daɗin maganarba,

  "Why ba zaki yi using da toilet ɗina ba,"?

"Idan kanaso,Sai nayi,"

Ta6a bakinshi ya ɗanyi"Sai inaso"?

  Girgiza kai tayi"Am Sorry,"

Ta ambaci hakan tare da saukowa daga saman gadon ta nufi toilet dinshi,ji yake tamkar yabita yayi mata wankan,amma yana jin shakkar ta6ata yanzu gudun kada a koma yar gidan jiya,ta burkice mashi tace Jikinta yake so,


Shiga toilet ɗin sehrish tayi tare da jan ƙopar ta rufe,saukowa sgr yayi daga saman gadon ya dawo bakin ƙopar toilet ɗin,ya jinginar da kanshi,don ya dinga jin motsinta,


Yana jiyo sautinta tana fadin"Assh..wash,"kamar ya faɗa toilet ɗin ya taimaka mata tayi wankan haka yake ji,


After some muninutes yaji motsinta a bakin ƙopar,komawa yayi gefen gadon ya zauna,yana jiranta,a hankali ta buɗe ƙopar,ta zuro ƙafarta kafin ta ƙarasa fitowa daga ciki,hannunta ruƙe da rigarta,skirt ɗin tajashi har saman ƙirjinta,gashin kanta duk ya rufe mata bayanta da  gefen fuskarta,natsuwa yayi yana kallonta batare da ƙiftawa ba,

   Tunda ta ɗago suka haɗa ido dashi,tayi saurin kawar da idonta,wani irin nauyinshi taji,


"Zan jiraki a palour,idan kin kammala shiryawa ki same ni acan,"

  Amsa mashi da toh,kafin Ya miƙe ya fuce daga ɗaikin,zubawa mirror ɗin ido tayi ganin babu glass ajikinshi,bata kawo komai aranta ba,mayukanshi na jiki masu ƙamshi tashiga shafe jikinta dasu,hada turarenshi ta fesa,bayan ta mayar da rigarta,sai da ta fara ɗaukar hijab dinta ta zurata,tukunna ta fito daga ɗakin,A saman Sofa ta same shi,ya jingina bayanshi jikinta,yayin da idanuwanshi ke a lumshe,a tsanake ta samu wuri gefenshi ta zauna,kafin ta ambaci sunanshi cikin sanyin murya"Yaya rafayet,"

  Buɗe idanuwanshi ya ɗanyi a hankali yana kallonta"har kin kammala,"ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

  Yana ƙoƙarin kai hannu yayi serving dinsu tayi saurin rigashi"Zan zuba mana,"wani irin kallon so suke bin juna dashi,zama su kayi gwanin ban shawa'a tana bashi abaki yana bata,atare suka ciyar da junansu,bayan sun kamala cin abinci,ta faɗa mashi cewa zata je ta canza kayan jikinta,tana ƙoƙarin miƙewa ya ruƙo hannunta,tare da janyota ta faɗo saman laps ɗinshi,matsa hancinshi yayi asaman suman kanta"when are u coming back"?yayi tambayar cikin sanyin murya,kafin ta bashi amsa ya kuma cewa"kona minti ɗaya kikayi nesa dani,zanyi missing ɗinki sosai,'gaba ɗaya ya kashe mata jikinta,sae faman sauke ajiyar zuciya take yi,hannayenta duka biyun suna a dafe dashi,

   "Zan dawo da anjima,"

"Promise me,"ya ambaci haka yayin da yake shafa sumar kanta da hannunshi,

  "Nayi maka alƙawari,"jinjina kanshi ya ɗanyi,Okey,zan zuba ido naga zuwanki,idan ma baki zo ba,Ni zanzo,don na baki maganinki"ba don yaso ba,ya saketa,ta mike tare da kai hannu ta ɗauki tray ɗin kayan abincin da suka kammala ci,a hankali take tafiya,yayin da ranta ke bata cewa yana kallonta,


Sai da takai bakin ƙopar,ta ɗan dakata dayin tafiyar,juyawa tayi don ta saci kallonshi,karaf suka haɗa ido dashi,murmushi ta sakar mashi,shima ya mayar mata da martanin murmushi na gefen fuska,dimple ɗinshi ya lotsa,juyawa tayi da sauri ta fuce daga ɗakin,


Tana tafiya tana tunaninshi sai kace ba yansu suka rabu dashi ba,tsananin ƙaunarshi take ji acikin zuciyarta,kitchen ta fara zuwa ta ajiye tray ɗin hannunta,kafin ta koma besdroom ɗinsu,kaitsaye ta faɗa saman gadon,yayin da idanuwanta ke kallon sama,A hankali ta furta"I luv u so much Ya rafayet,Mijina nakaina"


A 6angaren hosana kuwa,Lokacin da taje Kai ma Omar abinci,Cike da zumuɗi ta zabga sallama hannunta ruƙe da tray,sae faman zabga murmushi take yi,kamar wata zautacciya,kamar yadda ta saba shiga ɗakin shi ko sallama babu,a haka ta faɗa ciki sai da tashiga tukunna tayi sallamar daga baya"Assalamu Alaikum"a lokacin yana kwance saman gadonshi,hannunshi ruƙe da wayarshi,ɗagowa yayi tare da kallonta,wani irin kyau yaga tayi mashi,miƙewa yayi daga zaune yana kallonta batare da ƙyaftawar ido ba,gaba ɗaya ta tafi da imaninshi,ganin ya ƙura mata yasa ta ɗan turo baki tare da cewa"Ya omar,wai lafiya kake kallona,"

Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"hosana,wa yayi maki kwalliya?

"Ni nayi abunda,"

"Amma dai,ni akayiwa kwalliyar ko"?

Murmushi ta ɗan saki tare da ɗaga mashi gira alamar Eh,

  Ba ƙaramin daɗi yaji ba"Ki kaimun abincin falo,Yanzu zo muci tare ,

  Da sauri ta juya,tana shiga ta sauke tray ɗin a saman table,jiki na rawa ta zura hannunta cikin bra,ta zaro paper din da jahad ta rubuta mata kalaman soyayya,

  Karantawa ta farayi don ta samu ta haddace wasu kafin ya fito,

  "Ya Omar,inasonka so irin wanda uwa keyi ma jaririnta,kaine mutun na farko dana ji ya kwanta mun araina,nakeson kasancewa dashi na har abada,A matsayin mijina uban ya'yana,"tana cikin karantawa Tajiyo mutsu mutsun fitowarshi,A ruɗe ta nannaɗe takardar ta turata acikin bra ɗinta,


Ƙarasowa cikin falon yayi,hannu yasa ya ɗauki tray ɗin data ajiye saman table ɗin,Ya sauke shi saman carpet don suji daɗin cin abincin atare,


"Bismillah,"yayi maganar yana nuna mata wuri,da sauri ta zauna tare da lanƙwashe ƙafafunta,kamar yarda shima yayi,da kanshi ya zuba masu abincin Yace mata"mu fara ko'maƙe mashi kafaɗa tayi"Ae ni naci ya omar,kaidai kaci,"gyaɗa kai yayi batare da yayi mata musu ba,Ya soma cin abincin,

  Yana kokarin cin abincin karaf suka hada ido da ita,dakatawa ya ɗanyi"Wannan kallon fa"?

  Ƙayataccen murmushi ta ɗan saki tare da cewa"Kai dai kawai kaci gaba da cin abincin ka,"jinjina kanshi ya ɗanyi kafin ya mayar da hankalinshi kan abincin dayake ci,

  Tunani ta shiga yi,Ta manta kalaman data haddace,ganin hankalinshi baya akanta,yasa tayi sauri tura hannu ta ɗauko takardar duk ta cukuikuye,jikinta har kerma yake yi wurin karantawa,bayan ta kammala ta ninke ta mayar,

  Murmushi ta ɗan saki kafin tace"Ya Omar"ɗagowa yayi tare da kallonta yana jiran jin me zatace

   "Kasan yadda nakeson kuwa"?tayi tambayar fuskarta babu alamun wasa,

  Girgiza kai Omar yayi"a'a saikin faɗa,"

"Inasonka sosai ya omar,irin son da uwa keyi ma ɗanta,banajin zan iya rayuwa da wani ɗa namiji in bakai ba......'

Saboda tsabar mamaki baisan lokacin daya saki cokalin hannunshi ba,ya fada cikin plate ɗin gabanshi,zuba mata ido yayi yana kallonta,

  "Kaine tauraron dake haska zuciyata,dakai nake kwana dakai nake tashi Ya omar,bani da burin daya wuce in mallake ka a matsayin mijina......."

  A sukwane marshal ke kallonta,abun ya ɗaure mashi kai,kamar an sanya mata radio sai zuba take yi,abu kamar na hankali,ganin ta kakare yasa ta ɗan dakata tare dacewa"masoyina meyasa kake kallona?kaci gaba da cin abincinka mana,ni kuma zan cigaba da faranta maka rai"

   Shiru yayi yana tunanin taya akai hosana ta iya kalamai masu daɗi na hankali,Sam bai yarda da ita ba,

  "Hosana miƙe tsaye,"yayi maganar yana yi mata nuni da hannunshi,miƙewa hosana tayi,tsaf ya shiga kallonta daga saman har kasa,don yana zargin kamar karantowa take yi,ganin baiga komai ba yasa shi cewa tayi tsalle,

  Ranta ya 6aci sosai,a kule tace"Ni bazanyi ba,"

  Murmushin gefen fuska omar ya saki,

  "Shikenan,koma ki zauna,sannan kuma ki cigaba da fadamun daɗaɗan kalaman nan,inajin daɗinsu,"

Murmushi ta saki,cike da zumuɗi ta koma ta zauna,tana kokarin kai hannu ta zaro takardar ya kafe ta da idanuwanshi,duk tabi ta susuce,

  Ashagwa6e tace"Ya omar wai menene haka?ka ƙuramun ido,kaci gaba da cin abincinka mana,"

Girgiza kai yayi"a'a,nafi jin daɗin kallonki,yayin da kike faɗamunsu,"da biyu Omar yayi mata haka,

  Shuri tayi tana ta faman mazurai,domin kuwa bata iya komai ba,

  "Am listening to u,My baby "yayi maganar yana kallonta,

  Haushi ya isheta,daƙyar ta cigaba da cewa"yakai bunsurun dake cin ciyawar zuciyata,"

  Waro ido waje Omar yayi"Hosana!ni ne bunsurun"?da sauri ta sanya tafin hannu ta toshe bakinta,tana girgiza mashi kanta"wlh Ya Omar su6ul dabaka nayi,ba haka nakeso nace ba,kaine ka tsare ni da idanuwanka,"

   Harara ya ɗan jefa mata,Hannu yakai tare da ɗaukar lemu ya tsiyayashi Acikin cup,kafin ya ɗago tayi saurin Zura hannu ta ciro paper ɗin,hannunta nata kerma ta shiga dubata,da sauri ta mayar cikin bra ɗin ta ajiye,tana faman mayar da numfashi kamar wadda tasha gudu,

   Ɗagowar da zaiyi A furgice Yace"hosana!kyankyaso....."tana jin haka ta miƙe a ruɗe tana kakka6e jikinta,hada kuka nan take takardar da take ta faman 6oyo ta faɗo ƙasa a cukuikuye,tuntsirewa Omar yayi da dariya,hada dafe cikinshi,ya hasala ta sosai,Ta bubbuga ƙafarta,tare da fashewa da wani sabon kukan da gudu ta nufi hanyar fita daga falon tana kuka,miƙewa yayi da sauri yabi bayanta,har ya samu ya ruƙota tare da jangota jikinshi ya rungumeta,Yana ɗan bubbuga bayanta"Am sorry,banso na 6ata maki rai ba,nasan kinyi ne donki faranta mun raina,"


*Boss Bature*


A 6angaren Amrish kuwa,Har kusan one hour tana zaman jiran Kanal Yousouf,tuni ta jima da kammala Cin abincin,ta mayar da plate ɗin kitchen,A saman doguwar sofa ta kwanta tana jiran zuwanshi,har bacci ya ɗauketa,wuraren ƙarfe ɗaya da rabi,Motar shi ta ƙaraso bakin gate ɗin gidan,Yana yin horn baba mai gadi ya buɗe mashi,A mutunce suka gaisa da junansu,saboda ya ganeshi sosai,kuma yousouf yayi mashi bayanin zuwanshi,Bayan ya buɗe mashi gate ɗin ya wuce da motar cikin gidan,parking ɗinta yayi,kafin Ya fito ya nufi cikin gidan,A ƙopar shiga falon Ya tsaya yana zabga sallama shiru ba'a amsa mashi ba,kusan sau biyar,A karshe ya yanke shawarar shiga ciki,Da sallama abakinshi ya shiga falon,Tunkafin ya ƙarasa ciki ya hango Amrish,kwance tana bacci,gaba daya mayafinta ya zame ƙasa,tsayawa yayi yana kallon kitson kalabar dake akanta,manya manya,tayi mata kyau,baisan ta yarda zai tashe ta,Tunawa da makullin motar hannunshi Yasa shi yin dabarar girgiza key din saitin kunnanta,Sautinne Ya farkar da amrish daga bacci,mutsu mutsu ta fara tana kokarin buɗe idanuwanta,duk bata Lura dashi ba,har ta miƙe tsaye ta Sauko da ƙafafuwanta  ƙasa,Ta ɗaga hannayenta tana yin miƙa,Da sauri Yousouf Ya kawar da idanuwanshi,ganin yadda ƙirjinta ya fito sosai,

  Sai daga baya ta lura dashi,da sauri Ta ɗauko mayafinta,ta rufe kanta dashi,

  "Yaya yousouf,ka dawo,"

  Batare daya kalleta ba yace"Am sorry,na barki kina ta jirana,wani uzirine ya ruƙe.ni"

  "Babu komai,"ta ambaci hakan tare da mikewa ta ruƙo trolley ɗin kayanta,Gaba yayi tabi bayanshi har suka isa motar,kowa ya shiga ya zauna kafin ya tashi motar,ya nufi hanyar gida dasu,yana driving suna fira da ita,


*Boss Bature*


*Amani*


Tana cikin gyara kitchen tajiyo muryar Jahan daga falo yana kwaɗa sallama,fuskarta ɗauke da murmushi ta tunkari falon,A zaune ta same su saman Sofa,su biyu sun ɗauki wankan suits,ba ƙaramin kyau su kayi ba,dama duk in jahan zai zo zance,Atare da Ayaan suke zuwa,kamar yadda suke twins komai atare suke yinshi,


"Yau kune a gidan namu,"tayi tambayar tare da samun wuri ta zauna tana fuskantarsu,

  Haɗa baki su kayi wurin gaisar da ita"Ina yini aunty,mun same ku lafiya"?

  "lafiyalou,Ya kuke?ya mutanan gidan naku?Ya jikin junaid da fawan"?

  Ayaan yace"Kowa yana cikin ƙoshin lafiya,marasa lafiya kuma jiki yayi kyau,". 

  "Masha Allah abu yayi kyau,"acewar amani,

  "Bari nakawo maku abunsha"da sauri suka haɗa baki wurin cewa"a'a,bama bukatar komai,"

  Dariya ta ɗanyi,ba ƙaramin burgeta suke yi ba,har magana ma wani lokacin in zasu yi atare suke yinta,

  Ta lura da jahan sai faman waige waige yakeyi,

  "Amal ko"?tayi tambayar fuskarta ɗauke da murmushi,

  Murmushin gefen fuska Jahan ya saki tare da cewa"eh,tana ina ne?naga banganta ba"

"Bari nakira maka ita,"miƙewa tayi tare da juyawa ta nufi upstairs,

  "am so eager to see her,nayi kewarta sosai,"jahan ne yayi maganar yayin da yake zaro wayarshi daga cikin aljihunshi,

  Ayaan yace"In ka kwantar da hankalinka,Cikin ƴan kwanakin nan za'a shafa fatihar auranku,idan yaso saika mayar da ita madubi kayi ta kallonta,"

Harararshi jahan yayi "oh kana nufin zan aureta ne,kawai don na ajiyeta,na zuba mata ido ina kallonta?kaima ka sani wlh,"

  Dariya ayaan yayi,kafin ya ƙara cewa wani abu,Amal ta sauko jikinta sanye da riga da skirt na material maroon colour,tasha uban makeup,

  Da sauri jahan ya sanya tafin hannunshi Ya rufe ma Ayaan fuska,wai don kada ya kalle mashi matarshi,

  Buge hannun Ayaan yayi yana fadin"Me yayi zafi?Bari na tashi na baku wuri,idan kun kammala Zancen ka kirani in dawo in ɗaukeka,"yana kai ƙarshen maganar ya miƙe tare da nufar ƙopar fita falon yana dariya,

  Ƙarasowa Amal tayi,Tana ƙokarin zama ya nuna mata laps ɗinshi wai tazo ta zauna asama,waro ido waje tayi tana girgiza mashi kai"a'a kunya nake ji idan aunty amani ta gani fa,"

  Zare mata ido yayi"Ina wasa dake?zaki zo ki zauna ko sai ranki ya 6aci,"sam babu wasa a fuskarshi,dama haka take fama dashi,baida kunya ko kaɗan,ita kuma kunya gareta sosai,kuma sam bai iya soyayya ba,yafi ƙwarewa a harkar romance,ta ko'ina jahan yafi ƙarfinta,lalla6awa kawai take yi dashi don tana sonshi,


"Ni bazan zauna asaman cinyarka ba,Amma zan zauna a gefenka,in kuma hakan baiyi maka ba,ni zan koma ciki"idanuwanta cike tab da kwalla tayi maganar,

  Sassauta muryashi yayi"its ok,don't cry nima wasa nake maki,zoki zauna,"gefenshi ta zauna ya tsareta da idanuwanshi,sae faman gyara mayafinta take yi,saboda kallon ƙurullan da yake yi mata,. 

  "Baki yi farin ciki da zuwana bane"cikin sanyin murya yayi mata maganar,

  "Yakamata ki saki jiki dani,nan bada jimawa ba,za'a ɗaura mana aure,ko baki sona ne"?

  Ƙasa kasa da murya tace"inasonka mana,"

"To meyasa ko kallona bakya yi"?

Shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta,matsawa yayi tamkar zai shige mata,ruƙo hannayenta yayi cikin nashi,

  "Amal,"ta amsa mashi da na'am,

"Yakama ki koyi zama dani,tun yanzu in ba haka ba,zakisha wahalata,Kin cika kunya,ni kuma banason mace me kunya,its better ki cire kunyarki wurin nuna mun soyayya,kinji ko"?

  Ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

Shafa gefen fuskarta yayi"faɗamun idan munyi aure,a first night ɗinmu,me zaki yi mun,"shiru amal tayi tana tunanin amsar da zata bashi,hasalima bata gane me yake nufi ba, 

  "Kinyi Shiru bakice komai ba"?

Cike da jin kunyarshi tace"Ni bansan me kake nufi ba,"

  Dai dai satin kunnanta yakai bakinsa tare da cewa"I mean...idan zamuyi sunnah,"

Still bata gane me yake nufi ba, 

"Ya jahan ni ban fahimce kaba,"

Takaicine ya isheshi,a ƙule yace"oh,kina nufin bakisan Komai ba?a haka zamuyi aure?that's impossible,"

Ganin yadda ya 6ata ranshi yasa tace"Am sorry,wlh bansan kan me kake magana ba,"

  "Gaskiya idan har kinason mu zauna lafiya dake,to ki koyi yadda zaki farantamun kinji ni ko"?

  Ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

"Idan na tafi,kice ma Auntynki ta koya maki yadda zaki kwanta da mijinki,ina fata kinji ni"?

  Gaba ɗaya ta dabarbace,Amma tabbas bata gane me yake nufi ba,

  "Zan faɗa mata,"jinjina kanshi yayi yanzu naji magana......'ya jima a wurin Amal,kafin yayi masu sallama,ya kira ayaan ya ɗaukeshi suka koma gida,

[3/19, 2:58 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*



*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





Zazzafar haja daga Minjibir ventures,Ina masu buƙatar siyan kayan sallah Kada ku bari a baku Lafiya,Ga kaya na kece raini Na shiga tsara,Koda kudinka sai da rabonka,Kadan daga cikin abubuwan da muke siyarwa akwai Lace 

Veils

Atamfa

Shoes

Bags


Address

Hotoro ladanai  kan titin ring road

Chat 09126570345

Call 09136122503 saikun Zo💃💃💃💃





Remain few pages 😢







Bayan tafiyar Jahan,Amal ta sanarwa Amani abunda yace ta koya mata,tasha ruwan mamaki,amma ta wani 6angaren ba ƙaramin taimakonta yayi ba,tunda gashi Ya tuna mata abunda ta manta bata koyar da Amal din ba don tasan tana bukatar hakan,


A taƙaice cikin ƴan kwanakin nan,wata irin shaƙuwace a tsakanin Sgr da Sehrish,Soyayyarsu gwanin ban sha'awa,wani irin so suke yiwa junansu,a koda yaushe yana manne da ita idan har ba lokacin sallah bane tunda aikinshi na Nigeria Ya qare,jikinta yayi sauƙi sosai,tana samun kyakkyawar kulawa a wurinshi,komai atare suke yinshi,Cin abinci,bacci,da sauransu,Yanzu kowa na gidan hatta su Ammi sun gane cewa Sehrish da Sgr sun sasanta tsakaninsu,wannan yasa ammi bata ƙara neman Sehrish da su zauna akan maganar kar6ar takardarta ba,dama abunda suke fata kenan,


A 6angaren Omar da Hosana,abun sai son barka,hajiya azeema ta gyara mashi ita sosai,yanzu ta rage wannan soki burutsun nata,duk da akwai sauranta,Amma an samu cigaba,


Idan muka dawo 6angaren Romeo da Juliet,ko ban faɗa ba kunsani,Masoyane na gaske,duk da rashin jin Junaid haka Jahad ke son abunta,kamar yadda shima yake sonta,basu gajiya da bama furannin soyayyarsu ruwa,wata irin shaƙuwace a tsakaninsu,hakan yasa koda yaushe suke manne da juna,


A 6angaren Kanal Yusuf da Amrish kuwa,tuni ya bayyana mata soyayyarshi,kuma da Maganar aure ya fara zuwan mata,don baya buƙatar su 6ata lokaci wurin yin soyayya a waje tunda sun aminta da juna,abu ne kana so ana sonka,no need to waste time,hatta Abbansu yasan da maganarsu,



Saboda tafiyar Sgr da Omar U.s,Yasa aka shirya yin bikinsu a cikin ƙurarren Lokaci,gagarumin bikine aka shirya yinshi cikin sati guda,Wanda tuni an fara sanarwar ɗaurin Auransu wanda za'ayi ranar Juma'a,gaba ɗaya Social media ta ɗauka,gidajen talabijin dana radio,Ko'ina zancen auran Ƴa'ƴan Abban sojoji ake yi,Labarin ya karaɗe Duniya,wato bikine na zaratan samarin gidan wanda sukayi shura a duniyar nan tamu,daga cikin waɗanda za'a  daura auransu,Akwai Omar da Hosana,Junaid da Jahad,Jahan da Amal,Yusuf da Amrish,Osman da Khadija,Adam da Nafeesat,Fawan da Yusra ɗiyar abokin Abbansu Tafeeda,dama sun jima atare tun lokacin da yake tashen rashin jinshi atare suke da ita,kafin Allah ya shiryi kowannansu,Ayaan da Yuhana ƴar wurin ƙawar Mommynsu Dr Harriet,wanda Mommynsu ta haɗa shi da ita,Don ayi auransu atare da Jahan,saboda ya nuna cewa in dai baza'a ɗaura Auransu da Ayaan ba sai dai shima a fasa nashi,wannan dalilinne yasa Mommynsu ta haɗa Ayaan da Yuhana kuma cikin sa'a,A rana ta farko da Ayaan ya haɗu da ita yaji ta kwanta mashi aranshi,ita ma kuma haka,sun amince da junansu batare da sunsha wahala ba,bayansu kuma sai Uban gayya,Babban ɗa a wurin Abban sojoji,General Ishaq tare da Amaryarshi Hajjaju,Sai daga baya Abbansu yaji labarin rabuwarshi da Laila,Yasha faɗa a wurinshi duk da yayi mashi bayanin dalilin rabuwar aurannasu,daƙyar ya samu Abba Ya haƙura da maganar,

  Abusufyan ma yana ɗaya daga cikin wanda zasu Angwance,Shida Uwar ya'yanshi Zainabu Abu,


Waɗanda aka sanyama biki kuma,Hafsat da Ya mu'allim,bayan dagar da suka sha dashi,da farko taƙi amincewa da auranshi saboda malamine,Amma daga baya ta amince da auran nashi,gaba ɗaya sauran matasan gidan,tun daga kan Captain Najeeb,Jabeer,khaleed,da Talal,kowannansu An sanya ranar auranshi,


Murna awurin Family dinsu ba'a magana,musamman Abbansu yafi kowa farin ciki,burinshi na qarshe da ya rage mashi a duniyar nan shine yaga auran ƴa'ƴanshi,kodan yaga ƴan jikokinshi


Ba ƙaramin ƙoƙari Hajiya azeema tayi ba,tare da Mommy da Oummansu Sehrish,domin kuwa sune suka yi tattaki har zuwa Dubai wurin haɗa masu lefensu,jigunannun kaya haɗaɗɗun gaske,An kashe kuɗi kamar ba'asan wahalar nemansu ba,musamman a lefen Sehrish da Hosana da Jahad,shi Junaid ko sisi bai kashe ba,Komai da aka kashe ma Jahad Sgr ne ya ɗauki nauyin komai,hatta sadakin Junaid,Sgr ne ya biya shi gaba da baya auran gata za'ai mashi,Daga Hosana har Jahad sadakinsu da Gold aka biyashi irin na Sehrish,sauranne aka biya sadakinsu kowacce dubu ɗari uku uku,Amrish ta samu kyauta sosai a wurin Sgr da Abbansu,saboda sune suka biya kuɗin komai na kayan daki,da duk wani abu da zata buƙata,


Special Gift Sgr ya shirya ma Sehrish,Amma yace Sai sun koma California zai bata kyautarta ta musamman,Saboda ta bashi abu mafi daraja the most greatest gift,wanda kowani miji yake burin ya samu a wurin matarshi a rana ta farko daya kusanceta,tunkafin ma wannan kyautar acikin akwatinan lefenta hada na kayan adon mata,zallar Diamond ne acikinshi,


Ba ƙaramin gyaran jiki Amaren suke sha ba,masu gyaransu har daga kasashen ketare,koda yaushe cikin gyarasu akeyi,tun cikin satin da za'a ɗaura Auren,gaba daya amaren suka hallara a gidan,saboda programes da aka shirya,gidan yasha gyara sosai,An ƙawata shi,idan ka shiga cikinshi kamar ka bar Nigeria ne saboda tsabar haɗuwar da yayi,Naira tasha kashi,an ɗaukko masu aikin cikin gida,manya manya chefs waɗanda zasu gudanar da abincin bikin,da kuma Event planners wanda zasu tsara shagulgulan da za'ayi na bikin,

 Anyi shagulgulan biki na kece raini,An yi shiga ta alfarma,Anci ansha An godema Allah,kuma kowa ya nishaɗantu,


A ranar Juma'a,dubban Jama'a suka shaida ɗaurin Auran zaratan Samarin gidan Abban Sojoji A Abuja central Mosque,Masallacin ya cika maƙil da Mutane,ba masaka tsinke duk wani wanda ya amsa sunansa a Nigeria ya hallaci daurin auren,Bayan kammaluwar ɗaurin auran,A daren Ranar aka kawo duka amaren wanda acikin gidan Abba zasu zauna,don tuni an fara gine gine na wasu 6angarori da za'a ƙara,Amma kafin nan,kowaccensu zata tare a ɗakin Mijinta ne na wani lokaci,dama burin Abbane kowannansu in yayi Aure yafi son ya zauna a gidan tare da matarshi,saboda baison suyi nesa dashi,


Shirye shiryen tafiya U.s Ya kankama,tun ana saura kwana ukku ya rage jirginsu ya ɗaga,Sehrish ta lalla6a Sgr don ya kaita Gidan Yari taga Aunty azmee,Dayake yanzu farin cikinta yakeso,Baiyi mata musu ba,da kanshi yakaita prison,Lokacin da taga Azmee tasha kuka sosai kamar ranta zai fita,Azmee ta rame ta ƙanjame,idanuwanta daƙyar take buɗesu,Sun rungume juna sosai,koda Sehrish ta sanar da ita cewa zata sanya a sassauta hukuncin da aka yanke masu,sai cewa tayi ita batason fita daga gidan yarin saboda gudun ta ƙara faɗawa halaka,tafi son zama anan saboda tafi samun natsuwa wurin yin ibadarta da neman yafiya wurin Ubangiji,kuma ta nemi yafiyar Sehrish akan Laifin da tayi mata,tun daga kan juya mata da tunaninta da tayi,lokacin da ta manta dasu Hosana,tace ita tayi hakanne saboda halin da tashiga na yawan damuwa shiyasa ta mantar mata dasu,da kuma lalurar da ta ɗaura mata na yin gane gane,duk sai da ta nemi yafiyarta,ta kuma sanar da ita cewa itace take kiran Sgr a waya tana raira mashi kuka saboda Son da take yi mashi,Komai sai da Azmee ta sanarma Sehrish,A ƙarshe ta sanar da ita cewa Suyi ƙoƙari su nemo Haroon domin kuwa Haroon Jinin Salahuddeen ne,mahaifinshi Jabeer ɗane ga Aminullah,wanda ya kasance Ƙanin salahuddeen ne uwa ɗaya Uba ɗaya,Saboda ƙiyayyar da ke tsakanin duka 6angarorin guda biyu suka sanya dokar da zarar anga Jinin Salahuddeen A kashe shi,Suma kuma su Salahuddeen ɗin suka sanya dokar daga zarar anga Jinin Ubaid da Uba a kashe su,A sanadin tafiyar da Aminullah yayi tare da matarshi da dansu ƙarami wanda bai mallaki hankalinshi ba wato Jabeer,Akan hanyarsu ta dawowa gida,Ubaid ya sanya ƴan ta'adda suka farmakeshi,gaba ɗaya suka kashe shi tare da matarshi,Shi kuma Jabeer suka barshi yana ta gararanba a cikin garinsu,har Allah yasa wani malamin makarantar Allo ya ɗaukeshi,A wurin shi Malamin Jabeer ya taso,kunji yadda akai haroon ya kasance Jinin Salahuddeen,A wurin Saratu matar ya sayyadi Azmee ta samu labarin nan,Saboda ita kanta batasan wanene Jabeer ba,Ashe Danginsu sunsan komai game da Shi ita kaɗai aka 6oye mawa,sai daga baya take ji a wurinta,ta bata labarinne acikin ɗakin da aka kaisu dayake su biyune aka kulle acikinsa,kuma ta tabbatar mata da cewa Haroon ɗan Jabeer ne,domin kuwa Hamma Ghali baya haihuwa,shi kanshi ya san da hakan,Amma don baƙin zalunci ya 6oye mata komai akanshi,


Lokacin da Azmee ta kammala bata labarin nan,tasha kuka kamar kamar me,Ashe Haroon ɗan uwansu ne,abun ya ɗaure mata kai sosai,iya cuta dai sun cutar da rayuwarshi,sun kuma sanya ƙiyayyarshi acikin zuciyoyin ƴan uwanshi,bawan Allah,ko a wani hali haroon yake ciki ayanzu?


A nan Sehrish take sanar da ita game da aurarrakin da aka daura ciki harda na Amrish da Yaya Yusuf,ba karamin farinciki Azmee tayi ba ta kuma kara yin danasanin abunda ta aikata masu don Mutane ne su masu matukar hallaci,Bayan Sehrish tabar prison ɗin,Ta kwashe komai ta sanar da Sgr,Sam bai yarda da maganarta ba,har sai da ya tambayi Abbansu game da Labarin kawunshi Aminullah,Anan Abba ya kwashe komai ya sanar dashi har labarin mutuwar da su kayi shida matarshi,labarin yazo ɗaya da wanda Azmee taba Sehrish,kuma Abba ya sanar dashi cewa Bayan mutuwar Aminullah da matarshi,An tsinci gawawwakinsu Amma ba'a samu gawar ɗansu ba ƙarami da suka tafi dashi,wato Jabeer,tunda Sgr yaji hakan,nan take ya yarda cewa dagaske dai Haroon jininsu ne,Abun Ya ɗaure mashi kai,ya kuma ji tausayin yadda rayuwar Haroon ta kasance,bashi kaɗai ba,Kowa na gidan da yaji labarin Wanene Haroon,wasu har kwalla suka zubar mashi,Kuma yanzu ashirye suke dasu nemo shi,don su dawo dashi acikinsu,yaci gaba da rayuwarshi kamar kowa,


An sassauta hukuncin da aka yankewa Azmee da Saratu,An fito dasu daga ɗakin duhun sannan An rage masu shekarun da zasu yi a kurkukun,daga shekara 20 zuwa shekara 10 cuf,ba kowane yayi masu wannan ƙoƙarin ba fa ce Sehrish,ita ta nemi wannan alfarmar a wurin Sgr,Ya kuma amsa mata,


A 6angaren Aunty babba kuwa,Tuni an sallameta daga asibiti,ta koma gidansu kano,lokacin da ta samu labarin Auran General Ishaq da aminiyarta Hajjaju,Tasha kuka tayi danasanin rayuwarta fiye da tunanin me tunani,taji raɗaɗi da ƙunci acikin zuciyarta,Har abada bazata ta6a manta Asarar da tayi a rayuwarta ba,duk don saboda abun duniya,yanzu gashi ta tashi a tutar babu,da ita da zero basu da bambanci,


Daga cikin waɗanda zasu tafi U.s,Hada Junaid tare da Jahad,Ba don Abbansu Yaso ba,Saboda shaƙuwar da yayi dashi,Ya amince ne kawai saboda Sgr ya nemi daya bar mashi Junaid ya zauna a wurinshi tare da Jahad har ya kammala karatunshi acan,Kuma hada ƙarin Idan aka tafi da Sehrish da Hosana,Jahad bazata ji daɗi ba,tasaba da ƴan uwanta sosai,Abba baidamu ba saboda Allah ya hore mashi,idan yaso duk weekend zai iya hawa jirgi don yaje can ya ganshi,wannan abu ne mai sauƙi a wurinshi,tafiya dai ta kankama,Yau ta kasance rana ta ƙarshe da ta rage masu a Nigeria,Washe gari zasu tafi tunda Asuba,duk wani shirye shirye daya kamata suyi sun kammala shi,tafiyarce kawai ta rage masu,Gobe in Allah ya kaimu da Rai da Lafiya.



*Ayi hakuri da wannan Yau sai ahankali,da babu kwara ba daɗi,Amma in sha Allah zanyi kokarin yin long pages na Ƙarshe,ina sa ran Sunday in Allah Ya yarda littafin abban Sojoji zaiyo maku bakwana,Lahadi kenan😢waɗanda ke buƙatar karanta Littafin daga farko zuwa na uku Suyi mun magana ta whatsapp 08103884440*

[3/19, 2:58 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*



*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



Zazzafar haja daga Minjibir ventures,Ina masu buƙatar siyan kayan sallah Kada ku bari a baku Lafiya,Ga kaya na kece raini Na shiga tsara,Koda kudinka sai da rabonka,Kadan daga cikin abubuwan da muke siyarwa akwai Lace 

Veils

Atamfa

Shoes

Bags


Address

Hotoro ladanai  kan titin ring road

Chat 09126570345

Call 09136122503 saikun Zo💃💃💃💃





Remain few pages 😢




*Har weekend zanyi posting,in sha Allah Ranar Lahadi Zan saki Last page Na Abban Sojoji,😢waɗanda ke buƙatar karanta Littafin daga farko zuwa na uku Suyi mun magana ta whatsapp 08103884440*


Godiya ta musamman ga waɗanda suka ƙarfafamun guiwa tun daga farkon Littafin nan har zuwa ƙarshen shi,Saƙon godiyata yana nan tafe 😍










gaba ɗaya saida abba ya tara ma'auratan A babban Falon gidan yayi masu nasiha sosai,Ammi ma tayi masu nasiha,abusufyan ma yayi masu,gwaggon katsina dasu Aunty azeema duk saida suka yi masu nasiha,Jikin kowannansu Yayi sanyi,su jahad sunsha kuka sosai,Saboda tafiyar da zasuyi subar Iyayensu da ƴan uwansu,hatta hosana da bata da cikakken hankali sai da tayi kuka,lokacin da ake yi masu nasihar,tun a daren ranar suka fara yin bankwana da ƴan uwansu,kafin asuba su tafi,


Wuraren ƙarfe 12 da dare,Oummansu ta tarasu a ɗakinsu,Bayan sun kammala sallar nafila,kowannansu Na sanye cikin Hijabi,Sunyi kyau kamar larabawa,saboda gyaran da suka sha,fatarsu har sheƙi take yi,hannayensu akwai zanen ƙunshin jan lalle da akayi masu na bikinsu,Sae ƙamshi ke tashi ajikinsu,Suna zaune saman darduma,


"Oumma yanzu shikenan tafiya zamuyi mu barki da daddy dasu abba"?Hosana ce tayi tambayar,

  Abu tace"ae tafiya ba mutuwa bace,Idan da rai da lafiya wata rana zaku zo mana,muma kuma zamu zo maku,"tuni idanuwanta sun cicciko tab da kwalla,

  Fuskar jahad ɗauke da damuwa tace"Ina zullumin tafiyar nan Oumma,jikina duk yayi sanyi,Zamu tafi wata uwa duniya,inda bamu son kowa ba,bamu da dangi acan,Bamu san ya zasu kar6emu ba,"

  "Jahad,ki kwantar da hankalin ki,kidaina zullumi,kuma kidaina cewa baku san kowa ba,Idan har kuna tare da Omar da Rafayet to ku ƙaddara cewa tamkar duka family ɗinku suna atare daku,domin kuwa ina tabbacin cewa zasu baku kyakkyawar kulawa,fiye damu,Kada ku manta su ɗin jininku ne,Ƴan uwanku,Yayyanku kuma mazajenku,baku da wani makusanci daya wuce su aduniyar nan,bazasu ta6a bari rayuwarku ta wulaƙanta ba,ko yatsa wani yace zai ɗaga maku Bazasu ƙyaleshi ba,shiyasa ni bana shakku akansu,na yarda dasu sosai,Kuma ina matuƙar Alfahari dasu a matsayin 

Surukaina,Nasan zanyi kewarku sosai,Zan zubda kwalla akan rabuwa daku,Amma inna tuna cewa rabuwa  ta zama dole,wata rana ma duniyar zaku bari,ko ku tafi koni na rugaku tafiya,Sai inga wannan bakomai bane,duk mun nisan da zakuyi indai kuna acikin duniyar nan,zamuyi iyayin waya,harma Video Call,kuma zaku dinga zuwa mana,muma kuma zamu zo maku,shi Aure ba inda bai kai mutun......'hawayen da take 6oyewa ne suka soma gangarowa asaman fuskarta,da sauri ta sanya hannu ta sharesu,

  A hankali Sehrish ta ɗago da idanuwanta cike tab da kwalla tana kallon fuskar Oummansu,

  "Dole sai kunsa haƙuri A rayuwar auranku,kuma kuyi biyayya ga mazajanku matsawar bai sa6a ma Allah ba,duk abunda basa so ku kiyayeshi,duk wani abu da zai faranta masu rai kuyi kokari wurin ganin kunyishi,Sannan ku dage da yin addu'a banda wasa da ibada,duk wani jin daɗin duniyar nan ƙararre ne wata rana,kada ku shagala ku manta daku su waye,wata rayuwa kukayi abaya..,....."daƙyar abu takai ƙarshen maganarta,duk jikinsu yayi sanyi sosai,duk sun natsu suna sauraronta,gaba ɗaya idanuwansu cike tab da kwalla,

Sosai abu tayi masu nasiha,Ta kuma ƙara tunasarsu dasu game da yin tsafta,gyaran jiki,sarrafa abinci,kusan raba dare su kayi abu na koya masu rayuwar zaman aure,A ƙarshe tace"Allah yayi maku Albarka,Allah Ya baku zaman Lafiya da mazajanku,Ina roƙon Allah yasa Wannan auren da kukayi ya zama silar Shigarku Aljanna,'

  Da ƙarfi suka amsa mata da ameen,

"Allah Ya albarkace ku da samun zuri'a ɗayyiba,Allah Ya kare ku daga sharrin maƙiya da mahassada,"

"Ameen Ameen Oumma"

Ganin yadda duk jikinsu yayi sanyi yasa ta soma ƙoƙarin faranta masu rai donsu sakin jikinsu,

"Kunsan wani abu"?girgiza mata kai su kayi alamar a'a,

  "Lokacin dana taso rayuwata,danginmu duk sun watse,saboda talauci,kowa takanshi yake yi,babu wani haɗin kai,A wurin haihuwata Mahaifiyata Ta rasu,Mahaifina ya damƙani a hannun kishiyar Babata,Matar nan ta tsane ni,babban baƙin cikinta irin farin jinin da nake dashi,mutane har zuwa sukeyi suna roƙonta akan ta basu ni su raine ni,ganin irin baƙar wahalar da nakesha,Amma matar nan taƙiya,saboda gudun kada in samu rayuwar jin daɗi inyi arziƙi,ta tauyemun haƙƙina,Dama ance duk xakaran da Allah ya nufeshi da yin cara,Sai yayita,mutuwa ne kawai banyi a hannun matar nan Ba,nifa ban ta6a tunanin zan kawo wannan lokacin da raina ba, ban kuma ta6a tsammanin akwai wata rana wadda zata zo irin wannan ba,Hasalima bansan wanene abusufyan ba Shima baisanni ba,ina nijar shikuma yana a nigeria,Kaji wani iko na Allah,babu wanda yasan da wani,ban ta6a tunanin ma zanyi aure ba balle har in haifi ya'ya har ƴan uku,Sai gashi ƙaddara takai mahaifina aiki gidansu,Ni kuma silar mahaifina dayazo ya ɗaukeni sakamakon ganin irin wahalar da kishiyar babata take bani ya dawo dani nigeria,A gidansu Abusfyan,ƙaddara ta haɗani dashi,Har mukayi aure na haifeku,Yanzu gashi har kun girma kuma kunyi aure Wata rana kuma zaku haifi ya'ya,Lamarin ubangiji da girma yake,Allahu akhbar......."fuskarta ɗauke da murmushi takai ƙarshen maganar,

Dariya hosana tayi"Oumma,Nima Allah yasa in haifi ƴan uku,"

  Buge mata baki Jahad tayi"ko kunya babu,agaban oumma kike cewa zaki haihu,"dariya abu tayi,Sehrish kuwa murmushi tasaki,

  Ɗaure fuska Hosana tayi tana jifar Jahad da harara,tare da jan dogon tsoki,"

"Yakamata ku kwanta kuyi bacci,har kusan ƙarfe ɗaya da wani abu,gashi gobe tunda asuba zaku tafi,"

Amsa mata su kayi da toh oumma,


Asaman gado, oumma dasu jahad suka kwanta,Cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba dasu,banda Sehrish sai da tabari sunyi bacci tukunna ta fito daga ɗakin,Jikinta sanye da sleeping dress,Riga da wando Orange,ta yafa mayafi akanta,jikinta sai ƙamshi yake yi,yunwa ce ta fito da ita,tunda tasha ruwa bata ci komai ba,saboda zullimun tafiyar da zasuyi,dayake Yau da azumi ta tashi,bata nufi kitchen kaitsaye ba,Babban falon gidan ta shiga babu kowa,shiru kake ji,Kowa yana can manne da matarshi aɗaki,A hankali take bin ko'ina na gidan da kallo,Tabbas zatayi kewarshi sosai,Bazata ta6a mantawa da rana ta farko data fara zuwa gidan aiki a matsayin namiji,In ta tuna wasu abubuwan sai tayi murmushi,wasu kuma tayi dariya,Yayin da wani abun idan ta tunashi sai ta fashe da kuka 


Tajima acikin Babban falon tana zagaye shi,kafin ta juya ta nufi kitchen don ta zuba abincin da zataci,Koda ta shiga kitchen ɗin,ta soma neman abinci,bata samu komai ba duk an cinye abincin gidan,Kamar ta ɗaura hannu akai tayi ihu saboda takaici,ko kaɗan bazata Iya jure yunwa ba,rabonta da abinci tunda asuba da tayi sahur,tunanin ɗaura girki ta soma yi,batare da 6ata Lokaci ba,ta haɗa chicken pepper soup,bayan ta kammala ta ɗebo dankalin turawa acikin store ta  fere shi,


A hankali yake saukowa downstairs,Idanuwanshi da alamun bacci acikinsu,daga shi sai Short ajikinshi gajeran wando,Babu riga,daga gani atakure yake,Ya kasa bacci saboda rashinta a kusa dashi,Yayi jiran harya gaji batazo ba kamar yadda ta saba zuwa suna kwana a bedroom ɗinshi,Wannan dalilin ne yasa shi fitowa domin nemanta,yana ƙarasa saukowa babban falon kaitsaye ya miƙi hanya zai nufi corridor ɗin ɗakinsu,ba zato ba tsammani idanuwanshi suka hango mashi ita cikin kitchen ta juya baya agaban Gass Cooker,Abun ya ɗaure mashi kai,Kamar wata Aljanna,duk irin tsoranta amma sai gata a kitchen kusan ƙarfe 2 na dare tana girki,


Walking slowly ya nufi kitchen ɗin,A bakin entry ɗin ya tsaya,Yana binta da kallo,kasa kunne yayi yana sauraran waqar da take raira,

  "Nagode ma Allah dana cika buri,Na zama matar rafayet,Yanzu babu mai mun gorii,Sgr gashi gabana,umm umm matsayin miji mallaki na....."

  Murmushin gefen fuska ya saki har dimple ɗinshi ya lotsa,cikin sanɗa  yake tafiya har ya isa bayanta,tunani ya shiga yi taya zai ruƙota batare data tsorata ba,don yasan halinta,yanzu ko magana yace zaiyi mata Zata iya firgita,gashi tana agaban gass cooker,kada asamu matsala,

  Motsi ya soma yi da lips ɗinsa yana ƙoƙarin yin magana,yaji tace"Ina nake jin ƙamshin turaren ya rafayet,kodai hancina ne.....'bata kai ƙarshen maganar ba,a hankali Sgr,ya zagayo da hannunshi ya ruƙe hannunta dake ruke da turner ɗin da take juya chips ɗin data ɗaura,

 Har ta wage baki zata fasa ƙara,Yayi saurin cewa"its me,"Ajiyar zuciya ta shiga saukewa,ba ƙaramin tsorata tayi ba,kwantar da kanshi yayi asaman kafadarta,

  "I ave been waiting for u,kin manta da mijinki ko"

  "Am Sorry ya rafayet,kana araina"

 

 "Reesh..u know I can't sleep without you on my chest,saboda rashinki a kusa dani na kasa runtsawa,"yakai ƙarshen maganar tare da manna mata kiss asaman neck ɗinta,slowly ya xagayo da hannunshi saman stomach ɗinta"da kanki kike girki a irin wannan lokacin"?

  "Yunwa nake ji,nayi azumi yau,shiyasa na ƙaurace maka,kuma tunda nasha ruwa,bansamu naci komai ba,"

  "You did fast without my permission"?yayi tambayar tare da juyo da ita,Yadda zai samu damar ganin fuskarta,'

 A hankali take bin jikinshi da kallo,har izuwa saman fuskarshi,kullum ƙara kyau yake yi,ga cikakkiyar sura,hada ƙarin kwanciyar hankalin daya samu,lips ɗinsa sunyi pink,sae faman lumshe idanuwanshi yake yi,saboda baccin da yake ji,kamar yadda take kallonshi haka shima yake kallonta,

  Sunnar da kanta ƙasa tayi tana wasa da yatsun hannnunta,

  "Am sorry,nayi laifi ban sanar dakai ba,"

  "Azumin menene kikayi"?

"Nayi shine saboda kai,wannan alƙwarine na ɗaukarwa kaine,duk ranar da Allah ya mallakamin kai amatsayin mijina,A ranar zanyi fasting domin nuna godiyata ga Allah,daya bani the most greatest gift,bansamu nayi azumin ba,saboda yanayin da muka shiga,Sai yau Allah ya bani ikon yi,"

 Tunda ta soma magana,ya kafe ta ido yana kallonta,kamar ya haɗiyeta saboda tsananin son da yake yi mata,shi kanshi shaidane akan irin son da take yi mashi,

 "Da ace kin sanar dani,da munyi azumin atare,"

 murmushi ta ɗan saki,batare da tace komai ba,sam ta manta da chips ɗin da take frying

  "Ɗaya daga cikin nasarorin da nasamu arayuwata,hada mallakarki da nayi,wannan babbar nasara ce agare ni,Am so proud of u,I love u......'yana kai ƙarshen maganarshi,ya janyota jikinshi sosai yayi tighting ɗinta,kafin a hankali ya ɗago da kanta,zubawa lips ɗinta ido yayi,ba ƙaramin missing ɗinsu yayi ba,Tana ƙoƙarin buɗe baki tayi magana Yayi saurin haɗa bakinsu cikin na juna,zura tongue ɗinshi yayi acikin bakinta,Sosai ya shiga bata hot kissing,lokaci guda suka kacame ma juna,sosai sehrish ta shiga mayar mashi da martani,sun zunduma tsulundum,Gaba ɗaya hannayenta na acikin doguwar sumar kanshi,tamkar tana yi mashi susa,duk ta hargitsa mashi gashin da hannunta,


Tun hannunshi na a bayanta har yakai ga zagayo dasu cikin rigarta,ya soma shafa shafaffen cikinta har izuwa saman ƙirjinta,sam babu bra ajikinta,gashi abun tubarkalla,sun cika tamkar zasu fashe,tunda Sgr ya damƙesu,laushinsu ya fisgeshi,yabi ya susuce ya ruɗe,sosai ya shiga murzasu da hannunshi,sun manne ma Juna,gudun kada ta fara gajiya da tsayuwar yasa ya ɗauketa tamkar yar baby,asaman jikinshi,ƙafafuwanta na zagaye dashi,yayin da kanta ke asaman kafaɗarshi,Mayafin data yafa a kanta tuni ya jima da zamewa ƙasa,sumar kanta duk ta rufe fuskarta,gaba ɗaya ya sabule rigar jikinta,ya fito da boobs ɗinta,ya kafa bakinsa kamar jinjiri haka ya shiga sucking ɗinsu,duk ya zautar da ƴar mutane,gaba daya kalasa ta rufeta,ta lafe mashi,tana jin duk wani motsinshi ajikinta,


Chips ɗin da sehrish ta ɗaura,tuni ya jima da ƙonewa, ƙauri ya fara karaɗe kitchen ɗin,duk basu sani ba,Ana ta shan Love,


Gaba ɗaya sun fita cikin hayyacinsu,ko gajiya da tsayuwar baiyi ba yana ta biyan buƙatarshi,Kamar ance ta ɗago da kanta daga saman kafaɗarshi,Kwatsam Tayi arba da Abbansu junaid Ya nufo kitchen ɗin,Ta window ta hango Gifcinshi yana sanye cikin Jallabiya,A firgice Ta furta"Innallahi Ya rafayet Abba,'

 Ya kurmance baijin abunda take cewa,kiciniyar ƙwace kanta ta soma yi don ta sauko daga jikinshi,Wani irin ruƙo yayi mata bana wasa ba,Bugun bayanshi tadinga yi tana faɗin"Yaya Rafayet ka sake ni,Ga abba nan yana zuwa,"

   Sgr bai tashi ankara ba,Sai da sehrish ta gartsa mashi cizo asaman shoulder ɗinshi,Baiji zafin cizon ba,Amma Yaji koken da take yi,A firgice ya sauketa,da gudun gaske ta nufi ƙarƙashin dining table ɗin dake a  cikin kitchen ɗin,ta 6oye ƙarƙashin shi tana faman sauke ajiyar zuciya,


A hanzarce Sgr ya kashe gass cooker ɗin,ƙiris ya rage Wuta ta kama, frying fan ɗin yayi baƙiƙƙirin Wani irin baƙin hayaki ke fita daga cikinshi,gaba ɗaya yabi ya ruɗe,hannu yasa yana sosa sumar kanshi,yana jiyo takun takalmin abbansu yana shugowa Cikin kitchen ɗin,

  Cike da mamaki abba ya tsaya yana kallon bayanshi,farat ɗaya ya gane cewa Sgr ne,duk da ya juya bayanshi,Abun ya ɗaure mashi kai,Sgr a kitchen,

  Gyaran murya ya ɗanyi mashi don ya juyo,Shiru Sgr yayi mashi,don a halin da yake ciki yanzu farat ɗaya abbansu ya kalleshi sai ya gane a wani yanayi yake ciki,

  "Rafayet me kake yi a kitchen"?

Daƙyar Sgr ya iya buɗe baki yace"Dad...am cooking....'

 "Girki kuma?kai da kanka?sai kace mace?dama kasan hanyar kitchen"?yayi tambayar cike da tuhuma,

  Shiru Sgr yayi don baida amsar da zai bashi,

  "Idan yunwa kake ji meyasa ba zaka kayi magana a girka maka ba"?

  "banaso na tashi kowa ne,"ya bashi amsa a ƙule,Still bai juya ya kalli abban nasu ba,

  "Amma nayi mamaki gaskiya,Wai dama  ka iya girki"?ae nayi tunanin Ci kaɗai ka iya,"

  Yatsina fuska sgr yayi,tamkar ya fashe da kuka,sam baiso zuwan abbansu ba,

  Cike da zolaya abba ya kuma cewa"Wai tsayuwar me kake yi ne,Ka juyo mana muyi magana,"

 "Ina ƙarasa Soyawa ne,"

Jinjina kai abba yayi"Masha Allah, Ashe ba iya ruƙe bindiga kaɗai ka iya ba,hada girki,bari na zauna na jiraka,don wlh nima yunwarce ta koroni,yayi maganar yana shafa cikinshi,

  Da sauri sgr yace"Why not ka koma ɗaki zanzo na kawo maka dakaina,in na  kammala "girgiza kai abba yayi"A'a,nafiso muci atare cikin kitchen ɗin nan,Yau zan ɗanɗani girkin General ɗin sojoji,"takaici duk ya cika Sgr,baisan ya zaiyi da abbansu ba,kamar yasan me suke yi acikin kitchen ɗin yaƙi tafiya,A ƙarshe ma wuri ya samu ɗaya daga cikin dining chairs ɗin da sehrish ta 6oye a ƙarƙashin Table ɗinsu,Nan ya zauna,yana jiran Sgr Ya kammala masu girkin"'sam abbansu bai Lura da mayafin sehrish dake yashe kasa ba,ga kuma slippers ɗinta dake a ƙasan ƙafafun Sgr,bai kuma Lura da kaskon da Sgr ya sauke ba,

  "Rafayet wai ƙaurin me nake ji ne"?

 "Albasa ce ta ƙone,"

Yatsina fuska abba yayi"ƙaurin ba daɗin ji,dan Allah karka bari abincin ya ƙone,"

  Amsa mashi yayi da "toh"


Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin ƙafafun abba masu sanye da slippers,sai faman karkada kafafun yake yi,duk fargaba ta kamata,ta ƙanƙame jikinta a ƙarƙashin table ɗin,tuni zufa ta wanke fuskarta,har rage numfashinta tayi duk don kada abba ya ganta


  Daƙyar Sgr ya samu ya matsa,Ya ɗauko plate mai faɗi Ya zuba masu chicken papper soup ɗin da sehrish ta kammala,duk baiji daɗi ba,baiwar Allah tasha wahalar Girka abunta don tana jin  yunwa,Ga abba yazo zai cinye mata kazarta,


Duk wani motsinshi akan idon abbansu ya kafe shi da ido yana kallonshi,dama saida ranshi ya bashi cewa Shi yake kallo,a sukane ya juyo hannunshi ruƙe da plate ɗin,haɗa ido su kayi da abbansu da sauri Sgr ya kawar da idanuwanshi,

  Wani irin kallon ƙurulla abbansu keyi mashi,Duk yabi ya tsargu,murmushi yagani akan fuskar abbansu me haɗe da dariya,ɗaure fuska Sgr yayi tare da samun wuri ya zauna,Suna fuskantar juna shi da abban nasu,Sauke plate ɗin yayi asaman table ɗin ya turama abbansu"Gashi nan,bismillah,"

  "Kai bazaka Ci ba"

 Girgiza kai Sgr yayi"Na ƙoshi"

  ɗaure mashi fuska abba yayi"In har bazaka ci ba,nima na ƙoshi,tun ɗazu na lura dakai sai wani shan mur kakeyi saboda kawai nace ina jin yunwa,gobe fa zaku tafi ko irin missing ɗina baka yi,"ya ƙarasa maganar yana harararshi,

   Jin haka yasa Sgr ya saki fuskarshi don ya faranta mashi

  "Am Sorry dad..let's eat together,'yakai ƙarshen maganar tare da zura hannunshi ya ɗauki cinyar kazar yakai bakinshi yana tauna,abba ma ya sanya hannu suka soma Ci atare,sai faman lashe baki yake yi"Wai dagaske kai kayi girkin nan?

  Jinjina kai Sgr yayi alamar Eh,

 Abun ya ɗaure mashi kai"Danasan haka ka iya girki,da tun farko ban ajiye azmee a gidan nan ba....."

  Sakin baki Sgr yayi sototo yana kallonshi,shikuwa sai jin daɗi yake yi Sgr ya iya girki,.  

  sehrish dake la6e ƙarkashin table ɗin,ƙamshi duk ya cikata,Kamar ta fashe da kuka,saboda yunwar da take ji,ta kwalla fa rai sosai,"

  "Kasan wani abu"?girgiza kai sgr yayi alamar a'a

  Abba yaci gaba da cewa"ɗanɗanon girginka Sak irin na azmee ya akai haka"?

 Yatsina fuska Sgr yayi,kafin yace"May be dan inacin abincinta ne,yasa taste ɗin yazo ɗaya dana ta,"

 Murmushi abba yasaki"U are right...ka manta baka kawo mana abunsha ba?ƙishi nake ji,'


Har ya yunƙura zai miƙe,Abba yayi saurin dakatar dashi"koma ka zauna,Kasha wahalar yin girki nasan duk ka gaji,bari naje na ɗauko mana,"


Ajiyar zuciya Sgr ya sauke tare da komawa saman kujerar ya zauna,Abba ya mike yabar wurin,Kafin ya dawo Sgr yayi saurin ɗebo naman Ya zurama Sehrish ta kasan teburin,har saida ta tsorata ganin hannunshi,da sauri ta sanya hannu ta kar6a,ta shiga turawa abakinta tana ci,ƙasa ƙasa da murya ya furta"Am really sorry duk laifina ne,da banzo ba da duk hakan bata faruwa ba,"

 Murmushi ta saki batare da tace mashi komai ba,sake ɗebowa yayi ahannunshi ya miƙa mata,ta sanya hannu ta kar6a,ta tura abaki ta lamushe,cikin sanyin murya tace"Ƙishi nake ji,kuma ina jin bacci,"_

  Kafin ya bata amsa sai ga abba ya dawo hannayenshi rungume da bottle waters masu Sanyi,hada na Lemu ya haɗo masu,


Ajiyesu yayi asaman table ɗin,Ya zauna idonshi akan plate ɗin,A ruɗe yace"kai!ya akai naga an kwashe?duk kai ka cinyesu"?

 Ɗaga mashi kai Sgr yayi alamar eh,Sam abba mai yarda da maganarshi ba,saboda tun da suka fara ci ko cinya ɗaya bai iya ci ba,Amma daga zuwa ɗauko lemu da ruwa harya Cinye saura kaɗan kazar ta rage,


Tura mashi lemun yayi agabanshi'Take it,"

  "Ruwa nake buƙata"ya ambaci hakan tare da kai hannu ya ɗauki robar ruwa mai sanyi,mai maimakon yasha sai ya tsaya yana jiran abbansu ya fara kafa baki zai sha nashi,Shi kuma sai yayi dabarar mika mata ruwan,

  Lemu abba ya ɗauka ya buɗe shi ya kwafa abakinshi yana sha,A hanzarce Sgr ya zura hannunshi ƙarƙashin table ɗin ya miƙa mata robar ruwa,ta sanya hannu biyu ta kar6a,buɗe murfin tayi kafin ta kwafa a baki tana sha,


  Bayan abba ya kammala shan lemun ya ajiye robar ruwa,

  Da buɗar bakinsa sai cewa yayi"kai Ina ɗayar robar take ne?Guda huɗu ne na kawo mana,"hankalin Sgr ba ƙaramin tashi yayi ba,

  "Daddy uku ne fa ka kawo,"girgiza kai Abba yayi a'a,guda huɗu ne Ta lemu biyu ta ruwa biyu,Kodai ta faɗa ƙarƙashin table ne....'yakai ƙarshen maganar yana ƙoƙarin leƙawa ƙarƙashin teburin,A Ruɗe Sgr yace"karka kuskura ka leƙa......"tashin hankali sam baisan Ya furta hakan ba,tsabar ruɗi ne


  A ruɗe abba ya ɗago yana kallonshi"Rafayet ni kake ce ma kar in kuskura in leƙa?Saboda me"?

  Muryarshi na kerma yace"bansan nace haka ba,"

  "Kodai kayi ajiya a ƙarƙashin taburinne"?

  Da sauri yace"A'a,

 "To meyasa kace kada na leƙa"?

 Shiru Sgr yayi batare daya ce komai ba,"

  Sehrish dake ƙarƙashin table ɗin duk ta furgita,jikinta sai kerma yake yi,batasan ya zatayi ba idan abba ya ganta,


 "Shikenan,tunda baka so na leƙa,Amma ɗayar robar fa?ina ka kaita?

  Wani irin wahalallan yawu ya haɗiya,

 "Abba baka jin bacci ne?dare fa yayi sosai"

  "Na kasa yin bacci ne saboda tafiyar da zakuyi gobe,zanyi missing ɗinku sosai,".

  Murmushin yaƙe sgr yayi"but u ave to sleep,gobe zamu airport ba zaka rakamu ba"?

  "Kada ka damu da wannan,rashin baccina bazai hana in rakaku airport ba,"

  Jiki asanyaye Sgr yace"shikenan ae,"

  Dariya ce ƙumshe abakin abbansu,kar yake kallonshi don tunda ya shigo kitchen ɗin ya gane cewa bashi kaɗai bane aciki,zuba mashi ido kawai yayi don yaga iya gudun ruwanshi,


Wata dabara ce ta faɗo mashi,A hankali Ya sanya hannu tare da Cire murfin robar ruwan Daya kammala sha,Sgr Duk bai Lura ba,Janye hannunshi yayi zuwa ƙasan table ɗin yasan tabbas indai macace a ƙarkashin table ɗin da zarar ya wurga murfin zata fasa ƙara,tayi tunanin Ko wani mugun abunne ya faɗo,


Daddagewa Abba yayi da ƙarfi ya wurga murfin Robar ruwan kaitsaye ya faɗa saman ƙafafun sehrish,Aikuwa A gigice  ta fasa ƙara tana faɗin"Wayyo Allahna Ya rafayet 6era 6era...."

  Tuntsirewa Abba yayi da dariya hada dafe ciki,Sgr dake zaune tamkar an dasa mashi aya,Sam ya kasa motsi,wata irin kunyace ta rufe shi,ya kasa ɗagowa su haɗa ido da abbansu,sosai abba keyin dariyar hada hawaye akan fuskarshi,Miƙewa tsaye yayi daga saman gujerar,Ya nufi hanyar fita daga kitchen ɗin  yana tafiya yana dariya har yakai bakin ƙopar fita,ya ɗan dakata da yin tafiyar ya juyo ya kalli Sgr dake zaune Ya sanƙare duk yabi ya dabarbace,

  Gyaran murya abba yayi mashi Ya ɗago suka haɗa ido dashi,

   "Ɗan rainin wayau,da kace bakaso"?

 Ƙayataccen murmushin gefen fuska Sgr ya saki har dimple dinsa ya lotsa

  "Ashe kana nan ƙumshe da ƴar mutane,A kunnan abusufyan saina faɗa masa"yakai ƙarshen maganar tare da juyawa yabar kitchen ɗin yana dariya tare da girgiza kai,"


Ajiyar zuciya Sgr ya sauke,A hankali ya ambaci Sunanta"Reesh...."cikin shessheƙar kuka ta amsa mashi"Na'am ya rafayet,"saukowa yayi daga saman kujerar Ya zuƙunno kasan table ɗin,cikin sanyin murya ya soma magana"ya tsorata ki ko?"?

  Jinjina mashi kai tayi,fuskarta sharkaf da hawaye,sai faman shessheƙar kuka takeyi,ruƙo hannunta yayi tare da fito da ita daga karkashin table ɗin,Hugging ɗinta yayi ajikin shi,Yana shafa sumar kanta"Am really sorry,if u are still hungry i can cook for u...". 

  "A'a na ƙoshi,bacci nake ji," 

 ɗaukarta yayi asaman kafaɗarshi ya nufi hanyar fita daga kitchen ɗin,upstairs Ya wuce da ita part ɗinshi,ko'ina a gyare tsaf,A bedroom ɗinshi Ya sauke ta,

  "Zan shiga toilet,"tayi maganar tare da juyawa ta nufi toilet ɗin,bin bayanta yayi"lemme help u....'bata yi mashi musu ba,atare suka shiga toilet ɗin,bansamu damar leƙawa ciki ba, balle in gano maku me ke wakana,saboda sun rufe ƙopar,


After some minutes Sgr ya fito ɗauke da sehrish,irin ɗaukar da akeyiwa Jariri,su duka biyun Suna  ɗaure da towel a  qugunsu,launi ɗaya farare,


Kaitsaye ya sauketa Asaman gadonshi,Yana ƙoƙarin miƙewa ta sanya hannu ta damƙi towel ɗin jikinshi gaba ɗaya ta warwareshi,kamar jira yake yi dama bai gamsuba abba  ya katseshi,komawa yayi samanta,yayi mata rumfa da faffaɗan ƙirjinshi,Sam basu gajiya da juna, kamar zasu kashe kansu,sai da suka raba dare,kafin Allah ya kawo bacci yayi awon gaba dasu,ƙankame da juna,sai da ana kiran sallar asuba,ya tashi sehrish ya ɗauko mata kayan baccinta da kanshi ya zura matasu ajikinta,cikin sanɗa ta fito daga part ɗinshi ta sauko downstairs,sai da tafara zuwa kitchen ta ɗauki mayafinta tukunna ta wuce ɗakinsu,


Bayan Kammaluwar Sallar asuba,matafiya suka shirya tsaf,domin tafiya Airport,Dukansu matan suna sanye cikin jallabiya baƙa,Sun laga gyale akansu,Sgr Da Omar suna sanye cikin Shadda,Junaid kuma yana sanye cikin suit farare,


Gaba ɗaya mutanan gidan Sun hallara a babban Falon gidan, lokacin da kowa ya kammala fitowa,Suka ɗunguma izuwa Wajen da motocinsu suke,kusan dukansu zasu yi masu rakiya,Amma banda Amaren Gidam,tun anan Sukayi bankwana dasu,Amrish tasha kuka sosai,haka Amal ma,


A motar dr harris,gwaggon katsina da abu suka shiga,tare da saude wadda ke zaune A gefenshi

  Abba kuma tare da mommy suka shiga motar Fawan,


osman da adam a motar kanal Yusif suka zauna,


Najeeb kuma a motarshi Talal Da junaid suka shiga,


Sehrish da Jahad da hosana,Suna zaune a motar abusufyan Dakanshi zaiyi driving ɗin ya'yanshi,


Hajiya azeema tana acikin motar su twins,Jahan ne ke a mazaunin driver Ayaan na a gefenshi,


Akwai motocin Security dake gaba da bayan motocinsu,

Sgr yana acikin motarshi,motarsu Marshal Da major tana a bayan tashi,


Slowly motocin suke tafiya ajere har suka fito daga cikin babban gate ɗin gidan,koda su Jahad da sehrish suka ga An fita daga gate ɗin gidan sai suka fashe da kuka atare,Abusufyan sai lallashinsu yake yi,Shi kanshi daurewa kawai yake yi,idanuwanshi cike suke tab da kwalla,


Lokacin da suka ƙaraso Airport ɗin at the same time su kayi parking ɗinsu,A tsanake duk suka fito daga cikin motocin,idanuwan kowannansu Yana akan Katafaren Privet jet ɗin da aka tanadar masu,wanda ya kasance Mallakin Rafayet ne,jigunannan gaske,Mai ɗauke da Sunanshi Ajiki da manyan haruffa akayi rubutun SGR


Tunkafin su iso Airport din junaid keta kukan rabuwa da abbansu da ƴan uwanshi,Kowa jikinshi yayi sanyi,


Rungumeshi abba yayi sosai ajikinshi yana shafa sumar kanshi,

  "Junaid so kake nima inyi kukan ko"?

  Cikin shessheƙar yace"Abba bansan na tafi nabarka,"

  "Junaid aduk inda kake a faɗin duniyar nan,inaso ka sanya aranka cewa Muna atare da juna,zan dinga zuwa akai akai ina ganinka,"daƙyar abba ya samu ya lallashe shi,bayan ya saki abbansu Ya rungume Fawan yana kuka,kowa yayi tsaye cirko cirko gwanin ban tausayi,

  Bubbuga bayanshi fawan yayi"be a man mana,Kada ka bani kunya,dan Allah kadaina kukan nan,"

  "Ya fawan,tafiya fa zamuyi,"

 "Tafiya ae ba mutuwa bace junaid,just calm down ur mind,Da zarar babynka ta haifu zan wanko ƙafa inzo suna"cikin raɗa yayi mashi maganar a kunnanshi,har sai da junaid yayi dariya,bayan ya rabu da fawan ya rungumesu twins atare yana raira masu kuka,

  "I love u so much Ya jahan da Ya ayaan,Zanyi missing ɗinku sosai,"

  Atare suka haɗa baki wurin cewa"We love u so much Our shagwa6a boy,"

 Bayan yabar wurinsu Ya nufi kanal  Yusouf yayi hugging dinshi"yaya yusif yanzu shikenan.....'

  "Junaid banaso kana zubar da hawayenka,inda rai da lafiya wata rana zamu zo,kaima kuma zakazo,"

  "Amma ae bazan dinga ganinku kullum ba,"ashagwa6e ya ƙarasa maganar,ba wanda junaid ya bari,ɗaya baya ɗaya sai da ya rungume kowa hadasu uncle da hajiya azeema dasu Osman da Najeeb,


Bayan ya kammala nashi,Su Sehrish suka Soma bin kowa suna yi mashi sallama,Gwaggon katsian hada kukanta,Za'a tafi da ƴa'ƴan abusufyan ɗinta,Sosai ta rungumesu ajikinta,Suna kuka tana kuka,babu mai lallashin wani,daga wurin gwaggo wurin hajiya azeema suka wuce,Ta haɗasu duka ta rungumesu,tana lallashinshu,daga wurinta suka nufi wurin Mommy,Itama ta rungumesu ajikinta,daga wurin mommy suka nufi wurin saude ta rungumesu,Sai da suka gama da kowa tukunna suka nufi Oummansu,ta haɗasu duka ta rungumesu,hawaye jaga jaga akan fuskokinsu,bayan sun gama da matan suka nufi wurin Daddynsu da abbansu,Kowa ya sanya masu albarka,ɗaya bayan ɗaya suka bi mazan suna yi masu bankwana,a lokacin Junaid yana manne da oummansu,ta rungumeshi sosai,kamar zai koma cikin cikinta,


Sai daga bisani Omar da Sgr suka soma bin kowannansu suna yi mashi bankwana,Lokacin da suka zo wurin abba Ya shafa sumar kan kowannansu kafin yace"Omar Rafayet"ya ambaci sunansu,Suka amsa mashi,

Kafin yaci gaba da cewa"A matsayina na mahaifinku babu abunda banyi maku ba,duk wani nauyi naku dake akaina na sauke shi,Saura ku ya rage naku,Ga Amanar ƴan uwanku nan,Ku kula da rayuwarsu,saboda ƙaunar dake a tsakaninku dasu yasa zasu bar kowa nasu,iyayensu danginsu,zasuyi rayuwa daku a inda basu da kowa sai Allah daku ɗin nan,Ku ruƙe amana,kada ku bari koda kwallarsu ce ta zuba kasa,Ku share masu hawayansu,in suna da damuwa kuyi ƙoƙari wurin faranta masu,da zarar kun bar ƙasar nan  basu da wani makusanci daya wuce ku ɗin nan,Kune a matsayin Iyayensu, kuma danginsu........"sosai amma yayi masu nasiha,duk ya kashe masu jikinsu,


Lokacin da suka je wurin abusufyan,Ya kirasu Su jahad suka jera dasu,ya kuma kira junaid shima Yazo,Ruƙo hannun junaid yayi idanuwanshi cike tab da kwalla ya ruƙo hannun Jahad ya haɗasu wuri guda,Muryarshi na kerma yace"junaid ga amanar Jahad nan na baka,"kallon juna Junaid da jahad su kayi,idanuwan kowannansu cike tab da ƙwalla

  "Na yarda dakai sosai,Nasan Zaka ruƙe mun amanarta,"

  Jinjina kai junaid yayi"in sha Allah uncle,zan ruƙe maka ita amana,bazan ta6a bari tayi kukan rashinku atare da ita ba,"

Kowa dake a wurin saida ya saki murmushi,Jin abunda junaid yace,Yayi magana ta hankali,


Sakin hannunsu Abusufyan yayi,ya kuma ruƙo hannun Omar Ya ruƙo  hannun hosana dake ta kuka ya haɗasu wuri guda,

  "Omar Na yarda dakai sosai,na yaba da kyawun halayanka,Ga amanar ƴata nan,na baka,"

  Tuni idanuwan Omar suka ciko tab da kwalla,daƙyar ya iya buɗe baki yace"In sha Allah Uncle,Zan maye gurbinku a wurinta,Zan bata kulawa fiye da yarda zan kula dakaina,"


Murmushi abusufyan yayi bayan ya saki hannun Omar ya ruƙo hannun Sgr,tare dana Sehrish wadda ke ta faman shessheƙar kuka ya haɗa hannayensu cikin na juna,Kallon Sgr yayi yayin da shima Idanuwanshi na akan fuskar Uncle ɗin

  Cikin Zolaya abusufyan yace"Surukina nakaina"murmushin gefen fuska sgr ya ɗan saki,

  Mayar da idanuwanshi yayi kan Sherish"My daughter,"cikin shessheƙar kuka ta amsa mashi"Na..na...am daddy.."


   "Rafayet Bana kokwanto akanka,Na yarda dakai kuma na yarda da irin ƙaunar da kake yi mata,Ga amanar Sehrish nan na damƙa maka,"


In sha Allah Uncle,i will take care of her,bazan ta6a bari tayi maraici atare dani ba"

  Murmushi abusufyan ya saki tare da cewa"Allah yayi maku albarka gaba ɗayanku,"sosai yayi masu addu'a,Kafin daga bisani su kayi Sallama da kowa,Omar na ruƙe na hannun Hosana suka nufi stairs ɗin jirgin,Junaid yana abayansu hannunshi ruƙe dana Jahad,Sgr na ruƙe da hannun Sehrish,a haka suka hau matattakalar jirgin, sai da suka kusa shiga ciki,Suka juyo su dukansu suna kallon Iyayensu da ƴan uwansu,Atare suka ɗaga hannu sunayi masu bye bye,



Suma su Abba suka  Ɗaga hannuwansu  suna yi masu bankwana,da gudu abu ta shige cikin motar abusufyan tana kuka,komawa su kayi cikin motocinsu,A jere suka bar Airport ɗin,Tun suna akan titin komawa gidan,Jirginsu Sgr Ya gifta ta Saman iska,Suna jin ƙararshi,🛫😭



Bayan sun koma gidan babu wanda ya iya cin abinci acikinsu,tamkar anyi mutuwa,gidan duk babu daɗi,Babu Junaid babu Ya Omar babu Babban Yaya,Babu Sehrish babu hosana babu Jahad,Kewarsu duk ta kama ƴan gidan,oummansu har maganin ciwon kai tasha Saboda kukan da tayi,



Los Angeles


California🛬





💫💥💫💥💫💥💫💥💫💥💫


*_ALBISHIRINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE , SHAHARARRAR KUMA KASAITACCIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WADDA KUKAFI SANI MAMAN YUSUF YAR SOKOTO TANA YI MAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE CIKIN FADIN NIGERIA DA NIGER KARKU MANTA MACE MAI KYARA KANTA BATA BORANCI_* 💃💃💃💃💃💃💃  07069711327


_Akwai zafafan kayan Mata masu kyau da arha cikin sauki da rahusa Kuma duk inda kike zamu aika maki kayanki cikin aminci da yardar Allah ba cuta ba cutarwa don a Dade anayi sai gaskiya uwargida da amarya ku garzayo Kar abaku labari_


Munada kalolin Kaya kamar haka💥💫💥💫💥💫👇🏻👇🏻


Maganin sanyi sahihi Mai fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci na maza Dana Mata


Maganin gyaran nono domin dawo da martaban nononki hadin gargajiya da bashida illah ajiki


Maganin hips Mai tado da hips cikin kankanin lokaci


Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko dai dai misali kiyi kyau kema ki shigo cikin jerin Mata masu aji


Maganin rage kiba da tumbi Wanda zaisa ki sace ki koma Yar dai dai abin alfaharin kowane namiji,


Akwai kalolin gumbuna masu kyau da saukar da ni'ima


Maganin matsi masu ciko da gaba da matseki Kamar Yar budurwa uwa uba zasu Baki dandano Mai gamasar da maigida


Kalolin garrika masu bawa mace niima da jimawa ajiki


Kalolin tsumi Sha yanzu magani yanzu dasa Mai gida ihun Dadi


Zumar mallaka

Zumar goron Tula

Zumar ridi 

Zumar Mai rubutu


Hadin mallaka 

Turaren mallaka

Shu'umar humra

Turaren AL'AJABI

Matan gaske

Ak 49

Sirrin tafin k'afa

Turaren fuska

Hatsabibin turare

Kwallin mallaka

Zoben mallaka 

Jigidar maida tsohuwa yarinya

Maltinar Mata

Karya gado

Yajin Mata (yajin Mai ciko da mace)

Yajin maza (domin Karin k'arfi)




Muna dahuwar Kaya kamar haka💫💥💫💥👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻


Dahuwar zabo (mallaka)

Kazar Yar gata

Yan shila 

Ciccibi

Dambu

Zuciya 

Yan ciki

Kwai ukku

Tsoka Tara

Kifi 

Da sauransu



Akwai sirrika sosai da muke hadawa ga wacce kishiya ta addabeta ko wadda take fama da butsarin namiji ko mafadacin namiji ko namiji Mai yawon dare ko Wanda yake bin Mata insha Allah duk zaku samesu Kuma da yardar Allah za'asamu biyan bukata


Muna bada magani ga yarinyar da tsautsayi ya fad'a Mata ta rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji Kuma insha Allah zaadace da yardar Allah


Abubuwan da yawa gsky Wanda in nace Zan lissafasu sai nakwashi tsawon lokaci maiso tabini PC don ganin kalolin kayan da muke dasu ,


Karku manta mace Mai gyara kanta Bata boranci taku ce maman yusuf Yar mutan sokoto 07069711327

.

Don Allah wadda Bata shirya ba tabari sai ta shirya sannan tayimun magana🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼🙌🏼ngd 


07069711327

[3/19, 9:44 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*



*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*



Zazzafar haja daga Minjibir ventures,Ina masu buƙatar siyan kayan sallah Kada ku bari a baku Lafiya,Ga kaya na kece raini Na shiga tsara,Koda kudinka sai da rabonka,Kadan daga cikin abubuwan da muke siyarwa akwai Lace 

Veils

Atamfa

Shoes

Bags


Address

Hotoro ladanai  kan titin ring road

Chat 09126570345

Call 09136122503 saikun Zo💃💃💃💃








_California🛬_


_Los Angeles International Airport _



Alhamdulillah matafiya sun sauka Lafiya,lokacin da jirginsu yayi landing,Airport ɗin cike yake maƙil da dubban Sojoji sanye cikin kakinsu,ba masaka tsinke,danƙara danƙaran motoci tsadaddu kuma haɗaɗɗun gaske masu numfashi a jere,wasu daga cikin Sojojin hannunsu na ruqe da Flower,Abun gwanin burgewa,wasu kuma suna ruqe da Welcome Symbols Mai ɗauke da Sunan SURGEON GENERAL ALEXANDER AND MARSHAL OMAR,dama da zarar yabar Nigeria Sunanshi ya tashi daga Rafayet ya koma Alexander saboda shine real name da yake using dashi kafin ya musulunta,daga cikin waɗanda suka zo tarbarsu hada Uncle Donald tare da Matarshi da kuma ƴa'ƴansu guda biyu Eva da Jessy,gaba ɗaya kowannansu fuskarshi ɗauke da tsantsar farin ciki,don ba ƙaramin kewarsu sukayi ba,baka jin sautin komai saina National Anthem ɗinsu,


Lokacin da suka saukko daga saman jirgin hannuwan kowannansu na ruƙe dana matarshi Dubban Sojojin nan suka buga ƙafa tare da Sara masu,Su sehrish sun sha ruwan mamaki,Ganin Yadda Sojoji suka cika Airport duk don saboda Zuwansu Sgr,Lokacin da mutane suka fara Lura da Zoben Hannun Sgr Abun yayi matuƙar ba kowa dake a wurin mamaki saboda basu san da zancen Auranshi ba,Zoben hannunshi ne Yasa suka gane cewa Yayi aure,Don Bai ta6a sanya zobe ba dama su saida dalili ko soyayya ko aure kesa a liƙa shi a hannu,Mafi akasari ma Sai zasuyi aure suke sanya ring a yatsansu,Tun a cikin jirgi kafin su ƙaraso,Yaba sehrish Diamond ring ɗin agogonsa ta sanya mashi a hannu,Saboda bayason yasha wahalar yi masu bayanin cewa yayi aure da zarar sun gani a hannunshi zasu fahimci komai,Aiko dai sunsha ruwan mamaki,tunda Eva ta ankara da zoben hannunshi,taga kuma ya ruƙe hannun Sehrish,Sai ta fashe da matsanancin kuka,da gudu ta koma cikin motocinsu,shi kanshi Uncle ba haka yaso ba,Yayi burin Sgr Da Omar su auri jininshi saboda shi ya raine su,kuma ƴa'ƴanshi duka suna matuƙar ƙaunarsu,musamman Eva saboda Sgr  taƙi yin aure,takusa shekara arba'en babu aure duk don saboda Shi,ta ƙwallafa rai Akanshi taƙi kula kowa,Baiwar Allah,


Sam basu nuna komai a fuskarsu ba,Sunyi masu kyakkyawar tarba,Su Jahad sunƙi sakin jikinsu duk sunsha jinin jikinsu musamman da Eva ta juya tana kuka,Sun jima a Airpot ɗin Suna gaisawa da mutane Kafin daga bisani suka shiga cikin jigunannun motocin da akazo ɗaukarsu dasu,Wai ina Hosana,duk tabi ta furgice,taƙi yarda Omar ya saki hannunta,ta ƙanƙameshi,



Kaitsaye Suka wuce Gidan Uncle Donald,katafaren gidane haɗaɗɗen gaske,An ƙawata gidan sosai duk don saboda zuwansu Sgr,koda suka shiga cikin gidan Su Sehrish Sunƙi sakin jikinsu,Tsoronsu ma suke ji,gani suke kamar zasu cutar dasu ne,Lokacin da aka shirya masu breakfast,Ƙin ci suka yi,Kowa tace ta ƙoshi,Mommy Sai lalla6asu take yi tana faɗin Su saki jikinsu su ƙaddara kamar suna a gidansu ne,Amma suka ƙiya,kwara ma Jahad ta ɗan ci abinci,ita hosana abincin nasu ne baiyi mata ba,ta dai ci wani abun wanda ta saba gani a gida Nigeria,wani kuwa ko son kallonshi bata yi,ita kuma sehrish taso ta ci,wani irin tashin zuciyane yazo mata, daga tayi yunƙurin ci sai tafara yunƙurin amai,Wannan dalilinne yasa taƙi cin komai amma tasha Lemu mai sanyi,tasha fruit,


Haɗaɗɗen Bedroom aka basu inda zasu zauna,koda suka shiga ɗakin,Hosana ta rufe ƙopar wai kada a shigo akashe su,Saboda ta kalli wani film na turawa da suke nuna wariyar launin fata,😂


Sai da Uncle Donald ya tarasu yayi masu fada sosai akan auran da sukayi batare da saninshi ba,Yaso ace sun sanar mashi da ba abunda zai hana ya hallacci ɗaurin Auransu,Baiji daɗin hakan ba,duk da haka sai da Ya shirya masu Party A washe garin ranar da suka zo,Acikin gidan Akayi shi,Musamman aka ɗauko Makeup artists suka yima su Jahad kwalliya,Aka Sanya masu wedding gown,Mazan kuma Suka shirya cikin suits farare,manya manyan Mutane suka halarci partyn,hada shuwagabaninsu na Sojoji,abun ya ƙayatar sosai,An ci An sha,Anyi rawa,An kuma Yi hotuna,daga cikin hotunan da suka yi hada wanda Sgr da Omar suka yi da kakinsu,Hosana da Sehrish ma Aka basu Uniform na mata suka sanya,sunyi kyau over kamar Sojojin gaske,Shima Junaid sai da yasa Rigima Aka bashi Uniform ya sanya Jahad ma ta sanya aka ɗaukesu hotuna,Sun ji daɗin ranar sosai,kowa sonsu yake yi,duk inda suka shiga nuna su akeyi da Hannu,kowa so yake ya ɗauki hoto dasu,sun samu kyaututtuka masu tarin yawa,ɗaukaka Iya ɗaukaka,



Rayuwarsu acikin gidan duk atakure suke yinta,babu yadda Mommy batayi dasu ba akan su saki jikinsu Amma sun ƙiya,Hatta Eva daga bisani da Sgr Ya lallashe ta,Ta sassauto kuma har wurinsu tazo don su gaisa,Daƙyar suke yi mata magana,rashin sabone duk ya jawo hakan,Kwanansu Uku Sgr Ya yanke shawarar zai ɗaukesu daga gidan Ya mayar dasu Katafaren Gidanshi,


Haɗaɗɗiyar Daula ce,Aljannar Duniya,Hamshaqin Gidan Sgr na bugawa a Jarida,Tanƙameman gidane Gari guda,Idan nace zan tsaya bayyana kyawun gidan To tabbas A iya wurin bayaninshi Littafin Zai ƙare Har ma a shiga littafi na Huɗu,Baki bazai iya kwatantashi ba,

domin kuwa Ganinshi Yafi jinshi,duk wani abu daka sani na more rayuwa Na jin daɗin Duniyar nan to akwaishi aciki,Kai idan mutun ya tsinci kanshi acikin gidan nan,Sai  ma Ya manta cewa da tur6aya aka halicceshi,saboda shagala.



Rana ta farko da suka fara kasancewa a cikin gidan,hadda Family din Uncle Donald Suka yi masu rakiya,Basu bar gidan ba sai wuraren Ƙarfe 6 na marece,Su Sehrish sunyi murna kamar kamar me,Gidan Yayi masu kyau sosai,Atare da Junaid suka shiga zagaye gidan,Ko rabi basu yi ba suka fara gajiya a ƙarshe sai dai suka hakura,Gobe sun dasa daga inda suka tsaya,Amma fa sunsha Yawo,Security guards din dake tsaron gidan A ƙalla Sunkai mutun 20,Waɗanda ke kula da cikin gidan tundaga kan 6angaren Kitchen,Gyaran Gidan,A ƙalla sunkai Su goma sha biyar,In mutun na rayuwa acikin gidan nan ko tsinke wannan sai in yaso zai kawar dashi,musamman inya kasance malalacine shi,


Kusan 3 weeks da zamansu acikin gidan,Kullum sai sun zagaye shi,Wani lokacin Har Video Call Suke kiran su Oummansu Suna nuna masu abubuwan ban sha'awa na cikin gidan,tunda suka dawo Zama acikin gidan Omar da Sgr basu zauna ba Saboda Uban aiyukan dake jiransu,Idan suka fita da safe sai cikin dare suke shigowa cikin gidan lokacin duk sunyi bacci,Yanzu basu da wata sauran damuwa,Suna samun kyakkyawar kulawa ta ko'ina,A irin rayuwar da suke yi agidan tamkar Princesses ne in their Own Palace,Abunda suke so shi za'ayi,Masu aikin Gidan Command ɗinsu kawai suke Jira,


Yau tun safe aketa Tsuga ruwan sama,Ni'ema ta sauka ta ko'ina,yanayin weather ɗinsu gwanin ban sha'awa,Wata irin ni'imtacciyar iska mai sanyaya zuciya mai ratsa sassan jiki,irin wannan yanayin yafi da cewa da ma'aurata,


Kwantar da kanshi yayi jikin ƙopar ɗakin jikinshi na sanye da pyjamas,Ya jima atsaye yana ta yi mata magiya akan ta buɗe mashi ƙopar ɗakin ya shigo amman tayi kunnan uwar shegu dashi,Gashi yau a matse yake baya jin zai iya haƙuri wannan daren Ya wuce batare daya kar6i hakkinsa ba,A shagwa6e yake ambaton sunanta"My juliet pls,wlh ba abunda zanyi maki fira kawai nazo in tayaki,"Jahad dake ƙudundune cikin bargo ta kasa kunne tana sauraronshi,tsananin tausayinshi ne ya kamata,Amma bata jin zata iya buɗe mashi ƙopa,tsoranshi take ji saboda tasan halinshi bazai raga mata ba,Kamar yadda ya saba faɗi mata,shiyasa kullum da zarar dare yayi take kulle ƙopa don karya shigo ya addabeta,

  "I know you're hearing,pls My Juliet,wlh in baki buɗe ƙopar nan ba,Zansha poison..."Murmushi Jahad ta saki,daɗin sauraron muryashi take ji,ita kanta tana buƙatarshi amma akwai wasu dalilai dayasa take gudunshi,na farko tana fargabar kasancewa dashi,Na biyu kuma tana kunyar ta samu cikinshi,da wani ido zata kalli su babban yaya idan suka gane tana ɗauke da cikin ƙaramin ƙaninsu wanda ko School bai kammala ba,duka cikin ƴan kwanakin nan zai fara zuwa University Of Southern California,Itama kuma zata cigaba da karatun Secondary ɗinta,abunda take yima fargaba kenan,in har ta samu ciki abubuwa bazasu tafi dai dai ba,har magana sukayi da Sehrish akan tana buƙatar abunda zatasha wanda zai hanata ɗaukar ciki,Sehrish bata amince da buƙatarta ba,Sai ma shawarar da tabata akan ta bari ko first born ne ta fara yi kafin tayi planning,itadai ba haka taso ba,tayi nisa acikin zancen zucinta muryar junaid ta kuma katseta

  "Jahad,wlh idan baki buɗe ba, Zan kira Uncle awaya ince kin hanani Haƙƙina,"

  A firgice Jahad ta yaye lallausan bargon da ta lullu6a dashi,

  "You're Mad Junaid!Daddy zaka faɗa ma haka?baka da kunya ko?To ka faɗa mashi ɗin,"takai ƙarshen maganar tare da jan bargon ta lullu6e jikinta dashi,


Ta 6ata mashi rai sosai,zuƙunnawa yayi agaban ƙopar yana raira mata kuka,tana jinshi tayi banza dashi,


tsakanin part ɗinsu dana Omar dana Sgr akwai tazara,Na Junaid da Sgr Yana a Upstairs,Na Omar Yana a Downstairs,A kowane Part akwai ƙayataccen palour acikinshi,Akwai Bedrooms guda biyu masu ɗauke da toilet acikinsu,Sannan akwai kitchen a kowani part,Bayan babban kitchen ɗin dake akwai a downstairs,Wanda masu aiki ke shirya abincin gidan acikinshi,saboda tsabar kyan ginin yadda kasan da zallar glass aka yi shi,ko'ina ka kalla ɗaukar ido yake yi,


Tun Junaid yana raira mata kuka har taji yayi shiru,hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,don tasan cewa ya tafi,


Saukowa Downstairs yayi, wasu dogayen Twin stairs ne,Both left and right da kuma straight duk akwaisu ta ko'ina mutun zai iya hawa Upstairs,


Wani hamshaƙin palour ne Aljannar duniya Yaji tsadaddun furniture,Haɗaɗɗun gaske komai na cikinshi Golden Colour ne,


Jikinshi duk ya mutu haka yake tafiya,Hosana ya samu zaune saman Sofa tana kallo kamar Aljanna ita kaɗai jikinta sanye da doguwar riga tana shan ice cream,

Wata dabarace ta faɗo mashi,Ƙarasawa yayi tare da samun wuri gefenta Ya zauna,har sai da ta firgita da ta ganshi,

  "Hosana me kike yi anan"?

"Ya Omar nake jira"ta bashi amsa tare da mayar da idanuwanta kan ice cream ɗin da take sha,

  "Ina wayarki take ne"?

Ajiye robar ice cream ɗin tayi,ta ɗauko wayar dake ajiye saman Sofa hand ɗin ta miƙa mashi"Me zakayi da ita? 

  "Bani zanyi amfani da ita ba,ke nakeso kiyi amfani da ita,"

  Zuba mashi ido tayi tana sauraronshi,

  "Taimako zakiyi mun,Layin Jahad zaki kira a waya,idan ta ɗaga kiran,Ki fasa ihu kice wuta ta kama,"

Maƙe mashi kafaɗa tayi"wlh ni bazan iya ba,so kake in tayar mata da hankalinta"

Hannu yasa ya dunguri kanta"Umarni nake baki a matsayin yayanki,in kika ƙi yi mun biyayya zan faɗa ma Ya Omar ince kin raina ni,"

Yana kai ƙarshen maganarshi tace"Ae ba abunda zaiyi mun,"

  Jinjina kanshi yayi"tunda ba zakiyi mun abunda nakeso ba,bari naje na kwance karnukan gidan nan..."yakai ƙarshen maganar yana ƙoƙarin miƙewa Tsaye,a ruɗe Hosana ta ruƙo rigarshi"Dan Allah kada ka kwantosu zanyi maka abunda kakeso,"murmushi Junaid ya saki tare da komawa ya zauna,dama wayau yayi mata don yasan halinta shegen tsoron kare gareta musamman karnukan turawa jibga jibga masu gashi ajikinsu buzu buzu,


Ajiye ice cream ɗin tayi saman table ta ɗauki wayar ta dannama Jahad kira,Wayar na fara ringing Junaid yace"in ta fito kada kice mata ni nasa ki"daga haka ya miƙe a harzarce ya haye Upstairs part ɗinsu,A palour Ya 6oye Cikin Labule,


A lokacin Jahad tayi nisa acikin baccinta,wayarta ta fara ringing,cikin bacci ta zura hannunta saman gadon tana laluben wayar har Allah yasa ta cafkota,cikin bargon ta shigar da ita,daƙyar ta buɗe idanuwanta tana kallon Screen ɗin wayar,Tayi mamakin ganin kiran Hosana,Amsa kiran tayi tare da manna wayar a kunnanta,tunkafin tayi sallama ta jiyo ihun hosana tana faɗin"Wayyo Allah!Jahad wuta wuta......"a gigice Jahad tayi wurgi da bargon da ta lullu6a dashi,ta diro daga saman gadon,short gown ce a jikinta ko guiwarta bata kaiba,ta ɗaure sumar kanta da ribbom da gudun gaske Jahad ta nufi ƙopar ɗakin ta buɗe shi,ta shigo palourn duk a firgice,tana fitowa waje ta nufi downstairs tana faman baza ido don taga inda wutar ke ci duk hankalinta ya tashi,sai dai tana shigowa falon ta samu hosana zaune tana shan ice cream ɗinta ta ƙurawa faskekiyar plasma tv ido tana kallon tashar Bolly wood,A fusace Jahad ta ƙarasa tare dakai hannu ta buge robar ice cream ɗin ta faɗi ƙasa,


"Hosana uban meyasa kika kirani?don kawai ki tashi hankalina?ina wutar da kikace tana ci,"

  Tuntsirewa tayi da dariya,Hakan ba ƙaramin hasala Jahad yayi ba"Mahaukaciya kawai,bansan yaushe zakiyi hankali ba,kuma wlh a kunnan Ya Omar,Har Daddy saina kirashi a waya in faɗa mashi abunda kika yi mun,"

  Rai a6ace takai ƙarshen maganar ta juya ta nufi upstairs tana faman Jan tsoki,


Hosana dai bata tanka mata ba sai tiƙar dariya take yi kamar wata zautacciya,


Lokacin da Jahad ta koma part ɗinsu bata kawo komai aranta ba,tana shiga bedroom taja ƙopa ta rufeta hadda murɗa key,Kafin ta juya ta koma saman fankacecen gadon ta kwanta tana faman sauke ajiyar zuciya,hannu tasa ta janyo bargon ta lullu6e jikinta dashi har fuskarta,


Wani irin shu'umin murmushi Junaid yake saki,don tuni ya shigo bedroom ɗin Yana la6e cikin labulen ɗakin,hannu yasa ya zame curtain ɗin ya fito cikin sanɗa yake tafiya sai da ya fara zuwa wurin switch ya kashe hasken ɗakin tukunna ya nufi saman gadon,ta natsu cikin bargo sam bataji lokacin da ya kashe light din ba, agaban gadon ya tsaya tare da sanya hannu ya zame wandon baccin jikinshi,ya ɗebe rigar ya rage daga shi sai short,Ya haye saman gadon cikin sanɗa yake rarrafawa har yazo saitin inda jahad take ƙudundune cikin bargo,ba zato ba tsammani Taji mutun asaman jikinta,A firgice tayi wani yunƙuri ta jefar da bargon gefe ɗaya,bata iya gane wanene ba saboda duhu,Jikinta na kerma Ta shiga ambaton"La'ila ha'illa anta subhanaka inni kuntuminazzalumin!Wayyo Allah Wanenee....."hankalinta yayi mugun tashi,

Tuntsirewa yayi da dariya sosai,tana jin sautin muryar junaid Jikinta yayi la'asar,

  "Junaid ya akai ka shigo"?

Sai da ya tsagaita da yin dariyar tukunna yace"i will answer ur question tomorrow,i just need to disvirgin you right now....."wani irin tsoronshi ne ya kamata,Muryata na kerma ta soma magana"dan Allah junaid kada kayi mun haka,you know i love u ina son farin cikinka ka ƙaramin lokaci....."

Tunkafin ta kai ƙarshen maganar yayi hanzarin interrupting ɗinta"I can't wlh amatse nake Jahad,ki taimaka ki bani haɗin kai if not zan ƙwata ne..."jin haka yasa tayi yunƙurin saukowa daga saman gadon don ta gudu,Kamar yana ganinta Ya sanya hannu ya ɗamƙo gown ɗin jikinta ya janyota jikinshi gaba ɗaya ya rungumeta,fashewa tayi da matsanancin kuka tana yi mashi magiya....."

  "Ae wlh Jahad ko kukan mutuwa zakiyi saina yi abunda nayi niyya,so you wanna kill me,tun yaushe nake binki kina ja mun Class,haƙurina ya qare,its better ki daina yi mun magiya,"yana magana yana ƙoƙarin rabata da kayan jikinta,

Cikin shessheƙar kuka tace"Dan Allah Junaid...."

  "Am sorry my Juliet...."kafin ta ƙara cewa wani abu,taji saukar hannunshi asaman lallausar fatar boobs ɗinta,wata irin kasalace ta rufar mata,lokaci guda bakinta ya mutu ɗuff kakeji kanta ya fara ɗaukar chargy,gaba ɗaya ya tura kanshi cikin rigar jikinta,tashin sense tunda Allah yasa yayi grabing boobs ɗinta Yabi ya susuce ya haukace mata,tun suna daga zaune suka koma kwance,sai sukurniya yake yi mata har wani gurnani gurnani yake yi,duk ya takura kanshi acikin rigar,zafin da ta fara jine yasa ta soma kokarin rabashi da jikinta aikuwa ya fashe mata da kuka kamar jinjiri,cikin shessheƙar kuka yake faɗin"You're trying to kill me my Juliet mutuwa zanyi...."tana kuka yana kuka,ganin bazata bashi haɗin kai ba,yasa ƙarfi Ya sabule rigar jikinta tare da yin wurgi da ita,Ya tu6e short ɗinshi yayi throwing dinsa,hawa kanta yayi ta ko'ina ya kasheta a mace ta mutu yadda ko yatsanta bazata iya ɗagawa ba,wani irin ƙarfi ne yazo mashi tamkar ba junaid ɗin da ta sani ba,Sae sambatu yake yi da alama ya fara zaucewa,cikin shessheƙar kuka take Ambaton Sunanshi,"My Romeo...."sam takasa ƙarasa maganar,kuma duk intayi Calling name ɗinshi sai ya amsa mata da,My Juliet Am crazy about u,Am uncontrollable,Unstoppable,Ya haɗa uban gumi sai aiki yake yi,shessheƙar kukan da take yi ne yasa ya Haɗa bakinsu wuri ɗaya,Ya shiga bata hot kissing,tuntana mayar mashi da martani har jikinta yayi lakwas................."



*Reeshraf*


Sam ta kasa runtsawa saboda rashin dawowarsu Sgr,kusan ƙarfe 1:30 na dare,tana a tsaye agaban Glass window mai girman gaske,Ta jikin glass ɗin tana kallon yadda ruwan sama ke sauka gwanin ban sha'awa kamar ta faɗa cikin ruwan tayi wanka,ta jima tana sha'awar hakan amma tafiso suyi atare da Sgr sai ya fi daɗi,Babydoll ce ajikinta me matukar jan hankali,Pink colour sharara daƙyar ta wuce ass ɗinta,da rigar da babu duk ɗaya ne zallar net ne ajikinta,Gyaran gashin da akayi mata ba ƙaramin kyau ya ƙara mata ba,har wani lumshe ido take yi saboda iskar dake kaɗawa,ba ƙaramin daɗin yanayin take ji ba,bakowa take gani acikin idanuwanta ba face Sgr,komai nashi burgeta yake yi,miskilancinshi,murmushinshi,iya ɗaukar wankanshi,Jan ajinshi,kyakkyawar surar jikinshi da komai nashi,ta mutu akanshi sai kace ba mallakinta ba,Gayen ne ya iya Loving and Caring,kullum ƙara nutsar da ita yake yi cikin soyayyarshi,ta yadda bazata iya rayuwa batare dashi ba,aduk Lokacin da ya shirya zai tafi headquater sai taji tamkar ta fashe da kuka,daƙyar suke rabuwa dashi da hawaye akan fuskarta,Sam basa gajiya da juna,

  tana cikin wannan tunanin,ta fara jiyo jiniyar motocinsu,Wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,A hanzarce ta zuge glass door ɗin,Nan take iska ta soma busowa saman fuskarta Gashinta ya dinga reto ruwa na fallatsar mata,hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,Duk ta ƙagara ta ganshi,ba halin yin hakan saboda akwai tazara sosai,Slowly motocinsu suka shararo da matsakaicin gudu ta babban gate ɗin gidan suka shigo a jere,Motar Sgr da Motar Omar,gaba da baya motocin Security ne,uku gaba, uku baya,masu ɗauke da fusatattun Sojoji,


  Ƙura ido Sehrish tayi tana son ta leƙoshi ruwa ya hanata buɗe idanuwanta dakyau,bayan sunyi parking ɗin motocin,A hanzarce Security soldiers ɗinnan suka diro daga saman motocinsu suka ƙarasa tare da buɗe masu tasu,A hankali ya zuro ƙafarshi me sanye da army shoe,saukowa yayi daga cikin motan Jikinshi sanye da kaki,Daga sama ya ɗaura military Coat wadda takai mashi har ƙasan guiwarshi,kanshi ya sanya Hula ta kakinsu,Yayin da sumar kanshi ke ɗaure ya saketa har tsakiyar bayanshi,Fitowa Omar yayi daga cikin motarshi,shima yana acikin kakinsa,Biyu daga cikin Soldiers ɗin hannunsu na ruƙe da Lema sunyi masu rumfa asaman kansu don kada ruwa ya jiƙasu,sallama suka yi da Major da Amstrong kafin Omar ya ruƙo hannun Sgr acikin nashi kamar yadda suka saba,A haka suka nufi cikin gidan,A bakin Main palour ɗin Soldiers ɗin suka Juya,Suna shiga palourn da gudun gaske Hosana ta miƙe ta nufo su har tana tuntu6e zata faɗi,da sauri Omar ya ruƙota a jikinshi,Shafa Curly hair ɗinta yayi"My Hosana,me kike yi bakiyi bacci ba?

Ashagwa6e ta soma magana"kai nake jira Ya omar,"

Murmushi yasaki tare da kallon Sgr wanda tuni yayi gaba a hanzarce yake tafiya don yayi missing ɗinta Over,

Hannu yasa tare da tallabo fuskarta ya manna mata kiss asaman forehead ɗinta"Nayi missing ɗinki sosai hosanata,Ina fata kin ci abincinki"?

  "Ni banci komai ba,kai nake jira muci atare,"sarai yasan cewa ƙarya take yi mashi saboda bata da Jumurin yunwa,Duk da haka yaji daɗin maganarta,its Okey,Mu je ki tayani cire kaya,in yi wanka in na fito sai muci atare ko"?ɗaga mashi kai tayi alamar eh,ruƙo hannunta yayi tare da janta suka nufi part ɗinsu,sae murna takeyi Ya omar ɗinta ya dawo,


Lokacin da ya shiga part ɗinsu tun abakin door din palour yayi sallama ya soma ƙwala mata kira"Reesh!My baby....'dama jiran shigowarshi take yi,yana shigowa bedroom ɗin ta faɗa mashi asaman wide chest ɗinshi,wani irin sanyine ya ratsa zuciyarshi,a hankali ya shiga furta"Alhamdulillah Ya Allah,"ba ƙaramin daɗi yake ji ba aduk lokacin da ya dawo agajiye daga wurin aiki,Sehrish ta faɗa mashi a jikinshi,tamkar maƙoshine dake bushe a yanayi na buƙatar ruwa,yafi buƙatarta fiye da komai,a hankali ya sanya hannunshi asaman sumar kanta yana shafa lallausar gashin kanta,

  kashe murya tayi tare da cewa"Welcome back,My own husband,nagode ma Allah daya dawo mun dakai Lafiya,I really missed you,na yini acikin duhu,amma yanzu haske ya haskaka idanuwana da zuciyata,"

  daɗaɗan kalamanta ba ƙaramin tasiri suke yi akanshi ba,

    Duƙar da kanshi yayi zuwa saitin fuskarta,bayan ya dago da ita,irin gaisuwar da suka saba ma junansu,haɗe bakinsu yayi wuri guda a hankali yake kissing ɗinta,yayin da idanuwansu ke kallon cikin na juna,tamkar su haɗiye juna haka suke ji,ya jima before ya zare tongue ɗinsa daga cikin bakinta,ɗaukarta yayi kamar ƴar baby,Ya ƙarasa da ita gaban dressing mirror,ya juyo da front chair ɗin mirrorn tukunna ya ɗaura sehrish asaman kujerar yadda tsayinsu zaizo ɗaya,haka kullum sukeyi saboda ta taimaka mashi wurin cire kayanshi,Wannan ma wani sabon salon soyayyarne,Sae faman sakin murmushi sukeyi,

  "Ya gajiyar aiki,"tayi maganar tare dakai hannu ta zame coat ɗin dake ajikinshi,

   "Babu gajiya atare dani idan har ina tunaninki acikin zuciyata,Reesh kece ƙwarin guiwar da nake dashi,"

Murmushi tasaki har dimple ɗinta ya lotsa,

  "Yaushe zamuje Honeymoon"?

"Na baki za6i,kiyi choosing countries ɗin da kikeso muje,cos ur choice is mine,"

  Wani irin daɗi take ji kamar kamar me,zame vest ɗin jikinshi tayi ya rage saura army trouser dinshi,saukowa tayi daga saman kujerar ta zuƙunna ƙasa,ta sanya dukkan hannayenta tare da zare igiyoyin takalmin ƙafarshi ta ciresu,tare da safar,kafin ta miƙe ta zame belt ɗin wandonshi,daga shi sai short fari ta bari ajikinshi,tana kammalawa ta tattara kayan da ta cire mashi ta kaisu laundry,tana dawowa ya ɗauketa asaman kafadarshi ya wuce toilet da ita,kamar yadda suka saba,


Tun acikin bathtub suka fara having sex,almost more than 30 mins suna acikin toilet din,kafin ya fito ɗauke da ita a hannunshi,suna sanye da towel,komai atare suke yin shi,agaban dressing mirror ya sauketa saman kujerar,Sai daya bi ko'ina na jikinta ya shafe shi da cream dinsu,itama ta shafa mashi ajikinshi,hand dryer suka dauko suka fara busar ma junansu gashi,afterward suka bar wurin mirror din suka koma can cikin ɗakin da yake yana da faɗi sosai,wurin closet ɗinsu tanƙamemen gaske mai ɗauke da sliding door,ta cikin glass din kana iya hango jerin kayansu kamar a company,shaf shaf suka shirya junansu cikin pyjamas blue colour,yadda kasan tagwaye,hatta kayan sawarsu iri ɗayane,


"Me kake son ci in kawo maka"tayi maganar tana kallonshi,

  "Bana jin yunwa,"

Bubbuga ƙafarta tayi ashagwa6e tace"ni ban yadda ba Ya rafayet,wlh bakasan cin abinci,kana so kaga angry face ɗina ko,"

  Natsuwa yayi yana kallonta,idan tayi shagwa6a gaba ɗaya kashe mashi jiki takeyi,

   Tamkar zatayi kuka taci gaba da cewa"banfa ci komai ba Saboda kai,saboda nafi so muci atare,ina baka abaki kana baniii"ta ɗan ja maganar daga ƙarshe cikin shagwa6a,

  Murmushi kawai yake saki yana kallonta,

  Ruƙo hannunshi tayi"pls mijina nakaina,kafaɗamun me kakeso insa akawo mana,idan ma kanaso ni in girka maka zan shiga kitchen ne,"tana magana tana wasa da yatsun hannunshi,

Allah kaɗai yasan yadda yake jinta acikin zuciyarshi,ta iya soyayya,tasan takan miji,tunda ya kafeta da sexy blue eyes ɗinsa bai ko ƙyaftasu ba,

  Bubbuga ƙafafuwanta ta ƙara yi tare da faɗawa saman ƙirjinshi,tana cigaba da yi mashi shagwa6a,

Cikin sanyin murya ya furta"its okey,zanci,"ajiyar zuciya ta sauke,ta ɗago daga jikinshi,juyawa tayi da sauri ta ɗauko wayarta dake ajiye saman pillow,Call log ta shiga ɗaya daga cikin layin masu aikin gidan ta kira,ta basu umarnin su kawo masu dinner a part ɗinsu,bayan ta ajiye wayar ta ɗan juya tare da kallonshi har ya kishingiɗa saman gadon,

    "Am sorry,naso ace ni na girka maka abinci dakaina kamar yadda nasaba,don banason kana cin abincin masu aiki,"

  "I don't want u to Cook for me,duk wani aikin wahala banaso kinayi,ɗawainiya ma da kike yi dani ya isa basai kin ƙara da wani abu ba,duk kin shagwa6ani,ko Office nake kamar zautacce haka nake yini ina murmushi,kowa mamaki yake yi,wai Sgr ne da murmushi,"

  Natsuwa tayi tana sauraronshi har yakai ƙarshen maganar,kafin ta bashi amsa wayarta ta soma ringing,da sauri tayi picking,Amsawa tayi da "okey u can leave,"daga haka ta ajiye wayar,

   Moving tayi zuwa saitin fuskarshi"food is ready,in kawo maka anan ko a palour zamu ci,"

  Saukowa yayi daga saman gadon ya ruko hannunta suka nufi palourn,Dining area suka tunkara hannunsu acikin na juna,sai da suka isa sannan ta saki hannunshi,suka zauna suna fuskantar juna,


   Medium size table ne cike yake maƙil da kayan abinci,bayan ta kammala yin serving ɗinsu,ta miƙa mashi spoon ita ma ta ɗauka,gwanin ban shawa'a,Tana bashi abaki yana bata ahaka suke cin abincin,yayin da idanuwansu ke kallon cikin na juna,ganin ta dakata da cin abincin yasa shi kallonta,cikin kulawa yace"Reesh...lafiya,"ƙamshin fried fish ɗin dake a saman plate ne ya haddasa mata jin tashin zuciya,wani irin yunƙurin amai ne yazo mata a hanzarce ta miƙe da gudun gaske ta nufi bedroom ɗinsu,A ruɗe Sgr yabi bayanta,a sukwane ya faɗa ɗakin shigarshi keda wuya yaga ta shige toilet,A gaban sink ta tsaya a galabaice ta shiga ƙwarara aman,komai da ta ci sai da ta zubar dashi,

  "Reesh..."cikin sanyin murya ya ambaci sunanta,a yayin da yake shigowa toilet ɗin,ƙarasawa yayi gabanta a lokacin ta kunna tap tana kuskure bakinta,ɗagowa tayi cikin shessheƙar kuka ta soma magana"Ya Rafayet bansan meke damuna ba,wani irin tashin zuciya nake ji,komai na ci saina amayar dashi....."ashagwa6e take magana hawaye jaga jaga akan fuskarta,maimakon taga tashin hankali akan fuskarshi,sae taga yana murmushi,aruɗe tace"Ya rafayet,baka ji abunda nace bane....."

  Hannu yasa tare da janyota jikinshi yayi hugging ɗinta yana ambaton"Alhamdulillah ya Allah for the blessing....."tuni idanuwanshi sun ciko da kwallar farin ciki,lamo tayi ajikinshi sam bata fuskanci me yake nufi ba,

  Shafa sumar kanta yayi"thank u Reesh for everthing....."ɗaukarta yayi asaman kafaɗarshi ya fito da ita cikin ɗakin asaman bed ya kwantar da ita,zuba mashi ido tayi tana kallonshi,Gabas Ya kalla yayi Sujjada,abun ya ɗaure mata kai,ɗagowa yayi tare da ɗaga hannayenshi sama yana addu'a cikin harshen Larabci,zubawa sarautar Allah ido tayi,godiya yayi ga Allah subhanahu wata'ala,yayi mata addu'a ita kanta saboda jin daɗin wannan abun farin cikin da ya sameshi,bayan ya kammala addu'ar ya miƙe tsaye a hanzarce ya nufi hanyar fita daga ɗakin,

  Fashewa tayi da matsanancin kuka tana bubbuga ƙafarta saman mattress"Ya rafayet don't leave me alone i really need u close to me..."fasa fita yayi ya hakura zuwa gobe zaiyi mata pregnancy test don ya tabbatar da in cikin ne,duk da yaji aranshi cewa reesh ɗinsa tana ɗauke da cikinshi,hawa saman gadon yayi tare da janyota jikinshi,sosai ta shige mashi kamar zata koma ciki,hannunshi ya sanya abayanta yana shafa mata shi,saboda tayi saurin yin bacci,

  "Ya Rafayet"ta ambaci sunanshi,

"Reesh menene"?

"I love u so much...."zura hannunshi yayi cikin sumar kanta"I love u too My own wife.....". 

  Murmushi ta saki wani irin daɗi take ji,

  "Inajin sanyi,"jin haka yasa shi miƙewa ya saukko daga saman gadon ya kunna masu room heater wani irin ɗumi me daɗi ya gauraye dakin,still ruwan saman na sauka sosai,komawa yayi saman gadon ya kuma rungumota jikinshi,kafin yaja lallausan bargonsu ya lullu6esu aciki,moving yaci gaba da yi da hannunshi cikin rigarta yana shafa ƙirjinta,daɗin hakan yake ji sosai,runtse idanuwanshi yayi sosai yana cizon lips ɗinsa,dariya Sehrish tasa,hannunta na acikin trouser dinshi,numfashinshi sama sama ya soma faɗin"Reesh keep doing it,you're giving me fire........"suna cikin bama junansu nishaɗi bacci yayi awon gaba dasu,a ƙanƙame da juna,irin sosai ɗinan,



Sam ya kasa runtsawa zaune yake asaman katafaren gadonsu,Ya jingina bayanshi jikin headboard ɗin,daga shi sai short ajikinshi,Hosana na kwance gefenshi,hannunta ruƙe da wayarshi sai buga game take yi,aduk lokacin daya kalleta sai yaji tamkar bazai haƙura ba,a matse yake yana tsananin buƙatarta amma tausayinta da yake ji ya hana hakan,gani yake tamkar zai cutar da itane,gashi kullum ƙara kyau take yi,ko'ina na jikinta tubarkalla masha Allah,

  Gyaran murya ya ɗan yi mata"bakya jin bacci ne,"

  "Kai nake jira mu kwanta,naga ka kalli sama kana ta tunani,"

  Hannu yasa ya kar6e wayarshi dake hannunta,ya kasheta kafin ya ɗaurata saman drawer,

  "Hosana let's sleep yayi maganar tare da janyota jikinshi ya rungumeta,ko ba komai zai rage zafi ahaka,

  "Ya Omar,"ta ambaci sunanshi,

"Na'am menene"?

"Har yanzu shiru kakeji kamar An yiwa sama daƙuwa"

A ɗan ruɗe yace"me kike nufi"?

  "Cikin mana,naga an ɗaura auran tuntuni amma har yanzu ni bansamu cikin ba",hankalinta kwance take magana,

"Kinaso ne"?

A ƙagare tace"Eh,inaso,"duk a tunaninshi hosana tasan me take nufi,hakan yasa shi tunanin ko dai ya jarabata,wata'ƙil ma ta bashi haɗin kai tunda tanaso,

A hankali ya sanya hannu yana nannaɗe rigar jikinta,sae daya janyota har saman cikinta,sae faman sambatu take yi mashi sam bata ankara ba,hannu ya kai zai zame pant ɗin jikinta ashe bata sanya ba,yana shafa fatar wurin Karaf ta damƙi hannunshi,yayi wuri wuri da ido,waro ido Hosana tayi hankali atashe tace"Lalala!Ya Omar me hannunka yake yi anan?

  A gigice Ya sanya hannu ya rufe bata bakinta"Shut up,banason tsiwa,Gyara maki rigar zanyi,"a ƙule yayi maganar,ya sanya hannu ya gyara mata rigar,gani yayi ta miƙe zaune tana ƙoƙarin sauka daga saman gadon

  "Where are u going,?yayi tambayar yana kallonta,

Fuskarta a daure tace"palour zanje in kwana,"abun ya ɗaure mashi kai,tunkafin ma ta tabbatar da abunda zai aiwatar har ta fara gudunshi,

  Cikin sanyin murya yace"Look hosana,it was a mistake bazan ƙara ba,"girgiza kai tayi "a'a Ni dai ƙwara na kwana a palour,kada Allah ya kamani,"ta sauko daga saman gadon,ranshi ya 6aci,

  "Karki kuskura ki fita daga ɗakin nan,ranki zai 6aci,dawo ki kwanta,"

  Bubbuga ƙafarta tayi"Wlh sai naje,"zuba mata ido yayi yana kallonta,wato da ta bubbuga ƙafarta gaba ɗaya jikinta ke rawa musamman ƙirjinta dake acike,yana hangensu ta cikin rigar jikinta,


Lallashinta ya soma yi"pls hosana bazan ƙara ba,ki dawo ki kwanta,"maƙe mashi kafaɗa tayi,a ƙarshe ma ta nufi palour ta kwanta saman sofa,

Runtse idanuwanshi yayi sam baiso hakan ba,tabbas in ya biye ma Hosana ba ranar da zata bashi haƙƙinshi ne,


Wani irin raɗaɗi ya dinga ji acan ƙasan mararshi,kifa kanshi yayi jikin pillow yana mayar da numfashi kamar wanda yayi gudu,sam babu sauƙi ta ko'ina,kasa jurewa yayi ya yanke shawarar tunkararta don ya lalla6ata tunda tana sonshi,may be ta amince mashi,

  Saukowa yayi daga saman gadon ya shigo palourn kwance ya sameta idanuwanta a buɗe suke,tana yin arba dashi ta zabura ta miƙe zaune,bai hau saman kujerar ba,zuƙunnawa yayi tare da dafa kujerar,

  "Why hosana?banace maki kuskure bane?ɗaure fuska tayi batare da tace komai ba,

   Cigaba da magana yayi"koda ace da gangan nayi bazaki iya yimun afuwa ba"?wani irin kallo take jifarshi dashi,

  "Nifa mijinki ne Hosana,ba zaki iya taimaka mun ba,ina matuƙar buƙatarki pls"

  Ya marairaice mata fuska,don taji tausayinshi,

  "Ni ba ƴar iska bace Ya Omar,fyaɗe kakeso kayi mun,ae nagane," ae yana jin haka ya ƙarasa zama ya lanƙwashe kafarshi,cike da takaici yake kallonta,tunawa yayi da maganar Aunty azeema tace ta koya mata komai,

  Tausasa muryarshi yayi"My hosana Mommy azeema bata koya maki ba"?

  Yatsina fuskata tayi"Me"?tayi tambayar tana kallonshi,

  "I mean..dame dame ta koya maki,"?

"Ni bata koya mun komai ba,idan ma ta koya mun na manta...."a hasale tayi maganar,

  "Hosana ina soyayyar da kikeyi mun ne"?shiru tayi bata tanka mashi ba,

  "Ba kince kinason ki samu ciki ba"?da sauri ta ɗaga mashi kai,

  "In har ban ta6aki ba bazaki ta6a samunshi ba,kefa da kanki kika ce kaza sai da zakara take haihuwa,you know i won't cheat u hosana,zanyi maki komai a hankali,"lallashinta ya shiga yi harta ɗan sauko,

   "Amma Ya omar kada ka ta6a ni,zanbi ka mu kwanta,ka kalli hagu in kalli dama,ka amince"?

  Jinjina mata kai yayi"Na amince"dama burinshi ta shiga daga ciki,

  "In ɗauke ki"

  "A'a zan tafi da ƙafafuna,"takai ƙarshen maganar tare da miƙewa ta nufi cikin ɗakin,a hanzarce ya miƙe yabi bayanta,suna shiga Ya datse ƙopar,Saman gadon ta haye ta kwanta,takawa yayi wurin switch ya kashe hasken ɗakin kafin ya koma gefen gadon ya kunna fitila ta ɗan haskaka ɗakin,


  Hayewa saman gadon yayi kamar yadda ta umarce shi,ya kalli 6angaren hagu,sam ya kasa runtsawa,after some munites bacci ya ɗauki hosana,tunda yaji ta daina mutsu mutsu ya tabbatar da bacci ya ɗauketa,lalla6awa yayi a hankali ya juyo saitin inda take tana bacci tayi ɗai ɗai asaman gadon,


Natsuwa yayi yana kallon kyakkyawar fuskarta,ba ƙaramin cutuwa yake yi ba,rayuwa da suke yi aɗaki ɗaya,cikin sanyin murya ya furta"Am sorry hosana,haƙurina ya ƙare,bazan iya jurewa ba,ina cutuwa sosai,"Addu'ar saduwa da iyali ya farayi kafin a hankali ya kai hannunshi ya ruƙo rigar jikinta,gaba ɗaya ya yaye rigar har zuwa neck ɗinta,sai da dubara ya samu ya rabata da kayan jikinta,hankalinshi ne yayi mugun tashi,gaba ɗaya ya susuce ya ruɗe yayin da yake kallon kyakkyawar surar jikinta mai matuƙar jan hankali,Cikin fitar hayyaci Ya afka ma dukiyar fulaninta,bada wasa ba,kusan zaucewa Omar yayi,zafin Nipples ɗinta ne ya farkar da ita,a gigice ta fasa ƙara tana faɗin"Wayyo Allah!Na shiga uku!Na bani!Na lallace....."la66ansa na kerma yashiga fadin"its me hosana kada ki katse mun jin daɗina......"kusan dambe sukayi da ita saman gadon,bugu ta dinga kaimashi abayanshi,amma ina yayi nisan kiwo,Ya tsunduma tsulundum,kuka ta dinga yi tana bugunshi kamar ƴar wrestling,

  A ƙarshe da ta rikice ta fara sambatun kiransu Sehrish Don su agaza mata,sunan Daddy da Oumma dasu Abba dasu gwaggon katsina dake a Nigeria duk saida hosana ta ambaci sunansu a jere,Ko irin sanyin jikinnan kasala ta baibaye mutun hosana batayi ba,bakinta yaƙi mutuwa,

  Cikin shessheƙar kuka take faɗin"Ya Omar i hate You!" baima san tana yi ba,don ya rigada ya zauce,A ƙarshe da abu yakai abu ya tu6e short ɗin jikinshi,Me kankat kenan,tasha kuka kamar ranta zai fita,tayi masifar tayi bala'en har ta sume mashi,wata irin zufa ta wankesu,duk da irin sanyin da akeyi ga ruwan saman da ake tsalawa,wata irin kasalace ta rufeshi,A lokacin da ya kammala yin Disvirgin dinta,baisan inda kanshi yake ba,sam baya a hayyacinsa,wani irin yanayi mara misaltuwa shi kanshi bazai iya tantance awace duniya yake ba,


*Boss Bature*


Wani irin tsami jikinta yayi mata,tamkar an jibga mata kayan wanki,cikin shessheƙar kuka take ambaton sunanshi"My Romeo,"har cikin kunnanshi yake jin kiran sunan domin kuwa yana a rungume da ita,yunƙurawa yayi tare da miƙewa zaune yasa hannuwanshi ya ɗauro Jahad saman laps ɗinshi,

  "Am really sorry......."

Girgiza mashi kai tayi"Jikina babu daɗi,ko'ina zafi,ka taimaka mun,"sam baisan me zaiyi mata ba,

  "Inason shiga toilet,ƙafafuna basu iya ɗaukata,"tana magana hawaye na wanke fuskarta,tsananin tausayinta ne ya kamashi,yayi tunanin zata rufeshi da faɗa,kota bijiremashi amma sae yaga akasin hakan roƙonshi ma takeyi akan ya taimaka mata,ganin tana kuka yasa shima ya fashe mata da kuka"Bansan ya zanyi ba jahad,bari na kira Abba in faɗa mashi"dayake shi ya koya mashi komai,

  A rikice ta dakatar dashi"Ni bance ka kira kowa ba,ka ɗaukeni ka kai ni toilet,Ni nasan me zanyi,"shi kanshi jikinshi ba ƙarfi wani irin zazza6ine ya rufeshi,saukowa yayi daga saman gadon,da ƙarfinshi na ƙarshe ya kinkimi Jahad yana faɗin"Ash!wash"yana tafiya yana tangal tangal zai faɗi a haka har ya shige toilet da ita,da taimakonshi ta gasa jikinta sosai da ruwan ɗumi,tallabota yayi suka fito daga toilet ɗin ya ɗaura mata towel,wuri ta samu saman front chair na mirror ta zauna tana faman sauke ajiyar zuciya,jikinta sae kerma yakeyi kamar wadda sanyi ya kama 

Naɗe bedsheet din yayi ya ɗaukeshi,Ya dauko masu wani sabo ya shimfiɗashi,Kayan sanyi ya ɗauko mata farare na saƙa,Ya taimaka mata ta sanyasu ajikinta,sannan ya kamo hannunta ya taimaka mata ta kwanta saman gadon,Hada jan bargo ya lullu6e mata jikinta,

  Zuƙunnowa yayi saitin fuskarta"My Juliet am sorry,"yayi maganar tare da kama kunnuwanshi,idanuwanta cike tab da kwalla ta ɗago tana kallonshi,maimakon taji haushinshi,saima tsananin son shi da ƙaunarshi da ta ji,lumshe idanuwanta tayi a hankali kafin ta furta"kaje ka tsarkake jikinka,"amsa mata yayi da toh,ya miƙe a hanzarce ya nufi toilet,har ya kusa shiga ta kuma cewa"Kasan me zakayi"?

  "Eh Abba ya koya mun,"cizon le6enta tayi tare da cewa"Ya kyauta,"ƙarasa shiga kewayen yayi,tare da jan ƙopa ya rufe,


Baccine ya ɗauketa mai daɗin gaske,sama sama taji motsinshi a ɗakin,Shirin zuwa masallaci ya yi,jallabiya ya sanya ajikinshi,sai da ya fara zuwa saman gadon ya manna mata kiss asaman fuskarta tukunna ya fuce daga ɗakin,


Lokacin da ya sauko downstairs haɗuwa sukayi da Sgr yana saukowa a gaggauce Shima jallabiyarce a jikinshi,da sauri Junaid ya ƙarasa ya rungumeshi,shafa sumar kanshi yayi"how are u my boy,hope u slept well,"

  "Am fine,Nayi missing dinka,Jiya bamu haɗu ba,"

   "Naji jikinka da zafi?Lafiyarka kuwa,"yayi maganar hannunshi akan wuyan junaid,"

  ɗagowa yayi daga jikinshi"Lafiyata Lou,".  

"Anya,idan muka dawo zan dubaka,"

  Ya ruƙo hannunshi suka nufi part ɗin Omar,a ƙopar palourn suka tsaya,Ya zura hannu aljihun jallabiyarshi Ya ɗauko wayarshi,Layin Omar ya kira,Tayi ringing har ta gaji ta katse,sake kira yayi almost 3 times amma ba'ayi picking ba,Ga time ɗin salla na shirin ƙure masu,shiga palourn suka yi atare da Junaid,A ƙopar shiga bedroom ɗin suka tsaya,bubbuga ƙopar yayi ba'a buɗe ba,duk hankalinsu ya tashi,Text message ne ya shigo wayar Sgr,duba saƙon yayi

  Bayan ya kammala karantawa Ya kalli Junaid,

   "Ka jiramu a main palour,"Amsa mashi yayi da toh kafin ya fuce,knocking ya kuma yi"Omar zo ka buɗe man ƙopa,"baijima da yin maganar ba Omar ya buɗe mashi ƙopar,daga shi sai short ajikinshi duk yabi ya ruɗe kusan irin haukan da Sgr yayi,bai 6oye mashi komai ba game da abunda ya faru,

Layin Dr ɗinsu ta cikin gida ya kira,dama saboda Su Jahad suka ajiyeta koda ace basu kusa in wani bai lafiya zata iya duba lafiyarshi tunda suna da Medical room acikin gidan,"

  shaf shaf Omar ya shiga toilet ya tsarkake jikinshi ya sanya Jallabiya,itama Hosana ya gyara mata jikinta,ya sanya mata rigarta,jim kaɗan Dr Jonet ta ƙaraso,already tazo da duk wani abu da zatayi amfani dashi wurin treatment ɗinta,daƙyar Sgr  ya shawo kan Omar suka fito,sun bar Dr aciki tana dubata,Lokacin da suka sauko palour Junaid suka samu ya gyara kwanciyarshi saman 3 seater sai bacci yake yi,amma da alama baccin nashi baiyi nisa ba,tada shi yayi suka fito waje,Acikin motocinsu suka shiga,kafin suka nufi masallaci,




 [3/19, 9:44 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*




*💃LAIFIN DAƊI ƘAREWA💃*




Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*



*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




Zazzafar haja daga Minjibir ventures,Ina masu buƙatar siyan kayan sallah Kada ku bari a baku Lafiya,Ga kaya na kece raini Na shiga tsara,Koda kudinka sai da rabonka,Kadan daga cikin abubuwan da muke siyarwa akwai Lace 

Veils

Atamfa

Shoes

Bags


Address

Hotoro ladanai  kan titin ring road

Chat 09126570345

Call 09136122503 saikun Zo💃💃💃💃





Tun bayan sallar Asuba sehrish ta koma bacci,ringing ɗin wayarta ya tayar da ita,lalubo wayar tayi ta duba me kiran nata,Murmushi tasaki ganin Sunan Oummansu Ya bayyana,Picking tayi ta kara wayar a kunnanta"Oumma ina kwana,kun tashi Lafiya,"ta yunƙura ta miƙe daga zaune,

On the other hand Oumma tace"Lafiyalou rishina,ina fata kuna cikin ƙoshin Lafiya,"

  "Alhamdulillah yanzu ma na tashi daga bacci,"_

"An samu hutu ko?Ae naga hotonanku,kunyi kyau sosai hutu ya zauna maku,"

Murmushi sehrish tasaki"Ina Daddy Oumma,nayi missing ɗinku sosai"

  "Ya shiga toilet,nima nayi kewarku sosai,"

  "Yaushe zaku zo?

"Kinji ki da wata magana,daliline kawai zai kawo munan kinsan me nake nufi,"

  Murmushi sehrish tasaki"Allah ya kawo dalilin nan Oumma,i will keep praying har sai dalilin nan yazo,"

  tana jiyo dariyar Oummansu"ina Jahad ina Hosana,duk nayi trying Layinsu ba'a ɗaga ba,"

   "Ae yanzu basu isa su farka daga bacci ba,nima ringing ɗin wayarki ne ya tashe ni,kuma naji daɗi sosai,"

  "Ina surukin nawa yake"?

"Baidawo ba,tunda suka tafi sallar Asuba,Amma nasan suna akan hanya,"

  "Ki gashe mun dashi"

"Zaiji insha Allah,"

Shiru suka ɗan yi kafin Oumma ta kuma cewa"Bansani ba,kowani ya faɗa maki,"

  A ƙagare tace"Mekenan Oumma?Banyi waya da kowa ba,babu wanda ya faɗamun"

   "To Albishirinki".

"Goro,"ta faɗi tana murmushi,

  "Surukarki ta musulunta"waro ido waje Sehrish tayi,tsabar farin ciki yasa ta duro daga saman gadon ta daka tsalle bakinta yaƙi rufuwa"wayyo Allah Oumma,Mommy ta musulunta"?

  Dariya abu tayi"Bayan tafiyarku,ta kar6i addinin musulunci,Nima a wurin Daddynku naji,Yanzu tace batason kowa ya dinga kiranta da Alexandra,Sunanta FATIMA,"wani irin farin cikine Ya lullu6e sehrish,

  "Amma na tayata Murna,baki ji irin farin cikin da nake ciki ba,"

  "Albishir ɗin bai ƙare ba,Akwai saura,"

  A ƙagare sehrish tace"Ina sauraranki Oumma,"

  "Ina wannan yayan naku"?aɗan ruɗe sehrish tace"Wanne daga ciki"?

   "Ɗan wurin Azmee"A ruɗe Sehrish tace"Ya haroon?Ya dawo?an ganshi?bari na maida Video Call,nan take ta canza kiran zuwa Video,A gaban window ta tsaya ta ɗaga wayar suna kallon juna,kwance Oummansu take asaman gadon dakinta na Gidan Abusufyan wanda su Jahad suka ta6a yin rayuwa aciki,jikinta sanye da kayan bacci,Hutu ya zauna mata yadda kasan baturiya dama jawur take,ta saki gashin kanta gefe da gefe,

  Sai faman murmushi suke sakarwa Juna,

  "Oumma faɗamun Ya Haroon Ya dawo"?

Jinjina mata kai Oumma tayi"Ya dawo tare da wannan yayan naku,Brigadier general Abuhaisam,Ashe Lokacin da Azmee taba shi kuɗi akan ya gudu yabar ƙasar saboda gudun kada a Yanke mashi hukunci,sun shirya mashi komai na tafiya,Shi kuma yaji bazai iya tafiya ba,Saboda Yana son Ya nemi yafiyarsu Abba,maimakon ya tafi sai ya wuce Jos gidan wani abokinshi ya fara sauka yayi jinya,kafin Bayan wani lokaci yaje gidan shi Abuhaisam din cikin mawuyacin hali,bai 6oye mashi komai ba game da abunda ya faru ya nuna masa yayi nadama,Haisam ya taimakeshi sosai don abunda haroon din bai sani ba shine, lokacin an riga anga Junaid kuma alokacin duk sun san cewa abunda haroon din yake yi ba yin kanshi bane,Shiya kaishi Asibiti yayi jinya sosai,Kafin aka sallamesu,a gidanshi yake kwana,Ko Lokacin da Irfan Ya rasu daya zo gida Baisanar da kowa game da haroon ba,har yazo Shagalin bikinsu Yousouf,duk Haroon Na'a wurinshi,Sai da yaji Labarin Abba na nemanshi,Tukunna Ya nuna yana son dawowa gida,Cikin satin nan suka yi mana zuwan bazata,baki ga yadda ya canza ba,Babu ruwanshi bawan Allah,


Tuni idanuwan Sehrish sun cicciko tab da ƙwalla,

  "Allah sarki Ya haroon,Na tausaya mashi sosai,Aunty azmee zata ji daɗi sosai,idan taji labarin dawowarshi,"

  "Daddynku ya sanar dani cewa Zasu rakashi can prison ɗin don ya gana da ita,"

  "Naji daɗi sosai,Oumma ki gaishe mun dashi,"

  "Aikuwa dai yana ta tambayarku,musamman ke,"

"Allah sarki,idan Allah ya kawo dalilin da zaku zo nan,Dan Allah atattaro kowa da kowa yazo,"

  Fashewa abu tayi da dariya,daga ita har sehrish ɗin kunya suke ji,Dalilin da suke nufi bakomai bane face Ciki,In sun haihu lokacin suna zasu zo America,"

  "Kunyi waya Da mommy azeema ne"?girgiza kai sehrish tayi"a'a,tun jiya dai Da rana munyi waya da ita,

  Oumma tace"Yau da safe ta Koma Lagos,Mijinta ya dawo,"

  Waro ido Sehrish tayi irin mamakin nan"Dama Mommy Azeema tana da aure?" 

 Dariya abu tayi"Tana da aure mana,Mijinta business man ne,A dubai yake da zama,atare suke kasuwanci dashi,koda muka Je Yi maku siyayyan kayan lefenku,A gidanshi dake acan muka sauka,Mutumin kirkine Kamar ita haka yake,"

  Murmushi sehrish tasaki"Allah Sarki,gaskiya zanso na ganshi mu haɗu,"

 

  Sun jima Suna waya har Daddynsu ya fito daga toilet ya kar6i wayar suka gaisa da Sehrish,kafin tayi masu sallama,tana kokarin ajiye wayar gaban mirror,Taji shigowarshi ɗakin,juyawa tayi tana kallonshi,

  "Ya rafayet"ƙarasawa yayi tare da janyota jikinshi yayi hugging ɗinta,bayan ya manna mata kiss a gefen fuskarta holding hands dinta yayi"inaso kije ki duba jikin Hosana,"aruɗe tace"me ya sameta"?

  "Ba wani abu bane,she's not feeling well,inaso ki ɗan lallasheta,"Jinjina mashi kai tayi,a hanzarce ta fuce daga ɗakin,Side bed ya zauna,tare da curo wayarshi ya kira layin Abbansu don su gaisa kamar yadda yasaba,duk safiyar Allah sai ya kira Iyayenshi da Surukanshi a waya ya gaishe dasu,



Sehrish na shiga part ɗinsu,suka ci karo da doctor jonet tana ƙoƙarin fita,nan fa hankalinta ya ƙara tashi,Daƙyar ta tsaya suka gaisa kafin ta nufi bedroom ɗin,

Faɗawa ɗakin tayi da sallama abakinta,A kwance ta samu hosana jikinta lullu6e da bedsheet,saman drawer sirinjin allura ne,hada magunguna,

  Omar na zaune gefen gadon,fuskarshi ɗauke da matsananciyar damuwa,baisan da wani ido zai kalli hosana ba,Yadda ta ƙullaceshi aranta zaiyi wuya ya fahimtar da ita,don daƙyar aka dubata tana ihu tana ɗura mashi ashar,dole saida akayi mata allurar bacci tukunna ta lafa,

    "Ina kwana Ya omar"juyowa yayi tare da kallonta cikin sanyin murya Ya amsa mata"Lafiya lou Sehrish,"

  "Ya mai jiki"?

  "da sauƙi,Anyi mata allurar bacci ne,"miƙewa yayi tare da nuna mata gefen gadon"Ki zauna kusa da ita,"ƙarasa shiga cikin ɗakin tayi a gefen gadon ta zauna,Shi kuma ya koma palour,

   Bin fuskar hosana tayi da kallo,lokaci guda ta gane meya faru,murmushi ta ɗan saki"Su Hosana an girma,"


Lokacin da Junaid ya koma bedroom ɗinsu,Still Jahad tana ƙudundune cikin bargo tana bacci,hawa saman gadon yayi Ya zame bargon ya shiga ciki, janyota yayi jikinshi ya rungumeta sosai,Zafin da ya ji ajikinta ne ya tashi hankalinshi,da ƙarfi ya ambaci sunanta"My Juliet"

  Ƙasa ƙasa ta amsa mashi"My Romeo"

  "Are u okey?Naji jikinki da zafi,Bari naje na faɗa ma Babban yaya,"yana kokarin zame jikinshi daga nata tayi saurin ruƙo hannunshi"My romeo,Banason kowa yasan abunda Ya shiga tsakanina dakai...."ashagwa6e yace"But you're not feeling well,jikinki yayi zafi,"

   "Kada ka damu zanji sauƙi,Kaima naji jikinka da zafi,"

  "Amma nafi jin naki"

  Murmushi ta ɗan saki,tare da buɗe idanuwanta waɗanda ke a lumshe,Shafa gefen fuskarta yayi"I love u so much My juliet,kin faranta mun raina daren jiya,kamar zan zauce,Ashe dama haka abunnan yake?Sai mutun yaji shi A wata duniya yabi ya rikice,Allah Jahad ƙiris Ya rage numfashina ya ɗauke saboda daɗi....."bai kai ƙarshen maganarba,tayi hanzarin rufe mashi bakinshi"Its okey,abar maganar,"

   Cire hannunta yayi"Zan yi shiru,amma pls ki faɗamun kinji daɗi lokacin da nakeyi...."katse shi tayi"banaso Junaid,banace kayi shiru ba,"

  "Am sorry My juliet,but i need a second round,"

  Wurga mashi harara tayi"Ka kashe ni ka huta,"gudun kada ya sake yi mata magana yasa tayi saurin cewa"Yunwa nake ji,Bana buƙatar abu mai nauyi,Tea nakeso me ɗan zafi,ka haɗo mun da indomie,"

  "Dakaina ma zan girka maki a kitchen,"ya sauko daga saman gadon Ya fuce daga ɗakin,Sae zumuɗi yake yi,Murmushi tasaki cikin sanyin murya ta furta"Inasonka Mijina,"


A ƙa'ida ƙarfe 9 na safe masu  aikin Gidan suke shirya Breakfast ɗin gidan A dining,komai nasu a tsare Yake,"


Cikin ƴan mintuna Junaid ya shigo da indomie ɗin da romo sosai ya dafa mata ita,Ya haɗo mata da kakkauran Tea,da taimakonshi Jahad taci abincin,Taji daɗinta sosai,kuma dagaske shi ya dafa mata ita,bayan ta kammala,kwanciya suka yi a rungume da juna,duk da haka bai ƙyaleta ba,sai faman luguiguita ta yake yi,ba yadda ta iya dashi,


Sehrish tashiga zurfin tunani Hosana ta farka A hargitse take faɗin"Allah Ya Isa ban yafema ba,Mugu macuci Azzalumi wlh bana sonka Ya Omar...."hankali atashe Sehrish ta rufe mata bakinta da hannunta"Ya isa haka hosana!Ya Omar kike zagi"atsiwace Ta buge hannun Sehrish"Anje an zaga,Kuma wlh saina faɗama Daddy abunda yayi mun,Ya Omar ɗan iskane,Ni bana sonshi"

  Gigitacciyar tsawa Sehrish ta daka mata,Lokaci guda Hosana ta fashe da matsanancin kuka,Sassauta murya Sehrish tayi"Dan Allah hosana kiyi haƙuri,Ki yafe mashi komai ya wuce,Banji daɗin zagin da kike yima Ya Omar ba,Ina son da kike mashi ne?wannan abun fa da yayi maki Sunna ce ta Manzon Allah SAW,kidaina ce mashi ɗan iska Mijinki ne shi,Halak malak,kuma haƙƙinshi ne Ya Amsa a wurinki,Ni kin bani mamaki,Keda zaki taimakeshi yayi komai Cikin natsuwa Amma duk kin bi kin hargitsa komai,Shi kanshi dana yi tozali dashi lokacin dana shigo hawaye fa nagani Akan fuskarshi,duk ya shiga damuwa saboda ke ɗinnan,wannan abunfa ba kanki farau ba,Nima anyi mun,Kuma in mace nason haihuwa dole sai anyi hakan sannan zata samu ciki,kowa da kike gani ta hanyar hakan aka same shi,ko kin manta da abunda Mommy azeema ta koyar damu?"

  Tun Hosana na yin shessheƙar kuka har ta dakata da yin kukan tana sauraron Nasihar da sehrish ke yi mata,da alama jikinta ya fara sanyi,

  Sai da Sehrish takai ƙarshen maganarta,tukunna Hosana ta soma magana cikin shessheƙar kuka"Shikenan na haƙura,bazan ƙara ba,Amma yanzu zan samu cikin"?

  Ba sehrish ba,hatta Omar dake la6e a ƙopar ɗakin sai da ya fashe da dariya,

  ɗaure fuska tayi"na tambayeki kinyi shiru,"

  Jinjina kai Sehrish tayi"Zaki samu in sha Allah nan bada jimawa ba,Zaki haifama Ya Omar Baby boy or Baby girl"

Fashewa tayi da dariya kamar bamai jinya ba,murmushi Marshal ya saki A yayin da yake ƙarasa shiga bedroom din,Koda suka haɗa ido da hosana ɗaure fuska tayi,tare da kawar da kanta gefe,Miƙewa Sehrish tayi"bari na baku wuri,"

  "thank u so much My Sister"acewar Omar,don ba ƙaramin ƙoƙari tayi mashi ba,

  

Bayan fitar Sehrish ya koma gefen gadon ya zauna,rankwafa yayi saitin fuskarta"Babyn Omar,"A ƙule tace"Niba babynka bace,Babyn Oumma da Daddy ce,"Hannu yasa yaja kumatun ta"Am Sorry My Hosana,Yanzu ba gashi Anyi an wuce wurin ba,Saura jiran tsammani ko bakyason Baby ne,"

  "Inaso"ta bashi amsa a shagwa6e

"Yawwa,ki cigaba da bani haɗin kai,Nan da ɗan wani lokaci buƙatarmu zata biya na samun baby"Da wayau da wayau ya shiga lallashinta,sai gashi ta sauko sosai,hankalinsa ba ƙaramin kwanciya yayi ba,


Lokacin da Sgr yayi ma Sehrish Pt,result ɗin ya nuna positive,Farin ciki kamar wanda akayima albishir Da gidan Aljanna,Yini suka yi Manne da juna,ko ƙwaƙƙwaran motsi baiso tayi saboda cikin jikinta,tasha tarairaya,saboda cikin ga kuma laulayi da ta fara yi,Sgr Ya bata haƙuri game da zuwansu Honeymoon,Ya lallasheta akan tabari cikin nata yayi ƙwari sai su tafi,batayi mashi musu ba duk da ba haka taso ba,ba ƙaramin kulawa take samu a wurinshi ba,ya sanya mata ido sosai,Har masu aikin gidan Ya ba Umarnin su sanya mata ido,Da zarar sunga tayi gudu su sanar dashi,don ya hanata,gata gwanar yin tsalle tsalle,amma in har yana gida Har swimming pool suke shiga tare suyi nishaɗi aciki,suna jin daɗin hakan sosai,babu yadda batayi da Sgr ba akan karya sanarma kowa cewa tana da ciki,Ae tun a ranar da ya gane cewa tana ɗauke da ciki Ya kirasu Abba ya sanar dasu,Kowa saida yaji,Aka dinga kiranta daga gida Nigeria anayi mata Congratulation,tasha tsokana wurin Oummansu lokacin da ta kirata a waya,duk kunya ta cikata,Omar ma yayi farin ciki sosai,har shagali sukayi acikin gidan,batare da sunyi inviting ɗin kowa ba,A ranar Ya bata Special gift ɗinta Na key ɗin Mota,danƙareriya sabuwa fitigil Cikin Ledarta,ƙirar Bugatti chiron Kamar zatayi hauka ranar saboda tsabar Farin Ciki,Bata iya tuƙi ba,Yace da kanshi zai koya mata,Tun ranar suka fara ɗanɗana motar da zasu fita Tour (yawan buɗe ido),Zafafan hotuna suka ɗauka a beach(ga6ar teku)sunje cinema,Wurare daban daban suka je,lokacin da cikin Sehrish yakai 3 month,Suka shirya tafiya honeymoon ganin lafiyarta lou,ko kwaikwan ciki bata yi,A private jet ɗin Sgr suka yi tafiyar,Uk suka fara zuwa kamar yadda Mommy ta basu shawarar suje saboda akwai ƴan uwanta dake acan,Da kuma Sydney Australia,daga cikin ƙasashen da suka je Hada Turkey,Dubai,India,korea,ƙasashe daban daban,daga ƙarshe suka je Saudi Arabia sukayi Umrah,sun yawata sosai,Kafin su dawo Jahad da hosana Allah Ya albarkacesu da samun Ciki tun basu daɗe da yin tafiyar ba,A lokacin Cikin Sehrish ya tsufa,sati uku kenan da dawowarsu Los angeles,Ta fara naƙuda kamar bazata rayu ba,Hankalin kowa ya tashi,A katafaren Asibitinshi dake anan L.A aka kwantar da Sehrish,dole sai anyi mata C.s,ba ƙaramin tashin hankali Sgr ya shiga ba,tsoranshi kada Ya rasata,a ƙarshe da yaji bai iya jurewa,shiga ɗakin da za'ayi mata aiki yayi domin ayi atare dashi,Dama kullum saita roƙeshi akan Ya tsaya akanta a lokacin da zata haihu bataso kowa ya kar6i haihuwarta in bashi ba,cikin sa'a Akayi mata aiki,aka ciro mata triplet ɗinta,Kyawawan gaske,Sgr kamar zai zauce saboda tsabar farin Ciki,Zaratan samari ta haifa mashi guda biyu mace ɗaya,Farare tass dasu,kamannin Mazan sak irin na Sgr,hatta ƙwayar idonsu blue ce irin tashi,Macen kuma Sak kamannin fuskar Sehrish ne Amma Ƙwayar idonta blue ce irinta Ubanta,Kuma Hasken fatarta irin nashi ne,baturiya sak,Amma kana kallonta kaga sehrish,Tubarkalla ma sha Allah,Hada ƴan jarida suka zo ɗaukar rahotan haihuwar matarshi,Jariran Sunyi farin jini sosai,Kamar za'a lashesu,kowa sonsu yake yi,sai ɗaukarsu hoto akeyi,Omar yadda kasan Shi akayima haihuwar,Saboda farin ciki hada ƙwallarshi,


Haihuwar tazo mata da sauƙi,bayan da suka dawo gida,Anan Sgr yaci gaba da jinyarta tare da likitarsu ta gida,triplet ɗin data haifa Suna da ƙoshin Lafiya,Har tsokanarta Sgr yake yi,yana cewa yafita ƙoƙari shiyasa Suka ɗauko kamanninshi,next time ta bada himma sosai a samo masu kama da ita,a duk lokacin da yayi mata wannan Zolayar dariya yake bata sosai,


A can gida Nigeria,Lokacin da Labarin haihuwar Sehrish yazo masu,Tuni sun fara shirye shiryen Zuwa Suna America,Mommy tayi farin ciki sosai,ba ita kaɗai ba, mutanan gidan gaba ɗaya,kowa murnar haihuwar sehrish yake yi,Har video Call Sgr ya kirasu ta hanyar laptop din fawan da ya Ajiyeta a Palour,Ya kira kowa na gidan Suka taru suna kallon Ƴan ukunshi dayake nuna masu,kwance saman gado,an sanya masu kayan sanyi,Sunyi murna sunyi farin ciki sosai,


Saboda Shagalin Sunan da za'ayi a U.S,Matasan gidan suka ɗauki hutun aikinsu,dama an basu hutu tuntuni,tun lokacin da suka Farmaki Tawagar miyagun da suka addabi ƙasar,Aka Yankar masu hutu maitsayi basu yi ba,Gaba ɗayansu suka shirya halattar sunan,hada Amaren da akayi bikinsu Bayan tafiyarsu Sehrish,Waɗanda aka sanya bikin auransu,Hafsat da Ya Mu'allim da kuma Najeeb,khaleed da talal,Hada Na jos Abuhaisam shima ba'a jima da yin Auranshi ba,


Babu wanda yayi tsammanin zuwansu U.s,Sai dai kwatsam Aka gansu,gaba ɗaya Hadasu Abba da Mommy,Oummansu da Uncle abusufyan,Hajiya azeema da gwaggon katsina,Kanal yusif da amrish,Fawan Da matarshi,Kowa da kowa hada Haroon akayi tafiyar,Sunyi farin cikin ganin ƴan uwansu,A gidan kowa ya samu masaukinshi,Gagarumin bikin Suna aka shirya,A ranar sunan kowa Ya ɗauki wanka,Mai jegoma akayi mata ado na musamman Aranar ta sanya sarƙar gold ɗin da Sgr ya bata ta sadakinta,haɗaɗɗiyar gaske,Mai matuƙar ɗaukar ido,Kayan hausawa suka sanya,A masallaci aka raɗa sunan Jariran,Mazan Sunci sunan Abba dana Omar,Ita kuma macen taci sunan Oummansu Sehrish wato Zainab,Ba ƙaramin dadi iyayen suka ji ba,Musamman abu,Taji daɗi da Sgr yayi mata kara yasanya ma Ƴarshi sunanta,Haka Abba ma Yaji daɗi sosai,Omar yafi kowa farin ciki,Tun a lokacin yayi alƙawarin in har Hosana ta haifi ɗa Namji,Zai sanya mashi sunan Rafayet,


Bayan anyi suna da sati guda,Su kanal Yusuf suka shirya tafiya Honeymoon ɗinsu da basu samu sunje ba,gaba ɗaya matasan gidan suka shirya tafiya,Kowa da kowa,tun daga kan Yusif,Ayan da jahan,Fawan,khaleed,najeeb,Talal,harda su Ya mu'allim,Duka tare da matayensu,Sgr ya ɗauki nauyin tafiyarsu,Yanzu gidan ya rage Saura su Oummansu,Mommy,Hajiya Azeema,gwaggon katsina,dasu Ishaq da hajjaju,domin kuwa hadasu akazo U.s ɗin,sai Haroon,Duk yaƙi sakin Jikinshi,Har yafiya ya nema awurin Sehrish,Ta nuna mashi cewa komai ya wuce a wurinta,Shima ya manta kawai,Yaji daɗi sosai,musamman da ta bashi shawara akan Ya samu mata yayi auranshi,Bakowa tazo mashi aranshi ba,face Hayaam duk cikin matan da yayi mu'amala dasu ita kaɗaice Yayi mata ba'atare da son ranta ba,Ya haiƙe mata,shi kanshi yasan bai kyauta mata  ba,Yanzu itace a tunaninshi,Ya gama yanke shawara da zarar sun koma Nigeria zaiyi magana da Abba,A nema mashi auranta,dama Abuhaisam yayi mashi alƙawarin da zarar Ya samu wadda zai aura,Zai ɗauki nauyin komai na bikinshi, bayan tafiyarsu Yousouf Honey moon da Sati ɗaya,Aka ɗaura auran Eva tare da Amstrong  A church,bakowa bane Ya haɗasu ba face Sgr,gaba ɗaya saida suka halacci ɗaurin Auran,Abun burgewa Sgr ne yayi mashi babban aboki,kuma aranar Amstrong Ya kar6i addinin musulunci,Saboda kyautatawar da Sgr yayi mashi,Ya nuna yana ra'ayin komai nasu ya zo ɗaya,dama addinine Ya bambantasu,Yanzu Ya musulunta Ya ci sunanshi Muhammad,Bayanshi Uncle Donald ma Ya kar6i addinin musulunci saboda Ƙanwarshi da ta musulunta,Wato Mommyn su Junaid,Ganin Haka yasa ya'yanshi duk suka Musulunta suma,ba ƙaramin farin ciki suka yi ba,


Tsawon Watanni da tafiyarsu Kanal Yusif honeymoon,Aranar da suka dawo,Jahad da Hosana suka sauka a lokaci ɗaya,Allah ya albarkaci Junaid da samun Tagwaye Mace Da Namiji,Hosana kuma ta haifi Namiji ɗaya,duk zumuɗinta da haihuwa sai da tayi ƙorafi hada kukanta,Don me zata haifi ɗan ɗaya,Sehrish ta haifi uku,Jahad ta haifi Biyu ita kuma sai aka bata ɗan ɗaya,6alli ta tada masu aranar,Ta hana kowa sakat da koke kokenta,Har sai da Oummansu tayi mata nasiha sosae ta nuna mata in ta gode da wannan Allah sai ya bata fin dayan in zata kara haihuwa,amman in tana yin hakan tamkar bata gode mashi bane kuma hakan yana iya sawa taki ma kara haihuwar,jin hakan yasa ta haƙura,Ga Jinjirinta kyakkyawan gaske,Kamanninshi sak irin nata,Komai na Hosana yaron ya ɗauko Omar ba ƙaramin farin ciki yayi ba,Allah ya kar6i addu'arshi ya samu ɗa Namiji,A 6angaren Junaid kuwa,Lokacin da aka nuna mashi twins ɗinshi saboda tsabar farin ciki har sume masu yayi,da aka yayyafa mashi ruwa ya farfaɗo kuka ya dinga yi hawaye jaga jaga akan fuskarshi,Abbansu Ya bashi shawarar ya ɗauro alwala yayi salla,Ya nuna godiyarshi ga Allah,


Aranar Sunansu Jahad,Tagwayen Junaid,An raɗa masu sunayensu Macen Aka sanya mata Sunan Auntynsu AZEEMA,namijin kuma Aka sanya mashi sunan Uncle,Wato abusufyan,murna a wurin Mommy azeema da Uncle abusufyan kamar waɗanda akayi ma Albishir da gidan Aljanna,tagwayen junaid kamar yayi kakinsu Saboda kamanninshi da suka ɗauko,


Ɗan wurin Hosana kuwa Yaci Sunan babban yayansu,Wato Rafayet,Sgr Yayi murna sosai,ranar suna anyi shagali sosai,sun samu kyaututtuka a wurin ƴan uwansu da abokanansu Omar,Har kyautar Motoci Suka samu,Bayan wasu kwanaki da haihuwarsu,Gaba ɗaya suka ɗunguma zuwa Nigeria hada masu jego,A can zasu ƙarasa wankan jegonsu,Daga nan zasu zaga dangi,A sada zumunci kafin su dawo America,Sam Sgr da Omar basu so tafiyarsu ba,Junaid ma anan aka barshi saboda University ɗin da ya fara zuwa,Yana karantar Medicine & Surgery,duk cikinsu shi kaɗaine bai gaji Abbansu ba, yana ji yana gani aka tafi da Jahad da twins ɗinsa har da ƙwallarsa



Bayan sun kammala wankan Jego,suka shirya zuwa kai ziyara,Wurin danginsu,damaturu suka fara zuwa,Sukayi sati biyu acan kafin Suka wuce zariya wurin dangin Abbansu,duk inda sukaje hannu bibbiyu ake tarbarsu,Kowa sonsu yake yi,daga zariya suka wuce Kano,Ziyarar bazata sukayi ma su Maman Sadeeq,Sunyi farin cikin ganinsu sosai,kusan sati ɗaya sukayi a kano,Harsu Hayaam saida suka zo Gidansu Maman sadeeq wurinsu Jahad don su gansu,Hafsat ce ta sanar masu da zuwansu kano ta basu Numbar wayar Sehrish,Ita tayi masu kwatancen gidan sukazo,Hayaam tayi kuka sosai lokacin da taga Ƴan ukun Sehrish,Tabi ta ruɗe ta susuce,Kyawawan gaske,kamar Sgr yayi kakinsu saboda tsabar kamanceceniyar dake tsakaninsu,kafin Su sehrish su koma America,wasu daga cikin amaren Gidan suka haihu,matar Yusuf Amrish,da matayensu Twins da fawan,Amrish ta haifi tsaleliyar budurwa,Yuhana matar Ayaan ta haifi Namiji,Amal Ta Haifi twins maza,ɗaya yaci sunan Irfan,Ɗayan kuma Yaci sunan kakansu Salahudeen,sauran amaren wasu suna ɗauke da tsohon ciki,Sai bayan da akayi shagalin sunansu Amrish,Kafin Su Sehrish suka koma U.s,wurin mazajansu,Sunsha soyayya ranar da suka koma,kusan First night ɗinsu Sgr ya maimaita,Dama sunsha gyara wurin Mommy azeema,musamman saboda zuwansu Nigeria,tazo gidan don ta Gyarasu kafin ta koma ɗakin Mijinta,tamkar amare haka suka koma,


Sgr ya bada shawarar Ayi masu Family planning saboda su samu damar yin karatu,Omar yayi na'am da maganarshi,atare aka sanyasu Makaranta,private school ɗin Mommy matar Uncle Donald,gaba ɗaya S.s.one aka kaisu,duk da su Jahad basu kaiba hanyace kawai akayi masu ga kuma girman da su kai,da taimakon mommy aka yi masu komai.


Tabbas Family ɗin Salahuddeen sunyi babban rashi,wanda Yayi matuƙar girgiza su,na Kakarsu AMMI,Bayan Tayi jinya ta ɗan lokaci,ta koma Ga mahaliccinta,mutuwar Ammi ta girgiza su sosai,Sunji mutuwarta,A ranar Alhamis Ta rasu,A washe garin ranar da ta rasu,Su Sgr suka zo Nigeria,a Damaturu suka sauka don duk suna can zaman gaisuwa,satinsu ɗaya suka Koma America,

  

Kullu nafsin za'ikatul maut,


Ammi bata dade da rasuwa ba akayi bikin Haroon da Hayaam da farko taki amincewa dashi sai da suka yi waya da hafsat take sanar da ita komae game da haroon ta kuma sanar da ita cewa shi din jinin Abba ne,daga baya ta amince mashi aka daura masu aure,at last dae hayaam ta zama surukar Abba,ba'a dade da yin aurensu ba Allah ya Albarkaci Amani da haihuwar da Namiji sunyi matukar farinciki sun gode ma Allah,abunda suka dade suna nema,da farko amani har ta fidda ran haihuwa taba Abbas shawarar ya kara aure don ta san yana son yara,yace zai yi tunani cikin hukuncin Allah kafin ya yi tunanin sai ga ciki,indeed,Mahakurci mawadaci ne.


Bayan wasu shekaru,Alokacin sauran Amaren duk sun haihu, Kowa da ƴa'ƴanshi,Hada Hajjaju ta haifama Ishaq santalelan ɗa Namiji,Hafsat kuma ta haifi Ƴa mace taci sunan Mahaifiyarta wato Laila,Oummansu Sehrish itama Allah ya albarkaceta da samun Twins Maza sunci sunan Mahaifinta marigayi Baba buzu,Ibrahim da sunan mijin gwaggon katsina wato Nuraddeen,ba karamin farin ciki gwaggo tayi ba harda Dr harris ma yaji dadi sosae,shima suna katsina Saude ta haifa mashi budurwa har yarinyar ta d'an girma sunan gwaggo taci wato Ameenatu,ƙannansu Sehrish Masu kama da Oummansu sak,Jama'a gida ya cika maƙil da jikoki,Dama burin Abba kenan,duk inda ya waiga ƴan jikokinshi ne,Ƴan dugui dugui dasu,tun da yayi retired,Kullum Yana zaune cikin Jikokinshi,Yana wasa dasu,Ya Manyata sosai,kanshi Duk hurhura,Idan yana wasa Da Yaran Abun saiya baka sha'awa ya saka dariya,Har wasan Ƴar 6urun 6urun suke yi dashi,Sun saba da kakansu Fiye da iyayensu,Ya sangartasu sosai,daga zarar wani ya 6ata masu rai,Zasu zo wurinshi kawo ƙorafi saboda Yana goya masu baya,Mafi yawancin lokutta a garden Yake yin wasa dasu,ba ƙaramin nishaɗi yake samu atare dasu ba,sam bai da wata damuwa irin yadda wasu in suka yi ritaya sukan shiga damuwa saboda rashin zuwa aiki kullum sai zaman gida,




*Boss Bature*


*Ga duk Mai buƙatar Karanta Littafin Abban Sojoji Daga Complt a jere Daga Book One zuwa 3 Suyi mun magana ta whatsapp 08103884440*


 

[3/19, 10:00 PM] +234 810 388 4440: *💋ABBAN SOJOJI💋*




*💃LAIFIN DAƊI ƘAREWA💃*


   *FINAL EPISODE*


Join this link to follow my tiktok acct👇


https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1





قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*


*Father of soldiers*



*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




Zazzafar haja daga Minjibir ventures,Ina masu buƙatar siyan kayan sallah Kada ku bari a baku Lafiya,Ga kaya na kece raini Na shiga tsara,Koda kudinka sai da rabonka,Kadan daga cikin abubuwan da muke siyarwa akwai Lace 

Veils

Atamfa

Shoes

Bags


Address

Hotoro ladanai  kan titin ring road

Chat 09126570345

Call 09136122503 saikun Zo💃💃💃💃






*Boss Bature*


Bayan Wani Lokaci,


Alhamdulillah junaid Ya samu damar kammala Karatunshi,Ya zama ƙwararran Likita,batare Da 6ata Lokaci ba,Sgr Ya sama mashi Aiki a katafaren Asibitinshi na L.a,A 6angaren Su sehrish Kuwa Suma sun taƙarƙare karatun Secondry ɗinsu,Sgr Ya sama masu gurbin karatu a College of Nursing and Allied Health dake anan Los angeles,Rayuwa fa Tayi kyau,Ta ko'ina Sai sambarka,Hankali kwance suke yin karatunsu,Mazajansu suna ƙarfafa masu guiwa,Ƴa'ƴansu kuma Akwai Nannies ɗin dake kula dasu,hosana tana ɗauke da ƙaramin ciki,saboda takurar da take yiwa omar akan tana son baby tunda ita ɗaya gareta,a dole aka dakatar da planning din da take yi,


*Boss Bature*


Wuraren ƙarfe 9 na dare,Kwance suke a katafaren gadonsu,Komai na bedroom ɗinsu Pink colour ne,An ƙawata shi da duk wani abu na more rayuwa wanda yaro zai buƙata,triple bed ne,Guda uku A jere,da alama sunyi nisa acikin baccinsu,Kowannasu na sanye cikin Night dress ɗinsa,Mazan suna sanye ciki riga da wando White colour,Ƴar macen tana sanye cikin riga da wando Pink colour,ba ƙaramin kyau suka yi mata ba,Sumar kanta dark brown very smooth,kamar yarda Zainab take da dogon gashi haka mazan ma,domin kuwa sun ɗauka irin sumar kan Sgr,Gashin kansu ya sauko har saman kafaɗansu,A ƙalla yanzu sunkai shekara Biyar a duniya da ƴan watanni a duniya,da farko a gado ɗaya suke kwana,Amma saboda rashin jituwarsu yasa Aka kawo wasu bed ɗin biyu,abunda ke faru aduk lokacin da Iyayensu suka kwantar dasu,da zarar sunbar ɗakin,Ƴar macen zata Soma tsokanar mazan faɗa,Gasu miskilaine,Don hossein Halinshi sak irin na Sgr,ko kallo wannan Mutun bai isheshi ba,mugun jan ajine dashi,bai ɗaukar raini ko kaɗan,Mugun miskiline,Suna kiranshi da Gentle Ƙwara Little Omar,Shiya ɗauko Halin Sehrish,Hatta tsoran nan na Sehrish haka yake shima,Ko tsawa akayi sai ya gigice,Yaci ka sanyi,Bai bar komai na daga halinta ba,Zainab kuwa Tafi ƙarfi 6angaren Sgr,Sai dai ita ba miskila bace,mafaɗaciyace,Kamar ƴar dambe haka take,dama tun suna jarirai,In ta fara tsala ihu,Sai ta firgita kowa,Pretty suke kiranta,Allah yayi mata ƙarfi,tun tana ƙanƙanuwarta inaga inta girma,


A hankali ta turo ƙopar ɗakin sai kayi tsammanin babban mutunne zai shigo sai ka kalli ƙasa tukunna Zaga iya hangenta,azeema ce ƴar wurin Jahad Wadda suke kira da Beauty Saurin Shiga rai gareta ta,saboda sanyin Halinta,matsalarta ɗaya muguwar sangartacciyace,Ga shagwa6a Komai nata irin na junaid ne,hannunta na ruƙe dana ƙaninta Littafin abusufyan,shi halinshi Sak na jahad ne,Kowannansu na sanye Cikin kayan baccinshi yadda suke tagwaye haka kayan jikinsu ma Suka kasance Launi ɗaya,Riga da wando brown colour,wannan ɗabi'arsu ce duk mun dare bayan iyayensu sun kwantar dasu,In har suka farka to sai sun nemi ƴan uwansu,Abun ba ƙaramin ɗaure masu kai yake yi ba,kamar masu iskokai,Sunfi son kwana ɗaki ɗaya kamar yadda suka saba yin wasa atare,


Suna shiga ɗakin suka saki Hannun Junansu,Da gudu Little Ya haye Gadon Omar ya kwanta gefenshi,don sunfi shiri dashi,Beauty kuma ta nufi gadon Hossein zata kwanta,Tana ɗaura hannunata Ya ware Manyan blue eyes ɗinshi akanta,Gaba ɗaya ta furgice,Ashe idonshi biyu tun lokacin da suka shigo,Wani irin kallo yake binta dashi,Ko Uffan baice mata ba,Ya juya mata baya,Don karma su fuskanci juna,Bai hanata kwanciya ba,lalla6awa tayi saman gadon ta kwanta,


Basu jima da shigowa Ba,Sai ga Little Rafayet,Hannunshi ruƙe da ƙaton teddy ɗinsa har yaso yafi ƙarfinshi,Farin cikine Ya lullu6eshi ganin ƴan uwanshi duk sun haɗu guri guda,da gudu Ya ƙarasa Saman Gadon Zainab Ya haye ya kwanta,Tare da ɗaura mata teddy ɗinshi asaman Jikinta,Cikin bacci tajishi,aikuwa a harzuƙe ta farka,Tayi wurgi da teddy ɗin tare da ɗunƙule hannunta zata kai mashi naushi,koda tayi arba da fuskar Little Rafayet,Sai ta janye hannunta,Tana faman Cizon le6enta Allah yaso shine dayasha Naushi,juyawa tayi ta ɗauko mashi teddy ɗinshi ta miƙa mashi"take it,"a tsanake tayi maganar,

 Cikin harshen turanci don dashi suka taso amma suna jin hausa,Iyayensu nayi masu,saboda Suna yini a school,yasa suka fi ƙarfi ta 6angaren turancin da french,

   girgiza mata kai yayi"Naki ne,Na kawo maki,"murmushi tasaki har dimple ɗinta Ya lotsa,a tsakiyarsu ta ajiye teddy ɗin,a haka suka rungume juna,da ƙaton teddy a tsakiyarsu,cikin lokaci ƙanƙani bacci yayi awon gaba dasu,


*Reeshraf*


A hankali take saukowa daga saman stairs ɗin da zai sadaka Da Swimming Pool area ɗinsu,A yayin da Sgr Yake tsulundun acikin ruwan yana jiran ƙarasowarta,Ƙayataccen swimming pool ne mai faɗi,Ruwan cikinshi yayi blue sky,wata irin ni'emace ke sauka a wurin,Jin motsinta,Yasa  shi yin saurin kai idanuwanshi akanta,tun ɗaga ƙasa ya fara kallonta,Swim suit ne Ajikinta(Kayan wanka),Ƴar rigace me haɗe da pant,red colour,tabi shape ɗin jikinta,gaba ɗaya ta tafi da imaninshi,Santala santalan Cinyoyinta ba ƙaramin fusgarshi suke Yi ba,Iska sai kaɗa sumar kanta takeyi,Yalwataccen gashin kanta sai kaɗawa yake yi saman iska,yana ƙoƙarin rufe mata fuskarta,A hankali take kai hannu tana Janye gashin,Yadda kasan bata ta6a ɗaukar Cikin ƴan uku ba,Jikinta yayi kyau sosai,ba ƙaramin gyara take yi ma Jikinta ba,tana kiyaye duk wani abu da zai 6ata Shape ɗin Jikinta, kuma Tana yawan motsa jikinta,Ga mayukan gyaran jiki da take Using dasu kullum,duk cikinsu ita kaɗaice bata yi jiki ba,Duk da suma Su Jahad basu 6uttuke ba,



Lumshe idanuwanshi yayi a yayin da yake kallonta,A ƙagare Yake data ƙaraso Ya rungumeta Ajikinshi,da wata irin kasalalliyar murya yake ambaton Sunanta"Reesh....pls come quickly"sai ja mashi rai take yi,Koda ta ƙaraso Gaban pool ɗin,Zagayeshi ta shiga yi,duk in tayi taku ɗaya sai jikinta Ya girgiza,

  "Pls reeesh why kike yi mun haka?bazaki shigo ciki ba"?maƙe mashi kafaɗa tayi alamar bazata zo ba,sai faman haɗiyar yawu yake yi,

  "Kada ki bari na hasala,Zan damƙo kine,"

  Kashe mashi ido ɗaya tayi"Nafison haka,Kafin ka fito daga cikin ruwan ni kuma zan watsa a guje"

  ɗaure fuskarshi yayi"haka kike ce"?

  ɗaga mashi gira tayi,Kamar ta ƙara tunzurashi,batayi tsammanin zai fito ba,sai dai kawai taganshi akan ƙafafunshi,daga shi sai short ajikinshi,Faffaɗan ƙirjin nan nashi a buɗe kamar zaiyi dambe,A firgice Ta juya da gudu zata Koma Saman benen,Sai dai ina kafin takaiga stairs ɗin tuni sgr Ya cimmata,ƙwaƙƙwarar damƙa yakaima Qugunta,ya ɗago da ita sama ya nufi Pool ɗin da ita,Kamar tasan abunda zaiyi tadinga bubbuga bayanshi tana faɗin"Am Sorry Ya rafayet zanyi biyayya,"

  Wurgi yayi da ita cikin ruwan Ruwan  tsulundum ta faɗa ciki,Kafin shima Ya daka suka ya faɗa ciki,Tare da janyota jikinshi,suka fiddo da kawunansu daga cikin ruwan,Sae faman haki take yi,natsuwa yayi yana kallon kyakkyawar fuskarta,fuskokinsu sharkaf da ruwa,hakan ba ƙaramin kyau yayi masu ba,Hasken Electric bulbs ɗin dake a wurin sun haskakasu sosai,Babu kowa,dama babu mai zuwa wurin,Wannan swimming pool ɗin nasu ne musamman saboda jin daɗinsu,bashi kaɗai bane acikin gidan,Akwai wasu kusan guda biyu duk acikin gidan,


   "Reesh..."daƙyar ta iya buɗe idanuwanta akan fuskarshi,ruwan ya tsaya mashi adai dai stomach ɗinshi,ita kuma yakusa taddo chest ɗinta 

  Zuba ma juna ido sukayi Tamkar zasu haɗiyi junansu,ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,fuskarta akwai light makeup,hada janbaki tashafa red colour,duk da ruwa Ya jiƙa fuskar hakan baisa kwalliyar ta goge ba,slowly ya zagayo da hannunshi asaman ass ɗinta Ya ɗaura tafin hannunshi,tare da janyota,Ya haɗe gabansu sosai tun suna kallon juna,har yakai ga Haɗe bakinsu wuri guda,sosai suke kissing ɗin juna,moving ya shiga yi da hannunshi acikin rigar jikinta,Martani  ta shiga mayar mashi tafara sarrafashi da hannuwanta,lokaci guda yabi ya ruɗe ya susuce mata,Zame hannun rigar jikinta yayi,Ya sabule ta,Zuwa waist ɗinta Yadda zaiji daɗin ganin komai muraran,Bakinshi yakai ya kama nipple ɗinta,Sosai ya shiga sucking ɗinsu,duk ta fita hayyacinta,a lokacin ta dawo da hannunta cikin sumar kanshi,ƙara ƙanƙameshi tayi sosai,cos she is enjoying it,a ruɗe take Ambaton sunanshi"ya rafayet"ƙasa yayi da kanshi can can,Yana bin ko'ina na jikinta,Yana licking ɗinsa,rurruƙeshi tayi sosai saboda yanayin daya jefata kamar tayi hauka,batasan lokacin data fashe da kuka ba,wuta sosai yake bata,lokacin daya ɗago komawa jikinta yayi,Ya kwantar da kanshi saman kafaɗarta,yana mayar da numfashi,bata bari Ya gama mayar da numfashin nashi ba,Taso ma nata Salon,Zame mashi short ɗin jikinshi tayi,Tashiga sarrafashi,Ta gigitashi ya soma yi mata wannan sambatun nashi Aruɗe yake faɗin"keep!keeep!keeep doing it Reesh,You're giving me fire........."


Saida saukayi mai isarsu,Kafin suka dakata kowa Yana mayar da numfashi,sam idanuwansu sun gaza tsayuwa,Sae faman lumshewa sukeyi,a hankali Ya zura hannu cikin ruwan Ya janyo short ɗinshi Ya mayar,Ya ruƙo rigar jikinta,A hankali Ya janyo ziririn hannun rigar Ya mayar mata da ita,rungume juna sukayi sosai,A hankali Ya shirga furta"Reesh Allah yayi maki Albarka,daga ke ba ƙari,banga mace a duniyar nan ba,in bake ba,"kalamansa ba ƙaramin daɗi sukeyi mata ba,musamman idan ya sanya mata Allabarka,daɗi take ji sosai,

  "Allah ya faranta maki,Kamar yadda kike faranta mun,"

  "Ameen Yayana mijina,"

bacci sosai suke Ji su dukansu,So yake ya ɗauketa gashi Jikin nashi duk kasala ta baibayeshi,Daƙyar Ya tattara dukkan ƙarfinshi Ya sa6eta asaman kafaɗashi ya nufi stairs ɗin da zai kaisu kaitsaye Upstairs,part ɗinsu,Lokacin daya shigo da ita ɗakinsu ya sauketa,Shaf shaf suka Shirya kansu cikin Night dress ɗinsu Ash colour,Hannunsu ruƙe cikin na juna suka nufi ɗakin triplet ɗinsu,time din da suka shiga ɗakin,Basuyi mamakin ganinsu Little rafayet ba,Kallonshi tayi suka haɗa ido,Murmushi suka saki at same time 

  "Ina mamaki wannan al'amarin nasu,sunfiso su kwana cikin ƴan uwansu,ko tsoro basa ji,Su kwaso ƙwafa Don ma akwai haske ko'ina acikin gidan Shiyasa basa fargabar komai,"sehrish ce tayi maganar,

  "Ƙuruciyace da kuma Shaƙuwar dake tsakaninsu,nan da wani lokaci zasu daina ne,"yakai ƙarshen maganar tare shigewa cikin ɗakin itama tabi bayanshi,Agaban gadonsu suka tsaya suna ƙare masu kallo,

  "Yanzu wannan duk namu ne"?tayi tambayar tare da kallonshi"Are doubting"?girgiza kai tayi"a'a,Kawai tsabar farin cikine shiyasa na furta hakan,

   Ƙayataccen murmushi ya saki,kafin ya kuma cewa wani abu, sai ga Hosana ta faɗo ɗakin jikinta sanye da night gown doguwa,ta yafa mayafi akanta,juyowa su kayi atare suna kallonta jin shigowarta,

   Bayan tayi masu sallama suka amsata,sai ta tsaya shiru tana hangen little rafayet dake akwance saman gadon pretty,

   Murmushi sehrish tasaki"kinbiyoshi ne halan"?ɗaga mata kai tayi alamar eh,

  "Kawai na farka naga babu shi,daga ni har ya Omar bamusan lokacin daya fita ba,a tsakiyarmu muka kwantar dashi,Shi sarkin wayau hada sanya mana teddy a tsakiyarmu don kada muyi saurin gane ya fita,"

  Dariya sukayi gaba ɗayansu,Sgr Yace"its okey,kibarshi kawai tunda yafi so Ya kwana tare da ƴan uwansa,nan da wani lokaci zasu daina dakansu,"

  Jinjina kai tayi"shikenan,Sai Allah yakaimu,"

  "Mu kwana lafiya"juyawa tayi da sauri ta fuce daga ɗakin,murmushi sehrish tasaki,6ata ta6a tunanin irin wannan ranar zata zo ba,Yanzu hosana ta natsu,hankalinta ya dawo kan saiti,

  Ruƙo hannunta sgr Yayi"Bacci nake ji fa,"

  "Me too"


Kamar yadda suka Saba,Atare suka soma yi masu addu'a suna tofa masu ajikinsu,Bayan sun Ja masu lallausan blanket dinsu,ta Kashe masu hasken ɗakinsu,Hannunsu ruƙe dana juna suka koma bedroom ɗinsu,Saman katafaren gadonsu suka kwanta,yayi hugging ɗinta tighly,then Ya Janyo lallausar blanket ɗinsu Ya lullu6esu,

   Bayan komawar Hosana ɗakinsu,a zaune ta samu marshal daga shi sai short,

  "Ae dama saida na faɗa maki,"

Murmushi tasaki"ashe yana acan,Yaron nan yaci ka wayau,"

  Dariya yayi yana girgiza kai,Saman Gadon ta hau,Suka gyara kwanciyarsu rungume da juna,

  "Ya Omar"Ya amsa mata"Na'am My baby"

   "Kayi mun kalaman Soyayya mana kafin muyi bacci".  

  Gyara muryarshi yayi cike da zolaya yace"Yake akuyar dake cin ciyawar zuciyata"gaba ɗaya suka tuntsire da dariya,


*JunHad*


Tayi mamakin ganinshi zaune saman gadon,Ya jingina bayanshi jikin headboard ɗin gadon hannunshi ruƙe da hoton abbansu,ya ƙura mashi ido yana kallonshi ko ƙyaftawa baiyi,

  "My romeo,"ta ambaci sunanshi,batare daya juyo ba,Ya amsa mata"My juliet,"

  "Meyasa ka barni ni kaɗai"?

Murmushi ya ɗansaki"Am sorry,Yanzu nake shirin kwanciya,ina kallon Sanyin idaniyata ne"

  Miƙewa tayi ta zauna gefenshi,hannu takai tare da shafa fuskar Abba mai ɗauke da murmushi"Allah sarki Abba,we really missed you Ni da babyna,tayi maganar tana shafa sumar kan Junaid,

  "My Juliet"ya ambaci sunanta

 " na'am My romeo,"


"Idan su babban Yaya suka ajiye aiki zamu koma nigeria da zama,Ni nafison can,"

  "Nima nafison mu koma Nigeria,ba don bana jin daɗin nan ba,sai dan saboda ƴan uwanmu"acewar Jahad,


ɗaura hoton yayi a ma'ajiyarshi saman drawer,


  "Yaushe zamu ƙara samun baby"?

"Duk lokacin daka shirya,My doctor"

"Ae ni kinsan koda yaushe a shirye nake,ko yanzu ma,ko kina ganin wasa"?

  A'a,Na yarda da maganarka,Ae kai ɗin bana wasa bane tayi maganar tare dakai hannu ta ɗan bugi ƙirjinshi,murmushi yasaki"duk da haka bazan ƙyaleki ba,'tana ƙoƙarin buɗe baki tayi magana,Yayi saurin haɗe bakinsu wuri guda,Ba halin Yin magana,Sosai ya ruƙota ajikinshi,Romancing ɗin juna sukayi kafin daga bisani ,Suka gyara kwanciyarsu rungume da junad,A ƙanƙame,



Wuraren sallar asuba,yana cikin bacci Yaji shessheƙar kuka acikin kunnanshi,Gabanshi ne ya faɗi,A hanzarce yakai hannu yana shafa gefenshi saman mattress,Jin  wayam babu ita Yasa ya ware idanuwanshi,Yayi mamaki Ganin babu Sehrish asaman gadon,Ga kuma shessheƙar kukan da yake ji acikin kunnanshi,saukowa yayi daga saman gadon,kaitsaye ƙwayar idonshi ta sauka akan ɗigon jinin dake a ƙasan tiles ɗin ɗakin,A jere jinin yake har zuwa toilet ɗinsu,Lokaci guda Hankalinshi Ya ƙara ɗunguma,A gigice Ya miƙe ya nufi toilet ɗin Yana faman ƙwala mata kira"Reesh!reesh!where are u"?Hannu yasa ya tura ƙopar toilet ɗin,Sai dai kash adatse take,ƙwaƙƙwaran naushi yakai ma ƙopar,ta buɗe Ya afka ciki a haukace,tuni idanuwanshi sun ciko tab da ƙwalla,Kwance ya hangota acikin bathtub ruwan dake acikin kwamin wankan ya gauraya da jinin dake ajikinta,Alamu sun nuna cewa ta jima Da mutuwa,hawayene suka wanke mashi fuskarshi,Sam Ya kasa ƙarasawa cikin toilet ɗin,Zubewa Yayi asaman guiwowinshi,sosai ya fashe da kuka,fuskarshi tayi jaga jaga da hawaye,sam bazai iya jure rashinta ba,Zuciyarshi barazanar harbawa take yi,Jiya jiyan nan suka sha soyayya da daddare gashi yau Ya wayi gari batare da ita ba,ashe dama na bankwanane sukayi"?


Runtse idanuwanshi Yayi sosai,Kafin Ya buɗesu a hankali,zurfin tunani ya shiga,Ƙura ido yayi yana kallon ɗagon jikin dake a gabanshi,Yatsanshi yakai tare da dangwalo jinin Yana kallonshi,Kokwanto ya shiga Yi Kamar ba Jini ba,Sam babu ƙarnin jini Ajikinshi,Azafafe Ya miƙe ya ƙarasa shiga Toilet ɗin,Ya tsaya gaban Bathtub ɗin yana kallonta,cike da saran abunda yake zargi,

  Muryarshi na kerma Ya ambaci sunanta"Reesh...."shiru bata motsa ba,Almost 3 times Yana Calling Name ɗinta bata amsa mashi ba,jikinshi yayi sanyi sosai,dagasken dai ta mutu,Ya rasa reesh ɗinsa 

  Girgiza kanshi ya shiga yi la66ansa na kerma Ya shiga faɗin"Reesh why kika barni,Meyasa mutuwa zatayi mun yankan ƙaunane,wlh bazan Iya rayuwa batare dake ba,Zan kashe kainane,"A hanzarce Ya juya Ya fito daga toilet ɗin,jikinshi Na kerma Ya nufi bedside drawer ya ɗauko bindiga,cikin kunnanshi Ya saita bingidar Tare da rufe idanuwanshi,yana karanto kalmatusshahada,Sam batayi tunanin Sgr zai Iya aikata abunda Ya faɗa ba,da gudun gaske Ta fito daga cikin ƙwamin wankan daga ita sai undy data ja har zuwa saman ƙirjinta,tana ƙoƙarin buɗe ƙopar toilet ɗin Tajiyo ƙarar fitar bullet,Wata irin gigitacciya ƙara Sehrish tasaki,tana fitowa Ta same shi baje a ƙasa,jini duk ya wanke fuskarshi,Fashewa tayi da matsanancin kuka,A sukwane ta zube saman guiwowinta

  "Innallallahi wa'inna ilaihirraji'un!!Ya rafayet!ka tashi!Nifa wasa nake maka Wlh ban mutu ba Wayyo Allah nashiga uku,Na bani Na lalace,gaba ɗaya tabi ta rikice Ta ruɗe,hannunta duk ya 6aci da jininsa,jijjiga shi tadingayi tana kuka kamar ranta zai fita,a ƙarshe ta rungumeshi tana kuka,ta tsorata sosai,daga wasa tayi silar mutuwar masoyinta,sai da ta jigata sosai,duk ta fita cikin hayyacinta,Sautin dariyarshi data dinga jine yasa ta yin saurin ɗagowa Tana kallon fuskarshi,Zazzare idanuwanta tayi akan fuskarshi,Ganin Yana ta faman tiƙar dariya,ya buɗe idanuwanshi sosai,

  Daƙyar ya samu ya tsagaita da yin. Dariyar yace"Reesh ke kika iya tsara drama irin wannan balle ni da nake soja?I can do better than u,'

  Fashewa ta kumayi da matsanancin kuka Cikin shessheƙar kuka take faɗin"Meyasa kayi mun haka Ya rafayet!Nifa wasa nake maka,"

  Jifa mata harara yayi"haka ake wasa a gidanku?waya gaya maki ana wasan mutuwa?ko shima duk cikin Soyayyarne?da ace tunfarko ban gane so6o bane kika sanya me kike tunanin zai biyo baya,Zuciyata har kusan bugawa tayi lokacin da naganki kwance cikin jini,


Kowannansu Yaji jiki,

Sosai take kuka"Wlh bazan Yarda ba,Ya rafayet Ka tsoratar dani"tayi maganar muryarta na kerma,

  

  "So6on da kikayi amfani dashi kika ajiye bottle ɗin Saman fridge dashi nayi using na kwararama Kaina," Still  hawaye basu daina zuba akan fuskarta ba,har wani zazza6i take ji ajikinta,

Kafeta da ido yayi yana kallonta,Kamar wata ƙaramar yarinya,kowa ya bata shawarar tayi mashi irin wannan wasan,

  "Naji tsoran na rasaka,"tayi maganar ashagwa6e,

  "In har zaki cigaba dayi mun irin wannan wasan to kuwa tabbas wata rana zaki rasa nine,"

   Fashewa ta kuma yi da wani kukan  Sosai ta sanya mashi rigima,tana faɗin Wlh bazan  yarda ba,Ae ni ba haka nayi maka ba,ka tayarmun da hankalina......"


  Cikin sanyin murya Ya bata hakuri"Am really sorry,"

  Girgiza kai tayi"a'a Bazanyi haƙurin ba,"miƙewa Yayi daga zaune"Yanzu me kikeso nayi maki?wanda zaisa ki yafe mun,"

   "Frog jump"ashagwa6e ta bashi Amsa,

   Zaro Eyes ɗinshi Yayi "Frong Jump"?Ya maimaita abunda tace,

  Ɗaga mashi kai tayi"Eh shi nakeso kayi mun,"

   "Zanyi kneeling agabanki,In baki haƙuri"

   Bubbuga ƙafafunta Tayi"idan ba zakayi Tsallen kwaɗi ba,ni bazan haƙura ba......."

   Ganin Ya tsareta da ido Yasa ta Fashe da wani sabon kuka Hawaye duk suka wanke fuskarta,A ruɗe Sgr ya Zuƙunna tare da kama kunnuwanshi,


"Can zaka tafi,idan kakai saika dawo nan,"da hannu take nuna mashi inda zaije,Bakinta ƙumshe da dariya,Sam bai kawo komai aranshi ba,Ya soma Yin tsallen kwaɗi ya nufi inda ta nuna mashi Ya juyo Ya nufo inda take,

  Tuntsirewa Sehrish tayi da dariya Tare da buga tsalle Tana faɗin"Na rama !Na rama!"

   Abun ya ɗaure mashi kai,Sakin kunnuwanshi Yayi tare da miƙewa tsaye yana kallonta,Tsantsar farin ciki Ya gani akan fuskarta,Kamar wadda akayi ma Albishir da gidan Aljanna,A ruɗe yace"Reesh are u ok"?

   "bakaine kake sanyani Yin tsallen kwaɗi ba,lokacin  da muna a gida?Yau nima Na rama,Na sanya Surgeon General Rafayet Tsallan kwaɗi,",tana  kai ƙarshen Maganar,Ta watsa da gudu Ta faɗa saman faffaɗan ƙirjinshi Tana dariya,

 "Ke ko"?ya faɗi hakan fuskarshi ɗauke da ƙayataccen Murmushi,Abun ma dariya ya bashi,Wai ta rama,Ashe abun ya tsaya mata aranta,kamar zautacciya Haka taci gaba da dariya tana faɗin "I luv u Ya rafayet!Mijina nakaina"

   "I luv u too,matata takaina,"ya amsa mata cikin so da ƙauna..............." 


    💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃*HAPPY ENDING*




*💋Boss Bature💋




*Alhamdulillah!*   *Alhamdulillah!!* *Alhamdulillah!!!💃💃💃💃💃💃💃*



*A nan na kawo karshen littafin Abban sojoji wanda na dau tsawon lokaci ina rubutawa😍*


 _Dukkan godiya da yabo sun tabbata ga Allah subhanahu wata'ala,the most compassionate and the most omniscient,da ya bani ikon kammalawa cikin ƙoshin lpy kaman yadda na fara,to him be all the glory🙏,tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi muhammad(S.A.W)😍Darussan dake ciki Allah ubangiji yasa mu amfana dasu🙏 ya sadar da ladan gareni da mahaifana da yan'uwana da malamai na da dukkan masoyana a duk inda suke a faɗin duniya🥰kura kuren ciki Allah ubangiji ya yafe man🙏_


_Gaisuwar ban girma ga mahaifiyata Hajiya Rabi'atu Yahaya,she is my first luv and my everything💘,Allah ya ja da rai ya kara maki lafiya my sweetheart😘,My beloved Siblings💞waɗanda littafin nan Sadaukarwa ne a garesu,Nafisat,Aisha,Zainab,Khadija,maimunatu,Abdul'azeez,Fatima,Maryam,Ameenatu,I luv you so,so much,kune ni,in baku bani,I really appreaciate ur Encouragement💪,prayers and all-round support👍,Allah ya kara haɗa kawunanmu ya jiƙan mahaifinmu,Ameen_


_Special thanks to,Fadeela Lamiɗo,sadeeq Abubakar Ceo Lafazi writers,Abubakar Sadeeq AlQuramy,Maisalati,Kamala Kabeer,My Editor Aunty Zainab Laluh,whose contribution in no small measure serve as spices to this work,ina matukar godiya a gareki🙏da ƙarfafa man guiwa da kika rinka yi har zuwa kammaluwar wannan littafi ina rokon Allah kema ya baki ikon kammala littafinki lafiya Asanadin Maƙwabtaka😍and My P.A Munah Bature,ansha gwagwarmaya dae😂,ina matukar godiya agareki my other half😘_


To My Novel's Fans


Ba zan manta da yadda kuka rinƙa karfafa man gwiwa tsawon lokaci ta hanyar daɗaɗan Comment ɗinku,Summayer khutubi,Princess Bahilot,Meenarly Al'ameen,Oummi Sudeis,Asma'u Sani,Amjad (Mrs Rafayet),Maman shureim,ummu khaleel,maman aminu,Aunty hadiza,Xahra haroun,Hamida Yahaya ghandy,Asmieybash,Sadeeya attahuru kaoje,Zahra  da sauran waɗanda bansamu na lissafo sunayensu ba,ina sane daku,ina matukar godiya a gareku ur comments means a lot to me,

Members of Comment Section 1&2,bansan da wane kalmomi zanyi amfani wurin gode maku ba,sai dae ince Allah ya barmu tare don ku din kun wuce fans kun zama yan'uwana agareni,


*JINJINA Ta musamman Ga dukkan Masoyan Littafin  Abban Sojoji waɗanda suka Cire ƙyashi suka Biya kudin littafin Donsu karanta,ina magana akan Members Na paid group ɗina💃*


(1) Abban Sojoji 

(2)Abban Sojoji Vip 

 (3)Junaid Romeo(Takun ƙarshe)

 (4)Father Of Soldiars


*Allah Ya bar zumunci daga nan har Gidan Aljanna,Allah Yabiya maku dukkan bukatunku,Allah ya baku ikon Yin amfani da darussan dake acikin Labarin nan,Ina matuƙar godiya,Da irin haƙurin da kukayi,da kuma uzirin da kukayi mun har Allah ya bani Ikon Kammala Littafin nan,Yanzu gashi komai Ya wuce,Sai in Allah Yasa ina da rabon yin wani littafin kuma Ina fata zaku kasance A biye dani😰Zanyi missing dinku sosai*


*Littafin nan Ya ƙunshi darussa daban daban Na rayuwa,Ya ilmantar,Ya faɗakar,Ya kuma nishaɗantar damu💃💃💃*



*Wai ina mutanan dake cewa idan littafi yayi yawa ƙarshen shi baiyin daɗi😂da waɗanda kecewa Yayi tsawo yen yen yen Suka ishi mutane da surutu😂mahakurci mawadaci Yau dai Surutu akan Littafin Abban Sojoji Ya ƙare,No more Tsegumi No more Complain,No More typing No more Tension Boss Zatayi bacci hada minshari🥱🥱🥱*

   

*Hafsat Bature Muh'd*


  *Boss Bature*✍️

  

 *Ga masu Buƙatar Karanta Book na Abban Sojoji daga Book One zuwa 3 Complte Suyi mun magana ta whatsapp dina 0810388440*


No comments