Ubana ne ko Kishiyata Hausa Novel

 😭😔UBANA NE KO KISHIYA NA💔💔


WRITTEN AND STORY




           BY

NERNAH MARYAM

(MARTEY BEE)


Gargadi.....


Wannan littafin mallaki Na ne kuma bana yi shi don cin zarafin wani ko wata bane hasalima duk wanda ya ga ko ta ga labarin yayi daidai da tsarin rayuwar ta ko makamancin hakan to ina me bada hakuri,


Sannan ban yarda wani ko wata su juya mun labari Na ko su canza ba tare da neman izini Na,


Da sunan Allah me rahma me Jin kai,Allah yanda Na fara rubuta labarin nan lafiya Ubangiji ka sa Na gama shi lafiya,


..............

              Page one


**********Bauchin Yakubu


      GRA


Karan hayaniyan mutane tare da bugun gate in wani tangamemen gida ne yayi alarming securities in gidan kan bakin da me gidan ke expecting tun safe sun iso,


 Sunday ne ya mike tare da kallon mal Iro yace Iro I think they are here already make I do quick and open this gate before oga change am for me,dariya mal Iro yayi tare da bantaran goron sa domin shi Sam ba gane wanga turanci na Sunday yake yi ba,normal turanci ma ya ya kare da shi balle wata broken,


Shi ko Sunday cikin sauri ya tashi tare da nufan black gate in saida ya bude kofar ya leka ganin dandazon yan jarida ne ga sanya shi saurin bude gate in gaisuwa suka yi exchanging bayan sun shigo cikin premises in gidan,


 Masha Allah Na fadi sakamakon karewa gidan kallo da nayi,wata gida ne Wanda ya amsa sunan sa gida babban duplex building ne wanda aka kawata wajen gidan da flowers kaloli daban daban,kallo daya za ka yi wa gidan ka san mamallakin sa ba karamin attajiri bane domin duk layin zan iya cewa gidan Sen RILWANU AUDU WAZIRI .... Ya fi Na kowanne kyau,


Sa'eed ne ya fito daga cikin  main house in gidan sanye da black and white uniform, shine mafi kusanci da Senator Rilwan,


Cikin fara'a ya karasa gurin yan jarida domin an riga an San da zuwan su,sun zo ne domin tattaunawa da Sen RILWANU AUDU WAZIRI wanda aka tsayar a partyn su domin yin Takaran Gwamnan jahar Bauchi,ganin zabe ya karato  ne ya sanya ya hada zaman shi da kanshi domin bayyanar da wasu raayoyin shi tare da amsa wasu yan tambayoyi da suke ta son masa,


Ba karamin lucky da dadi yan jaridan da suka samu zuwa suka yi ba domin sun San ko banza bara su koma hannu Na dukan cinya ba domin Sen RILWANU an san shi da halin kyauta da son jamaa ka'ida ne duk wani Wanda ya zo ganin shi to baya zuwan banza,


Iso Sa'eed yayi musu zuwa ga wani babban Hall dake cikin gidan Wanda an yi shi ne daman domin taro,


Hall ne babba me kyau dauke da kujeru da Dan karamin tables Wanda ke dauke da snacks and drinks a kai,


Bismillah have a seat Sa'eed yace yana murmushi su din ma murmushin suka yi tare da fara kokarin zama,baran sanar da Sen zuwan ku kafin nan ku fara shan ruwa,


Ya wancin gurin ba karamin dadi suka ji ba domin ka je inda za a karbe ka a mutunta ka har a baka abun makulashe ma wani abu ne,nan suka hau Dan ciye ciye da dan shaye shaye kun san mutanan mu ba a ganin bati a bari lol....


Kusan 15 mints da fitan Sa'eed suka fara Jin alamun tafiya tare da magananganun mutane Wanda ya tabbatar musu gwamman goben su ne ke tafe,da sauri suka yi arranging kansu tare da kokarin setting cameras in su domin kowa so yake ya fara daukan sa a hoto,


Kofar aka bude Wanda securities in sa ne kusan su biyar a gaba sanye da irin same kayan da ke jikin Sa'eed sai wasu biyar in a baya sai kuma wasu mutane su uku a tsakiya ko wannan su ya hade cikin dakkakiyar shadda sai kyalli kawai suke zuba wa da kamshi,


Da sauri yan jaridan suka Mike suka fara daukan su a hato,daya daga cikin mutanan ke kirarin Senator Rilwan sai kayi gwamman mu Na gobe insha Allah sai ka mulki jahar Bauchi...


Wanda ake kira da Senator RILWANU AUDU WAZIRI Na bi da kallo,masha Allah na furta sakamakon ganin babban mutum me kamala sanye yake cikin farar shadda Wanda ta ji aiki da brown zare ta ko xauna masa damas a jiki duk da shi din ba ramamme bane ba kuma za a kira shi da kato can ba,


Brown hula takalmi tare da links ne a jikin sa,saidai duk gayun nan da ya ci yayi lacking Abu daya shine murmushi,


A cikin yan jaridun ne daya ya kalli daya yace Salman ya haka yau kamar abunda ke damun Sen domin daga fitowan sa jikin shi a sanyaye and ka dubi fuskan shi ko digon faraa babu bayan kuma shi mutum ne me yawan faraa,


Hmm Tahir manta kawai ni kaina jiki Na yayi sanyi domin tun duban farko da nayi masa na gano damuwa lulube a fuskan sa,ni dai ko ma miye ke damun shi Allah ya sa kar yayi affecting Alkhairin da zai mana,


Daya daga cikin yan jaridan ne ya tashi tare da mika gaisuwa bayan  Alhaji Rilwan ya zauna tare da manyan Aminan sa guda biyu,Alhaji Salis da Alhaji Kabiru,


Nan suka shiga masa tambayoyi akan zaben da ke tahowa ya yake ganin abun zai kasance tunda yana da abokan hamaiya dukda ma shi din mutum ne me Alkhairi hannun sa a bude yake ya sanya mutane ke kaunar sa sosai,


Mikewa yayi sai a lokacin Na ga yayi murmushi farko dai da sunan Allah ya fara sannan ya mika godiya sai kuma ya fara jawabin sa kamar haka......


Hakika farin jini da soyayyan da ya samu a gurin mutane daga Allah ne domin in za a tuna sanda ya fito neman senator haka nan mutane suka yi ta kauna shi,ya gode wa Allah da irin daukaka da nasarorin da ya samu a rayuwar sa sannan ya Na mika godia ga dumbin jamaar garin Bauchi bisa yadda da kaunar da suke nuna masa kuma in sha Allah muddum ya zama Gwamma to zai yi mulki bisa tsoron Allah zai kaunaci talakawan sa zai.nan dai yayi ta jero irin cigaban da zai kawo wa garin Bauchi,


Nan ko aka sanya tafi ana fadin sai kayi Gwamma in sha Allah uban marayu kuma gatan Bauchi,


Dan gurban ruwa yayi sannna ya cigaba da jero jawaban sa ,yanda Hall in yayi tsit baka Jin muryan kowa sai nashi,


Kamar daga sama suka ji an banko kofar Hall in kafin securities su kai ga sanin waye har ta shigo,


Sanye take da ash in dogon rigan material kanta ko dankwali babu dogon bakin suman kanta ya kwanto har kafadun ta,kafafunta ko slippers babu,da gudu ta hayo kan stage in,


Kallon Sen Salis yayi yace Alhaji kamar Princess nake gani lafiyan ta kuwa??


Wata kallan gumi ne ya tsattsafo wa Sen a fuskan shi wanda ya sanya bayan hannun sa ya goge ji yayi wani irin balain ciwon ciki da zafi ya durnuke shi lokaci daya duk da uban AC's in da ke cikin Hall in,


Tafi ta shiga yi hannuwa bibiyu tana yi tana fadin wow wow nice one, so tsayawa kuka yi don kuma baku da aikin yi irin sa yana cika ku da maganganun karya da yaudara ku kuma kuna saurara kuna cewa sai yayi sai yayi me.ta kare cikin murya me karfi idanun ta jajjawur hawaye Na zuba,


Wannan mutumin ne wai har kuka tsayar matsayin Dan Takaran ku wai wannan mugu mara mutuncin mutumin Wanda babu ko dikon tsoron Allah a tattare da shi kuke so yayi mulkin jahar Bauchi inalilahi wa ina ilaihi raju'un da kuwa masifa da bala'i ta afku a garin nan,


Cikin sauri Alhaji Kabiru ya tashi yace keeee  NADIYA kina da hankali kuwa wani irin shashanci da iskancin banza ke damun ki ko dai kin yi shaye shaye ne in to hauka kike to kiyi maza ki dawo hankalin ki uban ki mahaifi kike jefa da irin wanna kalmomin,


Cikin sauri ta katse shi da ka dakata mun karamin Dan iska ai ba da kai nake ba sarai Na san waye shi, Dan juyi tayi tare da nuna SEN in tace wai ko ba the greatest SEN RILWANU AUDU WAZIRI ba the most richest man in Bauchi ko ba shi ba,Wanda a idanun duniya yake Na Allah amman a badini fa,Allah Ubangiji ya tsine maka Daddy ya Allah Na roke ka,ka  hada shi  da masifan duniyaa da ba lahira babu masifa kamar kasancewa yar ka da nayi I regret being Ur daughter you are indeed a disgrace to all fathers around the world da yardar Allah bara ka taba samun mulkin jahar Bauchi ba yanda ka tarwatsa mun farinciki Na Allah ya tarwatsa naka I hate you so beyond word,


Da sauri Sen ya runtse idanun sa Wanda hawaye suka taru a ciki,


 Alhaji salis ne yayi alama da hannu wa Sa'eed su fita da ita mana domin ganin yan jaridan attentions in su duka Na kanta,da sauri suka nufe ta,don't touch me wawaye jakuna kun saida wa  imanin ku da lahiran ku ga wannan mugu Azalumin mutum,ta nuna Sen,


 Kama ta suka yi da karfi tana tirjewa tana kuka tana aunawa Sen zagi tare da dibe masa Albarka zagin sa take ta uwa ta uba tana kiran sa da mugayen sunaye Wanda duk Wanda ke gurin sai da jikin su yayi sanyi,



Ku tashi ku bashi guri dumin associating da irin wannan wlhy kan jawo talauci da kassanci ni dai shawara Na baku shine kalman NADIYA Na karshe kafin su Sa'eed suka fidda ta,


Wato yanda ka san anyi ruwa an dauke haka cak jikin kowa ya koma a cikin Hall in baka Jin komai sai sheshekan SEN RILWANU AUDU WAZIRI wanda ya kifa fusakan shi bisa tafukan hannun shi yana kuka,


Ba shi kadai ba jikin gaba daya yan jaridun yayi laasar domin wannan ba karamin abun girgiza da alajabi bane,ace 'Ya daya dilo a gurin Sen RILWANU ne ta fito ko Dan kwali babu tayi masa irin wannan mugun diban Albarkan kan kowa ya kulle,


Da kyar daya daga cikin yan jaridan ya mike tare da cewa yallabai ko za ka iya mana karin bayani game da abun da Hajiya NADIYA ta gama fadi,


Mikewa yayi ya kalli Dan jaridan idanun shi yayi jawur har ya bude baki kawai ya girgiza kai tare da Saurin fice wa daga Hall in domin ya cigaba da zama zai iya fashe wa da kuka bin shi suka yi suna yallabai yallabai ina ko sauraran su be yi ba,ya fice cikin sauri yana baza babban Riga Adduar shi daya Allah sa ba a dauka abunda Nadiya ta fadi ba in ko an yi hakan shike nan tashi ta kare magauta sun yi nasara a Kansa,



Duk yanda suka so su ji wani abu daga bakin Aminan sa kala basu ce musu ba domin har yanzu cikin shock suke,Sa'eed ne yanda ta musu jagora suka shigo haka yayi musu suka fice daga gidan zuciyar kowa da abunda ke sakawa game da abunda ya faru duk yanda aka yi akwai boyayyan alamari a kasa ammann babu me basu wannan amsoshin sai shi kan shi SEN in ........



   Toh fa wannna alamari da daure kai yake ace ya ce ke jifan uban ta mahaifi da irin wannan kalomin..


Ku biyo ni a sannun cikin wannan tafiya me cike da sarkakiya ,Na San ko wannan ku zai cika da tambayoyi Wanda Na tanadi amsoshin shi tsaf,😁

 

Ga masu son a tallata musu hajojin su za su iya tuntuba ta ta wannan layin:

                    08100046388.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA NA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM 

(MARTEY BEE)


I Dedicated this whole book to you my dearest ummu Mansur (uwar daki na🥹❤️),I love you so beyond words ........


My What's app group


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK

..............

              Page two


***************


Falmata!! Falmata ihun kiran sunan ta Sen ke yi daga ganin yanayin sa kasan yana cike da tsantsan bacin rai,


Jiki Na bari Na ga wata yar dattijiwa ta fito tana goge sauran ruwan dake hannun ta a jikin zanin da ke jikin ta alamun daga kitchen ta fito,


Gaban Sen ta zo tare da zubewa jikin ta Na rawa domin ko be fada ba ta san yau ta kade,


Kallon ta yayi Na yan seconds sannan ya ja tsaki ya watsar,cikin bacin rai da hargagi kamar ba shi ne mutumin ya gama magana cikin tattausan murya a gaban yan media dazu ba,


Da yatsar sa manuniya ya nuna ta sannan yace Ashe Falmata baki da mutunci ban sani ba,jikin ta Na rawa tace tuba nake uban gida Na wlhh tallahi ban san lokacin da uwar daki Na ta mike ba zato Na duk tana bacci Na shiga kitchen domin samar ma abun da za ka ci in kun gama taro sai kawai shigowar ta Na gani da su Sa'eed,


Dallah rufe wa mutane baki yar iskar mata kawai one task kawai Na baki shine lura da princess tunda Na sanar da ke ina da taro yau Amman kin shiga wai kitchen dafa abinci ai ko kin dafa abincin karshe ke nan domin yau din nan zaki bar gidan nan ya kare kamar zai duke ta,


Nan take ta hau kuka tana rokon shi Allah Annabi kar ya daga ta daga gurin neman Halal inta shekaru kusan nawa tana masa aiki yayi hakuri yayi over looking mistake in nan da tayi wlhy ta dauka NADIYA bacci take har yanzu duba da kwanan ta biyu tana bacci bata farka ba so bata dauka za ta tashi yanzu ba,


Alhaji Salis ne yace ya isa haka Sen is of no use ka tsaya kana venting anger in ka akan wannan worthless matar,let's go and face our problem ya fada calmly,


Tirjewa SEN ya ke yi while Salis Na jan shi domin barin gurin don ya ga alaman ranshi yayi kololuwa gurin baci,


Da kyar dai ya samu suka bar gurin bayan Salis ya ce da Falmata dake ta faman rokon SEN ta tashi ta koma kitchen ta cigaba da aikin ta,


Har sun kai ga shiga part in shi ya hango Sa'eed,kamar Wanda aka tsikara yace Salis kira mun wancan useless boy in, daga gurin Alhaji salis yayi wa Sa'eed magana kan ya zo SEN Na son ganin shi,


Da sauri kuwa ya karaso yanda suke tsaya cike da girmamawa ya dan rusuna yace Allah ya ja da ran ka gwamman mu Na gobe,


Gwamnan uwar ka SEN yace cikin tsantsan bacin rai bayan ya wanke Sa'eed da wata zazzafan Mari,da sauri ya dafe kuncin shi don ba karya Marin ta shige shi,


Don uban ka Sa'eed me kuke yi har NADIYA ta samu damar shigowa cikin press  confirence ina,nace uban me kuke yi ,


Kan shi Na kasa yace yallabai wlhh ba laifi Na bane laifin Muktar ne tunda su na bari a waje ni kan ba ina tare da kai a ciki ba,


Cikin bacin rai SEN yace Salis ka duba ka ji wannan wawan yaro yake fada mun waye chief security ina ba kai bane ya ci ace duk kai za ka kula da komai wlhy in har wani abu ya samu kujera ta wlhy tallahi gaba dayan ku baran raga muku ba shashashu kawai Wanda basu San yanda ke musu ciwo ba,


Jan hannun shi Salis yayi yace don Allah RILWANU stop all this is not that necessary ta ho mu shiga ka samu ka sha ko ruwan sanyi ne,


Bayi da option sai bin bayan Alhaji salis in Wanda ke matsayin Aminin shi kuma mataimakin shi domin shi ya tsayar as deputy governor in shi,ko ba don komai ba ya ci ya jiga makoshin Na shi don ba karamin bushewa yayi ba,


A tangameman parlor in shi da ya gaji da tsaruwa suka ya da zango,fridge ya bude tare da dauko bottle water me sanyi ya zuba masa a glass cup tare da mika masa have a sip yace da shi calmly,


Ba musu Sen ya karbi cup in ruwan tare da nufan bakin shi sa cup in Sai kuma ya tsaya kallon Salis yayi yace Salis wat will happen in har shegun yan jaridun nan sun yi recording scene in da  princess ta gama yi,


Numfashi Salis ya ja tare da zama kusa da shi yace kai I don't think za suyi shooting because gaba dayan mu are shocked am sure harda su ina za su samu daman dauka, Allah sa ba Wanda ya dauka domin in har an dauka yadawa za suyi a duniya and muddum aka yada shike nan makauta sun samu nasara akan mu,


Da yardar Allah bare ma faru that way ba just be faithful my friend,dan shiru suka yi duka kafin yace yanzu ina ita princess in,


Cup in hand in shi ya aje tare da furzar da iska yace an mata alauran bacci,


Gyara zama salis yayi sannan yace wai ni kam me ke damun NADIYA ne lfyan ta kuwa ni dai sani Na da ita bata da wata cuta da ya shafi brain inta balle nace shine ya tashi mata,


Ajiyar zuciya SEN ya sauke sannan yace wlhy Salis karan shigowar waya ce ta katse mishi abun da yayi niyan fada,tare da zaro wayar tasa daga aljihu,


Ganin Wanda ke kiran sa saida gaban shi ya fadi ba kowa bane illa shugaban party in su,Na shiga uku shine kalman da ya fadi be ma San ya fada ba,dafa shoulders in shi Salis yayi yace ka dauka komai zai tafi daidai,


Dauka yayi jiki ba kwari,gaishe shi yayi inda yayi sauran tsayar da shi ta hanyar cewa SEN RILWANU shin ka shiga social media kuwa yau,idanu ya runtse yana fatan ba dai video in abunda NADIYA tayi masa ke trending ba,


Cikin sarkewaan murya yace aa ranka ya Dade ban shiga ba wa niiii abuunnn ne ya faruuuu ya fada da kyar,


Lalle RILWANU au baka ma San me ke faruwa ba ko to gaba daya kafofin sadarwa Na duniya kama daga kan Twitter Facebook YouTube Instagram video in ka ne kawai yake trending wani irin shirme ne haka ace a dauki yarinya ka tana maka zagin tsamen nama a gaban media Inalilahi,Anya ba muyi zaben tumin dare ba kuwa za ka jawo bacin sunan party in mu daman can kai ba mutumin kirki bane wai,


Cikin tashin hankali yace yallabai kar ka ce haka wlhy tallahi nima yanda kake cike da mamaki haka nake Sam ba haka princess take ba duk Wanda ya sanni yasan akwai kyakkyawan soyayya da kauna tare da shakuwa tsani na da tilon yarinya ta,wannan definitely sa hannun magauta ne an ga nasara da daukaka Na tattare da ni,but don Allah sir kayi hakuri a kuma bai wa yan party hakuri in sha Allah I got this I can control it duk me nema Na da sharri Na fi karfin shi,


Hmm shike nan gaskia try your best ka wanke kanka domin wlhy banda maganar ka babu abunda ake yi a media kowa da irin abunda yake fadi son ranshi ka ga kuma kujeran gwamma ba karamin kujera bane,


Hakuri ya bashi tare da bashi assurance zai kawo karshen matsalan gobe in sha Allah,suka yi sallama tare da kashe wayan,


Wata irin wawan jifa yayi da wayar ta bugi bango nan take kuwa ta tarwatse,cikin ihu yace damn it meyasa haka zai faru da ni why za a yi using NADIYA ta domin bata mun siyasa ta why my baby ,rike shi Salisu yayi yace calm down in sha Allah za muyi coming over this,


Shiru yayi yana ta Dan nazari kusan Na mintuna sannan ya mike yace Salisu thank u so much you can take za ka iya tafiya,kace da Kabiru ina son ganin shi in ka fita,okay Ranka ya Dade a huta lfy Allah ya kyauta Na gama yace tare da barin parlor in cike da mamakin me ke damun Nadiyar har haka,


A hanyar fita daga gidan ya hadu da Kabirun sanar da shi yayi ya je part in Senator yana son ganin shi,da toh ya amsa suka yi saying good bye in su don shi Salisu gida zai koma,


Shi ko Kabiru kai tsaye part in Senator ya nufa inda ya tarar da shi ya kasa zaune ya kasa tsaye,


Dafa shi yayi yace SEN take it easy sanin kan ka ne dai over thinking baya solving problems, cikin murya me rauni yace Kabiru ya kake son nayi dazun nan shugaba party ya kira ni har yana ce mun sun yi Dana sanin tsaida ni zaa iya kwace ma kujera na a tsaida wani,


Calm down ba wanda ya isa ya kwace ma kujera yan gari ai suna bayan ka,wani irin baya Kabiru bayan an samu Dan iskan da ya yada video in nan yanzu haka shike trending a duniya,


Whattttttt Kabiru yace yana zaro idanu shegu tsiyan yan jarida ke nan munafurci Amman ba komai we got this in control zauna ka ji yanda za aka yi,


Nan ko SEN ya zauna shima Kabirun zama yayi suka shiga tattaunawa game da yanda za a yi,sai ga SEN har yana dariya suna tafawa da Kabirun ganin sun kawo karshen matsalan nan,Kabiru be bar gidan  SEN ba sai dab Magriba akan gobe yana so ya kara gayyato masa yan jaridun zai Kara tattaunawa da su a haka suka rabu ya tafi gidan shi akan sai zuwa goben,


Around 10 Na dare


   Senator RILWANU ne zaune a bakin gadon da NADIYA ke kwance kallo daya za ka mata ka gano baccin wahala kawai take yi,hannun ta Na cikin nashi ya tsurawa fuskan ta ido yanda take sauke numfashi a hankali, idanu ya damke da karfi tuno irin munanan kalmomin da ta jefe shi da su dazu da safe,



Hawayen idanun sa ya goge da hannun daya Allah ya isa miki princess ita an cuce ni wlhy dake an ga ba yanda aka iya da ni shine aka biyo kan abunbda Na fi kauna duk rayuwa ta,shiru ya dan yi tare da shafa kanta don't worry my love you will get well in no time,am so sorry baby but I have to do this I got no option ki yafe ni princess ita ya kare yana hawaye tare da daukan wayan shi tare da danna wata lamba,



Ringing uku aka dauka cike da girmamawa doctor Bashir Ubaidullah ya gaida Senator,amsawa yayi yace yauwa Doc kana jina make sure gobe karfe 11 Na safe ku iso gida Na ku tafi da ita domin haukan da ta mana yau ta baki ma bare iya fadan shi ba ya kare yana breaking down into tears...........



Kar amanta ana sharing sabida da Allah 


Gama su son a tallata musu hajar su za su iya mun magana ta wannan no in 


       08100046388.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA NA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY 

NERNAH MARYAM

.........


My what's app group


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


Don Allah duk wanda ta san bara tana yin comment ba to don Allah kar tayi joining, sannan wannan group in Na mata ne zallah banda maza don Allah🙏🏻,


Ga ma su son a tallata musu hajojin su, za su iya mun magana ta wannan no:

                 08100046388


.............

             Page three


*************


Karfe goma daidai doctor Bashir ya iso cikin gidan SEN shida workers in shi a cikin motan daukan marasa  lafiya wato (Ambulance),


A zaune suke a parlor in SEN daga ganin alamun su tattaunawa suke me matukar mahimmanci,


Doctor ne ya dago tare da kallon SEN yace ranka ya Dade ban ki ta taka ba saidai ina Jin tsoron abunda ke iya zuwa ya zo,


Look Bashir we do trust u ne ya sanya har muka damka amanar princess a hannun ka so pls don't let us down,Kabiru ya fadi yana kallon cikin idanun doctor,


In sha Allah Alhaji I will not let you down yanda kuka ce hakan za a yi,cike da alhini Sen yace I still can't believe this wai Nadeeya Rilwanu audu waziri ce tayi hauka ya salam,don Allah doc do take care of my princess for me I don't mind spending ko nawa ne ni dai all I want shine ta dawo normal ya kare kamar zai yi kuka,


Patting bayan shi Kabiru ke yi yana haba my friend be a man mana Na san da ciwo sosai ko dan kasancewar ta ya daya tilo a gurin ka ammman we are doing this for her own good,so allow the doctors to do their job pls,


Numfashi ya sauke sannan yace yeah haka ne you gat some point ne dai all am saying here is Bashir ka kula mun da princess kar a samu wata matsala make sure duk abubuwan da Kabiru ya sanar maka ka gane ko,


Da sauri Ubaidullah yace yeah sir Na gane in sha Allah bara a samu ko wani matsala ba ai mun sha dealing da cases in da ya fi Na princess ma in no time za ka ga ta samu lfy,


Nan take Kabiru ya ciro wayan shi tare da masa transfer in mil 5,debit alert ya nuna masa sannan yace ga shi for a start mu dai fatan mu komai ya tafi daidai and ta samu lfy make sure a siya mata duk abunda take so extra kula nake so ku bata,


Nan take ya washe baki tare da zaro idanu Jin huge amount in da aka ambata hakan ma wai for a start wow harka da gidan gwamnati akwai samu ya fadi a can kasan ranshi,while a fili kuma godia yake ta zuba wa tare da Kara jaddada musu kan cewa babu wata matsalan da za a samu daga Gare shi his daughter will be safe and sound,


Mikewa SEN yayi yace okay in dai haka ne ai no need of wasting time mu je ku tafi da ita kawai,


............... Nadeeyah


Ba yanda Falmata bata yi da Nadeeya ba kan ta tashi daga kwanciyan kukan nan da take yi tayi wanka ta sauya kaya ko itama ta ji dadin jikin ta domin Sen ya aiko ace da ita ta sanya Nadeeyan wanka za a tafi da ita,tayi kuka sosai tare da tofin Allah tsine ga duk me sa hannu a samun rashin lfyn Nadeeyan,


Kallon ta Nadeeya tayi da red eyes in ta tace wai Inna Falmata ke ma kallon mara lfy kike mun,wai me yasa kun kasa gane wancan mugun mutumin azzalumi ne,I thought in duk duniya sun kasa fahimta ta ke za ki fahimce ni duba da irin shakuwar da ke tsakanin mu,ta kare tana kuka don Allah Inna Falmata kar ki bari a kai ni ko ina tunda ke ma kin ce baki San yanda za a kai ni ba ni fa lafiya ta lau ta kare tana share hawaye,


Ita din ma Inna Falmata hawayen take yi tana Allah ya baki lafiya uwar daki Na tabbas an cuce mu an zalunce mu,in ba haka ace duk irin shakuwa da soyayyar dake tsakanin ki da Ranka ya Dade ace ki masa irin wannan diban Albarkan??,


Jin knocking in kofar da aka yi ne ya sanya ta mike wa da sauri Nadeeya ta  riko ta tana rokon ta don Allah kar ta bar ta,jiki a sanyaye tace yi hakuri uwar daki Na ina zuwa da sauri ta bar gurin don ta cigaba da zama kuka za suyi ta yi,hakika ciwon nan Nadeeya ke yi amman har cikin Jinin jikin ta take Jin zafi da radadi,


Bude kofar tayi ganin SEN ne da kanshi ya sa ta zube tana gaida shi ko amsa wa be yi ba yace ya Falmata ta shirya don za su tafi ne,aa ranka ya Dade tun safe nake binta tayi wanka amman Sam taki yi ko tashi taki balle tayi wankan sai kuka da sumbatu kawai take yi marasa dadin ji,


Goshin shi ya shafo sannan yace kai Nadeeya ina ba dai taurin kai ba,daman can ya balle yanzu ya hadu da lalura,matsa baran shiga da kaina,


A hankali ya shiga cikin dakin zuciyar shi Na bugawa domin daga jiya zuwa yau yar ta shi tsoro ta koma bashi,


A kwance ya same ta ta kifa fuskan ta a cikin hannuwan ta yana jiyo sheshekan kukan ta,


Zuciyar shi a karye ya zauna bakin gadon tare da dafo kafadunta da hannun shi,yace Nadeeyan Daddyn ta,


Da sauri ta buge hannun nashi tare da Saurin Mike wa ido cikin ido ta kalle shi tace kar ka kuma taba ni da wannan kazaman hannayen naka mara tsoron Allah,


Baki a bude yake kallon ta yace princess yau ni kike kiran hannaye na masu datti ,hannun da ya Raine ki ya koya miki tafiya ya ciyar da ke ya wanke ki,haba Nadeeya ta,


Cikin tsawa tace I beg u  in the name of Allah to drop this act ai wlhy an yi walkiya Allah ya tona ma asiri zan so duniya su San kai wani irin mutum ne wlhy ka sanya fuskan mutunci kana yaudara da zalumtar bayin Allah,in sha Allah Allah bare bar ka ba yanda ka tarwatsa mun rayuwa kai ma,dakatar da ita yayi saurin yi domin ji da yayi zuciyar sa Na kokarin bugawa,ya isa haka ko ma miye za ki ce baran ga laifin ki ba domin ba a cikin hankalin ki kike ba Allah ya isa an cuce ni,Allah ya baki lafiya my baby girl am so sorry I have to do this ni ma ba don raina ya so ba ya kare a raunane tare da cewa doctor you can come in,


Nan ko doc Bashir da wasu murdaddu majiya karfin mataye sanye da uniform su biyar suka shigo dakin,


Go get her shine abunda Bashir yace da Matan,


Jin haka ya sanya Nadeeya birkicewa ta dauko bed side lamp in ta ta rike tana rantsuwa akan duk Wanda ya taba ta sai ta kashe shi ita she is not mad,juyar da kai SEN yayi cause his heart bare iya daukan hakan ba,


Tsayawa cak suka yi matan suna kallon ta,tsayawa kallon ta za kuyi ko za ku dauko ta kun taba ganin mahaukacin da ya amsa kan cewa shi mahaukaci ne?dallah kuyi sauri kar ku bata mana time,


Nan fa aka shiga kokuwa inda Nadeeya Sam taki yarda su kama ta banda ihun neman ceto da kwala wa Inna Falmata kira babu abunda take yi,a garin haka har ta fasawa biyu goshi,ganin tana bata musu lokaci ne ya sanya doc bashir tsikara mata Alluran kashe jiki,in da a take ta kwalla ihu tare da zubewa a kan gadon,


Nan take jikin ta ya mutu in da ba wasting time suka dauko ta tare da fitowa da ita daga dakin,


Duk Wanda ke gidan saida ya zubda hawayen tausayin hajiya Nadeeya kar Inna Falmata ta samu labari tana ji tana gani aka sanya ta a bayan Ambulance,


Kusa da ita SEN ya zo tare da mata kiss a goshi sannan yace am so sorry my love,in sha Allah za ki samu sauki zan Na zuwa duba ki take care of your self for me I love you so much,ya kare yana hawaye


Ji take wata wutan tsanan shi Na Kara ruruwa a ranta tabbas da da akwai wuka a gefen ta sai ta luma masa,


Doctor make sure to take care of my daughter ita kadai Gare ni ina matukar kaunar ta,in sha Allah kar ka samu damuwa Alhaji shine kalman doctor Na karshe kafin ya shiga mota,


Ina ji ina gani aka rufe ni tare da Jan motan aka bar gidan mahaifina da ni,ban San ina yace su kai ni ba kila ma kashe ni za ayi halan yau ne Jan numfashi na Na karshe a duniya, tabbas da da yanda zan yi da Na gudu Na tafi wata nahiyar daban Na fara sabon rayuwa ta yanda babu Wanda ya sanni Amman kash ni tawa kaddaran da haka ta zo mun,


Fitan su yayi daidai da isowan yan jaridun,Wanda cike da mamaki suke bin motan ambulance in da kallo zukatan su fal da tambayoyi,


Kai tsaye Sa'eed ya wuce da su confrence Hall in SEN yanda suka yi taro jiya zaman su da be fi da 5 mints ba sai ga SEN ya shigo da makarraban sa,


Sai da suka zauna yan press suka mika gaisuwa sannan SEN ya mike da kanshi,


Gyaran murya yayi daga kallon yanayin sa kasan ranshi a tsantsan bace yake domin babu ko dikon faraa a fuskan shi, idanun shi sun yi jawur alamun ya sha kuka har ya gaji,


Kamar kullum da sunan Allah ya bude taron sannan ya fara magana kamar haka,


Hakika nin gaskia ina kara gode wa Allah da ya bani adon rai da lafiya har nake tsaye a gaban ku,nasan daga ku har aluman gari gaba daya kun zaku ku ji kundin labarin game da abunda ya faru jiya a gida Na,Wanda ko a tarihi ban taba Jin makamancin hakan ba har wasu Na tantaman Anya wannan yarinyar sa ce ko wasu suce Anya wannan asalin uban ta ne,


Numfashi ya sauke sannan yace tabbas Nadeeya yarinya ta ce ita ce ya daya tilo Wanda Allah ya mallaka mun Wanda nake son ta fiye da rayuwa ta,


Tabbas mulki daukaka arziki suna da shahara duk Na Allah ne,shi ke azurta bawan sa a sanda ya so kuma ya talauta shi sanda ya so,shi ke bada mulki kuma shi ke hanawa,


Soyayya da daukaka ta da kuma farin jini Na duk daga Allah ne,ni Na yarda da hakan,


Sannan duk Wanda ya sanni ya San ni mutumin arziki ne ba wai yabon kai Na nake ba,Amman an sani ina da kyakyawan muamala tsakanin Na da mutane Na,Wanda gama daga iyalan gida Na,abokai Na maaikata na, makota Na kai da ma sauran mutane baki daya,


Hakikanin gaskia duk musulmin da yace yana zaune Allah be jarabban sa to ya duba imanin shi,ni Na yarda da jarabawa kuma a shirye nake Na karbe ta ko ya yake,


Ni ban taba nufan kowa da sharri ba a rayuwa ta hasalima duk Wanda nake tare da shi da zuciya daya nake zama da kowa,sai dai kash an samu wani mara tsoron Allahn mara imani da ya jefi yarinya ta,


Woto an yi anyi a kassarani Allah be bada saa ba sai aka biyo kan abunda nafi kauna a rayuwa ta sabida an san cewa Nadeeya ta ita ce weak point ita,


Tabbas Nadeeya ce rayuwa ta kuma duk Wanda ya San ni ya San akwai tsantsan soyayya da muguwar shakuwa me karfi tsakani Na da tilon diya ta,wanda wasu ke cewa tun bayan rasuwar mahaifiyar ta yau fiye da shekaru 20 Na kasa Kara aure sabida gudun kar a cutar mun da ita,


Hawaye ya kuma sharewa sannan ya daura da fadin ban taba expecting akwai Randa ko Nadeeya giyan wake ta sha zata iya sauraran wasu Na zagi Na bata dau mataki ba balle ace ita da kan ta,tabbas ba cikin haiyacin ta take ba,domin am her role model,


Tabbas an cuce ni an kuma zalunce ni an yi hakan ne domin bata mun siyasata Wanda sun manta Allah shi ke bayar da mulki ga Wanda ya so,


Ni muslmi ne Na yarda akwai kaddara sannan baran zargi kowa ba ,saidai na bar duk Wanda yayi aikin nan da fitowan Rana da faduwar sa domin an cuce mu my innocent baby dole Na kira kwararan likitan brain don ya zo ya tafi da ita asibitin mahaukata,domin bata taimako don she is mentally unstable, ya kare yana kuka sosai,


Riko hannun shi Salis yayi yace is okay ba komai akwai Allah suna ganin sun karya mu ne don sun haukatar mana da yarinya Amman sharrin su kan su xai koma da yardar Allah,


Ba su kadai ba hatta ni jiki Na sanyi yayi,domin ganin yanda Sen ke kuka yana maimaita kalman an cuce shi ba zai taba yafewa ba in takarar ne ba a so yayi ai da ba a biyo ta wannan hanyan ba,


Gaba daya yan jaridun nan tausayin shi nee ya kama su,haba daman saidai in jifan Amman duk wani xan garin Bauchi ya San waye Senator RILWANU AUDU WAZIRI mutum ne me tsoron Allah da kuma mutunci,Sam kallmomin da yar sa ta jefe shi da su basu yi daidai da shi ba,kawai magauta ne suka yi hakan domin bata mishi siyasan sa kai mutane ba a tsoron Allah akan neman duniya ace a jefi yar mutum ta zo cikin bainan nasi ta kwashe masa Albarka haka,gaskiya Allah ya zaka maka shi ne abunda wasu ke ta fadi,


Wani daga cikin yan jaridun ne ya mike tare da cewa ran ka ya Dade in har da gaske ne jifan Hajiya Nadeeya aka yi,to ai magungunan gargajiya ya kamace ta ba wai asibitin mahaukata ba.....



Assalamu Alaikum mutanan arziki, ina yi wa kowa fatan Alkhairi da kuma fatan anyi zabe lafiya Ubangiji ya zaba mana shuwagabannin kasa Na gari,


Hakikanin gaskia ina matukar godia ga irin karba da kuma soyayyar fa kuke nuna wa littafi Na,Ubangiji ya sakar wa kowa da Alkhairi, ina kaunan ku fisabillah,


A cigaba da sharing pls,


 Sai ranar Monday kuma in sha Allahu.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA NA💔💔


WRITTEN AND STORY 

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEY BEE)


 .........


My what's app group


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


Kofa a bude take ga duk me son joining saidai duk wacce ta san bara ta Na sharhi ba to don Allah ta zauna ba sai tayi joining ba,and don Allah maza should stay away from this group domin Na mata ne zallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su kofa a bude take,suyi mun magana ta wannan no:

 

          08100046388


............

           Page four


***********


Ranka ya Dade in har da gaske Hajiya Nadeeya jefan ta aka yi to ai magungunan gargajiya ya kamace ta ba Asibitin mahaukata ba??


Tambayan da wani Dan jarida ya jefo wa SEN ke nan,


Madadin ya amsa shi da kanshi Alhaji Kabiru ne ya mike ran shi a Dan bace yace wai why are you people after rayukan mutane ne,can't you see irin stage in da yake and you guys are trying to rub salt on his wound,da wannan silly questions in naku,


Dafa shi Sen yayi domin ya san halin Aminin nashi da Saurin hawa and hakan ba karamar barazana bace ga siyasan sa,


Cikin calm voice yace allow them su tambayi duk abunda suke son tambaya,tunda ai ni daa kai Na Na gayyato su,beside ai ba wani tambayan ban haushi yayi ba,yana da gaskia don kowa ya ji statement ina ya kuma ji gidan mahaukata aka aika princess dole yayi mamaki,


Pardon my friend's behavior kasan ance,abokin da zai taya ka kuka yayin da wani abun rashin dadi ya same ka shine Aminin ka Na ainihi,


Kamar yanda ka tambaya yeah jifan Nadeeya ta aka yi Wanda duk mun sani Asiri gaskia ce tunda har fiyayyen halitta ma an masa ta kama sa,and kamar yanda ka fada haka ne maganin gargajiya ya kamaci Wanda aka jefe,saidai wannan jifan ta sha banban,


Domin a sanadin haka brain in Nadeeya ya tabu tabi Me girma ma,ya kare yana share hawaye,Wanda bani da option sai dai dole a kaita asibitin su fara magance wannan matsalan domin wani jijiya da Is connected to her brain yaa samu matsala Wanda ya ci a gyara shi domin ceto ranta,bayan nan sai a koma Na gargajiyar ganga ganga,duk da yanzun ma ba zama za a yi ba har sai an jira likita,


Wani ne ya kuma tashi domin yin wani tambayan,


Hannu Sen ya daga mishi tare da cewa don Allah ku bar Ni haka,bana cikin Jin dadi zuciya ta zafi take mun,ya ci Na sha magani Na kwanta ko zan samu hutu,domin yanda Na ga daran jiya haka Na ga Rana ko rintsawa ban yi ba,na gode sosai da zuwan da kuka yi,ina me bada hakurin rude behaviors in Nadeeya Na jiya,domin ba a cikin haiyacin ta tayi ba,Na yafe mata duniya da lahira Allah ya baki lfy princess ita,


Don Allah duk Wanda ya kalli video in nan make sure ya sanya Nadeeya Rilwanu Audu Waziri a addu'a,ya kare with pleading hands,yana cewa mu je Kabiru, make sure Sa'eed ka sallame su,da haka suka bar cikin confirence Hall in,


..........NADEEYAH


Ni dai tun ana tafiya ina tunanin ina wannan mutanan mara sa imani za su kai ni,har idanu Na suka lumshe bacci barawo ya kwashe ni,


Sun yi tafiyan mintoti kafin suka iso Teaching hospital dake nan garin Bauchi wato Specialist, 


Direct Psychiatric clinic suka nufa(wato bangaran masu tabuwan kwakwalwa),


Parking driver yayi a bakin clinic in,inda nurses in da Doctor Bashir yayi waya da su akan su fito da stretcher (gadon daukan marasa lfy),suna bakin gurin suna jiran isowan sa,


Bude kofa yayi yace where is Sister Kareematu,am here sis wata mata ta amsa tana daga hannu,


Maza ku dauke ta ku kai ta ku kai ta Isolated room in da Na miki magana akai,I hope an kai komai da komai da za ta bukata ko,domin wannan ba kamar regular marasa lafiya bane,wannan daban ce,don yarinya ce daya tilo a gurin SEN kin ga kuwa dole mu kula da ita yanda ya kamata,


Da mugun mamaki duk yan gurin ke kallon Nadeeya da ke kwance alamun bacci ma take abunta saidai daga yanda take baccin kasan Na wahala ne,


Mamaki suke yi me zai Kawo Hajiya Nadeeya Rilwanu Audu Waziri wannan asibitin a hakan ma wai mara lfy,rashin lfyn ma Na cutar brain,to wai yaushe ta haukace ne ma and miye silan haukan nata,shine tambayan da yawancin nurses in gurin ke wa kan su,


Tsawan da ya daka musu ne ya sanya suka ja ta a sukwane,kallon Sister Kareema yayi yace in kun kai ta meet me in my office, da toh kawai ta amsa shi sannan suka wuce,


Daki ne Na Alfarma Wanda saida nayi mamakin ganin dakin domin maraban shi da dakin gidan yan gayu kadan ne,domin harda T.v,Air con,table and resting chair,ga wata lafiyyar gado dauke da lallausan blanket akai color white and blue ga kuma drower in jera kaya tare da mini fridge sai kuma da  toilet a cikin dakin,


A gefen gadon kuwa chain ne daure(wato Ankwa),


A kan gadon suka aje ta tare shimfida ta,ido doctor Kareema tayi musu duk suka fice daga dakin banda,nurse Zaituna,


Kallon ta tayi tace Zaituna dauko mun uniform in ta a cikin drower muyi mu sa mata in yi sauri in je gurin wancan Dan tijaran kafin ya yi mun hayaniya nayi late,


Drower ta bude tare da dauko daya daga cikin jerin uniforms in da ke cikin gurin wanda Riga da wando ne kalan blue da fari,


Without waste of time suka tube Nadeeya tare da sanya mata uniform in suka gyara mata kwanciya tare da ja mata barko,


Shegiya Kareematu wato kwadayin ki ke hada ni da ke dake kin ga yar gidan maiko shine ke da kan ki kika sanya mata kaya ko??Zaituna ta kare tana dariyan shakiyanci,


Yo Zaituna ba dole Na ba kina ji dai yace mana yar gidan SEN RILWANU ne ai wlhy dole Na shege mata ko da zata kashe ni da duka Na samu Na yagi rabo Na halan in uban ta ya ga yanda nake kula da ita har kyautan gida da mota ya bani,ina dalili in cuci kai Na akan wayancan mahaukatan mutanan,da ba komai kake samu in return ba sai duka,ta kare tana dariya,daga haka suka bar dakin tare da rufe mata kofan,


Nan suka rabu ita Zaituna ta koma bakin aikin fa while Kareematu office in Doc Bashir ta nufa,



.......... SEN RILWANU


Amman Kabiru kana ganin karshen matsalan me nan ko,haba Amini na don Allah ka saki ranka bana son kana sanya wa kan ka damuwa am very sure by the time aka saki video in nan karshen matsalan mu ta zo sai dai mu fuskanci gaba,am very sure kiran wayan party chairman ne zai daga ka daga bacci gobe,


Ai tun farko ma mistake ne da wancan dan iskankan Dan jaridan ya dauki abunda ke faruwa,gashi gulman shi ya ja masa Na sanya a kamo mun shi sai Na ci uban sa daga yau bare Kara aikin jarida ba,


Da sauri SEN yace aa Alhaji Kabiru kar kayi masa komai don Allah ka bar abun nan kawai ya wuce kar mu kira damuwa wa kan mu,ba gashi komai ya tafi daidai ba,dadi Na da kai wlhy anger shi fa zaman duniya yar siyasa ce,


Hmmm ni kuma wannan sanyin kan ke bata mun rai wlhy ya kare yana girgiza kafa,but tunda kace haka shike nan bazan masa komai ba,


Hmmm Allah sarki Nadeeya ta ko tana wani hali yanzu sai Allah ya kare kamar zai yi kuka,


Dariya Kabiru yayi yace ni kan Anya na taba ganin mutum me son yarinyar sa irin ka kuwa,


Hmmm Kabiru bara ka gane bane wlhy Nadeeya rayuwa ta ce,saisa kiran wayan shi da aka yi ne ya katse mishi me yake shirin fada,share wa yayi ba tare da ya dauka ba domin wlhy ba karamin gajiya yayi ba,bacci yake son yi ma jira yake Kabiru ya tafi,


Jin an Kara kira ne ya sanya Kabiru yace ka dauka mana kila important call ne,be so ba ya dai dauki wayan,


Ganin No in United state of America ne ya sanya shi sakin murmushi domin ya San ba kowa bane Ila Afzaal,cike da shaukin ya dauki wayan,tare da cewa hello son,


A can bangaran ma Afzaal din cike da kauna yace Hi Daddy ya kake,ina lfy klau my son hope dai ba wata matsala ko,


Numfashi Afzaal ya sauke yace eh babu for now kam don kudin da Na tafi da su suna nan jibge,sai dai ina missing in ka ne sosai,ya kare kamar zai yi kuka,


Dan dariya SEN yayi yace ohhh Afzaal fitina ko Nima nayi missing in ka yaro Na,saidai abubuwa marasa dadi sun faru bayan tafiyan ka,domin Nadeeya hauka ne tuburan ya kamata yanzu haka ma Na kira doc bashir ya tafi da ita,


Oh good Ashe abun babba ne,ai ya wuce yanda kake zato,kai to Allah bata lafiya,ni dai yaushe xan dawo don Na fara gajiya da zaman USA??


Numfashi SEN ya sauke sannan yace not now son ka cigaba da zama har sai wannan kuran ta lafa tukun Na,zan sanya manager yayi maka transfer in 5mil make sure to take care of yourself bye,be jira amsan sa ba yayi ending in call in,


Kallon Kabiru yayi da ke cin abinci yace kai ka ji mun yaro ana ba guri yana ya kwanta wai dawowa yake son yayi,


Dariya Kabiru ya sheke da shi sannan yace ka ji Dan nema to ya dawo yayi me ana tsaka da wannan halin,oho fa ni kan zan shiga ciki Na huta mayi waya kawai,in ka fita kace da Sa'eed duk Wanda ya zo nema Na ace Na sha magani Na kwanta,kai kawai Kabiru ya gyada masa don ya cika shinkafa a bakin sa,


............Kaduna State


         44 barrack hospital ,


  Zaune yake shi kadai a cikin office in sa,sanye yake cikin white and black dress,shiru yayi tare da kura wa guri guda ido alamun he is lost in thought,


Ko karan bude kofan da shigowa doctor Mujaheed be ji ba,sai da ya taba shi tare da cewa Helllooooo wai tunanin me kake yi ne haka har baka ji shigowa ta ba,


Dago idanun shi yai masha Allah Na furta domin mutum ne me cikan halitta da haiba kyakkyawa dashi bara a kira shi fari ba haka zalika bara ace da shi baki ba,yana da long nose ba wai can ba kai in fact dai he damn cute and handsome,(domin duk creation in ubangiji banu munana),


Kallon Abokin Na shi yayi for some seconds sannan yace wlhy Mujaheed ya tabbata mutanan nan transfer za su mun hakan ma wai within 2 weeks,Doctor NAMEER ABDALLAH ya kare cike da bacin rai,


Numfashi Mujaheed ya sauke sannan yace ikon Allah kuma ina suka aika ka,


Dan guntun tsaki ya ja sannan yace wai Bauchi fa wata Teaching hospital nan aka jefa ni........


Aradun Allah Na gaji🤪,


Don girman Allah Arin ga yi ana kankaro mutunci gurin yin sharing and commenting🙏🏻,


Ina mika godia Gare ku masoyan littafin nan da kuma ni Na gode sosai Allah saka da Alkhairi,


Sai kun ji ni gobe in Allah yayi muna cikin masu rai da lfy,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi🙏🏻❤️

😭😔UBANA NE KO KISHI TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEY BEE)


.........


My what's app group l


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


Ina maraba da duk me son shiga wannan group in saidai in har kin San ba sharhi zaki nayi ba toh don Allah kiyi zaman ki kar ki shiga,haka ma Na miji Na roke ku da sunan Allah kar Na mijin da ya yi joining group in nan domin akwai matan aure a ciki,Na mata ne xallah🙏🏻


Ga masu son a tallata musu hajojin su kuwa suna iya tuntuba ta ta wannan layin:


    08100046388


...........

          Page five


**********


Dan guntun tsaki ya ja sannan ya ce wai Bauchi fa wata teaching hospital nan aka je fa ni,


Murmushi Mujaheed yayi sannan yace but Bauchi is a very nice city mutumi Na domin I have been there twice or thrice haka nan,duk da ba wata girma can Gare ta kamar nan ba and nan mun fi su yawancin abubuwa,but am very sure za kayi enjoying zaman ka a can,domin sun iya 

masa sosai,and ka ga kuma kai kana son masa,saidai fa mutanna Bauchi akwai Dan banzan rowa ya kare yana dariya,


Saisa ake musu kirari da yan Bauchi naman keya,ya kare yana Kara dariyan shakiyanci,


Tsaki Doc Nameer ya kuma ja sannan yace ni ina ruwana da Rowan su sai kace karamin yaro kawai daga zuwa Na gari sai Na hau roko haba dallah,


Ni fa ba fa kyan garin ko kyan mutannan garin bane a gaba na, duk abunda ke garin ni bana so Na fi son a bar Ni cikin family Na,


Hannun shi Mujaheed ya dafa sannan yace haba mana Nameer sai kace ba Na miji ba duk wani maaikaci ai ya kamata ya zama a cikin Jinin jikin shi yi masa transfer, don Allah kar ka bar Dan wannan abun ya Dame ka ka ji,


Hmmm Mujaheed bara ka gane bane wlhy duk abun da zai sanya ni nisa da Angel to wlhy Na tsani wannan abun with passion, ko kadan bana son nisa da ita,and sanin kan ka ne babu yanda za a yi Mama ta bari Na tafi da ita har Bauchi ni fa shine damuwan da nake yi,


Zama Mujaheed ya gyara sannan yace haka ne kam Mama ba bari za tayi ku tafi ba kam amman be faithful my friend in sha Allah komai zai zo maka da sauki am very sure sai ka bani labarin irin dadin da Bauchi ta maka domin garin akwai dadin zama,


Dan kallon shi Nameer yayi sannan yace ni kam dai ko yar bauchin nan kake son Kara ta biyu ne Na ga yanda kake backing up in garin nan bil hakki,


Dariya me Dan sauti Mujaheed yayi sannan yace kai mutumi na, shi din ma dariyan yayi kafin yace in tayi tsami ma ji ai,


Duk shiru suka Dan yi kowa Na dan danna wayar sa kafin can Doc Nameer ya dauko tare da cewa yauwa ni kam friend ka ga wani video kuwa dake ta trending daga jiya zuwa yau,


Hmm wlhy Na gani Nameer abun ya matukar daure mun kai wlhy ohhh duniya wlhy ina tsoron wannan rayuwan yanzu tsaban dibewan Albarka ai ubanka ko Dan giya ne bara ka fito bainan nasi kana masa irin wannan zagin karan dagin ba,balle ace mutum me tsoron Allah me dattaku irin SEN ace wai yau yar shi kwaya daya tilo ta fito cikin media ta masa zagin fitan hankali sabida bat ta kunya,daman tsiyan ka nuna wa yaro kana mugun son shi ke nan nan zaka ga yana fallin iskanci ya kare cike da Jin haushi,


Goshi Nameer ya dafe sannan yace dadi Na da kai ke nan Mujaheed yanke hukunci ba tare da kasan cikkkaken me ke faruwa ba,


Ka san me ya mata ne tayi masa hakan?a yanda aka ce akwai shakuwa da soyayya me karfi a tsakanin ta da shi meya sa for all past years in da suka yi spending together bata taba masa hakan ba sai yanzu dole akwai wani abu a kasa,


Miye a kasan iskanci ne fa irin Na yaran masu kudi wai su suna koyi da dabiar yahudawa,domin ita kanta Nadeeyan an ce bata cika zama a nan gida Nigeria ba sai da ta kammala karatun ta tsaf da aikin ma an dauka a can turan za ta yi,wlhy Nameer ba komai bane fa kawai iskanci ne fa da samun guri,Amman ace mutum kamar Audu Waziri wlhy duk duniya an sheda mutum ne me son aluma da kuma tausayin talakawa,ni in ba don yar sa bace sai nace tayi ne don ta bata masa siyasan sa,


Da ido kawai yake bin Mujaheed domin shi fa haka yake magana ce da shi har ta Allah tsine mamaki yake me ya Hana shi karantan Mass com ko wani law sai kuma ya kare da karatun malamin jinya,


Kayi shiru kana kallo na ko kai goyon bayan yarinya kake yi ne ya kare yana tsare shi da ido Wanda hakan ya baiwa Doc Nameer dariya,


Dan darawa yayi sannan yace ba ka da dama wlhy Mujaheed ni a ina Na san ta da har zan bi bayan ka,kawai dai ina magana ne daga abunda nayi tunani,yau da ace kamar daga waje ne wani ya shigo yayi masa irin wannan zagin sai muce daga magauta ne don ba a so ya ci,amman fa yar sa ce ta cikin sa,


Allah Na tuba duk da ance sanin mutum sai Allah amman ya ci ace ta san halin uban ta ciki da waje,kai ni fa sai sa Sam bana son politics kila ma hadin baki suka yi da yar ta shi tayi masa hakan domin ya samu sympathy in mutane a kuma Kara ganin kima tausayi da kuma mutuncin shi,ka zo ka tsaya kana kare shi kamar muna court room ya kare tare da mikewa,


Mujaheed in ma mikewan yayi sannan yace ai daman politics in ko hakan ne da Sen ya ban mamaki wlhy,kar wani abun da Dan Adam zai yi ya baka mamaki Mujaheed domin yanda ka ga mutum ka bar shi kawai,fatan mu dai shine Allah yasa muyi kyakkyawan karshe ya kare tare da fita daga cikin office in,da Ameen Mujaheed in ya amsa sannna ya bi bayan sa yana me yi masa wani hiran daban,


Nadeeya.......


Ba ita ta farka ba sai karfe 10 Na safiya sakamakon Aluran baccin da doctor Bashir ya shigo ya tsikara mata,


A hankali ta fara bude idanun ta Wanda sun riga da sun kumbura tsaban kukan da ta ke ci kwana 3 da suka wuce,a hankali ta ji kanta Na juyawa Wanda ta sanya hannu tare da dafe kan tana kokorin bude idanun ta Tas ta samu ta sanya wani abu a cikin cikin ta domin ba karamin yunwa take ji ba,don rabon ta da cin abinci tun shekaran jiya,


Hamdala take yi wa ubangiji a ranta da ya kubutar da ita SEN be sanya an mata komai ba domin har ga Allah ta tsorata time in da doctor Bashir suka zo daukan ta, ganin she is still alive ne ya sanya ta fara bin damin da take jiki da kallo,


Mamaki take yaushe aka kawo ta cikin dakin nan ina ne ma nan gidan waye and be take yi,ko dai ya sanya an kawo ta nan ne don ya ji dadin kashe ta,


Mamaki ne ya kamata tare da bude baki sakamakon ganin uniform sanye a jikin ta,Wanda harda no a jikin rigan domin ita ce no 354,


Hasbunallahu wa ni imal wakil,shine kalman da take Nana ta wa,in har ta canka daidai nan dai asibiti aka kawo ta ,saidai no in da ke jikin ta ne bata san Na miye ba,a hankali ta sauko daga kan gadon duk da ba wani karfi bane a jikin ta ta fara bin dakin da kallo, Sam brain in ta yaki responding balle ta samu ta fahimce inda aka kawo ta,saida idanun ta suka sauka akan chains in da ke jikin gadon,


A mugun tsorace tayi baya tare da furta kalman Na shiga uku ni Nadeeya kar dai abunda nake tunani ne,kar dai gidan mahaukata wannan mugun ya sanya aka kawo ni,shike nan Na kade shine kalman da take fadi tana kuka,


Ganin in ta zauna kuka ba inda zai kai ta domin burin ta be wuce ta ga ta tona wa SEN asiri ba,tana son duk duniya su san shi wani irin mutum ne,Amman abune me matukar wahala,


Kamar Wanda aka zabura tayi saurin mikewa domin bara ta zauna da hankalin ta a maida ta mahaukaciya ba,


Tunanin guduwa ne ya fado mata a rai, da za ta samu ta gudu daga kasar nan ma baki daya ta koma can wata kasan ta faro rayuwar ta daga farko yanda SEN bare ma San yanda take ba,


Da Sauri ta nufi bakin kofan saidai duk yanda ta so ta samu ta fice kasawa tayi,tayi kuka kamar ranta zai fita ta kuma ja wa SEN Allah ya isa ya fi 10 basket, nan kasa ta kwanta looking so very helpless tun tana kuka,bar tayi shiru tana tunanin mafitan da za ta samar wa kan ta,


..............Kaduna 


Shigowan shi ke nan parlor in hajiyar sa,bakin shi dauke da sallama,da gudu gudu sauri sauri wata yar cute baby Wanda bara ta wuce 2 and the half years ba ta nufo shi tana ware hannaye,ta fadi ta mike tana fadin Papeee daga ganin yanda take masa kasan murna take da zuwan shi,


Nufan ta yayi da sauri yana dariya domin yanda take gudun tana talle yan tiny legs in ta abun dariya ne,


Daukan ta cak yayi tare da juyi da ita sannan ya rungume ta tsam a kirjin shi yana Jin kaunar yarinyar ta shi har cikin Jinin shi,


Lallausan suman kanta ya shafa sannan yace my Angel wa ya bar miki suman ki a bude??,


Mama ne ta fadi cike da gwarance,mama ce ta bar mun kan Angel ita a bude haka,kai ta daga mishi tana dariya tare da tsale a kan jikin shi,


Lalle Haanan wato ni za ki yi wa Shari don kin ga Papan ki ko,ai ko zai ta fi ya bar Ni da ke a cikin gidan nan wata yar kyakkyawan dattijiyar mata ta fadi tana fitowa daga cikin kitchen,


Fuskan ta ta boye a kirjin shi tana dariya domin yarinyar ba dai wayo ba,


Shi kan shi Nameer dariyar yake domin drama in Mama da Haanan Sam baya kare wa,domin mama maida ta take kamar wata babbar mata tayi ta tsokana ta tana kiran ta Tsohuwa,


Dan risina wa yayi tare da cewa an wuni lafiya Mama, cike da faraar ta ta amsa shi da Alhamdulillah my son ya gurin aiki kuma,


Kai ya dan Sosa sannan yace wlhy mama gurin aiki ba dadi don maganar ma da nake miki yanzu sun yi mun transfer zuwa garin Bauchi,


Kai mama ta jijiga irin Na nuna alhini sannan tace ayya Abu be yi dadi ba Sam wlhy Amman ya aka iya toh,haka xa muyi hakuri ka tafi,gashi ni ba kowa Na sani a garin Bauchi ba,Amman ba komai Ubangiji ya sanya hakan shi yafi zama Alkhairi,


Ameen thuma Ameen Mama hope dai babu wata matsalan,aa Sam babu matsala Babana  Allah yayi maka Albarka ta kare ka a duk inda kake,Ameen ya Allah mama ta,ya kare yana jan yatsan kafan Angel,


Kuma yaushe ne tafiyar taka ,wlhy mama within 2 weeks suka ce,


Kai da wuri haka,toh Tsohuwa sai ki Bini a sannu don papa dai Bauchi zai tafi ya bar Ni daga ni sai ke,


Dariya ya sanya sannan yace aa mama da Angel ita zan tafi,hararan wasa tayi masa sannan tace ka ma isa,ai tun da kaki Kara auran nan to ba yanda za ka da ita,


Ace magana kullum mun yi tayi ke nan haba Baba Na yau margayiya shekarun ta biyu da rabi da rasuwa da ya ci ace ka Kara aure wlhy ko don yarinyar nan kar ta taso babu uwa a tattare da ita,


Numfashi me zafi ya furxar,domin har Ila yau in aka yi maganar mutuwar RA'ISAAH ji yake kamar jiya ta bar shi s doran duniyar nan shi kadai da little Hanaan in shi,


Nan take idanun shi suka kafa a hankali yace kiyi hakuri mama wlhy ba wai naki jin maganar ki bane ko auran ne bana son karawa, wlhy mama tunda Ra'isaa ta rasu ta tafi da duk wata soyayya ta,bata raye Amman har yanzu bugun zuciya ta tata ce bana Jin akwai wata macen da zan kalla har ta burge ni balle har Na ji shaawar auran ta ,ya kare kamar zai yi kuka,


Numfashi Mama ta sauke tana me tsananin Jin tausayin Nameer in domin ita kanta sheda ce ba karamar kauna yake wa margayiya ba,


Shike nan my son Na fahimce ka Allah ubangiji ya cigaba da yi wa Ra'isaa rahma ya sanya ta huta in namu ya zo ya sanya mu cika da imani,


Ameen thuma Ameen ya amsa tare da mikewa ya shimfida Haanan da already tayi bacci akan sofa yace  Mama bari na Dan shiga Na rintsa zuwa la'asar zan tashi, toh son abincin fa,bara ka bari ka ci abinci ba ka ji dadin kwanciya,aa mama abincin nan zai n tashi ya kare tare da shigewa daki,da kallon tausayi mama ta bishi domin ta san ba wani baccin da yake ji kawai hiran margayiya da aka yi ne ya tado mishi inda yake Mai kaikayi,



............Doc Bashir


Tsaye yake da waya a kunne alamun waya yake yi hakan ma da mutum me mahimmanci,ranka ya Dade tana nan a cikin koshin lafiya duk wani abun bukata da kace duk mun sanya mata, yanzu haka ma bacci take yi,


Ban ji abunda aka ce daga can bangaran ba sai ji nayi Bashir Na cewa aa ranka ya Dade ba a riga an fara ba,


Sorry ranka ya dade,injections in ne bamu da shi a nan Amman Na aika yana kan hanya gobe ko jibi za mu fara mata in sha Allah ka kwantar da hankalin ka yanda kake so haka zai faru ,Dan dariya yayi sannan yace godia nake ranka ya Dade Allah Kara girma......


Ayi mun afuwa da typing errors pls am trying all my best ban yi edit ba kuma typing in dare ne and keyboard ina yana bani matsala wlhy,


Masoyana ina Jin dadin irin karfin gwiwan da kuke bani,Allah saka muku da Aljannah,


Sai kun jinu gobe in sha Allah,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY 

           BY

NERNAH MARYAM 

(MARTEY BEE)


.........


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


Kofa a bude take kowa Na iya joining Amman,in har kin gan ba sharhi bane zai kawo ki don Allah to ki yi zaman ki ba sai kin shigo ba,and don Allah wannan group in mata ne xallah domin akwai matan aure a ciki,maza Na hada ku da Allah stay far  away from this group please🙏🏻,


Gama su son a tallata musu hajojin su kofa a bude take har yanzu za su iya mun magana ta wannan layin:


         08100046388


...........

          Page Six


********** A week later,


Nadeeyah na hango kwance a kuryan gado ta zuba wa guri daya ido alamun tunani take yi,


Hawaye ne ke zubowa daga cikin idanun ta,domin yau kimanin sati daya ke nan da kawo ta dakin nan aka rufe ta,bata cika ganin mutane ba sai doc bashir yakan shigo ya duba lafiyar ta a ce war sa wai tana da ciwon hauka,Wanda ta Riga da ta san sam ita lafiyar ta klau,sai sister kareematu da ke shigo mata da abinci Wanda sai ma an tambaye ta me take so ta ci,


SEN ya zo gurin ta har kusan sau hudu Amman sam taki ma ta bashi daman ganin nata domin toilet ta shiga ta rufe kan ta a ciki,in akwai hallitan da ta fi tsana a doran kasa toh bayan SEN ne,


Shiru kawai tayi tana juyayin yanda rayuwar ta ta kife lokaci guda,ace wai for all people yau ita ce Nadeeya Rilwanu Audu Waziri ke kwance a kan gadon asibiti da sunan wai ta haukace,ga shi wani abun haushin ta sha attempting guduwa saidai sam kasawa take because shi kanshi dakin da take ciki akwai security pin code Na bude shi da rufe shi,Wanda har Ila yau bata san miye pin in ba,


Jin alamun bude kofa ne tare da Dan magananganun mutane ya sanya ta gane dakin ake kokarin shigowa,kila doc Kareematu ce ta kawo mata abinci,


Yau dai by all means sai ta bi bayan ta a boye ta ga numbers in da take dannawa kofar ya bude,ko tayi mata Alkawarin kudi in har ta taimaka mata ta gudu domin ta ga alama ita mata ce me kwadayi da son abun duniya,


Saidai fuskan SEN da doctor Bashir da ta gani ne ya sanya ta ji ranta ya kuma baci,da sauri tayi kokarin mikewa don shigewa toilet coz ita dai bata ga amfanin zama tayi magana da wannan mara tsoran Allahn ba,


Cike da raunanan murya ta ji ya kira sunan ta princess,bata dago ba haka zalika bata ce da shi uffan ba,


A hankali ya taka tare da nufar inda take ya kamo hannun ta tare da cewa am sorry my love jiya ban samu Na zo ba wlhy kina rai Na meeting ne ya rike ni,


Dago da kanta tayi tare da watsa masa wata irin kallon tsana,sannan tace can you pls take off your hands a jiki Na,I told you to stop touching me da wannan hands in naka ko ka manta ne,


Murmushi yayi tare da cewa Allah sarki Nadeeyan daddy wlhy mutanan nan da suka miki wannan abun ba zan taba yafe musu ba,


Wow SEN shine abunda ta katse shi da shi wai was all this drama necessary I mean all the tears all the lies all the stories da kayi cooking up, har wai da kan ka ka sanya a kawo ni gidan mahaukata Daddy are u for real,ta kare tana kallon shi,


Daga ni har kai har wannan mugun doctor in mun san I am not mad lafiya ta kalau,me yasa bara ka bar Ni nayi tafiya ta ba,okay kana Jin tsoron zan tona ma asiri ne right ,fine SEN I promise you baran ce wa kowa koami ba I will hold my mouth to my self,all I want from you is my freedom wlhy am sick tired of all this game da kake playing ta kare tana kuka,


Tsunguna wa SEN yayi shima yana hawayen tare da kallon ta,yace haba Nadeeya do u think ina enjoying kallon ki haka ne??God knows irin rashin baccin da nake samu kullum akan ki,


Nadeeya I love you so much ke ce rayuwa ta and duk abun nan da kika ga ina yi sabida ke ne wlhy,


Kallon shi tayi da sauri sannan tace sabida Ni fa kace tana nuna kanta da yatsa,murmushi tayi Wanda ake kira ya fi kuka ciwo sannan tace kana yi dai sabida siyasan ka da kuma mutanan gari,


Daddy in har kana sona kamar yanda kace why not bara ka kawo karshen wannan abun ba,I won't you let me go, Na fada ma I will surely hold my lips,


Kai ya girgiza sannan yace doc ni yana ke ga kamar ciwon nata dada karuwa yake yi kuma kace da ni tana samun sauki,


Stop changing the topic pls ka tsaya muyi magana wlhh ma gaji shine abunda Nadeeya ta fadi tana kuka,hannun ta ta hade guri biyu in a pleading way tana fadin Na roke ka pls SEN set me free I want my freedom, I promise you in Na fito zan tafi can inda bara ka sake gani Na ba don Allah ka ji,


Kai ya girgiza sannan ya kara da wlhy an cece ni sanin kan ki ne Nadeeya bara iya jure zama babu ke ba,ni dai nawa kaddaran ke nan,ba komai akwai Allah in sha Allah zai saka mun akan abunda aka miki,Na sanya ana saukan qurani da sunan ki,sannan ni da Alhaji Kabiru kullum muna tsayuwar dare da sadaka tare da rokan Allah ya baki lafiya,ga Doc bashir ma is trying his best day and night don ya ga kin samu lfy in no time,kar ki damu Nadee dee ta you will be fine in no time zai zamo kamar ba a yi ba,za mu cigaba da rayuwar mu kamar da ko Doctor SEN ya kare yana kallon Bashir,


Da sauri ya daga kai yana fadin yes haka ne,hakuri kawai za ki kara Hajiya Nadeeya domin mu samu mu kawo karshen problem in ki ki koma gida, mutane Na haukan da ya fi naki ma su warke balle naki ai me sauki ne,


Dariya ta kwashe da shi sannan tace wlhy Doc bashir kai ma baka tsoron Allah wai ni kam nawa wannan mugun ya baka ne ka dage lalle sai ka lagaba mun cutar da bani da,1 mil,5mil,10 mil 20 or 50 mil,ta kare tana tsare shi da idanu,


Kame kame ya soma yi yana uhmm ahhmmm wani irin magana ke nan nawa kuwa zai bani bayan kuma aiki Na ne kula da marasa lafiya,


Wani darinyan ta kuma sannan tace it shows akan face in ka baka da gaskiya ka karbi kudin Senator,look doc wlhy I promise u in har ka sake ni Na fita I will double the amount in da ya baka,


Jin hakan ne ya sanya SEN cewa doc ka ji ko wlhy Nadeeya ta,ta tafi shike nan ya tabbatan dai princess ita hauka tayi,ya kare yana share hawaye,baran iya cigaba da zaman dakin nan ba doc mu je ka raka ni akwai abunda nake son fada maka,


Karasowa yayi gurin Nadeeya tare da shafa kanta sannan yace my baby girl ni zan tafi sai jibi in sha Allah ga shi fav chocolates in ki ne Na kawo miki,take care of yourself ko,yanzu zan ga doctor game da case in ki ko xa a canja miki treatment ne don Na ga jikin naki sai Kara rashin dadi yake yi,


Hawaye ke zuba a idanun ta, tana ji tana gani suka fita daga dakin ba tare da sun saurari ko sun tausayawa irin rokon da take musu ba,hurgi tayi da ledan chocolates in suka zube,tana kuka tana I don't want your money or chocolates freedom ina nake so,tunda Na bika ta lallami kaki yarda SEN mark my words sai Na tona ma asiri shine ihun da tayi Wanda am very sure daga shi har doc sun ji,


Kai kawai ga girgiza ba tare da yace komai ba suka nufi office in Doc bashir,


Suna shiga ya daga hannu cikin zafin rai tare da kwada wa Doc bashir wata irin Mari me zafi da Kara,tassss kake ji,


Da sauri ya rike kumatun sa da yake ji suna masa radadi,yace Yallabai lafiya,


Cike da bacin rai SEN yace lafiya kake tambaya ta Dan uban ka,ni za kayi wa karya Bashir ni?ya nuna kansa, Na gani jiyan nan sai da Na sanya aka kawo maka 5 mil duk za to Na kayi nisa akan aikin da na baka ace one simple job ka kasa mun sai cin kudi Na kake sabida gani Dan iska me kudin banza ko,


Da sauri ya ce a a yallabai wlhy sam ba haka bane, aluran ne har yanzu basu iso ba sun dan yi wahalan samu ne,


Dallah ka mun shiru yau abu kusan sati har yanzu ace Alura ya kasa samu,kasan baka shirya ba kace we can trust you with this iyeee ya kare cikin fada,


Shi dai doc be da baki da ya wuce hakuri don hakuri ya ringa ba wa SEN yana mishi Alkawari kan in sha Allah gobe za a kawo,


Da kyar ya samu ya sauko sannan yace da shi and wlhy Bashir Na ga alaman kana da son duniya muddum Nadeeya tayi maka wani offer a cikin haukan ta ka karba sai Na ci uban ka,sai Na daure ka tas kai da zuriar ka in har Na shigo ban ga yarinya ta ba,am doing this for her on good so bana son Jin wata bad news daga gare ka shine abunda SEN yace babu wasa a tattare da shi,


In sha Allah bara a samu ba baran baka kunya ba sir ,daga haka SEN be Kara cewa komai ba ya fice daga office in,duk Wanda ya gan shi sai ya kwashi gaisuwa inda duk wanda ya gaishe shi sai ya mai kyautan kudi, saisa yake kara siye zukatan mutane,domin video in da ya sanya aka yi Na biyun ba karamin sympathy ya samu a gurin mutane ba,domin haka aka din gi zuwa masa gida jajje wasun ma da yawa be san su ba,daga masu zuwa jajje sai masu zuwa kan sun san malami me karya sanmu,sai masu zuwa kan cewa sun fara yi wa Nadeeya sauka,ba karamin tausaya masa mutane suka yi ba,wanda hakan ya kwantar wa party hankali suka bar shi ya cigaba da Takaran sa,


Da harara Doc bashir ya bi bayan SEN tare da Kara susa kumatun shi sannan yace Allah ya isa na,haka kawai ni na san miye tsakanin ku da yar taka,nasan me ka mata kana neman maida komai kaina,(ni ko nace madallah ai kadan ka gani ko ba son kudi ba ),


Tsaki ya ja tare da kiran Wanda yayi order in aluran a hannun shi,nan fa ya hau surfa mishi tijara,ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba,hakuri mutumin ke bashi kan gobe da sassafe za a kawo mishi,da haka yayi ending call in,


Kamar yanda mutumin yayi alkawari kuwa sassafe aka kira doc bashir kan ya zo ya karbi order inshi,abun da yake ta jira ke nan tun tuni,be bata time ba ya je ya karba Wanda aka sako masa a cikin box,kai tsaye hospital ya nufa don so yake yanzu yanzu ya fara mata aluran don ya ga alaman SEN zai iya cin uban shi in be yi ba,


A hanyan shi ta shiga hospital in ne ya ga isowar doc Kareematu wanda daman shi ya kira ta tun yana hanya,a tare suka yi parking sannan suka shigo,


Kareematu aluran fa sun iso Na sanya wada ya kai mun office ina kuma yau nake son Na fara mata,


Kallon shi tayi sannan tace kai doc gaskia ni ina Jin tsoro kasan fa wannan aikin na da hatsari za a iya kwace mana lasisin mu muddum asirin mu ya tonu,


Ke dallah dadi Na da ke tsoro,ga dai ki da son abun duniya Amman akwai tsoro, taya asirin mu zai tonu daga ke ne fa sai ni muka San wannan batu,


Ke din ma don ina kaunar ki da arziki ne ya sanya Na fada miki,don ko banza ai ina moruwa da ke ya kare yana kashe mata ido daya,


Ni dai gaskia Bashir ina Jin tsoro wlhy Baban ta fa babban mutum ne,in ya sani baka tunanin mu kare rayuwar mu a prison,


Oh shit Kareematu wlhy Sam baki gane wa nace miki ki saki jikin ki,aluran nan ma fa bake za ki Na mata ba ni zan nayi  are u happy now,ya kare yana kallon ta


Gaskia ni kam Bashir ina Jin tsoro, Dan kakai ya girgiza sannan yace na gane matsalan ki bani account details in ki,ko da yake ma bar shi ina da shi I think,


Dan wayan shi ya daddanna sannan yace da ita,Na miki transfer in 1.5mil are u in for this or no,


Idanu ta zaro jin amount in da ya ambata,bakin ta har rawa yake tace are are you seri ous Bashir,


Dan dariya yayi sannan ya nuna mata debit alert in da aka masa,wanda take ta ji karan shigowan message,


Haba dan ihu tayi tare da rungume shi tana wlhy ya shigo Bashir kai 1.5 fa,shafo bayan ta yake yi cike da iskanci yace wannan somin tabi ne my love,in har kika bani goyan baya har mota sai Na canza miki,


Cike da murna tace wlhy har goyan jiki ma na baka Doc Bashir ina,


Shegiya kareema yaushe rabon da ki kira ni da haka,fari tayi irin Na yan bariki sannan tace ai yau a guest house in ka ma zan kwana, dariya ha kwashe da shi sannan yace to shi mijin naki fa,dallah ya tafi can ce masa zan yi night gare ni domin yanda ka faranta mun din nan sai Na jiyar da kai dadi Na musamman, (wa'iyazu billah, wannan rayuwa da muke ciki yanzu abun tsoro ne ace mata da auran su suna zina,Allah ka dada kare mana imanin mu da mutuncin mu),


A tare suka shiga dakin Nadeeya a kwance suka tarar da ita kamar me bacci,


Kan gadon Kareematu ta hau tare da shafa kan Nadeeyan sannan tace sannu maza tashi lokacin magani yayi,Nadeeya bata ko kula ta hasali ma ko ido bata dago ta kalle ta ba,


Kareematu tashi ki dauko drip in da muka shigo da shi ki daura mata domin she looks very weak and pale am sure taki sake wa ta ci abincin kirki,


Tashiwa kareematu tayi tare da dauko drip in,hannun Nadeeya ta kama tare da fara neman jijiyan ta,ko motsi Nadeeyan bata yi ba domin ita kanta tana bukatan karin ruwan,don gani take tsaban kukan da take yi ruwan jikin ta Na gab da kare wa,


Cike da nutsuwa, Kareematu ta samu ta huda Nadeeya tare da daura mata ruwan,


A hankali ruwan ya fara shiga jikin ta wanda ta lumshe idanu ,domin ji tayi kamar kanta Na juyawa,a sannu bacci yayi awun gaba da ita sakamakon aluran baccin da Kareematu tayi a cikin drip in,


Kallon Bashir tayi da ya gama hada aluran a sirinji guda biyu yana nufo Nadeeya ya sanya tace Doc anya kuwa wannan doss in basu mata yawa ba ,Na ga aluran nan duk masu karfi ne and biyu Na ga kana shirin yi mata,


Dan dariya yayi sannan yace my Kareematu ke nan,ai da uku ne ma soke dayan nayi domin zai iya zamo mata matsala nan gaba,sabida in no time nake son ya fara aiki ya sanya zan Na mata biyu daya a cikin drip while daya a jijiya,ya kare yana juye ruwan aluran a cikin drip in,


While dayan a nutse ya kama hannun ta tare da tsikara mata a jijiyan ta,yauwa kin ga an gama Na yanzu saura kuma an jima da yamma in sha Allah,


Da mamaki ta kalle shi  bayan ya ja wa Nadeeya bargo tace kana nufin sau biyu za a Na mata a Rana,yes sau biyu ne hope dai kin kalli yanda Na dama aluran da yanda nayi mata don in bana nan ke za ki Na mata,


Da kai kawai ta amsa shi sannan suka baro dakin yana cewa yi sauri ki karasa abunda kike yi nima Na samu Na gama aikin gaba Na mu samu mu tafi don wlhy tun dazu da kika di ga mun Zuma a baki hankali Na ya fara barin jiki Na........



Na san akwai lots of typing errors hakan kuma ya faru ne sabida rashin edit in da ban samu nayi ba,so ana mun afuwa pls🙏🏻,


Hakikanin gaskia bani da bakin da zan gode muku yan group ina bisa irin goyan baya da kaunar da kuke nuna mun saidai nace Allah ya saka da Alkhairi ya kuma bar kauna🥹❤️,


Ina mika sakon gaisuwa da kuma godia Gare ku masoyan book in nan Wanda Na sani da Wanda ban san su ba,Allah dai ya bar zumunci,


Sai kuma gobe in Allah me komai me kawo ya so,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY 

NERNAH MARYAM

(MARTEY BEE)


........


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


Ina marhaban da duk me son shiga wannan group in saidai in har kin san ba sharhi za ki Na yi ba toh don Allah kiyi zaman ki kar ki shigo, haka zalika maza na roke ku da Allah kar kuyi joining in group in nan domin Na mata ne zallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via:


  08100046388


.........

        Page seven


**********


Tabbas rayuwar duniyar nan abun tsoro ce Na kuma Kara yarda in har kana raiye to kana da sauran kallo,domin lokaci daya  Nadeeya ta koma abun  tausayi,duk wani me imani in har ya ganta sai ya zubda mata hawayen tausayi,


Yau kusan kwana biyar ke nan doc bashir nayi mata injections in nan ba daga kafa kullum biyu safe da yamma,irin yawan doss in da yake bata ya sanya ya fara nuna effect in shi akan ta,


Domin a halin da Nadeeya ke ciki yanzu ita kanta ba gane kan ta take yi ba,haka kawai cikin dare za ta fara ihu tana tsigan gashin kanta tana kuka tana surutai,ko kuma ta mike tayi ta rawa tana tafi ita kadai,


Sai abun yayi kamar ya lafa da ya kuma mata aluran shi ke nan sai kuma ta burkice ta fara behaving abnormal,


Ba karamin dadi doc bashir ke ji ba ganin aikin sa is working domin Jinin Nadeeya Sam be da karfi ya sanya within no time injections in ya fara aiki,kila da ukun yake mata,wataran saidai ta buge kowa ta fita da gudu tsirara kan titi tayi hauka tuburan, Nadeeya brain inta ya fara samun matsala, don ita kadai sai ta dauki fiye da awa tana hira da iska,ko kuma ta tashi da gudu tayi ta zagaye dakin tana tsalle,abun dai gwanin ban tausayi,


Yana da assurance tunda har ya fara aiki haka in har ya cigaba da bata to burin su zai cika zata yi hauka Na har gaban abada bara ta taba samun lafiya ba,


........... Kaduna 


Doctor Nameer ko tsaf ya hade kayan abun bukatun sa domin a gobe Sunday yake son shiga Bauchi Monday yayi reporting ya fara aiki,


Zaune suke da Mama suna Dan taba hira Haanan Na jikin shi yana mata wasa,


Hope dai ka dauki yajin da Na zuba maka a roba dai ina,Dan murmushi yayi sannna yace eh mama Na dauka,ai ko kin taimake ni domin ban San ko abincin restaurants in su Sam ba dadi,


Dariya mama ta sanya sannan tace Amman kam Babana baka da dama wai ni kam me ka maida Bauchin ne,yanda kake ganin Kaduna city ne haka ma bauchin take fa,garin Sam ba laifi ai nan muka kai yar gidan Aminiya ta hajiya Salma,


Shi dai be ce da ita komai ba domin Allah ya gani ba son zuwa garin nan yake ba,


Can kuma sai ya kalle ta yace Maama ko dai za ku shirya mu tafi tare ne,


Ai nan ma dariyan ta kuma sanya wa sannan tace yau kun ji mun Babana wai sai kace wani karamin yaro,kawai sai Na shirya mu bika gurin aiki,ni ba matar ka ba ina mahaifiyar ka,ai ka ga ranar aure yau da da matar ka ce ai ba sai ka tsaya neman shawaran ta ba,


Fuskan tausayi ya sanya sannan yace ayya Mama na yanzu don Allah bara ki Bini ba zan dai siya miki Sheraton wannan sallan a dinka miki,


Dakuwa tayi mashi da hannu sannan tace kaci gidan ku Babana to rike kayan ka in dai sai Na bika Bauchi ne kai sanin kan ka ne sarai tun kafin Na Auri Alhaji Allah ya jikan shi nake sanya kaya masu tsada,dariya ya kwashe da shi domin shi din ma ya fadi ne don Jin bakin mahaifiyar ta shi,


..........


Alhaji Abdallah Mai nasara Dan haifaffen garin Kaduna,daga shi sai kanwar shi guda daya tal me suna Hajiya Bilkisu iyayen su suka haifa,


Baban su me rufin asiri ne sannan ya yi kokarin wadata su da duk wani abun da yaro xai bukata na rayuwar yau da kullum,haka zalika mahaifiyar su mata ce jajirtatciya akan yaran ta domin sun samu tarbiya daidai gwargwado,


A haka har suka girma Abdallah ya samu gurbi a makarantar ABU inda ya hada degree in shi, dake mutum ne me son kasuwan ci sai ya fada kasuwa inda Allah ya sanya wa harkan Albarka budi sai shigo masa suke yi ta ko ta ina,


A haka ne watarana ya je garin Yola ya ci karo da matar sa kyakkyawan bafulatana in da a take ya nuna yana bidan auran ta,ba tare da bata lokaci ba aka tsaida musu Rana,domin an yi dace itan ma tana kaunar shi sannan yana da gida aiki har da abun hawan sa,


Ba tare da an ja lokaci me tsayi ba aka daura auran Abdallah da Amaryan sa Aishatu in da aka kawo ta unguwar badarawa anan cikin Kaduna,


Akwai shakuwa soyayya hakuri da kuma tsantsan biyayya a zaman Aishatu da Abdallah domin mata ce me kawaici da sanin ya kamata,ya sanya yan uwan shi suke Jin dadin zama da ita, auran su da wata bakwai lokacin ma har an samu rabo a tsakanin Allah ya dauki ran mahaifin Abdallah, Wanda ba karamin taba su yayi ba,an ci kuka kam domin sun yi babban rashi kafin suka fauwala wa ubangiji komai,


Allah ya Albarkaci Abdallah da Aishatu da samun yara uku biyu maza sai Autar su mace,


Dan su Na fari sunan shi Abubakar Sadiq Wanda a yanxu Baban Engineer ne,yana da aure harda yara uku suna xaune ne a garin Lagos,sai Na biyu Nameer,sai kuma Autar su Nana Khadija Wanda tai aure ita ma tana zaune a garin Abuja harda Dan ta Na miji guda daya,


Nameer Abdallah matashin saurayi ne me ji da jini a jika,akwai shi da cikar halitta da kwarjini tare da saukin kai,


Likitan mahaukata yake da burin karanta tun yana yaro ya sanya Baban shi biya masa kudi ya tafi Cairo don samun gurbin karatu a can,


Mutum ne me taka tsantsan da Rayuwar sa hakuri rashin magana da kuma tsananin tsoron Allah,mutum ne me yawan ibada tare da tsarkake da kuma mika alamuran sa ga Allah,ya sanya ya kasance mafi soyuwa a cikin yaran su domin shi Sam be da hayaniya ko matsala,mutum ne me balain kokari,sannan in dai abu be shafe shi ba to Sam baya sanya baki ciki,


Allah ya tsare shi baya shaye shaye balle neman mata,yana aji uku ne Allah ya hada shi da Ra'isaah Abdul Aziz,Wanda balarabiyar Egypt ce, soyayya ce me karfi tare da shakuwa ya shiga tsakanin su a kan kanin lokaci,ta zamo wani jini Na jikin shi,tunda yake be taba so ba sai akan Raa'isah Wanda yake Jin ta har cikin zuciyar sa,



 A nata bangaran ma hakan take,ba tare da bata lokaci ba ta gabatar da shi wa mahaifin ta ganin kamalan sa ya sanya kai tsaye mahaifin nata yarda da batun soyayyar ta su,ganin ya kusa gama wa ya sanya aka bar bikin sai bayan ya gama karatun shi,


Cikin ikom Allah kuwa gamawan shi da wata guda aka daura masu aure wannan ranar kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha don murna haka yake ji,domin shi kan shi mamakin irin yanda yake tsananin kaunar Raa'isaah yake yi,


Hidiman biki aka yi aka gama sannan aka bashi Amaryan sa domin ya sanar da ita shi bare iya nisa da iyayen sa ba,a malali Baban shi ya Gina masa gida me kyan gaske inda nan aka sanya Amarya,


Rayuwar auran su rayuwa ce me cike da tsantsan soyayya da fahimtar da kuma tattalin juna,ko wannan su rige rigen faranta ran Dan uwan shi yake yi,duk Wanda ya ga yanda suke gudanar da Rayuwar auran su to tabbas sai yai shaawa, domin Raa'isa mata ce ta kwarai me tsaninin biyayya, babu abunda daya ke boye wa daya,Raa'isah ta zo Nigeria bata Jin ko zo a yaran Hausa Amman bata dauki wata uku ba aka fara koya mata hausa,



Watan su uku da aure Allah ya azurta ta da samun ciki,tattali kula da soyayya take samu daga gurin Nameer,


Wanda hakan yayi daidai da rasuwar Mahifin su Alhaji Abdallah me Nasara sakamakon hatsarin jirgin sama da suka samu,


Ba karamin jijiga Nameer yayi da Jin mutuwar mahaifin shi ba domin akwai shakuwa me karfi tsakanin su,sun yi kuka sun ji ba dadi Amman hak a karshe dole suka hakura suka fawala wa Allah komai suka cigaba da yi masa addua,


A hankali rayuwa ta cigaba da tafiya cikin Raa'isah yana dada girma hutu Nameer ya dauka a gurin aiki domin bata cikakken kulawa,kama daga kan girki wanki,wanke wanke shara duk shi yake mata,ganin ta yi nauyi already,


Duk wani abun da zai faranta mata shi yake yi,haka zai kashe Rana daya ya zauna kawai yana yabon irin kyan da ta Kara sakamakon samun cikin nata,Wanda ita har mamaki take yi domin muni ta ga ta yi tare da kumbura Amman kullum Nameer kyau yake cewa tana masa,


Tabbas Nameer da Mama sunyi playing role me girma a rayuwar ta more especially ma lokacin cikin ta,domin duk wani kula da soyayya gata ta gani a gurin su,a haka har cikin nata ya shiga watan haihuwa,ba yanda mama bata yi da shi ba kan ya dawo da ita gurin ta zata fi kula da ita Amman Sam yace aa shi zai kula da Noor in sa,sunan da yake kiran ta da shi ke nan,


Suna zaune ranar Alhamis da safe yana matsa mata kafa yana mata hira akan in ta haihu bayan suna in sha Allah zai kai ta gida ta je ta ga family in ta,ba karamin dadi ta ji ba nan tayi ta murna tana she can't wait ta haihu,


Wannan daran haka suka raya shi cike da soyayya da shaukin juna,Wanda cikin dare naguda ya tashi mata gan ga gan ga,daukan ta yayi cak sai hospital, saida suka isa sannan ya samu ya kira mama,


Suna nan tsaye har asuba Amman Allah be yi ta sauka ba,har suna shirin shiga da ita tiyata cikin iko Na Allah sai ga kan jinjira a nan ta samu ta haife santaleliyar baby girl in ta fara me kyau da ita,in da ita kuwa Raa'isah ko shurawa bata yi ba tace ga garin ku nan rai yayi halin shi,


Ko da sakon mutuwar ta riski Nameer yankan jiki yayi ya fadi ya suma kwanan shi uku be San yanda kan shi yake ba,kafin ya farfado,


Da kyar da addua aka samu ya dawo cikin haiyacin sa domin kusan zare wa yayi,don ko kadan be yi tsakanin wai mutuwa Noor in shi za ta yi ba,ko ana gobe za ta  mutu zama suka yi tare da tsara irin yanda zasu yi rayuwa tare da babyn su ashe rashin sani tafiya za tayi ba tare da ko ta san me ta haifa ba,babu ruwan Allah baya barin wani Dan wani ya ji dadi,Alhamdulillah Raa'isaah tayi mutuwar shahada,(ya Allah kar ka dauki ran mu sai kana farin ciki da mu),


Kwanan su 5 a Asibiti sannan aka sallame shi,gidan ta mama ta wuce da shi domin ganin lamarin Nameer in dai da ayoyin Allah,


A haka aka yanka wa yarinya rago tare da maida mata sunan mahaifiyar ta suna kiran ta da Haanan,Wanda Sam ba a yi taron suna ba sabida rasuwar da aka yi,



Da kyar da nasihohi aka samu Nameer ya dawo haiyacin sa domin ko kadan ya kasa jure rashin mahaifin shi da LOML a cikin shekara guda,



Tun da aka samu ya dawo hankalin shi ya kara komawa wani shiru shiru,kullum yana zaune shi kadai yana tunanin Raa'isaah,tare da daukan soyayyan duniya ya daura wa Haanan,ba ya shiri da abunda zai taba ta ko kadan,


Ba yanda ba ayi da shi akan ya kara aure ba,Anty Bilki har gida ta kawo masa tayin diyar ta Amrah kan ha aura ,Amman Sam ya nuna baya so,


Domin gani yake bare taba samun mata kamar Noor ba ta so shi tun bayi da komai Allah ne yi za ta more shi a yanzu da samu ke ta xuwa masa ba,saisa ya dagr duk wasu kudadan shi daga Maman sai Haanan yake wa spending,


Kwata kwata yaki bude zuciyar sa yau fiye da 2 years balle har ya sanya wata diya mace a ciki domin a cewar sa tun bayar rasuwar noor to be ga wata ya macen da ta yi masa ya aura ba,and da aka Dame shi yayi aure ko Dan angel in sa,shi he can take care of her alone, bare juri ganin ya auro mata tana cin uban Haanan in sa ba,ya sanya Sam be ma da raayin Kara auran,


..........Back to story


Har bakin mota Mama da Haanan suka rako shi sai kuka take tana mika masa hannu kan ya dauke ta ya tafi da ita,


Jin kukan nata yake har ranshi domin ya San Mama sam bara ta bashi Angel su tafi can uwa duniya kam,


Addu'oi sosai Na tsari da fatan saa mama tayi masa sannan suka rabu ya ja motar shi tare da barin gidan zuciyar shi Na zafi,don kukan da angel ke yi har ransa yake ji,


Sai da ya biya 44 yayi wa mujaheed sallama tare da daukan sauran abubuwan shi har mota mujaheed ya rako sa yana masa tsiya kan in ya je Bauchi pls ya duba mishi ya SEN da wannan mara ta idon yarinyar ta shi suke ciki,da toh kawai doc Nameer ya amsa shi domin shi miye hadin shi da Sen balle wata yar sa,shi da da xai je asibiti ko ina zai gan ta har ya San ya suke ciki oho, da haka ya shige motar shi tare da daukan hanyan Bauchin Yakubu,sai mu ce Allah ya kiyaye hanya Doc Nameer.....


Keep on  sharing and commenting pls,


Ina matukar godia da irin kaunar da kuke nuna mun,Allah saka da Alkhairi,



Sai kuma zuwa Monday in Allah me komai me kowa ya so.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEY BEE)


.......


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


Ina maraba da duk me son yin joining Amman in har kin San bara ki Na yin comment ba toh don Allah kar ki shiga,haka zalika don Allah maza kar su shiga,domin group in mata ne zallah kuma mafi yawan su matan aure ne🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via:


   08100046388


..........

         Page eight


*********


Tafiya good five hours ne ya shigo da doctor Nameer cikin Bauchin Yakubu,ba karamin gajiya ya taro ba domin shi ya tuko motan da Kansa,it's been a while since da yayi long journey haka nan,


Tunda ya iso yake bin tsarin garin da kallo,shi ba kowa ya sani ba balle ya ce zai nufi gidan wani ya sauka,gashi yamma ta fara yi domin be yi iso wan wuri ba sabida tsaye tsayen da ya ringa yi a hanya,


Ganin be da option in da ya wuce ya nemi hotel ya kama,domin ya samu gurin kwana,Dan tsaki yayi tare da cewa tsiyan ka zo guri baka san kowa ba ke nan wlhy duk sai ka bi ka zama wani bako,


A ZARANDA HOTEL,ya yada zango inda ya shiga tare da biyan kudin dakin kwana uku, dole ya dan tsaya Na kwanakin kafin ya samar wa kansa,mahallin da zai zauna,domin Sam be kaunar zaman hotel,


A reception ya tsaya tare da biyan kudin daki Na kwana uku,aka ba shi key in dakin sannan masu aikin hotel suka dauko jakar kayan shi tare da nufar dakin Na shi da shi,


Godia yayi musu bayan sun aje sannan suka wuce,dakin ya bi da kallo,wow daki ne me kyau  kamar mutum yana gida, domin komai akwai a ciki,gado kujera harda fridge,


Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya fada kan gadon,oh my god am damn tired wlhy,ya kare yana shafe goshi,so yake ya dan huta kafin ya samu yayi wanka ya sanya wani abu a cikin nashi ko zai samu gajiyar jikin shi ya bar shi,


Ringing in da wayar sa ke yi ne ya sanya ya bude idanun shi a hankali tare da janyo wayan domin ya San ba kowa bane ila Mama,


Saidai ganin bakuwar no ne ya sanya shi mamaki,har ya yanke be dauka ba,sai da aka kuma kira sannan ya dauka,


Hello brother ya ji muryan ta ya doki kunnan sa,a hankali yace shit ba dai yarinyar nan ba,


Haba Brother yanzu kana ji Na ka share ni,ta kare cike da shagwaba,gashin kan shi ya shafa sannan ya ce Amrah yaushe kika shigo Nigeria and ina Maman ki,


Hmmm ai Yaya Nayi fushi kana tafiya Ashe jirgin mu yana landing I wanted giving you a surprise ya sanya ban sanar da ku zan zo ba,saidai am not lucky Ashe ka tafi Bauchi ta kare a shagwabe,


Hmm Amrah Na tafi ban ma Dade da isowa ba ya amsa ta da kyar, ayya sorry brother Na Na san ba Wanda ka sani a Bauchi you will be so very lonely ko dai in zo ne,


Idanu ya zaro a kasan makoshi yace what,a fili kuma sai cewa yayi kee Amrah are you okay kuwa,an ce miki ko ina ne irin Manchester ehyeee taya za ki biyo ni Bauchi,


Hey common  sweetheart nima dai wasa nake maka,ko kace Na zo am not coming ta kare tana dariya,


Tsaki yayi a hankali domin shi fa haukan wannan yarinyar ke hada ta da shi sam bata da kan gado,



Ina Mama shine abun da ya tambaye ta Jin tana son kamo wata shirmen nata daban,


Ga ta nan kusa da ni in bata,idanu ya zaro Jin wai mama Na gefen ta take wannan haukan sam rayuwar turai be yi ba wlhy,hello are you lost again ta tambaya tana fari da ido kamar yana ganin ta,


Bata shine abun da kawai ya ce da ita,ba musu kuwa ta mika wa mama wayan,


Sallama ya fara mata sannan ya gaida ta,ta amsa cike da kauna sannan ta tambaye shi ya hanya ya sauka lfy,wlhy Alhamdulillah mama saidai gajiya gaskia Bauchi da nisa,dan murmushi tayi sannan tace ai ka dade baka yi tafiya bane Babana ya sanya kake ganin nisan Na shi har haka,


Gaskia kam baki ji jiki Na ba wlhy mama kamar an mun duka,dariya ta Dan yi sannan tace haba dai son to waye zai buge ka din,shima dariyan ya dan yi sannan yace Ashe Amraah ta zo?


Eh wlhy kana fita ko 30 mints baka yi ba sai ga shigowar ta,basu ma dade da dawowa da Haanaan daga Havilla sun je shan ice cream ba,


Nan take yayi kicin kicin da fuska yace haba mama nawa Angel take da za a wani kaita shan ice cream in mura ya kama ta fa,gaskia a ce da ita kar ta kuma fitar mun da yarinya wani wai yawon shan ice cream,ya kare da iya kar gaskiar sa,


Baki mama ta bude tana mamaki irin wannan rashin kunya ta Nameer,sannan tace zan iya bata sai ka fada mata da kan ka,uban da ya fi kowa son yar sa,


Ayya Mama Na ga dai har yanzu Haanan baby ce ko 3 years fa bata yi ba,ai ice cream is not good for her health at all,ya kare a marairaice,


Hmmm son ke nan,ni kam a huta gajiya sai mun yi magana later hajiya Salma na kira na,da haka ta mika wa Amraah wayan tata,


Jin abun tace ne ya sanya shi kashe wayar da sauri domin Allah ya gani bayi da energy in tsayawa Jin abubuwan da wancan wawiyar yarinyar za ta ce masa,


Toilet ya fada kai tsaye bayan yayi placing order in abincin da zai ci,wanka yayi da ruwan zafi ya gasa jikin shi sosai yanda wahalan za ta warware sannan ya fito,


Shafa ya gama yi tare da combing in gashin shi, sannan ya sanya light ash in jallabiya a jikin shi,yana fesa turare yayi daidai da knocking in kofar dakin shi,


Ko da ya bude Waiter ne dauke da abincin da yayi order karba yayi tare da musu godia sannan ya koma daki,


A nutse ya zauna bayan yayi bismillah ya soma cin abincin shi cikin kwanciyar hankali, wow Ashe dai mutan Bauchi an iya abinci ya kare yana murmushi shi kadan sa,


Saida ya cinye abincin tas, yayi realizing ashe dai yana dauke da yunwa a cikin sa,a nan cikin dakin Na shi ya gabatar da Sallan Magrib da isha'i sabida rashin sanin masallaci da ke kusa,


Around 9 ya gama komai tare da hayewa kan gado ya janyo laptop in shi tare da kunna wani American movie ya shiga kallo,ganin idanun shi Na ya ji ne ya sanya shi rufe laptop in tare da yin Azkar in bacci ya ja blanket sai bacci,


.........Senator


Shigowan shi ke nan a matukar gajiye cikin part in shi domin ba karamin gajiya yayi a meeting in party da suka yi yau ba,babban rigan jikin shi ya cire tare da mikawa Saa'eed yana cewa kai wlhy am really tired,


Sannu yallabai ko dai sai an hada ma da tausa ne yau,aa Saa'eed in nayi wanka da ruwan dumi ma zan ji daidai,da haka suka kara sa shigowa cikin parlor in shi,


Ido waje da matukar mamaki yake kallon shi,Afzal ya kira sunan shi a Dan tsorace domin ba karamin mamakin ganin shi yayi ba Sam be dauka zai dawo Nigeria yau ba beside jiya jiyan nan suka yi waya ya sanya a tura masa kudi kan ba nan kusa zai dawo ba,


Cike da tsantsan farinciki Afzal ya taso tare da fadawa jikin SEN yana cewa Dad ya ka ga surprise ina?


Fito da shi yayi daga cikin jikin shi yace Why are you back Afzal?


Kallon Saa'eed Afzal yayi sannan yace Mal can you leave us alone,sorry sir shine abunda yace da sauri tare da ficewa daga part in yana mamakin me ya kawo Afzal gidan kuma,


Afzal why are you back, ina ce I told u not to come back until I'm done with things over here,


Fuskan yara Afzal yayi tare da narai narai da idanu kamar me shirin yin kuka yace but Daddy I have missed you ne,and kai ka ki bari Na in dawo,Na gaji da zama ni kadai a can USA and beside I thought you are done with things over here ne ai tunda kai da kan ka kace da ni I shouldn't panic za ka yi taking control in komai da komai, ya kare yana zumburo baki,


Yeah Na sani but am not done working out things yet,bara ka gane ba Afzaal abubuwa sun cabe da yawa wlhy,SEN ya kare tare da zama yana dafe goshin shi,


A kusa da shi ya zauna sannan ya dafa hannun shi cikin soft voice yace yeah Dad Na san you are doing all your best so relax pls don't be over stressing your self out,


Numfashi kawai SEN ya sauke ba tare da yace komai ba,domin shi kadai ya San irin halin da yake ciki a yanzu,


Duk shiru suka yi for so mints kafin can Afzaal yayi breaking shirun da tambayan,How is Nadeeya doing?


I hope she's coping well?


Hmmm Afzaal ke nan Nadeeya is not in a good shape at the moment, but Doc Bashir is trying his best,


Can we go and see her right now pls? 


Aa Afzaal dare ya Riga da yayi yanzu, and ka ga yau ka dawo daga USA am sure akwai gajiya a jikin ka,and ni kai Na a gajiye nake ka dai bari gobe da safe sai mu je ka duba ta,bayi da yanda ya iya toh kawai ya ce da Sen sannan SEN ya wuce dakin shi domin watsa ruwa,


.........Doc Nameer


Tunda yayi asuba be koma bacci ba,wanka yayi bayan ya kammala Azkar in shi sannan ya fito ya shirya cikin black trouser and white shit Wanda ba karamin karban shi suka yi ba,


Breakfast in da yayi order ya zauna ya ci cikin kwanciyar hankali, sannan ya tattara duk wani abun bukatun sa ya dau car key in shi tare da rufo dakin ya sauko kasa da key in,


A reception in ya aje musu key,sannan yace da su ya fita sai ya dawo,Allah kiyaye suka mishi sannan ya fada motar shi,da taimakon Map location da yayi setting a wayan shi ya iso Asibitin da aka mishi transfer, inda yayi parking a inda ake parking motoci,bayan an nuna mishi fanin da yake wato fanin Psychiatric,


Shiru kawai yayi a cikin motan yana me kare wa building in asibitin kallo tare da mutanan da kai kawo a cikin asibitin, yayi kusan mintuna yana zaune shi fargaban fitowa ma yake ji,


Like ka je gurin da baka San kowa ba and ba wanda ya sanka ya fi komai ban haushi,be ma san ta ina zai fara ba ko wa zai fara samu ma oho, yayi kusan 10 mints a cikin motan yana ta nazari kafin can yayi shahada yana me buda kofar motan,bakin shi dauke da adduar ubangiji ya sanya ya fara a saa, Allah ya bashi ikon da zai amfanar da mutane daga ilimin da yayi masa,Allah ya Hana ni zalintar kowa kuma ka tsare kowa daga zalinta ta,shine addu'oin da yake bakin shi yayin da ya fito daga cikin motan...



Ina matukar godia da irin so da kaunar da kuke nuna mun,Allah ubangiji ya bar mu tare,


A cigaba da sharing and commenting pls,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi❤️🙏🏻.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEY BEE)


.......

 

My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin San ba sharhi bane zai kawo ki toh don Allah kar ki shiga, haka zalika maza don Allah kar suyi joining domin group in mata ne zallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su,contact me via:


   08100046388


..........

         Page nine


**********


Cike da takun nutsuwa fuskan shi Na kallon kasa har ya shigo cikin clinic in hannun shi dauke da takardu,


Mutane daban daban ke kai kawo,Wanda yawanci nurses ne da kuma doctors sai workers, sai kuma tsirarun masu jinya da suke sanye da uniform a jikin su,don du samu su sha iskan safiya tare da hasken ranar hantsi,


Da ido yake bin su da kallo abun tausayi ganin haukan da suke yi tuburan,adduar samun lafiya yake wa ko wannan su,


Hey Mr Handsome in da ya ji an ambata ne ya sanya shi ja ya tsaya cak,domin tabbas ya san da shi ake yi,and duk Wanda ya kira shi da wannan sunan most be one of his old school friends and mate,


Da mamaki ya juyo domin ganin waye haka,a tsaye ya ganshi yana zuba masa murmushi,


Shi din ma murmushin ya maiyar masa tare da bin shi da kallon mamaki,tabbas ya gane shi, course mate in shi ne Wanda zai iya ce wa ma suna mutunci ba laifi domin har auran shi ya zo, canza wayar da ya yi ne ya sanya shi losing in contact in shi,


Doc Habeeb long time no see,Nameer ya ce yana mika mashi hannu,


Ka bari kawai mr Handsome I have been trying your no for a long period of time bana samun ka,har Na zo Na hakura,


Ayya wlhy Habeeb line ina ne ya samu matsala Na canza sabo,sai kuma nayi losing contact in ka,how have you been,wai me ma ya kawo ka Bauchi,


Dariya doc Habeeb ya sanya sannan ya ce see you ai kai zan wa wannan tambayan domin Bauchi kam ai garin mu ne,and wlhy a nan Na samu aiki,so ka ga am working here kai fa me kake yi a Bauchi,


Hmmm bari kawai Habeeb ni ba Na manta ba Ashe kai Dan Bauchi ne wlhy transfer aka mun daga 44 xuwa nan hospital in jiya shigowa ta ma,


Ayya toh ubangiji ya sa da abunda ya tare,where is madam ko ka bar ta a can masaukin ka,am very sure yanzu kam kuna da babies ko,


Jin abunda ya fadi ne ya sanya annurin fuskan Doc Nameer daukewa cak,lura da hakan ne ya sanya Habeeb cewa am sorry friend ko Na fadi abunda be dace bane,


Aa sam baka fadi abunda be dace ba ya daure ya ce,sannan ya kara da Alhamdulillah we are blessed with a little beautiful daughter, saidai unfortunately Noor ta koma ga me sama gurin haihuwar angel,


Allahu Akbar am so sorry for your lost friend,Habeeb ya ce yana girgiza kai,domin ba karamin mamakin mutuwar Tata yayi ba,and ya tausaya wa Nameer in domin shi kanshi sheda ne da irin kaunar da ke tsakanin Nameer da Margayiya,


Ubangiji ya mata rahma ya jikan ta sannan ya raya bayan ta,Ameen ya Allah Habeeb thank u so much,


Haba babu komai Mr handsome, so ina angel in take,wlhy Na baro ta Kaduna a gurin mama jiya da zan taho,


Allah sarki Allah ya raya ta bisa sunnah sannan yayi mata Albarka ya kuma baka mata ta kwarai Wanda za ta maye maka gurbin noor ta kuma rike Haanaan da amana,murmushi kawai Nameer yayi domin shi yana ji a jikin shi har ya koma ga Allahn sa bare kuma Kara soyayya ba balle har a kai ga batun aure,


A fili kuwa cewa yayi me hali baya fasa halin shi Habeeb har yanzu dai surutun Na nan,na biye ka sai mu kwana kana mun zuba,


Dariya Habeeb in yayi sannan yace ga ka kai kuma miskili ba baka kaunar surutu ko kadan saisa Sam bara ka iya zaman gida Na ba ashe domin daga ni har Madam da little boy in mu surutu gare mu,


Wait Habeeb wai kana nufin kayi aure,dariya ya dan yi sannan yace getting to 2 years ke nan da aure Na har Allah ya kawo karuwa mun samu baby boy,


Kai Masha Allah ubangiji ya raya shi da imani Allah ya kade fitina a zaman ku,ameen ya Allah doc Nameer ashe dai za mu Kara haduwa ikon Allah sai gashi guri daya za mu Na aiki,kai it was so nice seeing you again,


Smile Nameer yayi yace it was nice seeing too,ni dai yanzu nuna mun office in senior Doc in da ke gurin nan nayi reporting don Na samu mu fara aikin da kake murna an hada mu guri daya,


Dariya Habeeb yayi sannan yace bara ka gane bane,wlhy,Nameer haduwa da Wanda ka sani tun before dadi gare shi,mu je in gwada ma office in shi,sunan shi doctor Bashir sai kayi a hankali don mutumin Dan banza ne,


Kai kawai Nameer ya girgiza domin in dai surutu ne da gulma Habeeb to ya iya shi kamar wata mace,


Har bakin office in doctor Bashir Ubaidullah ya rako shi sannan yace da shi in kun gama da shi ma hadu a new office in ka ko nawa,da ki kawai ya amsa shi sannan yayi knocking in kofar bakin shi dauke da sallama,


A zaune ya tarar da Doc Bashir bayan yace da shi ya shigo,seat ya nuna mishi alamun ya zauan,bayan ya zauna in ne,yake tambayan shi daga ina,


Nan Nameer yayi masa bayani kan daga kaduna aka mishi transfer nan,


Saida ya kare masa kallo sannan yace ina takardun naka,


Akan table ya aje masa,sannan Bashir ya shiga dubawa a gadarance,ganin komai ya cika ne ya sanya shi dagowa yace well doc Nameer Abdallah Na ga takardun ka,komai normal ka koma gida daga gobe za ka fara aiki,


Da mamaki Nameer ke kallon shi why zai ce ya koma sai gobe ya dawo bayan shi ya dauka ya zai fara aiki,sai sa ma yayi sammakon sassafe,


Yana kokarin magana ne ya ji an bango kofan,a zuciye Bashir yace wannan wani irin Jaki ne haka zai bugowa mutum kofar office, ganin Nurse Kareematu ce tsaye tana watsa mishi kallon banza domin ta ji me ya ce wato ni ce jakar shine kalman da ta furta tana hararan shi,


Dariya ya dan yi sannan yace dadi Na da ke saurin fushi wallahi ai ban San ke bane,tsaki ta ja sannan tace wai ka je kayi baki,


Da mamaki ya maimaita kallman baki kuma ni kuma suka ce suna nema,


Ji wani tambayan iskanci Bashir in ba kai suke nema ba meyasa zan zo Na fada ma,SEN da wani matashi,


Jin sunan da ta ambata ya sanya da sauri Mike wa sannan yace haba Kareema why baki fada mun since ba kika sa zan bata masa lokaci ya kare yana gyara zaman lap coat in shi,


Nameer ya kalla sannan yace I got important issues a gaba Na so see u tomorrow kawai,ah Doc kace sabuwar hannu muka yi,Kareematu tace tana me bin shi da wani irin mayen kallo,


Jin abunda ta fadi ne ya sanya Nameer mikewa tare da watsa mata wani irin wulakantattcen kallo sannan ya bar office in,cike da mamakin wani SEN ne ya zo cikin asibitin nasu,


Doctor Bashir kuwa yanda kuka san zai yi wa SEN sujjada tsaban dukawa yana gaida shi,fuska sake SEN ya amsa shi tare da tambayan ya aiki,domin ba karamin murna yayi ba da jiya ya kira shi a waya ya sanar da shi plan in su Na ta working out,


Afzaal ya gaida wanda ya amsa shi cike da isa da gadara kamar Dan sarki,sannan suka nufi Isolated room inda aka killace Nadeeya,


Tun daga waje suke jiyo ihu da dariyar ta da alamun surutu take da kanta take irin wannan mugun dariyan,


Saida ya rubuta pin code in sannan kofar ta bude suka samu suka shiga kofar ta rufe,


A dantamalin kasan tiles suka same ta tayi zaman yan daukan karatu gashin kanta ya sauko sun rufe mata har fuska,Wanda su take irgawa wai don ta ga yawan,su sai ta kai quarter in counting in Sai ta manta shine abun yake bata dariya,


Da ido Afzaal yake bin ta da kallo domin ya kasa yarda wai Nadeeya ce wannan zaune a kasa hakan nan da sunan tayi hauka,


Kusa da ita SEN ya zo tare da taba shoulder in ta yana fadin princes look who is here to see you,


Juyowa tayi a razane don Jin an yi mata magana saidai Sam bata gane me yace ba,karaf idanun ta suka sauka a kan fuskan Afzaal,


Wata iriyan ihu ta sanya me mugun Kara Wanda saida kusan rabi yan cikin clinic in saida suka ji a ciki kuwa har da Nameer Wanda ke Dan zagawa don ganin ya tsarin gurin yake kafin zuwa gobe ya fara aiki,


Kamar Wanda aka tsikara ta mike da sauri har tana harde kafa tana kusan faduwa,flower vase in jikin gadon ta ta dauka kafin kowa yayi auni ta kwada wa Afzaal a goshi Wanda nan ya fashe kalban kuma ta yanka mishi fatan goshi nan take jini ya balle masa,


Wata iriyan Kara ya sake sakamakon azaban zafin da yake ji da kuma yanda jini ke zuba masa yake yi,baki bude Doc da Sen ke bin ta da kallo domin tunda ta fara haukan nata bata taba duka Ko attempting in ji wa kowa ciwo ba in ba kanta ba,


Kafin sukai ga mamakin ya sake su tayi wata super in Albarka tare da fitowa akan Afzaal Wanda saida ya kai kasa,


Wuyan rigan shi ta cukumo Wanda ya baci da jini,idanun ta Na fidda hawaye tana ihu ta hau cizon shi tana Marin shi ta ko ta ina a fuskan shi,


Ihu yake domin ba karya ba karamin azaba yake sha ba,domin in ta kama fatan yanda ka san ta samu fatan rago ko kaza yanda take ja ga shi zafin Marukan nata yake ji har cikin brain in shi,


Ihu yake yana fadi Daddy help me pls zata kashe ni,ina Nadeeya bata ma San yana yi ba duka take mishi ta ko ta ina kamar Wanda Allah ya aiko ta,tana kuma kan ihu tana surutan da ni kai Na ban San me take fadi ba,


Ganin tana kokarin kashe shi da duka ne ya sanya doc Bashir danna wani red button Wanda yayi alarming in nurses su taho da sauri akwai matsala,


Ai ko cikin sauri sai ga su Sister Kareematu da kyar aka samu aka banbare ta daga kan Afzaal tana ihu tana cizon nurses in tana fadin su bar ta sai ta kashe wannan dan iskan mara tsoron Allah,a bar ta ta ga bayan shi,domin barin irin wannan mugayen shi da Sen a doran kasa masifa ne domin Jinin su ya Riga da ya halatta,shine irin ihun kukan da take yi,da kyar da sidin goshi aka tsikara mata aluran bacci tare da kwantar da ita,tare da sanya mata chain a hands inta,ganin tayi bacci ne ya sanya Doctor Bashir cewa Kareematu ta ja Afzaal a je a gyara masa ciwuwukan shi,in an gama ya same su a office in shi,


Hannun SEN ya ja tare da fitowa da shi daga dakin har suka iso office in shi jikin SEN a mace yake da abunda Nadeeya ta aika ta,


Zaunar da shi Bashir yayi tare da ibo mishi ruwa me sanyi a cup daga dispenser ya mika wa SEN,yallabai ga ruwa ka samu ka sha,


Kofan SEN ya buge cike da tsantsan bacin rai Wanda yayi sanadiyar tarwatsewan cup in,


In sha ruwan me Bashir ruwan uwar ka kake son Na sha ya kare tare da wanke fuskan doctor Bashir da Mari,(Sen irin mutanan nan ne da Sam basu Iya controlling anger in su ba,in ran su ya baci in ba duka suka yi ba basa Jin anger in zai fita ko in ce irin masu saurin hannun nan ne),


Da hannu biyu Bashir ya dafe kumatun shi domin ba karya Marin ya shige shi,


Cikin zafin rai SEN yace Amman wlhy Bashir ban taba ganin Dan iska da ya raina mun wayo ba irin ka,Dan uban ka kace da ni Nadeeya tayi hauka ita kanta bata san waye ita ba balle ta san su waye a kan ta ya kare yana tsare shi da ido,


Ba karamin baci ran Doc yayi ba Amman haka ya daure yace ranka ya Dade kayi hakuri,wai hakurin uwar me zan yi kana nufin 50 mil in da ka karba a banza ne ko me?


Aa sam SEN ba haka bane, wlhy Na rantse ma da girman Allah a halin da ake cikin nan Nadeeya is not in her normal senses, tabbas ta yi nisa a hauka sabida injections In da nake bata,


In har ta haukace a taya ta gane Afzaal har tayi attacking in shi tana neman kashe shi,za ka fada mun gaskia ko sai Na sa an daure mun kai domin wlhy babu Wanda ya isa ya ci kudi Na ya kwana lfy Dan uban shi ba a yi shi ba,


Zufan goshin shi Doc ya goge yana Jin radadi a kan kumatun shi har yanzu kafin yace,


Ranka ya Dade maganar gaskia wlhy Nadeeya ta samu tabin kwakwalwa a yanzu haka,saidai one thing da nayi observing shine,har yanzu zuciyar ta ta kasa manta abunda kayi mata Wanda kila yana da hadi da wannan yaro da kuka zo tare,domin tun da muke da ita ko yatsan wani bata taba kamawa ba,


Tayu mun tsayar da aikin brain in ta mun kuma sanya shi kamuwa da tabuwa sabida aluran da muke bata amman abubuwan da ke heart in ta fa,ranka ya Dade daga gani akwai abunda kuka mata kai da Azaal Wanda ta kasa manta shi har yayi motsa ciwon nata har tayi attacking in ta,


Dan numfashi ya ja sannan yace sir zan iya sanin miye kuka mata da zafi har haka duk da tana cikin hauka ta kasa mantawa,domin ga dukkan alamu yarinyar nan zalintar ta kuka yi,


Baki a bude SEN ke bin bashir da kallo kafin can yace,lalle Bashir ka mance da waye kake magana,yanzu don asaraa a zuriar ku ta kare ni ne zaka kalli tsaban idona kace Na zalunci yarinya ta Na sanar da kai me muka mata,Dan uban ka har kayi girman da za ka fada mun wannan maganar banzan,ya kare tare da nufo kanshi,Wanda tsoro ya cika basir dam domin har fitsari ya fara digawa a wandon Shi, don ya ga alamun bugun bura uba SEN zai yi masa a cikin office in nan,


Afzaal ne yayi saurin riko shi Wanda shigiwan shi ke nan saman kan shi dauke da bandeji,


Take it easy dad kar ka ji masa ciwo,sake ni son Dan bura uba ni wannan matsiyacin ke fada min maganar da ya zo masa,Dan uwar shi dan Kabiru ya kawo shi ya ci arziki,saisa ni Sam ban so nan din ba Amman Kabiru ya nace,ka sake ni in samu in fasa wa Dan iska baki,


Gam Afzaal ya rike shi yana daddy pls try to control ur anger mu samu solution domin Na ga anya Nadeeya tayi hauka kuwa,I can see so much hate in da take mun daga cikin idanun ta,


A gaban SEN doc Bashir ya zube yana me rogon SEN afuwa kan ya yafe masa yayi kuskure,da kyar aka samu SEN ya hakura bayan ya kafa wa Doc last warning kan ya tsaya iya inda aka aje shi,


Duk shiru suka yi kowa Na tunanin ta ina ne mafita domin kan SEN gabadaya ya kulle gani yake da daga inda aka haukatar da Nadeeya matsalan shi ta kare,zagi da cin mutuncin da take masa zai kare,Amman me abun da tayi yau din nan ba karamin dada tsorata shi tayi ba ,although an ce tayi haukan but abun Na ranta wanda wat if wataran ta fada a inda be dace ba fa shike nan ta tona mishi asiri fa,kai ina bare yu ba shine abunda ya fada yana me girgiza Kansa,


I got an idea shine abunda doc ya fadi,go on dad yace da shi,cike da farinciki kila treatment zai canza mata,


Dan shiru yayi don be san yanda SEN zai karbi idea in nashi ba


Hmmm ranka ya Dade duba da nayi Nadeeya barazana ce a cikin rayuwan ka why not kawai a kau da ita,wat I mean hers is why not a kashe Nadeeya kawai ka ga shike nan hankalin kowa zai kwanta,


Ai ko be kai ga rufe baki ba ya ji saukan yatsu tassss a fuskan shi,wannan karan saida ya saki Kara sabida azaba,


Both daddy maganar Doc Na kan hanya duk abunda zai baka ciwon kai kashe wannan abun shine zaman lfyn ka since ai Na fada maka ka bari a kashe ta kawai ko ma samu mu huta Afzaal ya kare yana turo baki,


Tassss ya ji saukan Mari a fuskan shi Wanda cike da mamaki ke kallon Daddyn,


Ku Ashe mutanan banza ne mutanan wofi ban sani ba,wai Nadeeya muke maganar a kashe ka,kai Afzal ka mance Na fadin maka Nadeeya ita ce rayuwa ta,ko nesa da ni baran bari ta je ba balle ace ta bar duniyar,


Dole Nadeeya ta zama a raye,and wlhy wannan ya zamo Na karshe da za ku Kara yin irin wannan tunanin ko kuma wlhy ku kare rayuwar ku a cikin prison, wawaye Wanda basu da amfanin komai, shike nan ni da kai Na Na san mafitar da zan dauka,wuce mu tafi  yace da Afzaal yana fita daga office in,


Idanu taf da hawaye Bashir ya bi bayan SEN da shi Allah ya isa na,mutum yayi ta Marin ka kamar uban ka,ya San yana son yar tashi ya kawo ta nan in haukatar masa da ita,sannan yanzu ya zo yana ta faman marin mutane, akan me,(ni ko nace son duniyar ka ai duk me kwadayi yana tare da wulakanci, kadan ma ka gani),


**************Doctor Nameer 


Sister don Allah ihun Ms nake ji ne hka,and daga ina ihun ke fita haka,ya tambayi wata nurse da ta zo wucewa,


Hmm kila kai bako ne a hospital in nan,daga IR ne ihun nan ke fitowa,


Kallon rashin fahimta yayi mata sannan yace pls miye IR kuma,Dan dariya tayi sannan tace Isolated room, mamaki ne ya kama shi shi sannan yace kar ki ce Na fiye tambaya waye a IR in,


Baki ta Dan taba sannan tace eh wlhy Na ji dai an ce wai Yar gidan SEN ce a cikin dakin Nadeeya Audu Waziri,ta kare tare da barin gurin,


Wani irin mamaki ne da al'ajabi ne suka Kama Doc Nameer, domin shi wlhy tun Randa suka yi hira da Mujaheed ga me da case in su be kuma matsa wa kan shi sai ya San abunda ke wakana,domin shi duk daukan abun yake akan acting ne don ya samu sympathy in mutane,a haka ya fito ya shige motar shi don komawa masaukin sa,zuciyar shi cike da tarin tambayoyi kan me ya kawo Nadeeyan gidan mahaukata......



A cigaba da sharing ana commenting ina yi muku son so fisabillilah🙏🏻❤

️😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEEY BEE)


.......


My what's app group link



 https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


Ina maraba da duk me son shiga saidai in har kin san bara ki Na comments ba,toh don Allah kar ki shiga,haka zalika maza kar ku shiga pls wannan group in mata ne zallah akwai kuma matan aure🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via:


     08100046388


.........

        Page ten


********** Doctor Nameer


Har ya iso masaukin shi yana janjanta wannan alamari Na Nadeeya yar gidan SEN, ikon Allah toh ke nan da gaske dai haukan tayi to me ya hauka ta ,and akan me take yi wa uban ta mahaifi irin wanann zagi haka,dole akwai Abu a kasa,ruwa bata taba tsami banza,


Dole akwai boyayyan alamari da ke birne a kasa,haka kawai ya ji yana son sanin miye ke damun yarinyar nan like yana son ya sani miye ya same ta har ta haukatar ta haka,tun yaushe ne ma ta haukacen har da kai ta hospital in mahaukata,


And in har da gasken tayi hauka a irin kudi da taimakon SEN ai kasar waje ya kamata ya fidda ta domin nema mata lafiya ba wai a kawo ta asibitin Specialist ba,irin wannan tambayoyin ne ke ta masa yawo a cikin brain in shi,


Can kuma wata zuciyar tace da shi kai miye naka Nameer ina ruwan ka da ita ka san ta a ina da har kake Jin wani iri a game da abunda ke samun ta ka bi ka dage hankalin ka,ka San ta ne??


A fili ya amsa aa ni ko ganin ta ma ban taba yi ba sai a video ban San ta  ba kuma babu abunda ya hada ni da ita,Allah ya bata lafiya shine abunda ya ce tare da Saurin cire tunanin ta a ranshi ya fito daga cikin motar bayan yayi parking,


Key in room in shi ya karba tare da hawa sama ya bude dakin,kai tsaye toilet ya fada ya watsa ruwa sannan ya fito, abinci yayi order domin ba karamin yunwa yake ji ba(ni ko nace kai dai ka ji mutan Bauchi an iya girki ya sanya kake haba haban cin girkin su,lol)


Saida ya gama cin abincin sannan ya kira Mama,gaisawa suka yi sannan ya bata labarin yau ya je asibiti yayi reporting an ce gobe ya dawo in sha Allah,


Ba karamin dadi ta ji ba,addu'oi tayi ta masa na fatan Alkhairi da kuma tsari,nan suka shiga hira har ta bai wa Haanan tayi ta yi masa gwaranci,yana dariya abun shi,kusan 1 hour sannan yayi mata sallama tare da kashe wayan, yana Jin missing in Maman shi da little angel in shi,


Kashe kiran ke da wuya kiran Mujaheed Na shigowa, dauka yayi suka gaisa cike da barkwanci,


Mutumina ya hanya hope ka isa lafiya,ya ka ga garin to,


Dan murmushi Nameer yayi sannan yace baka da dama Mujaheed duk irin tambayoyin nan ni kadai,wlhy Alhamdulillah Na isa,Bauchi kuma is a very nice city,Na ma yi reporting gobe zan fara aiki In sha Allah,


Toh Allah ya kaimu Aboki Na ya sa a fara a saa,ka ga SEN ina kuma hope ka mika sako Na,


Goshi ya dafe sannan yace Mujaheed wlhy baka da hankali,ni a ina zan ga SEN Na ma zo barin hospital ne Na ji ihu...anan ya kwashe komai ya sanar da Mujaheed,


Idanu Mujaheed ya zaro sannan yace wai you mean Nadeeya Audu Waziri ne ke mental asylum in ku,wlhy nima abun ya bani mamaki sosai Mujaheed kai Na ma ya daure and da alamu ma ta kwana biyu a gurin,


Ikon Allah ke nan da gasken dai jifan nata aka yi,Allah sarki baiwar Allah toh Allah bata lfy,ka samu ka ganta ina,


Wlhy Mujaheed baka da hankali in ce ma an ce sai gobe a ina zan ganta beside kasan waye mahaifin ta so ba ma tare da sauran majinya ta take ba,a isolated room aka aje ta Wanda ban San a ina yake ba,kar ma ka tambaye ni a ina isolated room in yake ,


Dan dariya Mujaheed yayi sannan yace wlhy baka da dama Nameer,kai din ne ka cika tambaya ya bashi amsa cike da kosawa,nan suka cigaba da hirar Na su,


.........SEN RILWANU


Shigowan su part in shi ke nan,inda kallo daya zaka masa ka gano ranshi a matukar bace yake,


Jiki a sanyaye Afzaal ya ja legs in shi tare da zama a bakin kujera yana Jin gaba daya jikin shi Na ciwo,more especially fuskan shi,sakamakon dukan da ya sha a hannun Nadeeya,


Kallon SEN yake dake zagaye parlor in ya ma kasa zama,cikin muryan shagwaba yace haba daddy marin da ka mun dazu

was that necessary??


Juyowa yayi cike da bacin rai yace yes Afzaal Na ga alamun baka cikin hankalin ka ne,that slap nayi maka ne don ka dawo sense in ka,and ko yanzu ka kuma cewa a kashe princess sai ma kuma kwada maka marin da sai ya haukatar da kai,


Ban taba sanin baka da hankali ba sai yau in ce nan ni da kai nayi maka bayanin irin mahimmancin da Nadeeya take da shi a cikin rayuwa ta,and ka ce wai a kashe ta,in ka manta in tuna maka in har Nadeeya ta mutu to daga kai har ni Asirin mu tonuwa zai yi,aikin banza ya kare tare da Jan tsaki,


Tasowa yayi domin ganin ran daddyn yanda ya baci,a hankali yace am so sorry Dad tashin hakalin ka ne bana so ya sanya nace a kawar da Nadeeya in Na mance Ashe mutuwar nata tonuwar asirin ka ne,ko in ce mu baki daya,


Kallon Afzaal in yayi sannan yace is okay Amman kar ka Kara fadin Abu irin haka,baran Kara ba Daddy pls kar ka Kara Mari Na ka ji, ya kare a shagwabe tare da fadawa jikin daddy kamar zai yi kuka,


Bata mun rai kayi son Amman kasan ai da baran mare ka ba,ya kamata kana sanin Abu kafin ka fada,baran Kara ba shine abun da Afzaal ya fadi,(ni mamaki nake ganin yanda wannan katon mutumin ke zubawa SEN shagwaba domin a kalla Afzaal zai kai 33 years,yake Abu kamar Dan 6 years old),


Ciro shi SEN yayi daga jikin shi sannan yace now wat is the solution son,


Hmmm dad ni kai Na gaba daya ya kulle wallahi ban ma San me zan ce ba,


Dan shiru SEN yayi sannan yace okay ka kwantar da hankalin ka,i know what to do,Allah ya kaimu gobe dole zan je Kwara state,


Baki Afzaal ya zumburo sannan yace amamn tare za mu je ko,face in shi SEN ya shafa sannan yace capital no ni kadai Na zani kwana daya ko biyu zan yi Na dawo so ba sai mun je ba,bari Na shiga Na huta ka ce da Saa'eed yayi shiru sassafe za mu dau hanya domin a mota za mu je,sai ka samu ka shiga ruwan zafi ka gasa jikin ka ko za ka ji dadi,daga fadin haka ya wuce dakin sa,


Tun kafin ya rufe kofa ya shiga kiran layin Alhaji Kabiru sai da ya kira sau uku kafin nan ya dauka,murya duk a gajiye kamar Wanda ya gama aikin wahala,


Hello Senator ya kake ya fadi da kyar, tsaki SEN tayi sannan yace kana ina ne ina ta kiran ka,


Dan dariya ya sanya sannan yace ina ko zan ji kiran ka ina cloud 9 wlhy wasu zafaffan babies Na samu suke jiyar da ni dadi,


Tsaki SEN ya ja sannan yace kai dai wlhh Allah ya shirye ka,ya shirye mu tare Kabiru yace tare da tashi yana sanya bathrobe domin rufe tsiraicin sa,


Ina Jin ka akwai wani abun ne Na ji muryan ka wani iri,


Hmmm wlhy Kabiru ina cikin damuwa da rashin hankali kace da ni ina da mun sanya Nadeeya ta haukace shike nan komai ya zo karshe yau ba ka ga abunda ya same mu ba,nan ya kwashe komai ya sanar da Alhaji Kabiru, ikon Allah toh wannan abun gaskia babban Abu ne ya fara so ya fi karfi Na,


Haba Aboki Na ya zan yi ne wlhy kai Na duk ya kulle,ka taimake ni ban son asiri Na ya tonu kuma muddum ta cigaba da fade faden nan za ta iya tona mun asiri,


Hmm gashi kai kuma bara ka yarda a kashe ta ba ko,Kabiru ya kare yana dariyan iskanci,


Haba kai kuwa sai kace ka manta waye Nadeeya a gurina ai kashe ta ma is not an option,


Toh wannan abun kawai ka bar shi sai gobe ma tattauna in mun isa kwaran,tare za mu wuce ne ko in yi tafiya ta,


Aa kawai ka je abunka ni da Saa'eed za mu taho in sha Allah,to shike nan babu damuwa sai kun iso in,ka dai kwantar da hankalin ka ka samu ka mori rayuwar ka wannan yawan tsoro da furgicin duk ba naka bane,shine abunda Alhaji Kabiru yace kafin suyi sallama ya kashe wayan shi,shi wlhy har tsoron zuwa kwaran nan yake gobe,bayan tsoro kuma har ya fara tausaya wa kan shi sabida irin nisan tafiyar da za su ci,da haka ya gama duk abunda zai yi da wuri ya kwanta domin ya samu ya tashi da wuri goben,



..........Kwara state

                

            Offa village


A can cikin wata kauye wai ita Offa da ke karkashin Kwara nake ganin shigewar manya manyan motoci,baka Jin komai sai karan wuce wan su,Wanda yan garin Sam basu da kwanciyar hankali in har wata ta kama,domin shige da fice kam har sai sun gaji,


Bin motar da ya zo wuce wa nai,Wanda ke ta tsala gudu,sai kutsawa cikin kauyen yake yi,tafiya ce taki karewa har na ga an fara barin kauyen an sauka a kan titi an fara bullan cikin dajika,Wanda kallon shi kawai abun tsoro ne duba da irin shirun da gurin yayi da kuma yawan bishiyoyi da kuma yawan kukan dabbobi da ake ji,


Saida aka yi kusan tafiyar one hour,sannan Na hango wata irin katon building, mamaki ne ya kama ni,domin irin katon duplex building ne me dauke da kalan ja da fari,domin gate in kofar gidan ma Ja ne,


Mamaki ne ya kama ni waye zai Gina irin wannan katafaran gidan domin gida ne da mutane dari biyar ma sai suyi rayuwa a cikin ta ba tare da sun takura ba,ko gidan waye wannan oho,


Kamar an ce in daga kai Na idona ya sauka akan rubutun da ke manne a cikin mannyeb harufa a saman gate in gidan,BLAZE HOUSE (gidan wuta) Na gani a rubuce tare da alaman wuta a ci a gaban rubutun,


Mamaki be karasa kama ni ba saida aka bude gate in,Ashe ban ga komai ba daga waje domin gida ne me girman gaske,tambaya ce fal rai Na ganin different kaloli da designs in motoci Na Alfarma sun kai guda dari biyu a Parke a tsakar gidan,


Tsoro ne ya fara kama ni a haka dai Na daure Na kutsa kai Na cikin gidan,Wanda mutane ne birjit a cikin katon Hall in taruwa sanye da jajjaye da bakaken kaya,


Mamaki be Ida kashe ni ba sai da Na hango wani tsungune a gaban wata kujera a wani sashi Na gidan a tube haihuwar uwar sa,yana jiran shugaban kungiyar ya bayyana domin ya samu ya isar da kukan shi,kamar an ce da shi ya dago karaf muka hada ido,salati Na sanya tare da wurgi da biron hannu Na sakamakon tozali da nayi da Senator RILWANU AUDU WAZIRI.......



Wannan shine ana dara ga dare yayi,mu je zuwa masoya Na yanxu wasan zai fara dadi💃🏻,


Ina matukar godia da irin kauna da goyan da kuke nuna mun group members ina,ina yi muku son so fisabillilah,


Masoya Na Wanda Na sani da Wanda ban son su,ina matukar godia da irin goyan bayan da kuke bani,Allah ubangiji ya bar zumunci,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi,


   Sai gobe kuma in sha Allah 🙏🏻

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEY BEE)


........


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin San bara ki Na comment ba toh don Allah kar ma ki shigo,domin ko kin shiga zan fidda ki,haka zalika maza ma kar su shigo group in nan,domin group in mata ne zallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via:

     

       08100046388


........

       Page eleven & twelve


************


Odogwu Na shiga uku na lallace asiri Na ya dab da tonuwa a bai nan duniya,ka taimake ni in baka rufa min asiri ba ban San yanda zan yi ba,duniya za su yi mun tofin Allah tsine, komai da Na mallaka zai kare,sanin kan ka ne bani da burin da ya wuce na samu kujeran takaran gwamma na jahar Bauchi,SEN ya kare cike da kuka zufa duk ya wanke mishi fuskan shi kanshi a kasa ya hade Hannaye guri daya,


Wanda ake kira da Odogwu ko pimmm be ce ba illa wata katuwar maciya da ke gefen shi da yake shafawa,


Dago da idona nayi tare da kare masa kallo,ya subhanallahi Na furta domin wani irin mummunan halitta da nayi arba da shi,baki ne wuluk munannanne irin manyan mutanan nan Wanda kallo daya za ka masa kasan shi da tausayi da imani sun yi hannun riga, yana sanye da kaya kallan fatan damisa,fuskan shi a matukar daure daga ganin alamun sa kasan baya cike da farinciki sannan daga ganin shi bare yi tausayi ba,


Ganin be ce da shi komai bane har na tsahon lokuta ya sanya SEN ya shiga mishi kirari da yarbanci,yana yabon shi yana masa kirari da nuna tsantsan mulki irin nashi,fadi yake ya taimake shi kar ya gaji da shi,in har be taimaka masa ba waye zai masa,shine me amsan dukka rokon shi sannan ya share masa dukkan hawayen shi,in har ya juya masa baya,toh tabbas rayuwan shi zai daidaice,


(Waiya zu billahi,kai mutane mu ji tsoron Allah sabida neman duniya mu saida imanin mu har ka ji mutum Na daukan hakkin Allah yana baiwa wanin shi abunda Allah kadai ke iyayi Amman sabida jahilci ka dauka ka mika wa wanin shi,ubangiji ka tsare mana imani da mutuncin mu, Allah ka tsare mu da aikata  shirka🙏)


A gadaran ce Odugwu ya dago tare da kare wa SEN da ke durkushe a gaban shi kallo,me cike da tsantsan bacin rai,kamar bare yi magana ba kuma sai Na ga ya bude baki,


Cikin muryan mara dadin sauraro da hausan da bata ishe shi ba,yace RILWANU ya tabbata baka Jin magana,and Na ga alaman you are trying me ne wlhh,


Cikin sauri yace Odugwu ba haka bane Na tuba wlhy ni kai Na ban san yanda aka yi Nadeeya ta ji mu ba,


Wata irin tsawa ya daga wa SEN Wanda saida ya sanya shi kusan sakin fitsari,duk irin Dade war sa da irin kyautata wa Odugwu da yake yi a kunyar nan ba shi zai Hana in ya dan kuskure ya ci uban shi ba wani zubin harda punishment yake masa,


Sau nawa zan yi warning in ka,akan kar ka kuskura kana kira mana sunan God anan,kasan da shi ka zo nan,ko ba bukatun ka muke biya maka Wanda shi ya kasa biya ma ba,(ya salam jahilci be yi ba sam wlhy),


Cikin sauri SEN ya daga kai yana me bawa Odugwu hakuri,


Tabbas kayi babban kuskure da ka bari yarinyar ka ta san halin da kake ciki,Wanda bata da buri da ya wuce ta ga tonuwar asirin ka,Wanda tonuwar asirin ka ya shafi duka yan  kungiyar  BROTHERHOOD gaba daya,


Kuskure aka samu Na tuba Odugwu kai me rahma ne ka taimaka ka yafe ni sannan a san yanda za a yi kar yarinyar nan ta tona mun asiri,


Wata irin dariya me karfi Odugwu ya sanya Wanda saida dakin gaba daya ya amsa sannan yace,dole kashe ta za a yi,yau cikin dare zan sanya aje a ibo mun Jinin ta in baiwa dodon tsafi zai yi farinciki da kai sannan ina maka albishir in kai za ka ci zabe,tashi ka tafi matsalan ka ta kau,


Zabura SEN yayi tare da kwanta wa yana me rike kafafuwan odogwu cikin kuka da be ma san yaushe ya zo masa ba ya hau rokan sa,ka taimake ni Odugwu kar a kashe Nadeeya,yarinyar nan has suffered a lot,and kai kan ka kasan rayuwar ta shine cigaba Na,


Dariya ha kuma yi sannan yace duk wannan ba matsala bane ko tana raye ko bata raye in har kana tare da mu,za ka cigaba da shahara da daukaka,


Odugwu banda kashe Nadeeya ita ce rayuwa ta,ka mun rai ayi wani abun daban ba wannan ba,


Wani irin hangade shi yayi saida snake in jikin shi ya fadi tare da nufan Sen rai a bace yana neman kai masa Sara,idanu SEN ya kamkame bugun zuciyar sa Na karuwa domin ya San muddum snake in nan ya sare shi shike nan ya rasa rayuwar sa,



Hannu ya daga sai ga snake in ya tsaya,da kanshi ya sauko tare da daukan snake in,kanshi ya shafa tare da masa kiss a baki,sannan ya koma gurin zaman sa,


Dan shiru ne ya biyo baya kafin can Odugwu yace ya kake so ayi yanzu,you are one of my favorite costumers,domin kana baiwa kungiya abunda take bukata,saidai at times kana bani ciwon kai Rilwanu,ya kare yana kada kafafuwa,


Da sauri ya matso ganin shugaban nasu ya fara sauko wa,Na san tabbas in har Nadeeya ta bude bakin ta ko ta samu dama guduwa za tayi,sannan tonuwar asiri Na ya zo ke nan,duniya za tayi tir da ni ,ina so ayi mata aikin da baxa ta iya guduwa ba,sannan duk yanda za ayi bara ta iya magana ba,ya kare yana me addua a ran shi Allah ya sa shugaban nasu ya yarda da abunda ya ce,



Dan dariya yayi me razanar wa sannan yace kai mutum ne ne tsatsan son kanshi a kowani irin hali,ya sanya da ka tashi zaban hukuncin da za a wa Nadeeya ka zabar mata ma fi sauki,


Hmmm well tunda kai da kan ka ka zabi hakan Na yarda Amman dole kasan akwai paying price kafin aikin ka yayi right,and baka isa kace bara kayi ba,


Cikin sauri yace Na yarda koma miye zan yi odugwu just say it,am ready in yi koma miye,ya kare zuciyar shi Na bugawa domin shi har yau ya kasa sabawa da irin abubuwan da shugaban ke Sanya su,


Zama ya gyara tare da cewa well,this time around you have to make Sacrifice,


And wannan karon blood muke bukata Na kuma new born baby boy wanda aka haifa kar ya wuce 1 hour da fitowa duniya,in har ka kaba za ayi farinciki da kai sannan aikin ka zai yi,


Gumi ne ya karyo wa SEN yo shi ina zai samu new born baby boy har ma ya bada Jinin nashi wa dodon tsafi,ya shiga uku,


Odugwu be jira cewan shi ba ya bar gurin yana taku kasan gurin Na amsawa domin irin dogaye manyanan mutane ne,kato ne sosai,kai tsaye cikin Hall in ya koma domin ganawa da sauran mutanan gurin,


Jiki a sanyaye SEN ya mike tare da haurawa sama,wani daki ya shiga Wanda ba komai a dakin sai wani katon gunkin Na miji a tube,


Faduwa yayi a gaban gunkin bayan ya gama maza kirari ya taba kafafun shi don neman Albarka, sannan ya kama private part in gunkin tare da tsotsa sau uku,sannan ya mike,bayyanar kayan shi a bayan gunkin ne ya tabbatar masa sakon gaisuwan da ya isar an karba,and ga dukkan alamu fushin da ake da shi ya sauka,dole yayi takatsantsan duk laifin shi ne da ya bari had Nadeeya ta san asirin shi,


Cikin sauri ya dauki ja da bakin kayan da ya gani ya sanya a jikin shi,sanann ya sauko ,da Alhaji Kabiru suka ci karo a bakin stairs in,hope komai normal koh ya tambaya yana kallon shi,


Mu je a gama taron nan Na baka labari, nan suka jero suka shiga gaisawa da mutane Wanda kowannan su,Na dauke da wata bakar zobe a hannayen su,hade babban yatsan su suke guri daya tare da murxa zoben juna haka ake gaisuwan,


Guri suka nema suka zauna,nan masu bukatu da masu sacrifice suka fara gabatar da shi a gurin Odugwu,


Kusan hours in su uku,sannan ya tafa hannu nan take maaikatan gidan suka fara fitowa da tray a hannayen su Wanda ke dauke da naman mutum akan plate da kuma Jinin mutum a cikin glass cup,nan suka shiga serving babu tsoron Allah kowa ya shiga ci hankali kwance,baka Jin komai sai karni jini da Hall in ke yi,


Saida aka ci aka koshi sannan kowa ya shiga goge bakin shi,tashi Odugwu yayi tare da Kara karfafa su kan duk wani damuwar su da matsololin su ko wace iri ce zai magance sa,sannan kar su sake duk Wanda aka bashi aiki yahi a bayyane ko ha kuskure,domin tonuwar asirin daya kamar tonuwar asirin duka yan kungiya ne,kowa kuma yayi kokarin yin aikin da aka bashi ko kuma ya hadu da fushin shugaba, suna iya watsewa sai next month kuma in lokaci ya kai,daga haka ya bace bat bayan sun rusuna duka domin nuna tsantsan biyayyan su,


Sama kowa ya hau tare da canzo kayan su,nan suka fito tsab kamar ba su ba,


Mamaki Na yi ganin manyan fuskokin yan kasar nan a wannan gida,ikon Allah gaskia tsoron Allah yayi karanci a duniyar mun nan, mutum can go to any extend don ya samu abun duniya,Allah ka tsare mana imani da mutuncin mu,


Nan da aka hau gaisawa da juna suna shigewa motocin su Na Alfarma, ana sai kuma an hadu next month, ana ficewa daga gidan,fuskokin su cike da faraa bara ka taba cewa wa'in nan responsible mutanan ne ke kungiyar asiri,coz dukkan njn su suna da cikar halitta,(babu kamar Na SEN ni duk ya fi bani mamaki ma,a fuska kamar mutumin kirki Bini Bini ya kira Allah Ashe Dan iska ne mushuriki),



A mota daya suka taho da Kabiru sabida amotar shi ya bar wa Sa'eed a can wata expensive hotel me suna G_PINNACLE,


Normally a hotel in suke sauka duk sanda suka zo meeting,sai ya bar Saa'eed su wuce da Kabiru,


Suna tafe ne suna Dan taba hira, Abokina ya kuka kare da Odugwu ne,hmmm wlhy Kabiru ka mance kawai Odugwu yana gab da daina daga mun kafa,domin shi da kanshi fa yace a kashe Nadeeya bayan yasan irin mahimmancin da take da shi a guri Na,


Dan dariya Kabiru ya sanya sannan yace kai kuma Nadeeya yar zinare ce ko da bara a kashe ta ba,Na ga ko baka baiwa dodon tsafi Jinin ga ba za ta dai mutu,ba ya fi ta mutun ba da irin wannan rayuwar da  take yi mara yanci,mu yaran mu nawa muka bada,su ba ma son su su ne,


Are you talking about sacrificing in blood,kai kan ka sheda ne ne abubuwa nawa nayi sacrificing aa kungiyar nan,abubuwa nawa Na rasa,yanzu haka Nadeeya ta fa ke kwance a gadon asibiti mahaukata sabida ga San wani abu daga sirri Na,


Ganin ran SEN ya baci ne ya sanya Alhaji Kabiru maida abun wasa sannan yace to yanzu wat is the way forward ya kuka tsaya da odugwu, yace Na kawo mishi blood in new born baby boy ya San aikin da zai yi,kuma in yi making sure ban dau time ba,


Tab wlhy odugwu yana son ka inda wani ne yayi abunda kayin nan toh wlhy da uwar shi mahifiya za a ce ya je ya kwanta da ita sannan a bashi kyelle ya goga mata ya kawo wa dodon tsafi,


Baki SEN ya bude domin shi har yau in ya ji wani abun Na Brotherhood in nan sai zuciyar shi tayi raasss,


Hmmm kawai yace daga haka basu kuma magana ba a haka suka nufi hotel in,inda already Alh kabiru ya sanya an kawo mishi manyan matan yarbawa guda uku,yanda suka raba dare suna aikata sabon Allah, bayan sun gama ya faki idon su ya goga musu kyalle a gaban su bayan sun yi bacci, jaka ya bude tare da sanya wa ciki yana dariyar mugunta,ganin ya fi su wayo,sanin halin mutanan da ke zuwa offa ya sanya karuwan suka daina sanya pant don ibewa suke a bar su da jinya daga baya,


SEN kam be wani samu cikakken bacci ba,duk tunanin shi yanda zai samo Jinin new born in jariri yake yi,hakan ma wai Na miji, ga doc Bashir ba wai a gurin yan haihuwa ,balle ya kira shi ya bashi kudi,don ya San shi mayen kudi ne,da haka dai ya samu bacci ya dauke shi ,washegari sassafe suka dauko hanyan Bauchi bayan Alhaji Kabiru ya sallami babies in shi, su kuwa sun ga kudi harda basu no in wayoyin su wai in ya dawo next month ya neme su,karba kawai yayi suna barin gurin ya goge numbers in domin shi fa baya kwantawa da mace sau biyu, daman yana gamawa yake goga wa yarinya kyalle Wanda ke da haihuwa saida ki ji ana yi a makota,suna tafe tana yi wa SEN irin dadin da yaran nan suka jiyar da shi a daran jiya,Dan tsaki SEN yayi toh shi a ina zai ji tunda ba da shi aka ci uwar sabadan ba,don't worry my friend kaima ka kusa barin wannan abunda Odugwu ya sanya ka,a canza maka Na san ka gaji ko,hmmm wlhy ni Kabiru har Na saba, in ban yi ba bana Jin dadi,dariya Kabiru ya kwashe da shi sannan ya nufi kafadun shi yace shege Aboki na kace ka ji dadin abun Amman Na ga randa aka ce ka fara hankalin ka yafi Na kowa tashi, hmm bara ka gane ba nima one the Na zamo addicted,daga haka basu kuma magana ba kowa yayi shiru da abunda yake sakawa a ranshi,


.........

         5 Days later


Doctor Nameer ya fara aikin shi gadan gadan,babu wata matsalan da yake fuskanta a Asibitin sai Na Doc Bashir da kuma Na Nurse Kareematu domin ba karamin shige masa take yi ba,haka in ta ganshi za tayi ta karkada tana wani farfari da idanu tana lankwashe lankwashen murya,saidai har tayi ga gama be masan tana gurin ba domin yi yake kamar be san da halittan ta ba,Wanda ba karamin haushi take ji ba ganin irin halin ko in kula in da yake nuna mata,sai kuma Doc Bashir da ke yi masa kallon wulakanci domin lokaci daya ya ji ya tsane shi domin ya ga alaman yaron akwai brain kuma yana da hazaka, in ka cire  mutane 2 nan to baya fuskantan ko wace matsala aikin shi yake cike da kwanciyan hankali, saidai yana mamakin har yau da be hadu da Nadeeya ba domin haka kawai shi yake son ya ganta,


..........SEN


A kwance yake a kan gadon shi ya rasa duk abinda ke masa dadi,yau har kwana biyar sun wuce be samu ya yi aikin da aka bashi ba,shi sam wlhh be san inda zai samu Jinin yaron da ba a fi 30 mints da haihuwar shi ba,karan shigowar wayan shi ne ya katse mishi zurfin tunanin da ya fada,


Tsaki ya dan ja tare da janyo wayan domin ganin waye ke son takura shi haka,saidai kafin ya ga me kiran wayan ta tsinke,Kara shigowan kiran ne ya sanya shi Kara Jan tsakin tare da kallon screen in wayan, ganin Alhaji Salis ke kiran  shi ya sanya shi gyara zama tare da daukan wayan..........


Asaalamu Alaikum,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi tare da ban hakuri Na rashin jina jiya da kuka yi,hakan ya faru ne sabida dan rashin lfyn da nake fama da shi, ina godia da irin kulawan da kuke nuna mun, Allah ubangiji ya bar kauna,


Na so Na ga ya fi haka Amman Allah be yi ba,so bare with this pls,sai kuma Monday in sha Allah,


A cigaba da sharing and commenting pls


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEY BEE)


......


My what's app link 


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


Ina marhaban da kowa,ammman banda mutuane biyu,mara sa sharhi da kuma maza don ko kun shiga zan cire ku🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via:

 

    08100046388


.........

        Page thirteen


***********


Assalamu Alaikum shine abunda SEN ya fadi bayan ya amsa wayan,murya a sake don sun Dan kwana biyu basu gaisa da Abokin Na shi ba,


Wa alaika assalam,SEN an wuni lafiya, Alhaji Salis ya fadi murya cike da annashuwa,


Wlhy Alhamdulillah yi hakuri fa ina ta so in kira ka zama ne ban samu ba kullum ina gurin yar ka a Asibiti jikin nata sam ya ki dadi wlhy,ya kare murya a raunane,


Allah sarki wlhy nima tunda muka je nake son mu koma da kai,zama ne ban samu ba nima,Allah ubangiji ya saka mata sannan ya bata lafiya, Amman cuta kam an cuce mu,


Kai dai Bari SEN yace yana girgiza kai,da zan kama Wanda yayi aika aikan nan ai wlhy da hannu Na zan kashe shi,Allah ya sauwaka shine Abunda Alhaji salis yace, SEN ya amsa da Ameen ya Allah,


Ni ka ga Na ma kusa manta abunda Na kira don in fada ma,zama SEN ya gyara sannan yace ina Jin ka ina kuma fata dai komai lafiya,


Dan dariya Alhani Salis yayi sannan ya ce haba dai lafiya kalau sai Alkhairi wlhy,Albishirin ka,


Kana son Kara aure ko,dariya Alhaji salis ya fashe da shi kafin yace wai me yasa babu wata albishir in da zan maka ni da Kabiru sai Na karin aure,shima SEN in dariyar ya sanya sannan yace yo ku din ne wlhy akwai son mata,Na ga kuma duk abun ku matan nan kullum haihuwar su ake kuma yi,


Hmmm ni dai babu ni cikin list in nan Na Kabiru ne kawai and bashi Na kira Na fada ma ba,yar ka dai Zahra ta sauka fa,


Cike da farinciki SEN yace kai Masha Allah barka Ashe ko dole Na tanadi babban goron albishir in nan,me aka samu aboki ko kishiya,


Dariya Alhaji salis yayi sannan yace wlhy kai aka samu Na miji ta haifa tana bude ido ta ganshi tace wannan big daddy ne wai sunan ka take son a Sanya wa yaron,



Allahu Akbar Allah sarki my daughter,kai wlhy Salis nayi murna Alhamdulillah SEN duk ya ma rude ya rasa me ma ya kamata yace,shi ko in banda dariya ba abunda Salis ke yi don ya San abokin shi da yaba kyauta ya san ba karamin dadi ya ji ba Jin sunan shi za a maida wa jinjirin da aka haifa,wannan shine jikan shi Na farko, and sam be yi bakin ciki ba da Zahra tace sunan SEN za a sanya wa Dan ta,a cewan ta tana son ya dauko kyawun hali irin Na SEN,


Kuna gida ne ko asibiti, Aa wlhy muna Rimi clinic duka duka bata fi 15 mints da sauka ba,don Alhamdulillah normal haihuwa ce babu wata complication,


Gani nan zuwa yanzu SEN yace tare da kashe wayan,farinciki lullube a cikin ranshi,


Tashi yayi cikin sauri ya canza kaya domin ji yayi gaba daya damuwar da yake ciki ta kau lokaci guda,


Yana kokarin fitowa daga dakin ne ko me ya tuna sai yayi saurin komawa tare da daukan wata oil ya mulke hannayen sa da shi,tare da sanya hand gloves a hannun sannan ya fito,


Tun a kofar part in shi yake kwala wa Sa'eed kira Wanda a guje ya rugo gudun shan mari,


Baka ji ina ta kiran ka shine abunda SEN yace tare da shigewa bayan mota ya zauna,


Am sorry sir ina toilet ne,kai ni Rimi clinic shine abunda SEN yace tare da daukan cheque book in shi,5mil ya rubuta tare da yagewa ya sanya a aljihun gaban rigan shi,


Ba su dau time ba suka iso Rimi,da sauri SEN ya bude kofar motan,a bakin asibitin suka hadu da Alhaji Salis in da ya masa jagora har dakin me haihuwar,


Mutane sun fara cika kasancewar haihuwar fari,daga dangin Salis har Na iyayen mijin Zahra duk sun hallara,


Gaisuwa Na mutunci suka yi da Sen ya Na sanar musu shine Wanda aka yi wa me suna,dangin uban jariri suna ta tsokanan sa akan to kuwa dole ya dauke nauyin komai Na sunan takwaran shi,shi dai dariya kawai yake musu domin ya matsu ya ga ya dau babyn a hannun shi,


Ko da suka shiga a zaune suka tarar da Zahra da mijin ta yana dauke da babyn a hannun shi an nade shi cikin farin towel Na yara,


Dankwalin ta ta gyara fuskan ta cike da faraa tace Big daddy sannu da zuwa ina wuni,


Zama SEN yayi sannan ya ce my daughter alhamdulillah Ashe an sauka ubangiji ya raya shi bisa sunnah, a kunyace tayi murmushi tare da amsa ameen a kasan ranta,


Gaishe shi AL_ameen mijin Zahra yayi,inda ya amsa cike da sakun fuska tare da yi mishi barka shima,


Mika masa takwaran nashi ya gani tun a hanya ya ishe ni baaban naku akwai son yara,Alhaji Salis ya kare yana kallon Mijin,


Tasowa yayi tare da nufo SEN da babyn har ya mika mishi,SEN ya mika hannu zai karba sai Alhaji salis yace wait,Aboki Na ya Naga hannun ka da gloves kuma,hope all is well dai,


Ohhh God kasan Na manta,ciwo dazu Na ji a hannun shine Na sanya magani,to gudun kar infection ya shiga ne Doc yace Na sanya gloves for at least 20 mints don maganin ya samu ya shiga,shine fa Na manta ban cire ba,ya kare tare da cire gloves in yana mika hannu wa AL_ameen domin karban Dan jinjirin,


Yana karban shi,kuwa yaron ya wani Mike kamar Wanda aka jona wa shocking sai kuma ya lafe ya kwanta luf,


Kallon shi SEN ke yi cike da kauna da soyayya yaron tabarakallah me kyau da shi fari sol,bakin gashin kanshi har goshin shi, masha Allah shine kalman da ya furta,


Murmushi Alhaji Salis yayi yace ka ga yaro sak uban shi ko,aa Aboki Na wannan yaron sak my daughter ne harta hancin nata ya dauko,saidai Allah sa kar ya dauko rashin Jin ta,


Baki ta turo sannan tace komai naka zai dauko big daddy saisa ma aka sanya masa sunan ka,


Allah miki Albarka ke da yaron ki my daughter Allah ya raya shi ya kare tare da yi wa yaron kiss a goshi yana mika shi wa Maman shi domin shi ba iya daukan yara yayi ba,


Cheque in 5 mil in ya mika mata tare da Kara zanga mata Albarka yana kuma bata hakuri kan be sani da wuri ba ya sanya be siyo komai ba tayi hakuri tayi managing wannan har zuwa ran suna,yanzu in ya koma zai aiko Saa'eed da raguna da saniyar sunan yaron,sannan zai dauki nauyin karatun shi tun daga kan nursery har sai in da yaron yace ya gaji da boko,and in suna bukatan wani abu kar suyi hesitating su sanar masa,


Godia sosai Zahra da mijin ta suka hau yi wa SEN, da sauri ya Hana su godia yace kar su sake ai duty in shi ne tunda duk su biyun yaran shi ne,Albarka ya sanya musu tare da barin dakin Salis Na bin shi a baya,


Har mota ya raka shi suna wa juna tsiya wai yanzu kam tsufa ya kama su sunyi jika,godia sosai Alhaji Salis yayi wa SEN kafin su rabu ya ce da shi don Allah in ya samu Alhaji Kabiru a waya ya sanar masa domin ya kira dazu wayan sa kashe,in sha Allah zan sanar masa granny ni Na wuce sai mun yi waya,da haka Sa'eed ya ja mota wani bari Na zuciyar shi fess yake Jin ta wani barin kuma yana Jin da be aikata abunda ya aikata ba,but bayi da wata option opportunity ne ya samu har gida toh ya zai yi dole yayi using in shi,


*************Doctor Nameer


Get out of my office pls shine abun da ya ce wa sister Kareematu ko dagowa be yi ya kalle ta ba,


Tashi tayi tare da juyi a gaban shi sannan tace haba Doc Nameer wai me na rasa ne don Allah,ka dago ko sau daya ne ka kalle ni,Allah ya hore mun am beautiful sannan ina da welcome ta kare tare da girgiza dukiyar fulanin ta,and I got bye bye ta kare tana shaking bom bom in ta,


Ko ya dauko balle ya ga haukan da ta gama,out yace da ita cikin kakkausar murya,


Haba Doc Na ji ko bara ka iya soyayya da ni ba wlhy zan yarda Na zamo karuwar ka,zan jiyar da kai dadin da baka San akwai shi ba a duniyar nan just give me chance plsss,ta kare tana hada hannaye,


Tassss ta ji saukan mari a fuskan ta,Wanda saida ta dafe kumatun ta,lalle Kareematu Ashe ke karya ce ban sani ba wani irin kula ne bana miki da har sai kin bi wannan sabon yaron da baki ma San shi ba ke wata irin jarababbiya ce eheyee,doctor Bashir ya kare yana Galla mata harara,


Kai Nameer ya girgiza tare da barin office in ranshi a bala'in bace wannan wata irin mayyar mata ce sabida Allah tun randa ya fara aiki take masa tayin kan ta suyi iskan ci,kila matar doc bashir ne ya sanya yake Jin haushin shi can musu dai yana kuma yi mata fatan shiriya domin ko da mutuwa zata yi ta dawo duniya don maita,bata ishe shi kallo ba balle har ya yi having affairs da ita don Sam bata da kamun kai,


Yana Jin yanda suke musanyar yawu da doc bashir kan akan me xe mare ta shi mijin ta ne,duk matan da yake be an ce masa bata sani ba ne,sai a sannan yake gane Ashe ba mata da miji bane, baya so yayi zargi tunda haramun ne da sai yace suna neman banza ne shine yake nuna kishi a kan ta,tas tayi mishi sannan ta ce da shi kar ya kara kula ta,bata jira cewar sa ba ta fito daga office in har tana bangade doctor Nameer daga gani ranta bace yake,


Shi dai Allah ya kyauta ya ce tare da fitowa cikin haraban asibitin,kujera ya samu tare da zama yana kare wa majinya tan kallo yanda suke hauka tuburan abun tausayi,


Kamar ance kalli can ya hango ta zaune ta sanya fuskan ta cikin cinyoyin ta gashin kanta duk ya yi buju buju,be san me ya sa ba sai ya ji yana son ganin fuskan wannan baiwar Allahn, and although ya gan ta da uniform in mahaukata sai ya ga she look calm and worried to him,ganin har kusan 3 mints bata dago ba ya sanya shi Mike wa tare da fara nufan inda take zaune, hannun shi da aka kama ne ya tsayar da shi,yana juyowa kuwa ya ga Habeeb ne,


Haba Doc Nameer since ka shanya ni ina ta jiran ka,mu je ka ga gidan mana tun dazu mutumin sai kira Na yake yi,


Don Allah kayi hakuri Habeeb wlhy mancewa nayi,Amman bani 1 mint pls zan same ka a mota,


Wlhy babu mint in da zan ba ka wuce kawai mu tafi,da ka yarda za ka zauna a gida Na ai da shike nan ko,Na ga alama baka gaji da zaman hotel bane,


Na gaji man habeeb in da ban gaji ba taya zan ce ka nema mun gida,sabida Allah kuma sai Na bika gidan ka Na tare ai babu tsari,


Ko ma miye mu je ya kare yana Jan Nameer Wanda hankalin shi Na aman baiwar Allahn da ta sunkuyar da kai,babu in da be yi da Habeeb ba ya tsaya pls Amman ina saida ya sanya shi a mota hankalin shi ya kwanta,


To miye kake ta wani bata rai,don zan maka gata,habeeb ya kare yana kallon doc Nameer,


Ni fa ba bata rai nake ba,kace a ina ne aka samu gidan Fadami madan ne ko miye sunan area in,


Dariya Habeeb ya kwashe da shi sannan yace Aboki na baka da dama wlhy,yanzu Fadaman madan ne kake kira haka,kai wlhy suna yen unguwan nun kun nan akwai wahala su Bakaro,su Yakubu wanka,Bakin kura ne ko bakin zaki,ga wata ma wai Fadaman mada don Allah ji fa GRA ne kawai me sauki da dadin fada,


Dariya Habeeb ya kwashe da shi sannan yace ai in dai sunaye ne kadan ma ka ki,Na Kd in kun ma haka kuke da tarukucan sunayen unguwan ni,


Eh koma dai miye,gwara namu sau dubu da Na ku,shi dai Habeeb be ce komai ba domin sam musu da yan Kano da yan Kd akan garin su to ranka ne kawai zai baci,


A haka har suka iso fadaman mada layin Maman isa yuguda, nan Nameer ya fara bin unguwar da kallo,but Habeeb are u sure za a samu me yin masa kusa kuwa,


Kai dai da wannan masa taka akwai me yi cikin dare ne kawai suke sauke tukunya and masan su akwai dadi yanzu dai mu je ka ga gidan in ya maka to,



***********SEN 


Around karfe 12 Na dare har ya fara gyangyadawa ya ji zoben hannun shi Na juyawa tare da Kara matse shi sai kuma ta sake shi sai ga wani Jan haske Na fita daga zoben, Wanda ya farkar da Sen tare da mikewa zaune,


Dariyan samun Nasara ya saki domin ga dukkan alamu sacrifice in da yayi ya karbu and Odugwu yayi farin ciki da shi,yesssss yace tare da shiga zubowa Odugwu kirari Na kusan 5 mints sannan ya ja barko ya kwanta zuciyar shi fess tunda ya baiwa Odugwu abunda ya ke so to tabbas shima soon zai  ga result me kyau, nan take bacci ga dauke shi cike da mafarkin ya zamo gwamman jahar Bauchi.......


Ina wa kowa fatan Alkhairi and ina fatan anyi weekend lfy,Allah ya sa hakan ,Ameen.



Ina matukar Jin dadin support in da kuke bani,you guys are making me to go further wlhy,thank u so very much Allah kuma ya bar mu tare,



Sai kuma gobe in me kowa me komai ya sanya mun kai.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEY BER)


........


My group link 


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin San ba comment bane zai kawo ki to pls ki zauna kar ki shigo domin kar Na fidda ki ranki ya baci,haka ma maza should stay away from my group domin Na mata ne zallah,


Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via:


    08100046388


...........

          Page fourteen 


************

 

Kwana biyu ke nan da tare wan Doc Nameer a gidan da ya kama,gida ne well furnished, me dauke da daku Na biyu,big parlor kitchen toilet da kuma gaban gida me dauke da parking space,


Gida ne me kyan gaske domin ba karamin kudi ya kashe ba Amman a ganin shi hakan ya fi masa kwanciyar hankali sabida wannan biyan kudin hotel in caca ya dauke shi,


Da Habeeb suka shiga kasuwa suka yo siyayyan kayan cefane domin dole yana bukata sabida Emergency, tsiya sosai Habeeb ke yi masa wai gidan gwauro tunda ya ki aure zaman kadaici ya kama shi,shi dai dariya kawai ya bi Habeeb in da shi kafin ya ce da shi aure ai nufi ne Na Allah,


Cike da kwanciyar hankali yake zuwa asibiti yayi aikin shi in an tashi ya dawo Gida abun shi,sometimes ya kan yi take away wani lokacin kuma ya daura abincin da kanshi,tun sanda ya yi wa sister Kareematu tas a office in shi bata kuma kallon in da yake ba,ko sun hadu haka za tayi ta cin chew gum tana wani wani Harare harare, yi yake kamar bata san abunda ta ke yi ba,and ya ga alaman doc Bashir ya dauke shi da gaba domin ko sallaman shi baya amsawa,


************* Zahra


Fitowan ta ke nan daga wanka,daure da towel a jikin ta,kallon ta kanwar Maman ta tayi sannan tace Anya Zahra kin gasu kuwa ni irin wannan wanka naku da Baba sam baku Dade wa,


Baki Zahra ta turo tana goge hannun ta tace haba ,Anty Haleemah kin san zafin ruwan nan kuwa,haka fa take tsoma towel ta nada da ruwa ta juye mun a jiki Na ko tausayi babu,


Yar nema yo ba tausayin ya sanya nake miki haka ba wlhy Na bar ki jikin naki ya rube Ameenun  ya karo wata ki shiga uku,


Fatan ki ya sauka a kan ki ,Zahra tace tana hararan Baba yalwa,


Kin ci gidan ku Zahra ban son iskanci fa,Anty Haleemah tace tana ma Zahra dakuwa,baki kawai ta turo sannan tace to ni me nace kina ji fa fatan kishiya take mun tun ban tsufa ba haka kawai,


Dariya Baba yalwa tayi sannan tace oh yaran yau saidai a bar ku wlhy,ni maza zauna in turara ki ga tuwo nan da kunnun Kanwa ki sha,


Haba Baba don Allah wlhh duk yanzu an daina irin wannan abun ,turawa nawa ke haihuwa ki gan su garau ba tare da sun sha wannan bakar azaban ba,magani kawai ake basu su sha shike nan sun hade fa,sai mu nan ayi ta dirka mana wahala,


Baki bude Baba ke kallon ta,don Allah kar ki kula ta Baba rabu da ita,bara ta san gata ake mata ba,je maza ki dauki babyn tun dazu mustsu mustsu yake kila yunwa yake ji bashi nono ya dan sha kafin ki ci abincin,ta kare tana barin dakin domin Zahra sam bara ta bashi ba in har suna dakin,wai ita kunya,


Ba musu Zahran ta nufi gadon da babyn ke kwance cikin shiga Na Alfarma,bashi kam ya sha don tun dazu da nake masa wanka Na ji jikin shi da dumi kamar wani me zazzabi,Allah dai ya sa ba me laulayi aka samo mana ba,Baba yalwa tace tana barin dakin,


Zama a bakin gadon Zahra tayi tare da dauko babyn a hankali,ji tayi yayi mata nauyi a hannu kamar duk jikin sa a sake,fuskan shi take kallo,sai ta ga yayi mata wani irin haske yayi fayau da shi,yarinta ya sanya ba ta gano komai ba ta ciro nonon a hankali tare da yin bismillah ta daura mishi a baki,ganin be kama bane ya sanya hankalin ta tashi domin har bude bakin shi tayi ta sanya masa a bakin Amman be ja ba ko alaman tsotsa,


A zabure ta mike tana kwala wa Anty Haleemah kira ganin kamar yaron ma be motsi,


A rude Anty Haleemah ta shigo tana fadin ke lafiyar ki Zahra kina jego kina irin  wannan ihun ,miye?ta tambaya tana kallon zahran da kallo daya za ka mata ka gane a rude take,


Hannu take yarfe wa tare da Jan baya,idanun ta har sun kada zuciyar ta Na tsanan ta bugawa,tace Anty Haleemah Anty Haleemah junior ne Na bashi nono be kama ba,


Kamar ya be kama ba Anty haleemah tace tana nufan inda babyn ke kwance,Anty haleemah sai Na ga kamar be motsi fa,


Haba Zahra daga kin karban nono sai ki ce be motsi kila baya son sha ne baran duba shi,Baba daman tace kamar da zazzabi a jikin shi,


Salati ta sanya lokacin da ta dauko yaron domin kallo daya tayi masa ta gano Sam babu rai a jikin yaron,


Jin salatin ya sanya a tsorace Zahra tace Anty Haleemah me ya samu baby na bacci yake yi ko,don Allah ki sanar mun me ya samu yaro Na ta kare tana hawaye,


Da mugun tausayin ta Anty Haleemah ta bude baki da kyar tace Zahra ke musulma ce dole ki yarda da kaddara me kyau ko mara kyau,saidai muyi hakuri Baby kam ya koma Allahn da ya bamu shi ya karbi abun shi Allah ya sa me ceto ne,


Timmmm din da Anty haleemah ta ji ne ya sanya ta juyowa,ganin Zahra zube a kasa Towel in jikin ta har ya bude ya sanya ta aje gawan babyn da mugun sauri ta nufi inda take,tana kiran sunan ta,


Ganin babu alaman numfashi a tattare da ita ne ya sanya ta kwalawa Baba yalwa kira,tare da kiran Hajiya Hafsat(mahaifiyar Zahra),


Duk an rufu kan ta amman sam numfashin ta ya kasa dawowa,a rude hajiya Hafsa tana kuka ta Kira Alhaji Salis tace ya shigo a kai Zahran Asibiti,



Hour guda aka dauka sannan aka samu numfashin Zahra ya dawo daidai Wanda saida aka sanya mata drip sakamakon Jinin ta da ya hau lokaci guda,


Ko da ta farfado kuka kawai take yi kallo daya za ka mata ta baka tausayi domin lokaci daya ta koma wani iri,rungume ta gam Alhaji salis yayi yana tofa mata addu'oi domin aljanun ta tashi suka yi,fadi take a kawo mata Dan ta wlhy be mutu ba babu abunda ya samu Dan ta,kuka sosai Hajiya hafsa ke yi domin lokaci daya Zahran komawa tayi kamar Wanda tayi karamin hauka,saida aka mata aluran bacci sannan aka samu suka sauka mata baccin wahala yayi awun gaba da ita,


Jiki ba kwari Alhaji salis ya bar hospital in,shi da Alameen Wanda idanun shi sun kada sun yi ja daga ganin alama kukan zuci yake yi,domin miscarriage in Zahran 3 kafin suka samu wannan ya zauna ta haife Dan gashi kwanan shi 3 tal a duniya Allah ya karbi abun shi,


Nasiha me shiga jiki da kwantar da hankali Alhaji salis ke yi wa Alameen har suka iso gida,inda suka tarar an gama wanke jariri,an nado shi,ganin rashin kyautuwan a kai dan makwancin shi SEN be sani bane ya sanya shi ja gefe tare da dannawa SEN kira,


Yana zaune yana cin breakfast hankali kwance kiran Alhaji salis ya shigo,saisata kanshi yayi tare da danne farincikin da yake ciki,domin ko be dauka ba hakan ya tabbatar mishi an rasa jinjirin da aka haifa,


Daukan wayan yayi bayan ya kusa tsinkewa tare da yin sallama kamar kullum,


Murya a shake Alhaji salis ya amsa,cike da kulawa SEN yace Aboki na lafiya kuwa Na ji muryan ka haka me ke faruwa ne,


Hanci Alhaji Salis ya ja sannan yace wlhy SEN rasuwa aka yi,inalilahi waye ya rasu SEN ya tambaya sounding so very worried,

 

Takwaran ka ne ya koma yau da safen nan yanzu ma ana shirin yi masa sallah shine nace ya ci ace ka sani,


Allahu Akbar SEN yace kamar zai yi kuka Allah sarki Ashe yaro ba me zama bane,ikon Allah ba ruwan Allah yanzu kana nufin takwara Na ya koma,ubangiji ya sa me ceto ne gani nan zuwa yanzu,da haka ya kashe wayan bayan ya gama kwararo addu'oi,


Cikin sauri ya shirya tare da fitowa,saida suka biya ta gidan Alhaji Kabiru suka dauko shi sannan suka nufi makabar tan domin lokacin har an gama masa sallah, da su aka kai yaro makwancin shi Na gaskia,wanda saidai mu ce Allah ya jikan shi ya sanya me ceton iyayen shi ne,


Ganin irin damuwar da Sen ya shiga saida Alhaji salis da Kabiru suka shiga bashi hakuri suna cewa ya dau dangana in be karfafawa Zahra ba ai bare sanya ta kuka ba,da kyar ya nutsu domin ce musu yayi shi wlhy tausayin Zahran yake ji ba kadan ba,haka aka dunga xuwa gaisuwa domin Randa aka yi haihuwar labari ya bazu anyi wa SEN takwara so duk wani mutanan sa saida suka zo taaziya,


Kwanan Zahra uku a asbiti kafin jikin nata ya fara sauki aka sallame su suka dawo Gida,


Sati guda SEN ya dauka yana zuwa gaisuwa tare da kai goma sha tara Na arziki  don daukan nauyin abincin da za a ci Na mutuwar yayi,duk gurin kowa Albarka yake sanya masa ba kamar dangin Alameen da salis domin ba karamin nuna kula da damuwar shi yayi game da mutuwar nan ba,Wanda deep down kuma ba Wanda ya kai shi farinciki,


Randa suka hadu da Zahra jikin shi ba karamin sanyi yayi ba domin irin Rama da kukan da take tayi,lallashin ta yayi ta yi,tace da shi in sha Allah ko gobe ta Kara haihuwa sunan shi za ta maida,Allah kuma ya jikan wannan babyn nata da ya mutu,


Nasiha sosai yayi mata Wanda Alhamdulillah yayi tasiri akan ta domin har abinci ta ci me yawa wannan ranar, daman tun tana yarinya Allah ya hada Jinin ta da Sen haka kawai take kaunar shi zan iya cewa ma shine role model inta she look up to him,be bar gidan ba saida ya siya mata sabon mota ta mil 30 tare da biya musu ita da mijin ta Makkah da Manchester wai su Dan je hutun ko Na 3 months ne ko za ta manta da damuwar da ke damun ta,


Ba karamin dadi da godia Alhaji Salis yayi wa SEN ba yana ta sanya masa Albarka tare da yi mishi fatan gama wa lafiya,haba Aboki Na Zahra ai ya ta ce yau in ka fadi ka mutu ni ne uban ta so wannan ba wani abun godia bane,nayi mata hakan ne ko hankalin ta zai Dan kwanta, domin nasan dole ta ji ciwon abun Amman ya muka iya Allahn da ya bamu shi ya karbi abun shi Allah ya sa me ceto ne,baran wuce Hospital gurin yar ka,


Ameen ya Allah mun gode sosai SEN Allah ya bada lada,don Allah ka gaida Nadeeyan in sha Allah nima zan zo duba tan,to ba damuwa da haka suka rabu zuciyar shi cike da farin ciki,gefe daya kuma yana me Jin tausayin Zahra in,but da ya tuna nothing good ke zuwa cikin sauki ya sanya ya watsar da wani tausayin zahran at least ai yayi compensating in ta,ko gurin Allah he is sure be da wani laifi,he did it to protect his dignity,


(Ya Allah ka raba mu da son zuciya, Allah ka raba mu da son duniya,sannan ya mana tsari da cin amana ,tabbas mutanan mu sun dauki amana ba a bakin komai ba,kuma wannan a rubuce take duk Wanda ya amince da kai,ka ci amanan sa to tabbas Amana ma za ta ci ka,ina mamakin masu daukan hakki,hakkin ma Na ran Dan Adam ba tare da wata hujja ba suyi tsamanin za su ci bulus,rayuwar mu Na yanzu an maida ran mumuni Na a bakin komai ba,ya Allah,masu hali irin Na SEN Allah ka nisan ta mu da su ka kuma gyara mana halaye da kuma zukatan mu),


*************Nadeeya


A halin da ake ciki kam yanzu in akwai abun da ke gaba da hauka to Nadeeya tayi shi,sakamakon aluran da doc bashir ke dirka mata,Wanda sabida mugunta irin nashi har shock treatment ya sanya mata Wanda ya dada haukatar da ita,(Marin da SEN ya masa yake ramawa akan Nadeeya,sabida shi mugu ne shine harda sanya mata shocking),


Haaaaa Nurse Kareematu tace da Nadeeya da ke irga yatsayun hannayen ta tana dariya, ko kallon Kareematu bata yi ba,


Ki bude baki ki sha maganin ki mana, ta fadi cike da kosawa,


Harara Nadeeya ta Galla mata tare da cewa ooo,ran Kareematu ne ya soma baci tace zaki bude ko sai Na miki alura,


Jin haka ne ya sanya Nadeeya,bude baki da sauri domin ta tsani aluran da suke mata,cokalin maganin ta sanya mata a baki tana ai da baki sha ba da kin ga abunda zan miki, wai ke ga ki yar me kudi, har wani isolating in ki aka yi,banda ina samu a jikin ubanki da wlhy Rama dukan da kike mun zan nayi,


Bata kai ga rufe baki ba ta ji Nadeeya ta watso mata maganin bakin nata a fuskan ta,tana me tintairwa da dariya kamar wata karamar yarinya,


In ran nurse Kareematu sun kai dubu to duk sun baci yau,a zuciye tayi kan Nadeeya fadi take yar iska ni zaki watsa wa maganin baki,


Tashi Nadeeya tayi da gudu suka hau zagaye dakin tana wa Kareematu dariya Wanda sai binta take ita ala dole sai ta buge ta,garin bin ta da gudun ne ta harde kafafun ta sai ga ta a kasa ta fadi akan fuskanta, gwalo Nadeeya tayi mata tare da taka yatsun hannayen ta Wanda saifa ta saki Kara, ganin tana shirin tashi ne ya sanya Nadeeya nufan kofa da gudu tana dariya,


Lucky her kofar ba a kulle take ba,ganin tana ja ya bude ya sanya ta sanya ihun murna tare da ficewa da mugun gudu tana waiwayen Nurse Kareematu,


Fitowan shi ke nan daga office zai yana sauri zai nufi gidan Habeeb don ya gaiyace shi Lunch yace yayi sauri don harda masa matar shi tayi musu,(oh doc Nameer kai da Masa dai 5&6 ne Na ga alama,lol),


Waya ne a kunnan shi yana magana da Mama sai ji yayi kamar daga sama an bangade shi, Wanda saida wayan kunnan nashi ta fadi kasa,


Juyowan da zai yi don ganin waye haka ya sanya ta hardewa tayi taga taga za ta fadi da sauri ya riko waist in ta tare da manna ta a kirjin shi yana bin ta da kallon mamaki, domin daga ganin yanda gashin kanta ya rufe mata fuska ya tabbatar mishi da ita ce ya gani wannan ranar a zaune,


Jin bata kai kasa bane ya sanya ta sakin dariya cikin siririyar muryan ta tare da sanya hannu ta bude gashin kan nata in da nan take kyakkyawan fuskan ta ya bayyana,


Ya salam doc Nameer ya furta yana me zuba mata eyes ko blinking baya yi,ita din ma shi take kallo kafin can kamar Wanda aka tsikara ta fito da tongue in ta tare da lashe mishi kumatu sai kuma ta sanya dariya tare da daka tsalle,


Maganar Nurse Kareematu da ya ji a bayan su ne ya sanya shi dawowa daga Dan guntun sumar da yayi because he was totally shocked da abunda Nadeeya tayi mishi,


Go get her shine abunda Nurse Kareematu tace in da Sam Nadeeya ta ki sake Nameer daga ganin ta xaka San a tsorace take da Kareematun,domin zan iya ce wa she was so free with Nameer lokaci daya,duk da fitowa take ba,and daga ganin yanayin ta za ka san she is so depressed and scared saidai wannan childish behavior in nata da Nameer zan iya kiran shi watakil wai silan haduwar su,


Da kyar da sidin goshi aka ja Nadeeya zuwa dakin ta kuka take tana fadin ita bara ta je ba,ana yi mata injection me zafi bata so,shi dai doc Nameer Na tsaye cak har aka wuce da ita dakin ta tana mika mishi hannu idanun ta cike taf da hawaye....

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEY BEE)


.......


My group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin san ba comment bane zai shigo da ke to don Allah kiyi zaman ki,haka zalika maza kar su shigo mun cikin group domin Na mata ne zallah🙏🏻,


Ga masu son tallata musu hajar su contact me via:


    08100046388


...........

        Page fifteen


***********


Da kyar da sidin goshi suka samu suka sanya wa Nadeeya chain a hannun ta domin duka ta shiga kai musu ta ko ta ina, inda ta kai wa sis Kareematu wata hambara saida ta fasa mata baki sai ga jini, haka sauran workers in da suka kawo ta duk saida ta laka da musu duka saida aka mata aluran bacci kafin aka samu hankali ya kwanta,


Cike da bacin rai Kareematu ta fito daga dakin,domin kashedi Bashir ya mata kan ko me Nadeeya za ta mata be yarda ta buge ta ba in ba haka ba SEN uban su zai ci daga shi har ita,


Nameer Na nan tsaye har kareeamtu ta zo ta wuce shi,kafin ya dawo hayyacin shi,waye wannan yarinyar,me yasa ta rike shi haka,sannan wani irin injection ne suke mata Wanda take kira akwai zafi bata so,duk sune tambayoyin da ke ringing a cikin brain in shi,ganin wuce war Kareematu ne ya sanya ya bi bayan ta,domin babu me amsa mi shi wannan tambayoyin sai ita,



Da sallama ya tare ta,ganin shi ne ya sanya ta juyo a wulakance tare da kallon shi tana wani harare harare,


Sannu sister shine abunda ya fadi mata ko a jikin shi da irin kallon wulakancin da take bin shi da shi,


A yangance kamar wata yarinya karama tace hmmmm Na miji ke nan,in ce ni da kai Na,na biyo ka har office in ka amman kayi mun diban Albarka yanzu miye kake so daga guri na,ta kare tana hararan shi,


Dan karamin saki ya ja a ranshi yake fadi ji wannan kamar ce mata aka yi wani abun nake da bukata daga gurin ta,


Ka yi shiru ko baka da abun fadi nayi wuce wa ta,ta kare tana adduar Allah sa inviting in ta dakin shi ko in ce gidan sa zai yi,


Tambaya daman zan miki game da patient in dazu,wani irin tukukin bakin ciki ne ya tokare ta a kirji,wato shi ta Nadeeya ma yake ba ita ba,to wai ita me ta rasa ne da bare lura da ita ba,kyau ne ko diri bata da shi,in yayi zafi ne fa yace ta Dan fi shi a shekaru and miye a ciki ai age is just a number,ga yanda Bashir ke rawan kafa akan ta tana masa yar hali amman shi a karan banza za ta bashi jikin ta yana mata bura uba,


Tsaki ta ja sannan tace da shi ina ruwan ka da ita,ko ina ruwan ka da injection in da ake mata,patient in ka ce for your on information stay away from Nadeeya domin Doc Bashir ke handling case in ta,beside in kana da bukatar tayin da nayi maka har yanzu kofa a bude take za ka iya nema ta,Allah ya mun tsari shine abunda ya ce tare da barin gurin,


Kai tsaye motar shi ya nufa,gida direct ya wuce,takalman shi kawai ya iya cire wa tare da fadawa kan gado,


Goshin shi ya dafe tare da lumshe idanun shi,fuskan ta ke masa gizo yana kallon dariyar da take mishi,ya salam daman ita ce Nadeeya RILWANU Audu Waziri in,but ta ma fi kyau a fili Ashe akan kallon da ya mata a video in ta da ke treading ,


Shafo kumatun shi da ta lasa yayi kawai sai ya saki murmushi,lalle hauka bata yi ba,in ba hauka ba ai ko kudi za a bai wa Nadeeya ta yi mishi abunda ta yi masa he is very sure bara ta iya ba,zai iya ce wa this is the first time da wata mace ta taba shi bayan rasuwar Noor in shi,haka kawai ya tsinci kan shi cikin tunanin wani irin Alura ce haka suke mata da take cewa bata so,karan shigowar kira ne ya katse shi daga tunanin da yake yi,


Daukan wayan yayi tare da Mike wa don ganin Habeeb ne,nan ko ya hau shi da mitan wai ya shanya shi since an gama abinci,hakuri ya bashi tare da ce da shi gashi nan akan hanyan shi yanzu zai iso,


Be dauki tsahon lokaci ba ya isa gidan Habeeb kasan cewar basu da wata nisa,


Gaisuwa suka yi da matar shi Muhibbah sannan ta shige ciki don basu guri,


Suna cin abinci ne Doc Nameer ke ba wa Doc Habeeb labarin abunda ya faru saidai be sanar da shi kan Nadeeyar ta lashe me kumatu ba,


Saida ya kurbi ruwa sannan yace wlhy nayi mamakin da ta fito ma,domin ni tun da aka kawo ta ban taba sanya ta a idona ba,boye ta Bashir yake yi kamar wata Amarya,


Wlhy nima abunda Na gani ke nan,and ni wlhh Na kasa nutsuwa sam wai miye ma silan haukan nata ne,


Wa ni wlhy Nameer ban sani ba domin ko case file in ta ban taba gani ba,hasali ma da aka kawo ta Bashir cewa yayi shi zai yi handling case in kowa yayi staying away from her,saisa ma ko fitowa shan fresh air ba barin ta yake tana yi ba,beside kai miye Na daga hankalin ka abeg mu ci abinci kar yayi sanyi,


Daga haka Nameer be kuma cewa komai ba,Amman deep down ya dauki niyan in sha Allah ya je asibiti gobe zai tuntubi Bashir da maganar,in da zai yarda ma da ya bar mishi case in nata,haka suka gama cin abinci sai yaba girkin matan yake ,a gidan suka wuni har dare suna hira kafin yace zai koma gidan shi,dubu ashirin ya bai wa Muhibba kyauta wai a siya wa baby Fadeel pampers,godia tayi mishi sannan Habeeb ya rako shi har mota ya koma gida, 


Hira suka sha sosai da Mama,ya so ta bai wa Angel ta ce da shi tayi bacci saidai Amrah, mamaki yayi wai har yanzu ba ta tafi ba,mama za ta bata ya ce aa ta bari zai kira ta da kan shi, da haka ya kwanta bacci abun shi,


Washe gari sassafe a asibiti yayi mishi,direct in da ake aje files ya nufa domin shi fa ya kasa yarda Nadeeya hauka tayi, don maganar gaskia yanda ya gan ta babu Wanda zai ce mahaukaciya ce,zai fi ma yarda da maganar jefan da aka ce anyi mata,ya sanya yake son ganin case file in ta domin ya San matakin haukan nata,


Saidai kaf ya gama bincike cikin gurin Amman babu case file in Nadeeya,mamaki ne ya kama shi domin a iya sanin shi ba a karban patient ba tare da an rubuta case report in shi ba, ganin dai babu Na tan ya sanya shi fitowa tare da nufan office in doc bashir,


Gaishe shi yayi,ya amsa shi a dakile sannan yace da shi lafiya,uhmm daman Na zo ne game da case in number 354,


Da sauri Bashir ya mike tare da fadin and what about her,aa actually Nothing kawai dai if you don't mind ina son ganin case file in ta ne,because the why she is isolated haka Na san ita kanta she will be depressed,


Rai Bashir ya bata sannan yace ina kace if I will not mind toh I will mind in fact I want to advise you to stay away from her domin ni ke handling in case In ta,and about her isolation mahiafin ta ne ya bukaci hakan so I think we are done babu ruwan ka da ita carry on with your work and stay away daga abunda be shafe ka ba,


Ran Nameer ya sosu sosai da abunda Bashir ya fada mishi and right through his eyes ya gano akwai abunda yake boye wa,domin Habeb ya sanar da shi harda pin code aka sanya a kofar shiga inda Nadeeyan take,in har babu abunda yake boye wa miya sa ba a barin ta tana fito wa kamar sauran majinyatan,


Saidai ya hadiye bacin ran tare da yin murmushi yace well tunda kace haka daman I was just been concerned ne,and at least hospital daya muke aiki so duty Na ne nayi making sure duk wasu patients Na lafiya, tunda ka ce I should stay away ba damuwa zan yi yanda kake so,Amman kafin nan I want to know wani irin injection kuke mata ne,ko in ce wani irin treatment kuke mata Na ganin recovery in ta don tayi complaining ana yi mata alura me zafi,


Tashi Bashir yayi yace yo ga iskanci ganin ido Na,kila Dan sanda ne kai ko kuma lawyer me kariya right halan a court room muke,sabida tsaban ka raina ni,za ka zo har office ina kana mun irin wannan tambayoyin rai nin wayon,


Murmushi Nameer yayi sannan yace ko daya kawai dai ina carrying out duty Na ne,rai bace doc bashir yace carrying out duty ko kuma munafurci, daman ni can Na ga take taken ka munafuki ne kai,toh wlhy ba dai wa ni za ka yi wa munafurci ba yo har sai ka kama maganar mahaukaciya ,


I don't see any reason da zan tsaya explaining kai Na a gurin ka tunda ba uban ta bane kai,one thing da nake so da kai shine ka bar mun office ina right away kafin ka gama bata mun rai,


Kai kawai Nameer ya girgiza domin in ya canka daidai doc bashir yana kan Jin haushin shi ne akan abunda ya faru kwanaki,


I never thought magana ta za ta bata maka rai I was just being concerned ne but since ran ka ya baci am sorry and as u said babu ruwana so daga yanzu I am stepping back daga abunda be shafe ni ba,daga haka ya fice daga office in ran shi a bace,


Da de yafi maka bakin munafuki masu hana ruwa gudu tunda kaine ubana shine za ta zo kai kafi kowa son sauke duty,to Allah ya tsine uban me duty din ma,doc bashir ke ta sababi ko in ce kokarin kare kan shi,shi dai Nameer be kula shi ba office in shi kai tsaye ya wuce ran shi nayi masa zafi domin karara ya ga rashin gaskia a idanun Bashir Amman yayi masa irin wannan diban Albarkan, 


Saida ya sha ruwan sanyi sannan ya dan ji sassaucin zafin da zuciyar ta shi ke mishi, zama yayi tare da kura wa kofa idanu haka kawai ka bi ka takura kan ka akan Nadeeya ina ruwan ka da ita the best thing is to stay away from her shine abunda zuciyar shi ke fada mishi,


Saidai wata zuciyar Na sanar masa kamar yarinya tana cikin wani hali hali Na neman taimako and he will forever hold himself responsible yana da hali be taimaka mata ba,


To a taya zai ma taimake ta shi da be ma San takamammiyar abunda ke damun ta ba,ya dauka zai ga case file in ta ne,but daga abunda Bashir ya fada mishi ya gano tabbas akwai abunda suke boyewa shi da Kareematu to miye ne wannan abun,shine abunda yayi ta matsawa ranshi ya sani.....




Wlhy Na so ya fi haka saidai ina fama da ciwon hakori, Wanda yayi mun causing in ciwon kai,a sanya ni a addu'a don Allah,sannan ayi mun afuwa don nasan bara a rasa typing error ba wlhy da kyar Na samu nayi page in nan,


Ina wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY 

         BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


......


My group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin san ba comment bane zai kawo ki to dan Allah kar ki shiga, haka zalika maza kar su shigo don Allah group in mata ne zallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via:


    08100046388


...........

         Page sixteen


*********** Doctor Nameer



Haka wannan ranar Doc Nameer ya bata shi gurin tunanin ta wani hanya ne zai shiga cikin dakin Nadeeya,haka kawai he is so curious ya san halin da take ciki,


And abun haushin shine be san taya zai samu access to her ba,domin shi ba sanin pin code in yayi ba,and the only way da zai yi finding out shine through Bashir or Kareematu,Bashir kuma ya san ko mutuwa zai yi bare fada mishi ba domin bayi da ma gaskia,while Kareematu kuma ba sai na fada muku ba,haushin shi take ji already,


Yana kallon yanda suke ta kai kawo a dakin nata,har lokacin tashin shi yayi but sam he is not willing ya tafi gida,ko ba komai yana son Kara ganin ta,


A haka har Magriba tayi mishi a cikin hospital in wanda zan iya cewa tun da ya fara aiki be taba kai wa hakan ba,ganin be da wani way out ne ya sanya shi yin give up har ya soma hada kayan shi domin barin hospital in,



Yauwa Kawata don Allah taimake ni mana,Kareematu tace da Zaituna da ke kokarin kulle jakar ta,


Juyowa tayi ta kalli Kareematun da ta sha kwaliya har da su Jan baki,sai ina kuma shine abunda ta tambaye ta,


Ke dai Bari wlhy Alhaji Na ke waje yana jira Na yau ya shigo garin Bauchi da mun yi zan same shi a masaukin sa in Na tashi a gurin aiki,to sabida naci da rashin hakuri irin nashi shine saida ya biyo ni yana waje wai Na fito mu wuce,


Ke dai Kareema wlhy baki bin duniya a sannu,wai ke ko tsoron mijin ki ya kama ki ba kya ji,


Dan tsaki Kareematu tayi sannan tace ni dadi Na da ke kenan tsoro wlhy kin ga dare ya fara yi,da kike mun maganar mijina me Abdul yake da shi sabida Allah banda rabon yara da ke tsakanin mu,nayi kallan matar shi ne,da ni nace kar ya fita ya nema don sauke mun duk wasu responsibilities ina,tun da shi ya Gaza ai sai a taya shi ta kare tana kanne ido daya,


Hmmm Kawata wlhy baki da kyau,ko nayi wanka kuwa ta kare tana dauka jakan ta,


Yauwa har zan manta,ki taimake ni don Allah ki mika wa wancan mahaukaciyar abincin ta,tun Rana take hauka sai fashe fashe da Duke Duke take,kar Na tsaya kai mata ta batan lokaci da kwalliya Na,


Ah lalle Kareema wato ni ce bana son rai da lafiya ta ko shine za ki tura ni don ban yi kwalliya ba,


Dafa ta Kareematu tayi sannan tace common zaituna ta kin San duk hospital in nan banda kawa irin ki and da ke kadai Na yarda, wlhy Bashir sam be bari ana shiga gurin ta ne saisa zan tura ki,


Doke hannun ta zaituna tayi sannan tace ji iskanci to ni in ya kama ni fa,haba tawan bara ki iya taimako Na ba pls abinci kawai za ki kai mata,wlhy ni jira Na ake and ina bukatan kudi urgent wlhy,beside taya ma zai sani in ba ke kika sanar masa ba,nan dai ta kanenade ta da dadin baki harda mata Alkwarin bata kyautan 10k gobe da haka ta samu ta yarda za ta kai,


Pin cord in ta sanar mata sannan suka yi sallama akan sai sun hadu gobe za ta bata bayani,da haka suka rabu,


Abincin Zaituna ta hada akan tray sannan ta fito tana yan wakokin ta Na soyayya har ta iso kofar dakin,


A kan idanun Nameer ya ga wulgawan Kareematu Wanda ya tabbatar masa da ficewa za tayi,kamar shima zai fita sai ya hango Zaituna da tray a hannun ta ta nufi isolated room in da Nadeeya take,ganin hakan ya sanya ya bi ta a baya a baya yana me Jin farincikin haka kawai a cikin ranshi,


A Dan bayan ta ya labe kamar barawo tare da zuba wa madannin idanu,in da lucky him akan idon shi ta danna pin in,ganin kamar za ta juyo ya sanya shi saurin juyawa yana me Jin tausayin Nadeeyan domin yana iya juyo irin ihun da take yi at the top of her lungs kamar Wanda ake yanka ta sai kuma karan fashe fashe,a haka ya fita tare da fadawa motar shi,I have to see her again shine abunda ya fada wa kanshi tare da Jan motar,


Kai tsaye gida ya wuce in da yana isa ana kiran Magriba so tsayawa yayi tare da sauke farali,sannan ya shiga gida,


Kai tsaye toilet ya fada wanka yayi sannan ya fito ya hada coffee ya sha,sannan ya shirya in something light,


Laptop in shi ya janyo ya shiga yin research just to keep him busy(yo ba budurwa gare ka ba balle ka je hira ko kayi passing time,lonely soul,lol),


Around 9:00 ya mike tare da rufe laptop in car key in shi ya dauka tare da wallet in shi,ya fito daga cikin gidan,motar shi ya shiga tare da fitowa daga cikin gidan bayan ya rufe,


Kai tsaye Saje restaurant ya nufa Wanda ke opposite da Round about in Nasarawa,


Parking yayi tare da shiga,tun Randa Habeeb ya kawo shi gurin shike nan kuma ya haddace yana zuwa,domin ba karya abincin su akwai dadi,


Gaisawa suka yi da masu aikin gurin sannan suka taimbaye shi me za a kawo mishi,


Ce musu yayi take away yake so Na Sandwich da kuma rubber in ice cream, without waste of time kuwa suka hada mishi duk abunda ya bukata yayi payment sannan ya dauki ledan sai mota,


Kai tsaye Specialist ya koma,inda ya sanar wa watch man in mantuwa yayi zai dauki wani file ne,dake suna ganin mutuncin shi ya sanya without thinking twice suka bar shi ya wuce,


Saida yayi parking sannan ya fito, da ledan a hannun shi, yana tafe yana sanda kamar wani barawo har ya nufi kofar da Nadeeya ke ciki,


Idanu ya lumshe yana kokarin tuno numbers in da Zaituna ta danna dazu,4477 ya dannan ai kuwa sai ga kofa ta bude, wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke tare da kutsa kanshi cikin dakin bakin shi dauke da sallama,


A can kuryan daki ya hango ta jingine da jikin gado ta kife kanta a cinyan ta, tana ta shesshekan kuka,


Hey shine abunda yace da siririyar muryan shi,


A zabure ta dago idanun ta sun yi jawur vase in da ke gefen ta ta dauka tare da jefa masa,inda yayi saurin gaucewa saidai ya same shi a hannu,Wanda ya yi nasaran yanka shi har jini Na zuba,saidai yankan is not that deep,


Be ko yi gizo ba ya shiga takowa kusa da ita yana mamakin changing behavior nata,ihu take yi tana jefan shi da duk abunda hannun ta ke iya dauko wa Wanda bata samun shi sabida gaucewar da yake yi,


Har ya iso inda take tare da durkusa wa,hannun shi ya sanya tare da rufe mata baki domin ihun da take yi gudun kar ta tona musu asiri,



Shhhhhhh yace da ita yana me rike hannun nata,a hankali ya shiga hura mata iskan bakin shi yana fadin is okay calm down please,


Idanu ta zuba mishi kamar Wanda take gane me yake cewa,murmushi yake mata tare da fadin babu kyau violence and you look good jiya da muka hadu da kike dariya why the sudden change now,ya tambaye ta ba tare da yana expecting amsan ta ba,


Saida ya ga ta Dan nutsu sannan ya sake ta tare da kare mata kallo,she looks so pale and tired he is she has been crying tun safe ganin inda idanun ta suka kumbura,a hankali ya ke bin ta da kallo yanda gashin kanta duk ya cukurkude duk ta zama abun tausayi finger nails in ta duk sun fito kamar wata monster,


Caraf idanun shi ya sauka akan kafan ta da ke xubda jini,Wanda daga ganin Abu ta taka ya yanka ta,and ba a yi dressing in ciwon ba,tausayin ta ne ya kama shi kila abunda ya sanya take ta kuka da ihu ke nan,toh wai wani irin kula Bashir ke bata da har yake fadin ya fita a hanyan ta,Dan karaman tsaki ya ja tare da nufan inda first aid box yake a dakin ya dauko, gaba daya tayi gaja gaja da dakin don har ta TV in ta fasa shi,


A hankali ya tsunguna yana me Adduar Allah ya sa ta yarda ya gyara mata ciwon kar ya zamo miki,


Cike da nutsuwa ya kama tsintsiyar kafan nata, Wanda ta yi saurin janye kafan tare da kai mishi naushi inda ta same ki a kafada,ba tare da ya damu ba ya sake mata kafan yana murmushi domin ganin yau mugunta take ji,


Ledan da ya shigo da shi ya dauko, sanna ya dawo ya zauna kusa da ita,rubber in ice cream in ya bude tare da sanya spoon ya kai bakin shi,uhmmm dadi ya ce tare da lumshe idanu,


Da gefen ido take kallon shi ba tare da ta ce komai ba,ganin haka ya sanya ya mika mata rubber daya inda tayi saurin faucewa ta sanya hannu ta fara lakata tana sha,ganin hakan ne ya sanya shi saurin dawowa gurin kafan nata,


Cike da dabara ya shiga goge mata ciwon yana hura mata kafan da iskan bakin shi inda yayi nasaran cire glass in da ta taka, ba karamin tausayi ta bashi ba inda ita ko ko a jikin ta domin ko hawaye bata yi ba ice cream da sandwich in ta kawai take ci tana lashe baki da hannu abun tausayi, daga gani ta wuni da yunwa yau,


Saida ya gama sannan ya dawo kusa da ita ya zuba mata ido, inda take cin abincin ba karamin dariya take bashi ba,


Hannu ya mika mata wai akan ta samma sa inda ta noke kafada akan bara ta bayar ba,kai kawai ya girgiza sannan yace so you love ice cream, kamar daga sama ya ji ta ce more than anything ma kuwa,


Da mamaki ya dago ya kalle ta sai kuma ta kau da kai kamar ba ita tayi maganar  ba babu yanda be yi da ita ta fadi me tace ba Amman Sam ta ki,sai ma  cigaba da surutan haukan ta da tayi,


Haka ya tashi tare da gyara mata dakin tas in da ta fasa glasses in sannan ya zauna yana ta Jan ta da hira,inda ta ringa maintsinin shi tana Jan gashin shi,


Shi dai da ido kawai yake bin ta yana jan ta da hira har ta saki jiki da shi ta mika mishi sandwich in guda daya ba musu ya karba tare da gutaira sai ta sanya dariya tana tafa hannu,


Rayuwa ke nan,Allah yayi mana jarabawa me sauki a rayuwar nan,don Nadeeya kam haukan ta yayi nisa,


Haka Nameer daga cewa file zai zo dauka nan ya lallace a gurin Nadeeya suna ta shirme har kusan 12:30 Na dare sannan ya farga da dare yayi, lokacin ita ma bacci ya dauke ta,so blanket ya rufa mata tare da yi mata Azkar in bacci sannan ya fito,zuciyar shi cike da tausayin Nadeeyan,


A haka ya fito tare da creating excuse wa watch man in suka yi sallama ya nufo gida,wannan ranar haka ya kwana yana tunanin Nadeeyan Wanda Allah kadai ya san why ya kasa cire ta a cikin ran shi......



Ramadan is around the corner, so saura mana 2 pages in sha Allah sai kuma bayan sallah,


Ubangiji ya sanya mu riski Ramadan lfy Allah kuma ya karba mana ibadun mu,sannan ya sanya ya zama silan dace war mu,


Ina godia da kaunar da kuke nuna mun ina wa kowa fatan Alkhairi



Sai kuma Monday in sha Allah.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


......


My group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin san ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki to pls kar ki shigo,don ko kin shiga zan yi waje da ke,haka zalika maza should stay far away from my group please🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su kuwa contact me via:


    08100046388


...........

         Page seventeen


************


Tun daga wannan ranar doc Nameer ya maida isolated room gurin hiran daran shi, domin a kwana ukun nan baya missing kullum sai ya je gurin Nadeeya ,


Haka zai bari sai kowa ya tafi sannan ya bi dare ya dawo kamar wani barawo, and baya taba zuwa mata hannu haka ice cream dai wajibi ne sai ya kawo mata, sai ya hada mata da wani kayan dadin,


Tun tana duka da masa ihu in ya zo har ta gane shi ,tana ganin shi sai ta hau murmushi tana mika mishi hannu ta san ya kawo mata kayan dadi,a haka zai lallace a gurin ta tayi ta masa shirme yana biye ta har sai ya ga bacci ya dauke ta tukuna,ya Na son ya ga an gyara mata gashin ta an yanke mata nails in ta saida baya son yayi mata da kanshi don ba muharramar sa bace be son yana taba ta any how and be San ko tana da aure ko Alkwarin wani akan ta ba tunda ba ganin case file in ta yayi ba,saisa baya son tana shige masa jiki,


A matukar rude Kareematu ta shigo office in Bashir inda ta same shi ya tasa wata karamar nurse sai matse ta yake,


Tsaki ta ja kamar halcen ta zai tsinke sannan tace kai dai wlhy anyi Dan iska wlhy ka ji kunya wani irin maita ne wannan mutun ace jaraba ta fi karfin shi,


Da sauri yarinya ta sauka akan table in office in tare da Saurin ficewa shi ko tashi yayi tare da gyara zaman wandon shi sannan yace Malama uban me ya kawo ki office ina ba tare da neman excuse ba,


Yo kace haka ai Dan iska tunda Na kama ka da mace wlhy ka ji kunya in banda iskanci da kana tambaya ta me ya kawo ni office in ka ne,sabida yanzu ka ga karamar yarinya shine duk ka wani bi ka rude ta kare tana Galla masa mugun harara,


Look Kareematu daka ta mun and ya zamo karo Na karshe da zaki zage ni,jiki ne Kin ce bara ki sake bani naki ba,toh ai ba ke kadai bace me shi Na ga duk matan duniya da shi aka haife su,don haka ki jiga naki ki shanye sannna ki cire ido akan abunda zan yi domin ba ruwan ki,


Ba shakka Bashir ai ka fada mun komai an sha magoro an shanye dadin an yarda ba,toh wlhh baka isa ba,


Be ce da ita komai ba ya juya tare da kokarin barin office in Sai kuma ya juyo in kin gama surutan da iska kina iya fitowa ki rufe mun kofa,domin Na ga sabon likitan nan an sha wanka yau kya iya zuwa ya rage miki zafi don Na ga kamar a matse kike,


Bura uba Bashir ni kake wa bura uba duk Dan Na kama ka da mace,ka mun laifi sannan ka fi ni baki,Amana ta fa ka ci bura uba shine kake watsa mun magana son ranka,ta kare tana girgiza, shi dai be ce da ita komai ba,yana kokarin fita


Ai ka fita Amman ka fin ka bi shegiyar yarinyar ta ka ina so ka biya dakin Nadeeya ka ga halin da take ciki,domin am very sure in har ka ganta sha'awar kan ta sai ta dauke maka domin ka san waye uban ta sarai wlhy ba yarda zai yi ba,


Da mugun hanzari ya nufo ta yana fadin Na shiga uku Kareematu me kika yi wa Nadeeyan,hannun shi ta doke sannan tace ka ji mun Dan iska me kuwa zan mata ni ma abunda nake son in tambaye ka ke nan,domin ai kai ka ganta Na karshe jiya har ka jona mata shocking, halin da ake ciki yanzu dai,ai be jira karasa Jin ta ba ya nufi dakin Nadeeya a 360 zuciyar shi Na tsanan ta bugawa,yana adduar Allah sa ba wani abun ya same ta ba,to ko dai mutuwa tayi, Na shiga uku shine abunda ya fadi a fili tare da shiga cikin dakin,


A kwance ya same ta idanun ta a bude sai hawaye ke fita,zuwa yayi har gaban ta tare da tsunguna wa yace Nadeeya me ke damun ki,Jin shiru ya sanya shi cewa lfy don't you want to talk,


Nan ma shiru,hankalin shi ba karamin kadawa yayi ba ganin ko motsi bata yi,ga magana ma bata yi,ganin haka ne ya sanya ya dauko alura sanin ko ma iskanci take yi in ta ga aluran tana tsorata tayi ta buge buge Amman har ya tsikara mata ko tari bata yi ba,


Na shiga uku shine abun da ya fadi a bayyane ganin ko hannun ta bata iya daga wa,nan take cikin shi ya murde sai ya ji wani irin zawo Na kokarin zubo mishi, da sauri ya fada toilet in ta ganin zai iya yi a jikin shi, yana zawo yana hawayen tausayin kanshi domin ya San wlhy SEN ya ji labarin nan sai ya kashe shi, a haka ga fito jiki ba kwari ya bar dakin,


Kai tsaye office in shi ya koma tare da kiran Kareematu, da tagumi a fuskan shi ta same shi,dariya ta so yi ganin lokaci daya inda ya ficicike,


Hope ka ganta ko Bashir ka ga abunda nake ta fada maka,Na shiga uku Kareematu shine abunda yace kamar zai yi kuka,wai don Allah me kika mata ne,


Bura uba na rantse Bashir zan ci uban ka in ka kuma ce wa Na yi wa yarinyar nan wani abu,ni sau nawa ma Na taba mata Alura kai ke da in charge in komai nata,don haka am sure kai ne kayi mata wani abun,ka ga tun wuri baran kira uban ta in sanar masa kafin ka kashe musu yarinya a rufe mu da asibitin mu,Ashe bayan san kudi har kisa za ka iya yi,


Zufa ne ya wanke masa fuska cikin muryan tausayi yace Na rantse da Allah Kareematu ban yi wa yarinyar nan komai ba,ni miye hadi Na ko in ce miye riba ta in Na kashe ta ko Na nakasa ta,wlhy babu ruwana da ita,ni ban mata komai ba,don Allah kar ki kira SEN wlhy mutumin nan ba ganewa zai yi ba ki tsaya mu nemi mafita,


Mu nema ko ka nema ni miye nawa,and da kake cewa kar mu sanar wa uban ta,to uban wa kake so mu sanar wa,ai dole kuwa ya ji sabida ya san me zai yi,don hka ni yanzun nan zan Kira shi ba sai anjima ba,


Na shiga uku kareema in kina wa Allah ki rufa mun asiri sai kace ba masoyiya ta abar kauna ta ba,Kareematu Bashir in ki ne fa,


Tsaki ta ja sannan tace kamar ba wa ni ka ga ma yi wa diban Albarka ba sannan yace ka zo kana wani Kareematun ka ce,ai ka je can gidan yari Na San SEN zai sa a kai ka,


Cikin shine ya kuma murdewa yace haba tawan kar ki mun haka,zan tura miki dubu dari da hamsi don Allah kiyi shiru kar ki kira shi Na roke ki,ya kare yana hade hannayen shi,


Harara ta watsa mishi sannan tace dubu dari uku za ka tura mun kafin nayi shiru harda kudin Mari Na don ba banza ka mara ba,


Mamaki yake wai Kareematu ke masa barazana haka ikon Allah, bayi da choice haka a take ya mata transfer in dubu dari ukun,


Dariya tayi ta girgiza kai sannan tace Allah ya shirya ka Bashiru Na bari Na je, Allah kawo maka da sauki,


Da ido ya bita yana me jin haushin ta saidai bayi da choice da ya wuce ya bi ta a sannu domin ya san kwayancin kareema Sam bata da mutunci bata kuma da tsoro,



Kareematu ko tana fita wayan ta ta dauko tare da danna no in SEN, haka kawai ai wlhy Bashir sai Na tona ma asiri, ko ba ni ka mara ba,


Har ya gama ringing ba a dauka ba saida tayi kira sau uku sannan aka dauka,


Gaishe shi tayi cike da girmamawa sannan tace ita daya daga cikin nurses masu kula da diyar shi Nadeeya,yau tun safe take kuka take kiran sunan ka da alamun son ganin ka take yi,ta kare murya cike da biyayya,


Okay I will be on my way shine abunda SEN yace tare da kashe wayan, dan tsallan murna Kareematu tayi kafin ta maida wayan cikin aljuhu tana Jin ranta fesss ko banza ta hadawa Bashir,



...............SEN


Cike da mamaki yake bin wayan da kallo, Kabiru ne yace ya ne Aboki Na lafiya,


Hmmm kabiru bari kawai wlhy kira ne daga asibitin su Nadeeya wai tun safe take ihun kiran suna Na wai tana son gani na,


Ganin ka kuma, wlhy nima abun ya dauran kai Na dau by now bakin ta ya rufu kirif,Amman sai Na ji wani abun daban, kai kan ka fa kasan aikin odugwu kamar yankan wuka ne tunda har ka bada abunda ake so kuma kai kan ka kace mun an karbi sacrifice in ka Odugwu be taba karya alkwari ba,tunda har yace zai yi to wlhy zai yin ne ba fashi ,Amman tashi mu je asibitin Na karasa maganar a hanya,


Nan suka nufi mota sai hospital, kai tsaye office in Bashir suka fada wanda suka tarar ya kifa kanshi a jikin table,


Doc bashir Alh Kabiru ya kira sunan shi, a razane ya dago ganin SEN a tsaye a Kansa shida Kabiru ya sanya ya ji hanjin cikin shi ya kada,saidai yayi kokarin dannewa tare da mikewa, cikin karfin hali yace SEN sannu da zuwa lafiya Na gan ka ga  guri ka zauna,


Murmushi SEN yayi sannan yace aa ba sai Na zauna ba Na zo ganin princess ne,


Da sauri yace yallabai an ce ma wani abu Na samun ta ne,babu fa abunda ya faru da ita tana nan cikin koshin lafiya,


Da ido SEN ya kalle shi sannan yace Bashir ni ka ji Na ce akwai abunda ke damun yarinya ta,ko kuma laifi ne in uba ya zo ganin yar sa,


Kai kake masa bayani ma SEN daman ka fada mun yawa magana Bashir ke da shi ,dallah tashi  ka kai mu,muna da abun yi,


Jiki babu kwari ya mike tare da yin gaba suna bin bayan shi,SEN ke rada wa Kabiru ya yaga Bashir kamar yana cikin damuwa,yoo ni ina nasan wa Dan iska mu dai je mu gan ta first mu san halin da muke ciki,


Da sallama Bashir ta shiga dakin zuciyar shi Na bugawa uku uku,ji yake kamar ya rufe su a dakin ya ruga da gudu sabida gudun abunda SEN zai masa,saidai is to late yayi hakan,


Shi ko SEN karasa shigowa dakin yayi yana me hango Nadeeya a kwance lah bacci take yi ne ya tambaya yana nufan yanda take,


Da sauri Bashir yace eh ta samu bacci ashe mu je kar a tashe ta in ya so sai ku dawo ko jibi ne ku ganta tunda dai ai kun ga tana cikin koshin lfy,normally ba mu cika barin ana yawan ganin majin yatan mu ba,


Wani irin harara sen ya jefa masa sannan yace a yaushe kuka fara wannan tsarin iskancin, da rawan baki yace jiya cikin dare,ko kula shi be yi ba ya durgusa a gaban Nadeeya din da ya gani idon ta bude kamar ma hawaye take yi,


Kabiru ka ga Ashe ma idon ta biyu tana Jin mu,kanta ya shafa sannan yace hello princess, he was expecting ya ga ta janye hannun nashi kamar yanda ta saba ko ya ji tana jifan shi da mugayen maganganu saidai tsit ya ji ta,


Da matukar mamaki ya mike tare da kallon Bashir sannan yace why is she not talking, me ke damun ta kuma, Na ga yau ko ihun da ta saba da fashe fashe bata yi lafiya kuwa,


Nan take Bashir ya hau inda inda fadi yake hmmm ammmm ahhhhh daman,tassss SEN ya wanke shi da Mari sannan yace daman in uwar ka ka fada mun uban me kayi wa yarinya ta bata mun magana,


Cike da radadi tare da rudewa yace yallabai Na rantse da girman Allah dazun nan Na shigo Na gan ta haka bata magana ko motsi ma bata yi,ya kare yana kare fuskan shi da hannu biyu biyu,


Ai Jin haka ya sanya wata irin jiri kwasan senator sai ga shi yuuuuuu yayi baya zai zube a kasa,da sauri suka taro shi Kabiru yana fadin take it easy Aboki na in sha Allah babu abunda zai samu Nadeeyar mu.....


Manage this please aiki ya mun yawa wlhy,


Bi sa complain in da Na samu Na in Kara 2 more pages kafin Ramadan ya sanya ni yin typing yau, saura yanzu 3 more pages in sha Allah,


Bani kuma da bakin gode muku, masoya Na Wanda Na sani da Wanda ban san su ba,saidai nace Allah ya saka da Alkhairi da kaunar da kuke nuna mun,nima ina kaunar ku fisabillah,


Ina wa kowa fatan Alkhairi,


Sai kina gobe in Allah ya kaimu.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


.......


My group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin san ba karanta book ina and comment zai shigo da ke ba,to pls kar ma ki shigo, haka zalika maza should stay far away from my group pls🙏🏻,


Ga masu bukatar a tallata musu hajojin su contact me via:


   08100046388


............

          Page eighteen


************


Ruwa Alh Kabiru ya shafa wa SEN a fuskan shi Wanda ya dawo da shi daga duniyar sumar da ya fada,wata irin nannauyar ajiyar zuciya ya sauke sannan ya bude idanu a hankali,


Doc bashir ya gani tsaye a kan shi wanda kallo daya za ka masa ka fahimci yana cikin tsaka me wuya,


Ai da sauri ya mike tare da cukumo wuyar rigar Bashir sannan cikin ihu ya hau masa fada,Dan uban ka me kai wa yarinya ta eheyeee bara ka yi magana ba,ya dauke shi da Mari me zafi,


Kumatu Bashir ya dafe sannan ya shiga rantse rantse kan cewa wlhy shi ba abunda yayi wa Nadeeya,


Wani Marin SEN ya dauke shi da shi a Karo Na uku sannan yace har ni zan yarda da ba abunda kayi mata,nawa suka baka ka maida mun ya haka,toh wai miye ma ka mata ne,wato duk kudin da nake baka be ishe ka ba saida makiya suka Kara maka ka maida mun yarinya haka,haukatar da ita kawai nace kayi wawa ba wai ka nakasa mun rayuwar yarinya ba ya kare ya me tada jijiyoyin wuya,


Doc bashir baki ya mutu banda girgiza kai babu abun da yake yi,idanun shi har ya ciko da kwalla ya rasa da wani kalma zai wanke kan shi a gurin SEN,


Shigowan sister Kareematu ne ya sanya shi saurin nufan ta,fadi yake yauwa Kareematu Na gode wa Allah da ya kawo ki don Allah sanar da su babu abunda nayi wa Nadeeya,


Da kallon wulakanci ta bishi sannan tace ai daman Bashir saida Na fada maka aluran da kake bata sun fara yi mata yawa,Amman kaki ji karshe ka hada harda shock treatment kake mata,taya daman yarinya bara ta zama haka ba,


Ai bata hada bakin ta ba ta ji saukan mari me dankaran zafi Wanda saida ya sanya ta zaro idanu, sabida radadi,


Na shiga uku miye nayi da za ka mare ni haka ranka ya Dade,


Uwar ki kika yi matsiya ciya wato da hadin bakin ki aka kusa kashe mun yarinya, Na rantse da Allah SEN ni babu ruwa Na gashi nan shima saida Na Hana shi yace da ni babu ruwa Na ta kare tana nuna Doc bashir da ya zazzaro ido sabida tsoro,


Cukumo shi SEN tayi tare da Kara wanke shi da Mari Wanda saida ya sanya Kara,yanzu Bashir Ashe kai Dan iska ne ban sani ba miye nayi maka da har za ka sanya wa yarinya ta shock treatment,


Na rantse da girman Allah ba zan bar ku ba,daga kai har wannan shegiyar ya kare yana nuna Kareematu a gidan yari za ku karasa wahalalliyar rayuwan ku,shegu yan iska marasa mutunci, Kabiru kira mun police su zo suyi gaba da mugayen mutanan nan kafin bakin ciki ya sanya Na kashe su da hannaye Na,


Nan take cikin Kareematu ya duuri ruwa ita fa ta zo ne domin ta sanya Bashir a damuwa da matsala sai gashi ta samu rabon Mari harda za a kama su to akan me,


Kamar hadin baki sai ga su sun zube a gaban SEN suna hada shi da girman Allah kan yayi hakuri kar a hada su da hukuma,wlhy tallahi babu hannun su a wannan abunda ya farun,


Ba karamin kai ruwa Rana aka yi ba kafin aka samu SEN ya ce ya hakura bare kai gurin yan sanda ba Amman fa ya zama dole a dawo mishi da magana da kuma tafiyar yarinyar shi,domin bare yu ya basu yarinya da muryan ta da kafafun ta sannan yanzu a dawo da ita vegetable ba Sam bashi yuwa,


Haka dai suka yi ta bashi baki harda Alh Kabiru a masu bada bakin,sannan ya dan sauko daga masifar da yake yi,


Haba Alh Kabiru Na basu yarinya da lafiyar ta sannan yanzu ace ta dawo haka wlhy dole suna da masaniya,don haka Na basu Dan kankanin lokaci ko su dawo mun da yarinya ta daidai ko kuma Na kashe su da hannu Na,wuce mu tafi domin Na cigaba da tsayuwa ina iya aikata abunda be dace ba ya kare yana gallawa bashir da Kareematu mugun kallo sannan Alh Kabiru ya biyo bayan shi zuciyar shi cike da mamakin karfin hali irin Na SEN,


Suna shiga mota kuwa SEN ya kwashe da wata irin dariyar samun Nasara sannan ya zubo kirari da yar banci wa odugwu sannan ya kalli Alh Kabiru da ya zuba mishi idanu,yace ya aka yi ne mutumina,


Hmm Wlhy tallahi RILWANU tsoro ka koma bani,ban taba ganin makirin mutum ne fuska hudu ba irin ka,wlhy ko mace nan ta gan ka ta bar ka gurin tuggu,kwalba uwar sharri,ina tsoron ka wlhy,


Dariya SEN yayi sannna yace haba dai Kabiru kai da ka kwanta da Maman matar ka ka baiwa odugwu Jinin ta ban ji tsoron ka ba sai don ni da nayi wannan dan karamin drama in,


Tsaki Kabiru yayi sannan yace kai magana bata wuce maka maganar kwanciya da suruka ta nake maka ko ta draman da kai wa Bashir, sanin kan ka ne fa kai ne silan ciwon yarinyar nan Amman ka bude idanu ka nuna Sam baka da masaniya,kamar ma sune suka aikata,duk ka sanya su a guilty conscience,wlhy Sam baka da imani SEN,


Har in ana maganar imani za ka sanya baki,ko ka mance yar ka yar 3 years da kai raping ka kashe da hannun ka,sai dan dan wannan abunda nayi kake ce mun banda imani,


Don't forget duk abun nan muna yi ne don securing future in mu,and wlhy da asiri Na ya tono Na gwammaci ko ma miye ne nayi,but I have to protect my dignity shine kawai abunda Na sani,and so kake Na nuna nasan komai a gaban doc in look ina cikin mood in farinciki don Allah kar ka bata mun rai,beside Kabiru in mugunta ne har Na isa in kai ka abunda kayi ai ko zan mutu Na dawo ban isa nayi kwatankwacin su ba,


Aboki Na ke nan yau kuma tone tonan asiri ne ya tashi ke nan,Dan dariya yayi sannan yace komai kayi ba komai bane in har za ka samu kudi,go chase the bag,kar ka matsa wa kan ka legal or illegal ne in har za ka yi kudin shike nan,


Ah toh nima abunda Na gani ke nan,kai ne kake son fito mun da wata tsirfa tun farko da  bata san komai ba ai da yanzu muna zaman mu lafiya ko,sannan kasan am damn lucky Nadeeya ta San asiri Na Amman odugwu ya mun Alfarma Na bar ta a raye har yanzu,ka ga ko dole nayi ko me zan yi Na ganin bakin ta yayi tsit gudun tonuwar asiri,


Haka ne kam wlhy SEN baka da dama ko kadan,am very sure Bashir be isa bacci ba yau,dariya SEN yayi sannan yace siyasa ke nan mutumi na dole ka koyi dabaru nan ne zaka mori zaman duniyar,mu karasa gida domin a gajiye nake wlhy,Kabiru be sake cewa komai ba har suka iso gidan SEN, inda suka hadu da Alhaji Salis nan aka zauna SEN ke labarta mishi abunda ya faru yana kuka,ba karamin tausayi ya bai wa Alh Salis ba,nan ya shiga zubo tsinuwa da addu'ar samun lfy wa Nadeeyar,



***********Doc Bashir


Kadan ya rage be rufe Kareematu da duka ba domin ba karamin haushin ta ya jj ba,banda rawan kai uban me ya kawo ta office in shi  har da sanar wa SEN wai yana bata shocking,


Kallon ta yayi cike da bakin ciki sannan yace kin kyauta Kareematu Amman ki sani wlhy sai Na rama abunda kika mun tunda ke bakin ki sam be iya yin shiru, banza karuwa kawai,


Dariya ta sheke da shi sannan tace karuwai dai yanda nake karuwa haka kake karuwan Na miji,acewar ka banza ka mara ko,toh wlhy ka kiyaye ni, sannan da kake cewa sai ka Rama sharri nayi maka,Na gani duk abunda ke faruwa shine na fada,ni ban ce sai na rama ba akan ka an mare ni sai kai ne me hannun daukan fansa to bismillah,sakarai kawai wlhy in ka kuma kula ni ma sai nayi maka rashin mutunci, da haka ta sanya kai za ta fita,ko me ya tuna sai kuma ya bi bayan ta yana haba my Kareematy ai ba a Jin kan mu tsaya mu sasanta ko kallon yanda yake bata yi ba tayi gaba abun ta,



**************Doc Nameer


Gama wayan shi ke nan da mama yana sheda mata yayi missing in su yana son shigowa Kd this weekend in sha Allah, agogon hannun shi ya kalla ya ga goma har ya wuce,so yake ya shirya ya tafi gurin Nadeeya Amman sam yau baya Jin karfi a jikin shi,haka kawai kuma wani gefe Na zuciyar shi ke azaxxalar sa akan ya je ya duba ta din kamar tana cikin wani matsala haka yake ji a cikin ranshi ,saidai he is very tired yau be jin xai iya zuwa duba ta, alulan bacci ya dauro sannan ya kwanta bayan yayi adduan bacci tare da yaki ce tunanin Nadeeya a cikin zuciyar shi,


Saidai sam baccin ta kasa daukan shi ya kuma kasa daina tunanin Nadeeya,


Tsaki ya ja tare da mikewa jallabiya ya zura sannan ya dauko car key in shi tare da fitowa,


Saida ya biya Saje ya siyo mata ice cream da Shawarma sannan ya dauko hanyan asibitin,kamar kullum dan cin hanci da ya saba bai wa securities in ta bada tare da shigewa a bun shi,


Dakin nata ya nufa kai tsaye,yana adduar Allah sa bata yi bacci ba don kila ta gaji da jiran shi tayi bacci abunta,be taba sanin ya shaku da yarinyar ba sai yau da yace bare zo ganin ta ba har wai ya kasa bacci saida ya fito,


Da sallama ya shiga cikin dakin yana me Jin mamakin ganin komai tsaf kamar naughty girl in shi bata wuni a dakin ba yau,shirun da ya ji ya sanya shi tunanin kila baccin tayi,


Sleeping beauty har an yi bacci ke nan yace tare da nufo kan gadon nata,kwalbar da kafar shi ba buge ne ya sanya shi tsayawa tsak,tare da tsungunawa don ganin kwalbar miye haka, is not suitable ana barin kwalabe a dakin me jinya jinyan ma Na hauka,in ta ji wa kanta ciwo ba,idanu ya zaro tare da kare wa kwalban kallo,daidai lokacin aka bude dakin tare da shigowa,


Idanu Doc bashir ya tsaro cike da mamaki sannan yace kwal uba uban me kake nema ana dakin cikin daran Nan......



Remaining 2 pages in sha Allah sai kuma in Allah ya sa mun kai bayan sallah,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi,


Sai kuma gobe in sha Allah

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

          BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


........


My group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin san ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki toh don Allah kiyi zaman ki ba sai kin shigo ba,haka zalika maza should stay away from my group domin Na mata ne zallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


   08100046388


...........

         Page nineteen


***********


A razane doc Nameer ya dago domin sam be yi expecting ganin wani a wannan lokacin ba,caraf suka hada idanu da Doc Bashir,


Bura uba kai daman kai ne uban me ka aje a dakin nan da za ka zo dauka cikin daran Nan,ya kare yana nufo in da Nameer in ke tsaye,


Shiru doc Nameer yayi ba tare da ya kula shi ba domin gaba daya tunanin shi ya tsaya ne da kwalban dake rike a hannun shi,


Kwalan rigan shi Bashir ya cukumo,cike da bacin rai ya hau sababi,wato kai sam baka Jin magana ko,sau dubu nawa zan fada maka kayi staying away from Nadeeya ni ke handling case inta,Amman sam kunnan ka Na kashi ne,sabida ka maida mutane yan iska shine kake biyo wa dare kake shigowa dakin ta uban me kake mata,mara da'a mara tarbiya shege Wanda be da tausayi a cikin ranshi,


Irin kune mugayen doctors da ke taking advantage in patient kuke lalata da su a cikin dare in kowa ya tafi to Allah yau ya toni asiri ka Dan uban ka,kila kai ka jefa ta cikin wannan halin da take ciki aka zo za. a daura komai a kaina, ya kare har bakin shi Na kumfa,


Tasss Doc Nameer ya dauke doc bashir da mari, da mugun mamaki doc bashir ya dago ya kasa yarda wannan yaron ne ya mare shi,


Bakin shi har rawa yake gurin fadin kai ni ka mara,cike da tsantsan bacin rai doc Nameer yace an mare ka ko za ka Rama ne bismillah,


Tsoro ne ya kama doc bashir ganin inda idanun doc Nameer suka kada suka yi ja daga ganin kasan ran shi a matukar bace yake,


Cikin zafin rai yace sake mun Riga ko na yanke maka hannu yanzun nan wlhy kuma Na yanka banza babu abunda aka isa a mun,


Cikin sauri doc bashir ya cika mishi kwalan rigan domin sam be ga alamun wasa a tattare da doc Nameer in ba,daga haka Nameer be kuma cewa komai ba ya sanya kai tare da ficewa daga cikin dakin zuciyar shi Na tafarfasa bisa irin mugayen kalaman da Bashir ya jefe shi da su,


Shi ko Bashir mamaki ne ya kama shi da kuma Jin haushin kan shi,akan wani dalili zai sake shi ya tafi,be san ya aka yi ba sai ya ga yaron yayi mashi wani irin kwarjini,toh uban me ya zo nema a dakin Nadeeyan a taya ma ya san pin code in shiga dakin,Kareematu shine abun da zuciyar shi ta sanar masa, shegiya kila ita ta sanar mishi tunda ita ke ta rawan kafa a kan shi, ai ko daga shi har ita sai ya ci uban su gobe,


Tsaki ya ja tare da shafa kumatun shi,ji yake kamar ya danna wa Nadeeya pillow bare daga ba har sai ta daina numfashi ko ya samu ya huta daga azabar Marukan da yake karba,ace da girman shi da matsayin shi ana dauke shi da maruka haka bini bini, and daga shigowar wannan shegiyar rayuwar shi ne fuskan shi ya zamo available haka kowani Dan iska mara yake,ace wai har Nameer nawa yake da zai kwashe shi da Mari,toh in har dai a cikin asibitin nan yake aiki da yardar Allah sai ya hada mishi abunda zaman garin Bauchi ma sai ta gagare shi,tsaki yayi tare da Galla wa Nadeeya da ke kwance harara sannan ya fice daga dakin yana auna musu zagi a cikin ranshi,



*************Doc Nameer


Isowan shi gida ke nan ko parking me kyau be tsaya yi ba,ya fice daga motar tare da fadawa cikin daki,


Jallabiyar jikin shi kawai ya tube tare da shige wa cikin bandagi,domin yanda yake Jin zuciyar shi Na tafasa hakan nan in ba ruwan sanyi ya watsa a jikin nashi ba bare samu sauki ba,


Ya dauki Dan tsahon lokaci yana sheka wa kan shi ruwan sanyi wai ko zuciyar shi za ta Dan yi sanyi,Nameer mutum ne me saukin kai da sanyin hali Amman sam baya daukan wulakanci da kuma kazafi,


Saida ya dan ji dama dama sannan ya fito daga bandakin waist in shi daure da towel,kan gado ya fada tare da lumshe idanun shi maganganun Bashir Na dawo mishi cikin ka,


Daga jin tausayi ko in ce daga taimako shine zai na jefan shi da irin wannan mugayen kalaman,Allah Na tuba ni har akwai macen da za ta burge ni nayi taking advantage in ta ne,beside in da iskanci yake so ga mata nan birjit a gari,a cikin asibitin ma matan da ke kawo musu kan su sun fi guda nawa,ya Na ki,sai ace ya rasa Wanda zai lalata sai Nadeeya Wanda ke kwance bata ma san inda kanta yake ba,


A rayuwa babu abun da ya tsana kuma yake tsoran sa kamar zina,domin ya san bashi ce,in har ya bata yar wani to dole a bata mishi angel in shi tunda ai ya haifa,bare sanya kanshi cikin layin maza da basu da bukatan mace a tare da su ba ya sanya tun rasuwar Raa'isah ya lazumci yin azumin nafila da sallan dare domin kare kanshi daga fadawa halaka,


Hakika nin gaskia ba karamin sosuwa ranshi yayi ba yau,and yayi Alkwari daga Rana me kamar ta yau babu shi babu Nadeeya,ba zai Kara zuwa inda take ba balle har wani banza can ya kuma zagin uban shi da ya Dade da kwanta dama,


Nameer irin mutanan nan ne masu takatsan tsan da gudun shiga damuwa,saisa abu kadan in har ya same shi to sai ya zamo ya dame shi kuma,wannan daran gaba daya cikin bacin rai yayi shi,yayi danasanin zuwa ganin ta ma in the first place da be je ba ai da duk hakan be faru ba,ganin bacci yana kokarin gagaran shi ne ya sanya shi mikewa tare da dauro alola ya shiga yin sallah,ba shi ya samu ya rintsa ba saida ya gabatar da sallan asuba bayan ya gama Azkar in shi nan kan sallayan bacci ya dauke shi,


Karar alarm in shi ne ya farkar da shi,in da ya mike ya shiga wanka,cike da nutsuwa ya shirya cikin blue trouser and black t shirt Wanda ba karamin amsan shi yayi ba,


Combing in gashin shi yayi tare da feshe jikin shi da turaruka masu sanyin kamshi sannan ya fito, coffee ya hada tare da warming in sandwich in da ya aje a cikin fridge shi ya ci as breakfast in shi sannan ya hada all necessary abubuwan da yake bukata tare da fitowa don tafiya asibiti,


Saida ya zo bakin motar sannan ya tuna Ashe a cikin aljihun wandon shi Na jiya ya bar car key in,dan goshin shi ya dafe sannan ya koma cikin gidan, wandon ya dauka tare da sa hannu a cikin aljihun har ya dauko key in Sai kuma ya ji kwalban da ya sanya jiya,dauka yayi tare da aje wandon ya fito ya shige motar shi,shi ba ya manta ma da kwalban ba,wani Abu ke ce masa ya yarda shi ina ruwan shi tunda yace yanzu kam babu shi babu Nadeeya so ba bukatar ya je yana confronting in doc Bashir, saidai wani zuciyar ta shi ta ki yarda da ya yarda in,a haka ya sanya cikin aljihun shi tare da nufar asibitin yana Jin he is ready koma miye Bashir zai yi masa,


Cikin sanyin jiki ya ke gudanar da aikin shi,haka kawai sai yake ji kamar in ya ce ya rabu da ita be yi mata adalci ba sabida babu abunda tayi mishi ai,beside he is curious ya san me ke damun ta ya ji Bashir yana cewa wai shi ya jefa ta cikin halin da take ciki,shi dai ya san lafiya lau suka rabu da ita shekaran jiya,ji yake kamar ya je dakin nata ya duba halin da take ciki Amman kuma sai ya Hana kanshi,dole ya yakice tunanin yarinyar,to akan me ma zai na sanya ta a ranshi, a ina ya santa da har yake jin anya matakin da ya dauka Na nisan ta kanshi da ita shine daidai,


Wata nurse ce ta shigo office in nashi tare da sanar da shi ya je doc Bashir Na son ganin shi,


Dan guntun tsaki ya ja sannan ya mike daman ya san za a yi haka,shi dai he is not ready for all this dramas in,but be da zabi da ya wuce ya je gurin Bashir in suyi ta ta kare,


Cike da takun shi na nutsuwa ya nufi office in doc Bashir in,saida yayi knocking yace ya shigo sannan ya shiga bakin shi dauke da sallama,a zaune ya tarar da doctor Bashir ya daura daya kan daya fuskan shi sanya da wata bakar glass kamar wani boss irin baya cike da nonsense in nan lol,


A nutse Nameer ya ja kujera tare da zama yana wasa da ring in finger in shi,


Cike da kallon tsana ya dago ya kare wa Nameer kallo yana ji kamar ya shake shi ,amman ba daman yin hakan,


Cike da isa da izza yace waye ya baka izinin zama,dagowa Nameer yayi tare da nuna kanshi cike da izgilan ci yace wai ni ya kare yana nuna kanshi,


Ran Bashir ne ya baci ganin wani rainin wayo da Nameer ke shirin masa,aa da aljanin ka nake yi,


Dan dariya Nameer yayi sannan yace doc Bashir ke nan,wai duk tsannan nan Na miye ne,and da kake maganar kujera in ba mu zauna a kai ba su za su zauna akan kan su ne,


Mike wa Bashir yayi cike da bacin rai ya cire glass in sannan yace wlhy ban taba ganin Dan rainin wayo irin ka ba,ko ban fada maka ba kasan kai me laifi ne,maimakon ka bani hakuri Na rufa maka asiri shine kake mun iskanci son ranka,


Tashi Nameer yayi shima cike da bacin rai yace kai Bashir daka ta mun ba wai don fa ka gani a hospital in ku  muna aiki guri daya kayi kokarin ci mun fuska ba,baka San ni waye ba wlhy da ko kudi aka baka ka tsaya a gaba Na kayi mun ihu bara ka samo ba balle harda zagi Na,


Sannan kasan in har nace zan kai ka court akan furucin da ka mun jiya sai an daure ka sabida kayi mun kazafi, kace ina neman Nadeeya da lalata tunda muke ka taba kama mu,beside jiya da ka shigo ko finger in ta ka ga Na rike ne,


Katse shi Bashir yayi da cewa duk wannan abun da kake yi borin kunya ne wlhy ga ka dai a fuska kamar mutumin kirki,Amman Ashe ba haka bane, in har ba lalata kake yi da ita ba miye zai shigo da ita dakin ta karfe 11 Na dare me kake nema,ban sanar da kai kayi staying away from her ba,amman kaki,sabida akwai boyayyan nufi a ranka to wlhy ni babu ruwana zan Kira hukuma yanzu Na shigar da karar ka gudun abunda zai je ya zo ah toh babu ruwan uban yarinyar ba yarda zai yi ba muddum wani abu ya same ta,


Dariya Nameer ya sanya tare da tafa hannuwa sannan yace Wow Bashir just wow don Allah ka kira su yanzu ma nima zan fi son ka kira su din ka ga Na sanar da su miye empty kwalban CHLORPHENIRAMINE ke yi a dakin Nadeeya,


Idanu Bashir ya zaro tare da goge zuban da ke goshin shi,call them mana Na ga ni da kai case in waye xa a fara shigar wa Na ga ko uban yarinyar da ni da kai wa zai fi Jin haushi,


Ni da kai dukkan mu doctors ne and am very sure ka San  aluran miye kwalban shi ke dakin Nadeeya,


Yawu Bashir ya hadiye sannan yace a yaushe ne ka ga kwalban, and da kake cewa haka kana da sheda ne,


Dariya Nameer ya kuma sannan ya fiddo da kwalban daga aljihun shi Ni bana nufin kowa da sharri sannan bana magana ba tare da hujja ba,kasan in har nayi presenting wannan kwalban to taka ta kare,domin am very sure a prison za ka kare rayuwar ka,and am very sure sai an kwace lasisin ka in ba a yi wasa ba harta asibitin nan sai an kulle,


Don nasan ko ban fada ma ba aluran CHLORPHENIRAMINE bashi ya dace ana yi wa mara lafiya irin Nadeeya ba,shi alura ne da ake wa lafiyayyar mutum in ana son ya kamu da deep depression Wanda zai yi leading to haukan shi,


In har na can ka daidai aluran da kuke yi wa Nadeeya ke nan Wanda take complain yana mata zafi Na sanar maka kace I should stay away from her kai ke handling case inta,


Baiwar Allah Ashe lafiyar ta lau kai ne mugu Wanda wasu mugayen suka hada baki da shi ake son cutar da ita wlhy ka ji kunya Bashir, a hakan in an taba ka kace malamin jinya me kula da marasa lafiya  kai,


Ka fada mun in har da irin ku taya daman duniyar mu za ta cigaba, akan kudin da be taka Kara ya karya ba kake neman salwantar da Rayuwar yarinya in har yar ka aka yi wa haka fa,sam zuciyar ka ba imani, don baka da kunya har ka tsare ni kana fada mun maganganun banza,toh wlhy baran fada maka this should be the first and last time da za ka shiga harka ta if not I will fuck you up wlhy,sai na kashe ka Na cinye namanka tas ba tare da uban kowa ya sani ba,sannan ni baran iya zama in zuba ido ana zaluntar baiwar Allah ba,ya zama dole Na shigar da Kara ko Na nemi mahaifin ta in sanar da shi komai da ke faruwa,am done talking to u am taking my leave, ya kare tare da barin office in yana Jin sanyi cikin ranshi, daman aka ce in har kasan Na fada toh baka san Na mayar wa ba,


Na shiga uku na lalace shine abunda Doc bashir yace tare da safe kai, garin Yaya yaron nan ya gano aluran da yake bai wa Nadeeya, abunda ya sanya ya hana kowa zuwa kusa da ita ke nan,shi da ya shirya sirfa mishi buhun wulakanci in ta kama ya masa dukan tsiya shine rashe ta juya da mujiya, in har ya kai maganar nan gaba ya shiga uku,domin babu Wanda zai yarda SEN ne ya sanya shi ya haukatar da yar cikin shi,babu Wanda zai ma yarda da maganar don hankali ma ba dauka zai yi ba,wat if yaron nan ya fada wa yan sanda da gaske a prison zan kare rayuwa ta,nan take ya ji wata irin zazzabi ya sauko masa,abunda fa ya shigar da shi dakin Nadeeyar ke nan fa jiya don ganin ya mance kwalbar aluran haduwar shi da Nameer shi ya mantar da shi abunda ya shigo yi,ashe shegen yaro dauka yayi, yayi danasanin tsanan yaron da yayi tun farko ma,


Zaga office in shi ya hau yi yana Jin zuciyar shi kamar zai fito tsaban tsoro, kalman Na shiga uku kawai yake maimaitawa,ganin tsayuwa ba inda za ta kai shi ne ya sanya shi fitowa daga office in shi ya nufo office in Nameer in har yana kusan faduwa tsaban sauri,


A zaune ya tarar da au shi da doc Habeeb suna ta dariya da alamun hira suke yi, ganin yanda ya fada musu a fujajan ne ya sanya su mikewa suna tambayan doc Bashir lafiya??


Haushi ne ya kama Bashir in ganin harda Nameer yake tambayan wai yana lafiya, ji wani tambayan rainin hankali, Amman sai ya matse tare da gyara tsayuwar shi yace lafiya klau doc Nameer na dan gan ka mana don Allah, jin hakan ne ya sanya doc Habeeb excusing kan shi tare da ficewa ya bar musu office in.....




Yooooo 


Saura 1 page to go in sha Allah


Ina godia da kaunar ku a Gare ni ubangiji ya bar zumunci,


Sai kuma gobe in sha Allah


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

         BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


.........

MY group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin san ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki to don Allah kar ki shigo, haka zalika maza should stay far away from this house domin gidan mata ne zallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


   08100046388


ALHAMDULILLAH,A NAN ZA MU DAKATA DA LITTAFIN NAN HAR SAI ME KOWA ME KOMAI YA KAIMU BAYAN SALLAH,INA MIKA GODIA TA GA DUMBIN MASOYA NA WANDA NA SAN SU DA WANDA BAN SAN SU BA,INA GODIA DA IRIN KAUNAR DA KUKE NUNA WA LITTAFINA,UBANGIJI YA SAKA WA KOWA DA ALKHAIRI SANNAN YA SANYA MU FARA RAMADAN A SA'A,ALLAH YA SANYA WANNAN RAMADAN IN YA ZAMO SILAN SHIRYUWAN MU BAKI DAYA,UBANGIJI YA SA MU DACE SANNAN YA SANYA MUNA DAGA CIKIN BAYIN KWARAI DA ZA A YANTA DAGA WUTA ZUWA ALJANNAH,


SAI MU KASANCE MASU AIKATA ALKHAIRI DUK KANKANTAN SHI DOMIN DUK ABUNDA KAYI LADA NE A WANNAN WATAN,CIYAR DA MARA SA KARFI BABBAN LADA NE,ALLAH UBANGIJI YA BAMU IKON AIKATA AIKIN ALKHAIRI SANNAN YA RABA MU DA SABA MISHI A WANNAN KWANA 30 DIN,


DUK WANDA NAYI WA LAIFI YA YAFE NI SANNAN NA YAFI KOWA,DOMIN YANA DA KYAU KA FARA AZUMI BABU KOWA DA KA RIKE A CIKIN RANKA,UBANGIJI YA MANA ALBARKA BAKI  DAYA SANNAN YA AMSHI IBADODIN MU YA KUMA YAFE MANA KURA KURAN MU🙏🏻,


............

          Page twenty


***********


Da ido Nameer ya bi doc Bashir da kallo,daman yayi expecting ganin shi a daidai wannan lokacin, domin yana iya hango tsantsan tsoro da ya darsa masa a cikin zuciyar shi,


Cike da muryan shakiyanci yace ah Doc bashir kai da kan ka ai da aikawa ma kayi Na zo sai na zo ai,


Lebe Bashir ya dan ciza sannan ya yayi kwafa a cikin ranshi kafin ya sanya fuskan tausayi yace a a Nameer gwara dai Na zo da kai na din, ya kare yana isowa kusa da shi,


Kallon shi kawai Nameer ke yi yanda duk ya bi ya rude kamar ki ce da shi kitt ya ruga da gudu,


Haba Nameer a rayuwar nan me na tsare maka da ka tsane ni har haka kake son ganin baya Na,


Da mamaki Nameer ke kallon Bashir in kafin yace Allah raba ni da ganin bayan wani bawa naka,doc Bashir hakikanin gaskia ban tsane ka ba hasalima miye hadi Na da kai da zan tsane ka babu abunda kayi mun,banda yau da Na kama ka da rashin gaskia,and sannan kai kanka kasan abunda kake ai be kyautu ba ko tsoro baka ji wannan alurai da kake bawa yarinyar nan ya jefa ta cikin wani hali haba kar mu zama marasa imani mana akan abun duniya da a nan gidan duniyar za mu bar shi,


Bashir ji yake kamar ya rufe Nameer da duka domin sam shi wannan waazin da yake masa ba shiga kunnan shi suke ba,amman wai me neman sulhu sai yace,


Eh Doc Nameer duk Na ji me kace kuma Na karbi laifi na,nayi kuskure yanzu dai nawa zan baka don ka samu ka sanya wa bakin ka zip,domin maganar nan in har ta fita to wlhy akwai matsala,


Wani dariya Nameer ya kwashe da shi sannan yace daman nayi expecting haka,wato dai mara kunya ko a ina yake baya boyuwa,wai ce maka aka yi kowa ne me son zuciya irin ka,kana tunanin akwai kudin da zai siyi lafiyar yarinyar nan,to bari ka ji in baka sani ba Alhamdulillah I lack nothing a rayuwa ta ina da kawaa da zuci abunda ka rasa ni abun wani be taba tsole mun ido ba kan gaskia ta nake kuma aiki Na nake yi, don haka za ka iya barin mun office ka koma naka ka jira zuwan yan sanda,


Cikin Bashir ne ya kulle yayi danasani cewa zai bashi cin hanci ai ha ci ya gane ba kowa ke da son zuciya ba gashi garin ya gyara ya bata komai,


Amman dake tsohon Dan duniya ne sai cewa yayi,wai Nameer so kake kace da ni baka da son abun duniya,kar ka manta kudi sune maganin zaman duniya,beside miye halakan ka da yarinyar nan ne da ka dage sai ka ga tonuwar asiri Na,


Kai Nameer ya girgiza sannan yayi yar murmushi tabbas ina da babban halaka da ita domin yar uwa ta ce a musulince and humanity came first akan komai,da kake maganar son kudi babu Wanda zai ce baya so,saidai da Na ci kudin da zai hana ni kwanciyar kabari gwara Na mutu da talauci wlhy,


Ni ga alaman sam baka gane wa don Allah ka fitar mun daga office yanzu ba kuma sai anjima ba zan kira mahaifin yarinyar nan Na sanar da shi komai,bare yu ya baka amanar yar sa ba sannan ka zo kana cin amana,


Ganin fa yaron nan ya dage da gaske yake yi in har ya bar shi zai iya tona masa asiri ya sanya shi zuwa tare da zubewa a gaban Nameer in ya kama kafafunshi duk biyu,


Na roke ka da girman Allah ka rufa mun asiri kai ba mugu bane haramun ne saka sharri da sharri,kayi hakuri ka taimake ni kar ka sanar wa kowa koami,wlhy nayi kuskusre na kuma amsa laifi na,


Da mamaki Nameer ke bin shi da kallo yana kokarin jan kafar shi,doc Nameer in ka fada wa yan sanda wlhy a yari zan kare rayuwa ta shike nan tawa ta kare,ina da mata ina da yara da suka dogara da ni in har bana nan rayuwar su za ta daidaice,


Daidaice doc Bashir rayuwar Nadeeya da ka daidaitar fa,wannan hakki har ina za ka kai shi yarinya da hankalin ta ka dage sai ka hauka ta ita kuma fa me za ka ce akan wannan,


Cikin kuka Bashir yace wlhh nayi nadama Nameer Na yi danasani Na biye wa son zuciya Na aikata cuta wa baiwar Allahn da bata san komai ba,Amman tona mun asiri won't solve anything, kar ka manta ance duk Wanda ya rufa asirin wani Allah zai rufa nashi,


Bashir in har na rufa ma asiri rayuwar Nadeeya fa in bar ka ka cigaba da cutar da ita,kana tunanin Allah zai bar Ni ne ina ganin ana aikata zalunci akan ido na and Na gaza yin komai akai,me zan ce masa,


Wlhy in har ka rufa mun asiri nayi maka Alkawari zan zamo mutumin kirki ba zan Kara cutar kowa ba,I will be a change man,and Nadeeya what about her,


Nameer I promise you daga yau bazan kara mata injection ba,ka ga ni da kai sai mu hada force gurin neman maganin da xai yi curing in ta,ya kare yana cigaba da bashi hakuri,


Shiru Nameer yayi yana tunanin Anya ya yarda da shi kuwa,but why not kowa yana laifi and mutum in da aka fi so shine wanda zai gane laifin shi har ya zo neman afuwa, Allah da kanshi muna masa laifi ya yafe to shi waye da ba zai ba wa doc bashir second chance ba,


Cikin sanyin murya yace stop crying and begging me like a little boy,tashi I won't tell anyone anything,


Da sauri doc bashir ya dago yace are u serious, yeah I am miye riba Na in Na tona Na asiri,beside ni ba wa ni kai wa laifi ba,ita ya kamata ka nemi gafaran ta tunda har ka gane laifin ka and ka shirya canjawa Allah yafe mu baki daya,


But I want u to know one thing in har yaudara ta kake yi wlh bara tayi mana kyau ba daga ni har kai,


Da sauri Bashir yace you won't regret this I promise u,Na gode sosai doc Nameer Allah ya yi maka albarka, and am so sorry da irin abubuwan da nayi maka a baya,


Murmushi Nameer yayi sannan yace haba babu komai ai ya wuce,yanzu dai mu fuskanci yanda za mu warkar da baiwar Allahn nan,


To ba damuwa za muyi magana ai bari Na koma office ina Na gode fa, ya kare kamar zai kwanta wa Nameer a kasa,shi dai da ido yake bin shi yana mamakin yanda zuciyar mutun zai bushe sabida son abun duniya ya iya cutar da Dan uwan shi,no wonder mana ya Hana kowa zuwa kusa da ita,shege Ashe be kulla gaskia ba,dariya ya dan yi sannan yace Allah ka shirya mana zuriaar mu,


Doc Bashir kuwa cike da bacin rai da tsantsan tsanar Nameer ya dawo office in shi,Alhamdulillah ya samu yayi wa yaron wayo,Amman ba shakka sai ya muzanta Nameer a cikin asibitin nan yanda ya tozar ta shi sai ya Rama wlhyy, shegen yaro karami da shi sai kwarjinin bala'i,yanzu ya zama dole ya canza takun shi, domin yi wa Nadeeya alurai yanzu ma ya fara, (ni ko nace ba shakka ba ka samu be hada ka da hukuma ba,ai kace komai ma),



**************


Haka nan rayuwa ta cigaba da tafiya ba karamin taka tsan doc Bashir ke yi around Nameer ba,domin nuna mishi yayi eh fa da gasken gasken ya shiryu sannan ya canja,domin tun Randa abun ya faru ya bude wa doc Nameer kofa kan ze iya zuwa ganin Nadeeya duk sanda yake so,and ya nuna mishi ya daina bata injections in nan,he is even researching irin treatment in da zai yi curing in ta gaba daya,


Randa doc Nameer ya ga condition in Nadeeya sai da ta kusa mata kuka,shi sam ya ras why yake daukan damuwar yarinyar nan too personal ne,he wish da yana daa hali da ya warkar da ita, abun ya mata yawa ga hauka,ga rashin magana da rashin motsa jiki tana nan kwance kamar kayan wanki,sam shi be taba ganin irin case in Nadeeya ba,domin banda ido babu abunda take iya motsawa a jikin ta,


Nadeeya Na cikin halin da dole mutum ya tausaya mata,bata hmmm bare uhmm uhmm,saidai tayi ta bin mutum da idanu, at least in haukan ne kawai ai da sauki kana tafiya kana maganar ka,amman a halin da take ciki sai an daga sai an kwantar, banda hawaye ba abunda ke fita a idanun ta kullum kallo daya za ka mata ka gane she is in deep pain,


SEN gurin ta yake wuni in be da abun yi yayi ta kuka yana mata addu'ar samun sauki ke nan,in abun nashi kuma ya motsa ya gasa doc Bashir da zagi kan shi ya jefa yar shi cikin halin da take ciki,saida Alhaji Salis ya dage masa da nasihar karban kaddara kafin aka samu salama,



************ Doc bashir


Around Magrib yana kokarin hada kan komatsan shi ya je hotel in da suka yi da Kareematu za su hadu ya ji an shigo cikin office in nashi kai tsaye ba tare da neman izini ba,(Allah ka tsare mu da aikata zina domin shi zina kama rai Gare shi daga zaran ka fara to wlhy bari wahala yake maka,duk tsiyan da Kareematu tai wa Bashir ba shi ya Hana shi bin ga ya saukar da kai ba domin he is already addicted to her),


Dagowa yayi tare da zuba wa kofar ido domin ganin waye ne haka, cike da takun isa da takagama ya shigo cikin office in,


Da kallo doc Bashir ke bin shi yana kokarin so ya tuna a ina ya San face in nan, shade in idanun shi ya zare sannan yace ya aka yi ne Doc found it difficult to recall me,


Dan murmushi doc Bashir yayi sannan yace my god am so sorry Afzaal ko,


Baki Afzaal ya tabe sannan yace yeah Ashe baka manta Wanda ya taimake ka daga hannun SEN ba,


Dariya Bashir yayi tare da shafa kumatun shi don tuno Marin sen sannan yace have a seat mana ina zan na isa manta ka,shine ya dago ka cikin daran nan ai sa ya kira Na zo da kai Na gida,


Baki Afzaal ya kuma tabewa sannan yace Mal Bashir ke nan dadi na da kai son duniya, a tunanin ka kudi Daddy ya bani in kawo maka ko,


Da sauri Bashir yavr yeah in ba kudi ba miye zai kawo ka office ina cikin daran nan,


Zama Afzaal yayi tare da daura daya kan daya sanna yace I come to talk business ko in ce Na zo a Rama wa kura aniyar ta ne,


Zama shima Bashir in yayi sannan yace ban fahimci inda maganar taka ta dosa ba gaskia,


Dan dariya Afzaal yayi sannan yace bara ka fahimta ba daman ai,like I say business Na zo muyi ni da kai, sannan am willing nayi maka biya me tsoka, from 10 mil har abunda ya kai 50 mil ni me iya biyan ka ne in har za kayi abun da zan sanya ka,


Idanu Bashir ya zaro cike da rudewa ya ji kudi yace 50 mil fa,kai Afzaal wani aiki ne zan maka da za ka biya ni huge amount of money haka,


Zama Afzaal ya gyara sannan yace relax mana ba wani aiki bane me wahala, in har ka yarda za ka yi yanzun nan zan tura maka 50 mil cikin account in ka,


Da sauri Bashir yace fadi koma miye wlhy in har za ka bani wannan kudin ni ko zan iyaiya yi maka koma miye a take ma,


Kanshi ya shafa sannan yace well aiki ne me sauki amman zaka iya kallon shi kamar me wuya,


Afzaal in dai akan kudi ne nifa koma miye zan iya aikatawa kai dai fada mun kawai don Allah Na matsu Na ji karar credit alert,


Tashi Afzal yayi tare da kallon cikin idanun doc Bashir yace so nake a yau ba sai gobe ba ka KASHE MUN MATATA NADEEYA AUDU WAZIRI,


wani irin tsoro da jiri ne ya kama doc Bashir Wanda be ma san time in da ya mike ba,cike da rawar baki yace Afzaal kana da hankali kuwa Anya baka yi shaye shaye ba kafin ka shigo office ina,


Tsaki Afzaal ya ja sannan yace kana iyawa ko baka iyawa Na nemi wani,


Na shiga uku,wai kasan me kake fadi kuwa,kisan kai a hakan ma wai Matar ka Nadeeya audu waziri, wacece ita ma tukun Na,


Dariya ya so bai wa Afzaal ganin irin rudewar da yayi, sai ya dake yace yeah ka ji ni sarai Nadeeyar dai da ka sani yar gidan SEN Audu Waziri ita nake nufi, matata ce kuma so nake a yau ka kawo karshen numfashin ta ni kuma Na cika maka banki da kudi,


Shiru Bashir yayi yana me nazari shi kam be san a wani irin bala'i ya sanya kanshi ba,wani irin family ne haka me cike da dumbin secrets,for sure yasan Nadeeya matar aure ce Amman be dauka wannan bane mijin nata, shi sam be gane kan wanna family ba,at one hand uban ta mahaifi ke son a hauka Tata,and on the other hand wanna mutum da ke claiming mijin ta ke son a kashe ta,shi kam ya shiga uku, wannan samu baya fatan ya wuce shi, Amman in ya yarda ya ya kashe ta yace da Sen me,mil 50 ba karamin kudi bane shine abunda zuciyar shi ta raya mishi,


What do u say are u in or baka so Na nemi wani,goshi Bashir ya dafe yana me nazarin ya zaiyi wannan shine tsaka me wuya,


Cikin sanyin murya yace Amman Afzaal why keke so Na kashe ta,and baka tsoron SEN ya sani,


Dalili kake so ko kuma  mil 50 in ka,beside in har ka yarda za ka yi kar ka damu zan ji da komai, by the way mutuwar be fi mata sauki da irin rayuwar da take leaving yanzu ba ita da vegetable miye maraba, kawai ka kashe ta,ka ga taimakon ta ma za ka yi kayi easing pain inta,


Zufa Bashir ya goge yana me Jin tsoro can kasan zuciyar shi while ta saman ran kuma na hango mishi rayuwar dadin da zai yi a kasar waje da yammatan shi turawa,


Kayi shiru Bashir bani da time fa,kasan bature yace time is money za kayi ne ko aa,


Yawu Bashir ya hadiye sannan yace tura mun kudin yanzu zan yi yaushe kake son a kashe ta,


Dan ihun murna Afzal ya sanya sannan yace ko kaifa,gobe nake so a tashi da kukan mutuwar ta,sannan ina so ka sanya mutuwar tayi looking kamar normal mutuwa, kar ka bada kofar zargin mu,and no matter what ko ta  fashe kar ka kuskura ka ambaci suna Na,ka dai gane da kai Bashir ya amsa shi deep down yana ji abunda zai yi be dace ba, but yana bukatar kudin nan daga baya ya tuba,


A take Afzaal yayi mishi transfer in  55mil harda karin yin shiru in case in ta kwabe musu, tare da jaddada mishi kar ya sake a samu matsala, da haka suka rabu yana bashi tabbacin zai ji da komai a gurin SEN,


Har ya zo kofa sannan ya tsaya cak, dan dariya yayi sannan yace ka ji ni da hauka main abunda ya kawo ni ban yi ba,farar takarda ya zaro sannan yace nasan tana ji duk da tana cikin hauka kace da ita ni mijin ta Afzaal Na sake ta saki uku ga takardar ta,in an je lahira a nemi wani mijin domin bara ta mutu mun da jigilar aure Na akan ta ba,da gama fadin haka ya yarda takardar tare da ficewa daga office in yana Jin shi free kamar ya rabu da kaya ne,



Inda kasan anyi ruwa an dauke haka brain in docdoc Bashir da gangan jikin shi suka tsaya cak, shi kan shi bare iya misalta halin da yake ciki ba,tsoro ne aa miye ne nan take yaji cikin shi ta murda ya fada toilet in office in sai zawayi, yana yi yana tunanin taya zai fara kashe Nadeeya ta inda bara a gane shi bane, zuciyar shi ce ta raya mishi ya danna mata pillow kawai har sai ta daina numfashi shike nan ya fita y tafi wa ya sani, da wannan tunanin ya fito yana me Jin kwarin gwiwa, sai kace kan shi aka fara kisan kai, beside gaskiar Afzaal ne zai fi mata sauki da ta cigaba da irin rayuwar da take yi,haka ya yanke shawaran kashe wayar sa,don kar a Dame shi, zai jira zuwa cikin dare ya je ya danna mata pillow ya fito ya tafi abun shishi babu Wanda zai sani,


A haka ya zauna shi shi kadai kamar maye yana tunano irin pacakar da zai yi da kudin shi, Los Angeles zai fara zuwa ya dan huta kafin ya biya Abu Dhabi shima ya dan wataya,


Yana tunanen banzan shi har 12 na dare yayi, shi ba ga magriba ba balle isha,


 cikin sanda kamar munafuki ya isa dakin Nadeeyar,yana jin babu ko digon tsoro a ranshi, burin shishi ya cika aikin ko ya samu ya ci kudin shi lafiya,


A kwance ya tarar da ita Wanda da alamu bacci take yi dariya ya sanya sannan yace Alhamdulillah ke ba magana kike ba balle kiyi ihu asiri na ya tonu 


Pillow in da take kwance akwai akai ya zare Gare tare da cewa am so sorry fa zan kashe ki ba tare da kin min komai ba tsohon mijin ki ne Afzaal ya sanya yace na ce miki ya sake ki ga ma takardar ki nan kin ga sai ki mutu peacefully ya kare tare da aje mata takardar,sannan ya daura pillow in kan fuskan ta,


Forgive me if u can my dear, mil 55 ba karamin kudi bane yana kare hakan ya danna mata pillow in da karfi, inda Nadeeya dake bacci ta ji ta kasa numfashi ta hau mutsu mutsu,idanu ya zaro tare da dan sakin ihu tare da yarda pillow hannun sa sakamakon aluran da ya huda wuyan shi, a take ya zube a kasa sumamme......


A MUN AFUWA NA RASHIN POSTING DA BAN YI DA WURI BA, WWLHY WAYA KE BANI CIWON KAI TUN JIYA,


INA MATUKAR GODIA DA KAUNAR DA KUKE YI MUN, ALLAH UBANGIJI YA KARBI IBADUN MU SANNAN YA NUNA MANA BAYAN SALLAH DA RAI DA LAFIYA,


INA ME BARAN ADDUA A GUN KU, ALLAH YA BIYA MUN BUKATU NA NA ALKHAIRI SANNAN AKWAI MAHAIFIYAR AMINIYATA DA TA RASU GABANIN AZUMIN NAN KU TAIMAKA KU SANYA TAA CIKIN ADDU'OIN KU,


AKWAI MAHAIFIN KAWATA KUMA DAYA DAGA CIKIN GROUP MEMBERS INA RASUWA SHEKARAN JIYA SHIMA KU SANYA SHI A ADDU'A,


ALLAH YAYI RAHMA YA KUMA JI KAN DUK WANDA SUKA RIGA MU GIDAN GASKIA,IN NA MU YA ZO YA SANYA MU CIKA DA IMANI,


INA YI WA KOWA FATAN ALKHAIRI, ALLAH KUMA YA SA YANDA ZA'A DAUKI AZUMI DA MU MUNA MASU RAI DA LAFIYA YA SANYA A GAMA DA MU HAKA, UBANGIJI YA BIYA WA KOWA BUKATUN SU NA ALKHAIRI,


SAI KUMA BAYAN SALLAH IN ME KOWA ME KOMAI YA BAR MU A RAYE, ALLAH YA BAMU IKON AIKATA AIKIN ALKHAIRI A CIKIN WANNAN KWANA 30 IN.

😭😔UBANE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY 

                 BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


        Assalam 

           Masoyan 

               Asali❤💖


Before i begin to say anything, before wani ya riga ni, i want to be d first to wish beautiful pure souls like all of u guys, 


Ina so in fara da gode wa Ubangijin mu, mahallicin mu da ya bamu aran tsahon rai da lafiya har muka shiga wannan wata me tarin dumbin falala lfy, cikin aminci da yardar sa lfy, kuma ya nuna mana fitan sa lfy, wannan ba karamin arziki bane, duk da cewa Azumin Ramadanan bana ya zo ta daban kasancewar tsadar rayuwa da zafin da aka yi ta fama da Shi, amman duk da haka Alhamdulilah za muce, da har Allah ya nuna mana ranar Karamar Sallah, 


What a happy year har yanzu muna raye  Alhamdulilah, Allah muna kara mika godia a gare ka da ka kara ba mu aron rai har muka yi Azumin watan Ramadanan muna masu koshin lfy, kuma muka ga fitan ta lfy, ya Allah ba dan mu ba muna rokon ka ka karbi ibadun mu na gari, ka yafe mana kurakuran mu, ka sanya muna daga cikin yantatatatun bayi da aka yanta cikin watan, 


Gaskia I have to admit it that I have missed u guys a lot, in nace a lot i really mean irin sosai in nan fah, kamar yanda nima nasan kun yi missing ina together with Nameer &Nadeeyah 😋 right, but maganar gaskia wa kuka fi missing Ni ce koh Su Nameer  amman gaskia ya kama ta ya zama ni(lol) 


Kar na cika ku da surutu, ya kuke masoyana, ya ibada, ya aiyuka, ya rayuwa kwana da yawa, one whole month ba mu ji juna ba, Allah i missed u fah ji nai kamar nai kuka 😥😥😥, 


But Alhamdulilah i am back, and ina fatan duk kuna cikin koshin lfy, 


Happy Eid Al Fitir, 


To All my lovelies i love u guys, ubangiji ya sa mun yi karbabbiya sannan ya Kara mana lafiya da nisan kwana,Wanda suka Riga mu gidan gaskia ya gafarta musu,ya Sanya sun huta in namu ya zo ya kyautata karshen mu,


Thanks a lot for ur support guys, i really do appriete it, and I love each one of u with pure one heart, 


 ❤❤❤💖💖


.......


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin san ba comment bane zai Shigo da ke to don Allah Kar ma ki Shigo na gode,haka zalika Maza should stay away from my group don ki sun shiga Zan cire mutun, group in Mata ne xallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via:


  08100046388


............

            Page twenty-one


***********


Faduwar da doctor Bashir yayi ne ya bayyana Nameer dake tsaye a bayan Shi da sirinjin alura a hannun Shi,


Wani irin kallo me cike da tsana yake bin doc Bashir da Shi,ya kasa yarda wai Shi Bashir ya so fooling,so all those tears da rokon duk pretence ne, wow Dan Adam me wuyan gane hali,Banda son zuciya har akwai amount in da za a biya Ka Ka dauki ran dan Adam da shi ko kunya babu a cikin idanun sa,yo in ya kashe Nadeeya ya je gaban Allah aka taimabe Shi me tayi mishi ya dau ranta miye ne amsan da zai bada,tunda a iya sannin Shi bata taba cutar sa ba,ko ta taba ba Shi ya bashi daman daukan ran ta ba,


Har yanzu he is still  shocked da maganganun da ya ji a suka yi dazu a office in Shi,kallon Nadeeyah yayi da ke kwance,wani irin tausayin ta ne ya kama Shi Wanda be san time in da tears suka zubo mishi ba,


Wato daxu Allah ne ya aiko Shi office in Doc Bashir ya je domin yi mishi magana game da case in Nadeeya,kamar zai shiga sai ya ji magana abunda be taba ba evesdrop ya tsinci Kan Shi da labewa ya ji me suke Fadi,ashe taimako ke Kiran Shi,


In sha Allah yau ce ranar karshen wahalar ki zan taimake ki daga hannun wayan nan mugayen Wanda babu Allah ko kadan a cikin ran su,


Tsalleke Doc Bashir yayi da yake yashe magashiyan a kasa,Wanda garin haka har yatsun Shi ya murje,saidai sabida aluran baccin da yayi mishi ya Sanya be ji zafin ba,


Gaban gadon ya je tare da tsungunawa ya zuba Mata idanu, bacci take hankalin ta kwance,sai ya ji ta kuma bashi tausayi,


Cikin soft voice yace I don't know if wat am about to do is the right thing ko aa,I just don't know what to think or who to trust kuma,how on earth your own husband is willing to pay huge amount of money don kawai a kashe ki,


You got an innocent face dake nuna bara ki iya hurting ko da ant ba balle Dan mutun,saidai I don't know why ake neman rayuwar ki,


I don't know why Nadeeyah ji nake kawai ya zame mun dole na taimake ki, although ban san komai game da ke ba,but ba zan iya barin a cutar da ke ba,ya kare yana girgiza Kai, tare da mikewa,


Astaghafurillah yayi a cikin ranshi domin he is about to carry her,he got no option Banda ya dauke ta daga wannan asibitin kafin mugayen nan su kashe ta,


Daukan ta yayi cak kamar baby bayan ya cire Mata chains in hannun ta,farin takartar sakin ta ya dauka tare da sanyawa a aljihun Shi sannan suka fito daga cikin dakin Yana me jin kamar ya rufe doc Bashir da mugun duka,


Allah ya rufa mishi asiri dare ne so ba mutane a haraban asibitin,addua yayi ta yi har ya Isa motar da,a bayan mota ya shimfida ta sannan ya shiga ya ja sai gida,


********Sister Kareematu


Tsaki kam ta ja Shi ya Kai cikin kwando ta cika tayi tsam kamar ta fashe tsaban bakin ciki,ji take kamar ta kashe doc Bashir dan wahala tun dazu take ta Kiran Shi yaki dauka,ya Sanya ta ta shiryo ta zo hostel Amman yaki zuwa, Kusan hours in ta biyu,wayar ma tun tana Kira tana samu har ya daina shiga,


Tsaki ta kuma ja a bayyane sannan tace wannan akwai dan iska daman ya san be zuwa ya Sanya ni Shaye shayen magun gunan Mata to wai nayi yaya,


Mikewa tayi tana me hararan kofar dakin duk mostin da ta ji dauka take Shi be,wlhy Bashir ya cika Dan rainin wayo,don ya ga ma ina Kula Shi ne ya sanya yake mun Bura uban da ya ga dama,


Tsaki ta kuma ja tare da daukan jakan ta domin babu amfanin ta cigaba da Zama a cikin dakin ita kadai,


Fitowa tayi tana tafe tana kare wa Bashir zagi tare da alkwarin sai ta ci uban Shi muddum yayi Mata magana gobe,


Key in ta watsa musu suna tambayan madam lafiya,ko kallon su bata yi ba ta fito burin ta kawai ta nemi Wanda zai dan rage Mata zafi muddum ta kwana haka toh za a samu matsala,toh wa ma za ta samu,duk abokan shashancin nata ta sanar musu yau tana gida throughout Kar wanda ya Kira ta,domin haka Bashir ya sanya ta cewa yayi yau akwai till down Shi da ita(wa'iyazubillah)


Tafiya take tana hade hanya a harabar hotel in Allah Allah take ta Isa motar ta,bata da option da ya wuce ta koma gida gurin Abdul,buguwar da tayi ne ya sanya ta yin Baya zata fadi da sauri Alhaji Muhammad Jidda ya taro ta,


Jin ta a kirjin mutun ya Sanya ta Bude Ido cike da tsiwa,saidai arba da tayi da fari kal in mutun tsaye a kanta ya sanya ta shan Jinin jikin ta,wato ba karamin kwarjini yayi Mata ba wanda ya sanya ta saurin zare idanu daga kallon Shi,


Na gode ta samu ta Fadi da kyar domin daga kallo daya wannan magidan cin ya saye zuciyar ya kuma tafi da imanin ta,


Dariya ya Dan yi Wanda ya bayyana farar hakorin makkan da ke manne a bakin Shi,sannan yace haba babu komai ai yarinya me kyau,


Jin abunda ya Fadi ne ya sanya ta Kara wani gyara tsayuwa tare da murmusawa tace Allah Alhaji


Shima dariyar yayi tare da shafa tumbin Shi Wanda ke nuna kudi sun zauna sannan yace kwarai kuwa ya aka yi ne Yan mata muna shigowa kina fita,


Da sauri tace AA daman mantuwa nayi zani daukowa a mota ba tafiya xan yi ba,


Dadi ya ji a ranshi ganin cikin sauki ya samu kan yar banza,toh ya za mu je ne ki taya ni hiran dare ya kare yana kashe Mata Ido daya,


Da sauri tace ai girman ka ne Alhaji mu je kawai na ma fasa dauko abun,tayi gaba tana me juya zaunannan mazaunan ta,murna fal cikin ta wannan Shi Ake Kira farin dare,daga ganin kyakkyawan alhajin nan me kama da larabawa (dake shuwa ne),naira gare Shi,irin su kuma ba sanin zafin kudin suka yi ba,da haka suka shige ya karbi makullin daki ta bi bayan Shi zuciyar ta fal za ta cafki Yan kudade ta mance da Amanar auran da ke Kan ta Wanda za ta ci ta mance uwa ce ita akwai Amanar Yara Akan ta,ta mance kimar ta na ya mace idanun ta sun rufe,bata son mutun ba bata san daga ina yake ba miye intentions in shi ta mika kai buri ya hau,


(Ubangiji Ka tsare mana Imani mutunci da lafiyar mu,Allah Ka Raba mu da son abun duniya ya Allah Ka kare mu daga San zuciya,masu hali irin na Kareematu Allah ubangiji ya shirya Ku in masu shiryuwa ne Ku),


**********Doc Nameer


A hankali ya dauko ta bayan yayi parking har lokacin bacci take yi,Kai tsaye dakin baccin sa ya wuce da ita tare da shimfide ta akan gado,


Zama yayi tare da zuba Mata idanu,Yana me tunanin da be je ya ji me su Bashir ke shirya wa ba fa,kila da iyanzu wani zancen Ake daban,


Tabbas be taba ganin mugun mutun me son abun duniya irin Bashir ba,kana likita a hada Baki da Kai a yi kokarin kisan Kai,


Shi kuma Afzaal sam brain in Shi ya kasa yarda wai Shi mijin Nadeeya ne,wai daman tana da aure,toh me tayi mishi da zafi da zai biya don a kashe ta,


Wai shin ma ina Mahaifiyar ta take,and a yanda ya ji mahaifin ta na kaunan ta Yana ina har sirikin Shi ke son kashe mishi yarinya,


Kwata kwata brain in Shi ya kulle ya kasa sanin amsoshin tambayoyin da yake da su game da ita,


Ganin tunanin be da amfani ya Sanya Shi Mike wa,sai kuma zuciyar Shi ta tambaye Shi,wait Nameer da Ka dauko ta Ka kawo ta gidan ka wat about her family,


Numfashi ya sauke,maganar gaskia Shi be san wanda zai yarda da Shi kuma,haka kawai ya ke Jin yarinyar tana cikin danger,and haka kawai yake jin bazai iya yarda da kowa ba kuma,


Wat of her Father zuciyar Shi ta kuma tambayan Shi, actually har Shi ban yarda da shi ba for Allah knows why,domin ya Dade Yana tunanan nan akan Shi,why be tsaya kai da fata gurin samun lafiyar Nadeeyar ba,beside tun Randa ya ga injections in da Bashir ke Dura wa Nadeeya jikin Shi yayi sanyi game da lamuran Sen,toh daman can da lafiyar ta ya Sanya aka kawo ta gidan mahaukata,ko kuwa ta Dan yi haukan kadan shine Bashir ke dada birkita Mata brain, wannan duk tambayoyin ke ringing a head in Shi,


Tsaki ya ja tare da dafe goshi,har ga Allah be san ko daidai yayi ko laifi ba da ya dauke ta daga hospital in nan,shi dai kawai ya bi shawarar zuciyar Shi ne,domin tunda ya ji su Bashir na Shirin kashe ta ya kasa zaune balle tsaye,karshe ya yanke shawarar yi wa Bashir aluran bacci ya dauke ita Nadeeyar,


Wat if wani ya gan ka shine wani tambayan da zuciyar ta Shi ta masa,Nameer kasan aka gane kama Ka za ayi da laifin kidnapping,tunda daukan ta kayi ba tare da yardar ta ba,


Mikewa yayi tare da sauke ajiyar zuciya ya san tabbas haka ne toh Amman Shi a ganin Shi taimakon ta yayi,ganin in ya zauna tunani ne kawai zai cika masa kai ya Sanya Shi juyawa don shiga toilet ya watsa ruwa ko ya ji sanyi a jikin Shi da zuciyar sa,


Jallabiya ya dauka tare da quranin Shi da laptop in Shi ya ja Mata bargo bayan ya rage Mata sanyin AC in dakin sannan ya fito tare da rufe kofar,a palor ya Aje kayan tare da fadawa dayan dakin nan yayi wanka ya shirya sannan ya zo ya tada nafila,ya Dade Yana adduo'i ,kafin ya shafa ya shiga karatun Alqurani me girma,Saida ya ji ya fara jin bacci sannan ya aje ya kwana,a nan Kan kujera,


Bacci yayi hankalin sa kwance babu wani tsoro ko fargaba a ranshi,ji yake Yana daidai da kowa a cikin asibitin like he is ready wa koma miye zai faru,abunda ya sani dai shine be bayar da Nadeeya har sai Allah yayi ta warke,


Ba Shi ya farka ba sai asuba,Saida ya leka ya ga tana lafiya sannan yayi alola ya tada sallah,a nan kan sallayan ya maida bacci kafin alarm in Shi ta tada Shi,



Around 7:00 ya ji ana buga masa kofa Wanda karar bugun ne ya farkar da Shi da sallati a bakin Shi,ya mike yana me karanto adduar tashi daga bacci,wayar Shi ya dauka tare da ganin time,


Ya salam Ashe bacci Nayi sosai,time ya tafi,be ma yi wanka ba break balle Shirin zuwa aiki,Jin ana cigaba da buga gate in ne ya sanya Shi mikewa Yana me mamakin Waye haka zai zo mishi gida da sassafiyar Allah.....


Ayi mun afuwa na so ya fi haka wlhy Allah be yi ba🥹,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi da kuma fatan ayi shagalin sallah lafiya.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)



.......


My group link


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin San ba sharhi bane zai Shigo dake to don Allah na hutar ki Kar kiyi joining,haka zalika Maza stay far away from my group domin na Mata ne xallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

  

    08100046388


..........

         Page twenty-two


***********


Saida ya fito harabar gidan ne Jin an ki tsayawa da bugun kofar ya Sanya gaban Shi faduwa,Kar dai an gano Shi ya dauko Nadeeya,ji yake kamar Kar ya ma Bude kofar coz Allah ya gani be shirya wani drama da safiyar Allahn nan ba,


Aro jarumta yayi tare da nufan gate in yace Waye,Jin muryan Habeeb ne ya amsa da cewa Bude Mr handsome ni ne,ya Sanya shi sakin ajiyar zuciya,tare da Bude kofar,


Da kallo Habeeb ya bishi sannan yace dan wulakanci sai yanzu Ka ga daman Bude mun ke nan tun dazu nake tsaye,


Tsaki Nameer ya ja sannan yace bara Ka gane ba wlhy bacci ne ya dauke me,ko wanka fa ban yi ba,


Kallon Shi Habeeb yayi cike da kulawa sannan yace are u sure lfy kake kuwa doc,


Murmushi Nameer yayi sannan yace yeah gajiya ce kawai,by the way lafiya na gan Ka da sassafiyar nan,


Wlhy mafarkin Ka nayi wai wani mummunan Abu ya faru da kai har ta Kai Ka ga jinya ya sanya hankali na ya kasa kwanciya,ina yin sadaka nace sai dai na zo na ga lafiyar Ka,


Murmushi Nameer yayi yace Kai Habeeb shine Ka fito sassafen nan,AI mafarki ba gaskia bane Banda abunka,


Wlhy Nameer I was so scared ne na kasa samun peace of mind Saida na zo na gan Ka you are safe and sound Alhamdulilah toh,matsa mun na shiga na sha ruwa na Jira kayi wankan mu wuce hospital,


Har Nameer na kokarin matsawa sai ya tuno akwai Nadeeya a cikin gidan fa,da sauri yace AI kayi tafiyar Ka kawai babu ruwa a gidan nan,


Da kallon tuhuma Habeeb ke bin Shi da Shi sannan yace wani irin ba ruwa,yau lafiyar Ka kuwa to matsa na fasa shan ruwan mu shiga Ka samu Ka shirya mu wuce Kar muyi late,


Kai doctor Nameer ya sosa sannan yace kawai Ka je abun Ka zan biyo bayan Ka akwai abunda nake son na gama tukun na,


Mamaki ne ya kama doc Habeeb da Jin abunda abokin nashi yace,ganin Nameer in na kokarin komawa cikin ne ya sanya Shi ce what are you hiding ne,


Me,me zan boye kawai dai I don't want to waste your time ne just go I will soon meet you a asibitin,thank you so much for the concern bye bye,da haka ya rufe kofar abun Shi,tare da sauke ajiyar zuciya ya koma cikin gidan,


Da Ido Bude Habeeb ke bin kofar gate in,anya lafiyar Nameer kuwa,kafadu ya dage tare da shige wa motar Shi tare da fadin koma miye ne in tayi tsami za mu ji,



Toilet Kai tsaye ya fada a gurguje yayi wanka tare da shiryawa cikin kananun Kaya Wanda suka amshi jikin Shi,Saida ya gyara gashin kanshi ya feshe jikin Shi da designers in turaruka masu dadin kamshi, sannan ya fito ya shiga Kitchen,da sauri ya hada tea tare da saisatawa inda bare Kona wa mutum Baki ba,sannan ya fito da ya koma dakin da Nadeeya ke kwance,


Hamdala yayi ganin idanun ta a Bude suke,alamun ta tashi daga baccin ke nan,


Murmushi ya Mata sannan yace morning my naughty naughty girl,an tashi ke nan oya time for breakfast,ya kare tare da Aje tray in da cup in ke Kai a bedside table in dakin,har ya zauna ya mike Dan dariya yayi sannan yace sorry my bad Ashe ba ayi brush ba Zan Baki abinci,daga haka ya shige toilet in Shi,Sabon toothbrush ya dauko tare da matsa toothpaste a jiki sannan ya dauko bowl da soft towel ya fito,


Cike da tausayin ta ya dago ta Saidai sam jikin nata is not responding kamar wata vegetable,a haka dai da dabara da komai ya samu ya dan jingina ta a jikin Shi tare da support in jikin Shi da na pillow in da ya jingina Mata ya Fara wanke Mata baki a nutse a kuma hankali yanda bare ji Mata ciwo ba,


Towel in ya manna Mata a wuya sabida inda ruwan ke zuba daga bakin nata,while yayi using dayan gurin tsomawa a ruwa ya goge Mata ciki da wajen bakin,tunda ba iya zubo da ruwan za ta yi ba,


A haka dai ya samu suka Gama brush in sannan ya maida ta kwance ya mike tare da xubda ruwan,ya kuma Ibo sabo,


A nan kwance ya samu ya daura Mata alula,duk da ya san ba iya sallahn za tayi ba,sanna ya zauna ya shiga bata tea in a hankali da karamin spoon,inda ta shiga sha Sosai hakan ya tabbatar mishi da yunwa a jikin ta, Saida ya ga ta koshi sannan ya goge Mata baki tare da maida ta kwance,


Sannan ya shiga tattare wajen,Yana tunanin ya zai yi ba zai yu ya Kula da Nadeeya ita kadai ba, domin ba muharammar sa bace,dole tana bukatan wanka in tayi fitsari a gyara ta Wanda Shi kuma ba zai iya Mata ba,ya Zama dole ya samu Wanda za ta taya Shi Kula da ita Amman kafin nan Bari ya samu ya tafi hospital don yau kam ya Gama yin latti,da haka yayi Maza Maza ya gama shiryawa tare da Kara duba Nadeeyar Yana Jin kamar Kar ya tafi ya bar,ta Kar ta bukaci wani abun ba kowa Kusan ta, duk sai ya ji wani iri,



**********Doc Bashir


Kanshi ya rike da yake ji Yana barazanar fice masa sakamakon farkawar firgicin da yayi,a hankali ya shiga Bude idanun Shi da suke masa dishi dishi,da kyar ya Bude su tare da rike kanshi da hannu biyu Yana kokarin tuna me ya faru da Shi,


In har zai tuna dai ya Shigo cikin dakin nan domin kashe Nadeeya don har pillow ya dauka ya daura a fuskan ta Saidai daga time in be tuna komai ba ya dai ji sharp pain a wuyan Shi Wanda ya Sanya Shi sakin pillow in,


Idanu ya zaro sosai tare da saurin mikewa tsaye 

Nadeeya shine kalman da ya Fadi a tsorace kafin ya shiga bin dakin da kallo,


Tsoro ne ya kama Shi ganin babu Nadeeya babu alamun ta,Na shiga uku ni Basheer Nadeeya ya kwala mata Kira Yana sa ran Jin ta amsa😂😂,


Tsoro be Gama kama Shi ba Saida ya leka ko ina ya ga dai babu ita babu alamun ta,AI wani irin jiri ne ya dibe Shi a take ya zube a kasa don Ji yake kafafuwan Shi sam sun gaza daukan Shi,


Da hannu biyu ya kama Kai tare da kwala wani irin Ihu Fadi yake na shiga uku na lalace shike nan yau karshe na ya zo ina kike Nadeeya kuka yake hawaye biyu biyu Yana sumbatu,


Jin ihun Shi ne ya sanya sauran staff's in saurin  shigowa,ganin Shi a durkushe ya Sanya doctor Jameel nufan Shi tare da dafa Shi Yana tambayan lafiya doctor,


Da sauri ya dago idanun Shi jige da hawaye hanci duk majina,ya samu ya mike da kyar Yana Jin jiri,Amman gwamma jirin nan da abunda zai fuskanta a gurin Sen,


Cikin muryan kuka yace Jameel Waye ya Shigo dakin nan ya dauki Nadeeya,


Cike da mamaki suke kallon sa,kamar ya waya Shigo ya dauki Nadeeya Waye ma Nadeeya doc Haneefa tace tana hararan Shi,


Yarinyar Sen Rilwanu da na killace a cikin dakin nan babu ita Waye ya dauke ta cikin Ku,


Tsaki Haneefar tayi sannan tace Ka ji mun maganar banza Kai ma kace Wanda Ka killece ni tunda nake ban taba ganin fuskan yarinyar ba Ka nanike ta a daki kullum ko waje bata fitowa Shan iska,beside duk asibitin nan daga Kai dai Kareematu na ga ke shiga cikin gurin ta,domin na ga harda pin in munafurci a kofar dakin nata,toh idan ma dauke ta aka yi saidai in ko Kai ko Kareematu ya Ku yaku kuka yi abun Ku za ka zo kana wani ihu da kuka kana neman daga mana hankali,ta kare tana hararan sa,


Ke kika tsaya Kula Shi Haneefa,Shi daman haka yake Baya son Zaman lafiya da uban wa yace Ka boye ta daki Ka Hana kowa ganin ta,tunda Ka ga uban ta na da zagi da maiko nan kace da mu kowa yayi staying away from her Kai za Ka yi handling case in ta so yanzu am very sure wannan in ma you can handle it,Mr handler ,doc jabir ya kare yana Dariyan shakiyan ci,


Haba Ku kuwa Ku Bari mana,abun nan fa duk ya shafe mu kun Riga kun San Waye uban ta wlhy batan yarinyar nan baraxana ne ga mu gaba daya,


Allah sauwaka Jameel wa dai Shi wlhy be shafe ni ba,tunda tunda aka kawo ta daga Shi sai Kareematu ke shiga gurin ta bara a daura mun gawan da ba ni na kashe ba,in za su bazama neman ta ma gwara sun fara,kafin uban ta ya samu labari,in kana iya taya Shi toh Allah ya bada lada,ni dai Ka ga fita na ina da abun yi AI daman Kuda gurin kwadayi yake mutuwa,daga haka ta Sanya Kai za ta fice Jira ni Haneefa mu hada hanya domin ban ga amfanin Zama na a nan ba,



A nan kasa Bashir ya kwanta Yana kuka kamar karamin yaro,sai yanzu ya ga wautan Shi da be barin kowa ya rabi Nadeeya daga Shi sai Kareematu gashi yanzu babu Wanda ya Isa yayi blaming,wa ma ya Isa ya daura wa laifi bayan duk haushin shi suke ji gani suke ya kannenade komai ya Hana kowa dangwalan arziki a jikin Sen,


Ka kwantar da hankalin Ka Bashir in sha Allah za a same ta mu samu mu je gurin securities ko sun ga wani Abu,


Cikin shesheka yace haba Jameel a taya kake tunanin hankali na zai kwanta wlhy yanzu haka ban jin zan iya mike wa don Allah taimake ni Ka daura mun drip ko zan dan samu sauki,


Ba musu kuwa Jameel in ya ja Shi zuwa gadon Nadeeyan ya kwantar da Shi tare da daura masa ruwan,


Idanu ya lumshe zuciyar Shi na tsanan ta bugawa domin ya san tabbas Sen ya ji maganar nan ya mutu ya lalace,wata zuciyar ce ta rayo masa what of Afzaal in ya ji Nadeeya ta bata bayan Ka karbi makudan kudadan Shi don kashe ta me zaka ce masa,


AI sai ya fashe da kuka me karfi,na shiga uku na lalace wayyo ni,ya Fadi Yana daura hannu a Kai,


Haba Bashir miye haka sai kace yaro karami behave yourself mana,wlhy Jameel bara Ka taba gane halin da nake ciki ba don Allah cire drip in nan Ka rike ni mu je gurin securities in nan yarinyar nan ta bata wlhy asiri na ya tonu,ya kare Yana kokarin mikewa,


AA Ka dai yi hakuri ruwan ya Gama shiga jikin Ka tukun na,zai taimaka maka sosai,


Jameel Ka cire mun ko ni na cire Shi da kai na,amfanin me zai mun bayan na San ni mutuwa ta ta Kusa,ya kare Yana hawaye ba karya ya san tabbas in ba a ga yarinyar nan ba toh Sen sai ya kashe Shi,


Ba musu kuwa Jameel ya cire masa drip in,inda ya bashi daman tashi Yana Jin jiri da komai Amman haka ya daure suka fitowa,kallo daya za Ka masa Ka gane Yana cikin tashin hankali domin lokaci daya har ya fada,


Gurin securities in suka je tambayan duniya ya musu Amman sun ce sam su Basu ga wani bakon mota ya fita da kowa ba,ba yanda Bashir be yi ba Amman be samu komai ba karshe kuka ya Sanya tare da rufe su da duka Yana zagin su wai Basu iya aiki ba,da kyar Jameel ya ja Shi suka koma cikin asibitin,


Haka dai kafin kace me labari ya karade cikin asibiti an nemi yar gidan Sen Rilwanu Audu Waziri an Rasa ta,duban duniya sun yi cikin clinic in ga Amman sama da kasa an rasa Nadeeya,Banda kuka babu abunda Doc Bashir ke yi,sam ya Rasa gane garin yaya yarinyar nan ta bata,ita da ba tashi take ba balle ace guduwa tayi,dole shigowa aka yi aka dauke ta to Waye,a iya sannin Shi dai daga Shi sai Kareematu ne suka san pin in shiga dakin nata,toh Waye haka yake neman jawo mishi mutuwa,


Ana haka doctor Nameer ya iso asibitin,ganin inda duk aka yi carko carko ya Sanya Shi tambayan Habeeb lafiya kuwa,


Wlhy Nameer Bari kawai yarinyar isolated room in nan ne aka neme ta aka Rasa, subhanallahi Kar dai Nadeeya yar gidan Sen,


Wlhy Nameer ita fa,an wayi gari an rasa ta, subhanallahi toh tana ina,


Waya sani dazu dai da na Shigo na ji Bashir na cewa wai an Rasa ta ,toh kasan ance fadan da babu ruwan Ka dadin kallo gare shi daman can ya Hana kowa zuwa gurin ta to Ka ga Wanda ya Ibo da zafi bakin Shi sai yayi aikin neman ta,kowa madallah yake masa,


Ikon Allah toh wai taya za a ce babu ita ta bata,kuma har securities an tamabya ,wlhy dazu ma da zagi suka rabu da su wai su Basu ga komai ba,


Murmushi Nameer yayi sannan yace Abu Sam be yi dadi ba gaskia toh ubangiji ya bayyana ta Bari na je gurin Bashir in,


Ameen fa AI da kyar Ka gane Kan Shi domin sai Suma yake Yana farfadowa tun dazu,shege Ashe dai mara kunyar karya ne Yana tsoron zuwa prison,dariya Nameer yayi sannan yace Kai dai Baka da dama wlhy ni dai Bari na je in na dawo zan same Ka a office in Ka,da haka ya wuce office in Doc Bashir zuciyar Shi fes babu Wanda ya ganshi yana fita da ita jiya Ashe.....


Ayi mun afuwa na jina shiru jiya hakan ya faru ne sabida dalili🙏🏻,



Ina yi wa kowa fatan Alkhairi na gode sosai da kulawan Ku gare ni.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY 

                  BY

NERNAH MARYAM 

(MARTEYBEE)


........


My group link 


https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK


In har kin san ba sharhi da karanta book ina ne zai Shigo da ke ba toh don Allah yi Zaman ki ba sai kin yi joining ba,haka zalika Maza stay away from my group domin wannan group na Mata ne xallah ko Ka shiga Zan hidda ka🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

   

       08100046388


..........

         Page twenty- three


************


A kwance ya samu doc Bashir ana yi mashi Karin ruwa kallo daya zaka masa ya Baka tausayi,inda ya kuma duhu har Ramar dole yayi na lokaci daya,doc Jameel ke gefan Shi Yana me bashi Baki Kan ya dau komai a sannu za a gan ta in sha Allah domin daga fargawar Shi zuwa yanzu ya Suma ya Kai sau 8🤣🤣Ni ko nace madallah AI daman kwadayi aka ce mabudin wahala,


Da sallama doc Nameer ya Shigo inda doc Jameel ya amsa sallaman tare da Mika mishi hannu Yana fadin doc sai yanzu,


Hannun shima ya Mika suka yi musabaha sannan yace wlhy fa doc yau makara nayi,Ayya ai daman jiki da jini dole wataran a gaji, hope kana lfy,


Kujera ya ja ya zauna sannan yace Alhamdulilah wlhy ya aikin, Alhamdulilah fa,toh madallah,


Da kallon tsana ya bi doc Bashir ganin yanda ya ficiccike daga jiya da dare zuwa yau sai abun ya so bashi dariya,Amman sai ya daure yace,


Doc Bashir Ashe abunda ya faru ke nan,wlhy yanzu shigowa ta nake Jin wannan munannan labarin garin yaya haka ta faru,


Da kyar ya iya Bude idanu ya kalli Nameer in sai ya yi shaar da Shi,nan take tausayin kanshi ya kama Shi sai kwalla ya kuma kallan doc Jameel ya ga sai danna waya yake abun Shi,kuka ce ta kwufce masa,yayi danasanin Sanya kanshi a matsala kila da be bi son zuciya ba da shima Yana rayuwar Shi cikin Jin dadi da annashuwa,yanzu da wani yare zai sanar da Sen Kan cewa an sace yarinyar sa,ai ba ma zai kama zancan ba,


Doc kayi shiru yana maka magana,Jameel yace Yana mikewa,


Ajiyar zuciya me nauyi ya sauke sannan yace wlhy Nameer ni Kai na ban san garin ya haka ta faru ba,abunda Zan iya tunawa dai na shiga in duba ta ci abinci ko as da daddare sannan na bata maganin dare ganin Kareematu bata nan,shine wani makiyin Annabin Wanda babu Allah a zuciyar Shi ya soka mun alura suka dauke ta,


Subhanallahi toh garin ya su Waye su Ka san su ko Ka ga yawan su,a garin ya ma suka shiga dakin na ga da pin a jiki,


Wani zufa ne ya kuma karyo mashi domin tabbas babu Wanda zai yarda ba Shi ya sace Nadeeya ba tunda duk asibitin babu Wanda ya san pin in sai Shi kadai da Kareematu,ita kuma throughout jiya bata nan,ya Zama dole Shi za a tuhuma,na shiga uku shine abunda yace tare da matso kwalla,


Nameer dariya ce fal cikin Shi, farinciki kamar ya mutu,ba karamin dadin ganin Bashir a cikin tashin hankali yayi ba,AI daman duk wanda ya hau motar kwadayi tashan wulakanci yake sauka,


Cikin sanyin murya yace wlhy Doc Bani na sace yarinyar nan ba,


Goshi Nameer ya shafa sannan yace in har mu mun yarda da Kai doctor mahaifin ta da sauran alumma fa,kasan ko kwana dubu za Ka yi kana fada wa duniya Baka da hannu batan yarinyar nan babu me yarda domin wannan magana ce ma da hankali ba zai dauka ba,yarinyar nan hannun Ka take hasalima babu Wanda kake Bari ya zo ko kusa da ita,daga Kai sai Kareematu ke Kula da ita,to kuwa Ka ga duk wani alamomin zargi suna Kan Ka ne da ita,don haka Ka kara tunani da kyau,


Kuka Bashir yake yi hawaye biyu biyu Yana matukar tausayin kanshi,wallahi tallahi doc Ku yarda da ni na rantse ban san komai game da batan yarinyar nan ba,na san ni kadai da Kareematu muka san pin in shiga dakin ta Amman wlhy ni babu inda na dauke ta na Kai ta,kila aljanu ne suka sace ta tunda yarinyar ma ba iya motsi take da jikin ta ba,tunda na ji an ce aljanu na iya dauke mutane😂😂,


Dariya ne ya so kama doc Nameer Jin furucin Bashir,tabbas ya yarda doc Bashir na da matukar tsoro,Amman madallahn sa ai tunda junin Shi son zuciya da duniya ne,


Hmmm ni duk ba ma haka na,Ka dai san bare yu yarinyar Sen ta bata baida masaniya ko,ko Ka sanar masa ne,


Da sauri Bashir ya mike cike da kidima yace don girman Allah na roge Ka Nameer Kar Wanda ya sanar da mahaifin yarinyar nan,na rantse da girman Allah wlhy kashe ni zai yi har lahira,


AA Doc wannan Sam ba shawara me kyau bane,ya za a yi yar sa a nema a rasa bayan ya damka Amanar ta a hannun Ka sannan ace Kar a Bari ya sani,AI hakan be yi ba ko da dabbar gidan Shi kake kiwo ya bace dole ya sani balle Dan mutun,don haka Ka kwantar da hankalin ka a sanar masa kila ya san inda take tunda yana da connection,don haka ina so Ka Bani no sa in Kira in sanar masa halin da Ake ciki,


Aa Nameer Ka duba girman Allah da soyayyar da kake wa mahaifan Ka,Kar ka Kira Sen wlhy baka san Waye shi na rantse da Allah ba karamin so yake wa Nadeeya ba,in har ya ji babu ita toh wlhy rayuwa ta ta zo karshe,


Dariya Nameer yayi sanann yace Ka san da haka kake kokarin kashe ta a cikin ranshi while a fili kuma cewa yayi duk dai boye boyen nan babu inda zai Kai ka,abune ya riga da ya faru ba za mu iya canzawa ba,sannan Shirun amfanin me zai yi ba gwara a sanar masa ba let him do his worst in har za a same ta,AI lafiyar ta da halin da take ciki yanzu ne abun dubawa,so be a man babu abunda ya Isa ya maka abunda Allah be ma ba,so Ka kwantar da hankalin ka ka bani no in sa,


Aa Nameer don girman Allah Ka bari mu gani zuwa gobe in ba a ganta ba a sanar mashi wlhy tallahi Baka san Sen ba na rantse da Allah bare taba raga mun ba ya kare yana kuka,


Doc ke nan kana ganin za a same ta ne,Nadeeya fa bata cikin asibitin nan don da tana nan da an ganta tun tun,Ka dai Bari a sanar in,


Na roke ka Nameer Ka rufa mun asiri don kaunar Ka da Manzon Allah,zan shiga in fita in sha Allah za a samo ta,akwai wani malami da ke kan tudu naji Yana bada taimako Zan je ya bincika mun inda yarinyar nan take,


Nameer can't hold it Saida yayi dariya,kafin ya rike bakin Shi,sannan ya mike yace toh shike nan as you wish baran sanar masa ba Allah ya Baka lafiya, ubangiji kuma ya sa a ganta din,da ameen Doc Bashir ya amsa Shi tare da cewa Jameel ya cire masa drip in nan don Allah ya samu ya mike ya tafi gurin malamin,



*************Sen Rilwanu


Kwance yake kan tafkeken gadon Shi yana baccin Rana,domin ba karamin gajiya ce a jikin Shi kasancewar jiya ya dawo daga kasar waje,


Knocking in da Ake tayi ne ya sanya Shi jan tsaki tare da mikewa ran Shi bacci wani dan iskan ke son katse mishi baccin ranar sa,


Rai a bace ya Bude kofar Saa'eed ya gani fuskan Shi cike da tashin hankali,


Kai Dan uban Ka ban ce da Kai Kar uban da ya tashe ni ba,ina son yin bacci ya kare tare da wanke fuskan Shi da Mari,


Kumatu ya dafe sannan ya zube a kasa tare da cewa ranka ya Dade kayi hakuri hankali na ne a tashe ya sanya na kasa hakuri Saida na tashe Ka,


Harara ya maka masa sannan yace uban miye ya daga maka hankali beside ina ruwana da tashin hankalin naka,don Rashin kunya za Ka daga ni bacci wai kana cikin tashin hankali tashin hankali uwar me ya kare cike da Ihu,


Kayi hakuri yallabe, yanzu ne na ga wani posting Yana ta yawo wai an nemi karamar hajiya an Rasa,


Da mamaki Sen ke kallon Sa"eed kafin yace kamar ya wacece wata karamar hajiya (domin sam hankalin Shi be bashi wai akan Nadeeya Ake magana ba),


Shiru Sa"eed yayi Yana me jin tsoron sanar mishi ganin be gane me yake nufi ba,


Ba magana nake maka ba Dan uban Ka kayi mun shiru ya kare a harzuke kamar zai rufe Shi da duka,


Cikin sanyin murya yace Sen daman yanzu na gani Yana ta yawo wai an nemi Princess Nadeeya Sama da kasa an Rasa a cikin asibitin mahaukata,AI da Jin wannan zance wani irin jiri ne ya Debi Sen yayi baya yuuuuu,a tsorace Saa"eed ya mike yana yallabe kafin ya Kai ga taro Shi ina har ya kai kasa sai karan faduwar wa Tiiim kake ji........



Kuyi hakuri da ji na shiru jiya wlhy mara lafiya gare ni ina jinya,Ku Sanya ta cikin adduo'in Ku don Allah,


Na san na yau babu yawa ayi mun uzuri in sha Allah na samu dama Zan Kara page daya zuwa dare in kuma ban samu ba a yi mun afuwa sai zuwa Monday in sha Allah,


Na gode sosai da kulawa da kaunar Ku gare ni Allah saka wa kowa da khairan,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔 UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


             

WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM 

(MARTEYBEE)


.....


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


In har kin San ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki toh Don Allah kiyi Zaman ki ba sai kin Shigo ba,Maza should stay away from my group domin wannan group in Mata ne zallah 🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


  08100046388


............

            Page twenty- four


************


A matukar rude Saa'eed yayi Kan Sen Yana kuka yana yallabai Ka tashi don Allah domin Shi dauka ma yayi zuciyar sa ce ta buga ya mutu,


Daman ya sani muddum Sen ya samu labarin nan toh zuciyar Shi bara ta iya dauka ba ya Sanya yake ta Jin tsoron sanar masa tun daga lokacin da ya ga  abun na trending a social media(kun Riga kun san zamanin da muke ciki yanzu kafin ki Isa gidan ki ma in kika yi wanni abun sai ki ga ya watsu duniya,wani kamar jiran Ka ake wannin baka ma sanin an dauka Yana da kyau mu kasance masu aikata alkhairi sannan masu guje wa riya.da kuma sabon Allah domin wannan social media in saidai godiar Allah kawai,Allah yafe mana sannan  ya cigaba da rufa mana asiri duniya da lahira),


Ganin Sen Baya mosti ne ya sanya Shi a tsorace ya dauko waya Yana kuka ya shiga kiran layin Alh Kabeeru,


Kira biyu kuwa ya dauka,cikin rudewa Saa"eed yace yallabai akwai matsala,Sen ne tun dazu ya Fadi na yayyafa mishi ruwa har yanzu be motsa ba ina tsoron ko dai mutuwa yayi,


A zabure Kabiru ya mike tare da fadin what Saa"eed Ka ko san me kake Fadi kuwa miya samu Sen in,ko da yake ba lokacin bayani bane yanzu gani tahowa daga haka ya kashe wayan,


A hanzarce ya mike tare da zira babbar rigan shi sannan ya dauko makullin motar Shi,tsaban rudewa mancewa yayi ma wai Yana da wani driver,


Kai tsaye gidan family doctor in Shi ya nufa lucky him ya same Shi Yana nan a gida so da sauri ya ce da Shi ya fito su tafi,grabbing kayan aikin Shi yayi a box sannan ya fito ba bata time suka nufo gidan Sen,


A daki suka same Shi kwance be numfashi Saa"eed da sauran workers in gidan na tsaye bisa kanshi sai kuka suke suna ya tashi,


Tsawa Kabiru ya daka musu sannan yace kowa ya fice daga dakin ya koma bakin aikin Shi while Saa"eed ya Jira Shi a parlor,sim sim haka kowa ya fice, Doc bismillah check on him ko Yana Raye,


Da haka Doc ya shiga baiwa Sen taimakon gaggawa inda ya tabbatar wa Kabiru da Yana raye dogon Suma ce kawai yayi sabida wata yar firgici da ya samu,kuma muddum hakan ta cigaba da faruwa watarana kumbura zuciyar Shi za ta yi ta fashe Allah ya kyauta,Saida ya ga Doc ya dawo da daidaituwar numfashin Aminin nashi sannan ya fito domin ganawa da Saa"eed ya ji menene ya razana Shi  har ta Kai Shi ga suma,


A tsaye ya tarar da Saa"eed yayi tagumi daga gani Yana cikin damuwa,


Kujera ya nema ya zauna sannan yace ya Ka Saa"eed da sauri ya nufe Shi tare da zubewa a kasa nan gurin kafafun Shi,domin ya san halin Alh Kabiru Sarai da saurin fushi da kuma saurin hannu,


Miye ke faruwa da Amini na har ya haifar mishi da firgici har ta Kai Shi ga suma,


Cikin sanyin murya yace yallabai daman yau ne a Facebook na ga news in nan na ta trending wai an nemi Princess Nadeeya Sama da kasa an Rasa,


What Kabiru ya ce tare da mike wa,kamar yaya wai an neme ta an Rasa toh tana ina,ina ma securities in hospital in suke,waye ma yake da gut in shiga cikin clinic in ya sace yar gidan Sen Rilwanu Audu Waziri ya kare cike da Ihu da fada,Shi dai Saa"eed kasa yayi da kanshi be ce da Shi komai ba don be ma san me zai ce in ba,



**********Doc Bashir


A razane ya dago idanun Shi da suke masa nauyi tsaban kuka ya zuba su a kan Doc Jameel,


Cikin sanyin murya yace don girman Allah kace da ni karya kake,hmm wlhy Doc Bashir ba karya nake ma ka ba duk wani kafofin sadarwa da Ka sani labarin da ke ta trending ke nan na bace war yar gidan Sen da ke cikin asibitin mu,


Wani irin jiri ne ya kuma kama doc Bashir Yana nan a kwance,Shi tsaf ya ma mance wlhy a modern world muke yanzu duk abun da ke faruwa mutum ko a Ina yake Yana iya sani,thanks to social networking,ya tara mutane yayi musu kashedin Kar Wanda ya fitar da zancen nan shine aka samu wani mugun mara tsoron Allahn ya yada a yanar gizo,Shi be taba sanin haka yayi bakin Jini cikin hospital in ga ba sai yau,ban da Jameel babu Wanda ya zo kanshi duba halin da yake ciki,thank god ma Allah ya taimake Shi suna yi da Jameel in domin duk asibitin babu wanda yake daga wa kafa ko ya Bari Ka ci albarkacin Shi bayan Kareematu da Yan matan da yake latsewa,Sam sam bashi da good muamalat da mutanan asibitin(Tabbas iya Zama da mutane ma rahma ne,duk rintsi yar uwa ki zama me good muamalat da mutanan da kike zaune da su,domin shedar duniya Shi ke bin mutum har kiyama,mutumin da ya iya Zama da mutane,sai Ka ga ko gurin Allah yana saukaka mishi alamuran Shi ga kyakkyawan sheda daga bakin alummah,saisa duk wuya duk rintsi yi kokari ki zauna da kowa zuciya daya da ki cuta gwara a cutar da ke, Allah Ka zaunar da mu da jama'ar Ka lafiya,ya kuma tsare mu daga cutar da ko da dabba ne balle Dan Adam),



Shiru yayi kawai Yana me tausaya wa kan Shi yau tunda garin Allah ya Waye ya Bude idanun Shi yake haduwa da masifu,


Suma da zawayi be san sau nawa yayi su ba,lokaci daya ya koma mara lafiyan karfi da yaji, yanzu haka ma cikin nashi ta murda zawayin yake kuma ji,


Jameel kama ni mana ka raka ni toilet cikin ya kuma lalace mun,


Tsaki Jameel ya ja cikin ranshi don ba karya Shi kam ya Fara gajiya da dawainiya da Bashir da yake yi,kafin ya zo ya kama Shi din ya raka Shi toilet in Yana me Galla masa harara,


Fitowan Shi yayi daidai da shigowan Nameer,gaisawa suka yi sannan yayi wa Bashir ya jiki,amsawa yayi da kyar sannan Nameer in ya zauna


Doc ka ko san an samu wani dan iskan da ya yada batan yarinyar nan a social media,


Ya salam a garin ya Doc Jameel ai daman ilar wannan media in ke nan yanzu yanzu za a yi Abu sai Ka ga ya yadu,Allah dai ya sa mahaifin ta kar ya gani,


Wani gani ai wlhy Nameer ina maka tabbacin Sen zai ga abun nan ko da shi be gani da kanshi ba dole wanda suke tare da Shi in har suka gani za su sanar masa,


Wayyo ni Kan na shiga uku na lalace na mutu na lalace shike nan karshen rayuwa ta ya zo,wlhy Sen tsaf kashe ni zai yi tunowa da yayi da irin mugun warning in da suka mishi Randa za a bashi Nadeeya,Saida suka tabbatar mishi da ya Kula musu da yarinya Kar a ji Kar a gani,muddum wani Abu ya same ta toh wlhy bare ga da kyau ba,


Sabida zalama da zarmewar zuciya irin nashi ba tare da dogon tunani ba ya ce ya yarda harda dauka musu alkawarin Kan Kar su ji komai zai bata cikkakcen kulan da take bukata,inda hakan ya zame masa opportunity hanyan samun kudin Shi,ya ringa tatsan kudade a gurin Sen kamar Wanda Allah ya aiko Shi,sannan Rana tsaka ace an wayi gari yarinya ta bata,ai wlhy Sen bare yarda da wannan labarin ba,


Cikin muryan kuka yace na san any moment from now Sen is on his way ya zo hospital in nan,don Allah Ku taimake ni ku kama ni Ku kaini Airport na samu na gudu na bar kasan nan ni ko Burkina Faso ne na samu na fada kafin in kuran nan ta lafa na dawo,


Haba me Doc Jameel da Nameer za suyi in Banda dariya,Saida suka Dara sannan Nameer yace haba dai Doc AI wlhy ko Ghana bara ka iya tafiya ana tsaka da tashin hankalin nan ba in Ka gudu ya ma nuna kan cewa kana da masaniya a batan nata ke nan,just be a man stay back strongly and face your fear,sai Ka ga komai ya zo maka cikin sauki amman tunanin guduwa duk be taso ba,


Fada mishi dai Doc Nima tun safe abunda nake fada mishi ke nan mutum be Isa maka abunda Allahn Ka be maka ba,stop acting like a girl be a man dallah Ka kwantar da hankalin ka since sai Suma yake Yana farfado wa fa sai kace Wanda aka ce da Shi mala'ikan daukan ran sa ke tafe,beside Sen is not a bad person abun dai zai masa xafi coz zai ga kamar rashin Kula ne amamn bare yi komai ba am sure of that,


Hmmm wlhy su bara su taba gane waye Sen Rilwanu Audu Waziri bane,Akan wannan yarinya tashi babu abunda ba zai iya aikata wa ba,a Karin banza ma ya dauke Shi da Mari balle ace masa ta bata,a wlhy yau kashin Shi ya bushe,


Ganin duk sunyi shiru ne ya sanya Nameer mikewa tare da cewa am damn hungry thank god it's break time lemme go and grab something ko karyawa ban yi ba na fito,wanna go along ya tambayi Jameel,


Aa doc just carry on kasan ni ke Kula da matsoracin nan,so I have to stay back ko Dan shi just enjoy yourself,da haka Nameer ya bar dakin zuciyar Shi fes domin babu wani break in da zai je Nadeeya yake son zuwa ya ga ya take ciki,


Saida ya biya ta Saje ya Mata ice cream,sannan ya dauko hanyan gida Yana tunanin ta,tabbas wannan shayi da ice cream ba kosar da ita zai na yi ba,and a condition in da take ciki yanzu bara ta iya cin heavy food ba ba ma za ta iya tauna ba daga ganin alama,dole ya san abun yi,ya kama ta ma ya samo wacce za ta taya Shi kula da ita domin is not safe Yana barin ta ita kadai a gida Yana zuwa hospital,dole za ta bukaci taimako,da haka ya samu ya Isa gidan,



**********Sen Rilwanu Audu Waziri


Farfadowar Shi ke nan yayi daidai da karewar drip in da aka daura masa,cire masa doc in yayi tare da tambayan Shi hope babu abunda yake hi,kai ya daga mishi toh Masha Allah yallabai kana kokarin controlling temper naka domin gudun fadawa babban matsala,be ce da Shi komai ba sai kokarin mikewa da yake yi domin bayi da burin da ya wuce ya gan shi a specialist yanzu yanzu,


Haba Kai kuwa Sen ya daga cire maka drip sai kokarin mikewa take it essay pls Kabiru yace da shigowar Shi ke nan,


Essay I should take it essay fa kace Kabiru shin Ka san me ke ma faruwa kuwa,Nadeeya fa wai an neme ta an rasa Saa"eed ke sanar mun,


Bari na sallami doc na zo muyi magana Kar a bar Shi a tsaye,mu je Doc AI ba wani damuwar ko,


Eh komai lafiya Alhamdulilah na fada mishi Yana kokarin controlling temper in Shi sannan ya na Shan ruwa akai akai komai zai tafi daidai,toh mun gode I will transfer your money through your bank account,godiya yayi sannan ya fice daga gidan,



Kamo hannun Shi Kabiru yayi tare da zaunar da Shi sannan yace aboki na pls try to relax lafiyar Ka na gaba da komai,


Haba Kabiru wai wani relaxing kake son nayi Kai fa kasan wacece Nadeeya a guri na ba sai na sanar maka ba,and don iskanci da rainin wayo wai ace an neme ta an rasa yar tsana ce da za a ce ba a gan ta ba,


Wlhy Nima tunda Saa"eed ya fada mun nake ta nanata maganar a Raina,kwata kwata na kasa yarda,toh ba a gan ta ba ta je ina,


Shine Nima Kabiru yarinyar da tana kwance ko finger na ta bata iya lifting ina ta samu kafar da za ta gudu,toh ta gudu ta je ma ina,


Babu guduwar da tayi yarinyar da hauka take ko Ka mance,


Ban mance ba Kabiru ina sane na rantse da Allah yanzu ba sai anjima ba zani asibitin nan sai na tabbatar da na ci durun uwar Bashir da ni yake wasan,Kila saken da nake mishi ne ya sanya Shi zai mun Wasan banza,toh wlhy Zan iya daukan komai Amman Banda Nadeeya,muddum na je asibitin nan na samu babu yarinya ta toh wlhy Ka zamo sheda sai na kashe Dan iskan yaron nan da hannaye na,tashi mu tafi in kana zuwa domin sam ban ga amfanin Zama na a nan ba....




Don Allah ayi mun afuwa na jina shiru jiya wlhy sau biyu ina typing Yana goge wa😭,wannan ma da kyar na samu nayi,


Sannan Bana dan jin dadi Ku Sanya ni cikin adduo'in Ku pls,


Na gode sosai da kaunar Ku gare ni, ubangiji ya biya wa kowa bukatun su na Alkhairi,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi sai zuwa gobe in me kowa me komai ya Sanya mun Kai.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                 BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)



.........


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


In har kin San ba karanta book ina da comment bane zai Shigo da ke,toh na hutar da ke ba sai kin Shigo ba, haka Maza don Allah stay away from my group domin na Mata ne xallah 🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


       08100046388


...........

          Page twenty-five


*********


Aboki na don Allah Ka zauna Ka san dai yanke hukunci cikin fushi regret kawai yake jawowa ko,so pls Ka zauna ran Ka ya sauka tukun na koma miye ma je,


Da wani irin kallo Sen ke bin Alh Kabiru da Shi sannan yace wai wani Zama ne kake son nayi ne,for crying loud wai Baka Jin me nake fada maka ne,Nadeeya ta fa aka nema aka Rasa and you are telling me to relax,are you for real,ya kare yana karkada kafa kamar me Shirin dambe,


Hey common na sani ni Kai na hankali na a tashe yake but fighting won't solve anything,you have to stay calm ko don health in Ka wat if muka je a halin yanzu ranka na Sama Ka je Ka kashe shin kamar yanda Ka ce kayi ruining image and reputation in Ka ne fa,and for your own information you are going to end your life in prison which mean Kai da mulkan jahar bauchi har abada,


Da sauri yace I reject it you better stop saying that kafin Yan Ameen su amsa,Odugwu yace in har na ga ban hau kujeran gwammna ba toh mutuwa nayi,ko ni na koma nace Bana so,and ya ce da ni I should rest ba Zan mutu ba har sai nayi 8 years a Kan mulki so you better stop saying such things,ya kare yana Sanya babban riga,


Murmushi Kabiru yayi sannan yace Nima Kai na ai zan so Ka hau wanga kujera domin muddum Ka hau toh Kaka ta ta yanke Saka,ni dai try to control your anger that all am saying,


Dariyar takaici Sen yayi sannan yace see who is talking about controlling temper,any way I won't blame you,Kai source in samun kudin Ka na tare da Kai sai sa kake mun duk wannan surutun,are u going ko in yi tafiya ta domin ban ga abunda zai Hana ni zuwa dubo where about in yarinya ta ba,


Sanin halin Aminin nashi ya Sanya Alh Kabiru saurin mikewa tare da cewa mu je AI abunda ya shafe Ka ni ya shafa, let's get going da haka suka fito tare da shigewa cikin mota,



************Doc Nameer


Saida ya tabbatar da Nadeeya ta koshi ya goge Mata baki sannan ya fito daga dakin,in har ya canka daidai kamar tayi fitsara and dole tana bukatan a canja Mata Kaya,Wanda Shi bare iya yi ba,Shi sam be san me ya shige Shi da ya dauko ta ya kawo ta gidan Shi ba tare da tunanin abubuwa da yawa ba,


Shi ba auran ta yayi ba a taya zai na bata cikakken kulawan da take bukata,sanann Shi ba Mata gare Shi ba balle ace ya Sanya ran za ta Kula da ita,and a halin da Ake ciki be Isa ya dauke ta ya Kai ta Kaduna ba ana tsakiyar gurmin nan,don ya san can ne kawai za ta samu Kula a gurin Mamah,


Shi yanzu yaya zai yi,ya Zama dole ne ya samo yar aiki Wanda za ta taimaka masa ta gyara masa Nadeeya ko yayi wa daya daga cikin nurses in magana,abun haushin shine ba kowa ya sani a garin Bauchi ba Banda Habeeb,Shi kuma Habeeb bakin Shi ya fi karfin Shi he is not that sure his secret is safe with him,da wannan nazarin ya fito daga gidan har ya iso hospital in Yana me tunanin mafita because is not good ya na barin ta haka,dole ya Nemo Wanda zata taya Shi Kula da ita,



*********Sen Rilwanu


Ko parking be bari an gama yi ba ya balle murfin Motan cikin sauri ya sauko Yana gyara babban rigan Shi da ke neman tatile shi,


Tafiya yake cike da sauri domin bayi da burin da wuce ya gan shi a office in Doc Bashir,ya ji daga bakin Shi ina diyar Shi,


Da sauri Alh Kabiru ya fito tare da mara mishi Baya yana kara kwantar mishi da hankali Kan in sha Allahu za a ganta,


Be tsaya amsa gaisuwa da maulan mutane ba domin ba Shi ne a gaban Shi ba,yau yar fake concern and attention da yake baiwa talakawan Shi,Wanda su kuma suka yi masa uzuri kasancewar yawanci labari ya bazu,ba laifin Shi bane duk Wanda ke matsayin Shi fiye da haka ma sai yayi,


Da karfi ya bugo kofar office in Doc Bashir ko tsaya wa sauraran abunda Doc Hanifa be yi ba,sai Alh Kabiru ne ya tsaya tayi mishi bayanin Kan Bashir fa yana isolated room,


Bashir shine abunda Sen yayi shouting at the top of his lungs,where the hell are u hiding you low life of a person,Jin shiru ya Sanya shi shiga dube dube,


Baya nan shine abunda Alh Kabiru ya fada yana me karasa shigowa office in,


Yana ina kasan be nan in Ka sanya ni bata lokaci na,ya kare kamar zai buge shi,


A ina Ka tsaya balle har nayi maka bayani in,nima isowar mun wata Doc ke sanar mun wai tun safe Yana isolated room be fita ko ina ba, that's good shine abunda Sen yace sanann ya juya cikin sauri yace let's go get him,


Cike da tafiyar sauri suka iso dakin inda suka tarar da Doc Bashir kwance magashiyan a Kan gado sai numfarfashi yake saukewa kamar wani me Shirin haiwuwa🤣,


Bashir shine abunda Sen ya fara fadi yana me zaro idanu,so you are here relaxing and having a fun time of your life bayan yarinya ta is lost ya kare yana bin Maltina da madaran ruwa da ya ga anyi mixing a cikin cup,


A zabure Doc Bashir ya mike yana furta na shiga uku na lalace Jameel don Allah ce da ni mafarki nake kamar muryan Sen nake ji,ya kare yana zazzaro idanu a kan Sen don son ya gaskata shin da gaske Sen in ne ko kuwa mafarkin da ya wuni yake yi yake kuma yi,


Karasowa Sen yayi tare da daga hannu ba tare da wata wata ba ya dauke shi da Mari me dankaran zafi sanann yace Dan uban ka ni ne nan,shege matsiyaci Wanda be gaji arziki ba yau sai na ci uwar Ka na ga gatan Ka a cikin garin Bauchi,har ni ce zan baka Amana Ka zo mun da maganar banza wai an ce ta,uwar Ka ce ta sace ta ko gidan uban Ka aka kaita,shege Wanda be iya cin arziki ba,


AI da sauri Jameel ya mike tare da barin dakin domin be dauka abunda Bashir ke ta tsoro ba ke nan,Ashe this man is very dangerous har haka a fuska sim sim kamar bare iya cize yatsa ba,Ashe shima ya iya hayaniya,gudun Kar a hada dashi shida babu abunda ya sani taimako ne kawai yayi wa Bashir ya sanya Shi ficewa daga dakin don har ga Allah wannan Mari ya tsorata Shi,



Kabiru ne yayi saurin riko Sen Yana cewa haba don Allah Ka bar Marin nan haka let's talk this is the 5th time da ka mare Shi ba,


Fincike jikin Shi Sen yayi sannan yace let go of me Kabiru,Dan Bura uban yaron nan a kwance na same Shi fa yana shan Maltina wato Shi har Yana da peace in da zai sha Maltina da madara while ba a san wani hali yarinya ta ke ciki ba,


Cike da galabaita Bashir ya dago tare da cewa na rantse da Allah Alh Kabiru ba wai fun time of my life nake having ba tun da garin Allah ya Waye na bude Ido na ga babu Nadeeya hankali na be kuma kwanciya ba,I tried all my very best na gano inda take but ban samu ba,


I have been fainting and using the toilet tun safe na sha drip ya Kai Leda nawa duk akan wanna yarinya amman sabida rashin godia da tunanin wannan mutumin zai zo ya hau Mari da duka na,haba is this fair am tired wlhy am not a piece of doll to u da zaka na duka na duk sanda Ka so am a fucking qualified doctor for crying out loud with a good qualification for your own information,ya kare Yana goge Jinin hancin Shi,


Baki Bude daga Sen har Kabiru ke kallon doc Bashir,Kabiru kana ko Jin me shegen yaron nan ke fada mun kuwa,bura uba ai wlhy duk lalacewar goma ta fi biyar,


Miye Doc dan ubanka who do u think are you da zan tsaya ina fada kana maida mun,ya kare tare da cikumo wuyan Bashir Yana kara dauke Shi da Mari,so mun Zama playing mate right,ka sace mun yarinya sanann Ka zo kana musanyan yawu da ni sabida wuyan Ka ya Isa yanka,


Wai miye riba na in na sace maka yarinya meye zanyi da ita,na ga duk wani kudi kana biya na don Kula da ita,why will I take a vegetable na Kai ta ina,Akan wani dalili ma,beside ai farinciki ya kamata kayi na ga daman neman Kai kake da diyar ta ka,so godia ya kamata kayi wa duk Wanda ya dauke ta,Shi aka Bari da dawainiya,


AI wani kukan kura Sen yayi tare da danko wuyan Bashir yace Kai dan iska karamin shege wlhy kayi kadan Ka yaba mun magana son ranka,ba a haifi Wanda zai ja da ni ba wlhy,Dan uwar Ka ni kake cewa neman Kai nake da Diya ta ya kare Yana Kara dauke Shi da Mari,


Na rantse da Allah Sen in Ka kuma taba ni sai na tabbatar da na  Tona maka asiri duk duniya su san Kai ne Ka Sanya na haukatar maka da yarinyar Ka akan wani son zuciya taka,haba na gaji na gaji ni ba jaki bane kayi ta duka na kamar uban da ya kawo ni duniya Doc Bashir ya kare da dan Ihu......




Ayi mun afuwa wlhy har yanzu ba wani sauki na samu ba wannan ma da kyar na samu nayi Shi,😭🙏🏻,


Ina cigaba da baran adduo'in ku don Allah,am kind of sick😭😭,


Ina godia da kaunar Ku gare ni, ubangiji ya biya wa kowa bukatun Shi na Alkhairi,


In sha Allah in dai na ji Dana dama za Ku ji ni zuwa gobe,


Ina wa kowa fatan Alkhairi🥰❤️

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)



.......


My  what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


In har kin san ba karanta book ina da comment bane zai Shigo da ke toh don Allah yi Zaman ki na gode ba sai kin Shigo ba,haka zalika Maza Don Allah Kar kuyi joining group Ina domin na matan aure ne zallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


    08100046388 


...........

          Page twenty- six


**********


 Wata irin shegiyar dariya Sen ya sake har yana dafe ciki,Alh Kabiru na taya Shi,Wanda ya sanya doc Bashir wangale Baki yana ganin ikon Allah,


A tunanin Shi abunda ya fada zai Sanya hantan cikin Sen kadawa har ya firgita Shi ya haifar masa da tsoro Wanda zai Sanya Shi bashi hakuri Kan ya rufa mishi asiri,gudun Kar siyasar sa ta lalace,a karshe yayi amfani da daman Shi ya karbi makudan kudade a gurin shi,na rufin baki,amman sai ya ga sabanin haka, actually shi be ga abun dariya a maganar Shi ba da ya sanya wannan bayin Allahn ke dariya har haka,


Kujera Sen ya ja tare da Zama ya daura daya kan daya sannan ya tsagaita dariyar,


Alh Kabiru ni har yau mamakin talaka nake wlhy wato shi fa talaka bashi da abokin gaba da ya wuci me arziki,


Sam mutanan duniya saidai a bar su,Ka ga daga ka kawo Shi ya zo shima ya ci arziki, shine wai ni Rilwanu Audu Waziri yake wa empty threat,


Dan dariya ya kuma saki kafin yace wonder shall never end,me ma kake cewa,


Yauwa za Ka yi exposing na kan ni na sanya Ka haukatar da diya tah,yeah ni nace Ka hauka ta din amman dole nayi maka??


Kudi na maka offering Wanda son duniya irin naka Ka mance da matsayin so called qualification in naka,Ka karba ko dole nayi ma,


Aje ma wannan maganar in ana magana muna yi da evidence don ko karshen  court in duniya muka je tambayan farko shine kana da evidence in Baka da shi ya zamo deformation of character kawai kake son mun don Ka batan siyasata,poor me karshe har tara za a Sanya Ka bani am I right Alh Kabiru ya kare Yana smiling,


Kyalle Dan iska Sen ko Shi a gidan uban Waye aka ce masa ana sa'insa da masu kudi,AI duk abunda me kudi yayi daidai ne a gurin talaka irin Shi,


Haba dai ai na ga yayi baki ne,toh Allah na tuba don Allah Waye Bashir da har empty threat in sa zai tsorata ni,nayi dealing da wanda suka ci uwar Ka in sanar maka,


Na rantse da girman Allah in ban ce raping yarinya ta kayi,Ka kashe ta har lahira sannan Ka binne ta cikin hospital in nan,in kuma siye gaba daya staff's in hospital in nan su bata sheda a court room,a yanke maka hukuncin kisa da na rape Ka ga shike nan na rufe shafin rayuwar Ka har abada me kama da Kai ma babu,


Haba Sen a dan wannan karamin alhakin har sai mun wahala shigar da Kara court kawai mu kwantar Shi muyi masa yankan rago mu Kai wa police dogs in gidan Ka su cinye Naman Dan iska, daman sun Dade ba su ci naman mutum ba,Ka ga shike nan in ya shiga cikin kare ya cigaba da rashin kunyar tashi a can,


Hantar cikin Bashir ne ya kada nan take ya ji kamar zawayi za ta zubo mishi,cike da mamaki yake kallon su Sen,


Go on Doc ko has cat got your tongue ne,Sen yace cike da shakiyanci,


A mutunci irin nawa Zan Baka zabi na Kira police da media team yanzu na sanar da su kayi raping yarinya ta Ka kashe ta ko kuma mu bi shawarar Aminina mu kashe Ka kawai a baiwa dogs Naman ka,shike nan kowa sai ya huta in Ka je lahiran Ka cigaba da likitancin naka,ya kare tare da sakin dariya,


A sukwane bashir ya iso gaba Sen idanu cike da hawaye yace na roke ka kar Ka mun komai,wlhy Bana son ko daya,


AA qualified Doc dole muyi daya cikin biyun nan,tunda na ga ai kasan right in Ka,in ka je court sai Ka sanar wa judge ko ba haka ba Kabiru,


Haka ne Sen AI wlhy ni Bashir ni Ka baiwa kunya in hada Ka da Aminina don Ka ci arziki shine za Ka sace masa yarinya Ka bishi da rashin kunya har kana za Ka tona masa asiri,kila ma Ka riga da Ka tona since,


Kyalle Shi wlhy ko ya fadi babu uban da zai yarda da Shi,coz ina da good reputation a garin nan fiye da tunanin me tunani in ya ga dama,ya bi gida gida Yana sanar musu Shi za ayi wa kallon mahaukaci,daman an cappa likitan mahauka karshe shima haukan yake if care not taken,



Na rantse da girman Allah babu Wanda na sanar wa kai Ka Sanya ni haukatar da Nadeeya ba Wanda ya sani,daga ni sai Allah na,


Ni fa duk ba wannan ya dame ni ba qualified Doc ina yarinyar da Ka je har gida Ka dauko ta,


Gumin goshin Shi ya goge sannan yace na rantse da Allah Sen Ka yarda da ni ban san inda Nadeeya take ba,


Wannan ce abunda hankalina Sam bare taba dauka ba,in Baka yar cikin girma da arziki na cika maka account da kudi Kan zaka Kula mun da ita,na kawo ta da bakin ta da kafafun ta Ka maida ta babu Baki babu kafa,duk na dauka na jure yanzu a wayi gari Ka ce da ni babu ita AI kasan ko kwana zamu yi kana nanata mun zancen ga baza ta taba kama Kai na ba,


Bashir ina Nadeeya ta shine abunda Sen ya ce a tsawace Yana me mikewa tsaye,


Cike da rudewa shima Bashir in ya mike ya shiga zare ido yana yar fa yatsu kafin ki ce me mutane sun cika a dakin,su doc Haneefa and co makiyan doc Bashir abun ya Kai musu Banda dariya da Allah Kara babu abunda suke yi,


Cike da rudewa ya shiga be wa Sen labarin iya abunda ya sani Kan ya Shigo duba Nadeeya around 12 kafin ya tafi gida shine ya ji an caka masa alura be kuma sanin inda kanshi yake ba,Saida safe ya farka ya ga babu ita ba alamun ta,


Kai Doc Bashir Ka ji tsoron Allah wlhy duk fadin asibitin nan babu Wanda yake Bari ya je Kusa da dakin ma daga Shi sai Kareematu ne suka iya Bude pin in dakin,


Sen Ka rike su wlhy tsakanin Shi da Kareematu ne dayan su ne ya dauke ta mugun mutum ne daman Shi,Doc Haneefa ta kare tana hararan Bashir in,


Ji yayi kamar ya shake yar iska ana babu guri tana ta kwanta, cikin raunin murya yace na rantse ni dai ban dauki Nadeeya ba ni in dauke ta in yi me da ita,


Waya sani maka duniyar yanzu AI ba gaskia aka fiya ba kaidai kawai Ka ga mutun inda Ka gashi,wani Doc ya fada,


Nan fa aka hau ce ce kuce tsakanin Bashir da doctors suna cewa sam Shi ya sace Nadeeya while Shi kuma ya kafe be san komai ba game da bacewar Nadeeyan,Shi yayi danasanin sanin Alh Kabiru da ya hada shi da Sen har ya shiga wannan halin(ni ko na ce son zuciyar Ka ta janyo maka),



Kuyi wa mutane shiru dallah,da me ze ji da batan yar sa ce ko kuma da wannan hayaniyar ta ku da ke neman cika mana kunne,


Sen I think the best option here is to call the police tunda mun bishi ta lallami yaki sanar mana inda Nadeeya take kila in ya sha matsa a gurin Yan sanda zai yi bayani,Bari na Kira su Auwal su zo su tafi da shi,


Maza Kira su Kabiru saidai ba Shi kadai za a kama ba,duk wasu maaikatan cikin hospital in nan duk a kame su don Basu da gaskiya kace da su su zo da mota da yawa,


Yallabe a duba mu wlhy mu ba mu san ko mai ba,ni ko kallan fuskanta ban taba, gani ba


Ni wlhy ko kalan dakin ban ma San ya yake ba, tunda aka kawo ta bashir ya kange komai ya Hana kowa zuwa Kusan ta,daga Shi sai Kareematu kawai ke shiga duba ta,


Kareematu wacece ita shine abunda Alh Kabiru ya tambaya,


Nurse ce kuma tare suke komai da doc Bashir Baya boye Mata komai kila ita tasan yanda ya boye ta,


Tana ina shine abunda Sen ya tambaya, through jiya da yau bata zo asibiti ba Bashir ya amsa da kyar,


Wonderful sai Ka Kira ta yanzu kace ta zo,in Ka ga dama Ka bari ta gane kana cikin wani hali taki zuwa Kai kadai za Ka kwana ciki,


Jiki a mace ya dauki waya tare da dannawa Kareematu Kira,


Shigowan ta gida ke nan duk jiki a gajiya domin tun haduwar su da Dan shuwa bata dawo ba sai yau da yace da ita zai tafi Sudan ya mata sallama mafi tsoka domin 5 mil ya bata tare da bata complimentary card in Shi,ba yanda ba tayi da Shi kan tana son bin Shi ba Amman yaki,yace ta Bari zai dawo zai neme ta,a haka suka rabu  tayi masa kukan shagwaba wai bata son rabuwa da Shi,za ta yi missing in Shi,(ni ko nace ko a ina ta san Shi oho har tana ikirarin bin shi ko mijin ta da yaran ta tayi yaya da su sai Allah),


Da Abdul ta ci Karo a bakin kofar dakin ta,sai lokacin take tunawa Ashe fa tana da aure ta bar gida kan asibiti za ta bata dawo ba sai yau and bata Kira ta sanar da Shi ga dalili ba,


Da kallon mamaki da takaici yake binta kafin da kyar tace da Shi sannu da gida baban khairat,



Hmmm yanzu Kareematu kin kyauta abunda kike yi kina tunanin hakan ya dace,tsakani da Allah ace ki bar gida sai yau kike dawowa da sunan aiki wani irin aiki ne haka,Anya kina son gamawa da duniya lafiya kuwa,


Baki ta cuno sannan tace toh yanzu don girman Allah me nayi,Kai zuciyar Ka ta mutu ba fita nemowa kake yi ba,in ban Nemo ba uban me kake son mu CI ni da yarana,mu zauna yunwa ta kashe mu ko miye,Sam ba zai yu wa ba wlhy dole na fita na nema ko Dan rufa wa Kai na asiri,Kai kanka kasan akwai ni da son dadi, don haka Bana son dogon surutu a gajiye nake,



In da sabo ya Saba da wannan mugun halin matar tashi domin sam ita bata laifi a rayuwa Baka isa sanar Mata tayi ba daidai ba,Kai kawai ya girgiza sannan yace Allah ya shirya,


Ameen ya shirya harda Wanda yayi aure Baya iya yin cefane me kyau a gidan Shi,ta ja tsaki aikin banza mutun be da Sisi sai iskanci ai  sai kayi,


(Maza a ji tsoron Allah Ku sani aure bautan ubangiji ne Ka dauko yarinya Ka kawo ta gida,toh Ka sani nauyin ta na kanka,a ringa kokari ana ciyar da iyali daidai gwargwado Kar Ka zamo mugu,kana da Shi Baka yi,and Kar Ka zamo me mutuwar zuciya da karfin Ka don Ka Rasa aikin gwamnati shike nan bara Ka tashi Ka nema na,toh wlhy Ku ji tsoron Allah Shi dai hakkin ciyarwa tana Kan wuyan Ka ne,sannan Lada gare ta ci da iyali,and Yana tsare mutunci da gudun raini,muddum Ka kasance Baka ciyar da iyalan Ka sai sun tashi sun nema sun Baka toh wlhy Ka siyawa Kan Ka raini da wulakanci da kudin Ka,Mata kuma Ku ji tsoron Allah duk abunda me gida ya kawo komin kankantan Shi learn how to appreciate sai ki ga ya samu karfin nemowa gobe,rainako ko hangen na gaba da ke sam ba naki bane,my sisters duk halin kuncin da kuke ciki wlhy kin fi wasu,in kika ga wasu sai kin daga hannu kin ce Alhamdulilah, ubangiji ya ba mu ikon gyarawa,),


A Kan kujera ta yarda jakar hannun ta tare da fiddo wayan ta dake ringing,


Ko uban wake Kira na oho ni wanka nake son yi na hutawa raina,mitar da take ke nan tare da kallon screen in wayan ganin Bashir ke Kira ya Sanya ta lailayo ashar tare da kunduma mishi,


Lalle bashir Ka cika Dan rainin wayo to me kuma Ka Kira kace mun shine abunda ta Fadi bayan ta dauki wayan,


Yi hakuri Kareematu nasan haushi na kike ji Amman,


Amman me ruwan masifan da ke cin ta ya Sanya ta kasa gano tashin hankalin da ke dauke a muryan Shi,


AI wlhy babu abunda za Ka ce da ni, Bashir ni kareema Ka wulakanta,sabida Rashin mutunci Ka Sanya ni na je guri Ka ki zuwa,toh wlhy Kar Ka kuma Kira na in ba haka ba sai na yi maka abunda baza Ka mance ba ta kare tana jan tsaki tare da kashe Kiran,


Kuma Kira yayi taki dauka Kara Kira yayi sai a na uku ta dauka,cikin bacin Rai tace wai miye haka Ka bi Ka takurawa rayuwa ta fa,


Don Allah Kareematu kiyi hakuri nasan ban kyauta Miki ba Amman wani urgent Abu ne ya taso,ni da ke AI kin San bata Baci yanzu haka ma wlhy Sen mahaifin Nadeeya ne ya zo Yana ta barin kudi a staff's shine nace baran bari a barki a Baya ba kiyi sauri ki zo ki karbi rabon ki Kar ya tafi,


Nan take ta washe Baki ayya dan bashiru na,Ashe da arziki kake Kirana nake ma Bura uba ta saki dariya saisa nake kaunar Ka nawa,Sam in har Kan samu ne Baka mance ni,gani nan tahowa yanzu wankan ma na fasa Shi,


Toh Maza hanzarta ina jiran ki da haka ya kashe Kiran,haba mikewa tayi tare da karkabe dankwalin ta tare da kafa dauri,


Sannan ta dauko turaruka ta fesa tana Yan wakokin ta na haka za Ka ganni ayye,haka za Ka bar ni,tana daga murya don Abdul in ya ji,


Jakar ta ta dauka tare da mayafi,Bari na hanzar ta domin manyan nan Basu son Jira yau Allah so na yake da arziki,kila na je ma nayi mishi yayi inviting na guest house in Shi, dariya tayi tare da karkada kirji da kuwa Kaka ta ta yanke saka,da haka ta Sanya takalmi ta fito,


Khairat ce ta tare ta da Mommy mommy ina zaki ,kallon yarinyar tayi Sama da kasa kafin tace gidan da ubanki ya aike ni,Ka ji mun shegiyar yarinya dallah Ka ki Bani guri,


Da haka ta wuce yarinyar a kofar gida ta tarar da Abdoul zaune abun duniya duk ya dame Shi,


Yauwa Baban Khairat anyo Kirana na emergency a asibiti ni Zan wuce sai Allah ya juyo da ni,ga wannan ta Mika mishi 2k Ka baiwa Khairat tayo muku cefane don nasan ba abunda kuka CI tun safe,Kar a dafa da ni Zan ci abinci a hanya ta ta dawowa bye,ta kare tare da wucewar ta ba tare da jiran Jin amsan Shi ba,


Adaidai ta ta tare da sauri tace ya Kai ta TH dake a unguwar Railway suke so akwai Dan tafiya kafin a Kai specialist hakan ya Sanya doc Bashir Kiran ta,


Yi hakuri ga mu nan mun wuce Wunti yanzu za mu iso,okay kiyi sauri shine abunda yace tare da kashe waya,


Ita kadai sai sakin murmushi take gani take yau Allah ya Gama Mata komai,har Allah Allah take su Isa,


A haka suka iso asibitin cikin sauri ta sallami me adaidai tan,tare da cefa chewing gum a bakin ta tana tauna tare da taku irin na isasun Mata ta iso bakin clinic in Nasu,


YOU ARE UNDER ARREST shine kalman da ta ji daga bayan ta.......



Asaalamu alaikum


Ina fatan duk kuna lafiya Allah ya sa haka ya kuma Kara mana lafiya da Nisan kwana me amfani,


Na ga sakonin Ku ina godia ubangiji ya amsa ya kuma bar zumunci na gode sosai,


Ayi hakuri tun dazu na so posting yanayi na jikin ne be bar ni ba,


A cigaba da Sanya ni a addua don Allah 😭🤲🏻,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi,


Sai kuma zuwa Monday in me kowa me komai ya Sanya mun Kai.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY 

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


.......


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Don Allah in har kin san ba reading and commenting in book ina bane zai kawo ki toh kiyi wa Allah Kar ki yi joining in group ina,haka zalika Maza pls should stay far away from my group domin na Mata ne zallah ko Ka shiga zan hiddo ka🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


     08100046388


..........

         Page twenty- seven


*********


Jin kalman tayi kamar saukar aradu a ka,hakan ya Sanya ta ja ta kame da matukar mamaki take juyowa,ganin rundunan Yan sanda tsaye kanta da uniforms fuska daure bakake munana da su babu alamun sassauci ko rahma a tare da su ya Sanya ta shan Jinin jikin ta,duk iskancin Kareematu akwai ta da tsoron hukuma,


A hankali ta shiga waige waige wai so take ta ga da wa suke domin a iya sanin ta babu Wanda ta samu matsala da,lafiya Lau suka rabu da Alh Jidda babu abunda ta daukar masa balle ace ya zo karba,


Haka zalika a hanyar ta bata samu rikici ko matsala da kowa ba in ba Abdul da suka Dan yi kace nace ba Shi kuma be Isa dauko mata yan sanda ba,


Ganin ta tsaya Baki Bude ya sanya daya daga cikin su yace officer arrest her mana,


A zabure ta dawo daga duniyar tunanin da ta fada,bakin ta na rawa gurin fadin Arrest me ta kare tana nuna kanta,for what crime me nayi,


Be kuma kallan ta ba yace in mun je can station kya ma ji koma miye kika yi,


Mamaki ya Hana ta tabuka komai tana ji tana gani aka Sanya mata handcuffs tare da tusa keyan ta zuwa jerin motocin Yan sanda Wanda suka Ibo da yawa kamar Wanda aka zo kama Dan kinmashin🤣,



Tafiyar yan mintoci ne ya iso da su Yan doka road dake babu wani tazara daga asibiti zuwa gurin,kasancewar a nan babbar head quarters na Yan sandan duk Bauchi yake,


Haka aka wangale katon gate in police command suka shige da motocin su sai kara yake,ita dai Kareematu kanta a matukar kulle yake domin sam bata gane komai ba,rabo aka ce da ita ana yi ta zo da sauri ta karbi share in ta daga ina duk wannan tashin hankalin ke fitowa,ita ce a cikin police command a hakan ma wai crime in da bata ma san da Shi ba,


Jin tsayuwar motar ne ya bata daman gaining courage domin har ga Allah duk da ba Law tayi ba ta San right inta,domin ko banza tayi civic education a junior secondary school Inta, ba zai yu haka kawai ayi arresting inta without sanin me tayi ba,


Bude ta ke da wuya ta ga an hangado keyar doc Bashir,wani irin yankewa gaban ta yayi take zuciyar ta ta bada rassss,bata san sanda kalman na shiga uku ya kwace daga bakin ta ba,


Tsawa Dan sandan ya daga mata tare da cewa fito bakar munafuka AI you don't enter 3 sai bayan mun Gama azabtar da ke ma,


Jiki a sukwane ta fito domin ta fara gano kwanan zancan duk tsiya ta san Bashir ne kila yayi wata Bura uban ta shi aka kama Shi yayi involving inta a ciki,AI ko bata ga abunda zai hana ta ci wa Bashir uwa ba idan ya Bari ta fito,



Nan kasa aka yarda su domin Sen ya ja wa officer incharge in gurin Kan Kar ya kuskura ya raga wa doc Bashir ko Kareematu har sai sun fito mishi da yarinya,in ta kama yayi using ko wani irin azaba ne in har gaskia za ta fito daga bakin su,he don't bloody care ko da dayan su ko duka za su Rasa rayukan su,zai ji da wannan abunda ya sani kawai a fito mishi da Nadeeyar sa,


Zaman mayafin ta gyara sannan ta juyo tare da watsa wa Bashir wani irin kallon tsana me cike da sakon Ka kyauta Bashir ni za Ka Sanya a matsala,


Kasa yayi da idanun Shi domin sam bare iya juran kallon nan nata ba,


Bashir ubaidullah shine cikakken sunan Ka ko,eh sir Doc Bashir ubaidullah haka sunan yake,


Take polices in gurin suka sheke da dariya sanann daya yace ko ba Doc ba kai kana cikin wannan halin ai ko sunan uban naka kawai aka Kira amsawa zaka yi kayi godia ba wai Ka tsaya wa mutane iyayi ba,


Ya Isa Dauda Kai dadi na da Kai yawan magana,sorry sir shine abunda yayi saurin cewa,


Zama ogan Nasu me suna Jabiru ya gyara sannan yace are u ready to talk I mean kun shirya Ku sanar da ni gaskiar me ke faruwa cikin ruwan sanyi ko sai na fiddo gaskia ta karfin tsiya daga bakin Ku,ku kalle ni da kyau,wlhy Bani da mutunci I hate crime and criminals in har na ga me laifi toh hankali na be taba kwanciya har sai na san yanda aka yi nayi punishing in Shi,in such a way gobe ko kudin duniya za a bashi bare Kara aikata makamanciyar laifin ba ma,


Hantar cikin Kareematu ne ya kada domin kallon fuskan Jabiru ma kawai abun tsoro ne balle yanda yake magana cike da iza Isa da kuma Ihu,ga uwa uba ita har yanzu ba sanin laifin da ta aika tayi ba,



Cikin sanyin murya doc Bashir yace yallabai wlhy iya Kar gaskia ta na fada maka ni wlhy Bani na dauke ta ba,


Na shiga uku Bashir wa aka dauke Ake zargin Kaine Ka dauke ta yaushe Ka fara dauke mutane ban sani ba, Kareematu ta kare a matukar rude domin case irin wannan da kyar mutum ke fita in ba Allah ya taimake Ka ba sai Ka gan Ka har court daga nan a zarce da Kai gidan gyaran Hali,


Ke dallah ki rabu da ni in ji da daya ni a yaushe na sace Nadeeya through out jiya an neme ki an rasa kuma daga ni sai ke muke shiga gurin ta,yau kuma an wayi gari babu ita babu labarin ta toh ya Zama dole kina da masaniya Akan batan Nadeeya,


A Kareematu bata san sanda ta mike tayi wata tsallan albarka tare da direwa kan Bashir,


Kukan Kura ta Saka tare da danko wuyan rigan Shi,Bura uba Bashir ni Kareematu za Ka yi WA sharri na shiga uku na lalace yau ni na ga boni a yaushe na sace yarinya,


Jijiga Shi take tana fadin haba ai daman buri yayi kama da mutu,Banda hauka irin ta wa ko yaushe Ka taba Sona da harkan karuwa harda Ibo jiki na zo, Ashe tsiya da sharri kake nema ta da Shi,


Ubangiji ya Saka mun wlhy ban yafe ba,ke dallah cika ni AI maganar gaskia nake yi ko karya nayi Baki zuwa dakin nata,ko ba daga ni sai ke muke shiga ba,


Ganin suna neman maida guri filin dambe domin yanda zuciyar Kareematu ke Saman nan anjima kadan za su iya kicimewa da dambe ya Sanya oga Jabiru daka musu wata tsawa,


Nan kowa ya shiga hayyacin sa,Ku watsa mun su a cell sannan a kira me bada horo ya zo mun yi Baki,domin na ga alama suna da taurin Kai sai sunyi laushi tukun na,Yana gama fadin haka ya mike abun Shi,


Hawaye ne tab idanun Kareematu Banda zagi babu abunda take aunawa Bashir domin sai yanzu take gane komai,wato Nadeeya aka Rasa shine yake kokarin maida komai kanta,abunda tayi ta gudu ke nan,tana ji tana gani aka cire su dan kunne zobe abun hannu hatta Dan kwalin ta da takalmi ba a bar ta da su ba sannan aka tasa keyar ta zuwa cell da tunda uwar ta ta haife ta bata taba shiga  ba sai yau a sanadin Doc Bashir,Shi din ma cell in aka cilla sa sannan aka tafi kirawo me bada horo domin ya zo ya isar da umarnin oga,



*********Sen Rilwanu


Iya kan tashin hankali yau Sen Yana cikin shi,domin sam be dauka wai zai bar cikin hospital in nan ba tare da an gano in da yarinyar Shi take ba,


Abun Ku da abun social media tuni labari ya watsu Kan an nemi Princess Nadeeya yar gidan Sen Sama da kasa an rasa,a take abokai da mutanan arziki suka shiga Kiran layin Sen da na Aminin Shi Kabiru domin Jin shin gaskia ne wannan labarin ko karya,ganin mutane na neman addaban rayuwar Shi da waya ya Sanya Shi kashe wayar tashi Baki daya,zai yi cifa da ita Kabiru ya amsa,


Da kyar ya samu ya Sanya Shi cikin mota suka dawo gida domin lokaci daya ya ga wata zazzabi ne from no where ta kama Sen,


A hanya ya Kira doc Akan ya dawo jikin ya motsa inda suka dawo suka samu ya Riga su isowa,


Da taimakon Saa"eed aka riko Sen tare da Shigo da Shi part in Shi nan kan kujera a parlor aka kwantar Shi,alura doc yayi mishi sannan ya shiga Sanya masa drip da kyar ya Bari ma aka Gama Sanya masa din he was insisting a bar Shi shi fa lafiyar shi kalau,sabida tashin hankalin da ke kan Shi ya ci ace ya dan samu bacci domin harda aluran bacci aka mishi Amman sam ya Bude idanu tangararas,



Da haka suka samu drip in ya kare Yana ta uban Mita,doc ya cire tare da mishi adduar samun sauki sannan ya yi ficewar Shi,


Cikin hanzari Sen ya mike sannan yace Kabiru na shiga uku wasa wasa batan yarinyar nan Yana son Zama serious fa,wai ina Nadeeya ta ne ya kare kamar zararre,


Sen don Allah Ka kwantar da hankalin Ka za a same ta ba dai an danka komai gurin Jabiru ba just trust him yaron yasan akin Shi,


Are you talking about trust I should trust who Wanda Ka kawo, don't forget Kabiru kai Ka kawo mun Bashir kace I should trust him with my daughter na yarda nayi trusting and now kana ganin abunda ke faruwa,


Can you stop blaming me for crying out loud na gani ba dole nayi maka ba akan sai kayi trusting Bashir kawo Shi nayi kace yayi maka kaima so ni miye nawa laifin a ciki,Yana kokarin bada amsa suka ji sallaman Alh Salis,


Saida suka gaisa sannan ya shiga jajantawa Sen wai garin yaya ma haka ta faru daman babu tsaro ne a cikin asibitin,


Sai da Sen ya sauke numfashi sannan ya shiga baiwa Abokin na Shi labarin da Doc Bashir in ya bashi sannan ya kare da sanar masa ya Sanya anyi arresting in su,


Goshi Alh Salis ya dafe sannan yace oh Allah mun gode maka masifu dai haka nan daga wannan sai wannan,ko ina ma yarinyar take yanzu oho,ko tana cikin wani hali sai Allah ubangiji ya sa tana hannu na gari,


Ka Bari dai Salis wlhy me hanani cin mutuncin likitocin nan sai Allah na rantse da girman Allah ko a dawo mun da yarinya ta ko kuma a ga babu dadi a cikin garin Bauchi nan,


Da sauri Alh Kabiru ya tsayar da Shi domin ya San halin Aminin nashi muddum ran Shi ya Baci toh Baya iya sanin abunda yake fada ma,kafin ya je ya saki ba yayi Barin zance,


Cikin kwantar masa da hankali yace duk komai zai wuce za a ganta Ka yarda da ni,Bari na Kira Shi na ji ya Ake ciki yanzu,da haka ya sanya waya tare da dannawa Jabiru Kira,


Ringing biyu ya dauka,cike da ladabi ya gaida Shi sannan ya ke sanar masa tun dazu yake ta Kiran layin Sen Baya shiga,dan tsaki Kabiru ya ja sannan yace ya Ake ciki an ganta kuwa,


Goshi Jabiru ya dafe sannan yace gaskia ranka ya Dade wannan suna da mugun taurin Kai har yanzu Basu ce komai ba na sanya a shiga a ladabtar da su dole sun suyi magana I promise you bara a kai zuwa gobe ba sai sun fada mana inda suka kai Nadeeya,ace wa Sen ya kwantar da hankalin Shi yar Shi kamar ta ma dawo gida ne,toh shike nan Ka turo mun da account details in Ka kar Ka mance da haka suka yi ending call in,




A can cell kuwa kafin zuwa yamma kamannin Kareematu da Bashir ya soma canza wa sabida irin bugun da suke ci,domin Jabiru cewa  yayi sam kar a nuna musu sassauci a yi musu dukan da har sai ta Sanya su sun Fadi gaskia,



Kareematu tai kuka kamar ranta zai fita ta tsinewa Bashir ya fi kwando dubu,domin babu Abu mafi ciwo kamar a tuhume Ka da abunda Baka ma da masaniya a kanta,tayi nadaman zuwan ta, da ta sani for the first time in her life da ta ji maganar Abdul da Khairat inta kila da yanzu tana gida ta baje ta Sanya su yi Mata fifita,Amman sabida son zuciya Akan kudin da be taka kara ya karya ba ta jefa kanta a matsala,ita ba yi suke da makota ba balle tace za ta neme su su bada sheda Akan ta,Abdoul kuma bata ma San taya za ta soma sanar masa ba,domin tambayan shine tun farko miye hadin ta da Bashir tana matar aure upon all mutanan asibitin ya zabe ta tana karamar nurse wannan magana ko mara kai ya ji dole sense in Shi ya hasko masa wani Abu na daban......




Asaalamu alaikum


Ina fatan mun wayi gari Lafiya ubangiji ya sa haka ameen,



Ina matukar godia da sakon nin ku masu Kira duba ya jiki na masu mani addua ubangiji ya amsa ya kuma Saka da Alkhairi,Allah kuma ya bar zumunci,



Alhamdulilah jiki na Fara Jin sauki duk da har yanzu ina kwance,ina cigaba da baran adduo'in ku😔🙏🏻,ina kuma me Baku hakurin jina shiru da kuka yi komai yar lafiya ne, ubangiji ya kara mana lafiya da Nisan kwana me amfani,



Banyi alkwarin typing kullum ba domin ko nace Zan yi wahalar da kai na da Ku kawai Zan yi don ba fahimtar komai za kiyi ba Amman in sha Allah in har na warware za Ku ji ni,na gode sosai da kaunar Ku gare ni,



Ina yi wa kowa fatan Alkhairi🙏🏻

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


.......


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Don Allah in har kin San ba karatun book ina da commenting bane zai kawo ki toh Kar kiyi joining,haka zalika Maza Don Allah stay away from my group domin na Mata ne xallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


         08100046388


.........

        Page twenty- eight


***********



Doc Nameer******



A gajiye Nameer ke driver  domin drama in da Sen yayi creating tun safe ma ya Isa gajiyar da su,Habeeb da ke xaune gefan Shi ke ta zuba mishi hira Wanda da eh ko aa kawai yake amsa Shi domin Rabin hankalin Shi na gurin Nadeeya,


Shoulder in Shi Habeeb ya taba Wanda ya sanya Shi saurin juyowa tare da cewa Nadeeya,


Da kallon mamaki Habeeb ke bin Shi da Shi,goshi ya dafe tare da yin parking sannan yace ya aka yi ne Habeeb,


Nameer wat the hell is wrong with u ne,I have been talking since Ka share ni and yanzu Ka Kira ni da Nadeeya,


Dan kallon Shi yayi sannan yace a yaushe Kai dai kawai sabida an wuni maganar ta ne ya sanya kake ji kamar na Kira sunan ta,


Hmm wlhy ko kaffara bazan yi ba Doc Handsome akwai abunda kake boye wa,and am very sure Nadeeya na ji Ka Kira ba wani kunne na bane,


Shi dai Nameer be kuma Kula Shi ba mota ya ja tare da nufan gidan Habeeb in,Saida suka iso sannan yace da Shi Bari ya koma,


Nan ko Habeeb yace be san zance ba ya Shigo Muhibba ta gama abinci su ci sai ya wuce,ganin yanda ya matsa ne ya sanya Shi bin Shi cikin gidan,


A nan parlor inta suka yada zango,nan ta fito da warmers a hannun ta sanye da fararan kayan nursing,alamu daga aiki ta dawo ko kayan bata Kai ga cire wa ba,


Har kun Shigo shine tace tana smiling tare da nufan dining area in su,aa my love kawo mana nan kawai wlhy gajiya ce jikin mu sosai,


Bata ce komai ba ta dawo nan gaban Nasu ta Aje sannan ta gaida doc cike da sakon fuska ya amsa Mata,tare da tambayan ina baby,Yana bacci shine abunda ta amsa masa tare da mikewa,


Ke dai Hibbaty har yanzu ba a cire uniform ba,wlhy Ka Bari kawai yau din nan Nima a gajiye na dawo yanzu nake son yin wanka na canza kayan,daga haka ta shige kitchen tare da karasa Ibo musu abubuwan da za su bukata na cin abincin sannan tayi shigewar ta daki,


Nan ko Habeeb ya ware hannu ya shiga cin tuwon semo da miyar vegetables da ya ji Nama da kifi ga cup cike da zobo me sanyi a gefe,


Doc Nameer dai ya kasa Kai ko Loma daya,Shi be ga wautar Shi ba sam Saida ya dauko ta,toh ba tsayawa yayi dogon nazari ba kawai ya biye wa abunda zuciyar Shi ta Raya mishi ne,gashi yanzu duk ya gagara sukuni,


Ganin har yayi Rabin plate Nameer ko loma daya beyi bane ya Sanya Shi tsame hannun shi,sanann ya ce doc Nameer don Allah tashi kayi tafiyar Ka tunda har ni Baka dauke ni da mutunci kamar yanda na dauke Ka ba,



Da mamaki Nameer yace haba dai ban gane me kake Fadi ba kamar ya,


Eh kamar yanda Ka ji ace tun yau da safe ne nake bi dakai Ka sanar da ni damuwar Ka for Allah sake ko ban zamo silan daukewar sa AI na taya Ka roko gurin Allah amman sam kaki,is like you don't trust me or ko kana ganin ban Kai in san damuwar Ka ba,Wanda hakan ba karamin batan Rai yake ba,yanda na dauke Ka bazan so ganin Ka cikin matsala ba,domin ni a dan uwan Jini na dauke ba not just a friend,but is like ni ba haka nake gurin Ka ba, whatsoever ke damun Ka I promise not to ask again ubangiji ya yaye maka damuwar Ka ya kare tare da mike wa,domin har ga Allah abun ya bata mishi Rai,bubu dadi kana tare da mutun kuma kana ganin Sarai Yana cikin damuwa Amman ya boye maka,sai Ka ga kamar be yarda da Kai bane,



Hannun shi ya riko sanann yace haba Kai kuwa Habeeb toh miye abun fushin,


Yaya baran yi fushi ba Nameer a problem share is a problem solve Kai kan,Ka san two heads are better than one,ni sakar ni in Ka ga dama Ka ci abinci Ka yi tafiyar Ka ni na tafi dakin Mata na,


Dan murmushi Doc Nameer yayi sanann yace in Ka tafin toh Waye zai yi solving problems in nawa come back and seat down let us talk man to man,


Habeeb be ce komai ba face dawowa da yayi ya zauna Kusa da Nameer in sannan yace ina Jin ka,



Actually ban san taya zan Fara maka bayani ba,I don't even know how to explain myself,and I don't know da wani Ido ko fassara za Ka yi mun but trust me wlhy nayi ne with pure intentions,


Da Ido Habeeb ke bin Shi kafin ni fa Ka Sanya ni cikin duhu go straight to the point,


Numfashi Nameer ya ja sannan yace Habeeb I do trust you saisa Zan sanar da Kai damuwa ta don Allah don't let me down,da Kai ya amsa Shi domin har ga Allah Shi ya ma Fara Jin tsoro toh me Nameer in yayi haka,


A hankali ya ce Habeeb Ni ne na dauki Nadeeya,a zabure Habeeb yace Whatttt,


Nameer  Ka kuwa san abunda kake Fadi kuwa are u mad or something taya za Ka ce Nadeeya is with you ,how comes a ma tayaya a yaushe Akan me yasa,shine duk abubuwan da Habeeb ke Fadi,


Mikewa shima Nameer in yayi  tare da dafe shoulders in sa sannan yace I can explain but seat down first,


Nan take ya kwashe tun farkon haduwar Shi da Nadeeya har zuwa jiya da ya dauke ta daga hospital tare da tsitatar da ita daga mutuwar dole da Afzaal ya Sanya Bashir yayi mata,


Baki Bude Habeeb ke kallon Shi kafin ya ja ajiyar zuciya sannan yace lalle wannan doc Bashir in Ashe Dan iska ne,


Tambaya ta a nan shine why Baka sanar da mahaifin ta ba and akan wani dalili zai Sanya miji ya so ganin bayan matar Shi me tayi masa,


That wat I want to know Habeeb haka kawai nake Jin rayuwar yarinyar nan Yana cikin hadari,and maganar gaskia at this point ban san who to trust ba,haka kawai nake Jin a jiki na kamar Shi uban nata shima son cutar da ita yake yi,kawai I don't know why nake Jin bazan iya trusting kowa da ita ba,


Shiru duk suka yi kafin Habeeb yayi breaking Shirin da cewa Nameer kana son Nadeeya ne??


Da sauri ya dago tare da nuna kanshi kafin yace haba haba nooo ba wannan maganar kawai dai ji nake kamar ya za me mun dole na taimake ta and I don't know why Is just like kamar ina da strong connection with her or something,ya kare yana shafa Kan Shi,



Dan murmushi Doc Habeeb yayi sannan yace ban taba ganin actor irin Ka ba,Ka dauke yarinya ka Sanya dan iskan can a wani hali,na san Yana can hannun su Jabiru wlhy uban Shi za su ci,ya Kare Yana dariya tare da haskako fuskan Bashir in,


Kai kawai Nameer ya girgiza domin Habeeb ba dai mugunta ba,kafin yace can you help me pls,


Say it out Allah ya sa Zan iya,


Madam za ka bani Aron ta,pls ta samu ta je ta yi wa Nadeeya wanka a samu a canja Mata Kaya tun jiya suke jikin ta,na san by now sun dame ta,


Sure Bari na Kira ta,AI dole su dame ta ina za Ka bar ta ita kadai,ya kare tare da shige wa dakin Hibban,ba dadewa suka fito da dan first aid kit in ta,tare da babyn su a hannun Habeeb in,mamaki ful ranta a yaushe Nameer in yayi aure ba ta sani ba,da haka suka shige mota har ya tada motar tace ya tsaya tai mantuwa,da sauri ta koma ciki tare da dauko simple brown gown me hade da cap in Shi sabo gal sai kamshi yake zubawa sannan ta dawo suka taho,



    3 Days Later*******


Kwanakin ukun nan ba karamin azaba Ake ganawa su Bashir da Kareematu ba,oga Jabiru ya dage by fire by force sai ya samu information out of them,


Kareematu ba karamin kuka tayi ba barin ranar da Abdoul ya zo domin ya samu labarin abunda ya faru a asibitin su,babu yanda be yi ba Akan a bada bail In ta Amman sam Jabiru yace bare yu ba,karshe ma rashin mutunci ya karta wa Abdoul Wanda Saida ya sanya Shi kwalla da haka ya bar police command in tana kuka tana rokan Shi Kar ya tafi,Shi ya Rasa gane wannan rashin ji irin na Kareematu da ta daura wa kanta tun tana budurwa Allah yayi ta mace me shegen kadadi rawan Kai da shegen son abun duniya,abun haushin kuwa ubangiji yayi ta ba yar gidan uban kowa ba,sai shegen fadin Kai da hangen nesa,


Zai iya cewa kaddara da blind love da kuma rabon su Khairat ne ya hada auran su,domin rawar Kai kam ko kadangare nan ya ga Kareematu ya bar ta,


Aure na soyayya suka yi domin ya kasance Dan unguwar su ne wanda zai iya kiran sunan kaunar da yake Mata akan jarabawa,


Yayi matukar mamaki da ta saurare Shi tun ranar farko,wai gamon Jini daga Allah soyayya suka yi me tsafta domin Abdoul irin social uztaz in nan ne,sannan kuma malamin makaranta ne,


Haka ko da suka yi aure duk da rashin kunya da rawar kanta suna Zama lafiya har ta kammala karatun ta na Nursing wanda Shi ya tsaya Mata kai da fata domin har rancan kudin banki ya karbo duk don Faranta Mata,


Daga sanda ta samu aiki toh wannan lokacin suka yi sallama da farinciki don tunda ta Fara haduwa da doc Bashir ya Fara bude Mata idanu da fari ta ki yarda Amman ganin irin barin kudin da yake Mata,Wanda a lokacin samun Abdoul yayi Baya domin gidan da suke ciki ma Saida Shi yayi ya biya bashin bankij da Ake bin shi suka koma na haya,


Da haka Bashir ya siye zuciyar ta shike nan suka dinke ko bata da duty sai ta je hotel sun sheke Aya ita da doc Bashir,a sunan ta ta fi Night duty,Wanda Abdoul Sam be da masaniya kan irin wannan mugun dabia da Kareematu ke aikatawa,tun tana yi da Bashir har idanun ta suka kuma budewa ta Fara bin wasu Maza Jen can daban in har zaka bata kudi toh tabbas za ta Bude maka kafa,idanun ta gaba daya sun rufe neman duniya kawai ta Sanya a gaba,



Tsawa me razanar wa Oga Jabiru ya daka musu tare da fadin Ku wai ga Ku yan iska masu taurin Kai ko,bara Ku sanar mun yanda kuka kai yarinyar mutane ba,



Cike da kuka jiki duk tsami Baki duk ya kumbura,Kareematu tace yallabai wlhy tallahi iyakan gaskiar ke nan ni dai ina shiga duba ta time to time bisa umurnin doc Bashir amman ba ni na dauke ta ba,


Kin taba ganin criminal yayi confessing laifin Shi daman,har yanzu Baku bugu bane kila sai na sanya a tsinke muku gashin jikin ku ko an sanya muku shocking zaku samu Ku Fadi gaskia,



Cikin kuka doc Bashir yace yallabai kayi wa girman Allah Ka bar ni haka wlhy ko zama Bani iya wa sai kwanciya,


Dariya Jabiru ya sheke dashi kafin yace AI kadan Ka gani in har junin Ku taurin kai ne gaba kwanciyar ma kasa ta za kayi,


Sabida zarmewar zuciya ina Ku ina Satan yarinyar dan takaran gwammna,uban me za kuyi da ita,a taya ma zaku ba Ku bane dole a cikin Ku akwai mugun da ya dauke ta, domin duk asibitin sun Fadi daga Kai sai ita wannan munafukar ke shiga gurin ta,ko bayan Ku akwai Wanda ya San pin in shiga dakin,



Cikin zabura Kareematu tace yallabai wlhy na tuna akwai wata kawata a asibitin Nurse Zaituna rannan ita na baiwa abincin Nadeeya ta kai Mata bayan kwana biyu kuma shine aka neme ta aka Rasa, yarinya ta babu lafiya ya Sanya through out ban zo aiki ba,


Mikewa Jabiru yayi tare da kwada wa Kareematu mari me zafi da kara sanann yace shegiya dan uban ki duk kin san da haka kika tsaya bata mana lokaci a ina zan samo Zaituna ko miye sunan ta,


Idanu cike da kwalla tace tana cikin asibiti ita ma maaikaciya ce a can,


Daga haka be kuma ce musu komai ba ya Sanya Kai tare da bada umarnin a maida su cell,tare da daukan wayar Shi ya shiga Kiran layin Alh Kabiru,



**********Sen Rilwanu



Zaune yake a parlor ya zuba uban tagumi,kayan cima ta alfarma ce a gaban Shi Amaman sam ya kasa cin ko Abu daya,past days in nan Yana nan kawai ya Rasa me ke masa dadi a duniya,ya Sanya ya Hana kowa zuwa ganin Shi Banda Alh Kabiru sai Salis kawai yake iya gani,



Tunani yake toh wai shin Ina Nadeeya take ne ya shiga uku yarinyar nan in har bakin ta ya Bude Yana wani hali shike nan tashi ta kare muddum asirin Shi ya tonu Zaman garin Bauchi sai ta gagare Shi,wata yawu me daci ya hadiye da kyar tare da lumshe idanu,abun haushin wannan masifa ta Fado mishi ba time in haduwar kungiyar su ba,he is very sure da zai ga Odugwu da matsalan Shi ta kare domin sam babu wani effort da su Jabirun nan ke making,abun haushin kuwa shine ba a ganin Odugwu in ba ranar haduwa ba gashi shi sam Allah be bashi juriya ba yana shiga cikin matsala take nuna masa,



Fadowar da ya ji anyi a jikin Shi ana kuka ne ya sanya Shi zabura daga tunanin da ya fada tare da bin Afzaal dake kuka hawaye biyu biyu Akan kirjin Shi,


Da sauri ya Ciro Shi sanann ya bi Shi da kallon mamaki Yana Kai Afzaal uban me ya same Ka zaka zo kana irin wannan kukan,



Cikin kuka sosai har da shesheka yace Daddy Ashe Ashe,Ashe me Sen ya Fadi xuciyar Shi na bugawa,



Cikin kuka yace daddy Ashe Nadeeya ta ta mutu shine aka boye mun ba a a fada mun ba,Banda yau da jiki na ya Bani ba lafiya ba nace gwara na dawo na gani,



Be Kai ga karasawa ba Sen ya dauke Shi da Mari Tasssss kake ji,da sauri ya dafe kumatun Shi tare da mikewa,


Shima mikewar Sen yayi sannan yace Dan uban Ka ina Ka ji labarin Nadeeya ta mutu,shege me bakin Yan wuta.........





Assalamu alaikum🥰👏🏻



Ina fatan mun wuni lafiya ubangiji ya sa haka,



Alhamdulilah jiki Yana ta sauki na gode sosai da adduo'in Ku masu Kira masu turo mun sakon ni ubangiji ya Saka da alkhairi,Allah kuma ya bar kauna,



Ina me Baku hakurin jina shiru da kukai kwana biyu,Amman yanxu Alhamdulilah da sauki za kuna ji na akai akai in sha Allah,



Ina yi wa kowa fatan Alkhairi❤️


Sai zuwa gobe in me kowa me komai ya Sanya mun Kai.

😭😔 UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


.........


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Don girman Allah in har kin san ba reading novel ina and commenting bane zai Sanya ki joining to kiyi Zaman ki na gode ba sai kin Shigo ba,haka zalika Maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah 🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


       08100046388


..........

          Page twenty- nine


***********



Da matukar mamaki Afzaal ke kallon Sen toh ko dai dimaucewa yayi ne ya san dole ya ji a jikin Shi daman in Nadeeyar ta mutu Amman ya zai yi toh,aikin Gama ya riga ya Gama,


Domin Shi har ga Allah duk tunanin Shi na bashi Nadeeya dai babu ita a wannan duniyar,doc Bashir ya cika aikin da ya bashi,abunda ya Sanya Shi kirkiran tafiyar karya ke nan ya kashe wayoyin Shi Baki daya akan sai an yi kamar kwana uku da mutuwar sai ya dawo ya zamo comfort zone wa Daddy ya san in no time xai mance da mutuwar although ya san zai iya affecting in Shi both mentally and physically but with time zai mance,


Ba magana nake maka,kana jina Ka share ni wani Dan iskan ne ya sanar da Kai Diya ta babu ita ta mutu,Sen ya kare Yana tsare Shi da idanu, 


Kan Afzaal ne ya daure domin Shi fa a tunanin Shi ta mutun,toh yanzu kuma da ya ji bata mutu ba dole Sen ya tambaye Shi a gidan uban wa ya ji Nadeeya ta mutu,ko Karan hauka ce ta cije Shi bare ce Shi yace a kashe ta ba,


Suna cikin haka sai ga shigowar Alh Kabiru,kafadun Afzaal ya dafe sannan yace na san dole Ka shiga rudu but matar ka ba mutuwa tayi ba my son sace ta aka yi an neme ta Sama da kasa an Rasa cikin hospital in,


Idanu ya zaro tare da cewa Whattt impossible,a garin yaya aka sace ta,tana ina kuma yanzu,


Calm down case in na hannun Jabiru yace mana mu kwantar da hankalin mu Nadeeya za ta fito,ya kare tare da neman gurin zama,


Aboki na,Kai dai har yanzu bara Ka bar zafin nan naka ba,zo Ka zauna na zo da labari me dadi,


Tsaki Sen ya ja sannan ya zaunan Yana me fadin yaron nan kayan cika ciki gare Shi, banda iskanci ya zo mun da zancen wai Nadeeya ta mutu,ana ba guri Dan uban Shi Yana ya kwanta,


Kabiru dai Kai ya girgiza Yana jinjina ashar da wulakanci irin na Sen,yanzu Kai a haka za Ka Zama governor in a gayyace Ka taro gurin speech kana auna wa bayin Allah ashariyar Ka ta fama,kamar Dan maguzawa,


Ba sai na zagi uban da zai hana ni Zama governor in ba,yi sauri Ka Fadi mun abunda kace za Ka fada,



Zama Alh Kabiru ya gyara sannan yace yanzu Jabiru ya Kira ni wai sun kamo wata Nurse me suna Zaituna yanzu haka tana gurin su,Kareematu tace rannan ta ce ta shiga dakin Nadeeya Kai Mata abinci so ta shiga layin Yan zargi,


Tsaki Sen ya ja sannan yace wannan Bashir wannan Bashir akwai Dan iska wlhy,ni su Gama duk haukar su,su fito mun da yarinya shine kawai bukata na,



Afzaal da ke labe Yana Jin su a daki,wani tukukin bakin ciki ne ya tokari kirjin Shi,wato shi Bashir zai yaudara ya karbe masa Yan kudade har million 55 dan uban Shi kuma a banza,bata yu wa dole ya san abun yi bare yu ya ci masa kudi a banza ba,ya kare Yana huci kamar wani Wanda yayi race,




********Police command


Har cikin hospital oga Jabiru ya tura yaran Shi suka kado mishi keyar Zaituna tana tsaka da aiki,ba karamin tsorata tayi ba,ba ita kadai ba hatta sauran workers in sun tsorata ganin yanda Ake musu daukan dai dai,


Ko da aka kawo ta sai da ya tambayi Kareematu ita ce wannan,cikin sauri ta amsa da ita,


Ba karamin kuka da tsinewa Kareematu Zaituna tayi ba Jin sharrin da take neman daura Mata,


Fadi take Amman wlhy ke dai Kareematu akwai yar iska ki Rasa Wanda zaki wa sharri sai ni,me na Miki yallabai wlhy sau daya na taba shiga cikin dakin kuma itace ta Fadi mun pin in shiga abinci kawai na Kai Mata,Amman da ke butulu ce ita ka ji abunda take Fadi,Allah dai ya wadaran ki Kareematu,


Ke dallah rufe wa mutane Baki sai dai ke Allah ya wadaran ki ba ni ba,sharri nayi Miki AI kin shiga dake da wannan shegen kune last in shiga gurin ta,


Tsawa Jabiru ya daka musu sannan yace a zo a maida su cell har yanzu Basu Gama cin uban su na more especially Zaituna a tabbtar an lallasa ta in tayi laushi za tayi bayani,tana kuka tana Ihu haka aka kwabe ta ko Dan kwali babu aka watsa ta cell aka hau kirba kamar an samu sakwara,



Kwanan ta uku a hannun su,Banda uban bugu babu abunda suke ci,kuka kam sun yi Shi har Basu son adadin Shi ba,doc Bashir abun ba karamin mamaki ya bashi ba sai yanzu ya tabbatar da iyalan Shi Basu damu da Shi ba kamar yanda shima ya ke watsar da lamuran su,domin tun sanda aka daure Shi ko kafar makocin Shi be gani ba balle na Yara ko matan Shi,tabbas yasan duk rintsi za su samu labari domin duniyar yanzu kana kwance gadon baccin Ka labari ke iso Ka,be taba sanin mugun Zaman na su ya Kai haka ba sai yanzu wato Basu damu ba ko a raye ko a mace yake,ikon Allah abunda ya fi masa ciwo ke nan duk rintsi dai a Kan idanun Shi mijin Kareematu da yaran ta ke ta sunturin zuwa ganin ta suna me kwantar Mata da hankalin in sha Allah za ta fito haka ma Zaituna Amman Shi kam wai ko aboki be zo masa ba,



*******Doc Bashir Ubaidullah


Shine cikakkiyar sunan dan asalin garin Bauchi ne a karamin hukumar Burkacuwa,mutum ne Shi me tsananin son Mata da kuma abun duniya,


Like Akan mace toh ranshi ma zai iya bada WA,matar Shi ta farko auran Hadi aka yi musu Wanda sam be kaunar ta amman aka dage da auran a haka ya aure ta ubangiji ya azurta su da Yara 4,sannan ya Karo ta biyu Wanda yake Kira zabin nashi,


In takai ce muku zance dai Bashir Mayen Mata ne Wanda ya sanya Shi aure da sake,domin ya auri Mata sun Kai 10 a rayuwar Shi,likita ne kwararai na kwakwalwa,wanda kila abunda ya dan taba Shi ke nan kun san in karatu tayi yawa sai a hankali lol,


A irin son matan Shi ne ya sanya Shi Fara bin staff's in Shi,watsatsu irin Shi su bada Kai wasu su ki,kamar na Doc Haneefa babu yanda be yi Kan ya tatile ta ba sam taki ya Sanya sam tashi da ita Basu zo daya ba ya tsane ta haka ita ma ta tsane Shi,


Kareematu tafiyar su ta zo daya ne ta hanya mugun son kudin ta Shi kuma irin macen da yake so ke nan ya Sanya ya maida ta kamar matar Shi kullum tana cikin cewa ta tafi night duty hospital alhalin suna can guest house in Doc Bashir suna tsabon Allah in da yake Mata barin kudi domin babu karya Yana samun satisfaction iya makura a gurin Kareematu,


Mind you ko don an canfa ne daman an ce liktoci akwai son Mata sannan akwai su da mako Basu rike iyalan su at all(am sorry ba wai na Fadi don cin fuskan doctors bane base on abunda nake ji kuma nake gani ne,so ayi mun afuwa pls,ba cin mutuncin doctors nake ba ko wani aiki akwai na kwarai akwai bata gari🙏🏻),


Yaran Shi sun Kai 10 gaba daya in Ka gansu bara Ka dau uban su Yana aiki Yana daukan albashi na,ya sakar wa matan ragamar gidan domin kwakwaran cefane wannan ba yi yake ba balle aje ga biyan sch fees da kuma sauran abubuwan bukata na rayuwa,


Ko wace uwa ita ke fafutuka Akan yaran ta don ta samu ta rufa musu asiri,


Gidan da suke ciki wannan bara Ka dauka nashi bane,in kana son ganin bacin ranshi to Yana cikin iyalan Shi ko kuma sun yi demanding in abun kudi toh nan zai ta hada fuska Yana masifa,karatu kuwa be damu suyi ko Kar suyi ba,in uwar yaro tana da shawar boko sai ta Sanya Dan ta Amman Shi babu ruwan Shi,


Kudin Shi wa kanshi ne da kuma Matan banza,in one word doc Bashir dai MUGUN MIJI ne mara tausayi mara adalci sannan mara mutunci me tauye hakkin family in Shi,ya Sanya gaba daya ya fice musu a rai daga yaran gidan har matan gidan babu Wanda ke Jin dadin Zama da Shi gaba daya ya fice musu a rai,wannan ke nan,



Roka yayi Allah Annabi a Bude Shi ya je office in oga Jabiru akwai bayanin da zai mishi,domin bayan dogon nazari da yayi,gaskia Baya ji zai iya kara kwana daya a cell in nan ya gaji matuka gayya,burin Shi ya gan Shi ya zama free man shima,in har ya tuno kudadan da ke shake a cikin account in Shi sai ya ji Rabin azaban duk ya bar jikin Shi,Dan uban iyalan Shi Yana fitowa yau ko gobe in ya je asibiti ya dan karbi treatment sai airport bare zarce ko ina ba sai Los Angeles dole ya je ya samu kamar Sati biyu Yana hutawa a jikin fararan fata,



Da kyar da sidin goshi wani dan sandan ya Bude Shi bayan yayi mishi alkwari zai bashi kyautan  10k in ya fito,


Jiki a mace Yana jan kafafu ya nufi office in Jabiru,da sallama ya shiga,


In da ya tadda Jabiru zaune Yana Shan Maltina me sanyi ga namar suya a gefe Yana afawa,


Da tsawa ya ce kai uban me ya fito da kai,Saida Doc Bashir ya hadiye yawun kwadayi sanann yace yallabai na zo magana da Kai ne don Allah in bara Ka damu ba,


Be Jira amsan Shi ba ya cigaba da fadin yallabai jiya da na kwanta bacci nayi wani dogon tunani da nazari,tunda duk cikin mu ukun nan babu Wanda ya aika laifin nan toh tabbas na san shine zai aika ta domin tun zuwan Shi na ga alaman Yana yawan shige shige Yana son sanin komai ya kare Yana lashe Baki domin babu karya yawun Shi ya biya ,


Can in Jabiru ya aje tare da mikewa tsaye sanan yace Waye and for all this while Ka san Wanda ya aika laifin nan kake ta wahala mu har muna Shirin cike muku file mu aika Ku court ranar Monday,


Idanu Bashir ya zaro sannan yace yallabai na tabbatar ko da ba Shi ya sace ta ba toh dole ya san wani abu akai,


Waye Shi fada mun sunan Shi da hanzari kuma a ina yake,


Saida Doc Bashir ya nemi gurun zama sanan yace yallabai sunan Shi Doc Nameer ,duk tare muke aiki haka kawai zuciya ta bata yarda da Shi ba,kuma ina ji a jiki na kamar Shi ya dauke ta,


Da Ka san da haka Ka tsaya bata mana lokaci a ina za mu same Shi,


Yallabai ina na samu fuska gurin Ka kullum duka fa kake Sanya ayi mana,da Shi na ke breakfast nayi lunch harda dinner fa,Haba don Allah ba dole tunani na ya dauke ba,


Tsawa Jabiru ya daka mishi domin ganin ya Fara wuce Gona da iri,sallamar Shi yayi kan ya koma cell in Shi,za su koma asibitin yanzu domin bincike,da haka kuwa ya fice daga office in Yana me tsine wa oga Jabiru a ranshi na ranshin bashi suya da yayi,(ni ko nace kila Kai Ka Siya masa ai),


Nan ya tara yaran Shi babu bata lokaci be Jira ya sanar wa Sen ba ma domin Shi kanshi case in nan ya Fara fita masa a Kai,be taba Kai wa iyanzu Yana solving case babu solution ba sai this time around Yana adduar Allah ya sa zargin Bashir in ya zamo gaskia a rufe case kowa ya huta,


Ko da suka isa Kai tsaye office in Nameer suka nufa lucky them be Riga ya tafi gida ba,


Sama da kasa Jabiru ke kare masa kallon wulanci kafin cikin Isa da izza yace da Shi you are under arrest,


A nutse doc Nameer ya dago tare da kare wa Jabiru kallo sannan yace da Shi wa alaika assalam,


Kallon kallo Jabiru ke yi da yaran Shi kafin ya sheke da dariya sannan yace da kyau ustaz mike a Sanya maka ankwa mu wuce da Kai gidan Ka sauri muke,


Mike wa Nameer yayi tare da cewa wannan kuma shine impossible Kai look at me very well I know my right KO su Bashir da Kareematu da kuka kame su suka so suka kuma bar Ku,Amman ni kam na rantse da girman Allah Baku Isa kama ni ba domin babu abunda nayi,ya kare tare da koma wa ya zauna,


Kai Jabiru ke jijigawa domin ganin irin wannan confidence na yaron nan,Shi sai ma ya Fara bashi tsoro,irin wannan Ka tabo mutum ne Baka san Waye Shi ba,Amman sai ya daure yace,



Ka tashi mu tafi gidan Ka na karbo search  warrant domin Bashir ya sanar mana Yana zargin Kai Ka sace Nadeeya,


Dariya Nameer yayi har hakwaran Shi suka fito kafin yace a taya zan sace Nadeeya miye Hadi na da ita,hasali ma ni ko haduwa da ita ban tunanin mun taba yi,kawai dai yayi cooking up stories ne koh mun je gidan nawa am very sure babu abunda za Ku samu so a shawarce Ku koma abun Ku domin Bashir ba isashen hankali yake da ba,don anjima ma zai iya cewa Shi Sen da kanshi ya sace diyar ta Shi,ya kare tare da sipping in bottle water,


Duk bayanin nan be gamsar da oga Jabiru ba Saida suka sako Nameer a gaba Wanda sam be yarda sun ci mutuncin Shi domin idanu ya Bude musu,a motar Shi suka bi bayan Shi har suka iso unguwar nashi,


Gate in ya Bude sannan suka Shigo cikin gidan,zuciyar Shi sake sam babu tsoro ko wani alamu da zai nuna bayi da gaskia,


Kofar palor ya Bude sannan yace da Jabiru mu kalli search warrant in da aka bada,nan ya mika mishi Saida ya karance tsaf ya ga ba cooking up stories suka yi ba sannan ya matsa yace su shiga,su bincike ko ina,Amman da sharadi ko tsinke nashi ya Rasa ko aka lalata mishi wanni abun in the process in neman ta wlhy tallahi sai yayi Karan su court,da haka suka wuce, oga Jabiru yace wlhy kowa yayi taka tsan tsan in mutum ya fasa Abu ko ya lalata uban Shi zai ci,


Guri Nameer ya nema ya zauna tare da daura daya kan daya ko a jikin Shi,


Nan ko suka shiga dube dube da ke ya musu warning ya Sanya Basu masa binciken hauka ba a sannu suke komai ko ina sun duba saidai Sama ko kasa sun Rasa,babu ma wani alamun da zai nuna Nadeeya ta taba rayuwa a gidan,


Bincike sukai sosai Amman duk a banza domin Basu Sami komai ba,a haka suka fito,


Ina take kila kun same ta Nameer ya tambaya cike da shakiyanci,


Kwafa Jabiru yayi sannan yace Allah ya taimake Ka ba mu sami komai ba da Ka yaba wa Aya zakin ta,domin yanda kake da yawan maganan cikin minti daya Zan Sanya Ka shiru na watanni guda,


Kai kawai Nameer ya girgiza sannan yace officers ga can kofar fita tunda har kun Gama abun da ya kawo Ku you guys should get going daman na fada muku indai zancen Bashir za Ka dauka toh gantali yanzu ya kama Ka,daga haka yayi shigewar Shi cikin daki,ba karamin ciwo Jabiru ya ji ba saidai babu yanda ya iya haka ya tasa Kan yaran nashi suka fice daga gidan tare da daukan alkwarin sai ya ci uban Bashir ya in suka koma police command.



A cigaba da hakuri da ni komai yar lafiya ce,


Ina godia da dumbin kaunar Ku da kuma fatan Alkhairi da kuke a gare ni ubangiji ya Saka da alkhairi 🙏🏻❤️,


Sai gobe in me kowa me komai ya so,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                 BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


.......


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Don Allah in har kin San ba karanta book ina da commenting bane zai kawo ki toh yi Zaman ki ba sai kin yi joining ba,haka zalika maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


        08100046388 


..........

          Page thirty


*********



Doc Nameer*****


Habeeb wai ina Ka Sanya wayan Ka ne tun dazu I have been calling u Baka dauka,


Yi hakuri doc Handsome na shiga wanka ne,me ke faruwa ko Ka Kira Ka ji lafiyar Ajiyar Ka ne,


Murmushi Nameer yayi kafin yace I trust you gee na san tana nan lafiya,kasan me ya faru,


AA sai Ka fada Habeeb yace Yana goge ruwan jikin Shi da towel tare da Zama a kujeran gaban mirror,


As expected kasan yanzu Yan sanda suka bar gida na,


Idanu Habeeb ya zaro tare da fadin Yan sanda kuma na me toh,


Wlhy ina asibiti suka daga ni wai suna son su yi searching in gida na,wai Bashir ya sanar da su Yana zargin ni na sace ta,Saida sun yi late daman jiki na ya Bani za a yi haka Wanda ya tsane Ka toh zai iya yin komai don ya ga bayan Ka, gudun haka ya sanya nace da Kai Zan maida ta gidan Ka don nasan Bashir ba Bari na zai yi na huta ba,


Dariya Habeeb ya Sanya tare da fadin gaskia I salute you my friend kana da brain ni ban taba tunanin abunda ya Sanya ka dawo da ita nan ba,na dau kana gudun zama daga Kai sai ita ne gudun samun matsala,ya kare Yana dariya,


Zan zage Ka Habeeb dan iskanci ko ni na kawo jaraba duniya AI na tausaya mata balle kai kan ka shaida ne ni bana bin Mata,


Jiki da Jini aboki na an Dade ba a Hadu ba,ya kare Yana dariyar tsokana,tsaki Nameer ya ja sannan yace Ka ji da Shi dallah ni lemme shower in zo mu karasa magana domin yanda aka Fara zargi na din nan gwara as soon as possible in dauke ta mu bar garin nan gudun fada wa matsala,thank god yau Allah ya taimake ni,toh shike nan sai Ka iso Nima lemme pray da haka ya kashe wayar tashi,


Kai Nameer ya girgiza da ya shiga dakin nashi ya ga komai Yana nan fes kamar ba bincike aka Shigo aka yi ba,Yan iska ashe mara sa kunyar karya ne, da haka ya kwabe ya shige wanka Yana mamakin me yayi wa Bashir ne da ya tsane Shi har haka,



*********Police command


Rai a matukar bace oga Jabiru ya Shigo cikin police command in,Kai tsaye office in Shi ya wuce tare da bada umurnin a Shigo mishi da doc Bashir,


Jiki na rawa Bashir ya Shigo office in ganin yanda fuskan Jabiru ke a turbune nan take jikin Shi ya bashi ba a dace ba,cikin dauriya yace ranka ya Dade kun same ta,


Mikewa Jabiru yayi sanann yace a gidan uwar Ka muka same ta,ni zaka bata wa lokaci Kai ya kare cike da tsawa,


Nan take ya rude cike da rawar murya yace sorry yallabai kuskure aka samu,ba gidan doc Nameer nake son cewa ba,


Da kallon mamaki yake bin Bashir in kafin yace toh gidan wa kake son cewa,


Yauwa yallabai bayan dogon nazari da na kuma yi na gano Shi Sen da kanshi ya sace ta Dan kawai ya Sanya mu a damuwa ya kuma bata maka lokaci ya Sanya shi cewa mu ne muka dauke ta,Amman am very sure da za Ku je gidan Shi za Ku ganta,that man is very evil aswear to almighty God Yana samun pleasure a yayin da yake azabtar da wasu Kai ne Baka san Shi ba,


Be Kai ga hade lips in Shi ba ya ji saukan Mari tassss,tsaban bacin Rai har idanun Jabiru yayi jawur,


Cikin Ihu yace out of my office nonsense,na ga alama Kai ma brain in Ka ya Fara tabuwa daman an fada mun zaka ce Shi ne ya sace yar sa,Banda hauka taya babban mutum kamar Sen zai sace yar Shi ya daura muku Akan me me zai yi gaining in yayi haka, stupid an Jima ma cewa za Ka yi ita ce ta boye Kan ta ko kuma ni ne nan na sace ta na boye,and I promise you yau sai Ka sha bugun da tunda uwar Ka ta yafe Ka ba a taba maka irin Shi tunda Ka bata mun lokaci sai na fanshe a jikin Ka fice mun a office Wawa kawai ya kare har Yana kumfan Baki,


Sim sim doc Bashir ya ja kafar Shi tare da barin office in Shi wlhy ya gaji ya gaji sosai da irin wannan bakar hukuban da suke ci a hannun wannan mugun Dan sandan da be son darajar bayin Allah ba(ni ko nace Kai kan Ka ba sanin darajar Kan Ka kayi ba,domin duk wanda zai je ya kwanta da matar wani ko yayi kokarin daukan ran wanni ko ya hofantar da lamuran iyalan Shi toh tabbas be san darajar Kan Shi ba balle har wani ya San darajar Shi),



*******Doc Nameer


Saida ya Bari Rana tayi sanyi sanna ya shirya cikin kananun Kaya tare da nufan gidan Habeeb bayan ya hado su tarkacen kayan Wasa da madaran Yara,sai ya siyo ice cream don ya san Nadeeya na so saidai be San ko za ta iya sha ba domin har yanzu jikin nata dai babu wani ci gaba,ko ruwa in Baka yi da gaske ba dawo maka da Shi take in Ka bata,tana nan kwance sai an daga sai an kwantar da tube Ake samun abinci yake shiga jikin ta,Shi ya Rasa wannan mutuwar jiki da ta samu na ba gyara babu dalili,duk wani necessary gwaje gwaje yayi ya gano babu wani matsala tattare da kashin ta ko jijiyan ta Banda brain in ta da ya tabu sakamakon aluran da aka yi ta Dura Mata,to sam ya kasa gane miye ke damun ta da ya haddasa Mata halin da take jiki,


A nutse yake driving Yana sauraran wakar Bunna boy ft Ed Sheeran (for my hands),Yana bin wakan a hankali a haka har ya iso gidan Habeeb in yayi horn aka Bude masa gate ya shiga da motar Shi,


A tsakar gida ya tarar da Habeeb suna Wasa da dan babyn Shi da ba wai ya gama koyan tafiya bane,sai abun ya bashi shaawa nan take ya ji Yana missing little Hanan in Shi,wannan matsalan Nadeeyar ne duk ta dauke mishi hankali kwana biyu be Kira ya ji lafiyar ta ba,


Parking yayi tare da fitowa,gaisawa suka yi da Habeeb in sanann yace da gate man in Shi ya fito da kayan da ke cikin motar Nameer in ya Shigo da su parlor,


Karban babyn yayi sannan suka shigo,na san ko na ce Ka zauna Ka sha ruwa ba yarda za Ka yi ba in ba Ka ga Nadeeya ba mu je suna jiki da Muhibba,


Murmushi kawai Nameer yayi sanan suka nufi dakin tarar wa suka yi Muhibba na fesa wa Nadeeya turare alamu sun gwada wanka ta Gama Mata,


Da kallo kawai Nameer yake bin ta ganin yanda take kwance tana bacci hankali kwance sai tayi masa kyau domin har simple kwalliya Muhibba ke Mata time to time a cewar ta mace ce AI don jinya ta Gama ta bara a Kula da ita ba,


Babu abunda zai ce da Muhibba ko Habeeb saidai fatan Allah ya Sanya su Gama da duniya lafiya domin tabbas Yan uwan rufin asiri ne su,


Tun Ranar da ya sanar musu Nadeeya na gurin Shi Muhibba ta dauke ta kamar yar uwa komai bata kyashin yi Mata,saisa at times Akan ce dadin Zama sai bare domin yanda take kula da ita ko uwar ta sai haka,bayi da bakin gode musu wlhy,


Lah ya Nameer Ka zo ne ta Fadi tana murmushi,


Shi din ma murmushin yayi sannan yace eh wlhy mommyn Fadeel ya dawainiya kuma,na gode sosai ubangiji ya Miki Albarka sanann ya biya ki da Aljannah,


Murmushi tayi domin a rayuwa tana Jin dadin adduo'in nan da Nameer ke Mata kullum,tana matukar respecting in Shi don duk friends in Habeeb zata iya ce wa babu Wanda Jinin su ya zo daya kamar Nameer in kallon babban yaya take mishi,and ba kowa ne za Ka yi mishi abu yayi appreciating har ya San kayi masa ba,akwai dadi duk kankantar abunda mutun xai yi maka Ka gode Ka kuma nuna Jin dadin Ka,shima dai gaba ya samu karfin gwiwa,


Ameen ya rabil Alameen Ka Shigo mutuniyar tayi bacci,


Eh wlhy haka nake gani, ubangiji dai ya Baku ladan jinya,ita kuma Allah ya bata lafiya,Ameen duk suka amsa,sannan suka fito daga dakin,


Nan parlor suka baje ta kawo musu abinci suka shiga ci suna hira irin nasu na abokai a nan ne yake sanar wa Habeeb Yana so in sha Allah tunda gobe Saturday babu aiki Yana ga  gwara ya dauki Nadeeya ya tafi da ita Kaduna daman tunda ya zo be je ba,


Nan take kuwa ran Habeeb ya Baci Akan meyasa zai ce haka,gani yake Yana takura su ko kuma su din sun gaza bara su iya Kula da ita ba,


AA wlhy ko daya Ka fahimce ni ba daidai ba,gani nayi yanda aka Fara binciken nan toh ban san iya yanda zai tsaya ba gwara in dauke ta tayi nisa da garin nan gudun Kar in Sanya Ku a wata matsalar,


Da kyar ya samu Habeeb in ya fahimce Shi be bar gidan ba sai dare bayan yace da Muhibba ta shirya ta da wuri don Allah don asubanci yake so suyi,


Da haka ya koma gida,Saida ya kuma wanka sabida Yana yi na zafi kafin ya gabatar da sallahn Isha sannan ya dauki waya ya Kira Mama,


Idar wan ta ke nan itama tana lazumi kiran nashi ya Shigo,ajiyar zuciya me karfi ta sauke domin yau Kusan kwana uku ba suyi magana ba duk hankalin ta ya tashi addua kawai take Allah ya Sanya Yana lafiya domin ko sun Kira basa samun Shi,


Da sauri ta dauka tare da sallama,amsawa yayi sannan yace ina wuni Mama,


Baba na ba zan amsa ba Ka ga yanda Ka daga mana hankali kuwa ina Ka shiga ne haba baba na,AI ko sako Ka turo in ma busy kake in dai san kana cikin koshi lafiya,ta kare kamar za ta sa kuka,


Numfashi  ya sauke sannan yace kiyi hakuri hajiya mama wlhy ana ta dan rikici ne a gurin aikin na mu,


Subhanallahi ina fatan dai ba da Kai Ake rikicin ba dai ko,


Dan dariya yayi sanna yace haba mama ni kan AI bana rikici da kowa ba da ni bane,


Toh Alhamdulilah ina fatan kana lafiya sanan kuma kana cin abinci,ni wlhy duk hankali na ba a kwance yake da garin da Baka san kowa nan ba,ta kare tana jimami,


Dan murmushi yayi sanann yace hajiya mama ke nan toh ki kwantar da hankalin ki in sha Allah gobe a Kaduna Zan kwana asubanci ma Zan yi da yardar Allah kafin 10 ina gida, breakfast in ki ma Zan ci,


Cike da murna domin ita kanta tayi missing Dan nata tace da gaske kake Babana,Bani son zolaya fa,


Shima dariyar yayi sanann yace da gaske nake mama gobe Zan zo ba ma ni kadai zan zo ba,


Kai dawa ye ta tambaya,mama labarin da tsaho ki Bari sai na iso Zan Miki bayani za ki fi gane wa,


Toh shike nan ubangiji ya kawo Ku lafiya Allah ya tsare hanya,


Ameen thuma ameen Mama tah ina angel take,


Ka ganta can ta gama fitina ta na dake ta na hurga ta gado tayi bacci,


Haba mama nawa angel take da za a Mata dukan da har sai tai bacci ya kare kamar zai yi kuka,


Gidan Ku Baba na yarinya tayi mun bar na bazan buge ta ba,Ka fita a idona da wannan kwalafucin da kake Akan yarinyar nan fa,


Baki ya turo kamar karamin yaro sanan yace shike nan kiyi hakuri sai da safe,


Dariya ta Sanya sannan tace au don nayi fada shine zaka kashe wayar taka ko,


AA mama ba don haka bane fa,Allah ya shirye Ka Baba na da haka suka shiga hira irin ta " da uwa Wanda daga gani za Ka gane akwai tsantsan shakuwa da soyayya me karfi a tsakanin su,Saida suka yi Kusan 1 kafin suka yi sallama ya ya kwanta Yana Jin kamar ya janyo gobe tayi ya ganshi a gida,saidai wani gefen zuciyar Shi na tambayan Shi me zai ce da mama in ta ganshi da Nadeeya, inda ya samu kwanciyar hankali ya San Mahaifiyar tashi akwai saukin Hali da fahimta he is sure za ta fahimce Shi,da haka ya kwanta bacci me dadi ya dauke Shi,



Ko da ya tashi sallan asuba be koma bacci ba,kayan Shi ya hada Wanda ya san zai bukata Saida ya Gama sannan ya fada wanka,bayan ya fito ne ya shiga Kitchen cikin sauri yayi frying egg da plantain sannan ya hada tea ya fito,a nutse yake cin abinci don in yace zai Bari sai ya Isa ya ci abinci zai jigata,domin daga Bauchi zuwa Kaduna ba karamin tafiya bane,


Around 6:30 ya gama hada koman Shi ya zuba a mota,Saida ya rufe ko ina na gidan sannan ya fito ya shiga motar nashi,


Saida ya biya inda yake Siyan masa ya siyo don yayi alkwarin Kai wa mama,sannan ya biya Jifatu siyayya yayi musu sosai wa mama Nadeeya da kuma angel inshi sannan ya dau hanyar gidan Habeeb,


Da isar Shi kuwa ya tarar da Muhibba ta gama shirya Nadeeya cikin dogon Riga,dauko ta yayi zai shimfida Leda tace da Shi AI ta Sanya Mata pampers Kar ya damu har su Isa bara ta yi komai ba don ba wani ruwa sosai ta bata ba,


Godia sosai yayi musu inda a karshe ya dauki kyautar 100k ya baiwa Muhibba sam taki karba Akan ita fa ya wuci haka don Allah ta kula da Nadeeya,da kyar ta karba bayan yace da ita AI ance gaida me gaida Ka ko bare amsa ba,godia tayi mishi sosai don har da kwallan ta,sabida ba karya ta Fara shakuwa da Nadeeyar duk da ba magana take ba,


Sallama suka yi da Habeeb bayan ya sanar da Shi in sha Allah bare wuce week in nan ba zai dawo gudun Kar a zarge Shi,shima ya kuma mishi godia sannan ya shige motar sa,adduar Allah ya kiyaye hanya suka yi mishi tare da daga mishi hannu har ya fice daga gidan,


Cikin kwanciyar hankali ya dauki hanya Saisa ya zabi tafiyar samako domin gujewa idon sani KO kuma road safety suke ne ko yan sanda 🤣,da haka ya dauki hanya Yana tafe Yana duba halin da yar mutane ke ciki,sai muce Doc Nameer Allah ya kiyaye hanya,



*********Sen Rilwanu


Bugun kofar dakin Shi ne ya farkar da Shi daga baccin safen da yake yi,da kyar ya samu ya tashi ya nufi kofar domin ya sha maganin bacci jiya kafin ya kwantan,


Bude kofar ya ga Falmata ce durgusawa tai tare da gaishe shi,da hannu ya amsa ta,a ladabce tace da Shi ranka ya Dade kayi bakuwa,


Bakuwa ya maimata da mamaki,eh Waye shine abunda ya tambaye ta,


Yallabai Hajiya ce,idanu ya zaro yace hajiya fa kika ce eh tace da Shi a nutse,be koma cewa komai ba ya fada daki cikin sauri ya wanke Baki tare da wanke fuska ya xura milk jallabiya tare da feshe turaruka ya dauko carbi yana dan ja a nutse ya fito da murmushi Kan fuskar Shi,


A zaune ya tarar da yar dattijiwar matar da ke tsananin kama da Shi,sanye da hijabin ta har kasa tana jan nata carbin,


A gaban ta ya zube tare da fadin sannu da zuwa Hajiya Ashe kina tafe,


Kallon Shi tayi tsaf daga Sama har kasa saidai sam yaki barin su hada idanu da ita,


Kai ta girgiza sannan tace Abul bait wai me ke damun Ka ne,


Cikin saukar da murya yace hajiya magauta sun sako ni gaba na rasa yanda zanyi,


Anya kuwa Abul bait Anya,sai kuma ta girgiza Kai,tare da gyara zama,


Mikewa yayi tare da fadin Bari na sanya a kawo Miki abinci na san Baki karya ba kika taho,


Dawo Ka zauan ba abinci ne gaba na ba,magana nake son muyi ta fahimtar juna,


Ba musu kuwa ya dawo tare da zaunawa Kusa da ita,duk iskancin Sen Yana mugun shakka da tsoron Mahaifiyar shi (Hajiya Rakiba),



Abul bait,naaam hajiya ya amsa ta,na tambaye Ka miye damuwar Ka Amman kace Dani magauta sun Saka Ka gaba,na Rasa gane wani irin abu ke bibiyar Ka Ka duba fa ace tun mutuwar Mahaifiyar Nadeeya ace har yau shekaru Kusan 25 baka kuma aure ba,


In anyi magana kace mun komai yar lokaci ne,sannan ace yarinyar nan jarabawa ta fada Mata ni Banda nasani ya and kace da ni babu abunda kake boye mun,


Ina yawan mugayen mafarkai da Kai Wanda na Rasa gane dalilin haka,Ka ji tsoron Allah Ka fada mun in har akwai abunda kake boye wa duk duniyar nan Baka da kamata ni ce uwar Ka ni ce uban Ka,don haka Ka sanar da ni miye kake boye mun,


Kan Shi ya kwantar a cinyar ta sai ya Sanya kuka,hajiya mutane sun Saka ni gaba kaina aka Fara siyasa an samu wasu mugayen da suka jefi yarinyar nan hauka tuburan tayi hajiya bata komai sai auna mun zagi,


Kallon Shi kawai Hajiya ke yi kafin tace Ka tabbatar babu abunda kayi wa yarinyar nan Baka zalunce ta ta ko ina ba,


Dagowa yayi sanann yace haba hajiya ke fa kin fi kowa sanin halina,


Yo wani sanin Hali Dan mutun da Ka Haifa ne Baka Haifi halin Shi ba,AI kana iya canzawa a KO wani lokaci amamn da mamamki ace Nadeeya ke maka irin wannan diban albarkan da na gani a video,


Wlhy hajiya sa hannun magauta ne,


Kayi mun shiru in sanya hannu ne Miya Sanya Baka kawo ta gurina ba sanin Kan Ka ne Ubana babban malami ne kafin ya mutu duk garin Azare har nan cikin garin Bauchi babu Wanda be san da Zaman Shi ba,


Kawunan Ka wani irin ayoyi da adduo'in karya sanmu ne Basu San Shi ba Amman Ka dauke ta Ka Mika ta asibiti,tunda ga rannan nasan tabbas akwai wani Abu a kasa KO ba haka bane,ta kare tana tsare Shi da idanu don son karantar Shi,


Idanu yayi saurin saukewa domin wani yarrr yake ji a duk lokacin da ta tsare Shi da idanu har rawa jikin Shi ke yi at times,


Cikin kwantar da Kai yace wlhy hajiya Bani son daga Miki hankali ne na ga ba isashen lafiya gare ki ba,and Kabiru ne ya bada shawaran a Kai ta asibitin domin likita yace kwakwalwan ta ya dan tabu dole akwai bukatan ayi na asibitin kafin a yi na gidan,Jira nake in an Gama daman sai na kawo ta gurin ki,sai kuma aka yi rashin dace an bita can asibitin an sace ta yanzu haka case in na gurin Yan sanda suna bincike akai,


A Ka sace ta salati hajiya ta Sanya tare da tafa hannuwa wanann masifa har ina,Anya Abul bait ba wani Sabon Allah kake yi ba shine ya tashi kama Ka ta wanann hanyan,


Cikin sauri yace wlhy hajiya Bana aika ta komai ina sallah ina azumi ina zakka ina sadaka ina kyauta,ina sauke farali sannan Ina kyautata muamala ta da mutane da makota na uwa uba kuma ina Miki biyayya ke dai kawai in jarabawa ta samu mutum,


Dan shiru hajiya tayi sannan tace ina fatan dai kana gujewa haramun domin cin haram kadai Kan iya wargaxa ma lamuran rayuwar Ka,



Da sauri yace Allah ya mana tsari da haram hajiya Bana cin ta Bana kusantar ta kuma Bana kaunar me taammali da haramun,


Shiru suka Dan yi Basu ce komai ba sannan can tace ko dai za Ka hakura da neman wannan takaran ne haka kawai Bani da good feelings Akan takaran nan naka Abul bait,Ka dube Ka duk Ka Rasa nutsuwa yarinyar nan ba ma mu san halin da take ciki ba duk Akan neman duniya wani irin arziki da dadi ne Allah be azurta Ka da Shi ba,


Kirjin Shi ne ya buga,a taya zai ma Fara Aje takaran nan bayan abubuwa da yawa da ya Rasa sabida Shi,AI ina bare ma taba yuwa ba,


Kayi shiru ina yi maka magana,


Zama ya gyara sanann yace hajiya Nima da zan so ajewar tunda hankalin ki be kwanta da Shi ba,Amman kuma mutane zaki duba gabada hopes in su na ga Allah na gare ni don alummah ta nake son yi,domin kawo cigaba Amman in Baki so zan hakura,


Dan tsaki tayi sanann tace ubangiji ya shige mana gaba Ka dai dage da azkar yanda kace an sako Ka gaban nan Nima Zan na taya Ka,sannan Ka ji tsoron Allah a duk yanda kake in kayi Abu kana tunanin bazan sani ba Allah zai sani kuma Yana gani domin Shi ya yayi mu duka,Allah ya gani na Baka tarbiya da ilimi daidai iyawa ta,


Haka ne hajiya ina Kan ji wlhy ayi ta taya mu da addua in sha Allah komai zai zo ya wuce,maganar Nadeeya kuma yau Zan Kara Sanya yan sanda suna checking duk wani shige da ficen motoci sannan Zan Sanya ayi sanarwa duk Wanda ya same ta Zan bashi kyautan makudan kudade,da yardar Odugwu nan take zaki ga an same ta,


Idanu ta watsa mishi tare da fadan Waye wani Odugwu,Abul bait da hankalin Ka kuwa,wani irin sakarci ne hka,


Da sauri yace hajiya Odugwu Yana nufin shugaba ne ina nufin Allah ke nan,


Bana son iskanci fa wani hauka ke nan Allah za Ka wani kira Shi Odugwu wlhy ka na kiyaye halcen Ka Kar Ka je fa kanka a wuta da kanka,ta kare cike da fada,hakuri ya bata sannan ta mike tace ni kam Zan koma ubangiji ya shige mana gaba,


Haba hajiya ko ruwa fa Baki sha ba,ina azumi Abul bait daman Jin Shirun ne ya sanya ni cewa Zan zo tunda Kai ka gagara zuwa,


Nan ma hakuri ya bata sannan yace da ita Yana zuwa,daki ya nufa kudi ya Ibo masu yawa sannan ya fito yayi daidai da fitowan Afzaal da gajeran wando,


Kai ko ba Afzaal ba,eh hajiya ni din ne Ina kwana ya kare Yana Sosa keya,


Abul bait uban me yaron nan ke yi cikin gidan nan na gani Yana da gida KO ba haka bane,


Eh hajiya daman sabida laluran da ta sami Nadeeya ne ya sanya Shi dawowa nan domin Zama Shi kadai in babu daadi,


Harara hajiya ta jefa mishi sannan tace yaron goye ne Shi,yanzu hka ya dace inda yake yawo daga Shi sai guntun wando,wannan AI iskanci ne,nan ko ta hau Sababi,


Shi dai Sen hakuri ya yi ta bata da kyar ya samu ya lalabata tayi shiru suka fito tana kuma mishi nisiha Kan ya ji tsoron Allah a duk abunda ya Sanya gaba,sannan in ya samu lokaci ya ci ya zo ya gaida kawunnan Shi tunda Shi komai sai an fada ma ka,


Hakuri ya kuma bata tare da Mika Mata kudadan hajiya gashi ayi tsaraba tunda kin ki kwana,


Mota ta shige sannan tace rike kudin ma Abul bait Wanda Ka aiko wancan satin ma ko ficika ban taba ba,ni dai ina kuma maka nasiha da Ka ji tsoron Allah a duk inda kake,murtala ja Mota mu tafi,a haka suka fice daga gidan aka bar Sen tsaye da kudi a hannu duk jiki a sanyaye,toh ko dai hajiya ta san abunda yake aikata wa ne,in ko haka ne da ya shiga uku,wani zuciyar ce tace da ta sani hajiya bara ta iya shiru ba sai ta tare Ka da maganar,sai dai in ta Fara zargi na,AI ko ya Zama dole ya canza taku domin ko giyar wake yake sha bare so hajiya ko wani ya San asirin Shi ba,ajiyar zuciya ya sauke tare da komawa cikin gidan.




Asaalamu alaikum


Ina fatan anyi jumma lfy ubangiji ya kara mana lafiya da Zaman Lafiya Allah kuma ya amsa mana ibadun mu da adduo'in mu🙏🏻

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM 

(MARTEYBEE)


......


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


In har kin San ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki toh yi Zaman ki don Allah ba sai kinyi joining ba,haka zalika Maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah 🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


         08100046388


Alhamdulilah ya rabil Alameen 🤲🏻❤️Allah na gode da Ka nuna mun zagayo war haihuwa ta ina me Rai da lafiya, Happy birthday to my humble self  ubangiji Ka mun albarka ni da zuriah tah,Allah Ka kare ni daga dukkan sharri, sannan ya Karo mun shekaru masu Albarka 🤲🏻,I am a year older today ,y"all should say a prayer for me da bakunan Ku masu Albarka 💃💃💃


.........

        Page thirty_one


**********


   Tafiyar hours ne suka iso da doc Nameer cikin garin Kaduna,a matukar gajiye ya dauki hanyar gidan hajiya,


Numfashi ya Shaka sai ya ji wani irin sanyi a ranshi komai dadin wani gari garin Ku ya fi,ji yake kamar be da wani sauran damuwa cikin duniyar nan,a nutse yake driving bayi da burin da ya wuce ya ganshi rungume da little in Shi,


Da haka ya karaso gidan yayi horn aka Bude mishi gate,Wanda be sanar da hajiya ya iso ba,ganin motar kanwar Shi Khadija ne ya bashi mamaki toh yaushe ta zo jiya suka yi waya da hajiya har ya kashe bata yi Mai tadin khadija ta zo ba,Baki ya tabe sannan yayi parking tare da fitowa,


Sai a lokacin ya ji zuciyar Shi ta Fara bugawa be gane yayi hauka ba sai yanzu,toh me zai Fara ce da Mama game da Nadeeya Akan miya sa ma ya dauko ta ba tare da yayi shawara da uwar Shi ba abunda tun Yana karami be taba yi ba shine yanke hukunci ba tare da ya sanar da mama ba,duk abunda zai yi sai ta sani ta bashi kuma go ahead,toh ko ya fice ya kaita hotel ne wani xuciyar ta Fadi mishi,


Da sauri ya girgiza Kai tare da aro jarumta kawai ya fito tare da rufe motar ya nufi cikin gidan,fuskar Shi dauke da murmushi,


Bakin Shi dauke da sallama ya shiga parlor in hajiyar,


Da gudu Hanaan ta yo inda yake tana dariya tare da Bude hannaye tana Fadi tana tashi duk a zumman oyayo,


Fuskar Shi dauke da murmushi domin ganin ta kawai ya Sanya Shi farin ciki,be dauka hka yayi missing in tilon diyar ta Shi ba sai da ya rungume ta a kirjin Shi,


Cikin gwarance tace papa,tana dariya tare da tsalle a jikin shi,


Kanta da ya sha kitso ya shafo tare da amsa ta da ya aka yi my angel,kallon Shi take kamar tana fahimtar abunda yake Fadi,


Ah Babana har Ka iso,mama tace tana murmushi,har ga Allah tana tsananin Jin kaunar Dan nata Nameer a ranta,yaron akwai Shiga Rai and tana matukar tausayin Shi,ko don Rashin matar Shi da yayi,


Aje Hanan yayi Wanda take kokarin Sanya mishi kuka,


Ka ji yar nema da can da be nan ya kike yi don neman ta yau shine za ki mana kuka,Maza yi mun shiru,


Kai kawai ya girgiza don in yace zai yi magana mama haushin Shi za ta ji,an wuni lafiya mama ta,


Lafiya kalau Babana Ka iso lafiya,ya hanya,ya kuma aiki,


Wlhy Alhamdulilah mama na same Ku lafiya,wlhy duk Alhamdulilah tashi mu shiga Khadija ma na ciki dazu da safe suka zo,


Mikewa yayi tare da riko yar hannun angel suka karasa shiga cikin parlor,


Kujera ya samu ya zauna tare da sauke ajiyar zuciya wato ba karamin gajiya ya kwaso ba,


Daddyn Hanaan Ashe da rabon mu Hadu,khadija ta Fadi tare da fitowa daga dakin hajiya,


Juyowa yayi fuskan Shi da murmushi yace ah mutanan Abuja yaushe a gari,wlhy yaya dazu muka zo ya aje ni ya koma,ina ta missing in Ku ne nace  Bari dai na leko,


Murmushi yayi sannan yace toh sannnu da zuwa ina baby,bacci tace da Shi daga haka be kuma ce Mata komai ba,ita din ma haka ta juya tare da shigewa daki,


Ruwa da lemo yar aiki mama ta Sanya ta kawo mishi, sanna ta kawo mishi tuwon shinkafa miyar taushe ta sha Naman rago kifi da kayan Hadi,


Murmushi yayi Yana Kara Jin dadin samun mahaifiya irin maman Shi,


Fitowa tayi ta ga ko warmers in be Bude ba,kallon Shi tayi da mamaki bayan ta zauna sannan tace Baba na lafiya kuwa,


A hankali ya dago tare da cewa me kika gani mama,yo gani nai AI Baka taba komai ba,Kai da Ka Ibo gajiya AI Ka samu Ka ci Ka koshi,ko dai sai Ka watsa ruwa ne gajiyar ta fi sakin Ka,


Ni ban ma ga bakon da kace da ni za Ku zo tare ba,ko dai ya fasa biyo Ka ne,domin har na sanya an gyara mishi dakin Baki,


Sai a lokacin ya tuna da ya rufe yar mutane a mota ita kadai,da hanzari ya mike tare da kokarin yin waje,


Hannun Shi mama ta riko sannan ta janyo Shi ya koma ya zauna,idanu ta tsare Shi da su,Kai Baba na lafiya kake kuwa??


Shiru yayi domin har ga Allah be ma san ta inda zai Fara yi Mata bayani ba,be san ta ya za ta dauki maganar ba,


Kayi shiru ina maka magana,da alamu dai akwai abunda kake son fada Amman Ka kasa,yaushe muka Fara boye boye tsakanin mu Baba na wani abun ne ya faru na kalli gaba daya Baka da kuzari,


Jarumta ya aro tare da riko hannaye ta cikin taushin murya yace hajiya mama nayi Miki laifi ki ya yafe ni sabida Allah,


Kallon Shi ta dan yi na mintuna kafin ta nisa tace me kuma Ka aikata mun da har kake neman yafiya ta,


Mikewa yayi tare da saukowa ya zauna Kusa da kafafun ta kamar wani yaro karami tare da kama hannun ta,


Cikin sanyi murya yace mama ban ma san ta ina zan Fara Miki Baya ni ba,saidai ya Zama dole in sanar da ke domin Bani da Wanda ya wuce mun ke,you are the only one da nake da,and I don't know taya za ki dauki maganar I don't even know ko abunda nayi daidai ne ya dace ko be dace ba,but trust me mama ta wlhy I did it with pure intentions babu komai a Raina sai tausayi da kika koyar mun tun ina yaro,


Ita dai mama kallon Shi kawai take Kan ta duk ya kulle,don har ga Allah bata gane inda kalaman nashi ke nufa,


Cikin sanyin murya ya kwashe labarin Shi da Nadeeya from A to Z be rage komai ba sai inda ta lashe mishi kumatu😂 ya sanar wa mama,Yana Jin zuciyar Shi na bugawa domin a rayuwa babu abunda ya tsana kamar bacin ran Mahaifiyar shi(Yan uwa mu ji tsoron Allah mu kyautata wa iyayen mu iya iya war mu,domin suna silan duk abunda muka Zama a rayuwar mu iyaye ba abun Wasa bane,mu guji Saba musu ko Sanya su a kunci,domin Allah da kanshi yace yardar Shi na tare da yardar iyaye hka zalika fushin Shi na tare da fushin iyaye,duk wacce ta, ta taso ta samu iyayen ta biyu a raye to wlhy key in shiga Aljannah Inta na gurin su haka ma na wutar ta in tai musu biyayya musamman ma uwa toh ta samu rabo ta shige ta in ta Saba musu ubangiji ya kyauta wutar ta na nan in har bata tuba ba, ubangiji ya kare mu,ya kuma ba mu iko da juriyar kyautata wa iyayen mu har karshen rayuwar mu,Wanda iyayen su suka Riga mu gidan gaskia ubangiji ya Sanya sun tafi a saa,Wanda kuma Nasu babu lafiya ubangiji ya Basu lafiya ya kuma Yaye wahala,mu da namu suke a raye Allah ya Kara mana hakuri da juriyar kyautata musu🤲🏻),



Mikewar da hajiya tayi bata ce komai bane ya Sanya duk jikin doc Nameer yin sanyi,daman ya san za a yi haka,bayi da choice in da ya wuce ya maida ta Bauchi gidan mahaifin ta,in ya so ya bi ta da addua,



Babana yaushe Ka zamo mara tausayi ban sani ba, idanu ya zaro tare da mikewa Yana hajiya nayi wani abun ne,


Haba Kai kuwa ace tun shigowar Ka yarinyar nan ke cikin mota a rufe AI zafi ya kashe ta Allah ya kyauta,


Khadija Maza fito ki zo ki taya ni Shigo da bakuwa,idanu Nameer ya zaro cike da mamaki yace hajiya are you for real,


Murmushi tayi sannan tace Babana ke nan har akwai abunda za Ka kawo na kyamace Shi ko na ki babu wannan abun mu je Maza Ka Bude mota a fito da ita kafin Ka kashe musu yarinya,


Yanda kuka san Nameer ya zuba ruwa a kasa ya sha KO kuma ya taka rawa haka yake ji, Allah ke nan ance daman Allah maji rokon bayin sa,addua yayi ta yi Akan hanyar Shi Kan ubangiji ya Sanya Mahaifiyar shi ta fahimce Shi ba tare da an samu wata matsala ba sai gashi Allah ya amsa(Yan uwa mu yawaita rokon Allah a yayin da muke Kan abun hawa Akan hanyar mu ta tafiya domin duk wata addua da matafiyi zai yi to karbabbiya ce bata dawo wa,haka zalika me azumi, ubangiji ya ji Kan mu ya kuma cigaba da amsa mana adduo'in mu Allah sa mu dace🤲🏻),



Kira ta kuma kwala wa khadija,Wanda ta amsa da dan karfi don ta san ta ji kiran da tai Mata din,tare da fito wa,mama gani,tace tana gyara Zaman dankwalin ta,


Kira Zaliha mu je Ku taya ni Shigo da bakuwa,mamaki ne kwance fuskan khadija wace irin bakuwa ce har sai an yi gayya kafin a Shigo da ita,amman babu halin tambaya domin har su mama sun fice abun su,dakin zalihan ta je tare da Kiran ta kan su je mama na haraban gida,


A kofar motar suka tarar da mama ta zuba wa Nadeeya Ido dake bacci Wanda za mu iya Kiran Shi na gajiya ko wahala,


Da kanta ta shiga motar cike da nutsuwa ta dago Nadeeyar tare da manna ta a jikin ta,tana yaba kyawu da hasken fata irin ta Nadeeya,


Kama mun ita mu fito da ita Khadija kun tsaya kuna kallo na,


Idanu ta zaro sannan tace Hajiya wace ce wanann in da za a kamo ta ina kuma za a shigar ta,


Ni fa Bani son surutun banza da hofin kin nan Khadija Baki gani tare suka zo da Babana in kina kama mun ki kmaa mun ita in Baki yi ki matsa Zaliha ta rike mun ita tunda aikin kudin ta take na San baza ta ki ba,


Baki khadijan ta turo tare da kamo Nadeeyar nan dai suka samu suka fito da ita da kyar suka dauke ta suka shigar da ita parlor Kai tsaye mama tace a wuce da ita dakin ta,mamaki ne kwance fuskan khadija yo to a ina mama ta san wannan farar yarinyar me Sufan mayu,da har za a kule da ita uwar daka,mamaki be Gama kashe ta ba Saida ta ji mama na ce wa Zaliha ta shiga toilet ta hado Mata ruwa me dumi a bucket sannan ta dauko new towel a cikin drower tare da toothpaste da auduga ta kawo Mata,ba musu kuwa ta je ta hado duk abubuwan da Ake bukata,inda ta kawo ta Aje gaban mama,ce da su tayi su fita tana son ta gasa Mata jiki ko gajiyar tafiyar zai warware a jikin ta,duk yanda Khadija ta so suyi magaana mama nuna wa tai kamar bata gane me take nufi ba,ala dole ta fice daga dakin,zuciyar ta cike da tunanin wacece wannan haka,



********Police command


Sen Rilwanu tun safe yake police command in an buga yin duniya kan su Bashir su fito mishi da diyar Shi amman dai amsan ke nan guda daya Basu San yanda take ba,


Duka kam har na Bura uba sun sha ta a hannun oga Jabiru domin jika Shi da kudi Sen yake yi Wanda ke bashi daman yin Shaye shayen Shi yayi tatil ya zo ya sauke komai Kan su Bashir domin bugu kam sun sha Shi har na Allah ya Isa,


Matakan tsoron da aka zuba kuwa ba a cewa komai Ka dauka mulkin sojoji Ake yi,ko in ce Yan sanda domin duk wani gurare an zuba police masu duba shige da ficen mutane,bincike sosai Ake yi amamn har yanzu shiru don babu motar da zai Shigo ko zai fita da ba a bincika ba,


A kwanakin da suka yi hannun Yan sanda ba karamin wahala da azabtuwa suka yi ba,sun yi kuka in akwai na Jini bayan hawaye to Shi suka yi,Kareematu ta tsinewa Bashir ya Kai kwando dubu,haka zalika Zaituna ma ta tsine Mata ya fi abunda ya fi,


Ganin bata musu lokaci kawai suke yi ya Sanya aka cike musu FIR in da za a tangade keyar su sai court,domin Sen cewa yayi sam be san zancen ya yarda da su ba,


Kareematu tayi kuka kamar ta Rasa ranta tunda take a rayuwa ko Kusa da police station bata taba zuwa ba sai gashi karewar ta yau wai court za a wuce da su,


Suna ji suna gani haka aka kade kansu ranar Monday aka watsa su court,


A Zaman farko aka karanto case in su inda Ake zargin su da laifin hadin Baki su uku suka sace yar gidan Sen Rilwanu Audu Waziri (wato ana charging su da offence Conspiracy and abduction in Nadeeya),


Bugun farko alkali yace ko akwai Lawyer in me Kara,da Wanda Ake Kara,nan Barrister Hassan buba ya mike ya gabatar da kanshi GA court in tare da fadin shine lawyer in me kara,


Bayan ya Gama ne alkali ya kuma tambayan ko akwai Lawyer Wanda Ake Kara zuru suka yi da idanu kafin suka ce babu,


Nan alkali ya tambaye su wani yare suke ganewa kuma za su iya magana da duk turanci suka ce da Shi,nan ko ya tambaye su one by one do you plead guilty or not,gaba dayan su suka ce they are not guilty,


A karshe dai daga case in aka yi zuwa nan da 2 weeks masu zuwa kafin nan su tabbatar sun samu Lawyer saidai alkali ya bada umarni a wuce da su gidan gyaran Hali a Aje su har sai ranar da za a dawo Zaman court da haka aka tashi alkali ya mike ya wuce abun Shi,


Kareematu Ihu ta Sanya tana zagi Bashir tana kuka inda Zaituna a nan ta yanki jiki ta Fadi ta Suma,Bashir ko wani irin gumi ne ya karyo masa da ya san haka zai faru tun farko da be hada Kai da Sen ba,yau gashi ya Kai Shi ya baro Shi,


Haka nan aka watsa wa Zaituna ruwa aka tasa keyar su aka wuce da su suna kuka suna Ihu amman duk a banza,(ni ko nace Allah ya kara kadan ma Ku Ka gani indai son zuciya ce),



Asaalamu alaikum


Da fatan duk kuna lafiya,Allah ya sa hka,ya kuma ruwa ubangiji ya bamu damuna me albarka 🤲🏻


Ayi mun afuwa hidimar biki ce ta boye ni Amman in sha Allah gobe za mu kammala zan cigaba da typing kamar yanda na Saba kullum,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi🙏🏻,

😭😔 UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                   BY

NERNAH MARYAM

     (MARTEYBEE)


........


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


In har kin San ba karanta book ina da commenting bane zai kawo ki toh kiyi Zaman ki ba sai kin Shigo ba, haka zalika Maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah 🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

     

      08100046388


.........

       Page twenty-two 


*********


Doc Nameer*******


 Tsaye yake a bakin kofar dakin Mama, Yana me jiran umarnin shigowar Shi,


Shigo Babana mun Gama wankan tace da Shi,da dan karfi yanda zai ji abunda tace,


Cikin sallama ya Shigo cikin dakin,a kwance ya tarar da Nadeeya sanye cikin sky blue dogon Riga  ban da kamshi babu abunda take yi,idanu ya lumshe yana me kara gode wa Allah da ya bashi Mama a matsayin Mahaifiyar shi,


A kujeran dakin ya ja ya zauan sannan ya ce sannan da kokari Mama ta ubangiji ya Saka miki da gidan Aljannah,


Murmushi tayi sanann tace Ameen Baba na Bana fatan yanda kake kyautata mun kake tattalin rayuwa ta da farinciki na,a ce ka nuna abunda kake so na Gaza yi maka,ko na Gaza Kula maka da shi,ta kare tana murmushi,


Shima murmushin yayi domin sam be gane inda zancen nata ya nufa ba,


Zama ta gyara sanann tace ni kam Babana jikin yarinyar nan Anya kuwa ma tsaya na asibiti kawai, 


Shi din ma Zama ya gyara sanann yace wlhy mama Nima abun yana Bani mamaki,yanda kika ce tana yawan firgici cikin dare kamar me yin miyakun mafarkai,


Haka kawai fa Mama na gan ta ranar tsaka ta Zama haka,ko yatsa bata iya moving,ya kare cike da jimami,


Numfashi mama ta sauke sannan tace wannan lamari nata da daure Kai Babana babu komai Amman muyi ta fada wa Allah in sha Allah zai amsa ya bata lafiya,


Ameen ya rabil Alameen mama tah Bari na je 44 gurin Mujaheed tun shekaran jiya yake ta Kira nasan ya na can yana Mita na dawo ban neme Shi ba,kuna bukatar wani Abu ne,


Murmushi tayi tana me matsa kafan Nadeeya da ke bacci tace ubangiji ya kiyaye ya tsare Babana Bama bukatar komai,saidai in kana dawowa Ka biya ta Islamic chemist Ka karbo mana pure honey da man Habbatus Sauda,na gurina ya kare,


In sha Allah zan taho da su iya kan Shi kuke bukata??


Eh iya kan Shi ne Shi din ma ita nake baiwa tunda Manzon Allah da kanshi yace kuna shan Habbatus Sauda da Zuma domin yana magance ko wace irin cuta da ke jikin Ku banda mutuwa,


Haka ne kam Mama ubangiji ya Kara mana lafiya da nisan kwana me amfani Bari na je sai na dawo,


Toh ubangiji ya tsare,da haka ya samu ya fito daga dakin da kyar ya samu Zaliha ta Raba Shi da Hanan domin rikici ta Sanya Kan sai ta bishi,


Kai tsaye 44 ya nufa inda Saida ya tsaya aka gaggaisa da mutanan arziki sanann ya nufi office in Mujaheed,


A Bude ya samu kofar so shiga yayi Kai tsaye tare da sallama inda ya samu babu kowa a office in,guri  ya samu ya zauna Yana me kare wa office in kallo,


Rayuwa ke nan kamar be yi rayuwa a hospital in nan ba,shigowar Mujaheed ne ya katse mishi tunanin da ya dan fada,


Mikewa yayi fuskan Shi cike da annuri Ashe dai nayi missing in Ka my gee ya kare Yana Mika mishi hannu,


Harara Mujaheed ya watsa mishi kamar wani mace kafin yace dallah Malam zo Ka fice mun a office,


AI wlhy Nameer Ka gwada mun matsayi na ace sabida Allah yau kusan week da zuwan Ka Amman sai yau muke haduwa,haba daga zuwa Bauchi shine har Ka Hadu da abokan da suka Fini ko??toh wlhy Ka sani Shi dai tuwo sunan Shi tuwo ba a canza masa suna ni din nan dai nine Aminin Ka na tun yarinta duk Wanda za kayi Baya na suke eheee,


Nameer kasa rike dariyar da yayi ganin inda Majaheed ya rufe Ido yake surfa mishi masifa,


Nan ko Mujaheed ya kuma kulewa,harara ya kuma buga mishi sannan ya juya,ni baran bar maka office  in bare yu Ka Sanya ni gaba kana mun dariya ba instead Ka Bani hakuri kayi mun laifi,amman Ka zauna kana mun dariya kamar Ka samu mahaukaci,


Kasa kasa Nameer yace miye maraba Likitan mahaukata kam AI shima ya zautun,


Dadin abun kaima zautatcen ne Ashe ya kare tare da bugun kafadun Shi,nan duk suka kwashe da dariya,


Zama suka yi bayan sun yi musabaha sannan aka shiga gaisawa,


Mutumina gaskia Bauchi ta karbe Ka fa,Ka ga yanda kayi fresh Ka Kara kyau kuwa har Dan kiba fa na ga Ka Kara mun,


Kallon kanshi Nameer yayi sanann yace a hakan wai,domin Shi a tunanin Shi ma Rama yayi ko don pressure irin ta Sen da ya sanya musu,


Eh wlhy Masha Allah kayi kyan gani kamar wani Sabon ango ko dai ko dai,kayi gamo da kyakkyawar Diya a garin Bauchi dake Kula mana da Kai ne,daman matan Bauchi an canfa kyawawa ne akwai su kuwa da iya tatali da iya Kula da saurayi ko miji,


Dariya Nameer ya Sanya sannan yace AI ko sanin Hali ya Sanya na taho maka da number in wata me kawo mana tallan masa a hospital,ganin yanda kake ta son karawa Maman Afreen kanwa,


Allah ya sauwaka wlhh Ka ma cuce ni AI ko class ina ya zuba duk aji na na kare da me kawo tallan masa ya kare Yana checking Kan Shi in,


Dariya Nameer ya sanya sanna yace yanzu fa Ka Gama cewa matan Bauchi akwai iya Kula da rike Maza,Kai ina ruwan Ka da kyan ta in da za ta Kula da Kai AI lafiya Lau,


Be Kai ga bashi Amsa ba wayan Nameer tayi Kara,ganin Habeeb ke Kira Saida kunya ya kama Shi don zai iya cewa tunda ya dawo be Kira Shi ko sau daya ba sai Shi Habeeb in ke ta Kira,


Dauka yayi tare da sallama,amsawa Habeeb in yayi sanan yace wlhy Doc Handsome zumuncin Ka kadan ne,AI ko ba dan komai ba mana magana akai akai mu samu mu ji ya jikin Nadeeya domin Muhibba sam bata da kwanciyar hankali kullum tambayar ta ya me jiki,


Murmushi Nameer yayi sannan yace don Allah kayi hakuri ban kyauta ba Kan wlhy abubuwa ne suka hade mun Amman a baiwa sister na hakuri a kuma ce da ita jiki Yana ta kyau Alhamdulilah,


Toh Masha Allah ya mutan gidan duka su mama hope dai duk kuna lafiya ko,


Wlhh lafiya kalau Alhamdulilah ya baby boy,da kuma aiki,


Dan dariya ya Sanya sannan yace ba Ka gudu Ka bar Baya da Kura ba,Kai Ka ga yanda garin Bauchi ya burkice da jamian tsaro ,ko wani lugun da sako suna gurin bincike Ake na inalilahi,


Dan dariya Nameer ya sanya sanan yace su yi ta yi,kashe kudi ne wlhy be ishe su ba kila da kudin ma aje Shi yayi campaign in Shi da Shi,domin wanann Jabiru kana ganin Shi idon Shi idon kudi,karba zai yi ta yi gurin Sen,


Kai dai Bari AI yanzu kam abun ma ya bar hannun Shi sun shiga court na ji tun last Monday yanzu haka an dage shariar suna gidan yari an bada tsaron su sai nan da 2 weeks za a koma a cigaba da case,Zan so mu samu mu je mu ga idanun mutanan Ka ya kare da dariyar mugunta,



Allah ya shirya ka Habeeb wlhy,yanzu kama sun ne abun dariya ko me,


AI dole nayi Dariya Nameer duk Wanda ya sai kwando daman ya san za ta zubda mishi ruwa,ba dai su son abun duniya da kwandayi ba wlhy kadan ma suka gani,ni AI Zan so a yanke wa ko wannan su hukuncin ko da 3 years in prison ne with hard labour kila su shige hankalin su in sun fito,

 


Dariya Nameer ya sanya sannan yace amman wlhy Kai kam akwai mugu ,


Ba wani mugunta abunda Ka shuka Shi zaka girba in ji bahaushe,yanzu dai yaushe za Ka dawo in ban da abun court in nan Bashir is busy AI da yanzu ayoyin zargi sun dawo kanka,


Hmmm haka ne kam yanzu dai ina gurin Mujaheed ne Bari na koma gida I will call u,


Okay Ka gaida Mujaheed in da haka suka yi sallama ya kashe wayar Shi,abun har yanzu dariya yake bashi,irin wannan Ka amshi laifin da ba Ka ma san a yaushe Ka aikata Shi ba,Amman kana paying price haka,


(One thing in life shine Ka ji tsoron Allah Ka ji tsoron shiga ko daukan hakkin bayin Allah, mugunta kyeta son zuciya ubangiji Ka Raba mu da Shi,zalunci babbar musiba ce,Ka zalunci Dan uwan ka ya daga hannu yace be yafe ba Allah ya Isa and Ka dauki hakan ba a bakin komai ba,Kai kasan isan Allah kuwa,Ka kuwa san ta inda wanann Allah ya isan zai fada maka kuwa??kila Kan dukiyar Ka kila lafiyar Ka,kila kan ranka babu ta inda bata faduwa, saisa no matter how try your possible best Ka ga Ka zauna Ka kuma rabu da kowa lafiya,Manzon Allah SAW yace Ka zo da ko wani irin laifi ranar kiyama yayi alkwarin tsaya maka Amman Banda shirka,Sata,da kuma laifi tsakanin bawa da bawa,domin wannan tsakanin Ka da Dan uwan ka ne in ya ji ya yafe fine and good, ubangiji Ka Raba mu da zulantar Kan mu da Yan uwan mu,ya kuma Sanya mu fi karfin zukatan mu domin da Ka cutar gwara Kai an cutar da Kai,Allah kayi mana me kyau duniya da kiyama🤲🏻)


Kashe wayar Shi ke nan ya mike tare da zuba su a aljuhu ganin fuskan Aminin nashi cike yake da tambayoyi Wanda he is not ready ya amsa su,


Amman Sarai kasan dai ina son muyi magana Ka wani mike,


Agogon hannun Shi ya kalla sannan yace sorry friend I have to go mama ta aike ni but don't worry zuwa gobe in sha Allah zan dawo mayi duk maganar da kake son yi,bye bye a gaida Afreen da haka ya fice daga office in ya bar Mujaheed Baki Bude brain in Shi cike fal da tambayoyi Wanda babu me bashi amsoshin su sai Nameer in,


Nameer ko,be tsaya ko ina ba sai Islamic chemist in Zuma da Habbatus Sauda in ya siyo da yawa ya biya aka bashi sanann ya biya ya siyo musu ice cream kafin ya dawo gida,


Mama ya tarar ta Sanya Khadija a gaba tana yi Mata fada Wanda harda zagi,abunda zai ce rabon da ya ji har ya mance,


Da sallama ya Shigo dakin tare da neman guri Kusa da ita ya zauna tare da riko hannayen ta Mama me ya faru waya bata Miki Rai har haka,


Cike da fushi take fadin haba Babana yanzu ace kamar khadija ce za ta zamo me bakin Hali ta fita zakka cikin yara na,tun ranar da Ka kawo yarinyar nan cikin gidan nan Naga alaman ran ta be so ba,sai wasu irin halaye take yi ta matsa mun lalle sai na Fadi Mata daga ina take,ba dama in ce ta taya ni Kula da yarinyar nan sai tayi Mata yar ko oho ko kuma ta hau Mita,


Yanzu Dan ubanta ita ta fi karfin Allah ya Mata irin wannan jarabawar ce ko ma fiye da haka,and ya Zama dole sai Ka san mutum a rayuwa kafin Ka ji tausayin Shi ko Ka taimaka mishi,


Gida dai nawa ne and Babana Dana ne na ciki na KO Kuda KO kuliya kana da right in kawowa Ka aje cikin gidan nan tunda na mahaifin Ka ne,Akan me za ta Saka yarinya a gaba toh an ki sanar da ke daga ina take akwai abunda zai Kara Miki ne in kin sani??


Ya Isa Mama don Allah kiyi hakuri dole ta so sani Kin san duniyar yanzu ba tsaro,na san tana yin hakan ne for our well being,


Wani well being Kai mance mugun hali irin na khadija kake wlhh, toh ni dai ka fada Mata babu ruwan ta,in har bara ta iya taya ni Kula da Amanar da Ka Bani ba toh let her stay away Kar na kuma Jin tayi wasu kananun maganganu in ba haka ba ranta zai yi munanniyar Baci,ta kare tana mikewa,


Numfashi Nameer ya sauke domin Sarai ya san halin kanwar tashi za ta aikata fiye da hakan ma in dai Khadija ce,


Nan ya shiga yi Mata nasiha tare da Mata bayanin taimakon Nadeeya yayi,ta dai ji amamn ita har yanzu so take ta san miye dalilin da zai Sanya Shi dauko ta all the way from wani gari zuwa Kd,



      2 weeks later*******


 Yau ta kama Monday ko wani maaikaci haba haba yake ya samu ya Isa gurin aikin Shi da wuri,



Nameer ya dawo bakin aikin Shi tun bayan kwana uku da suka yi waya da Habeeb inda ya bar Nadeeya can Kd karkashin kulawar Mama, khadija ma ta koma gidan ta domin Allah yayi ta da wata irin zuciyar banza Sam bara Ka ce yarinyar mama bace,gidan ya rage daga mama sai Zaliha sai little,Saida ya bar musu duk wani abunda za su bukata kafin ya taho ya cigaba da aikin Shi cike da kwanciyar hankali like babu abunda ya sani,


Babu yanda Habeeb be yi ba Kan su shirya su tafi court ganin yanda za a karasa wai ance zuwa da Kai ya fi sako amman sam Doc Nameer yace Yana da abun yi da ya fi wannan mahimmanci Shi dai ya je in ya dawo ya bashi labari,


Da haka ko Doc Habeeb ya shirya ya tafi high court,


Kasancewar rashin zuwan alkali da wuri Shi ya dan yi delaying in su domin har an taho da su doc Bashir,an Shigo da su cikin court room,


Dariya ce ta kusa subucewa Doc Habeeb yayin da yayi arba da doc Bashir da Kareematu,yanda kasan an babbaka gallon a fuskan su,wani irin Baki muni da kwanjamewar da suka yi,Kar Zaituna ta samu labari daman can ba auki gare ta ba,


Shigowar alkali ne ya daidai ta surutu da hayaniyar da ke cikin court in duk aka Mike domin nuna girma wa alkali inda saida ya zauna sanann kowa ya nemi gurun Zaman Shi,nan ko aka shiga karanto cases har aka zo Kan su doc Bashir,


Nan aka Kara fiddo su inda aka nemi lawyern me Kara da Wanda Ake Kara su fito,


Ba sai na ja Ku da dogon surutu ba nan dai aka shiga gabatar da shariar su inda sam su doc Bashir sun ki karba laifin su acewar su babu Abunda suka yi,



Asaalamu alaikum


Ina fatan kuna lafiya


Ayi mun afuwa 2 days in nan ayuka ne suka Dan mun yawa,GA ciwon Kai da ya sako ni gaba 🙏🏻,


Na so in yi ya fi haka amman Allah be so ba,so bare with me pls


In sha Allah sai zuwa gobe in me  kowa me komai ya so,



Ina yi wa kowa fatan Alkhairi 🙏🏻

😭😔 UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

   (MARTEYBEE)


........


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA



In har kin san ba karanta book ina and commenting bane zai kawo ki toh Don Allah kiyi Zaman ki ba sai kin Shigo ba,haka zalika Maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah ko Ka shiga Zan cire ka🙏🏻,


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


       08100046388


Ayi mun afuwa nai mistake a last page in da nai yi madadin in Sanya 32 sai na sa 22 typing error ne🙏🏻,



..........

         Page Thirty_three 


**********


   Sen Rilwanu******


Zaune yake Shi da Alh Kabiru a gurin hutawar Shi,lemu Ka da kayan dadi ne cike a gaban su saidai daga kallon fuskan Sen za Ka fahimce bayi da kwanciyar hankali ko walwalan da zai iya Kai ko da ruwa ne bakin Shi balle har ya Kula tarkacan kayan dadin,


Sen ina so Ka saurare ni da kyau da kuma kunann basira because I got point a abunda nake fada,


Point fa kace Kabiru a taya kake expecting na janye karar nan bayan Nisan da aka yi a shariar nan AI kawai mu zuba wa hukuma Ido su fito mun da yarinya ta,


Dan murmushi Kabiru yayi sannan yace dadi na da Kai wlhh ga Abu a bayyane Amman sam sai kana yi kamar Baka gane ba,


Na sani Ka sani Nadeeya bata hannun su doc Bashir domin da tana nan wlhy a sanin da nayi wa Bashir tun sanda su Jabiru suka kama Shi Zai yi bayani,mutum ne mu Dan banzan son kudi saidai akwai Shi da tsoro ba na kadan ba,and in har Ka kalli abun nan from my own view wani hujja Bashir ke da Shi na sace Nadeeya a sani na da doc Bashir Yana da rikon Amana tunda har kuka Kula deal da Shi toh babu wani Dan iskan da ya Isa biyan Shi ya sace ta,so pls enough of all this mun azabtar da su yayi yawa,abun haushin ma duk a banza domin mun bar asalin me laifi Yana can,su kuwa bayin Allah are paying the price of abunda ba su San komai a Kai ba,ya kare a sanyaye,


Tsaki me sauti Sen ya ja sannan yace Kabiru in muka sake su toh princess ita fa??a taya zan gan ta,


Common sai kace yau Ka Fara zuwa blaze house ko dai Ka Fara kokonto Akan Odugwu ne??ko Ka mance ya Kan maida impossible ya zamo possible,zuwan mu da za muyi cikin week in nan Ka sanar da Shi am very sure kafin mu bar gurin zai sanar mana da inda take wa kuma ya dauke ta,AI tunda kana da Odugwu toh komai me sauki ne,ya kare Yana kurban lemo a glass cup,


Dan shiru Sen yayi Yana tunano irin abubuwan da Odugwu ya malaka mishi , Odugwu shine silan samun komai nashi a duniyar nan,ya maida Shi from poor to the most richest man in the north,ya maida mishi so many impossibles in Shi to possible, Yana da faith Akan Shi sosai wannan karamin Abu ne kamar yanda Kabiru yace zai masa finding solution kamar yanda ya Saba Odugwu the greatest babu abunda ya gagare Shi ya Fadi a bayyane,


Toh Ka gani so just chill kasa a ranka kamar an ga Nadeeya yanzu Ka Kira court Ka ce da su Ka janye karar ta Ka ayi freeing Nasu Kar Ka mance mulki kake nema voice in su kadai ya Isa bata maka siyasa,Shi kuma Bashir Ka bar ni da Shi in ma har yanzu zuciyar Ka be kwanta Akan bashi ya sace ta ba Zan yi handling komai,


Babu musu Sen ya dauki waya abunku da me Fadi aji,one phone call yace ya janye Kara ayi freeing in su a yau yau in nan,


*********Court


Ko da alkali ya ji haka shima farinciki yayi domin wanann case Nasu akwai daure Kai,an sauwakar da Shi, without waste of time kuwa ya sanar da su an janye karar sanan yayi freeing in su za su iya tafiya,


Kamar Wanda aka yi ruwa aka dauke cak haka suka ji saukan maganar nashi,ta Malam bahaushe wai yace kamar saukar aradu da Ka,


Tabbas sun ji ance za su iya tafiya saidai gani suke kamar mafarkin da suka Saba yi ne,Khairat da Abdoul Banda hawayen farinciki babu abunda suke yi,


Haka ma Yan uwan Zaituna da suka halaci Zaman court in,a ta bangaran doc Bashir kuwa ko mutum daya daga cikin family members insa Basu samu zuwa ba ko Ince sun ki zuwa,


A sukwane suka fito daga cikin Accused box in, kafafuwan ko wannan su rawa kawai yake yi,da sauri mamar Zaituna ta je ta taro Zaituna da ke kokarin faduwa hawaye take na farin ciki Fadi take Alhamdulilah tsarki da godia sun tabbata ga Allah daman ance Ramin karya kurarre ne yau gashi gaskia tayi halin ta barka Zaituna yau sai kwanan gida ta kare tana kuka,


Abdoul ma nufan Kareematu suka yi shida yaran ta tare da rike ta,haki take tana fadin Abdoul take me to hospital pls wlhy tallahi kafafu na rawa suke babu Jini a jiki na ruwan jiki na ya kare,Abdoul kafafu na bayana ciki na Zan mutu,


Rungume ta yayi ba tare da damuwa da tulun datti da warin da take yi ba,domin Rabon ta da wanka har ta mance,


Yi shiru Kareematu na in sha Allah babu abunda zai same ki Alhamdulilah tunda har an sake Ku yanzu za mu tafi gida kiyi wanka sai mu wuce asibitin ko,


Cikin kuka tace Abdoul bazan iya wankan nan ba ji nake kamar Zan mutu sai luuuu tayi Baya ta zube a kasa babu numfashi,


Su Khairat da Kannan ta ne suka yo kanta suna Kiran ummah ummah don Allah ki tashi,ganin bata motsi ya Sanya Abdoul saurin taran abun hawa da taimakon wasu Mata suka sanya ta a ciki ya nufi Specialist da ita,


Doc Bashir ko da dafe bango ya samu ya fito daga cikin court in be taba danasanin rashin nuna kulawan Shi ga family in Shi ba sai yau kowa dai sai nan nan yake da zuriar Shi amman  Shi kam ko fly be zo daga  family in Shi ba,haka a sannu Yana Jin jiri Yana komai ya fito daga cikin court room in Yan gulma da suka zo ganin case sai barka Ake yi mishi,


Ba karamin bakin ciki ya ji na rashin zuwan family members in Shi ba saidai wani side in heart in Shi in ya tuno makudan kudadan da ke shake cikin account in Shi sai ya ji duk damuwar ma ta kau,asibiti yanzu zai samu ya je a masa treatment Yana warkewa Los Angeles zai wuce ko bashi suka nuna wa rashin kauna ba toh wlhy sai ya nuna musu shima Dan iska ne,sai yayi good 3 months bayi gida sai sun Raina kansu is a promise ko kwayar shinkafa bare Aje wa ko wace shegiya ba,sai sun San shi suka wulakanta suka nuna mishi be Isa b bayi da gata,sai ya CI uban su gaba daya,gashi zai musu a sannu inda sai sun Kira suna kuka begging in Shi ya dawo,tsaki ya ja tare da yin kwafa sannan ya tare me adedaita sahu da kyar ya iya daga kafafun Shi da suka mishi nauyi ya shiga tare da cewa a Kai Shi RIMI CLINIC,ciniki suka yi ya shiga Akan sai sun Isa zai shiga ya karbi mishi kudin domin sisi wanann babu a jikin Shi,



*********Doc Nameer

    

     Kasan Allah Nameer ko kadan ban so aka Kori karar nan ba,Dan uban su da an yake musu hukunci duk an tura su gidan yari,


Murmushi Nameer yayi tare da daukan tissue a nutse ya goge gefen bakin Shi sannan ya goge hannayen Shi ,kafin ya dago idanun Shi ya zuba su Kan Habeeb,



Ni wlhy ban San me bayin Allahn nan suka maka ba Ka bi Ka tsane su,ya kare kamar ba Shi yayi maganar ba idanun Shi na Kan Habeeb in da is busy enjoying his slice of pizza,


Saida ya hadiye sannan yace wlhh Kai dadi na da Kai Baka da kirki,Ka ji iskanci kamar ba don Kai nake hakan ba,sabida tsanan da yayi maka fa nake taya Ka tsanar Shi,


Nameer can't help it Saida ya saki dariya wani abun ma dai saidai a bar Habeeb in yayi Abu kamar wani karamin yaro in Banda Habeeb wai kishi yake taya Shi can you imagine,


Ka cigaba da dariya ba dai ni Ka mayar Dan iska ba,ya kare a kufule,


Kafadun Shi Nameer ya Dan daka sannan yace dallah Malam tashi mu tafi na biye Ka sai Ka ci box takwa a rasa kudin Siya wa my boy madara,


Dariya Habeeb ya Sanya sannan ya mike shima Yana fadin dadin abun in ni na Rasa akwai Kai zaka siya mashi,mu je muyi clearing bills in mu mu samu mu koma asibiti Kar a neme mu,


Phones in su suka tattare tare da car key sannan suka nufo gurin biyan kudi,total aka musu Nameer ya bada ATM in Shi aka cire kudin sannan suka fito,


Habeeb jakan can ya mun kyau,ya kare Yana pointing wata mini bag daga cikin glass,


Hmm AI Beenazeer na kawo bags and shoes masu mugun kyau harda veils laces and Atampa,Saje is one of the best places da ke Saida Kaya na gani na fada,kayan ta duk masu quality ne saisa at times mutane ke complaining ta cika tsada,saisa ko taste in abincin ta daban ne da na sauran restaurant dake garin nan,ko za mu shiga Ka duba wa mutuniyar ne??


Wuce mu tafi Bani son gulma daga cewa jaka ya mun kyau,na san dai kan Nadeeya kake batun nan toh Banda abunka na Siya ma AI ba iya Sanya wa za tai ba,



Banda abunka kamar gobe ne za ta warke sumul in sha Allah mu zo mu sha biki tunda kace jikin nata da sauki sosai AI ko,


Kai Nameer ya girgiza sannan yace ni nace da Kai auran ta Zan yi,ko kun yi da ita za ta aure ni??


Ah Malam ni dai bazan ce komai ba time will speak wuce mu tafi,Beenazeer dai an Miki bakin ciki,ya ce bare Siya jakar ki ba,


Nameer be ce da Shi komai ba domin ya ga alaman neman maganar sa kawai yake yi,a haka suka shige mota sai hospital,


Duk inda Ka wuce babu chaptan da ake kasawa sai na su doc Bashir wasu suna musu barka an sake su while wasu kuwa ran su be so ba,suna bakin cikin doc bashir zai dawo hospital ya cigaba da zuba mulkin sa,



********Doc Bashir


Kwanan Shi biyu a kwance a hospital in da ya dace da wani abokin Shi doc ne a gurin so Shi ke Kula da Shi,


Ya sha drip sosai tare da magunguna harda Karin Jini Saida aka yi mishi,wanka yayi sosai tare da cude jikin Shi ya tsine wa Sen ya fi cikin kwando Dari,kwanan Shi nawa babu wanka babu wanki,ji yake kamar ya sauya skin in Shi,Shi kanshi kyankyamin kanshi yake yi,


Abokin Shi me suna Doc Ahmed Shi ya kawo mishi Kaya abinci da duk wasu abun bukatu har waya da wallet in Shi ya dauko mishi,ko da ya tambaye Shi ina matayen nashi tsaki Bashir ya ja tare da cewa rabu da Yan iska watan Kada su gida Yana gab da kamawa,


Shi dai Ahmed hakuri ya bashi tare da fada mishi hidimar Mata sai a hankali sai ana yi ana musu uzuri,hmm kawai Bashir yace tare da gyara kwanciya,


Ganin Baya son maganan ne ya sanya Ahmed mikewa yace Bari na dubo wata mara lafiya Zan dawo anjima,sai Ka dawo Bashir yace da Shi tare da komawa ya kwanta tare da lumshe idanu Yana Jin yanda ruwan drip in hannun Shi ke shiga cikin jikin Shi,


Karar Bude kofar da aka yi da mugun karfi ne ya sanya zuciyar Shi bugawa tare da saurin Bude idanu,domin har ga Allah a mugun tsorace yake gani yake kamar mistake kadan xai yi za a maida Shi hannun su Jabiru,



Idanu ya Bude da kyau domin so yake ya tabbatar zargi yake ko hakan ne,a taya ma wa ma ya sanar da Shi inda yake me ya kawo Shi gurin Shi,shine tambayoyin da yake ta running a kanshi,


Da kyar ya Bude Baki yace AFZAAL me ya kawo Ka guri na kuma???





Ayi mun afuwa Charge ne Bani da Shi ,na so ya fi haka yawa,



Yawan comments in Ku yawan typing da update in da za Ku samu,in kuka nade kuka yi shiru ghost readers toh Nima nadewa zan yi in sha Hutu na,



Sai zuwa gobe In me kowa me komai ya yarda,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi🙏🏻

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


........


NA DAINA AJE GROUP LINK INA DOMIN ANA SAMUN MAZA MARA SA TSORON ALLAH NA JOINING SUNA BIN MATAN AURE DA BADALA,DUK ME BUKATAR SHIGA GROUP INA SHOULD TALK TO ME IN TABBATAR MACE CE SAI NAYI ADDING IN MUTUM DA KAI NA,BUT PLS IN HAR KIN SAN BA KARANTA BOOK INA ZAI KAWO KI BA TOH KI YI ZAMAN KI BA SAI KIN YI JOINING BA,



Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


...........

          Page thirty _four


********


 

   Da kyar ya iya bude Baki yace Afzaal me ya kawo Ka gurina kuma???


Da karfi Afzaal ya sake kofar dakin inda Saida yayi making loud noise,sanna ya Shigo cikin dakin cike da takun Isa da kasaita,idanun sa suna Kan doc Bashir Yana jefan Shi da kallon me cike da tsana,


Afzaal am talking to u kana kin responding and kana Kan Shigo mun daki,for crying out loud wat are you looking for,let me be Bana son wani damuwa ko tashin hankali,


Da karfi Afzaal ya janyo kujeran da ke dakin tare da Zama,idanun Shi har yanzu suna Kan doc Bashir kafa daya ya daura Kan daya,tare da shiga girgiza kafan, 


Afzaal this is the last time da Zan tambaye Ka what brought you here,me kake nema,just let me be pls Bana son damuwa,


Damuwa damuwa fa kace Kai karamin Dan iska ne Ashe,Afzaal ya fada a harzuke,


Da Ka kara hakuri ma ni da kaina Zan maka bayanin me ya kawo ni gurin duk da already it's all writing over your face Ka san me ya kawo ni,so nake na Gama kallon fuskan munafuki kuma maciyi Amana irin Ka,


Mikewa Afzaal in yayi tare da cukumo kwalan rigar Bashir ba tare da damuwa da kwance yake gadon  marasa lafiya Yana Shan Karin ruwa ba,


Cikin Ihu yace how dare you little Bastard har Ka Kai ni Afzaal za Ka yi playing ,shiru yayi tare da jijiga Bashir in sannan yace ya muka yi da Kai,Dan Bura uba ni za Ka Raina wa wayo sabida Kai Ka fi uban kowa son kudi,Ka karbi makudan kudade na sanan kayi thinking you are free Ka CI su without yin abun da nake so???


Ina bazai yu ba a sau nawa na maimaita maka make sure Kar a samu wani matsala Ka Bani false hope Kan komai zai tafi yanda nace and yanzu yarinya na can a raye ba a ma San inda take ba sabida zalama da son abun duniya AI Ka neme ni kace toh Afzaal aikin fa be yi ba in dawo maka da kudin Ka ne KO ya???Amman sabida zarme war zuciya Baka yi ba,tunani kake za Ka CI banza ko toh Ka sani wlhy ko cikin rami Ka shige sai ka fito Ka Bani kudi na mutumin banza kawai,


Jin haka ne ya harzuka doc Bashir cikin sauri ya pincike drip in hannun nashi,tare da bige hannun Afzaal mikewa yayi tsam Kan kafufuwan Shi,idanun Shi jajur tsaban bacin Rai,


Sama da kasa yake kallon Afzaal sai haki yake sauke wa kamar Wanda yayi race,


Bani kudi na tsohon mara mutunci Afzaal yace Yana hararan Bashir,


An ki a bada kudin naka,doc Bashir ya ce without any fear,


Idanu Afzaal ya zaro like wat,


Yes Ka ji ni Sarai Nace baza a bada kudadan naka ba and so fucking wat,kudi ne dai sun Shigo Basu kuma fita Ka ji Ka sani,


Kana maganar Imani ko son zuciya akwai Dan iska irin Ka me son zuciyar tsiya AI ni daga Sen da aminin Shi ban taba ganin mugu irin Ka ba,


Sabida Baka da kunya matar Ka diyar Sen kake son kashe wa,Abu be yi ba wai har zuwa kake karban kudadan Ka,ko uban wahalan da nasha kuma WA zai biya ni oho,


Ah lalle bakin Ka ya Bude to hell with the wahala da Ka sha waya dama all I know is that 55 mil ina in gansu gaba na,


Dariya Yan iska doc Bashir yayi sanna ya ja kafa a sannnu ya koma bakin gadon Shi ya zauna,


Ni fa daman na san za ayi haka,tun Randa na baiwa Ahmed ATM ina ya Ciro mun kudi aka ce anyi freezing account ina nace aikin Ka ne,daman I have been waiting for you tun Randa na fito daga prison,


Akan Ka Afzaal har prison na je wani irin bakar wahala ce ban sha ba,da na so Zan iya Kiran sunan Ka in ma nuna evidence Kan cewa Kai da bakin Ka kace a kashe Nadeeya but ban yi ba, because ina da Amana and Ka yarda da ni ne ya sa haka,haka nayi taking blame in a ciki harda wasu nurses ina da ba su ji Basu gani ba,irin azaban da aka gana mana na Wasa ne???


Kasan kwana nawa nayi ban yi wanka ba??babu wanka babu wanki sai wanke idanu,abinci me dandano rabon da na CI tun yaushe???an katse mun rayuwa ta as a qualified Doc iri na wai na kare gidan yari duk sabida Kai and sabida Baka da kunya me makon Ka zo kayi mun godia sai Ka zo kana Bina da maganganun banza da iskanci,


Toh wlhy ni ba sa'an Ka bane,Baka san Waye Bashir ubaidullah ba Akan kudi babu abunda bazan iya aikata wa ba,don haka tun muna sheda juna Ka koma kayi unfreezing account ina KO kuma wlhy In Kai wa Sen evidence in da nake da Shi Akan Ka,ya kare Yana hararan Shi,


Da kallon mamaki Afzaal ke bin Bashir daman Yana da Baki haka,da kyar ya daure yace and wani evidence ne gare Ka da za Ka kaiwa daddy???



A cewar Ka am so stupid ne right gani kake Kai kadai ne me wayo,kamar na san wannan ranar za ta zo duk maganar da muka yi da Kai a office ina wancan ranar anyi recording in Shi,Ka ga in na kaiwa Sen shike nan wlhy har kyautan kudin da ya fi tsiyar da Ka Bani zai yi,Ka ga yanzu Kai za Ka koma abun zargi ba zai taba yarda yarsa bata gurin Ka ba,



Tsaki Afzaal ya ja tare da naushin iska,sannan ya daure yace okay fine Bashir let's do it this way Ka Bani 20 mil Ka rike 25 mil Ka ga shike nan AI ko mun Raba asara???



Dariya Bashir ya kwashe da Shi sannan yace Sisi Afzaal baran Baka ba domin na Riga nayi planning in kudadan nan,don haka ga kofa yanda Ka zo Ka bi Ka fita and make sure to unfreeze my account yau yau din nan domin ina da tafiya jibi if not wlhy tallahi sai dai Ka amsa Kiran Sen,


Idanu jawur Afzaal ke kallon Bashir haka kace ina,Kai Bashir ya daga mishi, murmushi yayi Wanda Ake kira tafi kuka ciwo sannan ya gyada kanshi then we shall see Bashir Ka Kira war wa kanka,In dai ni ne I will make sure to show u shege,da haka ya ja kafa ya fice ranshi a matukar bace tare da bugo kafar da karfi,



Hhhhhhhhhhhhh,in Ka so Ka karya musu kofan shegen yaro mara mutunci ni zaka koya wa bariki abunda a cikin ta na taso,kudi ne kuma na rantse da Allah ban bayar wa ko iyalai na ba kamshin su za su ji ba balle Kai banzan bazara acewar Ka Kai kadai Ka iya Bura uba,ya kare tare da komawa ya kwanta ya dauki wayar Shi Yana latsawa,ni ina Ahmad ne ya zo mu karasa maganar samun Viza ta domin wannan kywawan Yan matan da nake gani masu fararan jiki kamar madara in samu in je in rungume ko uku ne,in ji Suma fararan nan ya taste in su yake,




**************BLAZE🔥 HOUSE 


  

   Kamar yanda suka Saba haduwa don gudanar da meeting in su duk ending of the month,this time around ma haka ne,


Yan kauyen Offa Basu da kwanciyar hankali in har aka ce end of month ya zo,Karan shige da ficen motoci Kam kamar a cikin gidajen su Ake yi,sai Sanya duk ranar da meeting in ke holding kowa ke rufe gida Jen Shi Ka ji kauyen tsit kamar ba kowa,



Babban hall in da aka Saba taruwa don ganawa da Odugwu cike yake da mutane bila a dadin kowannan su sanye da Jajaye da bakaken Kaya mazan su da matan su, while wainda ke son ganawa da Odugwu don biyan bukatun son ransu ke zaune tsirara haihuwar iyayen su,domin doka ce ba a ganawa da Odugwu da Kaya,


Duhu hall in yayi guri yayi tsit sai wasu sautuka Mara dadin sauraro ke tashi a cikin hall in for about 5 mints sannan haske ya bayyana sai ga Odugwu xaune bisa kujeran tsafin iskancin Shi,


Da rawar jiki kowa ya mike tare da Fadi kamar yanda suka Saba suka zube suna me yi mishi kirari suna daukan hakkin Allah tare da bashi a karshe suka yi mashi sujada(wa iyazu billah,ya Rahman duk tsanani duk wuya Kar Ka bar mu muyi barin imanin mu,Ka Kara mana tsoron Ka da ikon bauta maka😭🙏🏻),


Idanu ya zuba musu Yana me jin Isa da mulki Ace duk fadin hall in ga duk gurin Shi aka zo neman biyan bukuta,sai ya saki dariya me ban tsoro Wanda ya so razanar da new members in da suka yi joining recently while Wanda suka Saba da Jin Shi kuwa sun San yau Odugwu na cike da farin ciki,


Umarni yayi musu da su Mike ba tare da bata time ba kuwa kowa ya mike tare da Zama Kan kujeran shi,


Nan yayi umarni da Wanda aka baiwa task KO masu kawo abun sacrifice su Fara kowa wa,


Nan aka hau layi kowa na Mika abunda aka umarce Shi da ya kawo,masu pant ne,used pads be,bra in Mata, masu kawo sassan jikin Dan Adam,zuciya aa koda idanu,rukakkun cikin su kuma irin su Kabiru this time  around jinjirai suka kawo,



Ba karamin dadi masu bada sacrifice in suka ji ba domin ganin yanda Odugwu yayi appreciating,Yana ta dariya tabbas sun San Jinin da suka bada ya karbu kuma yayi farinciki da su,hakan na nuna za su samu biyan bukatun son ransu ke nan,



Sam Odugwu yaki karban sacrifice in Sen kallo wanna ya ki duban Shi balle ya Sanya ran yin magana da Shi,hakan ba karamin kashe mishi jiki yayi ba,daman abunda yake ta Jin tsoro ke nan,saisa yace da Kabiru ma kamar ba zai zo ba don ya san tabbas Odugwu zai yi mugun fushi da Shi,Saida yayi ta kwantar mishi da hankali sannan ya lallaba Shi suka taho,tunda kuwa ya ga Odugwu ya ki karban abun hannun Shi ya San Shi kam yau ya shiga uku,(ni ko nace Baka shiga ba ai duk Wanda ya sake Allah ya kama wani Shi toh Shi da bakin ciki da damuwa sun kulla ke nan),


Bayan an Gama ne masu bukatu suka shiga iso gare Shi kawukan su kasa suna zuba mishi kirari kamar Wanda aka ce Shi ke rike da rayukan su ko numfashin su,


Cike da Isa da izza ya Fadi wa kowa abunda yake son yi in ko kayi Shi babu kuskure toh bukatar Ka tabbas za ta biya,


Bayan ya Gama ganawa da su ne ya mike tare da bin wata kofa Yana me nuni da Sen Kan ya biyo Shi Yana son ganin Shi,


Hantar cikin Sen ne ya kada,har ga Allah be taba Jin tsoron Odugwu irin na yau ba don ko Randa Kabiru ya kawo Shi be tsorata irin na yau ba,



Jiki ba kwari ya mike ya bi bayan Shi Saida ya kwabe tas tukun na ya shiga cikin dakin,


Baki Kirin ko palm in Ka Baka iya gani,AI sai Sen ya zube a nan kasa,cikin kaskantar da Kai,ya shiga rokon Odugwu Fadi yake na tuba na bika kayi mun aikin gafara,in Baka soni Ka tausaya mun ba rayuwa ta za ta tagayyara Kaine gata na, Odugwu Kaine gaba na da Baya na,Kai ne silan samun daukaka ta,na Roke Ka kayi hakuri fushin Ka azaba ce a gare ni ya kare kamar zai yi kuka,


Cikin tsawa me tazanar wa Odugwu yace Kaiiiii Rilwanu,



Jin yanda ya Kira Shi ne ya kuma tabbatar mishi da tabbas Odugwu Yana cikin tsananin fushi da Shi,


Cikin kuka yace na roke ka Odugwu the greatest of all Kar Ka bar ni Kar fushin Ka ya shafe ni,fushin Ka azaba ce gare ni Ka yafe ni na san na kasance me Saba maka,


Tokaran da aka mishi ne Wanda Saida ya Sanya Shi kwanciya flat da bayan Shi ya katse mishi rokon Shi,nan take kuwa huta ya bayana,


Fuskan Odugwu ne ya ga yayi Baki Kirin ya koma sak na katuwar macijiya idanun Shi sunyi kore sharr,sai fiddo da halce yake ta faman yi,


Ba karamin tsorata Sen yayi ba tabbas duk abunda zai Sanya Odugwu rikida har ya canza sufa toh ba karamin Abu bane,


Cikin fushi ya daga hannun Shi tare da matsewa sai GA Sen ya mike Sama Yana kakari sakamakon shake mishi wuya da Odugwu yayi,


Nan ya shiga jujuya Kai Yana tare kamar Wanda Ake zare wa Rai sam numfashin Shi ya kasa fito,Banda hawayen azaba babu abunda ke fitowa daga idanun Shi,a haka ya samu ya hade hanayen Shi guri Daya alaman dai roko yake har iyanzu,



Saida Odugwu ya ga Sen Yana neman mutuwa tukun na ya sake Shi tare da watsa Shi kasa ji kake Tim a take goshin Shi ya fashe,



Tare Sen ya shiga yi kamar ranshi zai fita idanun Shi sun firfito lokaci daya har ya canza kamanni,


Kafin ya Kai ga dawowa setin Shi sai Jin manyan kafan Odugwu Akan cinyar Shi ya take Shi,



Wata irin radadin zafi da azaba ya ziyarce Shi Amman sam babu daman Ihu hawaye kawai ke fitowa me dumi daga cikin idanun Shi,


Rilwanu Odugwu ya Kira cikin daga murya Saida dakin gaba daya ya amsa,


Naam Odugwu na ka yafe ni my lord,


Rilwanu you are playing with fire, Kai Kan Ka kasan Waye ni,tun zuwan Ka brotherhood in nan nake kaunar Ka kasancewar kana baiwa kungiya abunda take bukata a duk sanda ta nema,ya Sanya wasu cikin mu ke Jin haushin Ka suna ganin kamar na fi kaunar Ka ne,


Na daka maka kafa da dama a rayuwar nan na Baka abubuwa da yawa har da ma Wanda baka roka ba,na cika maka dreams in Ka da dama kuma ina Kan cika maka ma Zan ce,na maida duk wani impossibles in Ka sun koma possible,na Baka fame money ,da duk wani abunda kake takama da Shi,ita Kan ta Yarinyar da kake masifan kauna da ban so ba do you think za ta zo duniya ne??ya kare Yana tofa wa Sen yawu a fuska na tsaban masifa,



Zuciyar Sen Banda zafi da kuna babu abunda take yi,idanu kawai ya rintse Yana me sauraran maganganun Odugwu,



You have gain a lot tun sanda Ka shigo cikin mu from nobody na maida ka me fada a ji a duk fadin garin Ku, duk cikin harshen turanci Odugwu ke bayanin nan,


Amman na ga alaman gani kake kamar bazan iya punishing in Ka ba,mancewa kake da ni da ya sanya Ka crossing limits inka,


Tun haihuwar yarinyar nan nace da ita namu ce Ka Bani Jinin ta kaki yarda,Ka Bani soul in ta kaki,Ka Bani brain inta Ka ki, da kyar na samu Ka bamu WOMB in ta,why on earth Ka Bari tayi nisa da Kai???



Cikin kuka Sen yace na roke ka kayi hakuri Odugwu the greatest ni kaina neman ta nake babu dare babu Rana,


Ka kuwa san me hakan ke nufi??bacewar yarinyar nan tonuwar asirin Ka ne kuma tonuwar asirin Ka na mu ne Baki daya kamar yanda kullum nake fada,



Rilwanu Baka ji,tun haihuwar ta da Ka Bani ita da duk haka be faru ba,


Na sani Odugwu na sani kayi hakuri a Nemo mun ita Ka taimake ni Kai kadai za Ka iya mun wanna aikin,



Dariya Odugwu yayi me abun tsoro sannan yace kana da son Kan Ka Rilwanu,tabbas zan gano inda take amman kafin nan dole Sai an yi maka punishment in da Ake wa duk Wanda ya karya mana doka,



Hannu ya tafa AI kuwa sai GA wasu majiya karfi su hudu sun Shigo da bulalai masu kauri da girma a hannayen su fuskan su babu alaman Imani ko tausayi,


Sen be farga da abunda zai faru ba sai ji yayi an daga Shi an wulla Shi Sama tare da cabewa nan ko suka mike Shi,


Beat the hell out of him shine abunda Sen ya ji Odugwu yace,nan ko kamar Wanda Allah ya aiko su suka shiga tsula wa Sen bulalun nan a jikin sa,Ihu yake Yana kuka da hawayen Shi bazai iya tuna when last aka buge Shi ba,


Baka Jin komai sai Karan saukan bulalai da ihun kukan Sen Fadi yake Odugwu am sorry pls forgive me,tun Yana iya magana Har ya koma numfashi kawai yake iya saukewa,sai hawaye,


Basu suka dakata ba Saida suka ga Jini na zuba daga bayan Shi,sanann Odugwu yace da su aikin su yayi kyau su tafi,



Nan suka yarda Sen jiki ba dadi suka yi gaba abun su,


Yatsa wanann Sen ya kasa dagawa ba tare da Odugwu ya kalli KO inda yake ba ya sa Kai ya fice abun Shi,


Kabiru ne da ke bakin kofa yayi saurin shigowa cikin dakin tare da nufan inda Sen yake cikin sauri ya dago Shi ina babu numfashi jikin Shi,


Da gudu ya Ibo ruwa a toilet tare da watsa mishi wata irin wawan ajiyar zuciyar Sen ya ja sannan ya Bude idanun Shi,


Suna hada ido da Kabiru kuwa ya fashe da wani irin kuka Wanda Zan iya Kiran Shi da na takaici ne ko bakin ciki,


Sannu Aboki na yau kam tabbas ran Odugwu ya Baci da Kai,


Cikin kuka Sen yace Kabiru na gaji na gaji,shekaru nawa ina bautan Odugwu ina kyautata mashi ina bin umarni Shi amman Ka duba Ka ga diban Albarkan da ya sanya aka mun,ya kare Yana kuka,na gaji Kabiru Bana Jin Zan iya cigaba da Zaman kungiyar nan,I have sacrificed enough,abubuwa nayi losing daga Randa na shiga kawo yau,



And abubuwa nawa kayi gaining where u like this before???shine tambayar da Kabiru yayi mishi,



Maganar fita ma fa bata taso ba,abubuwa nawa Odugwu ya Baka,in ce na hadu da Kai kana fama da muguwar Talauci duk wani kayan wanka da Gaye na samari Baka da Shi, Odugwu miye be Baka ba ya Baka gida mota,kudi har mulki aboki na Kar Ka zamo butulu mana,



Butulu fa kace Kabiru duk abun nan da ya Bani are they for free??in ce Saida yayi demanding something in return miye ban yi ba abunda in duniya suka ji wasu daga cikin mugayen abubuwan da na aika ta sai sunyi mun tofin Allah tsine I don't think I can continue with this thing gaskia Sen ya Fadi da iyakan gaskiar da,



Dariyar you most be joking Kabiru ya yi WA Sen sanna yace Ka ma isa,as I told u in an shiga babu fita Ka kuma yarda Ka shiga you have to bare da duk abunda Ka gani,Ka ma gode wa Allah Odugwu na kaunar Ka ya Sanya aka yi maka punishment me sauki,Ka tashi Maza Ka maida kayan Ka mu je Ka Kara rokon Shi yafiya ya samu ya sanar da Kai in da yarinyar nan take lokaci na korewa kasan in aka Riga aka yi serving abinci toh ya Gama Jin complains kuma Sai dai next meeting.....




Assalamu alaikum



Ayi mun hakuri 2 days busy na shiga wlhy ziyara na je kuma inda na je ba a cika samun wuta ba ya Sanya kuka jini shiru,



Sai zuwa Monday kuma in sha Allah,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi .

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


........


NA DAINA AJE GROUP LINK INA DOMIN ANA SAMUN MAZA MARA SA TSORON ALLAH NA JOINING SUNA BIN MATAN AURE DA BADALA,DUK ME BUKATAR SHIGA GROUP INA SHOULD TALK TO ME IN TABBATAR MACE CE SAI NAYI ADDING IN MUTUM DA KAI NA,BUT PLS IN HAR KIN SAN BA KARANTA BOOK INA ZAI KAWO KI BA TOH KI YI ZAMAN KI BA SAI KIN YI JOINING BA,



Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


...........

          Page thirty _five


********


   Da kyar Sen ya Mika wa Kabiru hannu sannan  yace "kama ni in tashi Bana Jin Zan iya mikewa,Dan ba karamin duka na sha ba" Sen Rilwanu ya kare kamar zai yi kuka,hannu Kabiru ya Mika mishi tare da taimaka mishi ya mike da kyar jikin Shi duk yayi tsami,


"Ka yi sauri Ka maida kayan Ka mu samu mu je gurin Odugwu kafin a Fara rabon abinci Alh Kabiru ya kare mikawa Sen kayan Shi",


"Sanin kan Kane Kabiru in har za a gana da Odugwu dai ba Kaya ake sanyawa ba so mu je kawai!!ya kare a harzuke",Kabiru be ce da Shi komai ba Ila nufan kofa da yayi,'domin har ga Allah abun abokin nashi ya Fara bata mishi rai,Akan me Shi Ka dai ne ya san dadin jikin Shi Kenan,ko kuma kan shi Odugwu ya fara punishing masu laifi???ko ance dashi a kan Shi za a kare,ba kanshi farau ba ba kuma kanshi za a gama ba',da wannan maganar zucin ya bar cikin dakin,


Da kyar Sen ya iya jan kafafun Shi da suka yi mugun tsami ya samu ya fito da kyar yana me dafe bango,



A private chamber in Shi suka samu Odugwu yana zaune ya daura daya kan daya kamar wani sarki,zubewa suka yi gaba daya tare da yi mishi sujada(wa'iyazubillah)"cikin tsantsan nuna isa da iza Odugwu ya fara magana cikin murya mara dadin sauraro,Fadi yake na amsa bukatun ku za ta biya Kabiru, Rilwanu ya ci albarkacin Ka,da abubu abunda zan kuma yi da Shi,ya kare a harzuke!!",tashiwa suka yi tare da Zama a nan kasan sanann cikin tattausan murya Kabiru yace"duba muke Odugwu the greatest in Ka bar mu rayuwar mu za ta shiga garari,duniya za tayi mana dariya,Kaine kadai gatan mu, Kar ka juya mana baya,Ka cigaba da taimakon mu kamar yanda Ka saba Odugwun mu"


Dan Jim Odugwu yayi ya ki ce wa komai,'ganin hakan ne ya sanya Sen kankar da Kai ya shiga roko akan ya gane kuskuran Shi Odugwu ya taimaka ya mishi aikin gafara sannan ya sanar da Shi inda yarinyar Shi take',Saida Odugwu ya gama musu jan aji da kallon wulakanci,sannan ya mike,tafiya yake cikin Isa Yana girgiza jiki,jikin wani dogon Abu ya tsaya Wanda aka rufe da bakin kyalle,tafa hannuwa yayi sai ga kyallen ya yaye da kanshi,nan wata rangadediyar madubi ya bayyana,idanu Odugwu ya rufe "tare da Fara chanting in wasu yaruka marasa dadin sauraro,wanda Shi karan kanshi Bana tunanin Yana sanin abunda yake fada", 'ya dauki Kusan 3 mints Yana yi sai ga madubin tayi Baki Kirin,Wanda ya sanya shi lumshe idanu,domin in hakan ta faru yana nunin zai cimma burin shi ke nan,


Madubi ce da yayi masa lakabi da madubin tsafin shi,Yana daga zaune da ya bude mirror in ya shafa toh duk information ko wani sakon da yake son aikawa,a take zai tafi,


Idanu Odugwu ya zaro babu shiri sakamakon ganin har iyanzu madubin tana nan a bakin ta,babu alamun haske,balle ya sanya ran zai gano inda Nadeeyar take,amman dake kwararan Dan iska ne,sai ya kuma rufe idanu,tare da kara karanto wasu surkullan tashi,amman har iyanzu Yana nan a Baki babu haske balle ya sanya ran zai gano inda take,abunda ya fi bashi mamaki ma shine the more yayi trying gano inda take,sai ya ga madubin ta kuma Baki,Kusan 30 mints ya dauka yana baje duk wata basiran tsafin shi amman ina,babu Nadeeya babu alamun ganin wanda ya sace ta,a nan take gumi ya keto mishi,tunda ya fara wannan muguwar aikin nashi babu abunda ya taba gagaran Shi sai this time around,'wat so special about this girl ne?'ya tambayi kanshi Rai a bace!!,juyowa yayi tare da nufan kujeran Shi ya zauna,yana me maida numfarfashi kamar wanda yayi tsere wai duk a hakan ranshi ne bace,


Zama su Sen suka kuma gyara wa Kan su a kasa,suna jiran Jin bayani daga bakin Odugwu,Saida yayi gyaran murya sannan yace"Rilwanu akwai matsala ina Jin bacin ran da Ka sanya mun yau ne ya shafi dodon tsafi,shima da alamun yayi fushi sosai,don kwata kwata na kasa samun biyan bukata na",ya kare yana shafa kan katuwar macijin dake rataye a wuyar Shi,"Odugwu the greatest babu abunda ba Ka iya ba babu abunda ya gagare Ka,now wat is the way out pls,"Alh Kabiru ya Fadi kamar zai yi kuka,wani irin kishingidiwa Odugwu ya kuma yi Kan kujeran tsafin Shi kafin yace "dole ayi making blood sacrifice,and this time around Jinin me ciki Ake da bukata, both mom and the baby za a kawo,and make sure cikin nata ya Isa haihuwa  ,Jinin su muke da bukata"  'cikin Sen ya duri ruwa har ga Allah at times ya kan ji dama be Shigo kungiyar nan ba, domin wasu abubuwan da ake sa shi aikatu su' saidai babu yanda ya iya ne,kafin ya kai ga maganar a ina za a samu mace me ciki,ya ji Alh Kabiru yace"Odugwu babu komai Zamu kawo",


Nan ko suka shiga mishi kirari,Shi dai Sen duk jikin Shi a mace,da haka suka fito daga cikin dakin,bayan sun maida kayan su jikin su,hall in suka nufa inda suna Zama aka fara serving fresh Naman mutum a plate,with warm blood a glass cup, without tsoron Allah ko tunanin mutuwa gaba daya hall in kowa nutsuwa yayi Yana enjoying abunda yake ci,baka Jin komai sai tashin Karni,da kuma karan su cokula,Saida kowa ya gama cinyewa ya goge baki sannan duk suka mike suna me kara yi wa Odugwu kirari da godia,cike da isa da izza "yake nanata musu abubuwan da ya Saba Fadi musu kullum in an zo karshen meeting in,a karshe ya rufe da duk wata me bukata ko wace iri ne Kar ya tsorata ya zo gurin Shi in har ya bi abunda kungiya tace,toh bukatar Shi za ta biya,sannan duk wanda aka bai wa task yayi kokari ya ga yayi yanda ya dace,at the end kuma shine kowa ya guje wa tonuwar asirin shi domin tonuwar asirin daya na duka kungiya ne",ya kare cikin muryan tsawa!,duk nan suka zube tare da yi mishi sujada suna me zuba mishi kirari,ba su suka dago ba Saida suka ga,wata bakin hayaki alamun ya gwada Odugwu ya bace ke nan,kowa mike wa yayi aka Fara haurawa Sama domin canzo kaya,kamar yanda suka saba,bayan canza Kaya sai ka shiga dakin da gunki ya ke ka tsotsi private part in Shi,sannan su fito kamar mutanan kirki, fuskokin su cike da annuri sai gaisawa suke da Yan uwan su ana sai kuma next month,da haka suka Fara watsewa,wasu fuskokin ko bindiga za a daura miki a kai,za ki yi denying suna zuwa gurin Odugwu,sabida yanda suke nuna su na Allah ne a kasar nan,(saisa aka ce Kai dai Ka ga mutum Ka bar Shi,babu wanda ya san halin Dan Adam sai Allahn da yayi Shi,Allah duk tsanani duk wuya Ka bar mu da imanin mu),


A motar Kabiru daman suka taho,this time around ya bar Sa"eed a gida,so Kabiru ke driving har suka iso harabar hotel in da suka Saba sauka duk ending of month in sun zo meeting,


"Aboki na ya aka yi ne duk na ga mood in Ka wani iri,I hope all is fine ko"??Alh Kabiru yayi tambayan yana tsare Sen da idanu,



Numfashi Sen ya sauke,ya girgiza Kai a hankali sannan yace "babu komai Kabiru mu samu mu shiga ciki ina son gasa jiki na da ruwan zafi ko zan ji dama dama", "a tayaya za Ka ce mun babu komai,ba fa sanin jiya na yi maka ba Rilwanu just tell me wat is bothering you"??seat belt in jikin Shi Sen ya cire sannan yace Rilwanu am just thinking about Nadeeya yau Kusan month nawa don am sure ya fi weeks Amman babu yarinya babu alamun ta,and hope ina daya ne za mu gano inda take gurin Odugwu Ka ga shima ya kasa gano in da take",ya kare kamar zai yi kuka,


"Haba Sen Ka daina fadin ya kasa gano inda take,babu abunda ya gagari Odugwu fa,ko Ka mance he is the greatest of all ne,Kai kan Ka ba sai na baka labarin irin karfi da abubuwan da Odugwu yake yi ba,so kamar yanda yace fushi Ake da Kai,dole sai an bada blood in nan,now just chill and have fun har mu koma Bauchi mu Sami me ciki mu bada Jinin ta ba shike nan ba",ya kare yana murmushi,


"Hmmm Kabiru ke nan,yanzu in mun koma Bauchin a ina ne za mu Sami me tsohon ciki mu bada Jinin nata??, "Wannan duk ba matsala bane Ka bar komai a hannu na ni dai damuwa ce bani son ganin Ka a ciki,oya chill up Ka saki ran mu shiga a Nemo maka latsa latsan Yan mata,su taya Ka raba dare,ya kare cike da dariyar shakiyanci", "Bana son iskanci Kabiru kai sai kana abu kamar Baka San komai ba, beside ni ina naga nutsuwar da har zan ji wata sha'awa har na nemi mace,Kai dai jarababbe Ka je kayi ta yi"ya kare tare da Bude kofar ya fito,shima kabirun dariya ya Sanya tare da fitowan,a tare suka shiga cikin hotel in inda suka yi booking separate rooms,Sen ya shige nashi kai tsaye toilet ya fada,Yana me jin haushin Odugwu a ranshi Amman babu halin bayyanawa, domin Kabiru tun farkon joining in Shi ya sanar mishi duk abunda aka fadi a bayan idanun Odugwu yana ji,gudun Kara shan duka ya Sanya ya ja bakin Shi ya tsuke,ya shiga gasa jikin Shi da ruwan zafi,


While Kabiru ficewa yayi tare da Nemo tika tikan yaran yarbawa,wanda Allah ya zuba wa albarkacin jiki har su uku don zalama,Saida ya biya yayi musu take away don abincin hotel in be cika wa Sen dadi ba,sannan suka dawo,abincin ya baiwa Sen tare da yi mishi Saida safe,sannan ya wuce dakin nashi,Saida suka ci suka koshi suka yi nak, sananan ya haura kan gadon bayan ya tube tas,ya wani mikeke,Yana jiran yaran cikin Shi su jiyar da Shi dadi,(Allah Ka nisan ta mu da zina da masu aikata Shi,masu yi in masu shiryuwa ne ubangiji Ka shirya su,in ba masu shiryuwa bane Allah Kai Ka san yanda za kayi da su),haka wanann daran suka raba Shi gurun tambada da iskanci,ba su suka sarara ba sai dab za a Kira asuba,nan duk suka baje sai baccin gajiya, ganin haka ya sanya Kabiru tashi da sauri ya Bude jakar Shi,wata jar kyelle ya dauko tare da goga wa ko wanann su a gaban su,dariya yayi tare da girgiza Kai,Yana mamakin rashin wayo irin na su,Sarai sun san su Yan cultism ne amman ba shi zai hana su Bude musu Kafa ba,a wayon su sai su zo haka nan babu pant gudun Kar a dauke ayi kudi da su, without knowing in sun yi bacci,Akan goga kyelle gaban su,Wanda sanadiyar haka suke rasa womb na su,maida kyellen yayi akwati ya rufe sannan ya dawo ya kwanta tare da rungumo daya daga cikin yaran Arnan,babu lissafin wankan janaba balle sallahn asuba a cikin ranshi,nan ko bacci yayi awun gaba dashi,



Ba su suka tashi daga baccin asarar tasu ba sai around 10 in safiya,hakan ma knocking in Sen ne ya tashe su,


Kabiru ne ya Bude kofar tare da ba wa Sen guri ya Shigo,shigowa yayi tare da Zama a Kan kujerar dakin,


Yan matan yake bi da kallo Yana jinjina rashin tsafta irin na abokin nashi,in Banda haka ko wuka za a Sanya mishi a wuya bare iya kwana da irin wanann kazaman ba,gaishe Shi duk suka yi,ya amsa musu da hannu,


Da sauri Kabiru ya sallame su ganin har Sen ya shirya suka tafi bayan sun bashi no in su wai pls ya neme su in ya kuma dawowa,toh kawai yace da su,sannan ya fada wanka,Saida suka yi breakfast sannan suka dauko hanya suna tafe suna hira,




  **************3 days later



    Zaituna jikin ta yayi sauki,tana warkewa kuwa hospital ta nufa a take tayi resigning acewar ta baza ta iya cigaba da aiki a karkashin su Bashir ba karshe bata san wani irin sharrin za su kuma Mata ba,babu yanda sauran nurses in Basu yi ba don shawo kanta,Amman tace sam baza ta iya ba ta gaji,gwara ta canza guri,a haka aka yi rabuwar mutunci,suna yi Mata fatan Alkhairi ta fice,ta so ta Hadu da Kareematu ko kuma Shi bashir in Amman duk Basu zo ba,da tayi musu wankin babban bargo,



Hajiya Kareematu ma jikin ta yayi sauki domin Abdoul tsaye yake a kanta,Jira yake tace tana son Abu tuni zai Nemo Mata,komai Shi yake Mata wasu abubuwan ne su Khairat ke taya Shi,a haka har aka sallame ta ta dawo gida,bata yi resuming aiki ba tace sai ta kuma warware wa,ba karamin dadi Abdoul da yaran Shi suka ji ba,ganin kullum tana gida rabon da ta zauna cikin su har sun manta,nan Abdoul ya mike ya shiga neman kudi don cigaba da ciyar da ita dadi,tunda ta kwanta asibiti take cin kayan dadi har yanzu,ita har mamaki take irin wannan kauna da kulawar da Abdoul ke yi Mata,har yau be kuma tambaye ta miye alakar da ta doc Bashir ba,balle ya ji akan me yasa aka kama su tare,


Suna zaune ya na matsa Mata kafa tana dan fifita kasancewar ba wutan Nepa,kallon Shi tayi yanda yake matsa Mata kafa cikin nutsuwa da kulawa,sai ta saki murmushi tabbas Abdoul ya cika mijin da ko wace mace za ta so samu saidai matsalan ta daya da Shi,shine kuwa Talauci,abunda ya sanay ya fice Mata a kai ke nan,(Yan Maza Ku ji tsoron Allah wlhy duk wanda yake da halin CI da gidan Shi ya bar wa matar Shi ragamar gidan toh sai sun tsaya gaban Allah domin cin ta da Shan ta har sutura suna rataye ne a wuyan Ka,and ciyar da iyalai lada gare shi yana kuma daga cikin abunda yake Kara Sanya wa budodin samun miji ya Karu,sannan Yana kara wa miji martaba da kima,a idanun iyalan Shi),


Cikin taushin murya tace"ni kam Abban Khairat har yau in ta jiran in ji ka tambaye ni game da case ina da su doc Bashir amman shiru Baka tambaya ba,miyasa,


Murmushi yayi har hakwaran Shi suka fito sannan yace"Kareematu ke nan wlhh yardar da nayi da ke Bana Jin ko kaina na yarda da Shi haka,ba Zan boye Miki ba na ji ji maganganu da dama,Akan ki da Bashir Amman ban dauki ko daya ba,balle na Bari zargi ta shiga Raina,abunda na sani shine kawai abunda ya faru da Ku kaddara ce,ina son ki Kareematu na and na san ke ma kina so na,duk tsanani na san Waye ke tun kina yarinya,a bar ki da rashin Jin ki dai,da neman magana amman harkan bin Maza kam ko gurin Allah Zan shedai ki Baki yi,baki yi tun kina budurwa ba sai yanzu ne za a yi tunanin za ki bi Maza??don haka ni ban ma bai wa zancen nasu mahimmanci ba,bakin su ne ba mu Isa Hana su fadan abun da suka ga dama ba,yarda ne na mu,kuma ni dai na san na yarda da ke Dari bisa Dari bara ki taba cin Amanar aure na ba",ya kare yana murmushi,


Ba karamin sanyin jikin Kareematu yayi ba har hawaye ta ji suna bin idanun ta,wani irin kunyar hada ido da Abdoul in ma take ji,ana cikin haka kuwa Nepa suka maido wuta,mikewa yayi tare da cewa "barka an kawo wuta ki samu maza Ki kwanta, ubangiji ya kara sauki",bata iya bashi Amsa ba ma ya sanya kai ya fice daga dakin,wannan dare Kareematu bata iya bacci ba duk inda ta juya maganganun Abdoul ke dawo Mata a Rai,



*********Doc Bashir


     "Me gida tsakani da Allah kana ganin abunda kake yi ya dace ke nan,ace Ka aje Mata har uku a cikin gidan Ka Amman ciyar da su ya gagare Ka,kuma Allah ya rufa ma asiri ba wai babu bane,Anya kana tsoron Allah kuwa"??Hadiza ta kare tana me jefan Shi da kallon tsana,



Be ce da ita komai ba sai cigaba da hada kayan Shi cikin akwati yake yi,cikin sauri don jirgin karfe 12 zai bi,


"Doc magana fa nake yi sabida Allah rabon da Ka ba da kudin cefane a cikin gidan nan wallahi baran iya tunawa ba,kana ganin hakan daidai ne??sanin kan Kane dai ba wani aikin Azo a gani muke yi ba balle kayi tunanin sakar mana gida a hannun mu"ta kare a harzuke!!,


Saida ya Gama hada kayan Shi tsaf yayi zipping akwatin sannan ya dago cikin kallon wulakanci ya Gama kare Mata kallo sanann yayi kwafa,"da na bar Ku har yanzu kuna zaune mun cikin gida ne ya Baki daman fada mun magana son ranki,har akwai marasa tsoron Allah irin Ku,ace a kama ni kwana na nawa a daure,akwai Dan iskan da ya zo duba ni a cikin Ku,daga Ku har Yaran naku tara Ku nake wallahi Baku san waye ni ba Amman za Ku gane baku da wayo,kamar ni ace a rasa wanda zai zo duba ni AI wlhy Hadizatu Ku Kara gode wa Allah da ban Kada Ku gidan Ku ba,amamn tunda na ga alamun kun gaji Bari na dawo daga tafiyar nan sai na sallame ku a koma kauye",ya kare yana daukan akwatin Shi,


Yanzu Bashir don na fada maka gaskia shine za Ka mun barazana da saki,da kake maganar babu Wanda ya je duba Ka kila Ka bar mana kudin abun hawa ne,ko da kafafun mun kake son mu je har court mu duba Ka??, Amman babu komai duk abunda kake Allah na kallon Ka ai,da sannu zai bi mana hakkin mu",


"Ya bi mana tare a cewar ki ke kadai Allah ke so yanda kuke cuta na Nima sai Allah ya Saka mun,yan iska marasa mutunci"ya kare Yana hararan ta,


"Anty Hadiza da kin kyalle Shi domin yayi nisa Saida mu roki Allah"dayar matar Shi tace da ta Gama Jin duk yanda suka yi,be Kula ta ba ya dauki makulin motar Shi,


"Yanzu doc sai yaushe za Ka dawo??,Hadizatu ta kuma tambayar Shi",


Dariyar Yan iska ya Sanya sannan "yace yanda kuka banzartar da ni kuka nuna mun tsana to ko ba dawowar yanzu ba zan je inda za a so ni a martaba ni,a tattalani,in ta kama ma a Goya ni,sannan Kar wace yar iskar da ta kuskura ta dame ni da waya,in ba haka ba a bakin auran ta",


"Don Allah toh Ka taimaka ko dubu hamshi ce Ka bada mu samu ayi cefane kafin Ka dawo in,"


Nan ma dariyar ya kuma yi sannan yace"na rantse da girman Allah Sisi Hadizatu bazan bada ba tunda Baku da mutunci Baku san darajar aure ba,ban kuma yarda ko kafar gida Mata ta je ba,bautan aure kuka zo yi don haka a zauna ayi ta bauta, Aljannar mutun na karkashin kafa ta in na so in dage ya shige in naso in take Shi",ya kare Yana gefa wa Fatima da ta ce a yi ta hada Shi da Allah kallo alamun da ita yake ke nan,daga haka ya sa Kai ya fice Yana jiyo magiyar da Hadizatu wacce take uwar gida kuma uwar yaran Shi ke yi mishi Akan Kar ya tafi be bada kudin cefane ba,yaron su akwai Mata in su sun jure yunwa ba lalle yaran su jura ba,a irin haka Yara ke lalacewa,Amman ko a jikin Shi,akwatin Shi ya jefa bayan mota,sannan ya shiga, tare da bashi wuta,


Kai tsaye hospital ya nufa,Yana wani tafiya kamar ba zai taka kasa ba,wai Shi a dole me kudi,shiga yayi yayi cike ciken daukan hutun da zai yi sannan ya fito,a bakin asibitin ya Hadu da Habeeb da Nameer suna tsaye suna hira,


Gaban su ya iso,tare da kare musu kallo me cike da tsana,sannan ya daure yace"toh Doctors a Sanya mu a Addua yau kuma Sai San Francisco,a Kula da hospital sai Allah yayi mun dawo",be Jira amsan su ba ya sa Kai ya wuce burin Shi daman ya fada musu magana ne su San cewa yes Shi din fa ba matsiya ci bane,


Me Nameer da Habeeb za suyi Banda dariya,akan idanun su ya zo ya wuce da motar nashi,Kai Nameer ya girgiza sanann yace "Allah ya sauki Dan San Francisco lafiya"dariya ya Hana Habeeb amsawa domin in ya tuna shigar jikin doc Bashir sai ya kuma fashe wa da dariya,



Hanyar airport ya dauka yana tafe tana Jin waka,ga wata uban sun glasses a idanun Shi kallon Baki,waya ya dauka tare da Kiran Ahmad,ya sanar da Shi kan in ya Isa zai Kira Shi,ya zo ya dauki motar ya kai gidan Shi ya aje mishi har sai ya dawo,(Yana gudun ma kar iyalan Shi suyi using in Baya nan),


Wani irin wawan burgi ya ja ganin wani dattijo a gaban Shi ya Kusa bugewa,duk inda ya so Kar ya buge Shi amman Saida ya taba Shi,hakan ne ya sanya Shi Jan burki,tare da fitowa da sauri ya zare glasses in,tare da durkusawa Yana fadin"sannu tsoho hope Baka ji ciwo ba??",be Kai ga rufe Baki ba ya ga wasu irin gardawan maza manya manya Kusan su biyar a tsaye a kanshi,duk sanye da bakin mask in fuska,


Idanu ya zaro tare da saurin mikewa Yana "na shiga uku bayin Allah daga ina", gudu ya ke son sanyawa ya nufi motar Shi,Amman dayan ya Sanya mishi kafa tare da tatile shi,sai ga Shi a kasa timmm,ya buga fuskan Shi,Ihu ya Sanya Yana fadin "na shiga uku wai su Waye Ku,be Kai ga rufe Baki ba,ya ji saukar kan bindiga a kan Shi tunda ya Kara sakin wani ihun be kuma sanin yanda Kan Shi yake ba nan gurin ya sume musu,ganin ya Suma ne ya sanya suka dauke Shi suka jefa Shi mota dake hanyar airport in wajen gari ne ya sanya babu yawaitan mutane a gurin,mota suka ja a 360 tare da yankan daji a guje,daya daga cikin su ne ya dauki waya tare da Danna Kira,


     "Sai oga shine abunda ya Fadi" bayan an amsa Kiran,ban ji me aka ce daga can bangaran ba,sai ji nayi yace"mun dauko shegen yanzu haka ma mun kamo hanya",dariya ya Sanya sannan yace "Allah bar mana kai oga sai mun iso"da haka ya kashe wayan tare da cewa "dattijon da Bashir ya buge Kan ya Kara gudun motar su samu su Isa da wuri oga na jira".




Iya yawan comments in Ku iya yawan typing😊



Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


........


NA DAINA AJE GROUP LINK INA DOMIN ANA SAMUN MAZA MARA SA TSORON ALLAH NA JOINING SUNA BIN MATAN AURE DA BADALA,DUK ME BUKATAR SHIGA GROUP INA SHOULD TALK TO ME IN TABBATAR MACE CE SAI NAYI ADDING IN MUTUM DA KAI NA,BUT PLS IN HAR KIN SAN BA KARANTA BOOK INA ZAI KAWO KI BA TOH KI YI ZAMAN KI BA SAI KIN YI JOINING BA,



Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


I have always admired your work and am very happy that you were able to complete your book (Ya fita zakka),in spite of all the other demands on your time, Congratulations Mom sayyid Ubangiji ya karo kaifin basira.

   

...........

          Page thirty _six


**********


    A hanzarce Mama ta ida Azkars in idar da bayan sallah ta mike cikin sauri,don ko samu tayi Azkar in maraice bata yi ba,kasancewar sallar la'asar ta ida,cikin sauri ta mike,ba tare da ta cire hijab in jikin ta ba,ta nufi gadon da Nadeeya ke kwance,


Tun tana sallah take juyo numfashin yarinyar na fita kamar ana ƙoƙarin zare mata ruhi,Allah kadai ya san a tayaya ta samu ta ida sallar nan,


Kan gadon ta hau tare da zubawa Nadeeya idanu,wanda sai uban zufa take hada wa kamar wace ta hadiye kunama,idanun ta a rufe kirib,Amman daga ganin alamun ta za ka fahimci mummunan mafarkin da ta saba yi take yi,ganin inda take ta faman sauke numfashi da ajiyar zuciya da kyar,


Salati Mama ta sanya tare da fadin,"not again please"ta kare cike da jimami tare da kai hannun ta jikin Nadeeya zafi sosai ta ji wanda saidai ya sanya ta saurin janye hannun nata,cikin jarumta ta mike tare da dauko cup,jarkar ruwan zam zam in da ke gefan ta,ta janyo tare da zubawa a cikin cup in,nan  ta shiga karanto duk wasu addu'oin da ta iya ta shiga tofawa a cikin ruwan,


Kusan 5 mints tana addu'oin sannan ta iba a hannu tare da shafawa Nadeeya a fuska,nan take kuwa ta ja wani irin ajiyar zuciya,wanda saidai ya kusa razana mama don tsaban karfin ajiyar zuciyar har gani take kamar Nadeeyar ta mike ta zauna,sannan ta koma ta kwanta,


Jarumta ta aro tare da kara shafa mata,this time around ma numfashin ta kuma ja,sanan mama ta bude bakin ta wanda gam ta gade hakwaran ta,saida ta matse mata hanci da kyar ta samu ta raba hakorin nata,sannan ta dan zuba mata ruwan,saida ta ga ya wuce makoshin ta sannan ta sake hancin,(in ba hakan tayi mata ba sam ba shan magani ko wani ruwan addu'a take ba,sai tayi kamar ta hadiye anjima sai ka ga yana biyo gefen bakin ta),


 

Kwalbar Habbatus sauda ta dauka tare da kare matse mata baki ta bata spoon daya,sannan ta shafa mata a fuska,wuya,hannu,da kafa,aje wa tayi,tare da ɗaukan zuma,nan ma spoon dayan ta bata,sannan ta janyo wayan ta don kiran Nameer ta sheda masa halin da suke ciki,don har yanzu zafin jikin nata be sauka ba,



Kiran farko har ya gama ringing ba a dauka ba,saidai ta kuma kira sannan ya dauka,cikin muryan bacci Nameer yace"Assalamu alaikum"


"Wa Salam,Baba na ban hana baccin bayan la'asar in nan ba wa"??ta kare cikin muryan fada!!


Mikewa yayi zaune tare da goge idanun shi,sanann yace" kiyi hakuri Mama wallahi ban ma San yaushe baccin ya dauke Ni ba",


"Ina fatan kayi sallah dai ko,baccin yamman nan sam bashi da amfani Baba na,ko ka mance mafi akasarin cutukaka da yamma ake sauke su,and duk Wanda yayi baccin bayan la'asar in nan to da bakin ciki yake tashi,ina amfanin shi to"??,ta kare tana me cire hijab in ta,



"Hajiya Mama ayi hakuri ba zan sake ba in sha Allah,yau in ma kuskure aka samu"ya kare yana murmushi kamar yana ganin ta, "kayi Sallan??"shine tambayar da ta kuma yi masa,"eh mama Saida nayi Sallan sanann na kwanta,ban ma fa dade da kwanciyar ba kika kira,ina wuni,"



"Lafiya kalau,ya gajiyar aikin?? ubangiji yayi taimako,ya tsare sanann ya bada Sa'a",



Cike da jin dadin addu'oin mahaifiyar tashi ya amsa ta da "Ameen ya rabil alamin!, ina su Angel"?



"Haanan ta raka Zaliha kasuwa,Amman na san suna ma hanyar dawowa yanzu","toh ubangiji ya dawo da su lafiya",ya fadi tare da mikewa,



"Ameen ya Allah,Baba na daman na kira ka ne game da jikin yarinyar nan",


Da sauri yace "Mama wani abun ne ya samu Pookie in??"


"Pookie kuma wacece hakan"??Mama ta tambaya tana me taba jikin Nadeeya ta ji zafin ko ya ragu,


Murmushi yayi tare da shafa kanshi sannan yace"I mean to say ya jikin Nadeeyar,me ke damun ta ne?", "Wlhy ni abun yarinyar nan ya fara bani tsoro,baba na ita kadai sai tana firgita,at times numfashin ta kamar wanda ake shirin zare wa rai,yanzun ma hakan ne ya faru,na ida Salla na ga kamar tana shirin mutuwa,shine na mata tofi, na bata ta sha da kyar tare da bata habba da zuma,toh na samu numfashin nata ya dawo daidai saidai har yanzu jikin ta zafi kamar an manna mata garwashi,"ta kare cike da tausayin Nadeeyar!,


"Subhanallahi ko dai za ku je asibiti ne Mama a duba jikin nata da kyau"?    

          "Baba na Nima kaina nayi tunanin kai ta asibitin,saidai tsoro na ji kar a hadu da fuskan sani,in shigar da kai da kaina matsala",


'goshi Nameer ya dafe,shi Wlhy at times mancewa yake wai sato Nadeeyar yayi,da Mama bata yi wannan tunanin ba shi ai da asibiti zai ce su je,ashe da an samu matsala kuwa',


"Kayi shiru baba na babu wani alternative ne??domin har ga Allah jikin yarinyar nan yana bani tsoro,jiya kwana nai ban yi bacci ba,ina manna mata towel a jiki don yanda jikin ya dau zafi,da tofi da taimakon Allah na samu ta daina firgita da hauhawar numfashi bacci ya dauke,toh gashi yanzu ma jikin nata ya kuma tashi,and abun haushin ba halin Kaita asibiti" 

            "Ya isa mama kiyi hakuri ki kwantar da hankalin ki babu abinda zai same ta in sha Allah",Nameer yayi saurin katse ta domin ya san halin maman tashi in ta rude,"yanzu zan kira Mujaheed zai zo ya duba jikin nata, ubangiji ya bata lafiya da mu da sauran al'ummar musulmai baki daya",


"Ameen ya rabil alamin,ya kama ta kam ya zo ya ga jikin nata,bari na samu na canza mata kaya kafin ya zo din,and babana nasan shiririta irin ta Mujaheed don Allah kace da shi ya zo da sauri,and ka tabbatar ka rike azkars in ka kar kayi wasa da su,ka kuma kula da cin abinci,ka kuma cigaba da hakuri juriya da kuma tsoron Allah,da kwanta ta gaskia,sai ka ga komai ya zo maka a saukake, ubangiji ya maka Albarka ya kuma kare ka daga dukkan sharri",ta kare tana murmushi,


   Shi din ma murmushin yayi,wato a rayuwa samun uwa ta gari ba karamin dace bane,cike da soyayyar mahaifiyar tashi yace da ita"Ameen ya rabil alamin Mama ta i love You so much",Dan dariya ta sanya sannan tace" baka da dama wallahi,ni kam bari na je na hado ruwan wanka tunda Zaliha bata nan"da haka ta kashe wayar nata zuciyar ta cike da kewar dan nata,



Isowar doc Mujaheed ke nan gida yayi parking yana kokarin bude kofar motar ya ji wayan shi na ringing,be yi niyan daukan kiran ba,saidai ganin Nameer ke kira ne ya sanya shi dauka,tare da komawa ya zauna akan kujera,



  "Assalamu alaikum mutan Bauchi yau kuma mu aka tuna"?,dariya Nameer ya sanya sannan yace"Wlhy Mujaheed baka da dama,sai kace ba mu magana,in ce shekaran jiya nan har gurin dare muka raba muna chatting da kai",ya kare yana murmushi,


"Ah abun naka ne ai sai ina maka haka,kafin su Habeeb suyi replacing ina",dariya Nameer ya kuma sannan yace"Allah ya shirya mun kai wallahi,da fatan dai duk kuna lafiya ina babies ina?",


    "Wlhy duk muna lafiya,ka ga yanzu ma dawowa ta daga asibiti ina kokarin shiga gida ke nan ka kira",


"Ayya ubangiji ya bada Sa'a toh,'da Ameen Mujaheed in ya amsa, sannan duk suka dan yi shiru for sometime,kafin can Nameer ya yi breaking shirun da fadin"yauwa abokina taimake ni mana",


"Go on wani irin taimako zan yi maka,in na kudi ne ma ka sani bani da shi don ba a yi albashi ba", 

           Dariya Nameer ya sanya,kafin yace "hali zanan dutse Mujaheedu marowacin bazan,rike kudin ka ina da kudi plenty ma in fada maka,Ni mara lafiya gare Ni tana gidan mama za ka je ka ɗan duba mun ita",


"Ka ga laifi na ne things are hard and tight a kasar nan,tattalin dole gwamnati ta koya mana, beside waye babu lafiya,and me ke damun ta??


"Dadi na da kai tambaya,don Allah go and see her,in ya so I will explain komai to u in details in sha Allah zuwa dare",

          "Baka san yunwan da na dawo da shi bane Nameer Wlhy am damn hungry",


Katse shi Nameer yayi da fadin"don Allah Mujaheed ka je yanzu kar mama tayi fada,in ka je am sure bara Ka rasa abinci gurin mama ba,we will talk later okay pls make sure to take care of my Pookie,"be Jira amsan shi ba ya katse wayan,


Da kallon Mujaheed ya bi wayan,tare da maimaita kalmar"My Pookie!!mamaki fal ranshi,"to waye Pookie in?and a ina ya samo ta??ko labari be bani ba"shine abinda Doc Mujaheed ke tambayar kanshi,ganin be da me bashi amsa ne ya sanya shi kunna motar,tare da ɗaukan wayan shi,Matar shi ya kira ya sheda mata kan ya tafi gidan su Nameer Amman yanzu zai dawo,ta haɗa mishi abinci da ruwan wanka,



Dake ba wani nisa bane a tsakanin su,so tafiyar mintuna kadan ne ya iso da shi gidan Mama,


Da sallama ya shigo cikin gida,gidan ba bakon shi bane so direct parlor in Mama ya wuce,da Angel ya fara cin karo tana wasar yar baby a tsakar parlor,tana ganin shi kuwa ta rugo da gudu,tare da fadawa jikin shi tana dariya,


Shima dariyar yayi,tare da daga ta sama,wato tsananin shakuwar da ke tsakanin shi da Nameer har wasu ke fadin wai suna kama,kila kamanin Haanan ke ganin ya sanya take kaunar shi har haka,


"My baby"ya kira ta yana me shafa kanta,ba abinda take sai tsalle a jikin shi tana Dada,


"Mujaheed har ka iso?,mama ta fadi tare da karasa fitowa daga cikin dakin ta,


Durkusawa yayi tare da gaida ta,cike da sakun fuska,suka gaisa,sannan tace "afuwan my son Baba na ya dago ka ko"??,


Murmushi yayi sanann yace"haba Mama babu komai fa,ina Pookie in?ya jikin nata kuma"?,



Kai kawai Mama ta girgiza domin wannan Pookie Pookie!! In da Nameer ya lakaba wa Nadeeya ita ba sanin meaning nashi tayi ba,


"Mu je tana daki na",daga haka tayi mishi jagora har zuwa dakin nata,Saida ta ga ya fara bude kit in Shi sanann ta fice daga dakin don bashi space in duba ta,



Tsoro mamaki da al'ajabi ne suka cika Doc Mujaheed domin in har ba idanun shi ke yaudaran shi ba Nadeeya Audu Waziri yake kallo kwance a gadon maman Nameer,


Yaushe Nameer ya san ta?a ina ma ya ganta?yaushe ya kawo ta gidan su?,daman for all this while tana nan gidan su ake ta cikiyar ta,to miye dalilin shi na sato yar mutane?and miye ma ke damun ta?wannan shine tambayoyin dake ta yawo a kan Doc Mujaheed wanda ya sanya ko taba Nadeeyar ma be yi ba,Saida ya ji muryan mama tana fadin"ya ake ciki Mujaheed ko dai zamu kai ta asibiti ne"?ya sanya shi dawowa hayyacin shi,


'kila yar uwar su ce ban sani ba,shine amsaan da ya baiwa kan shi kafin yace da Mama "ina kan duba ta ke nan Mama",ya kare tare da mikewa ya shiga duba jikin Nadeeyar wanda Bara ka bata cewa  she is paralyzed ba,yanda Mama ke mugun bata kulawa babu wari ko wani hamami a tattare da ita,


Aluran zazzaɓi yayi mata sannan ya sanya mata drip kasancewar Bp in ta yayi low,be fito daga dakin ba saidai ya ga zafin jikin nata ya ragu sosai ,nan parlor ya tarar da mama warmers cike a gaban table,



"Sannu da aiki Mujaheed,hope jikin nata da sauki ko,me ke damun ta ne ma??shine tambayoyin da mama tayi wa Doc,


Nan kasa ya nemi guri ya zauna sannan yace"jikin da sauki mama don har ta samu bacci ma,jinin ta ne yayi low sosai hakan kuma baya da maraba da damuwar da take ciki,zafi n jikin kuma ina tunanin saukar jinin ne ya haifar mata fa zazzaɓi",ya kare yana wasa da yatsan hannun shi,har ga Allah so yake ya tambayi mama miye alakar su da Nadeeya amamn kunya bare Bari ba,



"Mujaheed anya saukar jinin ne kawai kuwa,ita kadai fa sai ka ga tana razana,numfashin ta na fita da kyar kamar wanda ake danne wa,duk haka saukar jinin ke causing??ta kare tana kafe shi da idanu,



Numfashi ya sauke sanann" yace gaskia Mama Nima abun ya bani mamaki don abinda kika lissafo low bp baya sanya su,gwara ma ƙaruwar bugawar zuciya,ko jin jiri,to a yanda na bincika kam bayan hakan babu wani damuwar da na gani",


"Ikon Allah wallahi Mujaheed da ka ganta dazu sai ka tsorata kai ma yi take kamar za a zare Mata rai,Amman tunda kace da sauki yanzu maza ka samu ka ci abinci Ka wuce kar a bar daughter na ita kadai tana ta jira,bari na shiga na duba ya jikin nata"da haka ta mike ta shige dakin don bashi guri ya ci abinci,babu musu kuwa ya nade hannun riga tare da fara cin abincin shi hankali kwance yana kara yaba irin dadin abincin mama,duk da ta manyan ta Amman in tayi maka abinci sai ka ji kamar ka tsinke yatsun ka,yana kallon Nameer na ta faman kiran shi Amman be dauka ba,ya fi so sai ya nutsu tukun na suyi magana ta fahimta domin ya lura akwai wani boyayyar abu tattare da yarinyar,



Saidai ya ci ya koshi ya sha zobo me sanyi cikin shi yayi nak,sannan yace da Mama zai wuce,turmin zani me kyau da tsada ta sanya mishi a leda tare da cewa ya kai wa Matar shi Jameelah,karba yayi tare da godiya,Albarka ta sanya mishi sannan tace da shi duk yanda jikin nata ya kasance za ta sanar mishi,


Ko da ya isa gida wanka yayi da ruwan dumi,abincin ma gagara ci yayi,Jameelah kuwa ba karamin dadin kyautar ta tayi ba, godiya tayi tare da fadin"ubangiji ya kara mata budi,Mama kam akwai budaddan hannu,


Shigowar kiran Nameer ne ya katse musu hiran da suke yi da matar tashi,


Bayan sun gaisa ne,Nameer ke tambayan shi ya jikin Nadeeyar?,



"Jiki da sauki na mata alurai tare da karin ruwa,na baro ta ma tana bacci,jinin ta ma ya sauka but da sauki jikin nata,saidai Ni kam ina da suggestion daman nace sai na nutsu da kaina zan kira ka", ya kare tare da mikewa yana nufan dakin shi,


"To Masha Allah tunda kace jikin da sauki and ba wani abun daga hankali bane,so miye suggestion in naka"?,



Dan dariya doc Mujaheed yayi sannan yace" You are very  funny aboki na wato You went straight to the point to avoid tambayar da zan yi maka rihht"??,


Kankan da idanu Nameer yayi kamar wanda yake gaban shi kafin yace "wani tambaya ke nan iyayen surutu?,


Dariya ya kuma sannan yace"ko yaushe aka hadu da yar gidan Sen har ta sace wa mutum zuciya,har ya gaza hakuri,ko tsoro yake bara a bashi ita ba,ya sanya ya sato ta sai Allah?,


"Wlhy Nameer ke bani mamaki,for all this while Ashe yarinyar nan tana gurin ka ko a labari ban ji ba,Banda yau ya zama dole da kila sai taron daurin auran Nameer da Pookie in Shi zani, tunda kai a rayuwa Ni ne baka yarda da ba",ya kare Yana hararan shi ta waya,



Goshi Doc Nameer ya dafe,sanann yace"Mujaheed duk abun da ka fadi ba haka bane, abun na mu ne very twisted wallahi Amman bari na baka labari ko za ka daina fadin ban yarda da kai din nan ba, daga haka kuwa ya kwashe labarin tun farkon haduwar su da Nadeeyar har inda ya kawo ta Kaduna be boye masa komai ba,


Banda salati da al'ajabi babu abinda Mujaheed ke yi, "yanzu a duniyar nan daman akwai mugaye irin su Bashir da Afzaal?tana matar shi yace a kashe ta harda biyan kudade,to me yasa ba ka kai ta gida gurin mahaifin ta ba?ka sanar da shi abinda ke faruwa ai ka daga musu hankali sosai wallahi",ya kare yana jinjina rashin mutunci irin na su Afzaal,


"Mujaheed wallahi Nima nayi tunanin kai ta gidan su at the first place,Amman zuciya ta ce tayi wani tunanin,Ni Wlhy haka kawai na ji ba zan kuma iya yarda da kowa akan Pookie ba,yarinyar nan daga ganin she has been through a lot,and tun farkon kawo ta asibitin mu nake zargin Sen,haukan da suke ikirari tana da shi sai fa in ta ga Sen ko wancan wawan yaron yake tashi,and nan na sanar maka da farko ashe kalau inta alurai Bashir ya ringa dura mata,kana tunanin Bashir yana da wanann mind in da zai haukatar da 'ya daya tilo a gurin Sen??,ai dole sai in yana da masaniya,don da tun farko neman lafiyar ta ce a gaban shi,da kasar waje zai fidda ta,gurin kwararrun likitoci su duba ta",ya kare yana me jan guntun tsaki,


     "Maganar ka kuma tana kan hanya,ace duk kudin Sen yar sa ke kwance asibitin mahaukatan Bauchi da ayar tambaya kam,manyan mutanan nan abubuwan su sai Allah,ta kare tare da sauke numfashi kafin ya ce,"amman aboki na this Pookie of yours ta ci sunan ta wallahi because she is damn cute and beautiful"ya kare yana dariyar shakiyanci,


  "Zan ci maka mutunci wallahi,baka da hankali ko,daga zuwa duba matar mutane kake kare mata kallo haka?"


Idanu Mujaheed ya zaro,kafin yace" Matar mutane!!,matar wacece"?,


Tsaki Nameer ya ja sanann yace"ban sani ba bani son iskanci,matar mijin ta mana,ko ance maka ta san ya sake ta ne?ko gobe ta tashi dauka za tai da auran ta",


Dariya Mujaheed ya sanya sanann yace"Alhamdulilah our little angel ta kusa samun new mommah!!ya kare out of excitement",


"Mujaheed wallahi zan zage tun daga first generation in ka har zuwa karshe,shike nan on  a normal basis bazan ji tausayin ta ba, can't U see tana bukatar taimako na"

??

          "Hmm na you say so,ni ban  zan ce komai ba",


     "Ya fi kam kar ka ce ina,baran samu nayi shirin zuwa sallah an kusa kira,make sure to take care of her please,we will talk tomorrow in kuma na samu chance za ka ji Ni anjima",Nameer ya kare yana me mikewa daga zaune da yake,"baka da damuwa daddyn Angel Zan kula da Pookie har ma fiye da yanda za ka yi,ya kare yana dariya,gobe zan je in ga jikin nata Duk yanda ake ciki dai we will stay in touch,take care and my regard to Habeeb,da haka suka yi sallama,Nameer toilet ya shige tare da dauro alola, zuciyar shi cike da tunanin jikin Nadeeyar.



*************Sen Rilwanu


   "Sen wai Bara ka kwantar da hankali ka ba da Allah,wai wani irin abu ne haka duk ka bi ka hana kan ka nutsuwa da kwanciyar hankali"Alh Kabiru ya kare yana ji kamar ya rufe Sen da duka,


Zama Sen ya gyara tare da tabe baki sannan yace "Kabiru  ke nan,gani kake kamar wai kwanciyar hankali na ne bana so,ko daya Wlhy tsoro na tunuwar asiri na, Kabiru sanin kan ka ne Nadeeya ta rika ta san sirri na wanda duk duniya daga kai sai Ni sai Allah muka sani,a taya kake tunanin hankali na zai kwanta,yarinya ace an neme ta an Rasa,in kuma ta dawo hankalin ta ta fada wa wani waye Ni fa??shike nan zan rasa komai fa zan koma gidan jiya,mulkin da nake takama da shi,shima rasa shi zan yi,ka ga kuwa dole hankali na ya tashi i have gone so far I can't stand losing komai da komai in a blink of eyes",


Tsaki Kabiru ya ja "kai Wlhy Rilwanu kana da damuwa,haba ko uban waye yace da kai za ka rasa komai ne,kai Odogwu fa matattace ne kawai be tayar ba amamn babu abinda a fadin duniyar nan zai gagare shi,na ga alaman ka mance baya ne,ka mance yanda kake a baya,da abubuwan da Odogwu ya baka,kar ka zama butulu mana",



Idanu Sen ya zaro tare da nuna kan shi"Ni in zama butulu Kabiru kana maganar abubuwan da Odogwu ya bani,ka fada mun abu guda daya da ya bani shi for free??,just tell me me ya taba mun for free without asking of something in return??,don haka stop saying all this kana nuna kamar favour yayi mun after all Abu ne na bashi sannan ya bani nima,is just like business Ka ga kuwa dole ina da bakin magana "Sen ya kare cikin daga murya,


Ganin yanda ran Sen ya ɓaci ne ya sanya Kabiru sakin murmushi sannan yace "common haba ranka ya dade gwamnan mu me jiran gado anger nan duk ba naka bane,ba dai Odogwu yace a bada blood ba am sure ana yi zai gano inda take,just chill and relax Nadeeya bara ta taɓa tona maka asiri ba,i can assume you of that",


Numfashi Sen ya sauke sannan ya ce "ana wata ga wata ko a gidan uwar wa zan samo me tsohon ciki oho",be Kai ga karasa maganar tashi ba sai ga shigowar Afzaal cikin parlor in,



  "Banda abun Sen duk ka bi ka daga hankalin ka a karan banza,duk inda Nadeeya take am sure da ta dawo hayyacin ta za ta dawo gidan nan,ko ba dan kai ba,za ta dawo don Afzaal domin miji yake a gare ta,ko da Bara ta iya cigaba da zama da shi ba,ka dai san mace bata sakan kan ta,dole sai in shi zai sake ta,and that will be the time da za muyi using mu rike ta",Alh Kabiru ya kare yana me mikewa don dare yayi sosai,


"Daddy ni fa Nadeeya is not my wife anymore",Afzaal ya kare yana zumburo baki,


A tare Sen da Alh Kabiru suka ce"What"kamar ya she is not your wife anymore,


"Sorry daddy na mance ban sanar maka ba,tunani nayi na duba na ga zama na da ita babu wani amfani, beside ita kanta ba sanin kanta tayi ba balle Ni,balle ta tuna tana da wani aure na,ya sanya nayi setting inta free,daman ta dade tana neman hakan,Nima kuma daman na gaji ka ga shike nan ai ko",



Wani irin gigitattcen Mari Sen ya dauke shi da shi wanda saidai ya sanya shi kaiwa kasa,


   "Kabiru kana jin wannan matsiyaci dan iskan yaron abinda yake fadi ke nan,Ni kam na shiga uku na",


   Tsungunawa yayi tare da cukumo wuyan rigar Afzaal in ya shiga dibe shi da maruka,"kai dan uban ka da uban wa kuka yi shawara kafin ka sake mun 'ya,har wuyan ka yayi kwarin da zaka saki mun yarinya ta ba tare da na sani ba,shege dan iska,saki nawa kayi mata mara mutunci ya kare yana kara dauke shi da wani marin,riko shi Alh Kabiru yayi yana fadin"bari haka Sen kar ka ji mishi ciwo mu bi komai a sannnu",


Fincikewa Sen yayi tare da mike wa"a sannu!!a sannu fa kace Kabiru last hope in da Ka gama sanar mun fa wannan dan iska wawan yaron me zubin yan daudu ya rusa fa,wai ka san fa fada mun yake ya saki Nadeeya ta,ka fada mun yanzu a yaya zan gan ta,a yaushe za ta dawo bayan duk abinda na aikata mata??Sen ya kare murya a raunane kamar me shirin yin kuka,


Dafa shi Alh Kabiru yayi sannan yace "kayi hakuri Sen ka kwantar da hankalin ka",


Centre table in parlor in Sen ya daga da hannun shi wanda a take ya fashe sabida glass ne,nan take kuwa ya yanke mishi hannu sai jini,cikin ihu yace "Kabiru!! Kabiru!!Kabiru!! Wai wani hankali ne kake ce mun na kwantar,na rantse da Allah in yaron nan be fada mun saki nawa yayi wa princess ba sai na ci uwar Shi",ya kare yana nufo inda Afzaal ke tsaye kanshi a kasa,


Tsakanin su Kabiru ya shiga sannan yace"kai Afzaal saki nawa ne wai kayi mata,and ai na ga bata san da sakin ba so Ni ban ga wani abun tashin hankali a nan ba",


Cikin sanyin murya Afzaal in yace "big Daddy saki uku nayi mata kuma rubuta wa nai,na aje mata kila wanda suka sace ta sun tafi da shi ko ya fadi ban sani ba",


Tassss Sen ya dauke shi da mari,"shege matsiya ci da bakin ka kamar saki uku nayi mata,tunda ka sake ta ai sai ka ci uwar da kake son ci,na rantse da girman me sama Kabiru in Baka fice mun da wannan dan iskan ba sai na tabbatar da na kashe shi da hannaye na,kuma na kashe banza,shege me son abun duniyar tsiya ya kare yana kuma kwashe shi da wani marin,


Ganin in ya tsaya Sen zai iya kashe Afzaal ne ya sanya Alh Kabiru jan shi har sun kai bakin kofa ya tsaya yace"bari na kai shi daki na dawo,don Allah ka bi komai a sannu",


"Ku je kawai Kabiru bana bukatar ganin kowa,i want to be alone don Allah ku kyalle Ni ya kare tare da bugo kofar parlor in tare da murza key,


Dakin shi ya nufa inda yake jin zuciyar shi kamar za ta fado, fridge ya bude da kyar tare da dauko sabon kwalbar Whisky,bude ta yayi ba tare da ya tsaya neman cup ba ya dage ta tare da kafa baki,ya shiga kwankwada kamar wanda yake shan ruwa ba giya ba,ba shi ya aje kwalban ba saidai ya ya sanye tas,


Hurgi yayi da kwalban ya bugi tiles in dakin a take kuwa ya tarwatse,kan shi ne ya ji ya fara juya mishi ya fara nauyi idanun shi a take suka kada suka yi jawur,a take ya ji ya fara daukan charge,


Tafiya yake yana hade hanya domin baya gani sosai,cikin kwalban ya bi a haka suka soke mishi kafafu ba tare da damuwa  da zafi ko jinin da kafafun shi ke yi ba ya isa gaban katon madubin dakin shi,


A hankali ya bude idanun shi da suka zama ja kuma suka kankance tsaban buguwa,ya zuba akan mirror in,kallon kan shi yake yana me mamakin a taya rayuwa ta zamo mishi haka,duniya tana kokarin juya masa baya,yau in asirin shi ya tonu ya kalli Hajiya abokai da sauran al'ummar gari da wani idanun,idanun shi ya rintse da karfi,tare da koma wa ya fadi akan gado,goshi ya dafe tare da lumshe idanun shi nan ya shiga tunano rayuwar shi na baya.....


*ALHAMDULILLAH* ❤️

_An yi sallah lafiya an gama lafiya, ALLAH subhanahu wata'ala ya karbi ibadun mu ya yafe mana kurakuran mu baƙi._

 _wanda suka je aikin Hajji🕋 _ALLAH Ubangiji ya karba musu ibadun da suka gabatar baki daya._


_Muna roƙon  ALLAH yasa muna da rabon zuwa aikin hajji Shekara mai zuwa, ALLAH ya maimaita mana_ 🥰



    Ina me Baku hakurin ji na shiru da kuka yi, hakan ya faru ne bisa ga dan rashin lafiyar da ke damu na,Amman Alhamdulilah am perfectly fine now🥰



   Iya yawan comments iya yawan typing✍🏻



   Ina wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)

 

   

        💖 

                THE TALENT TROUPE WRITERS💖💖

........


NA DAINA AJE GROUP LINK INA DOMIN ANA SAMUN MAZA MARA SA TSORON ALLAH NA JOINING SUNA BIN MATAN AURE DA BADALA,DUK ME BUKATAR SHIGA GROUP INA SHOULD TALK TO ME IN TABBATAR MACE CE SAI NAYI ADDING IN MUTUM DA KAI NA,BUT PLS IN HAR KIN SAN BA KARANTA BOOK INA ZAI KAWO KI BA TOH KI YI ZAMAN KI BA SAI KIN YI JOINING BA,


Wannan page in sadaukar wa ce a gare ki Anty Sadiya(Mrs BBK),Love you so much🥺💖


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


...........

          Page thirty _seven


**********


        Azare


    ******** 

              Unguwar Matsango



      'Unguwar Matsango,yana daya daga cikin makaskancin unguwanni a garin Azare, aka sarin mazauna unguwar masu fama da babun rayuwa ne,unguwa ce ta talakawa masu fama da babu,in one word dai in kana neman Ghetto area to Ka samu Matsango to kan kat ke nan,


Mal Audu Waziri dan Asali kuma haifaffen yankin Katagum ne,mutum ne me zafin nema da kuma taka tsantsan da rayuwar shi,samun ne kuma sai a hankali,domin talaka ne shi,don har kwatance ake da talaucin shi,


Noma yake yi wanda kuma gadon shi yayi gurin mahaifin shi,bayan rasuwar shi ya samu gadon gona, sha'ani na rayuwar yau da kullum ya sanya shi saidai gonar tashi,duk da kasancewar shi talaka me fama da rayuwa,hakan be sanya zuciyar shi ta mutu ya koma maula da roko ba,ace war Shi"duk wani me zafin nema to kuwa yana tattare da samu",


Nan cikin Matsango yake zaune shi da matan shi biyu da yara shida (6)


Matar shi ta farko Rakeeba wanda ta kasance Babar diya a gurin Sheik Ali Abbas babban malamin addinin ne da ke zaune nan garin Azaren,sabida ilimin shi da yada da'awar shi ya sanya ba iya garin Azaren da Bauchi ba har sauran makotan garuruka an San Sheik Ali Abbas,


Rakeeba ce babbar diyar shi wanda bata baro komai na shi ba,kama daga kan kamanin,tarbiyya nutsuwa da kuma ilimin addinin domin tana da shekaru 8 a duniya tayi saukan Alqur'ani me girma,yarinya ce me kawaici da kau da kai,da kuma hakuri,


Mal Audu ya kasance yana zuwa gurin Sheik Ali Abbas daukan karatu,nan ko Sheikh ya yaba da hankali nutsuwa da kuma nagartar shi,hakan ne ya sanya shi yi mishi tayin Rakeeba kan yana son hada su aure,ko da ya ji ba karamin dadi ya ji ba domin babu wanda zai samu mace kamar Rakeeba yace bayi so,


Ko da maganar ya ishi Rakeebar bata nuna rashin amincewar ta ba,ba a dauki lokaci ba kuwa aka daura aure,zaman auran nan su kuwa zama ne me cike da ban sha'awa da mutunta juna,domin Rakeeba matar rufin asiri ce,Allah ya albarkace su da samun yara biyu,dan su na farko Rilwanu wanda suke kira da Abul bait sai me bi mishi Usman,bayan haihuwar Usman in ne Mal Audu ya karo wa Rakeeba abokiyar zama me suna Zuwaira wacce suke kira da Gwoggo,



Zaman Gwoggo da Rakeeba sai son barka, domin zama suke na tsakani da Allah babu cuta ko kyashi ko mugunta a zaman na su,babu komai face zallan girmama juna da ganin mutuncin juna,


Rakeeba na da yara hudu,Rilwanu,Usman,Ali,sai autar ta mace me suna Ummi Salma,wacce suke kira da ummi,while Gwoggo yara biyu gare ta wanda yan biyu ne,duk mata,Nana Khadijah da Nana A'ishah,


Ba karamin kauna da shakuwa me karfi bane a tsakanin Rilwanu da Gwoggo domin,yanda ta ja shi jiki take kaunar shi,Rakeeba ba haka bane gurin ta ko tana yi mishi kawaici da ƙarar dan fari ne sai Allah,in har ba sani kayi ba ka zo gidan to dauka za kayi Gwoggo ce mahaifiyar Rilwanu saidai in Ka dubi tsantsan kamannin shi da Rakeebar ce wace suke kira da Hajiya za ka fahimci tabbas dan ta 

ne,


Rakeeba tayi iya kokarin ta na ganin yaranta sun samu tarbiyyar da ya dace,duk da kasancewar su ba masu hali ba amman tsaye Mal Audu yake da ita kanta,gurin ganin sun samu ingantacciyar tarbiyya da kuma ilimi,


A haka suka samu har suka shiga Secondary school nan cikin garin Azaren a wani government school,dake ba wani tazara ke tsakanin Rilwanu da Usman ba ya sanya suka kasance a aji daya,


Ko da suka kammala jarabawar fita daga Secondary nan Usmanu ya ce shi kam ya tsaya wa karatu,babu yanda Hajiya(Rakeeba)bata yi ba,akan ya cigaba da karatu,Amman Yace "a'a shi kam zai fada kasuwanci in Allah ya dafa sai ki ga na koma ciyar da ku da kanne na,tunda shekarun Baba ja suke,karfin shi na tafiya dole yana neman me taimakon shi,in Allah yayi da rabo ma koma bokon gaba,Amman for now Kam mun bar wa su Yaya Abul bait,shi ko Rilwanu cewa yayi ina duk inda kuɗi suka shiga suka fita,to tabbas Mal Audu ya nemo su domin shi kam sai yayi boko,sai ya ga karshen biro,domin a jikin shi yana jin sai ya zamo babban mutum ba ma iya Azaren ba har duniya sai an San da shi,don fadi yake zaman shi gidan Mal Audu ƙaddara da mistake ne domin sam be dace da kalan gidan ba,


Duk sanda Rakeeba ta ji yana irin wanann furucin abun yakan mata ciwo,domin a matsayin shi na babban yaron ta gani take shine zai zamo uba gurin kannan shi,saidai sam halin Rilwanu sai shi,domin wani irin yaro ne shi me tsinannan son abun duniya sam be dauko halin uwa ko na uban shi ba,akwai shi da kwadayi da kuma buri,uwa uba kuwa akwai shi da wasa da addini,sannan yana da kaushin hali sam halin Rilwanu sai Allah,at times yakan fadi magana ba tare da tunanin Mala'iku sukan taya mutum amsawa da Àmeen in yayi Addu'a ko ya fadi wani kalman,(ya sanya ya dace muna 

tsaftace halcen mu gurin magana ko addu'a domin ba mu san a yaushe bane  Mala'iku za su taya mu da Àmeen, ubangiji ya sa mu dace), 


Duk sanda ta nuna fushin ta kan maganar shi,Gwoggo ta kan ce da ita"haba Yaya kar ki dauki maganar Abul bait da mahimmanci baki ganin har yanzu yaro yake in ya kara girma da hankali,wlhy ko kudi aka bashi yayi wani abun bare yi ba,kiyi mishi uzuri harda yarinta a jikin shi",Rakeeba dai bata cewa komai domin har ga Allah tana mamakin kauna da shakuwar da ke tsakanin Gwoggo da Rilwanu,


Cikin taimakon Allah suka rubuta jarabawa result in Rilwanu kuwa tayi kyau domin a Jamb in Shi 200+ya ci,domin Allah ya bashi kaifin basira yana da ilimi kam,nan ko ya daga wa mahaifin shi hankali,akan nemo mishi admission a ATBU university na nan garin Bauchi,


Ba karamin tashin hankali Mal Audu ya shiga ba domin bayi da wannan kudadan sanya shi a makaranta a wannan lokacin,ganin inda Rilwanun ya matsa ne ya sanya shi shiga nema saidai duk a banza,


A nan haka Allah ma ji rokon bawan shi wani abokin shi yayi mishi hanya a gwamnati aka samu Scholarship aka cike sunan Rilwanun nan ko ya samu gurbin karatu a jami'ar ATBU,


Ba karamin dadi da murna yayi da jin labarin ba kuwa,nan ya shiga cewa "Gwoggo,tayi ta murna lokacin hutawan ta ya zo,domin yana gama karatun nan Siyasa zai fada domin Political science zai karanta da yardar Allah sai ya buga siyasa sai ya siya mata mota da gida",


Murna fal cikin ta tace"ubangiji ya dafa maka Abul bait ina ,Allah ya ida nufi,yayi taimako ya tsare,


"Àmeen ya rabil alamin Gwoggo ta,ai daman na sha fada Miki Ni dai zama na gidan mal Audu ƙaddara ce amman sam ban dace da rayuwar nan ba,ya kike hango Ni a office ina,mutane kamar 15 suna take mun baya,ana ranka ya dade sai kayi,in ina tafe ana bina a mota,duk inda na shiga a ce ga nan Alh his excellency Rilwanu Audu Waziri,sai ya sheke da dariya yace,za mu yi kudi na ban mamaki ma Gwoggo ke dai with time,kin Kusa cewa bye wa bakin talaucin nan,za ki daina cin bakin tuwo da bakin ruwa,


Rakeeba na jin hirar tasu saidai ta kasa cewa komai,domin har ga Allah wasu abubuwan in Rilwanun yayi to ya daina bata mamaki sai tsoro,tana mamaki a kananun shekarun sa  yanda yake da mugun son abun duniya,



A haka dai aka fara masa shirye shirye,dan abun da duk suka hada suka fidda don yi wa Rilwanun siyayya,dake Usman ya fara kasuwanci cikin Sa'a sai gashi Allah ya sa mishi albarka baya taɓa rasawa ba, don haka gurin shi aka samu rabin kudin da aka yi wa Rilwanun siyayya aka samu aka hada dan abubuwan da dan makaranta zai bukata na yaran mara sa shi,


Ba karamin bakin ciki Rilwanun ya ji ba,ganin wai a gurin Kanin shi aka samu kudin tura shi makaranta,abun yayi mishi zafi saidai ya daure(saboda bakin hassada),ba karamin Nasiha Rakeebar da Gwoggo suka yi mishi ba ana gobe zai tafi, kan ya ji tsoron Allah,ya kuma rike mutuncin kanshi,ya kuma tsare mutunci da addinin shi,ya kula da ibada ya kuma maida hankali kan abinda ya kai shi,nan ko ya nutsu kamar ya dauka abinda ake fada masan,


Ko washe gari da wuri ya shirya,Rakeeba da Gwoggo yan kudaden su suka tattare duk suka bashi kan wai kar dai ya ga na wani ya tsole masa ido,tunda sun san halin shi,ya ji dadi sosai,da addu'ar Alkhair da albarka suka raka shi,da kan shi Mal Audu ya raka shi makaranta,be dawo Azaren ba saida ya ga Rilwanun ya gama komai har Saida ya shige hostel in su sannan ya juyo zuciyar shi cike da yi wa yaron na shi fatan Alkhairi da dacewa,domin duk cikin yaran nashi Allah ya daura mishi kaunar Abul bait,


Nan ko ya maida hankali ya fara karatu domin babu wanda ya sani balle ya bi su,rayuwar makaranta kowa ji yake yi da kanshi, domin at time sai ka kai ko kai dan wani ne kake zuwa makarantar Abubakar Tafawa Ballewa University (ATBU),


Haduwar Shi da Kabiru da ba zai taba manatawa ba kuwa shine,wani rana bayan an tashi daga classes yana jin yunwa kayan abincin shi sun doshi karewa,so ya nufi shop in makaranta wai ko zai samu dan abun siye,me sauƙin kudi tunda at that time kudi suna da daraja ba kamar yanzu ba,


Ya je a nan ya hadu da Kabiru ya ji gayu cikin kananun kaya,tun daga nesa ya ji ya burge shi domin yanda ya dau wanka babu raini,anan ya ke ji ina ma shi ne ya samu irin kaya da takalmin jikin Kabirun,


Ko da ya isa nan ya dauki dan abunda ya san zai iya affording ya zo gurin me shagon don biyan kudi suka ci karo da Kabiru har ya sanya abun hannun shi zubewa,


Durkusawa Kabiru yayi da sauri tare da mika mishi,sanann ya kara da bashi hakuri, murmushi yayi sanann ya karba yace babu komai kaima kayi hakuri,nan suka nufi gurin me shagon ya fada musu kudin su,a take Kabiru ya Ciro ya biya musu,suka fito daga shagon,


"Lah ai da Baka wahala kanka gurin biya mun ba,ina da kudi a jiki na dai, Rilwanun ya kare yana murmushi,"haba wa babu komai ai yanzu kam mun zama abokai suna na Kabiru Ishaq daga garin Azare,ina karanta public administration Kai fa"??,



"Lah Ashe garin mu daya kuwa ban Sanka ba,ai Yan azare basa buya ya sanya tun daga nesa na ji ka burge Ni kuma kana da kirki ashe dan uwa ne,Nima Azaren nake,suna na Rilwanu Audu Waziri ina karantar Political science,


Nan ko suka zauna labarin garin su,kafin ka Ankara sun shaku, domin Rilwanu gani yayi Kabiru yana da dan kudi,don a yanda ya fada mishi unguwar su sun fi su hali nesa ba kusa ba,ya sanya ya make mishi da sunan abota inda ya rinƙa tatsan shi da kadan da kadan,


Kafin kace me idanun Rilwanu sun kuma budewa domin za Ni ne ta tatda mu je,don ba karya Kabiru ma akwai shi da tsantsan son abun duniya da kuma dogon buri duk da kasancewar shi kan ma iyayen nashi suna da rufin asiri,


Kafin kace me sun zama kamar yan biyu duk inda ka ga daya zaka ga daya,don daki daya ma suka koma,lecture ne kawai yake raba su,a haka har suka samu suka kammala degree in su da dadi da ba dadi,Allah ya taimake su kuwa Rilwanu ya fito da result me kyau don har ta fi ta Kabiru kyau,don ya fi Kabirun ilimi,


Ko da aka tashi posting in su zuwa bautan kasa gari daya aka tura su kamar hadin baki,ba karamin dadi kuwa suka ji ba,don sun yi shakuwa ta ban mamaki,nan ko suka je suka gama bautan kasar na su suka dauko hanyar dawowa gida ko wannan su da dogon burin samun aikin gwamnati me gwabi wanda za suyi kudi na tashin hankali,


Ba karamin dadin dawowan shi su Gwoggo suka ji ba,barin yanda suka ga ya kara murjewa yayi fresh Masha Allah,a nashi bangaran yayi mamaki sosai ganin yan canje canje da gyare gyare da ya tarar a gidan,inda yake samun labari ashe duk Usman ne yayi su,domin Allah ya sanya wa kasuwancin nashi albarka har ya bude shagon kanshi,yayi aure yanzu haka ma matar tashi tana da juna biyu,



Bakin cike da hassada be tashi kashe shi ba,Saida aka kwana biyu shiru,dauka yake samun aiki wasa ce kana gama karatu kake samun abun yi,shida Kabiru sun kada sun rawa Amman shiru kake ji,dan kudin da ake basu na bautar kasan nasu duk sun cinye ta,a Siyan kwalama da banza da wofi,


 A haka rayuwa ta cigaba da tafiya,har shekara ta wuce Rilwanu bayi da aiki sai zaman daka,Hajiya tayi tayi da shi akan why not Yana bin Dan uwan shi Usmanu kasuwa,ai ko banza zai samu taro sisi,tunda aikin gwamnatin da ya kwallafa wa rai har yanzu ta kasa samuwa,anan ya buga kasa ya dire,yace Allah ya sauwaka ya bi Usman kasuwa,haba ajin shi da ilimin shi ya wuce nan,su dai su jira su gani zai samu aiki yayi kudi na ban mamaki,


Tsaban bacin rai Hajiya bata ce da shi komai ba,tunda ta mishi kallo daya ta watsar bata kuma bi ta kanshi ba,babu yanda Gwoggo bata yi da shi kan ya bi Usman in ba amamn sam yace ba haka ba,


Haka rayuwa ta cigaba da tafiya shekaru 3 suka  zo suka wuce,Rilwanu yana nan daɓe a gida,babu tsuntsu babu tarko, don Banda zaman daki,sai kuma fita yawon gwaram domin shi gani yake ya fi karfi yayi aikin hannu don samun kudi, ranshi ba karamin sosuwa yayi ba da ya je gidan su Kabiru aka ce da shi baya nan ba kusan shekara biyu da rabi ke nan   da barin gida saidai ya leko ya koma,don yanzu ma ba a Azaren ya fiye zama ba,ya samu aiki a Bauchi,ba karamin ciwo da zafi abun yayi mishi ba,ace duk yanda suke da Kabiru haka zai yi mishi,a bangaran Usman kuwa budi yana ta shigo mishi Masha Allah don yanzu haka ya dauke nauyin karatun kannan shi suna wuyan shi,haka ma cefanan gida,



Sati biyu da faruwar haka aka tashi da mutuwar Abban Kabiru babu jinya bare rashin lafiya,ance dai yai complain in ciwon ciki da wuni daya aka wayi gari babu shi,ba karamin dadi Rilwanu ya ji da aka yi mutuwar ba ya san ko banza zai samu ya ga Kabiru,saidai ko rashin dace ne har aka gama zaman makokin basu hadu ba,



Rayuwa tayi wa Rilwanu juyin ban mamaki,yayi baki ya kare,sabida dogon burin da ya kwallafa wa kan shi,ya kasa achieving komai a rayuwar shi,Hajiya da Gwoggo sun yi fada har sun gaji,shi be dafi komai ba balle ayi mishi maganar aure sai uban dogon burin masifa,


Barin gidan yayi da yammacin Allah domin ya gaji da jin irin maganganun da Hajiya ke yaba shi,


Tafiya yake yi,yana kare wa manyan gidajen masu kuɗi kallo a ranshi yana jin dama shine ke cikin wannan Niimar to me kuma zai nema nan gidan duniya,haka zalika in ya ga motoci ji yake kamar ya kwace su zama nashi,


Shopping mall in da ya Saba zuwa roko with style ya nufa,babu yanda ba suyi ba kan ya zo su bashi aikin kwasan kayan mutane yana kai musu mota ana biyan shi ba,Amman Yace ina sun am raina mishi wayo,ya gwammaci ya zo in ya ga me kudi ya kashe shi da kirari in zai tafi ya ɗan yaga mishi wani abu,anan at times yake samun dan taro sisi,


Yana shiga harabar mall in kuwa ya ga wata dankareriyar bakar mota,nan take kuwa ya washe baki ganin yau kam bajau in shi yayi dace,zai hadu da babban Alh,


Nan ko ya shiga cikin mall in da duk wulakancin duniya an gwada mishi kan ya bar zuwa Amman sabida tsinannan son abun duniya ya sanya ya kasa dainawa,


A tsaye ya hango shi gurin biyan kudi yana waya yaci wata danyar shadda kalar kore uban uban su domin kallo daya zaka mata,kasan me tsadar ce,agogon hannun shi me kyalli Rilwanu yake ta bi da kallo,sannan ya sauke idanun shi kan takalman kafan shi,ji yake kamar ya je ya kwace komai na wanann mutumin,ya gudu da su,nan take ya ji wata bakin ciki ko ince hassada ta rufe shi bayan ya gama kallon mutumin ya kuma kalli kanshi,ya ga sam babu hadi,



Cikin mutuwar jiki ya karasa gurin da mutumin ke tsaye,daidai lokacin kuwa ya kammala wayar da yake yi,


Cike da ladabin kare Rilwanu yace"sannu ranka ya dade!!,juyowa mutumin yayi tare da zubawa Rilwanu idanu for some mints kafin ya zare Black shade in dake idanun shi,cikin excitement yace Rilwanu!!Rilwanu!!daman kana nan,ikon me sama,


Sai lokacin shima Rilwanun ya bude idanun tas wa ko zai gani Aminin shi ne Kabiru Ishaq,bakin shi har na bari gurin fadin K..A..B...I..R...U, what!!kai ne ka dawo haka??,



Murmushi Alh Kabiru yayi tare da dan dakan kafadun Rilwanun sannan yace nine mana,Aboki na ya kake ya kare tare da janyo Rilwanun ya rungumai a jikin shi,


Saidai Rilwanu kasa ma amsa shi yayi,domin mamaki ya gama kashe shi,wai anya idanun shi ba yaudaran shi suke yi ba kuwa a taya Kabiru yake sanye da irin wanann tufafin da irin wanann waya,agogo da takalmi haka,magana ce fal ranshi,ganin hakan ne da kuma sanin hali,ya sanya Alh Kabiru saurin biyan kudin aka kai mishi kayan mota,"mu je ko" shine abinda yace da Rlwanu nan ko ya bishi kamar ragumi,mamaki be karasa kashe shi ba Saida suka nufo motar Kabirun,baki bude tsaban ya kasa hakuri yace "na shiga uku Kabiru don't tell me you own this car what!!?,


Dariya Alh Kabiru yayi sannan yace"common mutumina wannan shine karami kuma mafi tsada a cikin motoci na,mu shiga ciki in kuna maka Ac ka sha raɓa inda na ga ka Ibo uban ranar nan",


Nan ya bude motar suka shige ciki suka zauna,Ac Kabiru ya kunna,banda kanshi da sanyin dadi ba abun da motar ke yi,


Idanu Rilwanu ya lumshe har yanzu shi ya kasa yarda wanann arzikin na Kabiru ne to a garin yaya,kabirun dai da ya sani ko bayan gama sch in su be samu aiki ba,to a yaushe ya samu aiki har yayi kudi haka?,shine tambayoyin da yake wa kanshi,


"Aboki na kayi hakuri nayi maka laifi ko,wallahi abubuwan ne sai a hankali ba wai da gangan nayi cutting in Ka off ba",ya kare yana me tada motar,


"Hmm ai Wlhy Kabiru ka bani mamaki ka kuma ci mutuncin aminta,yanzu ace kana cikin wannan daulan,Ni bani da komai ribar me za ka samu??,Kabiru haka kawai ka yi cutting ina off babu waya babu sako,babu rana ta Allah da ba zan je gidan ku duba ka ba,Amman kullum amsan daya ne baka nan,ashe wasu shegun kudi kayi,yau din ma robo ne ya rantse ya sanya na gan ka",ya kare yana me jin haushin Kabirun,


"Yanzu dai kayi hakuri bari mu samu mu zauna sai nayi maka bayani a hankali,yanzu dai mu je ka samu ka ci abinci,kayi wanka ka canja wannan tsunman jikin naka,sai muyi tadin yaushe gamo ko"??, Rilwanu be iya cewa komai ba don takaici,


A wani katon hotel ya ga sun yada zango,mamaki fal ranshi har ya kasa hakuri yace "Kabiru do U think kana da kudin da za ka iya affording in hotel in nan"?,


Dariya Kabirun ya sanya,sannan yace "ai kusan 5 days da zuwa na a nan na sauka,domin Allah ya gani,bazan iya zaman gidan mu ba,yanzu haka ma in na koma,ina shirin turowa ne a rushe ginin ayi musu sabon gini na zamani,don haka a nan nake zama,mu shiga ko ka samu ka ci wani abu,na ga bakin ka duk a bushe alamun akwai yunwa a jikin ka",


Nan ko ya bi bayan shi,suka haura sama,ya bude kofar dakin nashi,shi dai Rilwanu baki bude yake bin gurin da kallo wato masu kuɗi fa suna hutawa abun su,mamaki be ida kashe shi ba Saida yayi arba da hadaddiyar dakin da Kabiru ke kwana a ciki,da sauri ya karasa shiga ciki,tare da zama a kan katifar gadon da ta sha shimfida da farin zanin gado,


Toilet kabiru ya shiga for some mints sannan ya fito,"tashi ka shiga na hada maka ruwan wanka ka samu ka ɗan watsa ruwa",


Mikewa rilwanun yayi sannan yace"na roke ka Kabiru ka bar maganar wankan nan,ka zo mu zauna muyi magana a taya ya ka tara irin wanann arziki haka,tun muna sch dai ka san ba mu da burin da ya wuce muyi kudi na tashin hankali,yanzu kayi shine za ka mance Ni ko,haka amana ta ce?,ya kare yana nuna tsantsan fushin shi, murmushi Kabirun yayi sannan yace shiga dai kayi wankan ina jiran ka,be kara cewa komai ba ya shige toilet in da be taba ganin irin shi ba sai yau,wanka yayi  sosai domin ba karamin dadin ruwan ya ji ba sannan ya dauro towel ya fito,


"Ga kaya nan a kan gado harda agogo da takalmin da idanun ka suka kusa faduwa akai gurin kallon su dazu ka sanya,in ka gama ga abinci nan nayi mana order",dariya rilwanun yayi sannan ya goge jikin nashi,be wani bata time ba ya gama shirya wa,sai gashi ya fito fesss,


   "Wow mutumi na,kudi ba karamin kyau zai yi maka ba,ka ga yanda ka fito kayi fess kamar wani Sen",


Dariya Rilwanu yayi sannan ya zauna suka shiga cin abinci,Saida suka gama sannan Kabiru yace "bani labarin bayan rabuwar mu",


Hmm "Kabiru wani labari ne gare Ni me dadin sauraro,sam duniya ta tsaya mun cak,tun gana karatun mu nayi yawon neman aiki har na gaji,babu inda ban je ba amman abin yanzu wai sai in ka sani ko wani ya sanka,kafin nan ayi maka hanyar arziki,could you imagine wai Usmanu ne fa shine ke jan ragamar gidan mu yanzu,yayi aure har gidan kanshi yayi yanzu haka matar shi na dauke da wani cikin,Amman Ni kam babu wani cigaban da ba samu a rayuwa ta"ya kare kamar zai yi kuka,


Zama Kabiru ya gyara sannan yace "ai Ni zan sanar maka this life is no balance at all,yanda Ka wahala a neman aiki haka Ni ma kaina na wahala,babu inda ban je ba Saida ta kai ta kawo kudin Siyan omon wanki ma da kyar nake samu,ganin in na cigaba da zama talauci zai zamo ajali na,ya sanya Ni barin Azare na koma Bauchi,abinda ya sanya ban sanar maka ba kuwa nima na tafi ne ba wai ina da yakinin zan samu ba wai na gwada dai,shekarun farko ba karamin wahala na sha ba,babu irin aikin da ban yi ba don ganin na samu rufin asiri,kasan ance me zafin nema na tare da samu,gashi yanzu Allah ya mun ya buda mun nayi gida nai mota,nai sutura kai har mata na aura me mugun kyau yanzu haka ma ina da dan Yaro,sun tafi yawon shakatawa kasar Dubai da babyn wata sati za su dawo,aiki ne ya rike Ni ya sanya ko da na zo a rasuwar Abba ban zauna ba ya sanya ba mu hadu ba,ya kare yana me nuna wa Rilwanu hoton Matar shi

 da babyn shi,


"Kabiru!! Kabiru!!,na shiga uku wai kana so kace da Ni wanann zukekiyar iyalin ka ce harda 'da,kace wai sun tafi Dubai,kasar da muke jin labarin shi a gidan Radio,wai a yaushe ne kayi irin wannan kudin haka,wani irin aiki ne ma kake yi,wlhh a shirye nake ko fashi da makami ne nayi in har zan samu arziki irin naka Nima na auri mata me kyau irin ta ka,in sai mota in yi gida,don Allah aboki na ka taimake Ni ka daura Ni a hanya,yanzu abun farin ciki ne ace yanda nake da kai,kayi making in life while Ni babu abinda na samu,ko suturun kirki fa bani da su,na roke ka Kabiru ka daura Ni a hanyar samun arzikin nan Nima",



Murmushi Kabiru yayi sannan yace"Aboki na,ba a tambayar me kudi taya yayi kudi domin in ka ji labarin a tayaya yayi sai ka tausaya mishi,wani kusan bada rayuwar shi yayi kan ya samu kudadan nan,don haka bana tunanin abunda nayi na samu kudi kai za ka iya yi,ka cigaba da hakuri kawai ka nemo aikin gwamnatin ka",


Nan ko Rilwanu ya buga kasa ya rantse da girman Allah Kabiru be isa ba zage shi tas yayi akan ashe daman yana da mugunta a ranshi,yanda ya dauke shi ba haka ya dauke shi ba,inda shine ai ko be roka ba zai nuna mishi hanya,ire iren maganganun da Rilwanu yayi ta cakawa Kabiru ke nan,wanda da kyar Kabiru ya sanya yayi shiru don ya saurari abinda zai fada mishi,



"Shike nan Aboki na yanzu dai ka tashi mu je in maida Ka gida,domin ina da abinda ya dace na karasa yi don maybe cikin dare zan koma ko gobe da sassafe,gashi wannan card ina ne ka neme Ni in yaso za muyi magana,sai kuma wanann 500k ne na san zai ishe ka ka sauya akwatin ka ya kare yana mika wa Rilwanu damin kudin,


Ba karamin tsoro bane ya kama Rilwanu a haka ya karbi kudi da card in suka fito, zuciyar shi cike da tunanin a ina ne wai Kabirun yayi irin wanann kudaden har yake iya yin kyauta haka,har kofar gida ya kai shi,sannan suka yi sallama,rilwanu na jaddada mishi kan zai fa kira shi saura kuma ya kira yaki dauka, dariya Kabiru yayi sannan yace "zan dauka,kai dai bara ka taba canjawa ba",da haka suka yi sallama ya shige gida zuciyar shi cike da annashuwa,an samu na banza,ya samu kudin cin banza da wofi,



Cikin dare kuwa Rilwanu ya je ya siya waya, tare da sanya number in Kabiru da ya gani jikin card in ya Danna mishi kira,domin sam be jin yana da hakurin ko nutsuwar da zai iya bari sai an kwana biyu ya neme shi,gwara a yi me yuwa, ya zamo arzikin kanshi ne shima yana samar wa mara sa shi,saidai kiran duniya line yaki shiga a haka ya kwanta ranshi a matukar bace,


Washe gari sassafe wanka kawai yayi ya bar gidan Gwoggo na ta fadan ya tsaya ya ci wani abun Amaman Yace a'a,kai tsaye gurin Saida abinci ya nufa ya ci ya koshi ya sha lemon kwalba sannan ya nufi gidan su Kabirun,inda aka sanar da shi ai tun Jiya da dare ya zo yayi sallama kan ya koma,nan ya kuma kulewa ya wuce hotel in da ya kai shi juya,saidai suka ce sassafe ya tafi ai,in ranshi yayi dubu to ya ɓaci,a haka ya koma gida ya cigaba da trying number in shi babu dare babu rana,Amman amsan daya ne a kashe,a haka dai ya cigaba da cin kudin shi a hankali inda be sanar da kowa yana da sisi ba gudun kar a roke shi,shi zai ci me kyau ya sha me kyau a boye, cikin wata guda kuwa ya cinye kudin tas sabida rashin tattali,


Ganin be da sisi sannan har yau layin Kabirun baya shiga ya sanya shi yanke hukuncin shiga garin Bauchin,domin har ga Allah ba zai ga samu ya bar shi ba,


Saidai rashin sanin Address in Kabirun ne ya bata mishi rai,can kuma ya tuna ashe ya bashi card in Shi a nan ya dauko cikin Sa'a kuwa ya ga address in Shi a jiki,wannan ranar ya shirya tsaf ,a gurin Gwoggo ya karbi kudin mota inda ya sanar da su kan cewa ya tafi Bauchi neman aiki,Rakeeba dai da kallo ta bishi domin halin Rilwanu sai shi,da haka ya sanya kai ya tafi tasha,ya shiga motar Bauchi,ji yake kamar ya karbi motar ya ja don gani yake kamar driver in Baya sauri,a haka dai suka samu suka isa,be wani sha wahala sosai ba gurin gano gidan Kabirun,domin irin kaurin sunan da yayi yana daya daga cikin masu kudin Bauchi,zuciyar shi be tashi bugawa ba Saida ya isa kofar gidan Kabirun,be san sanda ya fashe da kukan bakin ciki ba,


Domin irin wannan gida shi ake kira da aljannar duniya,yanzu daman a wanann Mansion in Kabiru yake da zama,wai wani irin aiki ne wanann me kawo kudi haka,ai dole Kabiru ya daina kula shi domin shidin ba tsaran shi bane,ko kusa be isa hada kai da shi ba don the differences is clear,Saida ya gama kukan zuci da filin shi sannan ya buga gate in gidan,


Me gadi ne ya taso ya bude tare da tambayan"malam lafiya daga ina,wa kuma kake nema"?,



Kallon sama da kasa yayi wa me gadin sannan ya hankade shi tare da shiga cikin gidan yana ne cewa"dallah matsa mun yau ka ji mun sabon iskanci,shi Kabirun ne yace a hana Ni shigowa in na zo ko me,to aminin me gidan ne ni dan uban ka ya kare yana hararan me gadin,


Nan fa hayaniya ta ƙwaure a tsakanin su da har ya sanya matar gidan fitowa,ta ci kwalliya cikin wata hadaddiyar kace,


Cikin yar murya ta tace"kai malam Tasi'u wai hayaniyar me nake ji ne haka har cikin gida"?, 

      "Hajiya daman wannan mutumin ne ya zo wai shi aminin Alh ne nace da shi ba a sanar mun da zuwan shi ba ya koma,Amman ya ki Saida ya shigo",


Kallon rilwanu tayi wanda shima kallon tan yake yi,kafin tace"yi hakuri ban gane ka ba,


"Eh bara ki gane ba kam tunda ban zo bikin ku ba,suna na Rilwanu Audu Waziri ",ai da jin sunan nashi sai ta saki murmushi"sannu da zuwa ai ko my dear Yana yawan Bani labarin ka mu shiga daga ciki ka ibo hanya",nan ko ya bi bayan ta idanun shi kamar zai fado don ganin irin kayan alatun da ke gidan,har parlor ta kai shi ya zauna sannan ta kawo mishi abinci da lemuka,


Nan ya shiga ci suna dan taba hira,"wai don Allah Asiya kina so ki ce da Ni wanann katon gidan gidan Kabiru ne??,


Dariya ta sanya sanann tace"wlhy tashi ce ai wanann ma karama ce a irin gidan da yake gina mana wanda za mu koma ciki",


    "Ikon Allah,dare daya Allah kan yi Bature,to wai ina shi Kabirun ne ban ji ko motsin shi ba,sane da shi gani na zo",


Mikewa tayi sanann tace"ai ko jiyan nan yayi tafiya,ya tafi Kwara akwai wani meeting in da zai hallarta,Amman ina ganin in be dawo yau ba to zai dawo gobe",


Hmm "Kabiru an yi kudi ba zama to kuwa wlhh ina nan babu inda zani ya je ya gama yawon nashi,ya dawo ya same Ni,in ce akwai dakin da zan kwana,in ma babu Ni ko nan parlor na kwan,bani da tsanani tafiya ce da ba inda zani suka ya dawo mun zan ta",


Idanu ta zaro don jin abinda ya fadi,kafin tace"aa Rilwanu ka koma gida dai in ya dawo ka zo ko",


"Ke dallah yi mun shiru in je ina,wallahi in kin ga na bar gidan nan mijin ki ne ya dawo muka yi maganar da za muyi,Amman in be dawo ba ko shekara zai yi ina nan ina jiran shi ya kare tare da mikewa akan kujerar yana me lumshe idanun domin ba karamin  ciwon kai yake ji ba....



Ina me baku hakurin jina shiru da kuka yi hakan ya faru ne bisa yan wasu dalilai,


Na so ya fi haka yawa,Amman sau biyu ina typing yana gogewa,kuyi manage da wannan,



Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


            💖

                  THE TALENT TROUPE WRITERS💖💖

........


NA DAINA AJE GROUP LINK INA DOMIN ANA SAMUN MAZA MARA SA TSORON ALLAH NA JOINING SUNA BIN MATAN AURE DA BADALA,DUK ME BUKATAR SHIGA GROUP INA SHOULD TALK TO ME IN TABBATAR MACE CE SAI NAYI ADDING IN MUTUM DA KAI NA,BUT PLS IN HAR KIN SAN BA KARANTA BOOK INA ZAI KAWO KI BA TOH KI YI ZAMAN KI BA SAI KIN YI JOINING BA,


Wannan page in sadaukar wa ce a gare ki Masoyiya(mom sayyid),love you so much 😩❤️


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


...........

          Page thirty _eight 


********


    Kwanan Rilwanu uku a gidan Kabiru,inda ya bi ya addabi Asiya da kwadayi,shine ci wanann ci wancan kamar wani gidan shine,hakuri kawai take yi tana Allah Allah Kabiru yayi ya dawo ko za ta samu ta huta da fitinar Rilwanu,haka zai wuni yana ikon Allah wai duk wannan dukiyar na Kabiru ne,to a yaushe ne Kabirun yayi irin wannan mugun kudin haka,Ita dai bata kula shi domin ya fara kullar da ita,


Suna zaune da dare sun gama cin dinner ke nan,suka ji karan bude gate,da sauri ta mike tare da rikon hannun dan yaron jikin ta tana cewa"oyoyo ga Daddyn ka nan ya dawo",da jin haka kuwa yaron ya fara tsallan murna,


Cike da soyayya ta fito harabar gidan don taro masoyin nata,har rige rige suke ida da yaron nata me suna Ayman gurin rungumar Kabirun,duk a idanun Rilwanu dake hango su ta window ji yake kamar ya harbe su da bindiga Don takaici,nan suka gama rungume runguman su sannan ta karbi jakar hannun shi,while Shi kuma ya dauki yaron suka shigo cikin parlorn,


Mamaki da tsoro ne ya kama shi, wanda hakan Saida ya kusa sanyawa ya kusa yarda 'dan hannun shi,sakamakon arba da yayi da rilwanu tsaye a kofar parlor in,


Bakin Shi har rawa yake gurin furta"Rilwanu!!,me ya kawo ka gida na?,me ka zo nema"?,


Hannu Rilwanu ya tafa cike da al'ajabi,sannan yace "yayi kyau masu kuɗi uban matsiya ta,da kyau Kabiru,ana fadin mutum kayan Allah bana yarda in ance mutum mugun ice,Amman yau na yarda, wato sabida kayi arziki shine ka juya mun baya ka guje Ni,don na zo gidan ka har kake tambayan wai uban me ya kawo Ni gidan ka",ya kare zuciyar shi a ƙufulle yana me jin kamar ya rufe Kabirun da duka,


"Haba dai Rilwanu gida na kam ai gidan ka ne,ina mamaki ne dai yaushe ka zo,yanzu dai kayi hakuri baran aje jaka ta sai na zo mu zanta,ai ban San ina da babban bako ba Rilwanu Audu Waziri da kanshi a gida na,ya kare yana dariya,


"Kai dai ka ji da shi,idan ma pretending kake baka ji dadin gani na ba,babu inda za Ni,ina nan ina jiran ka tunda yau 5 days ke nan da zuwa na daman nace ka je ka gama yawon naka ka dawo ka sake Ni ina nan,ya kare tare da zama a kan kujera tare da daura daya kan daya,Kabiru be ce da shi komai ba,ila haurawa Sama da yayi Asiya na biye da shi,har suka shiga dakin sa,


"Sannu da hanya baran shiga na hada maka ruwan wanka","dakata Asiya a tun yaushe Rilwanu ya shigo gidan nan ban da labari??,


"Wlhy My dear Nima ganin shi nayi kwatsam nayi nayi ya koma sai ka dawo Amman sam yace babu inda za shi har sai ka dawo,yau kwanan shi 5 ke nan,thank god ma ka dawo yau in don wlhh ba karamin isa ta yayi ba,don yau na so na kira na hada ku ko ka kore shi da kan ka,kila ya ji ya tafi,ka ga wahalar da Ni da yayi,kullum yana cikin zai ci abu kaza,dafa mun abu kaza,sai kace aure na yake,ta kare a shagwabe tare da shigewa toilet in,tsaban takaici Kabiru be iya cewa komai ba,toilet in kawai ya fada,Saida yayi wanka ya gasa jikin shi da ruwan dumi don ba wani bacci me kyau ya samu ba jiyan,jikin kuwa duk ciwo yake masa,ko da ya fito be dauki time ba ya shirya tare da fitowa domin Sarai ya san halin Rilwanu na rashin hakuri tsaf zai iya biyo shi har cikin dakin baccin shi,don in dai akan son abun duniya ne to ba hankali ya fiya ba,


Ko da ya sauko in da ya bar shi haka ya tarar da shi,saidai ya cika tam kamar jira yake a taba shi ya fashe, hakan ya sanya shi sakun fuska tare da dan dakan kafadun shi,


"Amini na Rilwanu,ya kake to,yanzu Asiya ke sanar mun ashe ka kwana biyu da zuwa",


"Dallah dakata mun Wlhy Kabiru ka bani mamaki kuma ban taba daukan a tsakani na da kai akwai wulakanci ba,saboda rai Ni wayo don ka ga Allah ya Azurta ka Ni bani da komai,ya sanya ka dauki fake number Ka Bani nayi ta kiran ka bata shiga ko??to na ga ai kaima ba rawa kayi wa Allah ya baka arzikin ba,sannan in ta gaskia za a bi Ni ne nan ya dace nayi irin wannan kudaden ba kai ba,sabida ko da muke makaranta Ni ke rubuta maka jarabawa,Amman dake butulu ne kai har ka mance baya,ka zamo kaza da zata ci ta goge bakin ta ta mance ta ci,Ni ba kudin ka nace ka bani ba taimako na zaka yi ka daura Ni a hanyar da kayi kudi ko Nima zan dace,Amman sabida bakin hali Kabiru ka kiyi sai avoiding ina kake tayi kamar wanda na zo maula",ya kare a hasale,


Ran Kabirun ya ɓaci kwarai da gaske,cikin fushi kuwa ya hau fadin"ka ga rilwanu bana son wulakanci da cin fuska,abunda ya wuce kam ai ya wuce ko kyauta ka zana mun jarabawar??gani nai ai kudi na biya kafin kayi mun,da zaka zo kana fada mun magana son ranka,and da kake maganar naki nuna maka hanya,a cewar ka ne abunda na yi kai za ka iya don tara kudi,kasan ko fashi da makami nake yi??


"Look Kabiru dallah daka ta mun bani son iskanci da rainin wayo, nan nace da kai Ni fa ban damu ba as far as Zan samu kudi irin naka to wlhy ko yankan kai kake yi a shirye nake na yanka ko da Mal Audu Waziri ne in har zan samu kudi,nayi gida nayi mota irin taka",


Baki Kabiru ya bude cike da mamaki sannan yace"a'a banda Audu Waziri kam uban ka ne fa",,,"uban nawa din,wani abun arziki ya tsinanawa rayuwar tawa ta azo a gani,ko wani uba yana iya kan yin shi gurin ganin ya tara abun duniya,inda ko ya fadi ya mutu ya san be bar iyalan shi cikin garari ba,Amman sam banda mal Audu ji nake kamar talaucin duniya a gurin  shi ta kare don wannan tsohon kana ganin shi,ko takalmi me kyau bana ji za mu samu gadon shi balle a je ga maganar dukiya",,,"Allah ya kyauta,yanzu dai ka zauna ka cigaba da kallon ka,baran samu na ci abinci na huta zuwa gobe sai mu zanta ko",


Dariya Rilwanu ya fashe da shi sannan yace"Kabiru kana bani mamaki wallahi,dauka na kake bakauye don kayi kudi ko me,wai Ni za ka kalla kace ga tv na kalla,wai ko ka mance Ni ne dai Rilwanu da har kaya iri daya mun saka,Amman yanzu saboda kayi abun duniya kake abu kamar me ma zance,wlhy Kabiru in Ka ga ka ci wani abu to ka sanar da Ni yanda kayi kudi,domin zuciya ta an sanar mun ba wai iya aikin gwamnati bane kawai ya tara maka irin wannan kudaden,ko dai ka fara damfara ne bani da labari??? 


"Rilwanu gaskiyar bahaushe ne da yace ko after 10 years Ka hadu da mutum kar ka tambayi ya halin shi,domin halin nan yana nan ba canza shi zai yi ba, yanzu dai ka bari na ci abincin sai muyi magana ko,in baka ci ba ma sai ka zauna mu ci tare",


"Dallah hold it Kabiru Ni kam mancewa kayi da hali na wlhy ka mance waye Ni ne ko me,sanin kan ka ne dai hakuri kam bani da shi ko na kobo,in dai na so abu to kamar 'da ne ya so fita cikin uwar sa in be fito ba bare samu nutsuwa ba, Kabiru ka bani mamaki wlhy i never thought a rayuwar nan har akwai abinda zaka samu ka mance ko ince ka canza mun,ashe can amintar karya muka yi Ni da kai,ashe yanda na dauke ka Ni da zuciya biyu ka zauna da Ni, yau arziki ce ta haɗa mu ko,a shekaru nawa muna abota tun baka da komai,Nima haka,Amman yau Ni kake wulakantawa saboda na zo ka yi mun silan arziki,laifi na ne da na dauka Kabiru amini na na tun makaranta shine har yanzu ashe kudi ya canza shi,da na san wulakanta Ni za ka yi da wlhy ban bata kafa na na zo ba,babu komai Kabiru na gode sosai ba dai dukiya bace muna nan da kai Nima zan yi ta,ka ci ta ka ka more,and for your information cikin daran nan zan bar maka gidan ka,tunda daman can baka ji dadin zuwa na ba,amma ka sani kayi mun abinda ba zan taba mantawa ba a rayuwa ta,and wlhy ka sa a ranka in da Ni ne na samu wannan dukiyar taka ba sai ka neme Ni ba Ni zan neme ka kuma na daura ka a layi,don ka zo ka wani bani dubu dari biyar har wata kudi ce,da kake tunanin za su rike Ni,ka ban mamaki wlhy, ba kuma zan kuma neman ka ba, wulakanci ya isa haka",da gama fadin haka ya sa kai tare da fara tafiya,


Ba karamin sanyi jikin Kabiru yayi ba,duk sai ya ji be kyauta wa Aminin nashi ba,tabbas inda shi ne Rilwanun yayi wa haka ba zai ji dadi ba,tare suka taso,tare suka sha gwagwarmaya,and tare suke da plan in yin kudi na tashin hankali,saidai yana matukar jin tsoron sanar da Rilwanu hanyar da ya bi ya samu daulan nan,domin be da tabbacin zai yarda kasancewar gani yayi mahaifiyar sa Malama ce diya ga babban malami,in kuma be yarda ba ya tona mishi asiri fa??shi gaba daya ma kanshi ya kulle,yana son sanar da shi hanyar da ya bi yayi kudi Amman kuma yana jin tsoro,


Ganin har Rilwanu ya nufi kofar parlor in ne,ya sanya Kabiru cikin mutuwar jiki yace "Aboki na tsaya ka ji Ni pls,duk ba abun fushi da tashin hankali bane",,, Rilwanu be tsaya ba kuma be juyo ba sai cewa yayi "Are U ready to talk ko a'a??",,da sauri Kabirun yace "am ready come back pls let's sort it out,


Jan hannun Rilwanu yayi har zuwa dayan parlor in Shi,domin wannan magana da za suyi yana bukatar sirri ko Asiya bata sani ba kuma baya fatan ta sani,sai da suka isa sannan Rilwanu ya fincike hannun shi "ina jin ka",


Tsayuwar Kabirun ya gyara sanan yace "Rilwanu kusancin mu da kai,ya wuce na kira ka aboki saidai Amini,na yarda da kai ne ya sanya zan sanar da kai sirri na,ba zan boye maka ba at first Nima da kyar na yarda,don ko da na ji ance ana samun kudi,tsoro ya hana Ni,ganin talauci yana neman ganin baya na ne ya sanya bani da wani zabi,tunda karatun da muka yi aikin banza ya kare,aiki ya gagara samuwa,ba zan boye maka ba Randa na fara cafke mahaukatan kudade a hannu na tsoro da fargaba ba karamin kama Ni suka yi ba,domin ina daga daka na ga ruwan kudi ganin idona,wlhy kaine mutum na farko da ya fara zuwa min rai,saidai ina jin tsoro,kar ka zo baka yarda ba,ya sanya ko da muka hadu kayi ta bina na nuna maka hanya,na kasa don ina tsoron tonuwar asiri na",,,"abunda ya sanya ka bani number in Ka mara yi ke nan??kana tunanin Kabiru ko kisan kai kake Zan juya maka baya ne?kasan matsayin da na baka a raina kuwa,na dauka Ni din Abokin rufin asiri ka ne wanda za muyi kuka tare muyi dariya tare",


"Na sani wlhy Rilwanu yanda kake kauna ta haka nake kaunar ka,no in da na baka tabbas ta wa ce,kuma tana shiga,saidai in har banda contact in mutum ko ince in banyi saving number in mutum ba to ko shekara zai yi yana kira na line a kashe zai na jin ta,sabida gudun matsala ya sanya nayi haka,Amman kayi hakuri,zuwan ka gida na ya tabbatar mun da gaske kake son yin kudi ko ta wani hanya",


Kan kujera Rilwanu ya fada sannan yace"Kabiru ke nan kana manta waye dan gidan Audu Waziri ne wlhy, kasan kuwa yanda hankali na ya gaza kwanciya tun randa nayi arba da irin arzikin da kayi kuwa,na roke ka all this long turanci aje shi a gefe ka bani bayanin taya zan yi in samu kudi,ba fa kananun kudi ba,ina nufin mahaukatan kudade",


Shima Kabirun zama yayi kusa da rilwanu,sannan ya dafa hannayen shi"Aboki na in dai kudi ne ina tabbatar maka da matsalan ka ya zo karshe,za ka samu kudi daukaka,nasara Shahara duniya za ta san da kai,tauraron ka za ta haska,rayuwar ka za ta canza,za kayi gidaje,motoci,sai sai ka zamo abin kwatance da abin burge wa da sha'awa cikin mutane",


Nan take Rilwanu ya wage baki abin yayi masa sweet,cike da jin dadi yace"na roke ka,Kabiru ta shi mu je gurin kuɗaɗen nan cikin daran nan Ni a shirye nake"ya kare yana mike wa,,dariya Kabirun ya sanya sannan yace"aboki na dadi na da kai hanzari da gaggawa,ka koma ka zauna mu karasa magana,",a ranshi be so ba dai ya koma tare da zaunawan sannan yace "ina jin ka, miye kuma ya rage"??


"Rilwanu as I told U duk wani me kudin da ka gani,a duniyar nan shi kadai ya san irin wahalan da ya sha kafin ya same su, nothing good comes easier,you have to pay a huge amount of price kafin ka samu burin naka ya cika kayi irin kudi na kila ma kayi wanda ya fi nawa",,da sauri Rilwanu yace "name the price just say it wlhy a shirye nake ko miye nayi in har zan samu kudi,(kusan in mutum na matse da son samun cikar burin shi ko in ce biyan buƙatar shi,to hankali da tunanin shi gushe wa suke,har sai bayan ya cimma wanna burin nashi, ubangiji kayi mana tsari da son zuciya da kuma son abun duniya),


"Are u sure rilwanu a shiri kake da yarda da abinda zan fada maka,saisa da na so na baka time kayi tunani domin abu ne na idan na fada maka sirri na baka yarda ba daga Ni  har kai mutuwa za muyi, mutuwa mafi muni ma kuwa",,ba tare da tunani tsoro ko wani abu ba Rilwanu yace"fadi kawai Kabiru am damn tired of poverty,ina son nayi rayuwa cikin jin dadi,na kwanta na tashi kuma na taka Naira",dariya Kabirun yayi sannan yace har dollars ma in Ka so za ka taka su dan gidan Audu Waziri,well tunda kayi alkawarin yarda da abun da zan fada maka,to zan sanar da kai sirrin samun kudi na,



Kamar yanda na fada maka,yanda Ka wahala a neman aiki bayan gama bautar kasar mu haka nima na wahala, ganin talauci na neman kashe Ni ne ya sanya na gudo daga Azare na dawo Bauchi ina cigaba da neman aiki duk a banza, Saida na hadu da wani matashin yaro me kudi a jika sosai,to a sannu na samu na rabe shi inda a karshe na nemi,ya sanar mun a taya yayi kudi kamar yanda yanzu kaima ka nema ji daga garan,nan ko ya nuna mun hanya,da kuma na bi komai yanda aka ce gashi yanzu nan na mallaki duk abinda nake burin samu "Kabiru ya kare yana murmushin samun nasara,har yanzu kan Rilwanu a kulle yake,


"Ni fa Kabiru na fi son in zaka yi magana ka fito kawai ka fada mun a bayyane,wanann dunkullaliyar magana da kake mun sam bana fahimtar ta,me kayi ka samu kudi,and a ina ka je ka karbi kudin,ka fito ka yi mun bayyani kawai",,"Are you sure Rilwanu you are ready kayi komai don ka samu kudi??,,"da sauri Rilwanun yace Wlhy Kabiru raina ne kawai bazan iya badawa ba domin ance amfanin rai ga me shi,don in huta in fantama nake son yin kudin",


Numfashi Kabiru ya sauke sannan ya gyara zama"Rilwanu babu wani boye boye tsakanin mu since har ka gwada kana so to bani da zaɓin da ya rage in nuna maka hanya,kamar yanda ka fada ne ba aikin gwamnati bane ya kawo mun wannan makudan kudaden,ganin talauci na neman ganin bayana ne ya sanya,na bi yaron nan muka tafi har kauyen Offa da ke garin kwar",,"kar ka ce mun gurin boka kuka je Kabiru,bokan kauye ne yayi maka irin wannan kudadan?,daman da gaske aikin boka na ci ne??


"Dadi na da kai sam baka cin riban zance,Ni kam na gaji da yi maka long bayanin nan,Rilwanu CULTISM nayi joining,wato kungiyar asiri na shiga,da sauri Rilwanun ya mike idanun shi kamar sa fado kasa hannun shi na karkarwa yace"Kabiru kana so kace da Ni kungiyar shan jini ka shiga",,,,"yes rilwanu kungiyar shan jini da cin naman mutane na shiga,ina da wani option ne??this world is so wicked to us,da ilimin mu da komai,Amman aiki ya gagara samuwa,do U think ina da zabi ne,i just want to be fucking rich har hakan ya sanya bana duba ta halal ko ta haram kudi dai sunan su kudi,yanzu dai in aka tashi fadi cewa za a yi Alh Kabiru me kudi,waya damu da kudin shan jini ne,ya kare babu wani tsoro ko fargaba a tattare da shi,ba dai sirri na kake son ji ba to na sanar maka,so zabi ya rage naka in kana son jin dadin rayuwar ka,ka murza Naira yanda kake so to ka zo kayi joining Brotherhood in mu, Odugwu zai baka duk wani abinda ka taba dreaming samun shi a rayuwar ka,


Hannu Rilwanu ya sanya tare da dafe kai da bakin shi cike da firgici,har ga Allah be taba dauka wai kungiyar asiri Kabiru ya shiga don ya samu kudi ba,No wonder mana biri yayi kama da mutum,a ce lokaci daya mutum yayi irin wannan mugun arzikin,ai daman dayan biyu ko yankan kai ko kuma fashi da makami,ke nan abokin shi ɗan shan jini ne be sani ba,nan wani irin tsoro ya kuma kama shi,


"Kayi shiru Rilwanu,ka sanya na fada maka sirri na tare da ɗaukan alkawarin zaka yi joining,Are u ready to join in??ya tambaye shi yana me tsare shi da idanu,wata irin gumi ne ke ƙeto wa rilwanu baki na bari yace"Kabiru am scared wlhy ba zan iya shan jini ba,beside ina jin labarin yan cultism dole sai ka bada abu kafin ka samu kudi in return,and gaskia Ni,,,saurin katse shi Kabirun yayi gurin fadin"kai dallah can ka fiye tsoro wlhy sai ka zauna talauci ya ga bayan ka,kana gani nan na je kasashen duniya sun fi 10,mota kuwa ina da su ya fi 5,haka ma gidaje,ka ga sutura ta duk ciki babu ta kasa da dubu hamshi,ka ga matar da nake aure,mal wanke hannu ka taba,and Waye yace da kai ana shan jini,kai Blazed house fa ba irin wannan local cultism bane wanann ne aji da tsafta ne,(Ni ko nace yau ga iskanci,wai ba irin sauran kungiyar asiri bane,wannan me tsafta ce,daman akwai wata sabon Allah me tsafta da mara shine,Allah ya kyauta ya kuma  kyautata karshen mu),dokokin su sam ba na tashin hankali bane,abinda na san ba zai fi karfin ka ba,amman fa ba zan maka dole ba,ai daman ance amfanin rai ga me shi,duk yanda zan so maka arziki,kai za ka fi so wa kan ka,amman ina so ka tuna irin bakar rayuwar da kake ciki,ance ai da arziki a garin wani gwara ayi a garin ku,garin ma a gidan ku, gidan ma a dakin ka, malam ka ga ruwan kudi na zuba from no where,Dan numfashi ya sauke sannan ya kuma fadin,saidai fa Ni ba kullum zan na taimakon ka da kudade ba domin kasan ance bani bani kan sa a gaji,ba zai yu kare da shan bugu gardi da kwashe kudi ba,Ni da wahalar nema ka zo ka ci su a banza,don haka dabara ta rage wa me shiga rijiya"ya kare tare da mikewa,


Shiru Rilwanu yayi,deep down Yana Jin tsoron Allah,while dayan zuciyar na hasko mishi daula irin ta Kabiru,cikin sanyin murya yace"sai na ji kamar ka ce ruwan kudi a daki na,Kabiru da gaske kake Zan samu mahaukatan kudade in nayi joining??,dariya Alh Kabiru ya sanya domin da har ya fara jin tsoro kar Rilwanu yaki bashi hadin kai,da sauri kuwa yace "wlhy Rilwanu in dai kudi ne sai ka ce baka so,kai ba kudi ka dai ba,ba tun muna sch kake da ra'ayin siyasa ba to wlhh Odogwu sai ya sanya ka zamo gwamnan jahar Bauchin nan mutum ka yarda ka shigo,duk wani burin ka na duniya sai sun ciki",,"Kabiru wlhy na yarda tashi mu je cikin daran nan gurin Odagun na ka ya bani kudin don Allah,wlhy a shirye nake nayi komai don ganin na mallaki yan canji a jiki na",



    Dariya Alh Kabiru ya sanya sanann yace"da kyau mutumi na,yanzu na ji batu, welcome to the world of freedom and enjoyment,Kai da bakin ciki ko damuwar duniya kun yi hannun riga,za ka samu kudi me sunan kudi,kudin da sai sun kusa haukatar ka",,"don Allah tashi mu je Kabiru da zafi zafi ake komai",,,,"ka kwantar da hankalin ka zan kai ka gurin Odogwu Amman dole kayi hakuri sai zuwa ending of next month,domin sai karshen wata wata ake haduwa da shi, for now dai ka je ka kwanta kayi bacci,zuwa gobe sai ka koma gida kar a neme ka in ya so karshen wata sai ka zo mu wuce Offa in,ai da na sani ma da na jira ka mun tafi wannan meeting in tare nayi introducing in Ka to him, nan ko Rilwanu ya rufe ido yace Allah sam be san zance ba,babu inda za shi,nan gidan zai zauna har karshen watan su je ba shi zai zaga ba, kalan ya koma gida ya kasa samun shi,babu inda Kabiru be yi ba Amman sam Rilwanu ya nace ala dole ya kyalle shi aka gyara masa BQ ya tare ciki,tsaban mugun son abun duniyar shi,be damu ya kira gida ya sanar ba, idanun shi sun rufe kudin kawai yake hangowa,



A haka ya cigaba da zama a gidan Kabiru inda ya addabe su,amman haka Kabiru yayi ta hakuri,domin yanda ya halaka haka yake son halakar da rilwanu (a kullum ya sanya yana da kyau kayi abota da mutanan kirki,bature yace wai show me your Friend and I will tell you who you are,aboki na kwarai kan kusanto da bawa zuwa ga Allah,haka zalika abokan banza kan nisanta mutun daga Ubangijin sa, ubangiji ka sa mu kasance abokai na gari,sannan ka haɗa mu da mutanan kirki a duk inda muke),



Ko da Rakeeba ta sanya Usmanu kiran shi,don ya daga musu hankali kusan sati 3 ba waya ba kuma su san halin da yake ciki ba,nan ya sanar da ita kan cewa"tayi hakuri abubuwa ne suka sha masa kai,ya je nemo musu abun duniya ne,domin baya jin dadin ganin Usman ne kawai ke dawainiya da su,so ya tafi neman aiki ta sa shi a addu'a nan da wata sati zai dawo",sam bata ji dadin maganar ba,domin har ga Allah tsoron mutanan duniya take ji,a ina ne zai samu aikin,waye ma zai bashi,ganin bata da me bata amsoshin tambayoyin ne ya sanya ta mika wa Allah komai,domin lamarin Abul bait sai dai a bar shi da Allahn kam,don sam be da lissafi,addu'ar dacewa da samun nasara ta yi mishi sannan ta kashe wayan,bayan ta kuma jadada mishi kan ya rike ibada ya kuma ji tsoron Allah,da haka suka yi sallama,


Nan Rilwanu ya zauna gidan Kabiru har zuwa karshen watan,tun safe kuwa yake ta azzalan Kabiru kan ya tashi su tafi shi fa a matse yake,haka kuwa suka dauko hanya bayan sun gama karya wa sassafe domin long journey ne daga Bauchi zuwa Kwara kam,


Kabiru ne yayi driving har Allah yayi suka iso,kwara lafiya,ko da suka dauko hanyar kauyen Offa ba karamin bugawa zuciyar Rilwanu ya shiga yi ba,nan take wani irin tsoro ya lullube shi,gashi babu halin ce wa Kabiru ya koma bayan sun zo this far, tsoro be gama kama shi ba Saida ya ga Kabiru ya kutsa cikin dajikan nan,cikin muryan tsoro yace"Kabiru wai ina  za ka kai Ni ne?,ko dai Nima kai Ni za ka yi a yanke mun kai?,ba karamin dariya Alh Kabiru yayi ba kafin yace"Nima farkon zuwa na babu irin tunanin da ban yi ba,da sannu zaka saba,wuyan ta mu je sau biyu sau uku ne,kai da kan ka zaka kawo kan ka",,,"na ga kana da kudi why ba mu yi using Flight ba muka zo a mota irin wannan dogon tafiyar?,rilwanu ya tambaya yana me tsare Kabirun da idanu,"abokina baza ka taba ganewa ba sha'ani na brotherhood dole sai an bi a nutse,and ba daga Ni bane daya daga cikin dokokin kungiyar ne in har za a yi haduwa to,a mota ake zuwa ka fahimta??,,"hmmm na gane Allah ya kyauta ",daga nan ba wanda ya kuma magana a cikin su har suka iso Blazed house,ba karamin mamaki Rilwanu yayi ba, mamaki be gama kashe shi ba Saida suka shiga cikin gidan, motoci bila adadin ya gansu,be gama tsorata ba Saida yayi arba da mutane sanya da Jajaye da bakaken kaya harda Aminin shi sannan ya yarda da eh fa ya saka kan shi a damuwa,wato dai sak abinda yake ji a labari ko ya gani a movie,yau ganin idon shi ya gani,nan ko Odogwu ya fito aka fara abubuwan da aka saba yi,aka gama sannan yace "ko akwai me magana??,


Nan ko Kabiru ya mike,bayan ya fadi yayi wa Odogwu sujjada,ya gama koro kirarin shi,ya yabe shi sosai tare da ɗaukan hakkin Allah ya bashi sannan yace "Odogwu the greatest,Amini na na kawo yana da sha'awan joining in kungiyar nan",


Dariyar yan iska Odogwu ya sake sannan yace "he is welcome,Haka nake son kuyi introducing Brotherhood wai yan North mu samu members da yawa daga gurin,aikin ka yayi kyau,keep it up,


Nan ko ba tare da bata time ba aka matso da Rilwanu da ke ganin komai kamar a mafarkin sa,nan kuwa Odogwu ya kara masa welcome,sannan ya kara jaddada mishi ya zo gurin da babu fita saidai mutuwa,Are sure you ready to join this group??,


Zuciyar Rilwanu nan ta shiga dukan uku uku,taba shi Kabiru yayi irin ka ce eh din nan,har ga Allah zuciyar shi na son cewa a'a Amman be San a garin yaya ba ya ji bakin shi ya amsa da "Eh am ready to join",


Nan ko Odogwu ya saki dariya sanann yace"akwai test in farko da ake baiwa new members in sun cika hakan ke nuna eh da gaske za su iya zama,wanda wasu da yawa sun kasa cikawa hakan yayi sanadin rayuwar su,Shebi na money you want??,"da sauri Rilwanu yace"yes sir plenty of money self",,dariya Odogwu ya kwashe da shi sannan yace You have a bright future,and na ji ina son ka because daga gani za a fafata da kai so yanzu zan fada maka First Sacrifice in da za kayi making,Wanda in kayi kana daga daki Ni kuma zan yi maka ruwan kudade,in kuma ka kasa yi to mutuwa za kayi,sabida yau kayi joining kuma ina cikin good mood yau zan Baka task me sauƙin gaske,as I can see kana da Uwaye har guda biyu wace za ka bamu a ciki??,Ni nake zabi wa mutane Amman kai for the first time na baka zaɓi,


Wani irin gumi ne ya karyo wa Rilwanu nan take jikin shi ya fara bari,ba haka suka yi da Kabiru ba,ya sanar mishi da cewa wanann cultism in me tsafta ce a taya za a ce ya zaba a tsakanin Gwoggo da Rakeeba,a taya ma zai bada daya daga cikin su,be Kai ga bude baki ba sai jin wani abu me sanyi na lasan goshin shi,ya daga kai sai ya ga macijiyar dake rataye a kafafun Odogwu ne,from no where be San a taya ba sai ji yayi bakin shi ya furta "zan bada Gwoggo Odogwu",


Dariya Odogwu ya sanya sannan yace"kayi tunani me kyau,okay tunda ita ka zaba in ka koma gida gobe misalin ƙarfe 1:30 na dare za ka shiga dakin so call Gwoggon naka kayi having sex da ita for  1 good hours after that Ka tabbatar ka kashe ta har lahira,i won't tell you taya zaka kashe ta duk method in da akayi using in har dai ta mutu daidai ne,bayan an zo an Kaita ka dawo daki za ka ga abun mamaki,saidai in har Ka Bari wani ya gan ka time in da kake having sex da ita ko yayin kashe ta ko a ga fitowar ka daga dakin ta,to tabbas za ka mutu,mutuwa mafi muni ma kuwa"ya kare a tsawace....



Sai zuwa Tuesday kuma in me kowa me komai ya so,



Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


            💖

                  THE TALENT TROUPE WRITERS💖💖

........



https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


...........

          Page thirty _nine


**********


   Wata irin wawiyar jiri ce ta kwashi Rilwanu,yuuuuu yayi baya zai fadi domin baya ji sam ƙafafuwan shi ne ya ji sun gaza daukan shi sakamakon abinda ya ji Odogwu ya fada,cike da zafin Nama Kabiru ya riko Rilwanun tare da cewa"haba Rilwanu try to hold yourself mana baka san a gaban shugaba kake ba", fincike jikin shi Rilwanun yayi sannan yace "i should hold myself!!I should hold myself!!fa kace, Kabiru ka kuwa ji abinda wanann mutumin ke fada mun kuwa, anya ka ji me yace, Gwoggo fa, Gwoggo ta matar da nake matukar kauna na shaku da ita kamar mahaifiya a taya zan fara kusantar ta??just tell me" ya kare a dan tsawace,


"Why on earth are you shouting at me!!,wai dole nayi maka ne rilwanu??,gani nayi matsa mun kayi akan sai kayi kudi,na ce ka bari ka bari ka nuna mun ranka ya ɓaci,har ka san yanda ka yi na kawo ka,sannan yanzu ka zo kana mun ihu akan me??,


"Dakata mun Kabiru haka muka yi da kai?a nan ina ka ce da Ni wannan ba irin local cultism bane,wannnan classic one ne,ba a shan jini ba a cin nama sannan rules in su na da sauki sosai,and yanzu ka duba ka ji abinda ake ce mun",


"Kai dallah matsa to,in ma na fada maka karya nayi, Rilwanu ana cin nama ana shan jini,yanzu haka ma abinda muke zaman jira ke nan,ka koma ka fadi a gaban Odogwu ka bashi hakuri sannan ka ce ka ji ka yarda da abinda ya ce tun wuri kafin fushin shi ya shafe ka",


"Fushi!!Fushi!!fa kace Kabiru na rantse da Allah na hakuri ka zo ka maida Ni gida ba zan iya wanga abu ba"Rilwanu ya kare da iyakan gaskiyar sa,


Wata razananiyar tsawa da Odogwu ya daka musu ne ya sanya duk suka ƙame guri daya cike da tsoro,hannu ya daga sai ga wata karamar cup a hannun shi,cike da bacin rai ya mika wa Rilwanu cup in,cikin Isa yace"drink it all right now"ya kare idanun shi sun kada sun koma kore sharrr,cikin rawar jiki Rilwanu ya karbi cup in ya kafa a baki,abun baki kirin ko za a yanka shi be san miye ba,ban da gafi da karni wari babu abinda abun ke yi,haka nan yana yamutse fuska yana jin tashin zuciya ya kwankwade,nan take kofin ta bace,nan ya ji kan shi tayi wani irin nauyi,kirjin shi na buga wa da sauri da sauri kafin ya ji ya dawo daidai,


Cike da jin wani jarumta da be san daga ina ya same shi ba ya fadi a gaban Odogwu tare da yi mishi sujjada,ya shiga sheko mishi kirari,kanshi Odogwu ya shafa,sannan yace welcome to the world of freedom and enjoyment,now za Ka yi rayuwa kamar sarki,i can see a  burning  fire in your eyes, we have a long way to go together,in har Ka bi umarni na nayi maka promise sai na mallaka maka abinda baka taba zato ba,"take this"ya Mika mishi wata jar kyalle,"don't forget Ka goga mata after having sex with her",da haka dai rilwanu ya karbi kyalle yana jin duk wani tsoro ko shakkun da ke cikin ranshi sun tafi, haka ya jira su Kabiru suka gama cin nama da shan jinin suka haura sannan suka sauko duk sun sauya kaya,fuskan kowa dauke da annuri nan ko aka hau sallama ana sai kuma wata karshen wata,da haka suka fito suka shiga motan Kabiru ya ja suka wuce hotel,Saida suka ci suka koshi sanann Rilwanu yake cewa Kabirun"yanzu shike nan in nayi hakan zan yi arziki irin taka"?,"eh man ai Jin ka nake da kake cewa wai baza ka iya ba,malam kudin da za ka gani in baka rike kan ka ba za ka iya zaucewa",,,"Allah Kabiru,Amman gaskia wanann abu yayi tsauri da yawa,Ni fa tunda nake ban taba Zina ba ko budurwa wannan bani da, Gwoggo kamar uwa take a gare Ni",ya kare kamar zai yi kuka,


"Kamar uwa ai ba uwa bace,ko ance maka gurbin ido idanu ne??,to wai miye wani abun tashin hankali, Rilwanu dadin da za ka samu gaba nake hango maka,wlhy ka gode Allah Ni nan da kake gani na,ka ga dai Asiya matata ko,to wlhy Uwar ta na danne nayi raping kuma ta mutu ko a jiki na,da Ni aka kai ta muka sha Kukan mutuwar ta tare,wa ma ya sani,ko ce ma aka yi zai rubutu a goshin ka na yi having sex da kishiyar uwa ta??,abeg just chill and relax in ma tunanin ka taya tana tsohuwa za ta zama wanda ta fara karya budurcin ka,zan iya nemo maka yar karamar yarinya ta fara dandana ka ka ga shike nan ai ko,ya kare yana dariyan yan iska,shide Rilwanu da kallo kawai yake binshi,a gaban idanun shi ya fita ya Ibo mata uku,yana mamakin zalama irin ta Kabirun,ko da suka zo shigewa Saida Kabirun ya nemi ya baiwa Rilwanun daya daga cikin matan da ya kawo, yace a'a baya so,dariya yayi sanann yace"a sannu yaro za ka goge ka shigo system in",



Washe gari sassafe suka dauko hanyar Bauchi,ko da suka iso ko gidan Kabiru be shiga ba, kudin mota ya karba gurin shi da kudin tsarabar da zai kai gida,yana fadin wa Kabirun,ya rubuta ya aje wannan kudin bashin su ya karba da kudadan shi sun zo zai biya shi,dariya kawai Kabirun yayi sannan suka yi sallama,yana jaddada mishi kan cewa kar fa ya sake ya bari a gan shi,sanann ya tabbatar yayi one good hour in Yana so ma zai bashi maganin karin karfi,dariya Rilwanun yayi sanann ya shige mota yana fadin"kai kam dai sai mun yi waya,a gaida Asiya",ba Kabiru ya koma gida ba Saida ya ga tashin su Rilwanun,zuciyar Shi sakayau yake ji,at least ko yau ya mutu yana da abokin tafiya hell together,


Direct gida ya wuce suna isowa hannun shi cike da ledoji,a tsakar gida ya samu Gwoggo da Rakeeba suna cin tuwon masara miyar bushesshen kubewa,durgusawa yayi tare da gaida su,nan kuwa Hajiya ta rufe shi da fadan "abunda kayi  ya dace ke nan Abul bait ace yau fiye da wata baka cikin gidan nan,gidan uban wa ka je,kana babba uba ga kannan ka Amman ace wai har yau baka yi hankali ba",,,"haba yaya ai kya dai bari yaron nan yayi wanka ya ci abinci tukun na ayi mishi magana cikin nutsuwa ko,yanzu fa dawowar shi,and ya sanar miki kan cewa aiki ya tafi nema fa,kya tsaya ki ji ai ko an dace ko yaya",,,,wlhy Gwoggon su ki daina bin bayan yaron nan,sam abinda yayi ai be kyautu ba,duk wani yaron kirki zai bar gida ya yi wata be sanar ba sai a waya,wlhy Abul bait ka raba kan ka,kana bin duniya a sannu,duniyar nan abun tsoro ce",baki ya turo kamar yaro sanann yace"yanzu Gwoggo don Allah me nayi,na zauan kullum bata da aiki sai Usmanu yayi kaza Ni shiru aiki yaki samuwa,yanzu na mike don nema wa kaina da dukkan ku mafita shine kuma wani abun tashin hankali,Bauchi na je fa, gurin abokina Kabiru gashi yace mun in kwantar da hankali na aiki kamar na samu,ban dawo ba Saida ya nuna mun office ina da gida da motar da Company da ta dauken za ta bani,ga kuma kudin kashe wa a ciki gashi nan na muku siyayya a kudin,kuma Gwoggo kiyi murna soon za ku daina cin irin wannan abincin,dadi na nan zuwa domin kudi ne na ban mamaki za su shigo mun kwanan nan,Makkah da Madina saidai ku kai wasu ba ku ba",ya na gama fadin haka ya tashi ya wuce dakin shi,tagumi kawai Rakeeba tayi domin in da sabo ya ci ace ta saba da  bakin halin Rilwanu,ita abinda take jin tsoro ma wai ji da tayi yace Kabiru ne zai masa silan arziki,Kabirun da ba a san taya ma yayi nashi kudin ba a taya zai zama silan arzikin dan ta,


Ba yanda Gwoggo bata yi da shi kan ya ci abinci ba bayan ya yi wanka Amman sam yace shi a koshi yake,don anxiety bazai barshi ya iya cin komai ba,ba karamin dadi kannan shi da Gwoggo suka ji ba ganin kayan dadin da ya kawo musu,shi dai bayi da burin da ya wuce ya ga dare yayi ya samu yayi abun nan ko zai samu kwanciyar hankali,


Ko da aka ida sallan isa,nan Gwoggo tace duk a fito tsakar gida a yi hira,harda Usmanu da matar shi da bata dade da kara haihuwa ba sun zo,fruit ta yanko musu ta zuba a babbar tray suka zauna harda Mal Audu da be dade da shigo wa ba,nan ko aka zauna Rakeeba na fadin"ke dai Gwoggo da son hira da yaran nan kike",,dariya ta sanya sannan tace"Banda abun yaya in ba mu zanta da su ba waye za su sanar wa damuwar su,a haka ne ko bayan babu ni,in sun ga daidai wannan lokaci za su ce Allah sarki da Gwoggo na nan da yanzu ana nan ana shan hira",dariya Usmanu yayi sanann yace "in sha Allahu duk ba yanzu za ku tafi ba sai mun gina muku katon gida da mota,kun je Hajji",,,"hmmm Usmanu ke nan to ubangiji ya amsa,Ni dai duk basu bane gaba na wlhy bani da burin da ya wuce in ga Abul Baiti na ya auri kyakkyawar mata,sun haifo mana kyawawan yara",dariya Rilwanu ya sanya sannan yace"soon Gwoggo ta burin ki zai cika"da haka suka yi ta hira,har sai guraren gomar dare sannan aka fara watse wa don zuwa bacci,Usmanu ya ja matar shi suka yi gaba,dake Mal Audu dakin Rakeeba yake sai abun ya zo wa Rilwanu da sauki,Alola Rakeeba tayi sanann ta yi wa Gwoggo sallama kan sai zuwa Asuba kuma,fuska cike da murmushi Gwoggon tace "to yaya a yafe mu Ni da 'da na,na san mun bata miki rai fushin uwa ko bata furta ba bayi da dadi akan yaro",kai Rakeebar ta girgiza domin wanann yana daya daga cikin halayen Gwoggo bata taɓa bacci bata nemi yafiyar ta ba,in ko rilwanu na gida harda shi take haɗawa ta nema wa yafiyar"Gwoggon Abul bait ke nan,na yafe ku ubangiji ya yafe mu baki daya asuba ta gari"da haka ta wuce dakin ta tare da kullewa,itama Gwoggon mikewa tai tare da shigewa dakin nata,


Wannan daran sam Rilwanu be rintsa ba ya kai ya kawo haka yayi ta yi cikin dakin,da zai nutsu da kyau ya saurari maganar da ƙasar zuciyar shi ke mishi to a take zai tuba ya koma ga Allah,Amman ina idanun shi sun rufe baya ji baya gani, burin shi be wuce ya ga wannan ruwan kudin da ya ji Kabiru na magana akan su ba,a haka lokaci yayi ta tafiya gidan yayi shiru,baka Jin karar komai sai yan kananun kukan su Mage,a haka ya zauna shi kadai kamar tsohon maye,har karfe Dayan dare yayi,murna fal cikin shi ya bude jakar da ya dawo da shi tare da dauko kyallen,karfe 1:20 ya fito cikin sanda,ya leka ko ina Amman ya ji tsit alamun kowa bacci yake,da yayi tunanin Hajiya za ta iya tashi a daidai time in nan coz ba wani bacci take na dare ba at times takan tashi sallan dare tun 1 ko wataran 2 ko 3 duk lokutan tashi ta ne,ya sanya Saida ya leka dakin nata,amman baccin ta take sha cikin kwanciyar hankali irin bacci me nauyin nan,cikin sanda ya rufe kofar tare da nufan dakin Gwoggo zuciyar shi sai bugawa take yi,yana bude wa kuwa ya hango ta kwance akan gadon ta tana bacci peacefully,a hankali ya shiga tare da datse kofar Allah ma ya taimake shi babu wuta so dakin duhu,murna fal cikin shi zai yi ya gama ba tare da ta san shi bane,banda ya zamo dole ya na son yin kudin nan da ya hakura ai, a sidaɗe ya samu ya shiga cire tufafin jikin shi,cikin kankanin lokaci ya kwaɓe kayan jikin shi tas,sannan ya haura kan gadon nata this is the very First time da zai sadu da mace ke nan a rayuwar shi so yana ta jin wani iri,


Haka dai ya samu ya daure cikin sanɗan ya dalle kan gadon,tare da nufan inda Gwoggo ke kwance,yana me yakice duk wani tausayi ko fargaban da ke cikin zuciyar shi,cikin zafin Nama kuwa ya nufi in da Gwoggo ke kwance zuciyar shi na ingiza shi kan cewa ai yayi ya gama kawai tunda Allah ya taimake shi ma babu wuta,cike da wayo da dabara irin ta 'da na miji me mugun nufi ya samu ya kunce zanin Gwoggo tare da haurawa ruwan cikin ta,sam ji da ganin shi sun dauke,burin shi be wuce ya kusance ta ba,ya sanya ma be da wani ra'ayin tube ta har ya tsaya shafa ta,gwara kawai a buga one time a kwashe a ganin shi hakan zai fi mutunci,


A hanzarce ya ware kafafun ta wanda yayi daidai da farkawar Gwoggon jin nauyi a kan kirjin ta tare da jin bakon lamari tattare da ita,to me ya shigo da malam dakin ta shine tambayar da ta fara zuwa ranta,in ko shine,yau ai kwanar Rakeeba ce,bata gama wanann tunanin ba,ta ji wani dogo kakkauran abu na kokarin ratsa mata cinyoyi,firgici ne ta kama ta jin tabbas wannan ba abun mijin ta bane,a daidai wanann lokacin Nepa suka kawo wuta,sai ga Gwoggo tai mugun gani,arba da tayi da Rilwanu a kanta zindir haihuwar uwar shi idanun shi rufe yana neman hanyar da zai huda ta,wani irin tsoro ne ya kamata don mancewa tai bata kashe wutar dakin ba ashe,bakin ta har bari yake gurin fadin"na shiga uku Ni Zaliha Rilwanu kana hauka ne me zan gani haka?ko dai ka fara shaye shaye ne ta kare tare da hanɓare shi da iya karfin ta wanda Saida ya sanya shi yin kasa,da sauri ta dauki zanin ta tare da kokarin daurawa,fadi take "yau mun shiga uku,kai Abul bait ko dai jifar ka aka yi ne,za ka shigo daki na kana neman danne ni mugun ji mugun gani Allah tsare mu zo ka fice tun ban saɓa maka ba,ya sanya Yaya kullum take kukan ku rike Azkars in nan Amman ina san jiki tayi muku yawa,duniyar yanzu cike da take da shedanu da mugayen mutane ta kare tana me kokarin daura Zanin ta,har ga Allah dauka tayi ko jifan shi aka yi ko tabuwar brain ya samu,


A maimakon ya fice in kamar yanda tace da shi,sai dawowa yayi yana ne kokarin riko ta,hakan ya sanya cikin zafin rai ta wanke shi da wata irin gigitattciyar mari har sau uku,"kai Rilwanu dan uban ka Ni ba uwar ka bace da kake neman laluba ta,ka wuce ka bar mun daki tun ban yi ma ihun kwarto ba,ashe daman dan iska ne kai mara mutunci ban sani ba,Amman wlhy anyi asarar haihuwar ka duniya zata yi wadai da kai wlhh",be bari ta rufe baki ba ya sure ta tare da watsa ta kan gado wanda sakamakon hakan ta buge kanta da karfen gadon,take ta dan tsala kara,da sauri ya sanya hannu tare da rufe mata baki,nan ko ya kunce zanin tare da ware mata kafafu ya dalle kanta,babu wata wata ya afka mata,cikin zafin Nama ya shiga saduwa da ita,banda hawaye babu abinda ke fita daga idanun Gwoggo domin ya rufe mata baki babu halin ihu,kuka take na zuci da na fili babu abunda take fata da ya wuce Allah ya dauki rayuwar ta,wannan abinda ke faruwa da ita gani take kamar a mafarki,irin mugun mafarkin nan,Rilwanu yaron da ta kaunata ta raina ta wanke ta goya ta bashi abinci a baki,ta so shi fiye da yaran cikin ta,a rayuwa bata da tadi sai na shi,bata da burin da ya wuce ta ga ya samu ingantacciyar rayuwa da daukaka,daman an fadi duk abinda ka so ka kauna ta to in sha Allahu shi yake zama sanadin mutuwar ka,ko shiga kunci da damuwar ka,har yanzu ta gaza yarda wai Rilwanu ne yau ya tube,ya kwaɓe ta yake saduwa da ita,ji take numfashin ta na sama sama,wanda ko a jikin shi Saduwa yake da ita babu tausayi balle imani a tattare da shi,Saida ya dauki good one and the half hours in da Odugwu ya Fadi sanann ya sauka a kanta duk ya gama hade zufa,ƙafafuwan shi ne suka hau rawa,nan dai ya daure ya mike,yana hawaye ya durkasa a gaban ta"ki yafe Ni Gwoggo wlhh ba wai don rashin kauna bane ya sanya Ni yi Miki haka,hakan ne kawai zai zamo silan arziki na,Saida nace Banda ke bazan iya ba Amman suka nace akan tunda ina kaunar ki sai na bada ke,ina da burin yin kudi Gwoggo na so in yi kudi in kula da ke amman taki kaddarar haka ta zo,saidai na miki alkawarin zan kula Miki da su yan biyu zan zame musu uba,duk dadin da nayi niyar shayar da ke zan bai musu,da fatan za ki yafe mun",,,,,gaba daya ji tayi ta kasa motsi da ko da hannun ta ne, domin a yanda take jin ta da zata iya da ta mike ta shake wuyar dan iska kowa ya huta,da ta kashe shi ko da kuwa itama za a kashe ta,lalle Rilwanu ya cika butulu ke nan tsafi yayi da ita,yo Allah ta tuba ko da wahayi aka yi mata daga sama kan Rilwanu zai mata haka za ta iya ce wa karya ne,da kyar ta samu ta daga yatsar ta manunniya,tare da nuna shi,cikin muryan jin jiki tace"Allah Ubangijina ya tsine maka Rilwanu, Ubangiji ya hana ka kwanciyar hankali da nutsuwar duniya da kiyama, tana kuka me taba zuciya tace na bar ka da Allah na da sannu shi zai mun sakaiya,in sha Allah za ka ga yanda duniyar da ka zaba ka barar da lahiran ka za ta yi da kai",ta kare tana kuka lalle ta yarda da aka ce uwa Bara ta taɓa cin naman 'dan ta ba amma kuma 'da zai ci na uwar shi,tayi nadamar kaunar da ta nuna mishi har take hana Rakeeba bashi tarbiyyar da ta dace,tana cikin wanann tunanin ne ta ji ya goga mata abu a gaban nata da ke mata tsantsan radadi,nan take kuwa taji abu kamar ya shige mata ya fita sai ta ji wani sanyi,a take jikin ta ya hau karkarwa ta hau bari na wasu yan mintuna,numfashin ta ya hau barazanar dauke Wa sai bakin ta dake bude,Rilwanu yana nan tsaye a kanta har sanda ubangiji ya dauki kayan shi ta daina motsi,wata irin zufa ce ta karyo mishi ya kasa yarda yau shi ya aikata haka,yayi mintuna yana nan tsaye kamar sanda tsoro da firgici ne fal ranshi,kafin ya tattaro nutsuwa shi,cikin sanda da sauri ya nemo ruwa da tsuma ya wanke mata gaban nata tas sannan ya maida mata kayan ta,shima ya maida nashi,cike da tsoro don ji yake kamar za ta iya tashi ta kamo shi,cikin sauri ya tattare dakin tare da kwantar da ita kamar yanda ya shigo ya same ta,a sidaɗe ya fice daga dakin bayan ya gyara komai inda babu wanda zai zarge shi,dakin shi ya koma zuciyar shi na bugawa da sauri da sauri,ganin be ga ruwan kudin da Kabiru ke bashi labari bane abun ya so tsorata shi,kardai sola shi suka yi sun sanya ya sadu da kishiyar mahaifiyar shi a banza,da wanann sake saken ya fada kan gado duk cinyoyin shi ciwo suke yi masa, yanda za ku san Rilwanu tantirin dan iska ne,bacci ne me dadi cike da mafarkin yayi kudi suka tafi da shi,


Hayaniyar kuka da ife ifen da yake jiyowa ne ya farkar da shi daga baccin shi,cikin sauri ya fito,ai ko arba yayi da duk yan gidan wasu a dakin Gwoggo wasu a bakin kofa,cike da jarumta ya karasa tare da tambayar ummi "lafiya mike faruwa??,,,cikin kuka ta fada jikin shi tare da fadin"Yaya Abul Gwoggo ce Allah yayi wa rasuwa cikin dare",wani irin ihu Rilwanu ya sanya tare da zube wa a nan kasa babu numfashi,ba sai kuka ya koma biyu ba tuni aka yi kanshi aka kwashe shi sai daki,aka yayyafa mishi ruwa Amman be dawo hayyacin shi ba,hakan ya sanya Usmanu daukan shi tare da kai shi asibiti mafi kusa da su,inda Rakeeba da kanta tai wa Gwoggo wankan gawa tana kuka,domin in tace bata ji mutuwar ba tai karya ,mata me mutunci da sanin ya kamata,hakuri kawaici,don zaman su sam bara ka ce zaman kishiyoyi suke ba,tare da taimakon makotan da suka shigo aka gama gyara Gwoggo aka fito da ita,Mal Audu kanshi Saida yayi kuka,Amman ya za su yi Allah yayi lokacin ta yayi,yaran ta suna ji suna gani aka wuce da ita gidan ta na gaskiya,ta samu kyakkyawar shedan mutane kuwa(ubangiji ya sa muyi kyakkyawar karshe,Allah ka bamu ikon cikawa da imani in mun zo komawa a gare ka ubangiji ka bamu mutuwa me sauki),


Nan ko aka fara shigowa karban gaisuwa duk wnada ya zo ya fice bakin shi dauke da kyakkyawar shedan Gwoggo domin mata ce da bata da mugunta ko hassada,Rakeeba tayi kuka har ta gode wa Allah fadi take"babu ciwo ba komai cikin dare ace zuciyar mutum ya buga,me ya samu Zuwaira  har da zuciyar ta za ta buga,jiyan nan muga gama yi zata kwanta tace na yafe su ita 'dan nata,ashe bankwana take mana, ubangiji ya Miki rahma Gwoggon Allah jikan mu baki daya halayan ki na gari su biki,nan aka yi ta lallasan ta har zuwa yamma,ba karamin tausayi yaran suka bata ba,domin shakuwar da suka yi da Gwoggo basu yi da ita ba don ita ba ta cika jan yara a jiki ba,ba ma kamar Abul bait da ba a sallamo shi ba sai zuwa dare,haka dai suka sanya shi gaba da nasiha da rarrashi aka samu ya ci abinci yayi wanka sannan Rakeeba tace ya je ya kwanta ya samu ya huta,nan ko ya shiga dakin shi ya rufe,juyowar da zai yi kawai sai ya ga abun mamaki abunda before ya dauka tatsuniya ce,ruwan kudi farare yan dubu dubu yake gani suna zubowa daga rufin kwanon Shi from now where,cike da mamaki tsoro da jin dadi be san sanda ya saki ihu tare da daka tsalle "wayyo Allah na shiga uku na",jin ihun da yayi ne ya razana Mal da Rakeeba suka yi saurin fitowa suka nufo dakin nashi,cikin zafin nama Mal Audu ya fara buga kofar yana fadin "kai Abul bait lafiya me ke damun ka??shirun da suka ji ne ya sanya Rakeeba cewa"ba magana ake maka ba,ka bude kofar nan mana",cikin sanyin jiki Rilwanu ya bude kofar suna kokarin kutsawa cikin dakin yayi wuf ya fito tare da kulle kofar gam,da idanu Rakeeba ta tsare shi,tana jefan shi da kallon tuhuma"kai Abul bait lafiyar Ka kuwa??kake tsala ihu cikin dare haka?,Mal Audu ya tambaye shi,,,"Baba wlhy da na shiga dakin ne idanu na ke mun gizo sai na ke ganin kamar Gwoggo tana mun murmushin tan nan,ya kare kamar zai yi kuka,


Kai Rakeeba ta girgiza sannan tace "Gwoggo kam ta tafi inda duk muke sa ran tafiya saidai mu bita da addu'a,a kullum ina fada maka ka rike Azkars amman ina,shedanu ke neman maka wasa da hankali ka taba ganin wanda ya mutu ya dawo"??,da sauri yace "a'a ",,,"to kai Musulmi ne dole ka yarda da ƙaddara me kyau ko mara kyau,na san da zafi kam,shakuwa ake wa kuka ba mutuwar ba,Amman ba yanda muka iya babu abunda ta fi buƙata irin addu'a,maza ka zo kayi alola ka yi sallah ka roka mata Rahman Allah,zan aiko Babana ya taya ka kwana tunda na ga alamun a tsorace kake,malam mu je ko",,,,suka juya don komawa dakin su,da sauri Rilwanu yace "Hajiya ba sai kin kirawo Hydar in ba Zan iya kwana Ni kadai in nayi adduan da kika ce",bata kawo komai a ranta ba suka shige daki don kwantawa bacci,da sauri Rilwanu ya koma dakin gani yake kamar zai shiga ya ga babu kudaden shi,abunda ya kuma neman tsorata shi har yanzu kudin na zuba basu gama ba,tsalle ya daga cikin kasa da murya yace"wayyo duniya kudi masu gidan rana,barkan ku da shigowa hannu na, Odogwu You Are the best kayi mun abinda Allah na ma ya kasa mun(wa'iyazu billah,at times kun san out of excitement mutum na iya fadan abunda zai kai shi wuta,haka ma out of anger, ubangiji ya bamu ikon kiyaye halcen mu),


Nan ya shiga tsalle yana fadi cikin kudin ya dauki wannan ya shinshina ya rungumo su,kafin can ya mike ya nemo katon Ghana must go,da katon jaka ya shiga tattare kudaden zuciyar shi kal cikin farinciki,yo da ya san da wanann hanyar wlhy da tun randa ya mallaki hankalin shi ya mika Gwoggo aka bashi wannan tulin dukiyar,wannan daran be iya bacci ba domin gani yake kamar in ya kwanta ya tashi zai ga babu kudaden shi,


Bayan kwana biyu da rasuwar Gwoggon ne,ya fita ya dawo ya samu Hajiya tsaye da Usmanu da Ghana must go in kudin Shi a gaban su,nan take zuciyar shi ta buga,amamn yayi saurin dake wa tare da karasowa"sannu da gida Hajiya an wuni lafiya"??,


     "Abul bait!Abul bait!,wai so kake ka kashe Ni a duniyar nan ne ko me,me kake son zama ne Ni kam me yasa sam baka jin magana ta ne,tsakani da Allah kana son gama wa da duniya lafiya kuwa"??,cikin rawar baki yace "Hajiya me kuma aka ce miki nayi",ya kare yana gallawa Usmanu kallon banza,


"Abul bait wannan makudan dukiyar ta wacece??,ta kare tana me tsare shi da idanu, wani yaaar yake ji a jikin shi yanda ta kafe shi da idanun ta,"ba magana nake ba kayi mun shiru ka amsa Ni tun ban ci ma mutunci ba",cike da dakiyar zuciya yace "Hajiya kudadan ajiya ce Abokina Kabiru ya bani su saboda ya yarda da Ni,kudi ne wanda gwamnati ta bashi don gina wata katafaran Company na supplying crude oil wa kananun ƙauyukan yankin Bauchi,to shine yace da Ni yan fashi sun sanya shi gaba kan na zo da shi na aje mishi,na so kawo Miki ki aje mun sai nayi tunanin kuma kar ranki ya ɓaci na karbi abu ba da sanin ki ba",sam wannan maganar be shige ta ba amman ta kasa sanin a taya ta yarda da zancan tashi"Ni dai ina Dada gaya muku kullum ku ji tsoron Allah wlhh ku rike kan ku da talaucin ku,abinda hakuri be baku ba rashin shi ba bayar wa zai yi ba,kar ka je ka dauko mun magana Abul bait,gobe gobe ka dauki kudin mutumin nan ka maida mishi,kai ko tsoron wani abu ya same su baka ji ba,kudin da tunda uwa ta ta haifo Ni ban taba ganin me yawo irin su ba,gaskia hankali na be kwanta da su ba",nan dai ya lallaba ta da dadin baki da ban hakuri har ta huce,yayi alƙawarin gobe gobe zai kwashi kudin ya maida masa,ranshi a matukar bace ya shige daki,lalle ya zama dole in yana son cin kudin shi a hankali to ya kau da Usmanu daga rayuwar shi,don ya ga alamun dan sa ido ne,


Haka kuwa aka yi, washe gari sassafe ya dauki hanyar Bauchi,kwana uku suka yi da Kabiru inda yace ya taya shi boye mishi kudaden shi,be bar gidan Kabirun na Saida suka je aka yi cinikin wata madaidaiciyar gida ya siya ya biya sannan ya dawo Azare,


Haka rayuwa ta cigaba da tafiya,cikin taku da wayo Rilwanu yake cin kudaden shi inda babu wanda ya sani,cike da dabara Kabiru ke gogar da shi yana kuma koya mishi Siyan kadarori da kayan more rayuwa,a hankali ya goge idanun shi suka fara budewa, zuwa meeting in su na biyu  Odogwu yace Rilwanu ya baida jinin daya daga cikin kannan shi a take kuwa ba tare da yayi tunanin ba yace ya bada jinin Usmanu,a wannan ranar Rilwanu ya fara shan jinin mutum,ya kuma ci Nama mutum danye ba tare da ya ji wani abu ba,suka gama suka juyo washe gari,ko da suka dawo Saida ya kara kwana gidan Kabiru domin a matukar gajiye yake akan sai jibi ya koma gida, sassafe kuwa Rakeeba ta kira shi take sheda mishi kan cewa "Usmanu sun yi hatsari a hanyar su ta dawowa daga Bulkachuwa(dake matar ta shi yar can ne),Allah ya karbi ran Humaira da yaran ta,,,"Hajiya ina shi Usmanun ko shima ya tafin ne??,,,"A'a gashi nan muna asibiti har yanzu likitoci ne akan shi,be farfaɗo ba,salati Rilwanu ya sanya sannan ya ce ga shi nan tahowa ,haka kuwa ba bata lokaci ya shirya yayi wa Kabiru sallama kan zai tafi Azare,nan Kabirun yace ya jira su je tare,basu bata lokaci ba kuwa suka iso,dake motar gida ne,a lokacin har an kai Humaira da yaran ta,nan ko Kabiru suka shiga barin kudi a gurin makoki,har abun ya so tsorata mutane to a yaushe ne har suka yi irin wannan mugun kudin,


Kwana Usmanu bakwai a  asibiti jikin na shi ya ɗan yi kyau suka nemi a sallamo shi gida,domin an kasa gane kan ciwon nashi,daga kwankwason shi zuwa tafin ƙafan shi sam sun daina motsi,Rakeeba tai kuka har ta gode wa Allah,yan uwan ta da yaran ta ne suka yi ta kwantar mata da hankali,a haka rayuwa ta cigaba da tafiya cikin sauri,har yanzu babu cigaba a jikin Usman in,ala dole kasuwancin shi ya tsaya cak domin yaran shagon ganin babu shi,ya sanya kowa ke abinda ya ke so,haka suka sanya kudin a gaba duk ya lalace,Usman yayi kuka har ya gode wa Allah saidai ya bar wa Allah komai,daga kokarin kwace wa Bakar Akuya suka yi hatsari,hatsarin da yayi sanadiyar mutuwar Masoyiyar shi abun kaunar shi,


Haka rayuwa tayi ta tafiya Rilwanu yana murza duniya don a halin yanzu ma sanar wa Kabiru yayi ya fara jin sha'awar fara siyasa,nan yace da shi ya bari sai karshen wata in sun je meeting ya sanar wa Odogwu,haka kuwa aka yi,suna zuwa kuwa bayan an gama komai Rilwanu ya gabatar da kudirin shi,nan ko Odogwu yace da shi muddun ya baida jinin Mahifinshi to ya sanya a ranshi takarar Reps in da za a yi na bana shi ke da nasara, without any second doubt yace ya bada,domin a daidai lokacin ji yake ko duka dangin shi aka ce zai bada bayi da wani matsala,ya riga da yayi nisa baya jin kira sam babu tsoron Allah a cikin ranshi,baya iya tuna when last ya sanya goshin shi a kasa da sunan sallah,haka ko aka yi suna dawowa ya dawo gida washe gari da yamma aka kawo Gawar Mal Audu wai an tsince shi a gefen titi baya numfashi,a take Rakeeba ta yanki jiki ta fadi sumammiya,cike da tashin hankali yaran suka nufo ta suna kuka,me cike da bakin cikin rasa mahaifin su da kuma tsoron rasa Mahaifiyar su...



Ayi mun afuwa wlhy keyboard ina ke bani matsala ya sanya ban yi typing jiya ba,



Bare with the typing errors pls,coz ban samu time in editing ba,



In sha Allah sai in Allah ya kaimu Friday,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


            💖

                  THE TALENT TROUPE WRITERS💖💖

........



https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


...........

          Page forty 


**********



   Iya kan tashin hankalin da su Ummi suka shiga a daidai wannan lokacin baki bazai iya furta shi ba,mancewa suka yi da Gawar Mal Audu dake kwance,duk sun dukufa akan mahaifiyar su,suna kuka,banda Aliyu da ya ja ya tsaya a jikin bango inda yake sauke numfashi da kyar da kyar,domin duk cikin yaran babu wanda Rakeeba ke so kuma ta ja a jiki kamar shi,ya sanya yake tsananin kaunar ta,babu wanda ya lura da halin da yake ciki balle ayi tunanin taimaka mishi, banda kuka da ihu babu abunda suke yi, Rilwanu ne yayi karfin hali tare da fita ya tsaro abun hawa don a samu a kai Hajiya asibiti a duba lafiyar ta,nan ya dauke ta cak tare da sanya ta cikin  adaidaita yana me raya wa a zuciyar shi lokaci yayi da ya  kamata ya sai motar hawa na kanshi,ko dan guje wa irin wannan ranar, bayan ya aje ta ne ya shigo,ya samu har Ummi da su yan biyu sun shirya,nan ya Ciro kudi masu yawa ya mika wa Ummin,wanda da hankalin ta a jikin ta yake sai tsoro da mamaki sun kama ta kan a ina Yayan nasu ya samu kudi har haka,"yi maza ku fita ummi bari na kirawo Aliyu ya zo ku je tare ",ya kare tare da juyawa inda ya samu Aliyu tsaye idanun shi sun kafe a sama guri daya,


"Kai Hydar lafiyar Ka kuwa?,ka ja ka tsaya jikin bango tun dazu,yi maza ka bi bayan yaran nan ku kai Hajiya Asibiti in ya so Ni zan kira,Mal kallamu su taya Ni shirya Mal",ya kare yana kokarin juyawa,jin shiru Hydar in be motsa ba,kuma be amsa ba ya sanya shi juyo wa,tare da sanya hannu yana me taba kafadan shi"kai Hydar kalan ka kuwa",me zai gani sai ganin Hydar yayi,ya zube a kasa,babu alamun numfashi a tattare da shi,idanu ya zaro cikin mugun tashin hankali yace Na shiga uku yau me na aikata haka(duk cikin yan uwan shi ya fi kaunar Hydar in),da sauri ya nemo ruwa tare da yayyafa mishi,Amman ina a banza babu alamun rai tattare da shi,cike da tashin hankali ya fice daga cikin gidan,duk wanda ya ganshi ya san ba kalau ba,gidan Mal Kallamu ya nufa(Aminin Mal Audu ne),ba tare da sallama ba ya shiga a kofar suka ci karo da Mal kallamu in,Yana kokarin fita shi kuma na kokarin shiga,taro shi yayi tare da fadin"kai Abul bait lafiya kuwa",,cike da tashin hankali yace Mal,Baba na ne aka shigo da shi Allah ya masa rasuwa,hakan ya sanya Hajiya zube wa babu numfashi su Ummi sun tafi Kaita asibiti,to yanzu kuma Hydar gashi can kwance kasa baya numfashi ya kare jikin shi na kyarma,,,,"salati Mal kallamu ya sanya domin dazun nan rabuwar shi da Mal Audun dai bayan sun gama hira yake ce mishi ya kama ta yayi wa Rilwanu magana ya fito da matar aure,shekarun shi suna ta tafiya,Mal Ke sanar da shi in sha Allah zai sanar masa,ashe maganar su ta karshe ke nan,nan ya janyo Rilwanu suka dawo gidan su,inda ya nufi kan Aliyu take ya gano shock ce ta kama shi wanda ya sanya masa bugawar zuciya a nan take Allah ya karbi rayuwar shi,a haka aka yi musu wanka aka musu sallah aka je aka kai su makwancin su na gaskiya (ubangiji ya sa mu cika da imani),Usmanu na daki banda kuka babu abunda yake yi,babu halin fitowa ya kalli fuskan mahaifin shi da kannin shi na karshe,tabbas zuciyar shi na raya mishi wani abu game da Yayan nashi,saidai wai an ce zargi haramun bayi da wata hujja me karfi,a haka ya yi niyar alola,tare da yin niyar sallah ya dade yana roka wa Mahaifin su, Gwoggo da kuma Aliyu samun rahamar ubangiji tun da be samu an kai su da shi ba,


Ba Hajiya ta samu ta farka ba sai guraren bayan Isha,Matar Mal kallamu ta gani zaune da su Ummi idanun su duk sun kumbura alamun sun ci kuka sun goshi,nan take suka hau mata sannu,cikin karfin hali tace "Aliya har an kai Mal in ne"?,,"Eh wlhh Rakeeba Mal da Aliyu kam ashe lokaci yayi ubangiji dai ya musu rahama ya kuma kara muku hakurin rashi,amman a yan tsakanin nan kun ga jarabawa"(Aliya irin matan nan ne masu shegen bakin tsiya),


Wani irin dummm zuciyar Rakeeba yayi mata nauyi lokaci daya,a zabure ta mike don firgici har ta mance da karin ruwan da ake mata,da sauri Rilwanu ya zo ya taro ta tare da rungume ta,cikin wani irin tsoro tace "Abul baiti ka ji abinda Aliya ke fadi,wai Baba na,wai ya hakurin mu,sanar da ita Mal ne kawai ya rasu amman Aliyu na yana raye,ina shike ne ma ban gan shi ba",ta shiga leke leke,cikin zubda hawaye yace "Hajiya gaskia ne,faduwar da kika yi,da mutuwar Baba ya sanya Aliyu kasa jurewa har Saida ya hadiye zuciyar shi,Aliyun mu ya tafi tare aka musu sallah da mal aka kai su ya kare yana hawaye,wani irin kuka Rakeeba ta fashe da shi me cike da ban tausayi tana nan rungume a kirjin shi,shima yana taya ta,domin ba karya in yace be ji mutuwar yaron ba yayi karya,nan su Ummi suka zagaye su aka sha kuka kamar ba gobe,Saida Doc ya shigo ya hau Rilwanu da fada kan akan me yasa ake kara mata damuwa bayan jinin ta ya riga yayi sama sosai,so suke zuciyar ta ta buga,nan duk ya samu ya kora su,tare da yi mata aluran bacci,gida Rilwanu ya ce su koma shi zai kwana da Hajiyar,da haka suka rabu zuciyoyin su babu dadi, 


Haka rayuwa ta cigaba da tafiya,duniya tana yi wa Rilwanu yanda yake so,don shi ke jan ragamar gidan nasu yanzu,ya karbi responsibilities in komai,kamar yanda Rakeebar ke son gani,haka ya shiga ci da su da haram ya shayar da su da haram ya tufatar da su da haram,kudin makarantar yaran komai shi yake yi,inda ta sanar wa Hajiya kan cewa yana sha'awar fadawa siyasa,at first ta hana shi Amman ganin yanda ya nace ne ya sanya babu yanda ta iya ta yarda ya fada siyasan,inda ya shiga da kafar dama,don mutane har mamakin irin kauna da farin jini da ya samu ake,dake Rilwanu mutum ne shi me kyauta hakan ne ya batar da tunanin mutane akan zargin shi,aka dauka sabida kyautan shi ne ya sanya ake kaunar shi,abun ku da kudin banza ke gare shi ya sanya suka tafi da Kabiru Unguwar GRA nan ko ya sayi wata tamfatsetsen fili,ya zuba miliyoyin kudade akan a tada mishi gini,


Haka aka cigaba da tafiya har lokacin zabe ya zo,inda babu wanda ya taba kawo wa Rilwanu nasara kasancewar shi bakon fuska,a nan take kuwa ya lashe takarar kujerar Reps da aka yi,wannan lokacin ne suka hadu da Alh Salisu wanda ya kasance mutum me dattaku nutsuwa mutunci,da kuma tsoron Allah,dan siyasar ce shima,ganin yanda Rilwanu ke ambaton Allah a baki ne ya sanya babu wanda ke mishi zaton banza,akwai mutanan da har qurani za su iya dafa wa su rantse da Allah kan cewa Rilwanu ba makawa dan Aljanna ne,a nan suka kulla abota me mugun karfi a tsakanin su ukun,duk inda ka ga daya sai ka ga dayan,lokacin duk suna da mata shine kawai bayi da mata,bayan an ci zabe ne kuwa duk suka biya wa wa kan su da family zuwa aikin hajji,a fadin Kabiru wai su dan je su rage zunubai,


Hajiya Rakeeba,tunda ta je dakin Allah bata da addu'ar da ta wuce Allah yayi gafara wa mijin ta,kishiyar ta,surukar ta,jikokin ta,da kuma yaron ta Aliyu,sannan Allah ya fito wa Rilwanu da mata na gari ya samu yayi aure shima,Allah kuma ya kara mishi budi a cikin arzikin shi,sanan kuma Allah ya baiwa Usmanun ta lafiya,da sauran al'ummar musulmai baki dayaaddu'ar da tayi ta yi ke nan har suka je suka dawo,Rakeeba dai hankalin ta sam ya gaza kwanciya da irin wanann mugun kudi da rilwanu yayi na lokaci daya haka,saidai sam bata da damar tambayar shi,don a duk sanda tayi yunkuri zai ce mata aikin mai yake,ta tambaya ta ji yanda yake kawo kudi,sannan kuma ga siyasa ya fada da kafar dama(kamar ya sani daman ya sanya Odogwu rufe mata baki),mutanan gari musamman yan Azaren har yau mamaki suke yanda Abul bait yayi kudi haka,anya ba yankan kai ya fara ba kuwa,nan kuwa aka hau rade rade,ganin haka ya sanya shi ware wasu kudi masu nauyi yace a raba wa duk yan unguwar tasu da ma unguwanni kusa,a cewar shi yanda ya ci takarar nan yankin shi sai sun fi kowa jin dadi,su kayan sawa,kayan abinci duk haka aka rabar wa mutane,kun san mutanan mu da son abun duniya a take magana ta mutu,aka koma yabo da sanya mishi albarka,babu yanda be yi da Hajiya kam ta yarda ya dauke ta su koma can Bauchi tunda yanzu babu amfanin zaman ta a Azaren,Amman tace Sam bata san zance ba tafin son ta mutu a gidan da mijin ta ya gina,da gumin halak in Shi,ganin haka ne ya sanya aka rushe gidan tare da tsantsara musu sabon ginin zamani me masifar kyau,don shi a son shi ma ya canza musu unguwar ce su koma GRA amman Hajiya ta ki yarda,su Ummi kuwa makarantar jami'a ta kudi ya sanya su,inda sabida munafurci har kasar waje ya fita da Usmanu don a duba lafiyar shi,inda binciken duniyar nan yi ance babu komai,a nan Aliya wanda ta maida gidan gurin zuwa ta ke cewa Hajiya anya ba jifan shi aka yi ba kuwa,a take Rakeeba tace"Ni ban yarda da wanann abubuwan ba jarabawa ce daga gurin Allah,me Usman yake da shi da har wani zai jefe shi,ke dai jinya dai daga gurin Allah muna nan muna addu'a Allah zai yaye,amman Ni kam Aliya kin gan Ni nan bana zargi domin haramun ce,and in mutanan mu ba su ji tsoron Allah sun mika lamuran su gare shi ba suna cike da tashin hankali,abu ba abu ba kace an jefe ka shike nan Allah ba zai jarrabi bawan shi ba har sai ya zamo jifan shi wani yayi?Ni dai babu wanda ya jefe mun yaro kuma in sha Allah zai warke,nan tayi ta baiwa Rakeebar hakuri saboda kar tayi faushi da ita,dan abun duniyar da take samu ta daina samun shi,kwana biyu da yin haka,kuwa ta kuma dawowa tare da bijirowa Hajiya akan why not su hada auran yaran su,wato dai Rilwanu ya auri yar gurin ta Nusaiba,Hajiya ta so cewa a'a Amman gudun Kar ta ce ko dan ta ga yaron ta yayi kudi take kyamar hada zuri'a da ita ya sanya ta cewa"bari Abul in ya dawo zan sanar mishi",,,nan take kuwa Aliya ta washe baki"Ai Hajiya Rakeeba da ma kin bani number in Shi ne kin ga sai na bata tunda tana da waya,yaran zamani a take za ki ga ta shawo kan shi an samu an yi abun nan",baki bude Rakeeba ke kallon ta,'oh duniya wato sai in har kana da shi ne ka zamo mutun,ai a da dake bayi da komai ga Nusaiba nan a zube a gida Amman bata taɓa yunkurin maganar hada su ba sai yanzu da aka ga ya zama mutun',


    "Kin yi shiru Hajiya",,, murmushi Rakeebar tayi sanann tace "ba komai Aliya bari dai in ya shigo in za muyi magana duk yanda muka yi za ki ji mu",,,,"to madallah ki samu ki mishi magana kam sabida kin ga zai zamo mun kara kulla zumuntan mu ne,kin ga in aka samu ya amince ma sai a hada auran tare da na su Ummi ai",Ita dai Hajiya da kai kawai ta amsa ta,tana mamakin hali irin na mutanan duniya,


Aliya kam tunda ta koma gida bata ga ta zama ba,gurin wani malamin zaure ta je,a cewar ta abun sai an hada da neman taimako,domin idanun ta sun rufe kirib babu abinda take hangowa sai tulin Naira da daulan da diyar ta za ta samo musu,bata damu da zargin kudin shi da ake yi a gari ba,damuwar ta dai shine ta mallaki ko da rabin abunda Rakeebar ta mallaka,ya sanya ta kudiri aniyar ko ana mutuwa ana dawowa Sai ta aura wa Rilwanu Nusaibar ta don ta samu ta dankwali arziki,bata bar gurin Malamin ba sai da ya haɗa ta da wata turare a kwalba,tare da kwalli,akan Nusaiban tayi amfani da su ranar da shi Rilwanun zai zo,a cikin kudaden da take samu gurin Rakeebar su tayi using ta biya Malamin kudin sadaka in ji su da fada lol,


Nan ko ta zo ta labartawa Nusaiba game da hadin da suke son yi musu ita da Rakeebar(yau ku  ji mun karfin hali irin na Aliya),a tashin farko Nusaibar ta ki aminta da maganar mahaifiyar nata,domin akwai wani lecture a nan College of Azare da take karatu wanda da shi suke zuba soyayya har da alkawarin Aure suka wa juna,ai nan Aliya ta dage tayi wa Nusaiban tas tare da cewa wai tana yi mata bakin ciki ne ashe,da lallabi,da dadin baki tare da nuna mata irin tulin daulan da za ta samo in ta aure shi ta samu ta shawo kan yarinyar nata,ba a bar gurin ba Saida ta hure mata kunne tas, basu kwanta ba Saida ta nuna mata tsaf yanda za ta yi amfani da taimakon da ta karbo gurin malamin zaure,inda ta ce mata maganin kariya ce,domin soyayya da irin su Rilwanu dole sai kin hada da kariya don daga gani ba a rasa mayyun mata da suke son su ba,(yan uwa na mata mu ji tsoron Allah mu raba kan mu da yawaita karban abubuwan taimakon nan,wasu maganin farin jini,bakar mallaka,kiranye, da sauran su,wai duk a me kike wa hakan?yar uwa kan na miji ne fa da yau ko gobe dole za ki mutu ki bar shi,ita kishiyar da kike gudu in har tana cikin ƙaddarar ki to wlhy ba mallaka ba ko a kwalba kika sanya shi sai ya auro ta,wlhy abun yana mutukar bani mamaki yanda aka ɗauki hanyar shirka yanzu a fake da wai taimako ne,taimako ya wuce ki je gurin Allahn ki Allahn me maganin da kukan ki,ki ga in be biya Miki bukatun ki ba,wai har akwai na mijin da ya kai ki shiga wuta sabida shi?yar uwa akwai na mijin da ya kai kiyi barin imanin ki saboda shi??,don girman Allah mu kara jin tsoron Allah sanann mu guji kananu da manyan shirka,domin 90 percent in abubuwan malaman yanzun nan duk asiri ce wlhy,Allah Ubangiji ya datar da mu,ya kare kuma ya tsare mana imanin mu,kar ya bamu daman cuta kuma kar ya bada ikon a cutar da mu),


Ko kafin Rilwanun ya zo gida,Aliya ta zo ya fi sau uku don jin ko ya Hajiya suka kare da Rilwanun,Saida Rakeebar ta nuna fushin ta kan sintirin Aliyar kafin ta nutsu ta zauna a gidan ta, 



  Ranar juma'a da yamma kuwa Rilwanu suka shigo Azare da Aminan shi (Salis da Kabiru),nan gidan su Rilwanun suka sauka,inda Hajiya ta ji dadin ganin su kuwa,nan aka kawo musu kayan ciye ciye da shaye shaye,bayan sun nutsu an dawo daga sallan magrib ne,Hajiya ta shigo mishi da maganar ya dace yanzu kam yayi aure,har tana zolayan shi kan cewa"bata san wani shashashan bane ya bar shi ya ci zaben Reps bayi da aure,a haka yake shugaban ci,kullum kara kiba kyau da girma kake Abul bait ya ci ace kayi mata ai ko",,,,"Wlhy Hajiya ko Ni kullum sai mun fada mishi,zuwa ta Umarah ka kar ki ga yanda nayi ta sanya shi a addu'a,duk cikin mu shine kawai be da iyali,Kabiru gashi nan har yana shirin yin ta biyu,Amman shi ya tsaya tsoron matan",,, murmushi Hajiyar tayi sannan tace ayya Kabiru na mance ban maka gaisuwa ba ashe kuma Nuwairah Allah ya mata rasuwa, ubangiji ya mata rahma ya sanya ta huta,ta kare cike da alhini domin Rilwanun ya kira ya sheda mata mutuwar yarinyar,duk da Àmeen suka amsa(Nuwairah ita ce 2nd born in Kabiru ita ce kuma yayi raping tare da kashe ta ba tare da sanin kowa ba,


A nan ne Rakeebar ta samu cike da hikima ta shigo mishi da batun Nusaiban why not ya aure ta,bugun farko ya nuna shi ina baya jin tayi mishi,nan dai su Kabiru da Salis suka yi ta sa baki,har aka shawo kanshi ya ce zai je ganin ta,wanann ranar ko haka ta buda turaren ta sanya kwallin ta fito,cikin motar shi ta shiga inda sai wani far fari take mishi da idanu, dariyar shi ya dinga dannewa domin she looks funny to him,wai a zaton ta wanann haukan da ta sanya shine zai jawo attention in Shi to her ne ko me?, bayan sun gama gaisawar ne yace da ita "zan tafi",,,cikin Turo baki tace"har za ka tafi",kai ya daga mata"To baka bani kudin zance ba",ta kare tana Turo baki,kai kawai ya girgiza domin ta ma yi saurin tambaya ne don dama can yana da niyar bata, nan ya sanya hannu a aljihu tare da ciro sabin yan dari biyar biyar,ya bata bunch biyu,cikin rawar jiki ta karba,tare da cewa "thank you",ta shige gida, Aliya ruwa ne kawai bata zuba ta sha a kasa ba tsaban murna,gani take kwallin da ta karbo ne yayi aiki,bata ci na zama ba dole ta koma a kara yi mata wata hadin me mugun zafi,,,,,,,,,haka dai suka cigaba da nema kudi kam me sunan kudi Rilwanu kashe musu yake,domin Nusaiban akwai ta da tsinannan roko da son abun duniya,Hajiya har faɗa take mishi kan yanda ya ke zubar da kudin shi,amman sai yayi murmushi yace"Hajiya ai akwai su ne,da da babu su ai bana yi,daman an ce duk bayan wani wuya dadi na nan zuwa",


A haka ba a dau lokaci ba aka sanya auran su tare da na su Ummi,kayan gida da duk wani abun da uba ya dace yayi wa yaran shi, Rilwanu shi ya dau wanann nauyin,yayi musu duk wani abun da ake wa Amarya hakan ma fa yar gatan Amarya,a can bangaren ma kayan lefe na gani na fada aka kai wa Nusaiban inda duk maman gani take taimakon malamin zaure ke aiki,a haka aka yi hidimar biki aka kare,nan aka wuce da Ummi Zaria,A'isha Kano,ita kuma Khadijah Adamawa aka kai ta,while Nusaiba Amarya kuma aka wuce da ita Bauchi,


Zaman auran Rilwanu da Nusaiba zama ne dai na yancin kai,domin baya ce mata yi bare ya hana ta,inda ita kuwa ta mike kafafu ta ringa jidan kudaden shi a boye tana kai wa mahaifiyar ta domin hudubar da tayi mata ke nan,yana sane da satar da take mishi Amman ko a fuska be nuna mata ya sani ba,a haka har suka shafe watan su biyu  da aure,a nan ne Odogwu ya kuma ce da shi a kwai bukatar ya kuma bada wani jinin muddun yana son ya kame kujerar shi ta Reps, without any thinking yace ya bada Nusaibar,domin ba karamin isar shi tayi da rigimar banza ba,iyayi jin kai da son karya duk halin ta ne,a mugun isa da wulakanta mutane wai ita ga ta tana auran me kudi,nan take Odogwu ya bashi wani cream akan yayi using in Shi 30 mints before having sex with her,da haka suka dauko hanyar dawowa,


"Aboki na kai da za ka bada Hajiya,yaushe yasuhe kayi aure da har zaka bada Nusaibar",,,,,idanu Rilwanu ya zaro sanann yace"kai Kabiru wlhy Hajiya ta ci uwa ta ta yaga leda,kasan addinin matar nan kuwa,in Banda asiri har Manzon Allah (Sallallahu alaihi Wasallama),ta kama kana tunanin za a iya rufe mata baki ne,ai da Odogwu bazai iya danne mun ita ba, ni fa gaskia na gaji da bada family members ina,don su fa nake son in Tara kudin,daga randa Aliyu ya mutu jiki na yayi mugun sanyi,kasan yanda nake kaunar sa kuwa??,amamn na rasa shi,Mal Audu da ya dace na jiyar da shi dadi shi da Gwoggo duk fa na bada su,haba Kabiru ai yanzu wlhy Bana kuma bada kowa a cikin su enough is enough lokacin jin dadin su ne yanzu",ya kare da iya kan gaskiyar sa,Kabiru dai be kuma cewa komai ba, haka suka dawo gida,ko da ya dawo ya ga kudaden shi da yawa babu amman sai yayi kamar be san ma ta iba ba,nan yayi ta jan  ta  da hira, cikin dare kuwa be bata time in Shi ba ya shafa cream in Shi,tare da kusantar ta,zafi da radadi kam ta ji shi,wanda ko a first night in su bata ji irin hakan ba, kwana uku da faruwar haka,ta fara bleeding at first dauka tayi period ne ya zo mata ba a normal time in Shi ba,Amman ganin ya wuce seven days sai zubar jini ya sanya ta sanar wa Rilwanu tana kuka kan su je asibiti a ga miye,kwantar mata da hankali ya shiga yi,yana ce mata ba wani abu bane ta kwantar da hankalin ta kila ma miscarriage ta samu,a haka suka shirya suka je asibiti,likita ya duba ta yace babu wani Barin da ta samu,ya bata dai a je ayi scanning,nan ma dai result normal ya fito,haka suka dawo gida tana kuka,kafin ku ce me Nusaiba ta fara ramewa don in ta fara zuban jini,har guda guda ke fitowa,sai jinin jikin ta ya kusa karewa kaf,kafin a Kaita asibiti a kara mata jini,haka suka yi ta jigilan asibiti,inda a karshe Kabiru yace da shi ya maida ta gida kawai,don wanann ba rayuwa za ta yi ba,haka kuwa ya dauke ta ya dawo da ita gida yana kuka,duk wanda ya ganshi sai ya tausaya masa,domin ita ke jinyar Amman ya fita shiga damuwa,nan Aliya da Rakeeba suka shiga kwantar mishi da hankali,akan cewa za ta warke fa,da kyar ya iya barin ta a gida bayan yayi musu shopping in kayan abinci,ya aje musu mil daya,yace zai tafi Saudiyya zai je roka mata Allah,(a ranshi fadi yake daman duk wanda ya sai kwando ya san zai zubda ruwa,kwadayi Mabudin wahala,kudaden shi da ta sata,sun yi amfani da shi gurin jinyar ta,gaba sun kara ganin me kudi su bashi auran yar su ba tare da dogon bincike ba), 


   Haka suka shiga neman magani idanu a rufe,anyi gwajin duniyar nan lafiyar mahaifa da komai na cikin ta kalau,basu san miye ke causing zubar jinin ba,a nan ne Aliya ta dage akan cewa wlhy ture aka yi wa diyar ta an ga ta auri me kudi,nan dai suka yi ta jigila,Rilwanu saidai ya kira yayi ta kuka yana tambayar jikin nata,inda Saida Rakeeba tayi mishi fada akan kukan na miye ne, addu'a ta fi buƙata fa,kudi kam sun kashe shi aje gurin malamin zauran nan yace jifa ce,in ka je gurin wani kuma yace a cikin kawayen ta ne daya ta mata asiri,a haka dai watan ta daya ta na wanann jinyar ta bi ta kare ta koma abun tausayi,tayi fari fat(ba dole ba kullum ana zuƙan jinin baiwar Allah),a haka dai wata safiyar talata Allah ya karbi Kayan sa,kuka kam Aliya da Rilwanu sun sha ta,da kyar da kyar aka samu yayi shiru,don duk wanda ya ganshi sai ya tausaya mishi inda idanun shi suka kankance suka yi ja,Aliya ta so kara bashi kanwar Nusaiban wanda har an sanya mata rana da wani,Rilwanun yace a'a ta Bar shi kawai yarinya ta auri wanda take so,ranta be so ba dai aka bar maganar(iyaye mata wlhy tallahi mu kara jin tsoron Allah,akan son abun duniya iyaye da yawa sun halaka sun kuma halakar da yaran cikin su,my sister arzikin nan tun randa Allah ya halicce ki,ya rubuta Miki adadin arzikin da za ki samu,sannan ba za ki taba komawa gare shi ba sai kin cinye su tas,so akan me yasa kuke forcing yaran ku kan auran wanda baku san asalin shi ba ko kuma wanda yarinya bata so duk da sunan ai me kudi ne,in kin aure shi za ki huta,waye ce Miki auran me kudi shine cinyewar aure,ina ranar ka auri me kudin ya zo ya bada rayuwar ka at the end,wa aka cuta,wallahi duk yaron da ya auri yarinya ya san dan kudin shi aka aura mishi ita,to Bara ta taɓa mutunci a idanun shi ba,keep on praying for your daughter's duniyar nan na yanzu cike yake da mugayen mutane wlhy,yara nawa za ki ga sun auri masu kudin Amman kwanciyar hankali saidai gani a makota, don haka ki roka mata zabin Allah,wala me kudi ko talaka indai da tsoron Allah da kwanciyar hankali ai abunda ake nema ke nan, ubangiji ya kare mu daga san zuciya sanann ya tsare mu da aikata aikin danasani),



Ko bayan rasuwar Nusaiban,Rilwanu ya kara auran mata har 2 amman duk basu dade wa suke mutuwa,kowa kuma ta hanya daban daban da baka isa ka zarge shi ba,haka zai zo gurin mutuwa yayi ta kuka,kamar ranshi zai fita,nan mutane suka fara fada wa Hajiya kan sai fa ta tashi tsaye,domin daga gani an taba mata yaro ne,kila bakar aljana aka tura mishi ya sanya ta ke kashe masa mata,don an ga yayi kudi,in ko tayi sake shi da zama da mace har abada,Ita dai sam bata dauki wanann maganar ba a cewar ta kowa da irin ƙaddarar shi a rayuwa,sanann kowa da irin jarabawar da Allah ke yi mishi,Rilwanu ga dai arzikin Allah ya bashi,amamn sai ya jarrabe shi da rashin zaman mata in ya aura,babu wani aljana da ke jikin yaron ta,domin da akwai ta tun ran farko da ta shige shi,za ta fahimta,hakan ne ya sanya ta shiga kwantar mishi da hankali ta fada mishi kan kar ya damu da maganar mutane in sha Allah next auran da zai yi ba abunda zai samu matar,nan ya rufe ido yana kuka yace shi  kam ya hakura da auran,babu yarinyar da zai kuma aura ta mutu,ai sai ace shi ke cinye yaran mutane,nan Rakeeba ta kwaɓe shi akan kar ya kuma irin wannan maganar za ta je gurin yan uwan ta ta sanya suyi ta mishi saukan Alqur'ani in ma akwai wani abun da ke bibiyar shi zai bar shi,sannan tace da shi ya kuma rike Azkars in Shi,zama da alola sanann ya kiyaye sallah,kar kuma ya mance da yawan bada sadaka,jin ta kawai yake yi,domin a cikin rules in brotherhood babu batun bada sadaka saidai kyauta,sannan babu yawan sallah,don akwai month in da gaba daya har ta kare be kai goshin shi kasa da sunan zai gaida ubangiji in Shi ba,


Ba zai taba manta ranar da ya hadu da Bahiyya ba wace ta kasance sanyin idaniyar shi,matar da ya so kamar ranshi kuma ta kasance mahaifiyar Nadeeyar shi ba,



Kaduna  suka je wani meeting ,shi da Kabiru da Salis,don a lokacin yana shirye shiryen fitowa takarar Senator,sun gama meeting in da wuri,sai suka ce bari su dan huta su ga gari,kafin gobe sai su dawo,ashe rabon haduwa da ita ne,


Da yamma kuwa sun fito shi da Salis suna zaga gari,Allah ya yi suka biyo ta kasuwa,sai ko suka hango ta sanye da hijab in ta har kasa tana tafiya kamar tana tsoron taka kasa,da sauri Rilwanu yace Salis ya tsaida mota,domin tunda yake be taba haduwa da mace me kyau irin ta ba,Bahiyya irin Sadakayallan nan ne da suke zuwa cirani kasar Nigeria, kyakkyawa ce ta ajin farko Fara sol,duguwa me dirin daukan hankali,tana da manyan idanu gashin kai da gira kam ba a cewa komai,in one word dai irin matan nan ne da ake kira full option ko in ce da ku end of discussion😂😂😂,


Duk yanda ya so ta tsaya ta saurare shi bata yi ba,Saida suka jira ta gama siyayar ta sanann suka bi bayan ta har zuwa gidan su,inda suka ga ta shiga baban gida,ba tare da sanin ma suna bin ta ba,Salisu ya so su koma gida in ya so gobe su dawo amamn Rilwanu yace sam be san zance ba domin kallo daya da yayi mata ta tafi da gaba daya imanin shi,irin matar da ya dade yana son samu ke nan,nan take ya ji yana mata wani irin kauna me zafi,


A take suka buga kofa inda wani kyakkyawan dattijo fari sol,kamanin shi sak da ita Bahiyyan ya bude musu kofa,tare da cewa wa suke nema ko suna son ganin Alh ne baya nan ai,nan duk suka duka suka gaida shi sanann Rilwanu yace"Baba yarinya muka gani muka biyo in ba matsala", murmushi Mal Ahmadu yayi sannan yace da su shine mahaifin yarinyar wanda ita kuma sunan ta Bahiyya,ba tare da bata lokaci ba Rilwanu ya gabatar da kudirin shi akan yana son ta kuma auran ta yake son yi,


Mal Ahmadu ya ji dadi sosai saidai yana jin tsoro don daga gani Rilwanun me kudi ne,shi kuma ba kowan kowa ba,hasali ma bayan mutuwar Bahiyyar ce suka dawo Nigeria yake gadi a wanann gidan a nan suke samun rufin asiri,babu wanda suka sani a Nigeria gaba daya dangin su na Niger,


A nan take suka samu suka shawo kan Mal Ahmadu,tare da yi mishi alkawarin ya yarda da su bara su bashi kunya ba, ba su suka bar gidan ba Saida aka yi musu magana da ita,yarinyar kuwa babu ruwan ta,a ranar Rilwanu ya sai mata waya tare da bata damin kudade wanda da kyar ya samu ta karbi wayar,



Sai gashi su da suka zo da niyar yin kwana ɗaya tal,sun doshi sati a garin Kaduna,domin duk rana da dare na Allah rilwanu na kofar gidan su Bahiyya, cikin kankanin lokaci suka yi wani irin sabo na ban mamaki,soyayya suke wa juna na ban mamaki tana tsananin kaunar shi domin shine saurayi na farko da ta taɓa yi a rayuwar ta,inda shima a nashi bangaran jin ta yake kamar wani bangare na jikin shi,yana jin ta har jinin jikin shi,sam ta hana shi yawan kashe musu kudi da yake yi,don cikin sati dayan nan siyayyen da yayi  mata da mahaifin ta ba a magana,domin be bar Kaduna ba Saida ya tabbatar ya siya wa mahaifin nata katon gida,mota da kuma jari suka rabu akan cikin watan nan zai Turo ayi maganar auran su domin baya son a dauki lokaci,Bahiyya tana kuka suka rabu domin ta shaku da shi ba na kadan ba,


Haka ko ba tare da bata lokaci ba aka je aka yi mishi tambayar ta kuma aka bashi,aka sanya rana,ko da bikin ya tashi biki aka yi na kece raini anyi barin kudi kamar yaya,sannan aka dauko Amarya aka kawo ta mansion in Shi da ya gama karawa a GRA,gidan da duk wanda ya gani ya san anyi barin Naira,


Zaman auran su zama ce me cike da sha'awa,domin yanda suke tattalin junan su,yana son ta ita ma haka,Bahiyya mace ce me hankali da sanin ya kamata hakan ya sanya Rakeeba ke kaunar ta sosai,shekaran farko da auran su Allah yayi wa mahaifin ta rasuwa inda suka sha kuka sosai,kafin suka bi shi da addu'a,rasuwar shi da sati biyu zabe ta kama inda a take Rilwanu ya lashe takarar kujeran Senator a Bauchi, in da rayuwa ta cigaba da yi musu dadi,domin yanda yake musu barin kudi, kasar waje kam,sun je kasashe ya fi a irga,tattali da kula yake bata ba na kadan ba,babu abunda ta nema ta rasa sai haihuwa,domin duk cikin da tayi bata ma sanin ya shiga saidai ta ga jini wato dai saidai ta ga fitar shi,in da ta daga hankalin ta sosai,amman yayi ta kwantar mata da hankali yana nuna mata komai na Allah ne in  yayi za su samu ai,haka rayuwa ta cigaba da tafiya budi ta ko ina shigowa Rilwanu yake yi,har ma rasa me zai yi da kudin yake yi,da ta shi ne da yanzu ne daidai lokacin da ya dace ya fita daga kungiyar ko ya samu ya ci kudin shi a nutse don har tsoron next Sacrifice in da Odogwu zai ce ya bayar yake yi,sabida gudun kar ace ya bai da Bahiyya ne ya sanya ya roki Odogwu da karamar murya kan ya bashi yaran da za su haifa,hakan ne ya sanya duk samun cikin da za ta yi sai ya fita,


Bahiyya na jin dadin zaman auran ta in Ka cire zancen haihuwar nan da kuma rashin sallah da rilwanu yake yi,tana son yi mishi magana Amman tana jin tsoro don at times sai ta tashi tayi asuba Amman shi yana gado,duk da ita ma ba wani zurfin ilimin addini gare ta ba amman ta san Rilwanu kam be rike addinin shi ba,a haka suka cigaba da rayuwa,yanda mazan su ke aminai,haka matan ma suka hade kan nasu,Ita dai kullum bata da addu'a sai Allah ya Azurta ta da samun haihuwa,


Allah ma ji rokon bawan sa,5 years after marriage har ta cire rai ta hakura da batun haihuwar Allah ya Azurta ta da samun ciki,wanda yayi daidai da ana shirin yin zaɓe,inda Sen Rilwanu ya shafe 4 years in Shi na farko,yana kuma da burin kara komawa,be taba jin kaunar samun haihuwa ba sai wanann karon,ya sanya duk wani extra care yake bai wa Bahiyya don yanda yake ganin yaran Salis da Kabiru abun yana bashi sha'awa,haka suka cigaba da tattalin cikin,inda ya shiga judo musu kayan yara na kasar waje,kudi kam an kashe su,don musamman ya ware kudi ya biya musu suka tafi kasashen waje ita da Asiya da Hafsah matar Salis,a haka suka yi ta renon cikin ta har ya girma,ya shiga watan haihuwa,


Ranar da bazai taba mantawa ba,ranar da duniyar shi ta kusan tarwatsewa,be taba danasanin shiga kungiyar asiri ba sai wanann Ranar,a karshen meeting in su,ya sanar da Odogwu akan cewa yana son ya taimake shi ya kara bashi nasara ya koma kujerar shi ta Sen,nan ko Odogwu yace da shi abu ne mafi sauki Amman kuma dole sai yayi bada abun da ya fi kauna,nan take zuciyar Sen ta buga domin har ga Allah be shirya ya bada wanann babyn da yake jin kaunar shi har cikin ran shi ba,cikin sauri yace "Odogwu zan bada Nana A'ishah kanwa ta",dariya me razanar wa Odogwu ya sanya sanann yace "Ina jinin A'isha ba shi ake bukata ba,Matar ka na da ciki kuma nan da sati biyu za ta haifo kyakkyawar yarinyar irin ta,don haka zabi ya rage naka in kana son komawa kujerar ka ta mulki,dole ka zaba ko ka bada new born babyn da za a haifa maka,ko kuma ka ba mu Bahiyyar wane ka zaba??,,,cikin kuka Rilwanu ya zube a gaban Odogwu fadi yake"Odogwu kayi mun rai ka taimake Ni banda family na,ina son babyn nan Wlhy,kuma ina son matata ka rufa mun asiri,na yarda zan bada Ummi,A'isha da khadija kai in harda Usmanu kake so Odogwu zan bada su amman banda Bahiyya ta,banda kuma new born ita,pls Odogwu ya kare kamar zai shige cikin kafar Odogwun,


Nan ko ya sanya kafa ya tunkude shi, sannan cikin tsawa yace"Kai Rilwanu ka ma gode ina kaunar ka ya sanya nake baka zabi,har za ka tsaya kana mun kukan banza,ance maka wanann farin jinin da kake da shi a banza ne,in banda Ni din wani sabon dan siyasa ne bugun farko ya dace,sannan yake kan samun nasara,don haka zabi ya rage naka,in kana kaunar ka koma kujeran mulkin ka to ka fada mun jinin wa za ka bada"?,


Tabbas da badun ya riga da ya ɗan dana dadin mulki ba da ya ce ya hakura,amman ina baya ji yanda yayi nisan nan lokaci daya ya janye,cikin kuka da dakiyar zuciya yace "Odogwu na bada Bahiyya",dariya Odogwu ya sanya sannan yace "good kayi zabe me kyau domin yarinyar nan da za a haifa ita za ta zamo silar karin arzikin ka,daidai Lokacin da za ta haife ta,xan aiko a suke mun jinin ta,ka ga mutane za su dauka gurin haihuwa ce ta mutu,daga nan kuma ka sanya a ranka kamar ka koma kujerar ka ne",yana kuka haka ya ta sheko godia wa Odogwu sanann suka bar gurin,yana kuka,wanann daran kwana Kabiru yayi yana lallashin shi kan yayi hakuri miye ne ma a ciki,shi ma a haka ya baida matar shi ta biyu,gashi har ya kara aure wa ma ya sani,ko ta mutu zai samo wace ta fita ai,ya ma gode babu dangin ta nan balle a wani zurfafa bincike,shi dai Rilwanu jin shi kawai yake yi,be taba tsamanin Odogwu zai yi mishi haka ba,


Haka ko ya shiga bai wa Bahiyya kula tattali da nuna soyayya ta musamman tunda ya riga da ya san 2 weeks ya rage mata a duniya,cikin sati biyun kuwa sun kara wani irin shakuwa,ko baya gida suna makale a waya,baya ji a duniya zai kuma samun mata irin Bahiyya domin hakurin ta har ya so yayi yawa,cikin iko na Allah kuwa yanda Odogwu ya fada saura 2 weeks ta haihu,2 weeks in na cika kuwa ta tashi da matsananciyar ciwon mara inda a take ya dauke ta sai Rimi clinic domin ya fi kusa da su,a take a ka shige da ita dakin haihuwa domin nakuda ce ta zo mata,


Hankalin shi a mugun tashe ya kira wayar Hajiya ya sheda mata halin da ake ciki,a take kuwa ta sanya driver ya dauko mota,suka kamo hanyar Bauchi dake mata ce me cike da karamci a cewar ta kullum daman ta so Rilwanun ya kawo ta gurin ta,ta haihu a gaban ta,za ta fi bata kulawa tunda bata da kowa a kasar nan Amman ya ce a'a,ya sanya ta ce to duk sanda ta tashi haihu ya sanar mata za ta taho,



Su Alh Kabiru da Salis,wunin ranar su da matan su a asibiti suka yi shi har Hajiya ta iso,Amman haihuwa shiru,ba abunda Rilwanu ke yi banda kuka,wanda duk sun dauka na tausayin halin da matar tashi ke ciki yake,wanda a nashi bangaran yana kukan rabuwa da ita ne,daga shi sai Kabiru suka san kukan me yake,


 Cikin iko da hukunci na Allah bayan doguwar nakudar da ta dau lokaci tana yi,Allah ya bata ikon haifo kyakkyawa,ƙatuwar baby girl in ta,me tsananin kama da ita,yarinya na tsandara kuka Bahiyya ta ce ga garin ku nan,domin ko damar duban abunda ta haifa Allah be bata ba,ta dai ji kukan yarinyar sama sama,nan ko likita ya sanya aka wanke babyn aka nado ta a towel wanda sai kuka take kamar ana kokarin zare Mata rai,sanann ya karbe ta ya fito da ita,


Da sauri suka nufe ta,inda Sen da kyar ya ja ƙafafuwan shi da ke jin sun masa nauyi,ina ma Odogwu ya daga mishi kafa,ace da shi Bahiyyar shi an raye ,


Cike da fara'a Hajiya ta sanya hannu ta karbi jikar nata,wanda a take ta ji kaunar yarinyar,kallon fuskan yarinyar take tare da tofe ta da addu'a,tana me cewa"Barka da zuwa Ahalin mu kyakkyawar yarinya,kin wahalar mun da yarinya ta,dole in kin girma ki sai mata mota,ki Kaita hajji ki siya mata gida,duk dariya aka sanya,nan Hafsah ta sanya hannu ta karɓe yarinya tana me yaba irin kyan da Allah ya bata,



"Doc an gyara Bahiyyar ce,ta farka ko har yanzu tana bacci,Asiya ta tambaya,,,,"lah kin ga zumudin ganin jika ta ya sanya na ma mance da yarinya ta,ya jikin nata,ina fatan dai babu wata matsala"?,da sauri Rilwanu ya rintse idanun shi yana jin zuciyar shi nayi mishi nauyi,har yana ma jin tsoro likitan ya bude bakin shi,


Shima likitan jikin shi duk yayi sanyi,amman a haka ya dage,yace"hajiya saidai kuyi hakuri,haka Allah yake abun shi,ya baku kyauta ya kuma dauke mahaifiyar ta,Allah baya taɓa barin wani dan wani ya ji dadi,don da ya bar Hajiya Bahiyya ko dan wannan yar jinjiran nata, ubangiji ya baku hakurin rashin ta Allah yayi wa Hajiya Bahiyya rasuwa,ga can Gawar nata an gama da shi is ready za ku iya dauka",salati duk gurin suka sanya,banda Rilwanun da ya yanki jiki ya fadi babu numfashi,nan fa kuka ya ɓalle,da sauri doctor in ya zo aka ɗauki Rilwanu aka shige da shi don bashi taimakon gaggawa,inda Alh Salisu ya tsaya aka gama komai sannan suka taho da Gawar Bahiyya,Hajiya da kanta tayi mata wanka,sannan aka wuce da ita gidan ta na gaskia,Hajiya Hafsah da Asiya sun ci kuka kam,domin Bahiyya sam bata da matsala matar kirki ce bata da wani damuwa,haka Hajiya tayi ta dannan su tana basu baki da nasiha,domin ba kuka tafi bukata ba sai addu'a, Alhamdulilah ai ita nata yayi kyau tunda gurin haihuwa ta mutu,ta samu mutuwar shahada,(Allah ka sa mu cika da imani),


Kwanan Rilwanu uku be a san inda kan shi yake ba,sanann aka samu Allah yayi ya farfaɗo,kuka kam yayi shi kamar idanun shi za su nane,Saida Hajiya ta tsaya da addu'a da komai sannan aka samu ya ɗan dawo cikin hayyacin sa,domin da zaune kawai yake ba ya ci baya sha,kamar wanda yayi hauka sabon kamu,da taimakon Allah da komai aka samu ya dawo daidai,bayan wata daya sanann aka samu aka yi sunan yarinya inda babu wani batun taron suna ko wani abu,da Rakeeba ta so a maida wa yarinya sunan mahaifiyar ta,amma Rilwanu yace" a'a tun tana ciki muka zaba mata suna Ni da mahaifiyar ta,sunan ta NADEEYA", nan ko aka rada wa yarinya NADEEYA,wanda Rilwanu ke jin kaunar ta har ranshi,babu yanda Hajiya bata yi akan ya kara aure ba sabida a samar wa Nadeeya uwar da za ta kula da ita,Amman nan ya rufe ido yace ina shi nan zai iya kula da yarinyar shi,baya bukatar wace mace a rayuwar shi kuma yanzu,Bahiyya ce first and last love in Shi,don haka shi zai zamo uwa da kuma uba wa little Princess in Shi,Jin haka ne ya sanya Hajiya cewa za ta tafi da ita,ta rike ta a gurin ta,a nan ma yace sam be yarda ba don har kuka ya sanya saidai a bar mishi yarinyar shi yana ganin ta yana tunawa da masoyiyar shi,Saida aka kai ruwa rana Sannan ya yarda Hajiya ta tafi da ita akan in ta kai shekaru 3 sai ya je ya dauko abun shi.......Wata nannauyan baccin da tayi awun gaba da shi ne, sakamakon giyar da ya dura wa kan shi ne ya katse mishi dogon tunanin da ya fada,in da a take baccin kuwa tayi nisa,kafafun shi suna kasa rabin jikin shi ke kan gadon,daga ganin alamun shi dai baccin unexpected ce ta kama shi ba makawa kuwa in ya tashi babu abunda zai hana shi yin ciwon wuya da na jiki,



Afuwan wlhh jiya charge ina ne ya kare ya sanya baku ji Ni ba,



Sai zuwa Monday  kuma in me kowa me komai ya so,


Na san akwai lot of typing errors,sabida typing in dare nayi kuma ban riga nayi editing ba,so ayi mun afuwa ,


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


            

           

........


This page is yours Yar Mommyn tah,ina godia da kaunar ki gare ni🫶🏻❤️


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


...........

          Page forty one


**********


     Back to the story



     Doc Bashir*********


 

 A hankali Doc Bashir ya shiga bude idanuwan shi da yake jin su sunyi mishi wani irin nauyi,da sauri ya koma ya kwanta tare da barin kokarin mikewar da ya soma yi,domin wani irin amsawa da ya ji bayan kan shi yayi,ji yake kamar naman gurin ya kwaile,ko in ce yana jin kan nashi kamar ba a jikin shi yake ba,a hankali ya sanya hannu biyu biyu tare da dafe kan nashi wanda ke barazanar rabe wa gida biyu,sakamakon gindin bindiga da aka buga mishi akan wanda yayi sanadiyar sumar tashi,


Da sauri ya mike bayan ya samu hadin kai daga gurin brain in shi domin in har be mance ba tsayawa yayi don taimakon tsohon da ya buge a mota akan hanyar shi ta zuwa Airport,ai da Kai wa nan ya mike zumbur yana fadin"Na shiga uku na lalace kar dai Flight ina na tafiya Los Angeles har ta tashi babu ni a ciki",ya kare kamar zai yi kuka tare da kare wa bakin mummunan dakin da yake ciki kallo,dakin da babu abinda yake yi banda karni da wari,dakin da ko dabbobi in ka san darajar su bara ka sanya su cikin wannan dakin ba,"to uban me ya kawo Ni dakin nan Ni Bashiru??,ya tambayi kan shi yana me isa bakin kofar da take a rufe kirib,wani irin jiri ma ya fara ji yana ganin dakin yana juya mishi,ga kan shi da ke Bala'in ciwo har yanzu,a hankali ya dafe handle in kofar,Wanda ga mamakin shi ya ji shi kirib,kwata kwata brain  in Shi yaki haduwa guri daya balle ya hasko mishi kan cewa sato shi fa aka yi,cikin zafin Nama ya shiga kiciniyar ganin ya bude kofar,Amman sam kofa taki buduwa,


A garin hakan ne ya ji an bude kofar tare da bugo ta da karfi,wanda yayi sanadiyar gwaɓe mishi fuska,kasancewar a cikin kofar yake,be san lokacin da ya saki ihu ba "wayyo Allah na fuska na",ya kare tare da shafo fuskan,sabida radadin da yake masa,ji yake kamar an watsa mishi barkono, shigowar wasu katti majiya karfi,murdadu kuma munanan mutane ne ya sanya shi saurin shan jinin jikin shi,domin Allah ya gani kallo daya za kayi wa wannan mutanan ka fahimci sam babu alamun tausayi ko imani a tattare da su,haka kuwa suka shiga shigowa daya bayan daya,kamar wanda suke kan layi,duk wanda ka kalla a cikin su bara ka so ka kuma duban shi ba sabida bakake kuma munanan fuskokin da suke da shi,wanda kallon su kadai ya isa sanya ka cikin firgici da kadawar hanjin ciki,


Wani irin kakkauran yawu Doc Bashir ya hadiye wanda ko za a kashe shi be san a taya ya tara miyau in ba,a take jikin shi ya hau karkarwa domin har ga Allah wanann miyagun mutanan in suka damke shi to fitar shi sai kuma Allah ya so,tsoron shi daya kar dai su janye abinda zai hana tafiyar shi kasar Los Angeles in Shi,nan ya shiga bin su da ido daya bayan daya,ganin yanda duk suka zaro mishi Jajayen idanuwan su ne ya sanya shi saurin mikewa saboda tsoro har ji yake kamar yana kokarin sakin fitsari a wandon shi,


Basu ce da shi komai ba,ila kallon banzan da suke bin shi da shi,wanda in ka nutsu ka lura za ka fahimci kallon za ka ci uban ka yau a hannun mu suke yi mi shi,


A hankali ya samu ya mike,sannan ya kuma kallon su a karo na ba adadi,kafin a hankali yace "barkan ku dai majiya karfi",su kan su furucin nashi ya so basu dariya Amman sai suka basar kamar ba su ji abinda ya fada ba, ganin haka ne ya sanya ya kara tausasa muryan shi gurin fadin "ga dukkan alamu akwai little misunderstanding in da aka samu a nan, because ni ban san ku ba,ban kuma yi muku komai ba,balle ku ce revenge za ku dauka,kila wani kuka je dauka aka samu misunderstanding kuka dauko Ni,domin kallo daya nayi muku na gano ku din Kidnappers ne,to Ni dai bani da hadi da ku,kuma ba ku Sanni ba,so can you let me be ku Bude mun kofa,in tafiya ta salin alin kafin ku ga other face ina",ya kare yana me hade fuska,


Wani irin wawan dariya duka suka sake harda masu rike ciki,shi dai yana tsaye ya zuba musu idanu thinking wat so funny da za su tsaya suna irin wannan dariya haka,Saida suka dara sosai sannan babban cikin su ya hade fuska,tare da watsa mishi kallo,"kindly go back and seat down har oga ya zo kafin nayi maka abinda baka so",ya kare cikin tsawa,


   "Naki in koma in zauna in wai wa za kuyi wa karyan iskan ci,ko kun san waye Ni ma kuwa??,a wani iskancin naku wai ku kuna jin kan ku Kidnappers,wallahi tallahi,da badun darajan Aure da ya nitsar da Ni ba,ai da Ni yanzu ogan ku ne a Kidnapping,domin duk yanda kuke tunani kuna da son kudi ba ku kai Ni ba, banda darajar aure da qualification ina ai da yanzu maybe ma har smuggling in drugs Zan nayi,so in har kun san me ke muku ciwo tun wuri set me free I have an important trip a gaba na,so bude mun kofa na fice tun kan raina ya ɓaci",


      "And so fucking what!!,Aroooo I want you to beat the hell out of this stupid guy,beat him black and blue",Afzaal ya Fadi Wanda shigowar shi dakin ke nan fuskan shi da ya suntuma sakamakon bugun da ya sha hannun Sen a daure,alamun ranshi a matukar bace yake,


Doc Bashir jin abunda aka fadi ne ya sanya shi dagowa,don ganin wani dan iskan ne ke bada umarnin a dake shi har haka,dago fuskan shi kuwa yayi daidai da kwada mishi mari da Aroooo yayi,within a blink of an eye suka shiga dukan shi ta ko ta ina,banda ihun neman taimako da kuka babu abinda Doc Bashir ke yi,domin ba karamin azaba yake ji ba,jikin shi gaba daya radadi yake yi mishi,sanda Afzaal ya ga Bashir ya bugu iya buguwa,sannan yace da Aroooo da yaran shi su dakata haka  nan,nan ko suka tsagaita da dukan nashi,


Cike da takun isa,da gadara,Afzaal ya tako,har ya iso inda Doc Bashir ke kwance magashiyan kamar babu numfashi a tattare da shi,har gaban shi ya zo,sannan ya durgusa,bottle water in hannun shi,ya bude tare da kwara wa Bashir in a jiki da fuska,in da a take ya ja wata wawiyar ajiyar zuciya,jin yanda sanyin ruwan ya ratsa jinin jikin shi,a hankali ya bude idanun shi da yake jin sunyi masa wani irin nauyi da zafi,ya sauke su kan Afzaal da ke durgushe a gaban shi,ai arba da yayi da fuskan Afzaal be san sanda wani karfi ya zo mishi ya mike zaune ba,a take kuwa ya saki ihu"wayyo Allah na mazaune na,zafi", ya kare kamar zai yi kuka,a take kuwa Afzaal da su Aroooo suka sake mishi dariyar mugunta,


  "Bashir ke nan, wlhy Ni tunda na zo duniya bayan dan gidan Audu Waziri ban taba ganin me tsinannan son abun duniya irin ka ba,ya kare yana me dariyan yan iska,


Jiki a mace,bakin shi har rawa yake,yace"Afzaal! Afzaal!!me nayi maka a rayuwa da har za ka sanya a sato Ni,an zo an zubar mun da mutunci,an dage Ni me nayi maka,ya kare yana tari,,,,"kai dallah dakata mun har kana da bakin tambaya ta wai me ka tsare mun da zan sato ka,kai Bashir sanya idanun ka cikin nawa ka kalle Ni,na fi ka iskanci wlhy,na ci uwar rainin wayon ka na yaga leda,har Ni Afzaal zaka yi wa Bura uba,kai ga ka tsohon dan iska ko,uban da ya fi kowa son kudi,to wlhy tallahi tunda na Saida imani da mutunci na kan na mallaki abun duniya banga uban da ya isa ya ci kuɗi na in bar Shi ba duk fadin garin Bauchin nan,kai Wlhy ko uba na da ya kawo Ni duniya ne ya ci kuɗi na ba tare da umarni na ba sai na yaga mishi rigar mutunci,balle Kai banzan bazara,Bashir ubaidullah ina kudade na suke,yi maza ka bani su domin bani da time in tsaya wa dogon magana da kai,


Mikewa zaune Bashir yayi tare da hade fuska tamau kamar wanda aka aiko wa sakon mutuwa,"haba daman ai na sani ruwa bata taɓa tsami banza,saboda rashin tsoron Allah Afzaal Ni za ka sanya a sato akan hakki na,to wlhy kamar yanda na fada maka ne a baya kuma zan cigaba da maimata maka, sisi in na baka kwarankwatsa ya fado mun,tunda kai shege ne mara mutunci,Ni kuma tsohon dan iska ne me mugun son kudi,daman ance maganin shege sai dan iska,mu zuba mu gan...be kai ga karasa maganar ba Afzaal ya dauke shi da wawan mari,wanda a take yayi sanadiyar fashewar bakin shi,


  "Za ko ka gani,kar ka fasa nuna mun kai dan iska ne,inda ba zan gaji ba gurin nuna ma halin shegu,ka sanya a ranka daga yau kwanan ukuba,bakin ciki da azabar ka ta fara,in ka ga dama kar ka fito mun da kudade na,Amman ka sanya wa ranka Bara ka taba barin nan gurin ba,in har kudade na basu fito ba,Aroooo ku cigaba da hora mun shi,ku yi mishi dukan Kawo wuka,bugun Bura uba wanda sai ya ji me ma ya sanya ya san Ni a rayuwar shi,daga gama fadin haka ya juya ya bar gurin zuciyar shi na tafasa yana zafi,domin har ga Allah venting anger in abunda Sen yayi mishi yake yi a kan poor Bashir in,



      Kaduna**********


     "Mama ga wayar ki nan tun dazu ake ta kira kina sallah",Zaliha yar aikin Mama ta shigo parlor da gudu tare da mika mata wayan,karban wayar mama tayi tare da sanya farin tabaran ta dake kusa da ita, sha'ani na rayuwa idanun sai a hankali ba sosai ta cika gani ba,kallon screen in tayi ganin Umar ke kira babban yaron ta ya sanya ta picking,


   "An wuni lafiya Mama,ya gida ya su Haanan",zama ta gyara sanann tace "lafiya kalau Alhamdulilah ya iyalan naka??,,,,"duk muna lafiya da sun ma so zuwa a hutun nan,to sai mamar su tace a bari sai next time don za ta gurin family in ta da su,ya kare yana kurban lemo,


    "Hmmm Mama tace tana me mikewa,yayi kyau ai zumunci Abu ne me kyau,Allah ya kaimu next time in,ta kare ranta babu dadi,domin har ga Allah ba kaunar matar Umar in take ba,domin sam yarinyar bata kwanta mata a rai ba,tunda ta aure shi ta janye shi,komai sai dai ita da dangin ta ke Moran shi,thank god Nameer ya zame mata haske da kuma Sanyin idaniyar ta da bata san ya rayuwa zai mata ba,ya sanya kaunar Nameer in daban yake cikin ranta,


"Mama ina ta magana ko baki ji na ne",,,,"me kace network ke breaking ban ji ba",tace tana me cire hijab in ta,don har ga Allah bata jin ba sakamakon duniyar tunani da ta fada,,,,,,"cewa nai Khadijah ta kiran tana fada mun wai Nameer ya kawo mahaukaciyar da ba a ma San asalin ta ba gida,shine nace bari na kira na miki magana",,,,zama ta gyara sanann tace "yauwa Ubana ina sauraran ka",shima sai ya ji kunyan furucin nashi"a'a mama baki fahimce Ni ba,daman gudun matsala nake jiye miki, duk da kasancewar Nameer likitan Mahaukata ne,hakan be bashi daman maida mana gida,gurin jinyar mahauka ta ba,yarinyar nan kun ko san yar wa ya dauko ke kuma kika taya shi boye ta a cikin gidan ki??,to Mama in be ma fada Miki ba ni zan sanar da ke,Nadiya yarinyar Sen  Rilwanu Audu Waziri me neman takaran kujeran gwamman jahar Bauchi,kin san rikicin mutumin nan kuwa??,wlhh Mama tun wuri ki kira shi ya zo ya fidda ta,kafin ya gano inda diyar sa daya tilo take ya zo ya tafi da ke,da shi,harda mu baki daya ma,ya kare da iya kan gaskiyar shi,


Tsaki Mama ta ja kasa kasa,domin ba dabi'an ta bane yin tsaki,in kuma tayi to abu ya sosa Mata rai matuka"Farouk ka gama!!nace ka gama!!,ta fada a hatsale,wato har kayi girman da za ka kiran a waya kana fada mun maganar duk da ka so right??,ina ruwan ka da Babana ko,Ni ce dai ka ce ba ka so,ka zabi matar ka akan ni,to yanzu kuma miye naka a cika,ko kashi,ko kare Babana ya kawo yace na ajiye masa Ni me ajewa ne,sakarai shasha me mugun baki,in har ba kai zaka sanar wa so call Sen in ba uban waye zai fada mishi yarinyar shi tana gida na,kwantar da hankalin ka tsoron ka ina ce kar a kama ka ne,to in dai Allah muke bautawa ya ga niyar babana da Ni kaina akan cewa ba mu da mugun nufi tattare da yarinyar sa ba zai taba tona mana asiri ba,wlhy tallahi Umar ka fita ido na,daga kai har munafukar dake kawo maka gulma,duk zan hada ku nayi muku abinda zuciyoyin ku ba zai so ba,har yaushe kayi girman da za ka zo kana fada mun maganar banza,ko da ya kawo ka,na kira an nemi sisi a gurin Ka,domin jinyar ta balle kace da Ni ka gaji ya sanya kayi mun wannan maganar,to in Baka mance ba I am your mother!!you better watch your tongue while talking to me,domin in ka mance in tuna maka,shi fushin iyaye na tare da fushin Allah,ita uwa ko bata furta ba in aka bata Mata rai,Allah ya sani,tun wuri ka fice mun a idanu kafin na ci maka mutunci wlhy,ta kare a zafafe, zuciyar ya na zafi domin har ga Allah Umar in ya bata Mata rai,


"Allah ya huci zuciyar ki Mama Ni ban yi don bata Miki rai ba,ina jiye Miki fadawa matsala ne daman",,,,"Allah ya riga da ya kare Ni,ni da matsala Faruku saidai na ji ta a makota,kai dai da ka Ibo matsala a cikin gidan ka,ina maka addu'ar ubangiji ya raba ka da ita",daga haka ta kashe wayar ta,tana me bakin ciki da halayen babban dan nata,shi dai duniya in dai ba matar shi ba to babu abunda yake dauka da mutunci, scrolling contact in ta, ta shiga yi,cikin Sa'a kuwa ta samo Number in khadija a sama sama,nan take kuwa ta dannan mata kira domin so take ta ji uban da ya sanya ta kiran Umar in,


Bugu biyu kuwa ta dauki kiran,bakin ta har bari yake gurin fadin"Mama ina wuni",,,,"rike gaisuwar ki Khadija domin bata da amfani,ashe ke har yanzu mugun halin kin nan yana nan ko, Khadija da kika zo gida na me nace da ke game da yarinyar nan,ina ruwan ki da ita,da zaki je ki kira Umar sabida Ubana ne shi kin kai kara ta ya dau mataki ko me??,,ta kare a tsawace,,,,Sarai sun san halin mahaifiyar ta su tana sauƙin kai da sanyi hali Amman san bata daukan raunin wayo,,,"Mama don Allah kiyi hakuri,gani nayi daman ba mu san asalin ta ba Yaya Nameer ya kawo ta,ina jiye tsoron abunda kan je ya zo ne,,,,"gidan ki ne ko gida na???,akwai wanda ya ce ki zauna kiyi jinyar ta ne?,wallahi khadija daga ke har Umar ku fice mun a ido,kar ku bari wlhy fushi na ya sauka a kan ku,ina raba ki da munafurci da mugun halin kin nan baki ji ko,nan ko Mama tayi ta zazzaga mata buhun masifa, Khadijan na ta bata hakuri,don yanda suka banban ta da Umar duk iskancin ta tana tsoron fushin.mahaifiyar nata,da kyar ta samu Mama tayi shiru tare da kashe wayar ta,ba karamin sanyi jikin Khadijan yayi ba,har ma ta shiga dana sanin kiran Ya'yan nasu ta sanar masa abinda ke faruwa,


Aje wayar Mama tayi tana me cigaba da kananun mita,don yau kam su Khadijah sun kai ta bango,sallamar shigowar Mujaheed ne ya sanya ta yin shiru,har kasa ya durgusa tare da gaida ta,sannan ya tambayi ya me jiki,"jiki da sauki Mujaheed ka shiga tana ciki ban dade da gama goge mata jikin ba sabida zafin da yayi",


Nan ko ya tashi tare da shiga dakin,yanda ya bar ta jiya haka ya tarar da ita yau,alurar zazzaɓi ya kuma mata,sannan ya shiga duba ta,ganin komai normal har jinin nata ma ya ɗan hauro daga saukan da yayi jiya ne,ya sanya shi sakin ajiyar zuciya yana me jin dadi a ranshi,domin jiya sam be rintsa ba,Nameer damun shi yayi ta yi a waya,gurin tambayar ya jikin Pookie in tashi,a karshe Saida ya kashe wayar sannan ya samu ya rintsa,ina dalili akan wata Pookie da Nameer ya hana kan shi bacci😂😂,



Saida ya gama komai sannan ya samu ya fito parlor Mama tana nan a yanda ya bar ta,zama yayi nan kasa,kusa da kafafun ta,babu yanda bata yi da shi ya hau kujera ba amman yace a'a,yana daya daga cikin abinda ya sanya take kaunar Mujaheed ke nan saboda yana da tarbiya da sanin girman iyaye,


"Son ya ake ciki,ya jikin nata"??,,,"mama wlhy jiki Alhamdulilah don jinin ma ya fara haurowa,nayi mata alurai,saidai game da rikewar numfashi da furgicin da kika ce ne,nake da shawara akan hakan",zama Mama ta gyara sanann tace "go on son ina sauraran ka",,,shi din ma gyaran zaman yayi sanann yace"Mama jiya bayan na bar nan,nayi ta tunani tare da dogon nazari,don har Gee ma na kira,na so sanar mishi sai nace ban san yanda zai dauki maganar ba,domin ba kowa bane yake yarda in an fada mishi,duba da zamanin da muke ciki yanzu",,,,taran numfashin shi Mama tayi"ban gane inda maganar ka ta dosa ba??,


    "Mama tun jiya da na ga jikin yarinyar nan hankali na be kwanta ba,haka kawai nake jin tsikan jiki na yana tashi,(Mujaheed yana da jinnu tun yana karami),hakan ne ya sanya tun jiya na gaza samun kwanciyar hankali,domin wanann rashin lafiyar nata sam ba na asibiti bane,don gwajin duniyar nan na sanya anyi mata daxu da safe,don na iba jinin ta jiya,me i thought ma stroke ne ya kamata ko wani abun can,amman babu ko daya,don bata ma da Bp banda yanzu da ta samu low Bp,so dayan biyu ne,ko ciwo dai daga Allah ko in ce irin jarabawar nan da mutum kan kwanta jinya a rasa gane kan ciwon,ko kuma turan Aljanu wato sihiri wanda Ni na fi zaton hakan ma,don tunda na shiga na gan ta, hankali na ya gaza kwanciya,ya kare yana wasa da yatsun kafar shi,


Numfashi Mama ta sauke me nauyi sannan tace"ikon Allah wlhy kuwa ban taba kawo hakan a raina ba,ka san ko Habban da nake bata kullum,kawai bata nake yi,tunda Annabi da kanshi yace maganin ko wace irin cuta ce,and biri yayi kama da mutum,a duk sanda nayi playing karatun Qur'ani,ko nake karantawa kusa da ita,tayi ta fusge fusge ke nan kamar numfashin ta na kokarin barin jikin ta,sam Allah be taba bani  Sa'a balle nayi tunanin ko shafar Aljanu bane ko wani turan Aljanu,yanzu wat is the way out??,don wlhy yarinyar nan has suffered a lot,ta wahala iya wahaluwa",,,, murmushi Mujaheed yayi sannan ya mike"babu komai Mama ki kwantar da hankalin ki in sha Allahu wahalar ta ya kusa zuwa karshe,zan kira Gee yanzu muyi magana da shi,in sha Allah duk yanda ake ciki za ki ji Ni zuwa gobe,zan je yanzu gurin Mal Hukmullah zan yi mishi bayanin komai,in sha Allah zai taimaka mana",,,,"ubangiji yayi maka Albarka Mujaheed,Allah ya raya maka zuri'ar ka,ya kuma kare ka da kariyar shi",har ranshi yana jin dadin addu'oin Maman,"Àmeen ya rabil alamin Mama baran je sai zuwa goben",,,,"Bara ka tsaya ka ci abinci ba??,,,,"a'a Mama sauri nake na bar mutane a asibiti,zuwa goben dai zan zo da wuri sai in ci dumame,ya kare yana dariya,ita din ma dariyar ta saki,don sanin halin Mujaheed mutum ne shi me barkonci,wayar ta ta kuma janyo wa tare da dannawa Nameer kira......



  Assalamu alaikum



Ayi mun afuwa kwana biyun nan zama ne ban samu ba,masu cikiya ta, Alhamdulilah ina cikin koshin lafiya, ubangiji ya bar kauna na gode sosai🙏🏻,


Page in yau babu yawa,bare with it in sha Allah mun kusa zuwa karshe,and na San Bara a rasa lot of typing errors ba,don ban riga nayi editing ba,



Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


     This page is yours  Ummu Iman,ina godia da kulawa da kuma  kaunar ki a gare ni🫶🏻❤️

             

..........



https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


...........

          Page forty two 


**********


          Kai tsaye unguwar Kinkinau Mujaheed ya nufa bayan barin shi gidan Mama,domin a nan zauran Mal Hukmullah yake,ko da isar shi gidan,tarar da Mal yayi cikin daliban shi sun zagaye shi suna daukan ilimi,takalman shi ya cire, tare da hawa kan taburban da daliban ke zaune,


Kai tsaye gaban Mal ya nufa,tare da rage tsahon shi,yana me mika wa Mal hannu,sannan ya shiga  gaida  shi,cike  da mutuntawa,fuska sake Mal Hukmullah yace"ah Masha Allah wa nake gani a majalisi na yau,kamar Mal Mujaheedu", murmushi Mujaheed in yayi,tare da  sunkuyar da kai,ya kwana biyu be zo gurin Mal in ba,ya sanya a kunyance yace"afuwan Mal,na san nayi laifi, wlhy abubuwa ne suka sha kai na"ya kare yana murza yatsar hannun shi, murmushi Mal yayi sannan yace "Masha Allah tunda ai lafiya Lau,na ga jikin naka ma yayi kyau sosai Likita bokan turai, Ubangiji ya karo lafiya,ya kuma cigaba da bada sa'a","Àmeen thuma ameen Mal,jiki yayi kyau sosai, rabon da nayi mugun mafarki ma na manta why","yayi kyau, ubangiji ya kara wa rayuwa albaraka",da Àmeen ya amsa sannan ya nemi guri ya zauna a kusa da kafafun Mal,dan shiru ne ya ratsa majalisin tun isowar Mujaheed,don duk wanda ke gurin ya san kusancin da ke tsakanin Mal Hukmullah da Mujaheedu,don tun yana yaro ake kawo shi karban magani a gurin Mal,ganin haka ne ya sanya Mujaheed cewa"Mal ka gama da su in ka sallame su,daman magana na zo da shi",jin haka ne ya sanya Mal cigaba da koyar da daliban nashi, Mujaheed na nan zaune,har Mal Hukmullah ya gama,yayi nasihar da ya saba kullum bayan gama karatu,sannan ya tambaya "akwai wani me tambaya?,ko me bukatar taimako,ko gurin mutane,ko kuma yana neman a taya shi da addu'a a gurin Allah"?,nan ko masu bukata suka shiga fadi,daidai karfin Mal ya shiga taimakawa,inda Mujaheed ya sanar da Mal ya zo da buhun shinkafa uku,da gallon in mangyada,a dauko a raba wa masu bukata,ga kuma dubu dari nan cash ya mika wa Mal,ba karamin dadi Mal Hukmullah ya ji ba,domin Mujaheed mutum ne shi me son Alkhairi,ya sha janyo Nameer su zo gaishe shi,haka za su kawo mishi sha tara na abun arziki,


Saida aka gama rabon,sanann kowa ya tafi zuciyar shi kal,domin a halin babun nan da ake ciki ka samu kwanan shinkafa,da mangyada harda kudin cefane to me ka rasa,banda addu'ar Alkhair babu abinda suke wa Mal da Mujaheed,


"Yauwa Mal Mujaheedu,ko ciki za mu shiga ne,a kawo maka kunu da kosai,na san iyanzu  kam Innan ku ta kammala,murmushi yayi kafin yace "A'a Mal a koshe nake,in na ci yau ai Jamila Zane ni za tayi",dariya Mal ya ɗan yi sanann yace"sha'ani na mata sai dai a bar su,zauna da kyau Mujaheedu ka ce da ni magana gare ka",ba musu kuwa ya gyara zaman nasa,sannan yace "Mal wallahi matsala ce babba ke damun matar da Amini na zai aura"katse shi Mal yayi da fadin"ba dai Mal Nameeru ba"?,"eh Mal,shi fa,numfashi ya sauke sannan ya kwashe labarin jinyar Nadeeya tas ya sanar da Mal in,numfashi Mal ya sauke sannan yayi dan jim,na dan mintuna sannan yace"ikon Allah,gaskiya mutanan mu akwai mugunta a ran su","Mal zargi Nima nake ba wai na tabbatar kan sihirin aka yi mata ba,kasan ance zargi haramun","yo Mujaheedu ai duk wasu shifofin Sihiri akwai a jikin ta,daga labarin da ka bani,amman babu komai in sha Allah zai zo karshe,duk wani shedanancin bakin Aljani,Ayoyin Alqur'ani sun fi karfin shi,ban san yaushe ne za a daina amfani da Aljanu muyagu ana cutar da bayin Allah ba,amma babu komai,ka je ku zo da ita nan da kwana uku ,kafin nan zan san abun yi",


Da sauri Mujaheed yace"a'a Mal,halin da yarinyar nan ke ciki,bana jin za mu iya kwana uku ba tare da taimakon ka ba,wlhy tana cikin yanayi na azabtuwa,abun sai wanda ya gani,rabon da ta ci abinci me sunan abinci har mun mance,sai through feeding tube take samun cin abinci,at times kuma drip, her condition is getting worst day by day,Ka taimaka Mal in zo in dauke ka mu je gidan na su gobe,kamar yanda nayi wa Maman Nameer alkwari",ya kare yana fatan Mal ya yarda domin sam baya zuwa gidan mutane da sunan rukiya,saidai a dauko me jinya a kawo masa,a kuma samu waraka da yardar Allah,to duba yayi da irin halin da Nadeeyar me ciki,in aka ce a dauko ta,zai zamo da takuri da kuma wahalar da both Nadeeyar da Mama,ya sanya shi rokon Mal Hukmullah in, dan jim Mal yayi kafin yace"babu komai Mujaheedu, ubangiji ya sanya mu kai gobe in, sananan Allah ya mun ludifi ya zamo sila na ta samu waraka a gurin Allah,mu namu daman addu'a ce,sauki kuma 'min indillahi ne', ubangiji ya kare ku sannan ya kara mana lafiya baki daya",cike da jin dadi Mujaheed ya shiga godia wa Mal, daga nan kuma suka shiga dan taba hira,yana nan gurin Mal har aka kira sallar Magriba,sai bayan sun yi sallah an kawo kunu da kosan da ya ki ci dazu,ganin da dumin shi yana tiriri ya sanya ya wanke hannu,suka ci tare da Mal(daman Daughter ta ce Mujaheed ba dai kwadayi ba🤣🤣),


Ba shi ya bar gurin Mal Hukmullah ba sai bayan sallan Isha,kai tsaye gurin me gasa kaji ya nufa,Saida ya siyo,tare da Drinks sannan ya dauko hanyar gida,a parlor ya tarar da Jamila ta hade cikin wasu kananun kaya,ta sha gyaran gashi,sai ta fito kamar wata baturiya,idanu ya zuba mata,cike da murmushi kuwa ta zo ta tarbe shi,shima murmushin yayi tare da janyo ta ya rungume,yana sanar da ita irin kyan da tayi yau,dariya ta sanya sanann tace"kai dai baka da dama wlhy,gani nai ai kamar ana shirin mun kanwa ya sanya nace bari na tashi tsaye a san dai har yanzu Jamceey na nan ba wai tsufa nai ba"ta kare tana turo baki,


Dariya Mujaheed ya fashe da shi,sannan ya manna mata kiss a lips inta da ya sha red lipstick,sannan cikin kasa da murya yace"wa ya isa!Ina mutum ya isa karo wa Jamceey beauty kanwa,ai mutum ma ya kira ruwa wa kan shi bayi da umbrella"ya kare yana dariya,jakar hannun shi da ledar ta karba sannan tace"ba wani dadin baki,ba ga alamu ba,kwana biyun nan you seem to be very busy,sau biyu kama kin cin abinci na,for Allah sake My love ka duba fa yau sai bayan isha kake shigowa gida,kusan 9:30 ake nema fa,in ba zance ka je ba to ina ka tsaya,Ni kawai in mutum aure yake son karawa gwara ya sanar mun ai",ta kare tana me matso kwallan gulma,janyo ta Mujaheed yayi tare da rungume ta,tana jikin sa ya fada kan kujera"zo ki ji yar baby ta,wlhy kwana biyun nan gidan su Gee nake zuwa, patient gare su,and saboda yarda ya sanya ya danka mun case in a hannu na kin ga ai baya nan,yanzu haka ma daga gidan su gurin Mal na wuce,gani nai jinyar nata kamar ba na asibiti bane,ya kare yana kokarin tusa hannun shi a dan rikar jikin ta,da sauri ta mike sannan tace"ai ko mutum ya taimaki kan shi,domin Mujaheed mijin Jamila ne daga duniya har lahira babu kari in sha Allah",dariya ya sanya kawai yana me kafe ta da idanu,wato sha'ani na mata sai dai a bar su,duk ashe kishi da zargin karin aure take zai yi,ya sanya tun jiya take fushi da shi,yayi tambayar duniya ta ce babu komai,sai kuma yau ya ga ta hade cikin kananun kaya harda su gyaran gashi wanda rabon da tayi ta kwana biyu,(Mata a dinga gayu da daukan wanka hilisssss,ba wai in an haihu ba shike nan gayu ya kare,akwai wasu matan daga haihuwa daya ko biyu to wlhy shike nan mata ta saki jiki,dan kayan gayun nan an daina sanya su ke nan,in ba fita taron biki ko suna ba,sai ki ji har fadi wasu suke,wai to gayen me kuma zanyi Ni da nake da yara,ai gayu mun dai yi da yanzu kam sai dai yan bayan mu🤣🤣,kun ji mun  wawiya,what I believe is mace bata tsufa saidai in ita ta tsufar da kan ta,and duk mace babu me muni,saidai in bata san yanda za ta gyara kanta ba,kazan ta dai shine abinda ke halakar da wasu matan,miji in ya gaji ya ce zai karo aure,ki hau hauka kina daga jijiyoyin wuya ke ala dole wai an ci Amanar ki,ko Amanar me aka ci miki oho🥱,na miji ko kazamine yana son ya ga Matar shi me tsafta ce,don Allah ana kokari ana kulawa da tsaftace jiki,muhalli,da kuma yaran ki, ubangiji ya datar da mu,don shi tsaftan nan ma cikon imani ne),


"In sha Allahu Jamceey na,Ni naki ne duniya wal Akira,are you happy now"?,fuskan ta dauke da murmushi tace"yes my love,yanzu dai ka tashi mu je ka samu kayi wanka,sai ka zo mu ci abinci",babu musu kuwa ya bi bayan ta,Saida yayi wanka ya shirya cikin kaya mara sa nauyi sannan suka fito parlor,already babyn su yayi bacci since so tsakiyar parlor suka baje,cike da soyayya kauna da tattalin juna suka shiga ciyar da juna kazar da ya zo da shi,shigowar kiran Nameer ne ya katse musu hiran da yake bata, daukan wayar yayi da ta kusa

 tsinkewa,cike da iskanci Nameer yace

    "uban me kake yi da ba ka ɗauki waya ta da wuri ba Saida ta kusan tsinkewa"?,cike da iskanci Mujaheed ya bashi amsa da"abinda ko wani na mijin aure ke yi da matar shi in dare yayi",baki Nameer ya bude sannan yace"abun naka harda bakar magana?,babu komai lokacin ka ne,dan iska ai da ka fito ka fada mun abinda kuke yin a fili,laifi na ne ma da na kira ka",dariya Mujaheed ya kwashe da shi sannan yace"ko baka kira ba Ni nan daman ina da niyar kiran ka,domin na ga Iri a gidan ku,and in Ka ji zafin magana ta,dan uban ka,ka nemo mata mu daura muku aure kuma ku fara neman lada babu dare babu rana ",ya kare yana dariya,shima Nameer in kasa rike dariyar nashi yayi,wato ya lura iskancin Mujaheed kara gaba take yi,



"Allahu ya shirya mun kai Mujaheedu,hope Kuna lafiya,ina babies  ina?,da Mommyn su ko sun kwanta"?,


"Yaran ka kam anyi bacci gobe akwai sch,Maman su kuma muna nan muna planning having baby number 3 Ka katse mu da kiran ka,wlhy Nameer zan ci maka mutunci idan kana kira na cikin dare,wai kai baka san Ni na mijin aure bane",ya kare ya na me daure fuska wai duk ya nuna irin he is serious in nan,"ai wlhh in Baka hadiye ta,ta koma cikin ka ba,ban yarda kai na mijin aure bane,ka ji mun dan iska!Ce maka aka yi Nameer bayi da abun yi ne,sai kiran mazan aure,ka fita ido na Mujaheed yau da ban taba auran nan ba ai da ka jefa Ni cikin damuwa irin wannan temptation haka",dariya Mujaheed ya kuma yi domin shi fa haka ya ke in ka gane shi Zaka ji dadin zama da shi,domin mutum ne shi me sauƙin kai da kuma son barkwanci,


"To how far ya aikin?,"Wlhy Alhamdulilah, dazu Mama ta kira ni network babu kyau,ita ce ma tace na kira ka wai za ka mun Magana game da Pookie,hope lafiya?,juyawa Mujaheed yayi don ganin ko Jamila na kusa da shi,sai ya ga ashe ta tashi tayi daki,yana daya daga cikin halayen Jamila da yake so,sam bata tsaya wa ears dropping in yana waya,duk da ta san Nameer ba sanin yau ba amman bata tsayawa in ta ga yana waya,ta kan ce privacy wa mutum ma is something (Mata masu son Jin kwaf 🤣🤣miji na waya ki labe ke kina son sai kin san komai,ko masu binciken wayan miji,to a ji tsoron Allah a haka kike sanya wa kan ki kumburin zuciya a karon banza,ance wai kazantar da mutum be gani ba,ai tsafta ce ko),


"Ai gwara da ka kira,don ko baka kira ba ina da niyar kiran ka,Ni fa daman tun randa na ga wanann Pookie in ta shige mun zuciya,big bro yane?,za a bani ita muyi magana Ni da kai?,ko in je gaban Mama direct gobe",ya kare yana danne dariyar shi,from no where Nameer ya ji zuciyar shi na mishi nauyi,a take ya ji ranshi ya ɓaci,wanda be san me yasa ba,Amman sai ya ke ganin kamar daga kamar da Mujaheed ya gama yi ne,"kayi shiru My Gee,ko dai

 sai mun hada da gurin Mama ne gobe,nayi sammako"?


Tsaki Namer ya ja wanda shi kanshi ya mance yaushe rabon da yayi ta,cikin bacin rai yace"Amman Allah Mujaheed kai dai ban san damuwar ka ba,yanzu kan wanann maganar ka sanya Mama cewa na kira ka,wlhy i thought wata zancan arziki za kayi mun",,"Ahh lalle sannu Nameer yanzu wannan in maganar tsiyace,Ni fa ba da neman banza nake son ta ba,suna nake son mu raya,auran ta xan yi",ya kare yana dariya kasa kasa,


Dogon tsaki Nameer ya ja kafin yace"Amman wlhy Mujaheed baka hadu ba,dududu yarinyar nan yaushe ka aure ta,kwata kwata yara biyu gare ku dai,shine har kake planning karo mata kishiya?,Are You for real!and mind you ita wace kake magana akan ta,kar ka mance yarinyar nan ita kanta ba fa ta san yanda kan ta yake ba,wani maganar banza ce ma wai ka na son auran ta,Aure!Aure!!as in how ma wai? Nan fa Nameer kamar wanda aka fadi wa wata babbar magana,ya shiga zubo wa Mujaheed bakaken maganganu,ta inda ya ke shiga ba ta nan yake fita ba,shiru Mujaheed yayi kawai yana sauraren yanda Abokin nashi ke zubo masifa,wanda ba zai ce ya taba jin tun tasowar su Nameer yau sun yi fadi in fada da wani ko wata ba,har ta kai shi ga yin masifa sai yau,mamaki yake ashe Nameer na da bakin tsiwa har haka,jin yaki yin shiru ne ya sanya shi kwashe wa da wata irin dariyar mugunta har yana rike ciki,a kufule kuwa Nameer yace 


       "A'a pls Mujaheed just hold it,ba na son iskanci,and could you mind explaining what the fuck you are laughing at?,kila nayi maka kama da joker ne?,ko kuma kana tunanin na samu tabin brain ne",ya kare a kufule,kamar zai daki Mujaheed in,


Cike da shakiyanci Mujaheed yayi wata yar gajeriyar dariya sanann yace"oh my God!,Nameerun Mama wai daman haka So yake ne wai?,zama ya gyara sanann ya daura da fadin,wai daman haka kake da zafin kishi,lalle ba sauki NADEEYA yar gidan Audu Waziri ta tafi da zuciyar Doc Nameer Abdullahi",ya kare tare da dan saka ihu,ba tare da damuwar dare bane,


Goshi Nameer yayi saurin dafewa,sai a lokacin ya shiga sauke ajiyar zuciya jin da wasa Mujaheed yake ba son Nadeeya yake ba,"Shege ai wlhy da nayi maka shiru zuciyar ka ta buga,tunda kai a rayuwa yarda da Ni ne kawai bakayi ba ,kuma na rasa dalili,in da ni ne jiki na bari zan kirawo ka,da dogon baki na in shiga zubo maka zance,Nima wlhy soon zan daina bude maka ciki na","Ni fa Mujaheed kar ka yi mun sharri,bana son sharri eheee,laifi ne don na ji tausayin ta?,yarinyar nan kamar amana take a gurina,so shine ya zama don nayi kokarin standing up for her,ya zama wai son ta nake yi"?,


"Kai dallah rufe mun baki,sai bakin magana,ji shi kamar da gaske,saidai ka fada wa Habeeb wanga zance ba wai ni ba,don ni kam Sarai ka san hali na,you better made up your mind as soon as possible,Ka fahimce kana so yarinyar nan,kafin ta dawo hayyacin ta,ta gan ni,tace in bani ba sai rijiya"ya kare yana dariya,"Allah Ubangiji ya shirya mun kai,think wat ever you want to think,ba zan ce komai ba","ka ma ce mana in ban fasa bakin rashin kunya ba,kana ji dallah kafin na mance dalilin kiran ka",zama Nameer ya gyara sanann yace" ina sauraran ka ",


"Yauwa" kana ji,nan ko ya kwashe duk yanda suka yi da Mal Hukmullah ya sanar wa Nameer,ya kare da fadin "mun yi da shi kan jibi a kawo ta,Amman na roke shi akan ya biyo ni mu je gida,kuma ya yarda so gobe in sha Allahu za mu je,ya duba jikin nata,shine daman nace bari na sanar maka kar nayi gaban kaina na ga Pookie in kishin ta ake sosai"ya kare yana dariya,


"Hmmm, Mujaheed ikon Allah,Ni dai ba zan fasa maka fatan shiriya ba,and na ji dadi sosai da kayi wanann tunanin,wlhy kwata kwata kamar wanda brain ina ya toshe,ban taba tunanin hakan ba fa,ko da na rana daya,Amman babu komai in sha Allah zan san yanda za a yi na shigo Kd gobe da wuri kafin ka zo da shi, don ma yanzu dare yayi ne da na dauko hanya",


"Da kyau Sharukh Khan baban yan soyayya,ya kare yana clapping hands in shi,Allah dai ya daga kafadun Pookie in mu,in ta kuskura tace bata yin aboki na in fasa mata baki,har sai hakwaran ta sun zuba","wlhy kuwa judge ne zai raba mu da duk wani dan iskan da yace zai taba Pookie"ya kare ba tare da ya san yaushe ne ma maganar ta fito ba, Mujaheed na kokarin magana,yayi saurin katse shi da "Malamijo am damn tired of all your surutu,ears ina har ciwo suke mun,abeg i want to rest,my regard to Jamila","before you hang up Ka taho mun da Masar Bauchi pls in da gasken za ka zo goben",ba tare da ya amsa shi ba ya kashe wayar tare da fadawa kan gadon shi,idanu ya lumshe,sai yanzu maganganun da suka tattauna da Mujaheed ke dawo mishi,akan me yasa ya ke jin zuciyar shi kamar zai fado a sanda Mujaheed ya ambaci yana son Auran Nadeeya,"Na shiga uku na, what's wrong with me ne?,ya tambayi kan shi ba tare da ya bai wa zuciyar shi daman bashi amsa ba,wanann daran be iya yin Bacci ba,haka kawai ya sanya wa kan shi tunanin wat if da gaske Mujaheed son Nadeeya yake, although ya sanya zai iya zama barkwancin Mujaheed,amamn wat if in ta warke kuma tace be yi mata ba,kamar yanda Mujaheed in ya fada,wata zuciyar ce kuma tace da shi,'banda abun ka, duk damuwar nan da kake na mece ce?,Nadeeyar da taimakon ta kawai kayi saboda kana jin tausayin ta,ko da tace baka mata ba miye zai dame ka,tunda ba son ta kake ba,da sauri ya yarda da maganar zucin nashi,a haka dai bacci ɓarawo ta sace shi,ba tare da ya sani ba,




       7:30 Am************


     Karan ringing in wayar Shi da ake ta kira nonstop ne farkar da Sen Rilwanu Audu Waziri daga wahalalliyar baccin da ta dauke shi a daran jiya,bayan yayi Mankasss da giya,


Da kyar ya iya bude idanun shi,da yake jin shi sun yi masa wani irin nauyi,kokarin tashi yake ya samu ya dauko wayar shi don ganin waye ke kiran shi haka cikin tsakan dare na Allah,Bara a bar shi ya huta ba,Saida wani radadin zafin da ya ji ya jiyar ci wuyar shi,da kafafun shi ne ya sanya shi saurin komawa ya kwanta,


Lamo yayi a kwance tare da lumshe idanun shi,domin ji yake kamar kan shi yana kokarin rabe wa gida biyu,shiru yayi for some mints ba tare da yunkurin kara mikewan ba, kafin can kuma ya bude idanun shi da har yanzu basu dawo farare ba,dakin nashi ya zuba wa ido,ganin yanda yayi kaca kaca,a nan ne ya matsa wa kan shi don kokarin tuno abinda ya faru a jiyan,da ya haddasa mishi tashi a wannan yanayin,gama tunanin nashi kuwa ya kara jin ranshi ya kuma baci,ji yake da jiya Kabiru be rike shi ba babu makawa sai ya kashe dan iskan yaron nan kowa ya huta,tsaki ya ja,sannan yace a fili"shi tsiyan Talaka ke nan,sam ba a iya dandana mishi arziki ba",jin har yanzu kiran wayan nashi ake ya sanya shi yin ta maza,tare da mike wa,har yanzu yana jin jiri,ga wani irin ciwon kai,a haka dai ya samu ya hade kan shi guri guda tare da saukowa daga kan gadon,ya nufi in da yayi jifa da wayar tashi a daran jiya, luckly expensive phone ce bata daina aiki ba,


Ba tare da ya san inda yake jefa kafafun nashi ba,ko har yanzu giyar bata gama sakar sa bane sai Allah,a garin haka ya tattake kwalban da ya fasa a daran jiya,a take kuwa suka huda mishi kafafu ya hau jini,saidai ko gizau be yi ba,balle ya lura da zafin da kafar tashi take,har ya isa gurin wayar tashi,dauka yayi a daidai Lokacin kiran ta tsinke,bin screen in yayi da kallo don ganin waye haka ke kiran shi cikin tsakiyar dare,saidai ganin karfe bakwai da rabi na safiya har ta wuce ne,ya sanya shi ɗan zaro idanu,"ashe har safiya tayi",shine abinda ya fada a bayyane,kara shigowar kiran Kabiru ne ya sanya shi saurin dauka tare da manna wayar a kunnan shi,


"Allah ja da ran Distinguished hope dai an tashi lafiya"?,ya fada cike da tsokana,dan tsaki Sen ya ja sannan yace"Kabiru ka mance kawai,kasan kwalbar giya nawa na sha a daran jiya kuwa?,wlhy wannan yaro anyi dan iska la'ananne,sam yaron nan ba yaron kirki bane,Kabiru da bakin cikin shi na kwan,da kuma shi na tashi,as in saboda shi tambadade ne last hope in nawa ya sanya kafa ya rushe ta"Sen ya kare kamar zai yi kuka,


"Calm down Rilwanu a kullum ina fada maka ba a handling situation ta zafin rai,komai cikin sannu da hankali ake bi har a dace a samu abunda ake nema,maganar kyautawa kan yaro be kyauta ba,Amman ya muka iya the damaged has been done already,so way out ya kamata mu nema ba wai mu tsaya tada jijiyoyin wuya ba",ya kare cike da lallami,"Kabiru ke nan wlhy da kasan yanda nake ji ko,uhmmm sai kuma yayi kwafa,wlhy ji nake kamar in sanya bindiga na harbe kan dan iska kowa ma ya huta",ya kare a zafafe,


"A'a Rilwanu ka san kuwa wannan ba best idea bane,kai kan ka,ka sani yaron nan in har ya bude bakin shi ,to wlhy ta ka ta kare,kana dauka Nadeeya ce kawai ta san sirrin ka,sannan kana mancewa da shi kan shi Afzaal in babu abinda be sani ba,ko dukan da kayi mishi jiya ban so ba,domin wat if yayi fushi yayi deciding ya bude mouth in Shi,ya kake tunanin zai same Ka?,shiru Rilwanu yayi don shi at times Yana mancewa da Afzaal kan iya tona mishi asiri wata rana,"yanzu dai abinda nake so da kai,shine ka shiga toilet kayi brush,kayi wanka,sannan kayi break,ka samu ka fara tunanin yanda za a samo me cikin nan don ka bada Sacrifice in Ka,kafin time ya kure maka,shi kuma Afzaal son samu ka bishi da lallabi in zai yu ma ka bashi hakuri,don am very sure ya ji zafin dukan da kayi masa jiya,na san yanda za muyi da shi,a Karan bana shike maganin Zoman bana,so duk ba wani abun daga hankali bane,ina da abubuwa ne a gaba na,don i think ma zan yi tafiya da na shigo gidan naka na duba ka,amman make kayi yanda nace sannan try to take care of yourself,in har da Odogwu i can feel it matsalolin ka sun kusa zuwa karshe",da haka ya samu ya kwantar wa Sen da zuciya,ba shi ya kashe wayar ba Saida ya kalli Sen ya sake har dariya yake yi,sannan yayi mishi sallama,yana me kara jaddada mishi kar ya manta da neman mace me ciki da Odogwu ya sa yayi.........

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


     This page is yours Daughter (my little Pookie),ina godia da kaunar ki a gare ni, ubangiji ya kara zaman lafiya ke da In law na,sannan ya kawo mana  yara na  gari nan kusa🫶🏻❤️

             

..........


My what's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


******************


    Tallah! Tallah!! Tallah!!



   

   Ina uwar  da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


  Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


   Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


    To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌

    

https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:

 

         08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌           


...........

          Page forty three 


**********



      ***********Doc Bashir


   A firgice ya mike daga baccin wahalan da be ma san lokacin da ta dauke shi ba, sakamakon sanyi da zafin da yake ji da ya hade masa lokaci daya,sakamakon ruwan sanyi da Aroooo ya watsa mishi,wanda yake jin sanyin ruwan har cikin kashin shi,zafin kuma kwance akan fuskan shi yake jin ta, sakamakon gigitattciyar marin da Afzaal ya dauke shi da ita,


Hannun shi dafe akan kumatun shi,ya mike ya zauna,yana me rawan ɗari,don yanda aka yada shi,a empty room in nan,ko arzikin pillow ko blanket be samu ba a dakin nan dandamalin kasa ya kwanta,inda yake cike da datti,at first kasa kwanciyar yayi,ya dade ya na nazarin yanda zai yi ya gudu,ya bar hannun wannan mugun yaron, amman sam be ga alamun akwai hanyar tsira, tunanin da ya raba dare yana yin su ke nan jiya,domin har iyanzu baya jin akwai abinda zai sanya shi mikawa Afzaal makudan kudadan nan a karon banza da wofi,yoo wallahi da yaron shi aka samu aka yi Kidnapping ba shi ba,babu abinda zai hana shi barin kasar,wayar shi zai kashe ya ci duniyar shi da tsinke sai in har dan kan su,sun ga damar sakin shi to,ya dawo gida gurin uwar shi,sai kuma aka yi rashin sa'a shi aka dauke,wallahi da ya san Afzaal yana da niyar mishi haka,da ya zage ya ci masa uba tun randa ya zo suka yi magana a Rimi clinic,



Tassssss Afzaal ya kuma dauke shi da wata gigitattciyar mari,wanda yayi saurin dawowa da shi hankalin shi daga karamin tunanin da ya fada,da sauri ya mike,hannun shi dafe da kuncin shi,da ya ke jin yana yi masa raɗaɗi kamar an watsa mishi barkono,shi ma Afzaal in mike wa yayi,idanun shi akan Doc Bashir,yana bin shi da kallon banza,wanda babu komai a cikin sa sai zallar tsana,


Bakin Doc Bashir har ɓari yake gurin fadin"Afzaallllll! Afzaal,Ni ka mara?Ido cikin ido Afzaal yace"An mare ka din,ko bayan kai akwai wani ne?Akwai uban da ka isa kayi mun don na mare ka ne?A kufule Doc Bashir da ke jin zuciyar shi kamar ta fado don bakin ciki ya yo kan Afzaal tare da cikumo kwalar rigan jikin shi,cikin dacin rai,ya shiga fadin"How dare you!Don Ka ga nayi shiru ba shine ya baka daman yi mun duk wulakancin da ka so ba,ko ban ci darajan komai ba ai na ci na shekaru ta ko?Tunda a babu a babu,tsaf zan baka 10 good years in ma be fi ba", hannu Afzaal ya sanya tare da gwaɓe mishi baki wanda Saida ya sanya shi sakin kara,



"Za ka mun shiru,ko sai na zubar maka da hakwara,to hell with the shekarun da ka fini,who fucking cares about your age? Kasan ya girme me mun din,me yasa shekarun naka be hana ka yi mun sata ba??And kana tunanin shekarun naka ne zai sanya na tausaya ma ka?,Mal hold your age to yourself and give me back my money,in sake ka salin alin ka koma wa useless family members in Ka",,,"Idan kuma na ki bayar wa fa?"Bashir ya fadi yana me galla wa Afzaal harara kamar idanun shi za su fado kasa, dariyar mugunta Afzaal yayi sannan yace "Ai wanda ya kai,ba ya fadan abinda zai iya yi,ko wanda ba zai iya ba,ya fi kyau ayi shi a aikace, bahaushe yace wai Me yi baya fada,Aroooo!Me kuke jira kun bar shi da yunwa,ina so ku bashi best breakfast ever"Ya kare yana murmushin mugunta,rufe bakin shi ke da wuya kuwa Aroooo da yaran shi su ka yo kan Bashir,ba tare da tausayi,ko imani ba,suka rufe shi da bugun tashin hankali,ta ko wani sassan jikin shi,a take kuwa ya hau ihu da kuka,a harzuke Afzaal yace"Aroooo ku rufe wa dan iska baki bana son jin kukan banzan shi,ai duk wanda ya kira ruwa,to shi kadai ruwa kan duka,Wawa shashasha,kana Na miji baka iya juriya ba",ya kare yana me jan tsaki,tare da barin dakin,ran shi a matukar bace,ya rasa ta inda zai bullo wa wanan me mugun taurin kan,ya samu ya karbi kudaden shi,in har ya ki bashi cikin sanyi,to ba yi da choice da ya wuce ya bi ta ko wani hanya,don ganin kudaden shi sun dawo,domin ya rantse da Allah ko kwandalar shi ba zai bar wa Bashir ba tunda shi ɗan iska ne maciyi amana,



**************Kaduna state


             

         "Wa nake gani kamar Babana"?Mama tayi tambayar tana me bin Nameer da shigowar shi gida ke nan da kallon mamaki,kai ya sosa cike da jin kunya  domin be sanar da ita kan zai zo ba,cikin kasa da murya kamar mara gaskiya,ya durgusa tare da cewa"Hajiya Mama ina wuni,na same Ku lafiya"?"Baba na muna nan lafiya kalau,me kuma ya dawo da kai,ina fatan dai lafiya ba wai wani serious abu bane,don na ga jiyan nan mun yi waya maman baka ce da ni kan za ka dawo yau ba"Ta kare tana me tsare shi da idanu,


Ganin yanda ta tsare shi da idanu ne ya sanya shi sunkuyar da kai sannan yace"Mama is just that am missing you guys sosai ne,ya sanya na ce bari na dawo na gan ku,ko zuciya ta zai yi sanyi,and mun yi magana da Mujaheed jiya,yake sanar mun kan cewa za su zo da Mal Hukmullah,to kin ga faduwa ya zo daidai da zama,kin ga ma  taimaka ko da a gurin tsayuwa a kan ta ne,Ni da nake don tabbatar da kayan ta be yaye ba",ya kare da iyakan gaskiyar shi,baki bude Mama take bin shi da kallo,wato dai in ta fahimta daidai,Nameer akan Nadeeya ya dauko hanya all the way from Bauchi zuwa Kaduna, murmushi irin ta su ta manya tayi,sannan tace"Sannu da kokari Babana,sannu da hanya,maza a shiga ayi wanka a ci abinci,na san duk inda Mujaheed yake sun kusa isowa da Mal,in ya so ayi komai a gaban naka",ta kare tana yar dariya,ba tare da yace komai ba ya shige dakin shi, zuciyar shi na gurin Nadeeya,don ya kwana biyu be ko sanya ta a idanun shi ba,haka kawai ya ke jin yana tsananin son ganin ta,kuma haka baya wuce da nasaba da zancen da Mujaheed yayi mishi,na cewa yana son Auran ta,duk da ya san Mujaheed in wasa yake,Amman yana tsoron kar ya zaga shi,ya sanya shi daukan leave a gurin aiki,dadin abun ma yau jumma'a,ya zo mishi a daidai za a shiga weekend,babu yanda Habeeb be yi da shi kan ya bari su zo tare ranar Asabar,har da Muhibba ma don ta na son ta ga Nadeeyar, amman yace ina be san zance ba,yau sai kwanan Kaduna,



A gaggau ce ya samu ya kammala wankan,cikin sauri ya shirya cikin jallabiya,turaruka ya fesa a jikin shi,a gaggauce ya gyara gashin kan shi,sannan ya fito,


"Baba na,ka fito daga wankan?","Eh wlhy Mama na fito,na dade ko?",ya tambaya yana murmushi,da kallo ta bishi sannan tace"Wani dade wa,Ni tunda na ke da kai ma,anya na taba ganin randa kayi saurin fitowa daga wanka irin na yau ba", murmushi yayi sannan yace"Mama sauri nake na kwana biyu ban ga Angel ba,am missing her like crazy","Angel ake missing ko Mommah in ta,Paaki take ko Popoo" Mama ta fadi tana dariya,kunya ce ta rufe Nameer ji yayi kamar kasa ta bude ya fada,wato gaskiya ne,duk yanda ka kai ga boye boye,baka isa ka boye wa wace ta kawo ka duniya komai ba, wai aka ce wanda ya riga ka zuwa duniya ya fi ka wayo,ganin yanda ta tsare shi da idanu ne,ya tabbatar mi shi da cewa amsan take bukata,hakan ya sanya shi zama kusa da ita,tare da riko hannayen ta,bude baki yayi da niyar magana suka ji sallamar Mujaheed,amsawa Mama tayi sannan tace da shi ya shigo,


"Mama!Wa nake gani kamar mutan Bauchi? Mujaheed ya fada ya me karasowa cikin parlor in,idanun shi akan Nameer,yar dariya Mama tayi sanann tace"Mujaheed taya ni duba wa fa, wanga Popoo ai yar gata ce, musamman aka zo gari ya gari,don ganin ta","Haba Mama nan dai nayi miki bayani tun muna mu biyu,kan dalilin zuwa na,Amman za ki ce haka a gaban wannan munafukin,ke ma Sarai dai kin san halin shi,dauka zai yi gaskiya ne ai"Nameer yayi caraf in fadin haka,yana me daure fuska irin kar ma a dauka don Nadeeyar ya dawo,



Dariya Mujaheed ya kwashe da shi,sanann yace"Allah dai ya bar mana ke Maman mu,kiyi tsahon rai,ki koya yaran Pookie yar gatan Gee ina",pillow Nameer ya dauka tare da jefan shi da shi,"Mujaheed kayi mun shiru ko na ci maka mutunci wlhy,ni munafurci ne bana so eheee,Ni ban shiga harkan mutan ba,don haka mutum ya daina shiga nawa"Ya kare yana hararan shi,



"Mama,kin ga Gee ko,daga fadin gaskiya yana neman cire mun idanu"Mujaheed ya kare kamar me shirin kuka,"Kyalle shi son,in tayi tsami za mu ji,zurfin ciki ne da wanann Gee in naka kamar yaya,kuma kar a kara jifan mun yaro da pillow,in ko aka taba mun lafiyar shi,ba yarda zan yi ba,sai mun yi Shari'a da mutum eheee",Mama ta kare tana kallon Nameer alamun da shi take yi,ganin za su yi mishi taron dagin,ya sanya shi share su, mikewa yayi tare da shigewa dakin Maman yana raya yanda zai ci mutuncin Mujaheed in sun hadu anjima,


A kwance ya tarar da Nadeeya,daga kwancen da take yake hango blue hijab a jikin ta,wanda ya karbi farin fatan ta, karasowa yayi tare da haurawa kan gadon yana me zuba mata idanu,ko keftawa babu,in ba idanun shi ba,sai ya ga tayi masa wani irin kyau yau,hancin ta makalle da feeding tube,ko dan be taba tsayawa ya kare mata kallo bane sai Allah,gashin gaban goshin ta ko in ce kai hade da sajen fuskan ta,ya kwanta luf,tayi wani irin haske da kyau,ga hancin ta nan Masha Allah har baka kamar an diga biro,shagala yayi yana me kallon ta,be taba sanin ana samun nutsuwa da kwanciyar hankali by kallon mutum kawai,ba tare da an yi magana ba sai akan Nadeeya,har wani ajiyar zuciya yake saukewa ,be ki ya kare rayuwar shi a haka yana me kallon kyakkyawar fuskan ta ba,ko motsi ba tayi ba,balle ya sanya ran ta san da shigowar na shi,a yanzu bayi da burin da ya wuce ganin samun lafiyar ta,itama ta warke kamar kowa,he misses her little sweet voice,with her cutest sweet smile,Yana fatan Allah ya dube su ta samu lafiya,a samu a cire wanann tube in,ta koma cin abinci kamar yanda kowa ke ci,ta yi tayi,ta zauan kamar yanda kowa ke rayuwar shi,itama a ce ta cigaba da nata Rayuwar,he just can't wait yayi rayuwa da ita a gida daya,don daga gani it will be fun living with her,



"Mama an wuni lafiya,garin tsokanar Nameer na mance ma ban gaishe ki ba","wlhy Alhamdulilah my son,yanzu na kama tunanin ka nace,kila aiki ya rike ka bara ka samu zuwa ba,ya aikin?",



"Wlhy Mama dan abu ne ya rike ni,kuma Saida na tsaya Malam ya gama karatu da dalibai, sannan na biya na dauko shi,yana ma waje a mota,yace na shigo in sanar da zuwan mu sannan ya shigo","Mujaheed gidan ku,yanzu ace tare kuke da Mal ka shigo,kana ta zuba ka bar shi a waje shi kadai,maza tashi ka je ka shigo da shi, Ba musu kuwa ya mike tare da fito compound in gida,inda motar shi ke aje ya nufa,Mal na ciki  a zaune yana jiran fitowar Mujaheed in,jargora yayi wa Mal har cikin parlon Mama,



Da sauri Mama ta gyara zaman hijab in jikin ta,tare da mike wa tana me amsa sallamar Mal,dan rusunawa tayi tana me yi mishi sannu da zuwa,cike da fara'a ya amsa mata,sannan suka gaisa cike da Mutun ta juna,zama yayi a daya daga kujerun parlon,sannan da kanta Mama ta shiga kitchen ta hado mishi abun sha,da kuma na motsa baki,gidan kawai yake bi da kallo yana observing in wasu abubuwa,


Bayan Mama ta zauna sun kara gaisawa,tare da yi mishi godiya,akan kashe schedules in Shi da yayi,don ya zo duba jikin Nadeeyar,sannan ta kare da ya ɗan taba wani abu mana kafin a fito da ita,


Murmushi kwance a fuskan Malam yace da Mama Azumi yake,ya kuma gode da karrama wa,in zai yu yana bukatar gaushi kamar a kasko biyar,don yana da bukatar kuna hayaki a gidan,sannan yana da bukatar sallaya,ruwa a dan baban kwano,sannan in zai yu a cire duk wani hoto da ke makale a jikin bango,a kuma rufe duk wani madubi da ke bude,sai a fito da yarinyar,bayan an yi clearing kan table in da aka aje mishi kayan dadi 😂😂,gudun kar a samu matsala yayin rukiyar,


Ba tare da bata lokaci ba Mama ta kira Zaliha,aka yi abinda Mal yace,sannan ya mike ya kara dauro alola,"Bismillah Hajiya a fito da ita, Amman so samu a daura mata alola kafin ta fito in",Malam ya kare yana me daidai ta zaman shi a nan kasan carpet yana me facing in sallayar,



"Son shiga daki Baba na yana ciki,ka taya shi fitowa da ita,fama nake da ciwon kafa,bazan iya dauko ta ba",mikewa Mujaheed yayi tare da nufan dakin Maman"yauwa ka ce da Zaliha ta shiga ta taya Ni daura mata alola kafin ku fito da ita",Mama ta kare tana me gyara zama,kai Malam ya girgiza yana me mamakin wanann bakaken shedanu da aka aiko wa baiwar Allah,"Wato har tafiya suka hana ta,Hajiya"Mal ya tambaya yana me jajanta lamarin,


"Hmmm wlhy Mal yau watan Ni nawa tana kwance kamar kayan wanki,bata uhmm bata uhmm uhmm,sai an daga an kwantar,ba tafiya babu magana, balle cin abinci,tana kwance dai ita ba me rai ba,kuma ba wace ta mutu ba",Mama ta kare kamar za ta yi kuka,dan murmushi Mal yayi sannan yace in sha Allahu Hajiya da yardar Allah ba yarda ta ba,wahalar ta ya zo karshe,in dai aka dace ba tafiya ba har gudu sai tayi,magana kuwa ko sabon gidan radiyo albarka",Ykare yana murmushi,itama murmushin tayi,kafin tace "Allahu ya sa, Allah ya amsa,amma wahala kam,ta wahalu,Allah ya sa bakin wahalan ke nan".......




Ayi mun afuwa hidima muke wallahi ya sanya kuka ji Ni shiru,na san yayi kadan,ayi hakuri ayi maneji🥺




        Ina masu sha'awar shiga Adashen online,inda za a rike miki Amanar kudi,ba tare da runto ko Ojoro ba,inda za ki zuba ki kuma kwashi kudaden ki, cikin kwanciyar hankali da yardar Allah,ba tare da wata matsala ko tashin hankali ba,


Akwai Matan da sam kudi be cika zama musu a hannu ba,da kin samu sharp an kashe su,someone like me🥺lol,to yar uwa ta shiga Adashe a nan ne,zaki tara kudin ki hankali kwance,



Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L7ai2fYGh4UAIK9MhC9awJ


Kindly ki shiga cikin group in nan,2500 weekly,I can assume you Bara ki samu any disappointment ko Damfara ko wani rikici ba, 


For more information,chat her up via:


       08149541182

 Sai mun ji ku🙌😍

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


     Wannan page in na Ku ne :


Fatima lawal(Maman Sultan)

Maman Humaira

Oum Maryam (momcey na)

Maimuna Aliyu(Mommy ta)


Kuyi yanda kuke so da page in nan sadaukar wa ce a gare ku,


Ina godia da dimbin  kaunar ku  a gare ni🫶🏻❤️

             

..........


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


******************


    Tallah! Tallah!! Tallah!!


   

   Ina uwar  da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


  Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


   Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


    To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌

    

https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


         08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌


...........

          Page forty four


**********


    Da sallama Mujaheed ya shiga cikin dakin Mama,inda ya tarar da Nameer ya shagalta da kallon Nadeeya da bata ma san wainar da ake toya wa ba, murmushi yayi tare da girgiza kai, ganin Aminin na sa be ma san da shigowar shi ba,matsawa kusa da shi yayi, tare da dakan kafadun shi da dan karfi,


"Mal talle,kar dai ka ce da ni Maita ka fara😳,ka kayi joining secret cult ne ban sani ba", Mujaheed ya kare yana me zuba mishi na mujiya,


A dan firgice Nameer ya juyo, domin be ma ji shigowar Mujaheed in ba,"Kai Wlhy matsala ta da kai Mujaheed har yanzu kana da sauran yarinta,yanzu kamar kai sai an fada ma,ana yin sallama kafin a shigo dakin mutane"?Ya kare yana hararan shi,"Ka kafe kyakkyawa a gaban ka da idanu kam,a yaushe daman kake expecting jin sallama ta,am sure ko su Mama da Mal da ke parlor sun jiyo,balle Kai,kila cikin kunnan ka zan zo in yi next time kafin Ka ji,by the way wannan kallon dai yayi yawa ga wanda ake jin tausayin ta kawai,irin wanga da ba dun ni Aminin ka bane na kuma san halin ka,ai da sai in ce kana shirin lashe wa baiwar Allah kuruwa ne,kallo haka an sake baki da hanci,kamar duk Kaduna babu mata,haba ai sai ka ba da mu wlhy","Mujaheed na rantse da girman Allah zan ci maka mutunci,wai kai,duk abinda nayi must you comment ne??Ka ga ka fice a idanu na tun wuri na rufe",cike da dariyar shakiyanci Mujaheed yace"Da gudu ma na fice Uban yan tausayin duk duniya,aswear to God da na san inda zani in karbo maka award na wanda ya fi kowa tausayi,da ko nawa ne sai na sanya kudi na siyo maka,cos you deserve it",ganin Nameer in ya yo kan shi ne,ya sanya shi fadin "Hold on Malam kar ka ji mun rauni,kayi mun bakin cikin samun zankaɗa ziya irin Pookie in na je Bauchi",kai kawai Nameer ya girgiza yana me bin shi da kallo,don in kace za ka sanya maganganun Mujaheed a rai,to kai ne kadai zai dama,yau da be san halin shi bane sai ya dame shi,


"Yauwa Uban yan tausayin kasa da kasa,Mama ce tace na shigo na sanar da kai wai ka kira Zaliha ta daura wa Hajja Pookie alola,sai in taya ka cicciɓan ta,mu kai ta parlor Malam na jiran ta",wanni uwar hararan da ya watsa mishi ne ya sanya shi,dimtse dariyar shi,ba tare da ya kula shi ba,ya mike tare da zare tube in hancin nata a hankali,sannan ya tallabo ta cike da nutsuwa,


"Kai amman tare fa Mama tace mu dauko ta,na ga kana kokarin daukan ta kai kadai,and tace Zaliha ta daura mata alola",


"Wai Mujaheed for God sake nawa Pookie take da har sai an ce mu dauko ta mu biyu,banda abun Mama,ni kadai ba sai in dauki Pookie in zaga gidan nan sau 50 tana baya na ba,and alola tun shigowa ta na daura mata,don haka mu je kawai,mun gode i can carry her my self",ya kare yana me tallabo ta kirjin shi,daman da biyu Mujaheed yayi maganar,don ya kunno Abokin na shi ya ji me zai ce,"Ke nan in je in ce da Mama,wai kace baka son shawarar da ta bayar,You can carry your babe by your own self"? Mujaheed ya kare yana me daga mishi gira daya cike da iskanci,harara kawai Nameer ya watsa mishi tare da ɗaukan Nadeeya cak a hannayen shi biyu,irin daukan Bridal  style,


"Malam Nameeru a je ta a tsakiyar sallayar nan",Mal Hukmullah ya fada wa Nameer yana me nuni da yatsan hannun shi inda za a aje ta,


Ba tare da musu ba kuwa Nameer ya kwantar da ita a in da Malam ya ce,ji yake kamar kar ya bar kusan ta, amaman Malam yace "yauwa Masha Allah,kana iya tashi",,ba tare da gardama ba kuwa ya mike,


"Hajiya za ku iya tashi ku shige daki,don ban sani ba ko kuma daya daga cikin masu tsoron Aljanu",Mal ya kare yana yar dariya, idanun shi kafe a kan Nadeeya da har yanzu ko yatsar ta bata motsa ba,


"A'a Mal babu wani tsoron da muke ji,we will all  stay"Nameer yayi carfa in fadi ,


"To Masha Allah,duk wanda be da alola a cikin ku,ya samu ya daura kafin mu shiga rukiya,and in kowa zai zauna dole Mujaheedu ya bar gurin nan,ko ya fice daga gidan baki daya,ko kuma a kulle shi a daki,don in Allah be kiyaye ba,a garin cire su na shi za su iya tashi,wanda ba ma fatan hakan,sannan duk wani abinda kuka gani,ko kuka ji,ku daure kar wanda ya tsorata ko ya yi kokarin guduwa,in kuma Bara ku iya zama ba tun wuri ku tafi a bar ni da ita",


Ba tare da Mujaheed ya ce komai ba ya mike tare da shigewa dakin Nameer,tare da umurtan Nameer ya kulle shi ta baya,Mal ne yayi shouting"Kar ka kuskura bakin ka ya yi sake da ambaton Allah,duk wani abinda za ka ji,fight it and hold on to praising Allah,in sha Allah babu abinda zai same ka",da haka Nameer ya rufe kofar sanann ya dawo ya kalli Mama,


"Mama ko zan kai ki daki ne"?,kai ta girgiza sanann tace"in da Khadijah ko Farouk ne a wannan halin za ka ce mun haka?,Nadeeya amana ta ce,kamar 'Yar ciki na na dauke ta,don haka babu inda za ni,ina nan har sai na ga yanda Allah zai yi da mu",ta kare tana gyara zaman ta,


Mikewa Mal yayi,tare da nufan inda Nadeeya ke kwance,zama yayi gefen ta yana me zuba mata idanu for some mints kafin can cikin kakkausar murya ya kira sunan ta"NADEEYA!!,ko gizo bata yi ba balle a sa ran amsa war ta,dan murmushi Mal yayi sanann yace"Bayin Allah,ina hada ku da girman Allah, kuyi hakuri,ku fita jikin yarinyar nan,kun azabtar da ita yayi yawa,ku sani in musulmai ne ku,ko kuma kafirai babu inda Allah ya hallata yin zalunci,ya haramta wa kan shi da kan shi,balle bayin shi,duniya karamar guri ne,duk daran dade wa dole za mu bar shi,mu koma gare shi,and na rantse muku da girman Allah sai kun tsaya a gaban 'Azza wa Jallah,sai ya yi mu ku Shari'ar cuturwan da kuka yi wa baiwar sa,ina me ba ku shawara ku fice cikin salama,sannan ku koma ga Allah ku tuba bisa biye wa son zuciya da ku ka yi,aka aiko ku jikin baiwar Allah bata ji ba bata,gani ba kuna daukan alhakin ta,domin shi Ar_rahman ne,sanann kuma Ar_raheem ne,da sannu zai shirya ku sanann ya yafe muku zunuban ku,Ni kuma na yi  muku Alkwari,in har kuka fita ba tare da kun wahala Ni, da ita ba,ba zan taba kona ku ba,zan bar ku cikin lafiyar ku,sanann zan taya ku neman yafiya a gurin ubangijin mu"


Ko gizau Nadeeya ba ta yi ba,balle ya sanya ran za ta amsa mishi,dan karamin dariya me sauti yayi sannan yace"ba wai ayoyin kona ku bane bani da shi,ba kuma wai ina jin tsoron ku ba ne,ina so wai na bi ku a hankali ne,domin ayi rabuwar mutunci,Amman tunda ku sam ba ku gaji arziki ba,bari nayi muku yaran da ko ba ku taba wucewa kun ji shi ba,zai ratsa ku,ya kona ku sannan ya fatatta ke ku,daga jikin ta,tunda ku mugaye ne makiya Allah,ba kuma zan muku ta dadi ba,tunda na nemi ayi shi a mutunce amaman Sam kun ce ba ku san zance ba",ya kare cikin bacin rai,don ya ga alamun Aljannun nan yan iska ne,shi kuma sam baya shiri da mugunta ko kuma sabon Allah,


Da zafin Nama ya mike,tare da bude jakar da ya zo da shi,kwalban misk,da Ma'ul khal ya dauko tare da kullin wa su magunguna,gaushin da aka kawo ya bi tare da barbada maganin da ke cikin kwullin a cikin ko wani kasko,nan take kuwa daki ta turmuke da wani irin wari,hayakin da ke fitar war kamar wani yajin barkono me dan karan zafi,a take kuwa ya shige wa su Nameer wuya suka hau tari,saidai Mal ko ta kan su be bi ba,hawa kan sallayan yayi,tare da dafe goshin Nadeeya,karo na farko da ta juya kanta cikin mugun firgita,kwafa yayi sanann yace"Ai ban so ma kuka nuna kuna kusa ba,da kun bari na gama kona ku da ayoyin Allah,kwa motsa a sannan ne zan fahimci ku din masu taurin kai ne",


Kwalban Misk in ya bude tare da dibo wa,be yi sanyi ba ya mulka mata shi a fuska da hancin ta,nan take kuwa tayi wani irin ba karewa wanda ya sanya Nameer saurin zabura zai mike Mama tayi saurin riko shi,


Kunnan ta Malam ya fitar daga cikin hijab in ta,sannan ya tsunguna tare da manna bakin sa a kunnan nata,cikin kira'ar sa me sanyi da dadin sauraro,ya shiga yi mata kiran sallah a kunne,a take kuwa ta fara wani irin numfar fashi,tare da jujjuya kan ta kamar wanda ake shirin zare wa rai, idanu Mama suka zaro domin duk tsahon zaman su da ita,ko yatsa bata taɓa motsa wa ba,balle har ta kai ta ga juya kai, ko dar Mal be ji ba,ila daukan ruwan da ya sa a kawo a kwano yayi,cikin iklasi ya shiga karanto ayoyin Allah tare da janyo ayoyin karya Sihiri sannan ya tofa a ruwan,kallon Nameer yayi bayan ya gama karatun sannan yace "Za ka iya rike mun ita?,don ana son ruwan ya ratsa makoshin ta",cike da kwarin gwiwa Nameer ya mike tare da nufan inda take kwance,


Dago ta yayi tare da matse ta tsam a kirjin shi,sannan ya karbi kwanon,bude bakin ta ya shiga yi,amman ina sam baki yaki buduwa,yayi yayi Amma ina a banza,ganin ya takura ta ya sanya ta shiga kiciniyar kwatan kanta,wanda hakan ya ba su mamaki, saidai Mal yace da su kar su damu daman haka aikin Sihiri yake,za su ga abubuwan ban mamaki,ya kada ya rawa ta sha ruwan ko kadan amman ta ki ko bude bakin ta a garin haka ma ta bude kwanon ruwan ya zube mata a jiki,inda a take ta kwala wani irin razananiyar kara,ba Mama kadai ba har shi kan shi Nameer Saida ya razana yayi saurin sake ta,


Dan dariya Mal yayi sannan yace Alhamdulilah,"tunda kun ce Bara ku fita cikin salama ba sai kun wahala baiwar Allah to nima kuwa ba kyalle ku zan yi ba,wallahi na rantse muku da girman Allah na,ba ku kadai zan kona ba har shi wanda ya aiko ku ba zan bar shi ba tunda ku ba ku gaji mutunci ba",ya kare ranshi a matukar bace,


Nan fa ya  tashi ya dauko wani dan zare a cikin jakar shi,hade babban yatsun kafan ta yayi tare da daure su kam,sannan ya dauko Ma'ul khal tare da sheka mata shi a hanci,da jin ya ratsa ta kuwa ta saki wani irin ihu,cikin wata razananiyar murya Saida dakin gaba daya ya dauka,cikin daga murya Mal ya fara karanto mata ayoyin rukiya,gurnani take numfashin ta na fita da kyar da kyar,


Duk wani ayoyin kona Aljanu da warware Sihiri su Mal Hukmullah yake karantawa,da yaki nin Allah ya dube shi Aljannun nan su bar ta,tun tana jujjuya kai har ta fara zunduma ihu cikin kakkausar murya,ihu take da iya kan karfin ta,tana birgima,fa sauri Nameer ya mike zai je gurin ta Mama ta rike hannun shi gam,


Hour guda Mal ya dauka yana rukiya iya galabai ta, Nadeeya ta galabai ta,tayi ihu tayi ihu kamar makoshin ta zai fashe,haka zalika ma kuka,ji take kamar ta kashe kan ta,saidai har yanzu bakin nan kirib babu abinda ya shiga sanann taki fadin komai, ganin haka ne ya sanya Mal kara rike wuta,rukiya yake da iya kan karfin shi yana watsa mata ruwan addu'a a fuska,wani irin bankarewa take tana wani irin gunjin kuka,ganin numfashin ta na neman barin jikin ta ne ya sanya Nameer fincike hannun shi daga gurin Mama,da sauri ya nufe inda take kwance dago ta yayi a take kuwa ta fada jikin shi babu numfashi tattare da ita,sai jini da ke malala daga cikin hancin ta,cikin raunanniyar murya Nameer yace"Mal na roke ka da girman Allah ka daka ta,kar ta rasa rayuwar ta,ko numfashi bata yi fa,ina tsoron kar fa mutuwa tayi,wallahi Mal i can't stand losing her,don Allah a bari haka",ya kare idanun shi sun kada, kamar me shirin kuka,jin haka ya sanya Mal yin shiru,a take kuwa jijigan da dakin ya ke ya tsaya cak,wata wawiyar ajiyar zuciya ta sauke tare da kara lafewa a jikin Nameer in har yanzu jinin be tsaya ba,


Mintuna biyar sannan kuma ya daidai ta a dakin,zama Mal yayi tare da cewa "Hajiya wannan dan na ki ya kamu da soyayya me zafi",ya kare yana murmushi,


"Malam kayi hakuri,ka san sha'ani na dan yau,kar ka kula shi a cigaba,ko sun fita a jikin nata"?,


"Suna nan basu fita ba,da dai ya kara hakuri suna gab da ficewa domin na riga da nayi musu ila,hakan ya sanya sam bana son rukiya a gaban family members,don za a samu me raunin zuciya,jinin hancin da kuke gani,duk dabaru ne irin na miyagun Aljanu,Amman babu komai in sha Allah nasara ta mu ce",,"Mal don Allah kayi hakuri,a taimake mu a karasa,kar ka kula Baba na tashi ma zai yi, in hade in  kulle su da Mujaheed"


"Haba Hajiya babu komai wlhy, sihirin ya kwana biyu a jikin ta ya sanya zai yi wahalar karyuwa, dole ta sha wahala,ban ga laifin Malam Nameeru ba,Hajiya babu wanda zai so ganin abun da yake so a wahale,don haka kamar yanda ya nema,a bar ta ta huta yau din, in ya so gobe sai a cigaba"


"Mal mun gode sosai goben,in sha Allah Ni da kaina zan kawo ta gurin ka,in tafi da shi sai an gama mu dawo don na ga alama Ni mace ma na fi shi juriya",


Nameer na jiyo su,pimmm be ce ba domin zuciyar shi baki daya na kan Nadeeya da har yanzu ba ta farfado ba,saidai jinin hancin ya tsaya cak,haka ma juyin da take yi,duk ta koma sak Nadeeyar da ko motsa yatsa bata yi,sai fuskan ta da yayi jawur ya kumbura haka ma kasan idanun ta,baya jin akwai abinda zai sanya ya kara yarda ayi wa Pookie so called Rukiyar nan,Rukiya ko ana neman a ga bayan ta,in da ba dun Allah ya  taimaka ba,ai da ba a cire Aljanu ba ita an raba ta da ran ta,a bar shi da asarar(Ni ko nace Nameeru na ka a wanne,😂😂,wai a bar shi da Asara,ku ji mun dan nema,kai da tausayin ta ka ke ji,a bar Sen Rilwanu da asara dai),


"Malam Pookie za ta farfado kuwa?,na ga har yanzu ko numfashi ba ta ja,ina fatan ba mutuwa ta yi ba ko",baki Mama ta rufe da hannun ta biyu,tana mamakin rashin kunya irin ta Nameer,"kai Baba na!Lafiyar ka kuwa ina manners in Ka suka tafi?,ta kare sounding serious,


"A'a Hajiya babu komai fa,kyalle shi don Allah,in sha Allah za ta samu lafiya karbi ruwan nan ka wanke mata fuska sannan ka bata ta sha,in sha Allah za ta farfado,",da sauri kuwa ya mike ya karbi cup in da Mal yayi tofi a ciki,cike da ikon Allah kuwa ya samu ya matse bakin ta ya zuba mata ruwan,tare da wanke mata fuskan,a take kuwa ta ja ajiyar zuciya,wani irin sanyi ya ji a cikin ranshi wanda ya sanya shi sakin murmushin da be ma san yaushe yayi shi ba,


Zaliha ce ta bude Mujaheed daga dakin Mama fitowa yayi yana tambayar"Mal hope an dace ina Amaryan ta mu in ja kunnan ta na wahala mana Gee ina da tayi ",


"Mujaheed babu kai babu jan kunann Pookie,da me za ta ji,in banda mugunta irin na ka nawa take da har za a ja mata kunne,and Ni babu wani  wahala ni da tayi ",ya kare yana hararan shi,tsaf ya mance Mama da Mal na zaune cikin parlon saida Mama ta mishi dakuwa tare da fadin"yayi kyau Baba na",



Mal ba su suka bar gidan ba,sai bayan sallan Magrib wanda shi ya ja su da kan shi, addu'oi sosai suka yi bayan idar wan su, sannan  Mama ta hado wa Mal kayan bude  baki,na alfarma,da kyar Mal ya yarda yayi iftar a gidan Mama,hakan ma saida ta kara da ko dai baya son ta samu ladan ciyar da me azumi ne?, guri su ka bashi ya karya azumin shi hankali kwance,sannan suka dauki haramar tafiya,godiya sosai Mama tayi musu,tare da jadada wa Mal kan ce wa gobe da wuri in sha Allah za su kawo Nadeeyar,


Nameer be so raka su mota ba,domin gani yake yana giftawa wani abu kan iya samun Nadeeya,Saida Mujaheed yayi mishi tass sanann ya rako su,


"Na Pookie ba da kan ka a guntile ka koma gida ka ce da Mama ya fadi,😂😂wato da gaske kake da kace mun za ka dawo, aswear to god na dauka tsiya kake mun,wayyo Ni Mujaheedu rabon da na ga irin wanga kauna tun ina neman Jamila","wlhy Mujaheed zan ci maka mutunci,Ni fa in ban shiga harkan mutun ba ya fita a nawa,ka wuce ka maida Mal gida tun raina be baci ba in ce ya aika maka Aljannun jikin Pookie ko za ta huta",mota Mujaheed ya fada yana dariya "haba Mal ai bude idanun ka tas ka kalle ni,na ci uwar aljanun ture na yaga leda",


"Subhanallahi Mujaheedu zagi kuma"Mal ya fadi yana tsare shi da idanu, tsaf ya mance gaban Mal suke,"ai Mal wlhh Mujaheed sai an hada da rokon Allah sam baya ji fa",dariya Mal yayi sanann yace "wanann maganar ku ce,Ni ba zan shiga ba,amman ana kiyaye halce banda zagi ko miyagun magana,domin ranar Alkiyama za a tsaida mu kuma za su maimaita, ubangiji ya kare mu ya kuma,tsare mana jin mu da ganin mu,na manta ka fada wa Hajiya a sanya karatu yau ya kwana yana yi,sanann ku tabbatar kun sanya mata idanu,domin gudun kar ku neme ta ku rasa,don jinnu babu abinda basu iya ba,a kuma kula da ambaton Allah",da haka suka yi sallama da su Mal Mujaheed yana ta tsokanan shi,saida Mal ya shiga tsakani,


"Baba na zo nan ka zauna,ka fada mun miye kake ta wani kananun maganganu tun dazu?,zama yayi kusa da ita tare da daura kan shi a kan cinyar ta,cikin muryan shagwabe da ya dade be yi ba yace


"Mama game da Pookie ce,anya za a kuma mata Rukiyar nan kuwa,ki ga fa Mama kamar za ta rasa ran ta,ina jin tsoron wani abu ya same ta","always think positively Baba na,Allah mu ka sanya a gaba in sha Allah babu abinda zai same ta,banda yau kayi interrupting ma ai da yanzu wani zance ake ba wanann ba,ko wani bawa da na shi ƙaddaran,and ka tuna babu cutar da Allah ya saukar babu magani,kai ka fi son ka cigaba da ganin ta a haka,ko kwance a gadon jinyar za a daura muku auran?Kana so mu sha dinner party babu Amarya ne",ta kare tana dariya


"Lah Mama kar fa ki biye wa Mujaheed,me ya kawo maganar dinner kuma","afuwan Baba na mancewa nayi ashe tausayin ta fa kake ji,in ta warke na baiwa Mujaheed ita,na san shi kam ba zai ki ba",,"shike nan Mama sai aka ce Miki ita kuma za ta yarda da Mujaheed in?In kuma tana da wanda take so fa?",


"Kai Ni kyalle Ni da maganar Popoo in nan,bari dai ta warke in ma gani,for now dai a tashi maza ayi wanka a ci abinci,don i can say tare kuka yi sharing pain in nan kai da Popoo in ta ka,so kana bukatar Hutu kai ma bayan long hours journey in da kayi",ta kare tana mike wa,


"Mama it's Pookie for Allah sake,not Popooo!, poopoo fa kashi ake nufi,and ita kuma Pookie ne name in nata"ya kare yana turo baki,


"Kai dallah kai suna ya dama,yarinya ga sunan ta nan me dadi,na yan gayun,an lakaba mata wani poopoo, ina dalili,ta kare tana kokarin shiga dakin ta,


"Yauwa Mama Ni kam ban ga Angel ba tunda na dawo","Ayya duniya wato sai yanzu aka tuna da yar marainiyar Allah","lah Mama wlhy ke ko,ya kare yana dariya,


"Na kai ta makota can za ta kwan saboda abun Rukiyar nan kar ya dame ta,kasan abun ka da yaro,yanzu haka hayakin nan ma ta fara damu  na,zan shiga in mata wanka,in bata ruwan addu'ar da Mal ya kawo,make sure dai ka ci abinci Ka kuma yi wanka,sai ka samu ka kwanta sai zuwa gobe da safe kuma ma maida ta,don da kunya mu ce Mal ya kuma zuwa",,"Mama yanzu don Allah sai ta kuma going through wahalar nan,ya kare kamar zai yi kuka,


"Fita a idanu na Baba na,in ce nan na gama maka bayani kamar ka gane,Majnun Sarkin kauna,ai ka bari a nema wa Lailan lafiya tukun na ko,maza ka je ka ci abinci zan shiga ina ji sai da safe",ba don ranshi ya so ba yayi mata fatan tashi lafiya sanann ya shige daki,ya so ko ba komai ya kara ganin ta,just to know wani hali take ciki,ko zai samu peace of mind,be san me yasa ba kwana biyun nan yake jin yarinyar very close to his heart,idanu wannan in ya rufe fuskan ta ke yi masa yawo,wanann daran kwana yayi yana Sallah yana roka mata sauki a gurin Allah,



***************

              4:30 na Asuba


Aroooo ke durkushe a gaban Afzaal da ke zaune kan wata plastic chair ran sa a matukar bace,


"Kai Aroooo wani irin sakarci da iskanci ne ke damun ka,a ce duk kwarewar ku a harkar garguwa da mutane,dan wannan small task in ya gagare Ku,yau kwana nawa eheee!!,ace har yau dan uban baban Bashir ya ki fito mun da kudade na,in an yi magana ku ce a ji tsoron ku don Allah ya baku muni da fuskan abun tsoro,kun je kun ci karfe kun yi building jiki,Amman brain kam zero babu shi babu alamun shi,kullum kuna cikin karban Kudi a guri na,babu result har yanzu me dadi,to wlhy na gaji da ciyar da katti,ba zai yi ku maida Ni dan iska ba,yanda mu ka yi da kai,tun ranar farko da kuka dauko shi,kace nayi hakuri ya farfaɗo a wannan ranar kudade na za su dawo,yau how many days suka wuce?up till now shiru ya kake son nayi?",ya kare a tsawace,


Cikin muryan bugaggu, Aroooo yace"Sai oga,na rantse maka ban taba haduwa da kolon dan iska irin wanann tsohon najudun ba,shegen taurin kai kamar jinjirin jaki,wannan da a zamanin Annabi Musa da Fir'auna ya zo,babu abinda zai hana Ni ce wa shi dan uwan Fir'auna ne",


"Kai dallah rufe mun baki,sai shegen zuba kamar sabon gidan Radio,ka san ba ka san yanda za a yi kudade na su fito ba,ka ce da ni i should trust you on this,aikin ku ne,24 hours ka bani kudi na za su dawo,yanzu har kwana uku,Jaki ka maida ni,ko Shashasha?",


"Oga wallahi wanann mutumin ba karamin dan Akuya bane,irin dukan da muke mishi kullum ya ci a ce,ya dade da fiddo maka da  zaran ka, amaman sam ibilis yayi mishi fitsari a kunne, Amman fa kar ka damu oga na san yanda za a yi da shi,


"Daka ta mun! Babu wani maganar ka da zan kuma dauka daga yanzu,tunda baka san abun da kake ba, banda shaye shaye babu abinda ka sa a gaba,tunda ya ce shi tsohon dan iska ne,Ni kuma Afzaal zan gwada mishi ni nan rikakken shege ne,ka rubuta ka aje a yau ba sai gobe ba kudade na za su dawo hannu na, in na so ma harda kafin riba,Will you get out of my sight!!kafin Rai na ya gama ɓaci in ci uwar ka da sanyin safiyar nan",da sauri Aroooo ya mike domin sam ya lura ba imani Afzaal ya fiya ba,"And don't forget Ku tabbatar kun bashi best breakfast ever wanda ko bayan ya tafi ba zai taba mantawa da shi ba",ya kare yana kunnawa weed in da ya gama rolling a Rizla wuta ya shiga zuga, yana tunano hanyar da zai bi ya karbo kudaden shi a hannun Bashir,don yayi rantsuwa ba kuma zai yi kaffara ba,yau ba sai gobe ba kudaden shi sai sun fito,


Daga zaunan da yake yana ji yo ihun azaba da neman daukin da Doc Bashir ke yi,bari yayi aka daka shi sosai,jikin shi yayi laushi,duk da be gan shi ba amman ya san a halin da yake ciki yanzu ko yatsar shi da kyar ya iya daga wa,tashi yayi cike da isa ya nufi dakin da Bashir in ke ciki,tun zuwan shi ba su bashi abinci ba sai ruwa, sai jiya ne ma da yayi Sa'a suka bashi 5 slices of bread,Yana ci yana kukan takaici,in banda yunwa babu abinda zai sanya,me kudi kamar shi cin gayan breads,


Nan gaban Bashir in ya zo tare da durgusawa,cike da muryan rashin mutunci,yace"Su doc an ci wuya,are You ready Ka bani,kudade na ko har yanzu taurin kai za ka gwada mun,in sanya a cigaba da ci mun uwar ka"?,


"Afzaal in za Ka sanya su kashe ni don duka,saidai su kashe domin sisi nace da kai ba fa zan ba ka ba,domin sam kai ba yaron kirki bane in taimaka in rufa maka asirin shine za ka yi mun haka akan abun duniya",ya fada a wahalce,


"Har kai kake maganar ni ba yaron kirki bane?Kai din tsohon arziki ne?,da kake maganar tona mun asiri,kai ne kake gudun tonuwar asiri,domin ka ganni nan,ko yau na je prison ba zan kwana ba ina da connection in da za a fiddo Ni,wani ko nan na ji labari,ko fly be je duba shi ba a sanda aka kama shi",ba karamin cakan shi maganar Afzaal in nan yayi ba,a take ya kuma jin babu abinda zai hana shi kara kaimi gurin cin uwar iyalan shi in ya koma gida,domin ƙarara suka nuna mishi rashin kauna a idanun duniya,


"Don haka shege ka fasa,in ka samu ka fita da ran ka ma shine za ka yi tunanin nuna wa Sen so called evidence in da kake da shi,Kai Ubaidullahi!!,na gaji da iskancin rainin wayon da kake mun,na bika ta lalalmi ka bani kudade na ka ki ji ko?,to wlhy bare yu ba,tunda har yanda kake na bi ka,na ce na yarda mu yi 50 50 akan kuɗi na, Amman ka nuna mun ka fi ni son su, har ka na ce wa,saida in sanya a kashe ka da ka bani kudade na da duka ko?To kwantar da hankalin ka tunda na ga alamun mutuwar ka ke da bukata,ido rufe ni nan Afzaal zan taimaka maka,yau ba sai gobe ba za ka bar duniyar nan,after that ban damu ba,in an zo biyan magada suke ko miye na sanar da su akwai bashi na a gurin ka,in ta kama ko gida da motocin ka a siyar a ban kudi na, amman for sure yau za ka bar duniya,zan maka kisa me zafi,da raɗaɗi,gaba ko da a lahira muka hadu za ka san shegen yaro ya fi tsohon dan iska",ya kare yana me mike wa,tare da kwalla wa su Aroooo kira,


Idanu a warwa je Bashir ya ke bin Afzaal da kallo,cikin shi ne ya ji,yayi masifan kulle masa,wani irin tsoro da firgici ne suka kama shi,ka fi ka ce me sai ga Aroooo da mutanan shi sun shigo,cike da ladabi yace"Sai oga,komai ya kammala, mushrikin kawai ya rage ka bada umarni mu jefa shi jahannama",ya kare yana nuna Doc Bashir,


"Afzaal me kake shirin sanya wa ayi mun ne?","dadi na da kai gaggawa,tunda ka ki mu yi a mutunce to Bashir Kona ka zan sanya ayi da ranka za a jefa ka cikin wuta,ko babbake,ka kone,Naman ka ya kwaile,qashi ya fashe,brain in Ka ya tawarwatse,kayi mutuwar wulakanci,tokan ka in zube su a ruwa,asiri a rufe babu uban da zai san Doc Bashir ya bar duniya,ko ba haka ba Aroooo",dariya suka kwashe da shi,


Ai nan take Doc Bashir ya ji kamar zawayi na shirin zubowa a wandon shi,"Me kuke jira Aroooo ba ku kama shege ba,wuta na ta ci a banza gwara an jefa shi kowa ma ya huta,and na ta tsere harda girman Allah tunda ka ce baka da mutunci Nima sai ka ga rashin imani na,ku tabbatar kun hada wutar ya hadu da kyau",ya kare yana busa A Z in Shi cikin kwanciyar hankali,


A take kuwa suka yo kan Bashir tare da kamo shi,yana ihu yana komai suka fita da shi, firgici be gama kama shi ba,Saida ya ga wutan da aka hada yana ta ruruwa tunawa wai shi za a jefa ciki ne ya sanya shi zunduma wani irin ihun neman agaji,rufe bakin shi ke da wuya,ya ji Afzaal na watsa mishi Kerosine a jikin shi,sannan yace"Aroooo ku tube shi tas, don me tafiya lahira wani sutura yake da bukata,na riga na watsa mishi Kerosine ana sanya shi bare yi wahalar zamo wa ashes ba",


Har ga Allah Doc Bashir be taba kawowa mugunta da rashin hankalin Afzaal ya kai haka ba sai yau,domin duk abinda yake mi shi,dauka yake duk as cika baki,be taba yarda Afzaal first class bane a yan iska sai yau,domin a yanda ya fada wallahi cak suka daga shi suna kokarin cilla shi wuta,ganin babu wani sarki sai Allah don daga yanda yake zafin tururin wutar na taba mishi fata,wani irin azaba mara misaltawa yake ji,be san sanda ya zunduma ihu yana pleading"Afzaal na haɗa ka da kaunar ka da iyayen ka kar ka kona Ni,wlhy na yarda mu yi 50 50 in,Zan sanya a kawo maka kudin yau yau ba sai gobe ba,don Allah majiya karfin nan su aje Ni kar su kashe Ni, wayyyooooo Allah na na shiga uku na lalace Ni Bashiru, Afzaal kayi mun rai,na roke ka,ya kare yana kuka domin saura Kiris ya ji shi cikin wutan,


Hhhhhhhhhhhhh"haba tsohon dan iska,ya kuma za ka ji tsoron karamin Shege da wuri haka,ba dai kai kace ba ka ji ba,wlhy na ci uwar ka na shanye a rashin ji",


"Na yarda da koma miye za ka ce, Afzaal kai ne babba kuma master na yan iska,na amince You have won I and  lost!Amman na roke ka,kar ka raba Ni da rayuwa ta, Afzaal Allah da kan shi ya haramta azaba da wuta,ka mun afuwa ka ce su sauke Ni"ya kare yana hawaye,domin har ga Allah Doc Bashir be taba tsorata irin na yau ba,yana da mugun tsoron wuta,ya sanya duk ƙan ƙantar shi tsoro yake ba Ni,


"Are You ready to return all my Money back to me?,ba tare da dogon tunanin ba Doc Bashir yace"Afzaal i swear to God Zan Kira a kawo maka kudaden ka,ko biyar ban ci ba, saboda na san ba kudi na bane",


Dariya Afzaal ya kwashe da shi sanann yace"Bashiru Ubaidullahi!ke nan,Ni na fasa ma ka rike kudin,ran ka kawai nake da bukata,shine ladar wahalar da Ni da su Aroooo da kayi",


A firgice yace "noooo pls Afzaal kar kace haka ka duba Ni,ina da yara kar ka maida su marayu kayi mun hakuri ka ji,ya kare yana kuka,


Da kyar da kai ruwa rana aka samu Afzaal ya janye maganar jefa Bashir a wuta,aka sauko shi duk ya bata jikin shi da kashi da fitsari 😂😂idanu sun yi lufu lufu,Ni ko nace daman ai in da kwadayi dole a samu wulakanci, 


Jiki na bari ya karbi wayar hannu Afzaal,da ya mika mi shi,cikin rawan da jikin shi ke yi,har wayar ma na faduwa a hannun shi yana kuma dauko wa,banda zufa,babu abinda ya ke yi,don har ga Allah ya firgita matuka,


Cikin rashin sa'a kiran farko da yayi a layin Hadiza har ta gama ringing ba a dauka ba,ganin kallon da Afzaal ke bin shi da shine ya sanya shi kara danna mata kira,domin duk matan shi ita ka dai ne,ya haddace number in ta,ita din ma dalili ne yayi dalili,cikin Sa'a kuwa har ta ku sa tsinkewa ta daga muryan ta dauke da sallama,


"Wato Hadiza don bakin ciki,da dauka na ba a bakin komai ba,har kin yi kaurin sunan da zan yi ta kira kina kin daukan waya na?,to wlhy da kin sake wani abu ya same Ni saidai ki kwan gidan ku,don ba zan dau iskanci da rashin kula ba",hararan da Afzaal ya maka mishi ne fa ya dawo da shi hankalin shi,tsaf ya mance da wayar wasu yake magana,hakan ma wai fa kira yayi ya sanar an yi Kidnapping in shi,cikin sanyi murya kuwa ya tsinkayo maganar ta,


"Me gida kayi hakuri,wlhy Hafiza ce babu lafiya,ga ta can kwance sai zazzaɓi take,sisin da za mu tafi asibiti ma babu,gashi ka ce kar uban da ya fita,ko ya kira ka,da na shiga makota ko bashi ne na karbo,kai na duk ya bi ya kulle, sanann ban dauka kai bane ganin bakon number,kuma na san ba dabi'ar ka bace kiran waya in kayi tafiya",kunya ne ya mugun kama Doc Bashir domin wayar a speaker take,


"Saurare ni,don Ni duk ba wanann na tambaye ki ba,Hadiza ko kin san,babu tafiyar da nayi,domin a hanya ta na tafiya yan garkuwa da mutane suka dauke ni",wani salati tayi saurin sake wa tana fadin"Kamar ya me gida wani irin yan garkuwa kuma,yanzu haka kana ina?",


"Hadiza ina parlor a gida ina shan coffee da naman kaza!Don iskanci in da na san yanda nake ai da yanzu bana kasar,ina fada miki an kame ni kina yi mun maganar banza,Are you normal?",


Nan take ta fasa kuka,tana cigaba da salati tare da fadin "shike nan asirin mu ya tonu,na abinci ma ba samu muke ba balle yanzu ana maganar kudin fansa,karshe Tijjani zan kira ya zo ya dau takardun gidan nan,a sanya shi a kasuwa a Saida a basu kudin su sako ka,ko wa sai ta koma gidan su da yaran ta in Ka fito ka san ya za ka yi, duk da ba dadin ka muke ji ba, Amma ya muka iya,hannun ka baya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar",ta kare tana jan hanci,


Ba su Aroooo ba har shi kanshi Afzaal Saida ya ɗan dara,yana mamakin mugun hali irin na Na miji,wato ko iyalan shi ba su son ya samu wannan makudan kudade ba,


"Kar uban da ya sanya mun gida a kasuwa Hadiza,50 mil suke da bukata,da sauri ta katse shi tana me dafe kirji"Na shiga uku na lalace ni Hadiza,mil 50  wannan kudi ai sun yi yawa,ko gidan aka daga aka siyar,a ina za mu hada wannan tulin kudin",


"Ke dallah ki rufe mun baki,ba ki bari mutun ya ida mutuwa kike kokarin binne shi,ki yi maza ki kirawo Tajo,ki ce da shi nace wai ya yi maza ya je WEMA bank,ya cike Form sannan ya ce su bashi 50 mil cash,sai ki ba shi jakar da babu wanda zai yi zaton kudi ya dauko,yayi maza ya kawo Dark real garden ya aje a gurin yanzu yanzu,saura ki tsaya kailulan ki na fa ma,da haka Aroooo ya karbe wayar daga hannun shi,


Tun sanda ta ji mijin nata ya ambaci wasu kudi masu shegen nauyi,da bata taba ji ko ganin su ba saidai a T.v a rayuwar ta,in har bata saɓa ji ba,kamar Bashir ce wa yayi a je a ciro Mil 50 daga account in Shi,waya ba shi kuɗaɗen nan?a ina ya samu?,ko dai rudewa ne ya sanya shi fadin haka?,sanin halin mijin na su ne ya sanya ta jan baki tayi shiru,tare da saurin nemo Tajo in(Tajo yaron Doc Bashir ne ,amintatce na hannun daman shi kuma,shine kadai yaron da ya yarda da shi a rayuwar shi,fiye da Matan shi da yaran cikin shi,don duk wani shige da ficen kudaden shi,Tajo ke mishi),


Ko da ya zo,Hadiza bata rai tayi,tare da ce wa Tajo"ya ce kayi maza ka je WEMA bank ka ciro mishi mil 52 cash,zan ba ka jakan da za ka je da su,50 in Dark real garden za ka je ka aje wai garkuwa aka yi da shi,ana neman kudin fansa,mil biyun kuma ya ce ka kawo gida ka bani na aje masa",bayan jajanta wa da ya yayi ta yi,sannan ya mata sallama bayan ta hada shi da jakan kuna,a take kuwa ya wuce bank in,


Be dauki lokaci me tsaho ba,da ke akwai idon sani,a take aka yi mishi cike ciken da duk ya dace sanann aka zuba mishi kudaden shi a haka,ya hayo mota ya dawo gidan Bashir in,time in da ya danka wa Hadiza bag in cash na 2 mil in nan suma ne kawai bata yi ba,ba ta taba sanin mugunta da mugun halin na miji ya kai haka ba,ace mijin ka uban yaran ka,yana da irin wanann kudin,Amman cefane na arziki ba yi yake a gidan shi ba,sutura wanann ba dinka wa yake wa iyalan shi ba,duk wani abu me kyau saidai yayi wa kan shi su kuma ko oho,in sun ga dama su tashi tsaye su nema,kullum yana musu abun karanta,ba karamin dadin wanann garkuwa da shi in ta ji ba wlhy,domin kamun Allah ne,kawai tace bari ta gwada daura wani abu a kai ka ga ko yana da kudin yake boye wa,sai ga shi zaton ta ya zamo gaske 2 mil cash rike a hannun ta,abun da bata taba zaton a duniyar nan za ta rike su ba,a take kuwa ta sanya aka kira wo doctor har gida ya shiga duba jikin Hafizar,ya gama a take ta biya shi,wanda ya so ba wa sauran matan mamaki domin a iya sanin su sisi babu wanda yake magani,


Ba tare da ta rufe musu ba kuwa,ta sanar da su duk yanda aka yi,mamaki da takaici kusan kashe su duka yayi,a take kuwa ta raba musu kudin,inda ta dau dubu dari biyar wa kan ta,Zahra ma ta bata dubu dari biyar,haka ma Amaryar su ma hakan ta bata,sauran dari biyar in kai da aka fara fasawa kuma ta kira babban danta aka zauna aka yi list in kayan abinci ,da dan abin da ba a rasa ba tace a siye na sauran canjin,ba karamin dadi da murna yaran da kishiyoyin ta suka yi ba,godia da albarka kam ta sha su sun fi kwando dubu,kafin suka shirya suka wuce kasuwa,


"Kai Aroooo are you sure kuɗaɗen nan sun cika 50 mil cash", Afzaal ya tambaya yana bin Aroooo da kallo,


"Sai oga zare sun cika dam,babu ragi,babu kari",ya kare yana mika wa Afzaal kudaden,


"To Bashiu ubaidullah!Yanzu wa gari ya waya hmm,upon all the pain and azaba da kayi going through last last dai ga kudade na a hanaye na,Ni ban taba ganin Wawa wanda be san ciwon kan shi ba irin ka,da tun da farko ka yarda da shawara ta da mun raba kudin nan a mutunce ka dauki share in Ka wuce Abu Dhabi ne,ko ina ne kasar da yake wakar shi kullum?,da sauri Aroooo yace"Los Angeles ne oga na",a tare suka sake wa Bashir dariya,kan shi na kasa yana me jin bakin ciki,dana sani ya fara yi akan me ma ya sanya ya fada wa trick in Afzaal yayi saurin cewa a kawo kudin,da ya dage a ba zai bayar ba ya san tabbas Afzaal be Isa kashe shi ba,don in ya kashe shi be san inda zai samu kudaden shi ba,sai a yanzu yake tabbatar wa da gasken shi wawan ne kamar yanda Afzaal ya fada,tsaban bakin ciki be san sanda hawaye suka fara zubo mishi ba,


"Aroooooo this deal is over,a tashi ayi shirin maida shi gurin iyalan shi,tunda  kudade na sun dawo",


"Afzaal ka duba kusancin mu,da irin rufa maka asiri da nayi,and all the struggles I have been through all because you,Ka kawo kudin nan muyi 50 50,"Doc Bashir ya fadi hakan yana fatan Afzaal in ya yarda,


Hannu ya sanya tare da buge mishi baki wanda Saida yayi jini sanann yace"tunda nake ban taba haduwa da mara kunya irin ka ba Bashir,don ka maida ki sa'an ka!Kudade na 55 mil ne na hakura na karbi 50 sanann duk da haka be ma ba,time in da na so muyi 50 50 in ai kin yarda kayi,sai yanzu ne za ka ce kana so muyi,to ba za a yin ba,ko ka bi su Aroooo su maida ka gida,ko wlhy in bar musu kai su cigaba da tatsan kudi a gurin ka,ko yanzu na nuna maka kai karamin dan iska ne wlhy,and ko gaba za ka kiyaye ba ko wani kudi ake ci a zauna lafiya ba,Wawa sakarai wanda ba shi da wayo", ya kare yana me watsa mishi kallon banza,Doc Bashir ji yake kamar ya tashi ya kashe dan banza,yau da yana da bindiga kuma ya iya harbi babu abinda zai hana shi kashe su Aroooooo da Afzaal ya dau kudaden shi yayi tafiyar shi,yana ji yana gani su Aroooooo suka watsa shi motar shi,sanann suka ja,babu abin da yake yi sai kukan zuci, ji yake kamar yayi manipulating in su Aroooooo su yi Kidnapping in Sen ko kuma Afzaal in, he just can't believe it wai kudaden shi da ya sha uban wahala akai yau out of the blue wani can ya kwace masa su,sai ya fashe da kuka,ko kallo be ishe su Aroooooo ba balle ya sanya ran za su ba shi baki ko wani abu,Saida suka kusa gari sanann suka fice daga cikin motar,suna masu yanka cikin daji,kifa kan shi yayi a kan sitiyarin motar,wani irin ihu ya fasa,yana jin zuciyar shi kamar zai fado,yayi kusan mintuna 30 a haka,kafin ya ba wa kan shi hakuri,tare da ɗaukan wayan shi,Allah ya so shi ba su taba mishi komai a motar shi ba,layin Tajo ya kira tare da kwatan ta mishi inda yake,kan ya zo ya kai shi asibiti don yana bukatar ganin likita,and a halin da yake ciki ba ya jin zai iya yin driving ya shigo cikin gari,




    ************* 

                           Kaduna state


Nameer ke ta kai kawo a parlon Mama sam ya kasa zaune ya kasa tsaye,ban da duban agogo babu abinda yake ta faman yi,


"Baba na ka zo ka ci abincin nan kar ya gama yin sanyi,ina lure da kai tun safe dai baka ci komai ba",


"Mama haba don Allah wanann wani irin rukiya ce haka ta ki kare wa,tun safe fa, tun around 8 mu ka kai Pookie gidan Mal,yanzu har Magrib ake nema,shiru shiru be ko yi waya ba,a taya zan ci abinci don Allah",baki bude Mama ke kallon shi,don daman can shi be so aka kai ta ba,wai wahala za ta sha,


Bude baki Mama tayi da niyar magana,wayan Nameer in ya hau ringing,da sauri yayi picking ganin Mujaheed ke kiran shi,


   "Angon Pookie ba da kan ka a sare","kai dallah Ni Mujaheed ka rabu da Ni,kana ma ina ne?","ka ji mun dan rainin wayo,munafuki in na kira ka angon Pookie har kasan ranka dadi kake ji amman shegen iyayi wani wai in rabu da kai,to an ki rabuwa da kai din",ganin za su tsaya fadi in fadan su mara amfani ya sanya Mama karbe wayar,


"Assalamu alaikum Son ya ake ciki,ka ji daga gurin Mal kuwa?",Saida ya gaishe ta sannan yace"Mama shine ma ya ce in ce da ku wai ku je,amman kin ga Gee zai tsaya mun iyayi","rabu da shi Mujaheedu,wai fa nan tsaban tausayin yarinyar nan har abinci mutumin ka kasa ci yayi",Mama ta kare tana dariya,"Lah ai Mama kina shirun ki soon za ki ga Award an bashi na best of masu tausayin duk duniya",shima ya kare yana dariya,


Daki Nameer ya fada a gurguje ya kimtsa kan shi,don shi ba ta Mujaheed da Mama yake ba,in yace zai tsaya biye su ran shi ne kawai zai ɓaci,ko da ya fito samu yayi sun gama wayar,Mama ta aje mishi wayar akan kujera ta tafi shiryawa daki,Saida ya jira ta gama shirin sannan suka fito,ji yake kamar Bara su isa gidan Mal ba,don Saida suka biya suka dauko Mujaheed,sanyawa Mama tayi suka tsaya a kasuwa kayan abinci aka siya tare da su sabulun wanki da Omo,sanann suka dauki hanyar gidan Mal kowa da abinda yake sakawa a ran shi,


Ko da suka isa,iso aka yi musu har parlorn Mal,inda Matan Mal suka shigo aka gaisa cike da fara'a da mutunta juna,sannan suka ce Mal in na wanka,sun dan jira shi kadan kafin ya gama kimtsa wa ya fito,

Cike da fara'a shi ma suka gaisa sanann ya gyara zaman shi da kyau,yana dan tsokanan Nameer in,


Cike da fargaba Mama zuciyar ta na bugawa ta dai daure ta ce"Mal ya ake ciki,an dace kuwa?,"Hajiya gaskiya sha'ani na jinnu akwai wahala, su wahala wanda suke jikin shi,haka zalika kai kan ka me cire wa wahala ka suke,yi tun safe da kuka kawo ta,muke tsaye a kan ta,ban taba ganin Sihiri me karfi irin nata ba,idan nace zan baku labarin wahalan da muka sha sai kun yi mamaki,wlhy Hajiya tun safe kin ga sai yanzu Allah yayi na samu na zauna bayan nayi wanka,dan jim yayi sanann ya cigaba da fadin,daman na fada Miki nasara ta mu ce Hajiya,duk bayan ko wani tsanani akwai sauki,Allah cikin ikon shi ya bani Sa'a na samu damar karya wanann sihiri da ke jikin baiwar shi,ba ma wannan kadai ba su kan su Aljanun ban bar su ba saidai na musu mummunan rauni,in da gaba ko ya aka yi da su Bara ma suyi lafiyar da wani zai samu daman using in su don cutar da bayin Allah ba,domin bakaken Aljanu ne",wani irin kabbara baki daya suka sake, Nameer ji yake kamar ya tashi ya je ya rungume Mal tsaban murna,


Cikin muryan murna yace"Mal kana nufin shike nan ta warke,za ta iya magana,tafiya harda zama da cin abinci",yayi tambayar kamar wani karamin yaro,Saida Mal ya dan dara sanann yace"duk za ta yi fiye da hakan ma Mal Nameeru,jiki kam ai yayi kyau,in sha Allah ba Aljanu ba babu wanda kuma ya isa ya kara kokarin cutar da ita,da can ma saboda karancin tsari ne da babu a jikin ta hakan,ya sanya duk wani irin nau'in jifa ko asiri bare yi wuyar kama ta ba",babu yanda Mujaheed be yi a sanar musu waye yayi turan Aljanun ba amman Mal Hukmullah yace sam ba a haka,hada husuma ce tunda an dace ta warke,ai lafiya Lau,sannan shi kan shi wanda yayi abun ba zai tsira ba,don da kyar in out of anger Aljanun ba su taba shi ba,


Nan ya zauna yayi ta jan hankalin su tare da ba su shawarwari yanda za su tafiyar da rayuwar su,duniya da lahira su tayi kyau bisa tafarkin koyarwan Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama,sannan ya nuna musu mahimmancin rike Azkars in safiya da maraice,tare da falalan kwana da kuma yawan zama da alola a jikin mutum,sannan a karshe ya kuma hora su akan mika dukkan nin lamuran su ga Allah,duk rintsi kuma su guji cutar da dan Adam,sanann ya rufe da tunatar da su amfanin yawaita zikiri ambaton Allah,salati ga Manzon mu,rike sallah sannan kuma yawaita karanta Alqur'ani,


Magunguna ya baiwa Mama tare da yi mata bayanin yanda za a na wa Nadeeya amfani da su,ya kuma kara da duk sati ana kawo ta gurin shi har zuwa wasu lokutan da ya iba, don yana son yana observing in jikin nata,don in ya fahimta daidai wanda yayi turan nan ba barin ta zai yi ba,don tun bugun farko ya gano so ake a bada soul in ta ga dodon tsafi amman Allah be yi ba,yayi mamaki sosai ya kuma ga abubuwan al'ajabi da yake mata rukiya,haka tayi ta aman jini da wasu bakaken abubuwa,Sihiri me karfi ne a jikin yarinya,wanda cikin yardar Allah Saida ya raba ta da shi baki daya,


Suna nan gidan Mal har bayan Isha'i, sannan suka yi haramar tafiya,don Mal yace Nadeeya is so weak,tana bukatar taimakon asibiti kuma,godia sosai suka yi mishi,Nameer ne ya dauko ta,wanda har ranshi ji yake kamar yayi ta mata kuka,don kallo daya za ka yi mata ka fahimci ba karamin azaba da wahala ta sha ba,ta galabai ta sosai,don kar a ma ce ya wuce gona da iri ne da sai ya ce har ramewa tayi daga jiya zuwa yau in,but Alhamdulilah tunda an dace ai shike nan,a bayan mota ya kwantar da ita,kan ta na kan cinyar Mama,


Ko da Mal ya ga tilin kayan abincin da suka kawo,Sam cewa yayi ba zai karba ba,da kyar Mujaheed da Nameer suka shawo kan shi,don shi gani yake wai ladan aiki suka biya,wanda shi kuma yayi ne tsakanin shi da Allah yana jiran ladan shi a gurin Allah,dubu dari biyar cash Nameer ya aje wa Matan Mal,sanann ya kuma ba wa Mal wata dari biyar in ya ce ayi sadaka wa almajirai,sai sannan Mal ya tuna,yace"ku yawaita yin sadaka domin ita sadaka tana tunkude masifa",a haka dai suka samu Mal ya karba kudin da kyar,Saida ma ya ji kalman sadaka sanann hankali ya kwanta,


Cike da mutunta juna suka yi sallama,har waje Mal ya rako su,yana tsokanar Nameer kan yayi haba haba in Nadeeya ta gama warware wa a daura musu aure,kafin wani ya riga shi,


"Haba Mal ai shi Nameer da kake gani, tausayi ne da shi sosai,yana da pure heart of gold ne, amman sam ba son ta yake ba,Ni ne dai Mama tace za ta bani ita,in yi na biyu daman", Mujaheed ya kare yana dariya,


Da sauri Nameer ya kunna mota sannan yace"Mal koma ciki abun ka,ka samu ka huta,iska ke wahala me kayan kara,don ko zai mutu ba bashi ita zan yi ba",da sauri Mama tace"Kwantar da hankalin ka Mujaheedu yarinya dai diya ta ce,zan ga wanda ya isa ya fi ni iko da ita,in kana so Ni kuwa zan baka",Nameer be ce komai ba sai taka mota da yayi,Mal na dariyar drama in su suka yi sallama sanann suka dau titi,Saida suka biya babban chemist suka hado duk wani abubuwan da ake bukata sannan suka biya suka aje Mujaheed a gida yana ta faman tsokanan Nameer, shi ko Nameer banza ya baiwa ajiyar shi don hankalin shi tas na kan Pookie,



    Bare with the typing Errors 🥺ban yi editing ba,



     More comments more updates 😸


         

            Ina yi wa kowa fatan Alkhairi.



Ina masu sha'awar shiga Adashen online,inda za a rike miki Amanar kudi,ba tare da runto ko Ojoro ba,inda za ki zuba ki kuma kwashi kudaden ki, cikin kwanciyar hankali da yardar Allah,ba tare da wata matsala ko tashin hankali ba,


Akwai Matan da sam kudi be cika zama musu a hannu ba,da kin samu sharp an kashe su,someone like me🥺lol,to yar uwa ta shiga Adashe a nan ne,zaki tara kudin ki hankali kwance,


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L7ai2fYGh4UAIK9MhC9awJ


Kindly ki shiga cikin group in nan,2500 weekly,I can assume you Bara ki samu any disappointment ko Damfara ko wani rikici ba, 


For more information,chat her up via:


       08149541182

Sai mun ji ku🙌😍

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


     This page is yours dearest Fanash Scents 


Ina godia da kaunar ki  gare ni🫶🏻❤️

             

..........


My What's app group link


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


******************


    Tallah! Tallah!! Tallah!!


   

   Ina uwar  da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


  Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


   Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


    To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌

    

https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


         08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌


...........

          Page forty five


**********


     5 days later


     A guje ta biyo Haanan,kamar wanda suke tsere,babu abinda Haanan in ke yi banda kyalkyale dariya,domin har cikin ran ta,dadin bin na ta,da Nadeeya ke yi ta ke ji.


Buguwa da tayi da Nameer da ke kokarin shigowa cikin parlon ne ya sanya ta ja da baya tare da yin taga ta ga za ta fadi,cikin zafin Nama ya sanya hannu tare da janyo ta,yana manna ta akan kirjin shi,idanu ya zuba mata wanda ita din ma shi din take kallo,for some mints kafin ta bude bakin ta within a blink of an eye,ta watsa mi shi ruwan brush in da ta kunshe a bakin ta,ai da Jin ruwan ya ratsa fuskan shi,be san sanda ya sake ta ba,timmmm ka ke jin ta fadi a kasa ta buga bom bom in ta,wani irin talle baki tayi,cike da shagwabe ta fashe da kuka.


A take kuwa Nameer ya rude,sai ya hau blaming kan shi akan why ma ya sake ta,what if ta ji wa kan ta ciwo fa?,just because of dan ruwan brush in da ta fesa masa a fuska shine zai sake ta,har tayi irin wannan buguwar haka.


A hankali ya riko soft hand in ta,tare da damke wa a cikin na shi,cikin murya kasa kasa yace"Hey Pookie!"Dago Lulu eyes ɗin ta tayi idanun ta sharkaf da hawaye daga gani kasan na sangar ta ne ta zube su a na shi,"Am sorry okay,pls can you stop crying?,ya kare kamar zai fashe mata da kuka shima.


Baki ta bare tare da sakin wani sabon ihun,wanda ya firgita Mama, wanda bata san time in da ta fito daga daki ko dan kwali babu a kan ta, hankalin ta a tashe don daga jin kukan Nadeeyar ta san ba na lafiya ba,turus tayi da ta fito ta gan su nan durgushe yana ta aikin ban baki,in da, Nadeeya ta face hannun ta sai jibgan shi ta ke,ta ko ina.


"Baba na me kayi mata?Mama ta tambaya tana me tsare shi da idanu,da sauri Nadeeya ta mike tare da nufan Mama,tana me fadawa jikin ta,cikin hauka da ta fara maida ta kamar yarinya karama tace"Mom Papa  pushed me and ya sa na buga Bom bom in na" ta kare tana kokarin dage dogon sleeping gown in jikin ta,a zummar nuna wa Maman  bom bom in na ta da ta buga,har yanzu kuma tana kan kukan.


Da sauri Mama ta riko ta,tana girgiza kai,wato ƙwaƙwalwa shine komai a jikin mutum,duk wanda ba shi da shi,shi da dabba ma daya suke,cikin muryan lalashi tace"stop crying darling,bar Baba na zan zane shi ne tunda ya sanya mun ke kuka",ta kare tana me rungume ta a jikin ta,juyowa tayi fuskan ta dauke da dariya wanda ya kara wa farin fuskan ta kyau,har yayi sanadiyar lotsawar gefen kumatun ta (dimple),sannan ta zaro tongue in ta alamun wai gwalo😝take mishi,irin Mama tace za ta zane shin nan,baki ya turo gaba tare da yin narai narai da fuska sannan ya yi pointing in Kan Shi,yana tambayar ta kasa kasa,Ina ni ko??,da sauri ta daga kai tana kara zaro mi shi tongue in nata.


"Mu je maza ayi shirin wanka kuma ko?, kin ga Haanan tayi miki wayo, ta riga ki yin brush,haka ma wankan ma tana son ta riga ki"Mama ta kare da yaran turanci,don tun farfaɗo war Nadeeya sun lura ba ta cika yi mu su Hausa ba,ba musu kuwa Nadeeya ta bi bayan Mama,tana juyo wa,tana yi wa Nameer dariya da gwalo,har suka shige dakin Mama.


"Alhamdulilah"shine abinda Nameer yayi murmuring,wato God have been so great to him,babu abinda zai yi wa Allah sai godia, Mujaheed,Mal da Mama ba yi,da abinda zai biya su da shi sai fatan su gama lafiya Allah kuma ya dube su,ya ba su Aljanna,domin ba karamin rawa su ka taka a rayuwar Nadeeya ba,tun ranar da suka dawo da dare,ya daura mata drip tare da alurai,yana tunanin she is so weak, har yana tsoron ko sai ta kai su ga zuwa asibiti ne, Amman cikin iko na Allah washe gari,tun asuba ta tashi musu da kukan banza.


Be taba kawowa zai kuma jin muryan ta nan kusa ba sai gashi kafin safiya ta cika su da surutu,sai a lokacin ya kuma jin dadin shawarar Habeeb domin shi ya bashi shawarar ana yi mata physical therapy,in da be yi rejecting shawarar ba,a take ya tuntubi wani friend in Shi wanda ke aiki nan cikin 44 hospital in,ya biya shi kudi inda duk sati yake zuwa har gida sau uku a sati ake yi mata Musculoskeletal Physiotherapy (the most common type, which deals with musculoskeletal system, encompassing bones,muscles,and joint), cikin yarda da iko na Allah ko da ta tashi farfaɗo wa bayan tashon  kwanaki da ta dauka tana kwance,tana tafiyar ta ko ina,amfanin gashin qashin ke nan,don da Habeeb be yi dabarar nan ba, shi sam be zo kan shi ba,da sai bayan warkewar ta kuma a shiga kiciniyar koya mata yanda ake tafiya da zama.


Alhamdulilah jikin Nadeeya tai kyau,tana cin abincin ta,da kyau burin shi ya cika,tana iya cin abinci ta sha ruwa da ice cream kamar kowa,don har yanzu be mance tana kaunar ice cream ba,hakan ya sa,duk dare na Allah sai ya siyo mata,tana zama tana tafiya,gashi har yau ya gan ta suna guje guje da Haanan,don da suka dawo Mama bata yi wasa ba gurin bata maganin gurin Mal,haka zalika gidan kullum ba a raba shi da karatun Alqur'ani,shi da kan shi ya yarda Nadeeya is a fighter,domin jikin ta respond to treatment cikin sauri,yarinyar is very strong.


Tunda Allah ya yi bakin ta ya bude haka take cika su da surutu ita da Angel domin daukan kan ta take kamar Angel in,in akwai abinda ya rage mishi a duniya yanzu be wuce ganin Nadeeya ta rabu da cutar haukan nan nata ba,duk da ma Mama tsaye take a kan ta babu wanda zai ce Mahaukaciya ce ita,Sai dai ɗin ta yi wani abun rashin kan a gaban mutum nan a ke sani.


Wata irin shakuwa ta ban mamaki ne ya shiga tsakanin Nameer da Nadeeya,kullum tana makale da shi,haka zai kashe duk ayyukan gaban shi don ya zauna tare da ita,Habeeb yayi kiran duniya ya ki kula shi,abincin wanann tare suke ci,wani irin kyakkyawan tattali yake bata,tare da kula, kullum suna makale da juna,Papa take kiran shi domin haka ta ji Haanan na  kiran shi,kamar jela duk inda yake haka za ta zo masa,ita da Haanan,in abun ya ciwo ta kuwa har Angel make ta take yi,a haka dai cikin lallami da tattali,Nameer ke kulawa da ita,kudi masu nauyi ya ware tare da yi mata siyayyan kaya masu kyau da aji,Mama ta sanya aka dauko me saloon ta zo har gida,da daru da kuka,doke doke aka samu aka wanke kan nan da yayi datti tas,ba yanda ba a yi a mata kitso ba, Amman ta ki zama sam, ganin haka ne ya sanya aka mata gyaran kai,na gani na fada,nan take ko ta fito kamar wata Barbie doll 😍.


Kai ya girgiza,ji yo ihun ta, daga dakin Mama ga dukkan alamun shirya ta ake yi,jin kukan na ta ya ke har cikin ran shi,amman ya san in ya je Mama sai ta yi masa tas,don jiya ma Saida ta yaɓa mi shi magana,a kan wai miye ta ha ya na wani,shishige wa Diyar ta,kar fa ya mance ba son ta ya ke ba,tausayi ne,kuma yanzu Alhamdulilah sauki ya sa mu,so ya ci ace an daina tausayin haka nan,daura wa tayi da fadin"jira na ke ta warke,My son ya fara zuwa zance gurin ta,domin ya nuna yana so kuma Ni kam zan ba shi ita",be ce da Mama komai ba ila barin gurin da yayi,tun wannan ranar be kuma barin Mujaheed ya zo gidan ba,da yayi maganar zuwa to in sha Allah ka fin a dau time zai shirya saidai Mujaheed in ya gan shi a gidan sa, Although deep down ya san Mujaheed ba son Nadeeya ya ke ba,in ba haka Allah ya rubuta ba ma,ba zai taba auran ta ba,domin shi kan shi sheda ne da irin kaunar da ya ke wa Jamila,ya rasa sanin me ya sa a kullum in Mama suka yi irin maganar nan ya ke ji kamar ya rataye kan shi,wani irin nutsuwa da kwanciyar hankali ya ke samu a duk sanda ya ke tare da ita, ya kan ji rashin nutsuwa a duk sanda ba ta ku sa da shi, abinda ya hana shi komawa Bauchi ke nan,Mama tayi magana ya ce wai yana leave ne,sannan so ya ke ya ga ya yana yin jikin na ta tukun na, before dai source of joy in Shi bayan Mama Angel ce,domin ta na daya daga cikin abun da ke sanya shi farin ciki a rayuwar duniyar nan,to yanzu kuma yana jin Nadeeya so very close to his heart, ringing in wayar Shi ne ta dawo da shi daga tunanin da yake yi.


"Angon Pookie ba da kan ka a tsare,ya aka yi ne mutumin",goshi Nameer ya dafe tare da shigewa dakin shi yana me zama a bakin gado sannan yace"Mujaheedun Jamceey ikon Allah",dariya duk suka sheke da shi.


"Ya kana gida ne,ina so in leko daga nan ma samu mu zanta Ni da Pookie ta".."Mujaheed na rantse da Allah zan fa ci uban ka!Wai me ya ke damun ka ne?.."Soyayya da kauna"yayi saurin ba shi amsa,"thunder fire that love and affection da ka ke magana a kai,yo an ce ma ka,ban da hankali ne da zan dauki Pookie in Baka"?,"Dadin abun mutum tausayin ta kawai ya ke ji ba shi ne uban ta ba,ban zan ji wahalar wanke kafa in tafi Bauchi gurin Sen neman auran diyar shi ba,kuma sai ka ga abun rabo ne ya bani ita",wani dogon tsaki Nameer ya ja sannan cikin bacin rai yace "wai kai Mujaheed son ta kake yi ne?,na ji in ma kana son na ta,Jamila fa?"..."in ban so ta ba,kai son nata ka ke yi?,yayi tambayar ya na me fatan Nameer ya amayar da soyayyar da ya dade yana yi wa Nadeeyar,domin be taba sanin Nameer sakarai bane sai yanzu,ya dade da gane  Nameer in ya kamu da muguwar kaunar Nadeeya,wanda shi kan shi be ma san son na ta yake yi ba,har ya ka sa controlling in Kan Shi ya fito da kishin da yake mata ƙarara,rashin sanin halin da ya ke ciki,ya sanya ka na taba shi zai ce ma ka wai tausayin ta yake ji.


"Ni ban ce maka ba,kawai ina ta ya yar uwa ta kishi ne,ka ji ka sani daga kan Jamila ka rufe kofa,babu kai babu kara kallon mace ma balle har ta kai ku da soyayya,har ta zarce da Aure",kai Mujaheed in ya dafe domin sam ba abinda ya so ji ba ke nan,ya so ya ta ya Aminin na shi gano ya fada soyayya,ko zai samu nutsuwa da kwanciyar hankali,duk wani abinda yake yi da tsokanar yana son Nadeeya yana yi ne ko wa zai samu Nameer in ya fitar da abinda ke ran shi.


"Yanzu dai duk ba wanann ba,za ka zo ne ko kuma ni in zo,ka kira tun jiya,ka ce kana son magana da ni,na ce zan zo,don bakin ciki ka ce Nooo sabida kar in ga face ɗin  pretty Pookie ɗin mu ko"..."Allah ya shirye ka Mujaheedu,ja bari yanzu zan yi wanka sai in ta ho,ka na tuna mun, it's very important for us to talk,in same ka a gida ko a ina zan same ka, dan dariya Mujaheed yayi sanann yace "ka dai yi wankan,za mu yi magana in Ka gama shiryawa, kar a manta a gaida mun Pookie",ba tare da Nameer ya amsa shi ba ya kashe wayar,yana me lumshe idanun shi.


***************Sen Rilwanu


"Kabiru na shiga uku na!,wlhy ina cikin matasanan ciyar tashin hankali,duniya za ta yi mun dariya",ya kare kamar me shirin yin kuka 


    Tsaki Alh Kabiru ya ja kasa kasa kan yace"Ni wlhy Rilwanu wanann rikicewar da yanda ka ke daga hankalin ka,kan kananun abu ke bani mamaki,haba ka tashi hankalin ka haka nan,ka hana kan ka nutsuwa for wat reason,wai me kuma aka yi yanzu da duk ka rude,har kake shirin fashe mun da kuka over the phone?,ya kare yana hararan wayan,don har ga Allah Rilwanun ya fara kai shi bango,sam kamar ba na miji ba,be can't handle things on his own,in an yi magana yace ai shi ya yi introducing in Shi to Brotherhood don haka duk abinda yayi kyau,shine in ya Baci still shine zai yi kuka tare,to tsakani da Allah don ya yi introducing in Shi,shike nan kullum yayi ta sauke mishi damuwar shi,abun nan ba dole fa yayi mishi ba.


" Kabiru ina ta magana ka yi mun shiru,abun nan fa kai ka sanya ciki,dole ina fada maka duk wani damuwa ta",dan tsaki Alh Kabiru ya ja as expected kafin yace"Yi hakuri Distinguished na dan fada tunani ne,me kake cewa?


"Cewa nayi na shiga uku!na lalace,ka san har yau ban samu mata me cikin nan ba balle in ba da jinin ta da yaron cikin ta,ga time sai tafiya ya ke,and kar ka manta Odogwu ya ce in na dauki time akwai gaggarumar matsala da za ta biyo baya,wlhy duk kaina ya kulle,i just don't know wat to do,ga zabe sai kara karantowa yake,Kabiru bana son in ji kunya,har ta kai mu ga duniya ta na mun dariya",ya kare hankali a matukar tashe.


"Wlhy Rilwanu in ba ka iya rike kan ka,kana kokarin danne damuwa ba, za ka kashe kan ka,yanzu miye wani abun tashin hankali a dan wannan aikin,ba fa uwar ka ka ce kayi wa ciki ka jira ya kai watan haihuwa ba sannan ka bada ita da dan cikin na ta,"KABIRU!!,you better watch your tongue while speaking to me",ya kare yana huci,ran Kabirun ya ɓaci da ihun da Rilwanu yayi mishi amman sai ya daure yace"common dude ni fa ban ga wani abun tashin hankali akan dan wanann task in ba,Mata nawa ke yin ciki a kullum su na kuma haihuwa a garin Bauchin nan sannan ka ce da Ni ka gaza samun wanda za ka bayar,ka ji abinda kake fada kuwa?..."Kabiru Bara ka gane ba wlhy,na rasa gane ta inda zan ɓullo wa lamarin nan,titi zan yi ta bi ina neman me ciki ta zo wuce na kamo ta,ko kuma gida gida zan na shiga?,duk kai na ya kulle wlhy".


" Kai Wlhy Rilwanu zan ga sanda za ka fara abu da kan ka,ga shi Ni kuma bana ma garin,balle na taimaka gurin nemo maka,Ni shirin tafiya California na na ke,akwai abinda zan yi a can,da na dawo,amman ka gwada zuwa asibiti kuwa?.


"Kabiru so kake na je asibiti gurin da is very crowded asiri na ya tonu,ka san yanda ake cika dai a specialist in nan",katse shi Kabirun yayi da"kai dallah sai ka ce shi kadai ne asibitin garin Bauchi,ina ka bar Rimi?,ka shirya kawai kayi Basaja,kasan daman asibitin kudi ne to ba wani cika aka fiya yi ba,in ba shi ba ma ga As_salam na ga ba a dade da bude asibitin ba,ka ga cikin sauki za ka yi abun ka ka fice babu wanda ya lura balle ma ya sani",dan jim Rilwanu yayi yana nazarin shawarar Aminin nashi,"kuma fa ka kawo shawara wlh sam ban yi tunanin haka ba,ina ta yawo a unguwa wai a tunani na ko zan dace,yanzu dai babu lokacin bata lokaci bari nayi sauri in ta fi Rimin na fi connection a gurin".


"Yauwa kayi sauri kam,i can feel it za a dace,duk yanda ake ciki just let's keep in touch,na so ina nan da cikin sauki za mu gama komai,but i trust you can handle this by your own self,stay strong okay komai zai yi daidai",godia ya yi kishi,sannan ya kashe wayar bayan yayi mi shi fatan sauka lafiya in ya tafi.


Kashe wayar ke da wuya kiran Ummi Salman ya shigo,mamaki dauke a fuskan shi ya dauki kiran don sun kwana biyu ba su gaisa ba,tun bayan rasuwar yarinyar ta basu kuma magana ba,daukan wayan yayi 


"Yaya Abul an wuni lafiya?","Ummi kuna lafiya ya gida ya iyalan na ki?,"wlhy yaya muna nan lafiya,ya aiki,ga zaɓe ya karanto ya shirye shiryen zabe?..."to Ummi ga zabe kam ya kawo kai,ayi ta sanya mu a addu'a kawai,don makiya sun sako mu gaba".


     

"Yaya in sha Allah ku ke da nasara,duk wani me neman ka da sharri mun fi karfin sa,yaran ka ma kullum suka yi sallah su na cikin maka addu'a,ai Allah ya san kai mutumin kirki ne,sannan with good and pure intentions ka ke son hawa kujeran mulkin nan,don haka Allah zai taimake ka,gobe ma zan sanya ayi maka sauka in sha Allah"


"Yauwa Ummu na na gode sosai Allah ya Miki Albarka".."Àmeen thuma ameen yaya,Ni kam ya batun Nadeeya ne,wai har yanzu shiru babu labari",ta kare cikin alhini


"Ke kam bari Ummi abu kamar almara yau ana neman watanni nawa babu Princess babu labarin ta,an yi cikiya har an gaji".."Yaya wlhy Ni kai na da zancen batan yarinyar nan kullum na ke kwana na ke kuma tashi,abu kamar almara,ace an sace dan mutum guda kimanin watan ni nawa,babu ko labari,gaskiya akwai mugayen mutane a duniya,wlhy yaya don a daga ma ka hankali a hana ka focusing a siyasar ka ce ya sanya aka biyo ta kan Nadeeya,so ake a maka yakin cikin gida a raba maka hankali gida biyu,in ba haka ba ace har yau yarinya shiru,in da kidnapping in ta aka yi,ai ya ci ace sun kira an biya an sake ta since,amman shiru fa,yau how many months suka yi passing ko wani hali ma ta ke ciki sai Allah",ta kare kamar za tayi kuka.


"Ba komai Ummi mu yi ta addu'a Princess za ta dawo gida soon kar ki daga hankalin ki,mu yi ta addu'a duk me mugun nufi zai koma kan shi,in dai aka yi zaben aka kare duk in da Diya ta take am very sure za ta dawo gida,abinda in na tuna at times nake kwantar da hankali na ke nan".."Allahu ya sa,in sha Allah nasara ta mu ce,Allah kuma ya cigaba da tsare ka".."Àmeen thuma ameen,ki turo mun account number in Ku,ke da su yan biyu,an kwana biyu da na tura muku kudi,i wasn't feeling myself ne,a kuma gaishe da yaran ",godia sosai Ummi ta yi,sannan suka yi sallama ta kashe wayar ta,zuciyar ta cike da kaunar dan uwan nata,tayi missing in Shi don tun rasuwar yarinyar ta da ya zo ba su kara haduwa ba,haka ya tsaya kai da fata ya yi abun sha tara na arziki,har ya bar Zariya yabon shi ake yi.


    ************Doc Bashir


     Tun bayan faruwar abinda ya same shi,da Tajo ya dauko shi direct gidan Doc Ahmad Abokin shi ya ce ya kai shi, ganin yanda ya shigo mi shi gida hajaran majaran ya so daga wa Ahmad hankali,shi sam ya rasa gane in da Bashir ya sa gaba,sam Bashir ba ya jin magana,a kullum cikin fada yake mi shi,kan yanzu girma ya fara zuwa musu ya ci ace akwai abinda ya kama ta ya daina su,amamn sam Bashir ba ji ya ke ba,kwanan shi 5 a gidan Doc Ahmad nan gida yayi jinyar sa har ya warke tas,be sanya ranar komawa gida ba,ganin haka ne Ahmad ya fito ya fada mi shi kan ya gaji gaskia ko ya tafi ko kuma ya fara ba da kudi ana cefanai domin sisi tunda ya je gidan Ahmad ba badawa ya ke ba,nan ko Doc Bashir ya wanke ido yayi wa Abokin na shi tass,wai be taba sanin Ahmad mugu bane mara tausayi sai wanann ranar,ace ayi Kidnapping in Shi,babu abinda ya boye mishi na daga azabar da ya sha a hannun Afzaal har kudin da suka yi demanding ku ma ya bada duk ya fada mi shi,abu guda ya boye shi ne asalin kudin na Afzaal ne ya ba shi kan ya kashe Nadeeya aka samu matsala ta tsira be kashe ta ba,shine ya zo karban kudin shi.


A nan ko shi ma Ahmad ya zage suka yi wa juna tas, sa'annan suka yi rabuwar rashin dadi,Tajo ya kira rai bace ya ce ya zo ya dauke shi ya maida shi gida,a kan hanyar su ce ta koma wa gida,ya ce da Tajo su biya WEMA bank ya na son cire kudi,domin yanda ya ji jikin nan dole ya yi kamar wata guda yana shan malt da madara tare da chickens ko zai samu ya farfaɗo ya maida jiki,da rawar baki kuwa Tajo kamar wanda aka aike shi yace"Dafta ai ina ga babu bukatar sai mun biya banki ka ciro kudi"


Harara Doc Bashir ya galla mishi sannan yace"to dan iya,i too Sabi in ban je na ciro kudi ba,kila kai zan na mika ana bani kayan dadin da zan ci in murmure in, domin ka gan ni nan?Sisi bani magani,don haka in kana kai ni Banki to ka wuce mu je"


"A'a Dafta ba ka fahimci ni bane,ranan Maman Hafiza da ta aike ni banki ta ce mun ka ce a ciro Mil 52,2 mil in kawo mata ka ce wai a aje maka,sauran 50 in kuma in Kai in da ka kira ka ce a aje kudin",ai be Kai ga rufe baki ba ya ji saukan mari akan fuskan shi,ji kuke tassssss.... A take kuwa Tajo ya taka burkin motan.


"Bura uba!Tajo dan uban ka ashe ba ka da amana ban sani ba?Ni za ka ci wa amana shege da fuska kamar kashi,wato da kai za a hada baki a damfare Ni a kuma ci amana ta",da sauri Tajon ya kwace wa marin da Bashir ya kuma kawo mishi sannan yace"Dafta  na rantse har da girman Allah babu bakin da a ka haɗa da ni,haba Dafta shekaru na wa muna tare duk wani kayan dadi,ko harkan kudaden ka Ni ke yi fa,ko yaran ka ba su taba sani ba,balle matan ka,wannan in ma da na ji an ce kai ka ce ne ya sanya na ciro na kawo"


"Ka yi mun shiru!,wlhy Tajo ka ba ni mamaki kuma in sha Allah daga kai har Hadizan sai na ci uwar ku,sai na yi mu ku rashin mutunci,wlhh bara ku maida Ni mutumin banza ba,haba don Allah da me zan ji🥺,Ni kuke son tsiyata wa ina",shiru Tajo ya yi mi shi ba tare da ya amsa shi ba, domin sam ya ga alamun Bashir in ba yi da kirki,shekaru na wa ya na mi shi bauta,don yau an sa mu kuskure,abinda ba wani bare su ka ci ba iyalan shi ne fa,miye abun tashin hankali.


"Za ka taka motar nan ka kai Ni gida in ci uban maciya amanar nan ko sai na maka dukan Kawo wuka"ya kare a zafafe, Tajo be iya kara ce wa komai ba,ila motar da ya taka tare da daukan hanyar gida,har su ka iso Doc Bashir na aika mi shi manya manyan zaguna,ko tsayawa be yi Tajo ya gama gyara parking ba ya bude kofar motan tare da fitowa zuciyar shi na tafasa saboda bakin ciki,har harɗewa ya ke gurin tafiya,burin shi be wuce ya gan shi gaban Hadiza ba ya cukumo kwalar shegiya ya ji akan wani dalili ya sanya ta ce wa a ciro mata kudadan shi,wani gefe na zuciyar shi na addu'ar Allah ya sa da gasken don shi ta sa a ciro kudin ta aje mi shi very safe,yo in Banda abun shi ma daman Hadiza ta isa ci mi shi kudade ne har kudi ma su yawa haka,matar da ke tsananin tsoron shi,ya san ma ba ma za ta fara  ba.


Sumar tsaye ya kusa yi shigan shi tsakar gidan, sakamakon arba da yayi da yaran shi kusan su 5 zaune ga babban tray in sliver aje a tsakiyar su,shake da farfesun kaza da ku ma ledojijin bread su na zaune,fuska dauke da fara'a suna yagan bread in su tare da dandalawa a roman farfesun su na ci,cike da annashuwa.


"Bura uba!!me nake gani haka,kai ku tashi dan uwar ku a gidan uban wa kuka samu Farfesun nan?"


Ba tare da sun dago ba daya daga cikin su ya ce"Umma ce ta ba mu",da sauri dayan ya caɓe da cewa"Baba ai tun bayan tafiyar ka dadi mu ke ci a cikin gidan nan",wani irin abu ne ya ji ya cake shi a kokon zuciya,ai ko ya yo kan su be yi wata wata ba yayi fello da tray in farfesun,da sauri kuwa yaran cikin su suka ɓare baki sai kuka.


"Wai wani irin kukan iskanci ne kuke ji da shi yau eheee Abba da Ramlat in ce Umma ta ba ku kazar ku to fadan me kuke yi wa mutane"Zahra'u ta fadi tana me fitowa daga dakin ta,turusss tayi sakamakon arba da ta yi da Bashir a tsaye yana galla mata harara .


"Ah ah me gida ashe ka shigo,sannu da zuwa"ta fadi fuska babu yabo babu fallasa,domin har ga Allah ba ta ji dadin dawowar ta shi ba,don babu abinda kake tsinta in yana nan ban da takaici da bakin ciki tare da horon yunwa,fuska ya hade tamau sannan yace"karamar munafuka bari na gama bincike na in tarar har da ke aka hade baki aka cutar da Ni,wlhy duk sai na ci uban ku,ba Ni kuke banzan tar wa,ina mijin ku a sace ni ace babu yar iskan da ta damu"...Murja ce wanda ta kasance Amaryan shi tayi saurin fitowa daga dakin ta.


"Wlhy me gida saidai ka ce Umma da Zarah'u ne ba su damu ba,don wlh tun randa ka sanya kafa ka bar gidan nan,nake cikin tashin hankali,ko abinci wanga ba wani cin sa nake ba",baki bude Zahran take kallon ta,tana mamakin hali irin na Murja.


"Ke dallah rufe mun baki,ai in ya tabbata har da ke wlhy ke ma sai na ci uban na ki,Bara ku maida Ni dan iska ba,ina ita hamshakiya uwar dabar ta ke,don isa tana jin murya ta ma ko ta fito,irin Shege kayi dai ka gama sababin na ka bani da time in Ka don ina da kudade na ko?...."haba wa me gida Sarai ka san Umma kam ba za ma ta yi haka ba,bandaki ta shiga wanda na tabbatar ba ta san da shigowar ka ba,da ka gan ta ai"..."ke dallah rufe mun baki tun ban fasa miki shi ba, Hadiza!Hadiza!!wlhh ki shafa wa kan ki lafiya ki fito tun wuri kar in shigo in same ki cikin bandakin nan",jin muryan na shine ya sanya ta saurin gama bukatar da ya shigar da ita tare da wanke hannu ta fito da sauri zuciyar ta na bugawa, ba dai ya san ta sanya an zaro mata kudaden shi ba,in ko haka ne yau ta shiga ukun ta,wani zuciyar ce ta karfafa ta tare da nuna mata babu wani laifin da ta aikata,hakan ne ya bata karfin gwiwan fitowa ta na me ji a ran ta yau kam a shirye ta ke wa Bashir ta gaji da cin kashin da ya ke ma ta,saidai duk abinda zai faru ya faru yau din.


Ganin yanda ta fito fuska a tamke ne,ya sanya Zahra saurin kora yaran kan su fita waje su yi wasar su,duk da kasancewar Bashir mutumin banza hakan be hana Umma tsayuwar dirshen akan kafafun ta gurin tarbiyyar tan da yaran ba, duk baki dayan su bata ware kowa ba duk wani tarbiyyar da za ta baiwa dan ta haka za ta bai wa dan Murja da Zahra'un,yana daya daga cikin halin da Umman ta koya wa Zahra'un kan no matter fadan da za su yi da Bashir kar ta bari su yi shi gaban yara,domin babu abinda ke saurin affecting yaro irin ya ga iyayen shi suna fadi in fada (My sisters ke mace ce kuma uwa, misunderstanding and arguments are Normal in ko wani irin relationship ne,Amman kar ki sake ki bari yaran ki su san fadan ku ke da mijin ki,domin Bara ki san irin effect in da zai musu ba,abun mamaki sai ku ga wasu matan don iskanci mace ta tara yara tana sanar da su abinda Uban su yayi mata na rashin daidai,har su zauna su kare mishi zagi ba tare da tsoron Allah ba,and a hakan kike kiran kan ki uwa me ba da tarbiya 😏kina tunanin in aure ya kai su gidan na su mazajen ya za su yi ke nan,ki kasance mace me sirri me kuma taya yaran ki gurin biyayya wa Mahaifin su ba wa ke kadai ba,duk rintse ki kina kokarin rike tongue in ki,da nuna wa yaran ki mahimmanci hakuri da biyayya,in ya so in daga ke sai shi ne kwa yi fadan ku,Amman don Allah ana kokari ana boye wa yara fadan iyaye don wlhh yana mugun affecting brain in yaro, ubangiji ya kara mana lafiya da zaman lafiya a gidajen mu).


"Ah me gida sannu da hanya,ashe ka dawo,maraba, Zahra'u ya ku ka bar shi a tsaye be shiga parlor ya ci abinci ba shi da ya Ibo gajiya"ta kare tare da kokarin bude kofar parlor in na shi.


"Amma Sarai kin ji dai kiran ki na ke za ki zo kina wani ya ba a shigar ni parlor ba,ni da gida na har sai na tsaya an shigar da ni parlor 😏"ya kare yana hararan ta


"Ka kiran ina banɗaki ne,kuma gani nayi daga hannun yan garkuwa kake,Ni wlhh na dau ma rai a hannun Allah za a shigo da kai,ganin irin yanda ka ke magana da kyar randa ka kira,ka ga kuwa ka na bukatar wanka da kuma abinci,sannan ka huta,sai ka ba mu labarin ya zaman ka ya kasance a hannun yan Kidnapping,"ta kare tana kokarin shiga cikin parlon.


"HADIZAAAAA!"ya kwala mata kira kamar zai daga gidan,cike da rashin tsoro ta amsa shi da ihu ita ma"NAAM BASHIR",ta juyo tare da dage masa gira daya🤨


"Ah lalle wuyan ki ta kai yanka,dan iskanci Ni kike kiran suna na gatsau haka nan,sa'an ki ne ni,ban ga laifin ki ba,matar da ta iya damfara miye a cikin in ta maka rashin kunya,bakar munafuka,by the way ba wai dogon turanci nake son yi Ni da ke ba,ina kudade na da ki ka sanya Tajo ciro mi ki su,yi maza ki dauko mun su,domin kudin ajiya ce masu shi suna jira na",ya kare yana karkada kafa.


Kallon tsana ta ke bin shi da shi zuciyar ta na tafarfasa,she has been enduring this pain for how many years,bata taɓa bude baki ta amayar da abinda ya ke mata ba,yau over 20 years of marriage in ta da shi,zai tsaya a gaban kishiyoyin ta yana kiran ta wai yar damfara ta fito mi shi da kudin shi,ba ma wanann ya fi mata ciwo ba wai ita ya ke kira bakar munafuka ,abun da ya fi ci Mata rai ma wai rainin wayon da zai musu wai ba kudin shi bane,a yanda ta ke jin ta yanzu ba ta ki ta tube su bugu da Bashir in ba,cos she has tolerated  enough! ya riga da yayi pushing in ta bango,babu wani sauran respect da take mishi kuma,yo ina respect in daman Mutumin da ciyar da gidan shi sai  an kai ruwa rana ake samun ya yi.


"Za ki fito mun da kudi na ne ko sai na  ci uban ki,na miki bugun da sai kin kusa haukace wa😠"ya kare  yana nufo in da take,"in ka fasa duka na Bashir ka raina uwar da ta haife ka",jin furucin ta ne ya sanya shi ja cak ya tsaya, domin tunda suke mai kama da haka ma be taba shiga tsakanin su ba,duka zagi babu wanda baya mata Amman haka za tayi ta ba shi hakuri,wai a sunan biyayyar aure.


"Wai har kana da bakin kira ta madamfariya Amman Bashir ban taba sanin kai mugun dan iska bane sai yau,har akwai mugun da ya kai ka,ka tara mata uku yara kusan 20 ka gaza ciyar ko shayar da mu,kai za ka ci me kyau ka sanya me kyau ka hau me kyau Amman iyalan ka ko oho,kana hauka ne?And sabida Ka Raina mun hankali ka zo kana zagi na gaban matan ka,ai bautar aure ba hauka bane,Kai Bashir tun da kuruciya ta aka hada mu aure da kai,amman yau abu daya ba zan nuna in ce ga albarkan auran da na samu da kai ba bayan yaran da muka haifa tare,su ma kuma ina danasanin kasancewar ka mahaifin su,daman auran hadi hauka ne?ko ka maida mata yan iska ne?,tunda na ke da kai, ko sau daya ba zan ce ga abun Alkhairi da kai yi mun ba,tana kuka ta cigaba"duk wani dadin gidan miji da mace ke tunkaho tana ji Ni ban san shi ba,tunda kuruciya ta har kawo yanzu da shekaru suka ja mun,Bashir wlhy in kayi wasa Bara ka gama da duniya lafiya ba,domin ban taba ganin mutum me tsananin son kan shi irin ka ba,in mu matan ka kana kyashi ba mu wat of yaran ka?baka tsoron su fada mugun hali saboda kai?,nan ka sanya kafa ka fice ko biyar ba ka aje mana ba da sunan ka tafi yawon bude ido,aka yi dace aka sace ka aka yi ta gana maka azaba,kudin da ba ka baiwa iyalan ka ka sanya su farin ciki Allah ya ba ka lada,ka tattare aka baiwa yan garguwa da mutane.


Hawaye ta goge sannan ta cigaba"Nan na sanar maka Hafiza na kwance rai a hannun Allah Amman ba ta ita ka ke ba,kai a kullum needs in Ka ne gaba da komai,wlhy a kullum na kwanan duniya ina danasanin auran ka domin in ana neman kalman da za a misalta ka to a kira ka da MUGUN MIJI me tsanani son kan shi,kuma kudin da ka ke magana a kai,yessss Ni ce nan na sanya Tajo ciro mun su,domin wannan mata da yara da ka aje ai ba da yawun baki na zan ciyar da su ba,da shi aka musu cefane da Siyan abinda bara a rasa ba,in ce na fada maka yanda kudin ka suke sai ka shafa mun lafiya,kudi dai mun ci kuma ba mu yafe maka azabtar da mu da barin mu da yunwa da kayi ta yi ba tunda kana da fiye da mil 52 a account in Ka kullum kake mana kukan babu"ta kare tana me kokarin shigewa dakin ta.


"Kar ki kuskura ki shigar mun daki,ai ban taba sanin ba ki da mutunci kuma baki da kunya ba sai yau, shegiya ɓarauniya duk wani borin kunyar da za ki yi,wlhy saidai kiyi ki gama kudi na sai kin fito mun da shi",


"Na rantse da girman Allah Bashir kudi ya ciyu kuma ba za su fito ba,da kake maganar rashin kunya har akwai mara mutunci irin ka,na mijin da be iya ciyar da iyalan shi,karatun su be dame shi ba,har akwai Shege da ya wuce ka me bin matan banza a waje?Ko ce maka aka yi bani da labarin biye biyen matan waje da kake?,mutumin da be rike addinin shi da kyau ba, ina daman ake tunanin zai rike mace,balle Kai don zari ka aje su har uku,komai mutum zai yi yana dai tunawa da akwai rayuwa bayan mutuwa sannan duk sai mun tsaya a gaban Allah,wlhy auran ka Ƙaddara ce mafi muni gare Ni Bashir ina takaicin hada zuri'a da kai....ba ta kai ga kulle baki ba ta ji saukan mari a fuskan ta"Shegiya watsatsiya har Ni kike Allah wadai da aure na to na sauwake miki yanda kika gaji Ni kai na ba dadin zama da ke na ke ji ba,sai ki tafi gidan uban ki na SAKE KI SAKI UKU!!.


"Inalilahi wa ina ilahi raju'un haba me gida,abin har ya kai haka da za ka saki Umma har saki uku,ba fa SAKI DAYA kayi mata ba UKU fa,lafiyar Ka kuwa",a zafafe ya juyi"zaki mun shiru Zarah'u ko sai na zubar Miki da haƙora"..."kyalle shi Zahra to shine me in ka sake Ni abu daya zan yi dana sani shine in na fita daga gidan ka ban rama wannan marin da ka mun ba,tana rufe baki kuwa ta dauke shi da wawan maruka har uku,tana huci tace"ko yanzu na bar gidan ka bani da danasani sai na jinin da muka hada da kai,sannan kuma na bar ka da fitowar rana da faduwar shi,in sha Allah sai Allah ya fidda mun hakkin zalunta na da ka yi ta yi,Wawa shashasha kawai,har wata tsiya ce gidan na ka da In an bar ta mutum zai tagyayara,ko yanzu zan daga hannu in gode wa Allah na ya raba Ni da Qaya,zan je nayi rayuwar farin cikin da na rasa tun da kuruciya ta "ta kare tana me jan dogon tsaki.


"Me gida sam wlhy ba ka kyauta ba,ace duk irin abubuwan da Umma ke yi cikin gidan nan akan laifin da ba ita kadai ta aika ta ba za ka sake ta?Kudin da kake maganar an damfare ka a kai duk mu uku mun cancanci hukunci tunda tare Umma ta raba mana kudin"..."caraf Murja ta ce"ke Zarah'u ki ji tsoron Allah ta raba muku dai ke da ita da yaran ku, amman Ni kam sisi ban gan shi ba,tunda daman can ba sanya Ni kuke a abubuwan ku ba",cike da mamaki Zahra take bin Murja da kallo.


"Ai no wonder kike ta kare ta ashe tare kuka raba kudin satan,no wonder kike ta tada jijiyoyin wuya,to wlhy ke ma ki je na SAKE ki SAKI DAYA,ke kuma Murja Allah ya cece ki ba ki ci mun kudi ba,wlhy da sai kin koma gida ke ma,shegu ɓarayin banza a fuska kamar mutanan kirki,sai a bi wani yarimar ayi mishi sata ba Bashir ba",ya kare yana shige wa dakin shi ran shi a matukar bace.


"Murja Amman kin bani mamaki wlhy,ashe ke munafuka ce ban sani ba?"Ke dallah daka ta mun Zarah'u aka ce Miki kowa ce Mahaukaciya irin ki,wai akan an saki kishiya madadin ki yi farin ciki,Amman saboda rashin rabo da kini bibi kike wani tada jijiyoyin wuya har kika zawo wa kan ki saki saboda rashin rabu,ke da za ki sauke kai aci arziki tare da ke,amman tunda kin yi wa kan ki ya sauwake Miki a koma gida ayi zaman zauranci kuma,Ni kin ga ma tafiya ta miji na ya dawo daga hannun yan kimmashin yana bukatar Hutu"ta kare tare da shigewa dakin Bashir in,mamaki ba karamin kama Zahra yayi ba,Hadiza ce ta dafe ta tare da fadin"kyalle ta Zahra sanin halin mutum sai Allah daman,na baki daban na zuciya ma daban,Amman sam ban ji dadin yanda kike biye shi har auran ki ya kare ba,ko banza ina farin cikin in na fita yara na will be safe a hannun ki, Amman yanzu daga Ni har ke shan ruwan mu ya kare a gidan nan"...."haba Umma mutumin da ya kasa zama da ke duk kyan halin ki, ai ba abokin rayuwa bane,Auran Bashir kamar yanda kika fadi ƙaddara ce,kuma Allah ka dai ya san me ya tanadar mana da ya sanya ya sake mu,ba zan ji ana ci Miki mutunci nayi shiru ba,domin ke mata ce me kawaici da hakuri,kin ja Ni a jiki kamar yarinyar ki ba kishiya ba",dadin sosai Umma ta ji,Saisa a rayuwa zama da mutane lafiya ya fi komai dadi,ko bayan babu kai dole a yabe ka,a haka wanann ranar suka bar gidan Doc Bashir cike da kewan yaran su,inda Umma ta ringa kwantar wa Zahra da hankali kan za su na zuwa duba yaran su,sannan zumunci kam yanzu suka fara,duk da dalilin Bashir suka hadu don sun rabu da shi ba za su daina zumunta ba.



***************Sen Rilwanu


Around 4:30 na yamma Sen Rilwanu ya shiga cikin asibitin Rimi fuskan shi dauke da face mask,in ba ka san shi can ba za ka gane shi ba saboda disguise in da yayi,mota daya tal ya zo da shi,be dauko bodyguards in Shi ba,gudun tonuwar asirin shi,cikin takun nutsuwa ya shiga cikin asibitin hannun shi dauke da goron faro(bottle water),idanu ya baza yana kewaya wa cikin asibitin yana neman me tsohon ciki,haihuwar yanzu yanzu.


Dan tsaki ya ja sannan ya ce"wani abu sai Odogwu wlhy yanzu a ta ina ne zan samo me tsohon ciki in ba cikin labour room zan  shiga ba,da na shiga kuma in tona wa kai na asiri"gajiya yayi da zagaye,hakan ya sanya shi neman gurin zama tare da yin shiru yana kallon shige da fitan mutane,a gaban shi masu ciki kusan uku suna wuce wa tare da maza jen su,saidai duk be kai watan haihuwa ba,yo ko ma ya kai a taya zai fara tunkarar su.


Fitowan ta ke nan daga dakin haihuwa domin nakuda take tun kwana biyu da suka wuce amman haihuwa ta ki zuwa,yanzu ma gajiya tayi da kwanciyar,shine ta ce bari ta dan fito ta sha iska kila kafin nan haihuwar za ta zo,tayi dana sanin matsawa mijin ta ya kawo ta kasar Nigeria gurin family in Shi haihuwa,da ta sani da nan Dubai suka yi zaman su in ya so bayan ta haihu sai su zo,don ta san da a can ne kila da tuni ma ta manta da haihuwa,da kyar take daga fararan kafafun ta da ya sha jan kunshi,kallo daya za ka yi wa kyakkyawar fuskan ta ta baka tausayi,don yanda ta kumbura za ka fahimci ba karamin wuya cikin ke ba ta ba, kyakkyawar matashiyar Balarabiyar budurwa tana sanya da gown in asibiti,daga ganin ta ka san ba yar nan kasar bace don ta fi kama da larabawa,zama tayi a dogon bench in da Rilwanu ke kai,sai sauke ajiyar zuciya take yi,don ko daga nan zuwa nan tayi tafiya sai numfashi,zaman ta ke da wuya kuwa wayar ta ya hau ringing,Saida tayi murmushi sannan ta dauki wayar"Jaazmeen wai har yanzu shiru",Ayman mijin  ta ya yi tambayar cikin halcen larabcin da be gama kware wa a kai ba.


Saidai ta sauke ajiyar zuciya sannan tace"Babe am so tired wallah ,Har yanzu babyn ya ki fitowai just can't take this pain  anymore pls hurry up I need you by my side"ta kare kamar za tayi kuka,"my love injection na je siyo wa yanzu haka am on my way back,yanzu Zan zo kin ji,just stay strong for me okay,you can do it,I love You so much 🥺❤️ Jaazmeen don Allah ki daure babu abinda zai same ki",Baki ta bude da niyar bashi amsa sai ta ji kamar abu ya shake mata wuya,a fujajan ta shiga tari kamar za ta amayar da ranta ta baki,jin haka ya rudar da Ayman don sai kwalo mata kira yake ta waya Amman ina bata ma jin shi don har ta fara fita daga hayyacin ta,akan dan karamin shakewar da tayi da yawun bakin ta,ganin haka ne ya sanya shi kashe wayar tare da kara gudun motar don a rayuwar nan bayi da abinda yake masifar kauna sama da matar shi Jaazmeen ko fly baya son taba ta balle yanda ya ji tana tarin nan ta tsora ta shi.


Da sauri Sen Rilwanu ya mike tare da nufo inda take zaune tana tari,daman can yana hankalce da duk abinda ke faruwa,cikin sauri ya shiga jero mata uwar sannu tare da bude mata bottle water in Yana me mika mata,da sauri ta sanya hannu ta karba tare da kafa kai ta shiga moɗan ruwan,ba ita ta cire goran ruwan a bakin ta ba Saida tayi rabin shi,tukun ta na sauke ajiyar zuciya jin tarin ya tsaya cak ta dago don yi mishi godia saidai wayam ta ga babu kowa,aje goron ruwan tayi tare da dage shoulders in ta irin shike nan ɗin nan,abinda bata sani ba tun sanda ta kai goron bakin ta Rilwanu yayi saurin zame jikin shi tare da barin Asibitin zuciyar shi cike da farin ciki,yana ji kamar ya kira Kabiru tun kan ya isa gida ya shafa mi shi labari,cikin sauki ya samu me ciki ya bada ita,saidai ya ce bari dai ya bari ya isa gidan tukuna,fitan shi daga cikin harabar asibitin yayi daidai da danno kan motan Ayman mijin Jaazmeen.


Kamar wasa ta ji cikin ta da yanayin ta ya shiga canzawa, kafin kace me mata ta hau sansandare wa,kafin a ankara ta fadi nan kwance a kasan tiles in gurin babu numfashi tattare da ita.


Wani irin wawan ihu Ayman ya sake a lokacin da yayi arba da Jaazmeen kwance a kasa kamar kayan wanki,ga cikin ta nan a gaba tayi wani irin fayau tayi haske sosai,da sauri doctors suka fito tare da ɗaukan ta, unfortunately sai hakuri suka bashi don Jaazmeen kam rai yayi halin shi,daga ita har abun da ke cikin ta wai jinin jikin su ne ya kare,ba karamin girgizar shi mutuwar tayi ba,kukan ma kasa wa yayi sai sauke ajiyar zuciya yake ta yi yana kallon gawan matar shi da ke kwance, shigowar waya ce ya sanya shi dauka kamar zararre ya manna a kunnan shi.


"Hello son ina ta kiran ka baka dauka ba,ya jikin Jaazmeen in,hope ta haihu?...wata  matsananciyar kukan da yake ta dannewa ya sake sannan ya ce"Dadddyyyyy i lost her,my Jaazmeen is no more,yanzu doc ya ce wai ita da baby duk sun mutu.....da sauri Alh Kabiru ya tunkude karamar yarinyar da ke lashe mishi jiki tare da mike wa zauna yace "WHATTTTT Ayman Jaazmeen ɗin ce  ta mutu........



    


     Bare with the typing Errors 🥺 pls ban riga nayi editing ba



    In na ga ruwan comments kuma za ku ga ruwan updates 😸



   Have a  lovely weekend 😘


   Ina yi wa kowa fatan Alkhairi,sai zuwa Monday in me kowa me komai ya kai mu,



 Ina masu sha'awar shiga Adashen online,inda za a rike miki Amanar kudi,ba tare da runto ko Ojoro ba,inda za ki zuba ki kuma kwashi kudaden ki, cikin kwanciyar hankali da yardar Allah,ba tare da wata matsala ko tashin hankali ba,


Akwai Matan da sam kudi be cika zama musu a hannu ba,da kin samu sharp an kashe su,someone like me🥺lol,to yar uwa ta shiga Adashe a nan ne,zaki tara kudin ki hankali kwance,


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L7ai2fYGh4UAIK9MhC9awJ


Kindly ki shiga cikin group in nan,2500 weekly,I can assume you Bara ki samu any disappointment ko Damfara ko wani rikici ba, 


For more information,chat her up via:


       08149541182

Sai mun ji ku🙌😍

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


     This page is yours A'ishatu Ummul khair (sweetheart),


Ina godia da kaunar ki  gare ni🫶🏻❤️

             

..........


My What's app group link


https://chat.whatsapp.com/BitkDSSUNsLEcljCFONkr4


In kin San ba karanta book ina da sharhi bane zai kawo ki,don Allah ki yi zaman ki ba sai kin yi joining ba☺️


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


******************


Tallah! Tallah!! Tallah!!


   

   Ina uwar  da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


  Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


   Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


    To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌

    

https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


         08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌           


...........

          Page forty six


**********


"Whaattttt Ayman,kana so ka ce mun Jaazmeen in ce ta mutu"ya kare sounding worried,tare da saurin mikewa zaune,


Cikin sheshekan kuka,kamar wanda ya ke shirin zare wa yace"Daddy am serious yanzu Doc ke fada mun wai sun mutu,Ni kam na shiga uku na lalace Daddy wayyooooo Allah",ya kurma wani irin ihu,ba karamin firgice wa Alh Kabiru yayi ba,cike da lalashi ya shiga kwantar wa dan na shi da hankali"ya isa haka my boy stay strong okay,just keep calm,ina Mommyn na ka take?",cikin jan hanci yace"ta je gida hado wasu abubuwan na kai ta,Doc ya ce in biya ta Pharmacy in siyo injection,dawowa na kawai na tarar da Jaazmeen ita a kwance",be Kai ga karasa maganar ba yayi breaking down into wani sabon  kukan,iya kaduwa hankalin Alh Kabiru ya kadu,domin a rayuwa Allah ya jarrabe shi da kaunar first born in Shi Ayman yana kaunar yaron sosai,hakan ya sanya yaron ta shi saka ka babu kan gado balle wani batu na tarbiyya,rabin rayuwar shi ma zan iya ce wa a kasar waje yayi shi,domin iya kan shi primary sch ne yayi ta a nan Nigeria,kama daga kan Secondary har jami'a duk can ƙasar waje yayi su,to abun ku da uban daman kudin banza ya tara,ai sai a kashe shi ta hanyar banza.


Ayman na daya daga cikin big boys in garin Bauchi da ake ji da su,domin duk wani harkan karya da kayan wanka na karya daga gurin shi ake fara gani,don Kabiru ba karamin bakin pocket in Shi ya ke sake masa ba,don ko cikin yaran shi kaunar Ayman ya fita daban,a haka ya taso ya kuma girma a sangarce yaron Daddy a rayuwar shi be son babu ba,shi Kabiru daman ba tsoron Allah gare shi ba balle ya tsaya neman Mata saliha wace za ta baiwa yaran shi tarbiyya me inganci,Asiya wace ta kasance Mahaifiyar Ayman itama wayewar ta iya boko ne ilimin zaman duniya da kuma murza Naira,Amman babu abinda ta sani game da Addinin ta(hakkun Allah yayi gaskiya,da yace Yaran ku da Dukiya kan zamo fitina a gare ku,wani kazamantatciyar kudin,da samun ta ka kashe ai  gwara ka koma ga Allah kana wanda ya fi kowa talauci a duniya,sam mutanan mu suna mance wa idanun su ya kan rufe a gaza banbance Halal da Haram,and mu kan mance duk wani sisi ko Nairan da muka kashe babu shakka ranar gobe kiyama,sai Allah ya tsaida mu gaban shi,ya tambaye mu a garin yaya muka samu wanann kudin?,and ta wani hanya muka bi don kashe duk wani kudin da ya shigo hannun mu, Ubangiji ya nisan ta mu daga cin haramun tare da wanda ke cin sa, Allah kuma ya buda mana kofofin samun halal in mu,ya kuma ba mu ikon tarbiyan tar da yaran mu,domin amana suke a hannun mu,da sannu Allah zai tsaida mu gurin tambayan ta wace hanya mu ka bi don ganin mun kula da Amanar yaran mu  da ya ke wuyan mu)


Asiya zaman ta da Kabiru ganin ya fi ba wa duniya mahimmanci ya sanya ta watsar da Addini ta,tare da mara mishi baya gurin ganin sun mori duniya kuma su ji dadin rayuwar su,hakan ya sanya a gaba daya yaran Kabiru babu na kirki, ko wannan su shegen kan shi ne, Kukan da ya ji Ayman in ya fashe da shi ne ya sanya shi saurin dawowa hayyacin shi,tare da shiga lallashin shi"yi shiru Baba na,ka daina kukan nan pls, don't you know big boys like you ba sa kuka fa"..."Dadi am not a big boy I just want my love back,Daddy I want my Jaazmeen, wlhy Bana jin zan iya rayuwa babu ita,na shiga uku na lalace Daddy wayyooooo zan mutu",ya kurma wata irin wawan ihu numfashi shi na sama sama,cikin rigicewa da gigice wa Alh Kabiru ya shiga kwala wa 'dan na shi kira"Son!Son!!Ayman!!talk to Daddy don't do this to me pls"ya kare hawaye na zubowa daga cikin idanun na shi,abinda ya jima be yi ba a rayuwar shi,Ayman jin shi yake kamar rayuwar shi,and Sarai ya san irin dimbin soyayyan da Ayman in ke wa Jaazmeen matar shi,domin daga shi har Asiya ba su so ya aure ta ba, Amman ya kafa ya nace ita ya ke kauna,ala dole ya fi karfin su,suka mara mishi baya har ya auri Jaazmeen,suna kuma zaune a Dubai,ba yanda Alh Kabiru be yi kan su dawo Nigeria ya zabi duk gidan da ya masa ya sanya ta, Amman sam yace a'a domin gani yake rayuwar Nigeria zai takura wa Balarabiyar matar shi wanda yake son ta kamar ran shi,Haihuwar fari ne,da matsawar ta da na Asiya aka samu Ayman ya yarda zai dawo da ita Nigeria ta haihu,ashe ajali ke kiran ta,tabbas ya san tunda Ayman ya rasa Jaazmeen to in be yi wasa ba ya na daf da rasa yaron shi da yake masifan so da kauna.


"Alh kayi hakuri and get a grip of yourself,Ayman is under us now and za muyi trying all our very best,na ganin mun ceto rayuwar shi,but for now Yana bukatar addu'an ku,don his life is in danger",doc in da yayi attending kan Ayman da ke kwance babu numfashi a jikin shi,ya gama koro wa Alh Kabiru bayani yana me kashe wayar.


Cike da iskanci da salon bariki yar mitsitsiyar yarinyar da ke kwance a kusa da Alh Kabiru ta mika hannun ta tare da sauke su kan kirjin shi,ta shiga shafawa a slow, tare da fiddo tongue in ta tana me lashe mishi fuska tare da making wasu irin kananun sound masu fitar da duk wani na miji me lafiya daga hayyacin sa,a zafafe ya sanya  hannu tare da damke tongue in nata ya ja with full force,wani irin zafi da raɗaɗin azaba ne ya ratsa ta wanda ya hana ta kwakwaran motsi ma,sai da ya ga yarinya na shirin mutuwa hannun shi na damke da tongue in ta,idanun su daga shi har ita sun yi wani irin jawur,sai yarfe hannu take ta faman yi cike da gigin azaba,tukun na ya sake mata halcen nata.


Wani irin gigitattciyar mari ya dauke ta da shi,a both kumatun ta sannan ya shiga dibgan ta kamar wanda Allah ya aiko shi"Dan durin uwar ki ashe baki da mutunci?baki da hankali balle tunani,shegiya ce miki aka yi kowa ne dan iska irin ki,ehyeeee!Ya kara yana me kara dauke ta da wani wawan marin,bugun Bura uba yayi mata without duba kananun shekarun ta,he was just venting out his frustration on her,gani yake ba ta san ciwon kan ta ba,and is just like bata tausaya masa halin da yake ciki shi da yaron shi ba,in banda Arnan mutum,a hakan ma wai karuwa da ba komai bane a gaban su,banda su raba jiki wa mazan banza su samu su sami abinda za su rufa wa kan su asiri, in banda haka tana jin yana kukan an yi mi shi mutuwa,amman da ke yar iska ce wai za ta fidda dirty tongue in ta,tana trying lashe mishi jiki,sai da ya tabbatar yayi mata lisss sannan ya jefa mata damin dubu dubu guda biyu,cikin ihu har hotel room in na echoing voice ɗin na shi"OUT OF MY ROOM YOU BITCH"ya kare kamar me shirin rufe ta da duka,don ji ya ke gaba daya ta fice masa a rai(Ni ko na ce haba dai Alh Kabiru har wani abun azo a gani aka yi maka da ran ka zai ɓaci,ai a shawarar ce da ka adana anger in naka har sai kun hadu da Aminin ka😉),ganin Alh na neman dawowa inda take ne,ya sanya ta saurin mike wa, ta tattara yan komatsan ta,riga wannan da pant sai a wajen kofar dakin hotel ɗin ta samu daman sanya su.


"Hello Asiya kina ji na ko?,be Jira amsan ta ba ya daura da ki yi maza duk wani abinda ki ke ki bar shi,maza ku tafi Rimi Ayman na cikin wani hali",ihu Asiyan ta sake Sannan tace"Na shiga uku na Me gida me ya samu Ayman ina,ina ce yanzun nan ya sauke Ni a gida,ya koma asibitin dududu mintuna nawa ne a tsakani",ta kare tana fashe wa da kuka.


"Ke dallah get a grip of yourself",ya daka mata tsawa,sannan ya daura"kira na yayi wai Jaazmeen ta mutu,ba tare da ya tsaya sauraran sallallamin da ta ke jero wa ba yace"Ni kai na ban fahimci yanda zantukan na sa suka dosa ba, doctors dai sun ce yana critical condition, don haka kuyi maza ku shirya ku tafi asibitin nan,Nima yanzu zan yi kokarin samun flight in taho Bauchin,duk yanda ake ciki muyi waya kawai",be tsaya  jin ta bakin ta ba ya kashe wayar ta shi yana jin kukan Ayman in har yanzu yana dawo mi shi a kunnan shi,zuciyar shi wani irin zafi ya ke masa,ya Odogwu zai masa haka,ai da ya sanar mi shi tunda wuri kan Jaazmeen za ta rasa ranta gurin haihuwa da sun san matakin da za su dauka tunda wuri,kila da ya fada mishi da wuri ma bare bari Ayman yayi mata ciki ba,ko kuma  da an cire womb in ta tun day one,kila da an yi preventing in ta from dying (Wa'iyazubillah 😭, Jahillici be yi ba Wlhy),da duk Ayman in Shi be shiga cikin wannan halin ba.


Tsaki ya ja a karo na ba adadi,kafin ya janyo wayar shi,ya shiga kiran agent in da ke masa komai na tafiye tafiyan shi,ba mutuwar Jaazmeen bane ya daga mishi hankali ila tuno irin halin da Ayman zai shiga bayan ita, domin shi kan shi ya san yaron na shi ba dan karamin soyayya yake wa Jaazmeen in ba,har ya gama ringing be dauka ba,be hakura ba ya kuma kira,Saida ya kusa tsinke wa sannan ya dauki wayar,nan ko Kabiru ya rufe shi da fada kan ina ya jefa wayar ta shi,Saida Yakubu ya bashi hakuri,sannan ya sanar da shi Flight yake nema from Abuja to Bauchi yanzu yanzu.


"Alh ya batun tafiyar ka California in,don an riga an gama processing komai,daman abu guda na je karbowa,ina shirin kiran ka in sanar maka ke nan sai ga kiran ka"..."Yakubu ka bar maganar tafiya California in nan,yanzu dai zan samu Flight zuwa Bauchin ko ya?"


"Assha!Ai kuwa Alh duka duka be fi 20 mints ba jirgin ya tashi,ba ka fada da wuri ba"..wata wawan tsawa Kabiru ya masa sannan yace "Yakubu I don't fucking care yanda za ka bi ka samo mun jirgi,all I know is that ya za ma dole na tafi Bauchi,i don't care ko P J ne,ka nemo mun kasan Ni dai me iya affording ne,so am not taking No as an answer",ya kare yana mike wa tsaye,"shike nan Alh give me some mints Bari na bincika na gani,just get yourself ready",da haka Kabiru ya kashe wayar tare da mike wa a rude ya shiga hada kan kayan shi


K'aran shigowar waya ce ta sanya shi jan tsaki,domin a halin da yake cikin nan baya jin ko uwar sa ce da za ta dawo duniya ta kira shi zai dauka,cigaba yayi da hada kan kayan shi,don ya san ba Yakubu bane tunda mintinan da yace ya ba shi ba su riga sun cika ba,jin kiran ya ki tsayawa ne ya sanya shi janyo wayan ganin Sen Rilwanu Audu Waziri ke kiran shi,ya sanya shi jan tsaki a fili tare da yarda wayar kan gado"aikin banza wannan ko ni na kawo shi duniya albarka,wlhy Rilwanu ka ishe Ni,da na san haka za ka gallazi rayuwa ta da ban kai ga Brotherhood ba,haba for wat reason, can't you just leave me alone,Kai Ka daga hankalin ka Nima ka kadan nawa,tsaki ya kuma ja sannan yace kai a baka task ɗin kuma kana expecting ni zan na maka komai kullum, Ni gurin uban wa nake zuwa neman taimako,saidai kayi ta yi wallahi,in ka so kar ka nemo mace me cikin ka zauna nan kana kira na, Odogwu uban ka zai ci,domin Nima damuwar gaba ta ya ishe ni",ya kare yana hararan wayar kamar Rilwanun yana gaban shi.


Lucky him Yakub ya kira tare da sanar mishi an samu Flight ba tare da 

wasting time ba kuwa,ya hado komai tare da fitowa,aje key in dakin yayi a reception sannan ya shige motar haya,tafiyar yan mintuna ne suka iso shi Airport in ba tare da bata lokaci ba kuwa jirgin na su ya daga,a flight mood ya sanya wayar shi,domin Rilwanu ya ishe shi da kira,and shi ba ya good mood in da zai saurari haukan shi.


***************Kaduna state


Cikin nutsuwa Doc Nameer ke driving,while Mujaheed na zaune a seat in me zaman banza,dan nisawa Nameer in yayi tare da kashe wakar What if I say (na Fire boy),da ke tashi a motar,sannan ya kalli Mujaheed for some seconds kafin yace


       "Gee kana ganin in muka je gurin na shi babu wani matsala?,dan tsaki Mujaheed in ya ja sannan yace"wlhy Nameer ina gab da in fara dukan ka,yanzu akan haka ne ka kashe mana waka,bayan ka san irin kaunar wakar nan da nake yi?,na fada maka bayi da matsala,Aminin yaya Hydar ne so in sha Allah cikin sauki zai yi mana komai,kai dai ka kwantar da hankalin ka, Pookie dai ta kusa samun sauki",idanu ya lumshe a hankali sannan ya bude su,har ga Allah yana son ganin ta samu lafiya,but in ya tuna za ta rabu da su in ta warke dole ta koma wa family in ta sai ya ji kamar ya fasa nema mata lafiyar,but wani bangare na heart in Shi na tuna mi shi a kullum,yana duba ta,ya take ciki?how many months bata tare da family in ta?,akan na shi farin cikin kadai bare yu ya fasa nema mata lafiya ba,domin in yayi hakan ya tabbata he is selfish,Wanda ba zai so hakan ba,hakan ya sanya bayan doguwar tattaunawar da suka yi tsakanin shi da Mujaheed jiya,ya dauki shawarar Mujaheed kan su kai ta gurin kwararre kuma babban Neurologist  (likitan ƙwaƙwalwa),wanda ya kasance babba sosai,kuma ya san kan aikin shi,duk wani matsala da ta shafi brain in dai ka je gurin Doc Akim Mustapha to in sha Allah matsalan ka ta kau.


Tafiyar kusan 1 hour ce ta iso da su private hospital in na sa,da ke nan ta dan waje wajen gari, tun daga waje tsarin ginin asibitin zai burge ka,domin an kashe kudi sosai gurin gina shi,da ido Nameer ke bin asibitin da kallo,har suka shiga cikin shi,haduwa da tsaruwar shi hannu ba zai iya rubutawa ba readers🤣kamar dai mutum yana kasar waje,wuta da ma'aikata ne ta ko ta ina,domin asibiti ce babba,dake Mujaheed ba bakon asibitin bane ya sanya shi ke wa Nameer jagoranci har suka iso office in Doc Akim Mustapha.


"Aboki na za ka bar kalle kallan banzan nan ne mu shiga ko in shige in bar Ka,in ka gama za ka biyo ni?"...ajiyar zuciya Nameer ya sauke sannan yace"Gee wlhy tsarin asibitin nan ya burge ni sosai,ina da passion in gina asibiti nima,one day in sha Allah zan gina hospital something like this ya kare yana murmushi", shoulders in Shi Mujaheed ya ɗan daga sannan yace"by Allah sai ka gina wanda ya fi wanann,in sha Allah ka fada a bakin Mala'ikun rahma,yanzu dai ka zo mu shiga mu samu muyi abinda ya kawo mu, Doc Akim is a busy person although na kira shi ya san da zuwan mu,in muka yi wasting time gurin dreaming in future ma rasa shi".."kai dai in magana ce ai ko parrot nan ta gan ka ta bar ka,mu shiga kar ka cika mun dodon kunne"ba tare da Mujaheed ya kulla shi ba,ya murda handle in kofar tare da bude wa, office ce ƙerarre wanda ta hadu da furniture's in kasar waje masu aji da tsadan gaske,zama Mujaheed yayi akan daya daga cikin classic chairs in da ke office in,"Doc Akim yanda ka san  Maggoti baya zama guri daya,yanzu fa na kira na sheda mishi muna kan hanyar mu Amman wai har ya fice wani gurin",zama Nameer ɗin shima yayi a daya daga cikin kujerun sannan yace "maybe wani important abu ne ya taso,na san koma miye he will be on his way tunda ya riga da ya san da zuwan mu",rufe bakin shi ke da wuya kuwa aka bude office in,nan ko Doc Akim Mustapha ya shigo bakin shi dauke da sallama,amsawa suka yi fuska sake ya basu hannu suka sha,yana me basu hakurin aje su da yayi,ya kare yana me zolayar Mujaheed,domin shida ya'yan shi Hydar Aminan juna ne.


Saida ya kawo musu ruwa da Drinks,wanda ya dauko daga mini fridge in da yake office ɗin sannan suka shiga gaisawa,ba tare da bata lokaci ba kuwa Nameer ya shiga karanto mishi halin da Nadeeyar ke ciki,ko da gama jin bayanan shi nisawa Doc Akim Mustapha yayi sannan ya kalle su for some mints kafin ya buɗe baki cike da ingantacciyar turancin shi na wanda yayi karatu kasar waje yace "And where is the patient??..."mun bar ta gida,daman Ni nace masa mu fara zuwa mu sanar da kai tukun na,ya sanya ba mu zo da ita ba".


"Well,doc Nameer right??.. murmushi Nameer yayi sannan ya gyada mishi kai alamun yessss,"have heard all you said,but for now abinda zan iya ce da ku shine You have to bring her here so that we can Conduct A CT scan on her brain",


"A CT scan kuma, what's all that and doc is that supposed to be necessary? Mujaheed yayi tambayar yana kallon Nameer,dan dariya Doc Akim Mustapha yayi sannan ya ce"You said your friend here is also a Neurologist,how comes baka sani ba, although is not your field but ya ci ace Ka sani ai,ko ba ka koya mishi komai ne"ya kare yana kallon Nameer,goshi Nameer ya dafe Sannan yace "Mujaheed yau Computed Tomography scan of the brain ne baka sani ba?'to is a Noninvasive diagnostic imaging procedure that uses special X_rays measurements to produce horizontal or axial, image (often called slices)of the brain".


"Exactly,good explanation doc Nameer , actually abinda ya sa nayi suggesting CT scan ɗin is to know  the exact abunda ke damun ta, although Ka ce  you are thinking due  to some injection ne ya taba mata brain in nata,so yana da mahimmanci ayi scan in don sanin actually inda injection in ya taba,ko kuma wani abu ne daban yayi causing haukar na ta har ya zama kamar harda memory loss a ciki",ya kare yana me sipping in ruwan da ke aje akan table in gaban shi,ko an taba yin CT scan in brain in nata,sai a kawo result in na gani?,kai Doc Nameer ya girgiza alamun a'a,"Okay yana da bukatar ayi hakan" 


"Eh Doc zuwa yaushe ke nan za mu zo da ita",dan jim yayi kafin ya kai ga ba da amsa Mujaheed yayi caraf "big Broz za mu dawo da ita gobe sassafe tunda already yanzu dare ya fara yi, sai a samu ayi mata pls"ya kare yana hade hannayen shi duk biyu,dariya Doc Akim Mustapha yayi sannan yace"your wish,Ku je ku zo da ita din,i will be here waiting for you",godiya suka yi masa,kafin suka fito daga office in na shi,Nameer farin ciki tare da kaunar Mujaheed ne lullube a cikin kasar zuciyar shi,yau in da babu Mujaheed a rayuwar shi be san yaya zai kare ba,this time around Mujaheed in ne ke driving,zuciyar Nameer da tunanin shi na gurin Nadeeya,yana kawai hasko yanda rayuwar shi zai koma in ta samu lafiya ne,ya san dole za ta tafi ta bar shi,after being so attached to her,he just can't picture himself without her being around him,like she has just become part of him, in maganar gaskia zai yi kuma a yanda yake jin zuciyar shi baya jin zai iya rayuwa babu ita.


"Hmm thinking about her right?,Dan guntun tsaki ya ja ya rasa gane why Mujaheed ke saurin gano halin da yake ciki,like ko motsi yayi at times Mujaheed ya kan ce ga dalilin yin ta,wai an ce daman in Zama tayi dadi kuma tayi zama dole a karanci juna a  kuma san komai game da juna,ko ba haka bane readers??,


"Wrong!am not thinking about anybody","hmm Gee ke nan wai why do you always want to run away from gaskiya ne?,Geee look at me do you think you are doing the right thing by punishing yourself?kayi wa kan ka da zuciyar ka adalci ke nan?..idanu Nameer ya zuba mishi for some mints sannan yace "Mujaheed in which way na ke hurting kai na,and punishing my heart?shima Mujaheed ɗin kallon Nameer ya ɗan yi,yana yaba karfin hali da taurin kai irin na abokin na shi,yau shi ya ga abun mamaki ga dai na miji har na miji amman wai ya kasa sanin me ke damun shi balle har ya gano soyayya ya fada,tun ba yau ba ya gano Nameer ya fada soyayyar Nadeeya,as in so me karfi ma kuwa wanda rashin sanin hakan yake lakaba wa kan shi kalman tausayin ta ya ke  ji ba so ba,zai iya ce wa maybe shekarun da aka dauka bayan mutuwar Raa'isaa ne ya mantar da shi soyayya,ko kuma bayan mutuwar na ta ne ya kasa bude zuciyar shi har ya bata abinda ta ke so,duk wanda ya san Nameer ya kalle shi a yan kwanakin nan zai tabbatar da yana cikin matsananciyar damuwa,wanda ba komai ya haddasa hakan ba kuwa sai so da kaunar da ya ke wa Nadeeyar,gefe guda kuma ko be fada ba ya san a matukar tsorace ya ke ,ba kuma komai ya haddasa tsoron ba sai tunanin rabuwar su da ita ta zo da ya daura wa kan shi.


Hannun shi Mujaheed ya dafe Sannan ya yi parking in motar a gefen titi,tare da dafe hannayen shi da suka dau sanyi"Hey Gee listen to me,can you go easy on yourself plz,na ji ko ba za ka fada mun damuwar ka ba,but it's kills me in na gan ka cikin damuwa wlhy,why za Ka tsaya kana daga hankalin ka,what if in wani abu ya same ka?who will take care of Mama, little Angel and Pookie?,kamar an soso yanda yake mishi ƙaikayi cikin turo baki yace"Mujaheed Pookie tana da family in ta da za su yi looking after her,Mama ne kawai da Angel ita abun tunani,after all in ta warke ai tafiya za tayi ta bar mu ko?,dan dariya Mujaheed in yayi sanann yace"is that why you are keeping the boring face?,Kai to miye na ka, let's assume son ta kake yi ka ga shine abinda zai daga maka hankali in ta warke ta koma gidan su,Amman babu ko daya iya kan ku tausayi ne,tausayin ta kake ji and za ka fi kowa farin ciki ganin ta warke,ta koma wa family in ta,and wlhy ba karamin dadi za su ji ba,don na san duk yanda su ke hankalin su yayi dubu a tashe sun yi kuka har sun gaji"..."wai Mujaheed sam ba ka gane abun da nake fada wlhy🥺,i mean in ta warke shike nan fa za ta yi tafiyar ta,ta mance da Ni?ya kare kamar zai yi kuka.


"Mantawa kam ai da gudu ma kamar ta mance ne,kila ma tana da wani wanda take so,ko a family akwai me son ta,tunda ka ga daman ka ce mijin ta ya sake ta,and saki uku cif yayi mata babu wani Idda akan ta,kila tana komawa ma da sati biyu a daura mata sabon aure,don yanda take da kyan nan,barin ta haka hatsari ne,in kuma za ka raka ni,sai mu je Bauchi in nemi auran ta ka ga na dawo wa Mama da Angel da Pookie in su",wata uwar harara Nameer ya sake mishi"don't even try that shit with me,or you regret it, Mujaheed! Pookie is MINE!!!ya kare kamar zai yi kuka,zama Mujaheed ya gyara sannan ya ce "yau na ga ikon Allah wai na kwance ya fadi🤔a ina ne Pookie in ta zamo yours kuma?,ya kare yana tsare shi da idanu,goshi Nameer in ya dafe sannan yace"i mean for now she is under my care,so kamar Mine take ai ko like she is my responsibility yanzu ai ko,and am just a bit angry ya za a yi in sanya mata suna da kai na sannan ka ce wai ka dawo wa su Mama da Angel da Pookie in su, that's my Pookie you are talking about fa"dan tsaki Mujaheed ɗin ya ja tare da kunna motar don har ga Allah Nameer in kuma yanzu ya fara bashi haushi,shi tunda ya zo duniya be taba ganin dan iska irin Nameer ba,wai ya fada yana son yarinya ya tsaya iskanci wa mutane,ai ko in yace zai kure shi wlhy zai bashi mamaki sai ya sanya mishi ciwon rai,tunda common expressing love ne ya gagare shi,tsaki ya kuma ja a fili ba tare da ya kalli Nameer ɗin ba yayi kwafa a ran shi yana me fadin,da ni kake wasan,za ka san ba ka da wayo soon,ganin yanda Nameer in ya wani tsuke fuska ya so ba shi dariya amman sai ya basar,ya cigaba da driving in shi tare da bin wakar da ke tashi a motar,seat Nameer yayi adjusting tare da kwanta wa yana me lumshe idanun shi zuciyar shi cike da damuwa.


****************RIMI CLINIC 


    A fujajan Alh Kabiru ke tafiya cikin asibitin Rimi yana baza babbar riga kan nan ko arzikin hula be samu ba,kallo daya za ka mi shi ka fahimci yana cikin tsananin tashin hankali,don daga yanda yake jefa kafafun na shi in ba sanin shi kayi ba ka dauka ai hauka ce sabon kamu ta kama shi.


Saukowar shi ke nan daga jirgi,motar da ta zo daukan shi direct asibiti ya ce a kawo shi,ba tare da ya je gida ba balle a kai ga batun wanka cin abinci da canza kaya,shi sallah kam daman ya dade da cire shi daga cikin schedules na shi,coz tunda ya shiga Brotherhood suka yi bankwana da yin Sallah,daman can shi din ma ba gwanin ibada bane,ya sanya ko da ya shiga Odogwu yace babu shi babu sallah,ya ce ta fi nono fari,don kama daga Sallah,Azumi,Sadaka,da Zakka,ba yi ake in an shiga Brotherhood ba,yo daman can ibadar ba damun shi ta yi ba,(domin fadin Allah ne cewa ita Sallah tana kare mutum daga fadawa da aika ta Alfasha tare da Munkar,duk wanda ya kiyaye ta to zai yi rayuwa cike da kwanciyar hankali da farin cikin,aka ce ko wani aiki kake mara kyau in ka rike Sallan ka hannu biyu biizinallah za ka daina aika ta wanann aikin,in kuwa ka ga baka daina ba to tabbas ka bincike sallahn ka baka yin ta yanda Annabin Rahma ya koyar, ubangiji ka dauwamar da digadigan mu a bautar ka)


Ba tare da ya kula da sannun da Asiya,kishiyar ta da yaran shi ke mishi ba ya wuce su tare da fadawa office in babban doc in da ke asibitin,Saida shi kan shi Doc ɗin ya tsorata ganin inda Alh Kabiru ya fado mi shi office kai tsaye ba sallama balle wani neman izinin 


"Doc ina Ayman ina yake hope ya tashi?,ya kare kamar zai rusa ihu,numfashi Doc Hussain ya sauke sannan ya ce"Alh you have to calm yourself down"


"How do you expect me to be calm after all yaro na yana kwance in a critical condition fighting for his life?,just tell me ya jikin yaro na yake, hope ya tashi,maybe he have been calling my name right? take me to him doc I want to be the shoulder in da zai yi kuka a kai,his dad is here,take me to my son".


"Alh ka kwantar da hankalin ka pls,ka dai san sarai kana da high blood pressure,so ko don health ɗin Ka you have to stay calm,Ayman up till now he is in danger,but zai farfaɗo just let's keep on praying for him",katse shi yayi cikin sauri"Hussain can I see him?,"Alh Ka dai kara hakuri har ya samu ya farfaɗo,don am sure bara ka ji dadin ganin shi ba"..."zuwa yaushe zai farfaɗo?sanin kan ka dai Sarai na tsani jira a rayuwa ta,yana daya daga cikin reason in da ko ciwon Nails nake na gwammaci na tafi Abroad su duba ni tsaf,i think I have to call Doc John from United State yayi mana making arrangements gwara mun tafi can maybe za a fi saurin ceto ran shi",ya kare yana kokarin fita daga office in.


"Alh for Ayma's good Kar a fita da shi ko ina, because he isn't in a good shape in da za a iya long journey da Shi ba,all the way from Nigeria to United State,so ko da fita da shi kake da niya,just wait a little longer ya samu ya dawo daidai tukun nan"ba tare da Alh Kabiru ya so ba dai ya yarda bayan lallashin shi da Doc Hussain ya yi ta yi.


Fitowa ya yi,a kan kujera ya tarar da su a zaune kowa yayi tagumi,masu goge hawaye na yi,abun haushi duk cikin su babu me kiran sunan Allah balle a kai ga sun yi addu'a wa dan uwan na su da ke kwance fighting for his life,balle a kai ga maganar nema wa Jaazmeen rahma gurin ubangijin ta.


Zama yayi kusa da  Asiya,da idanun ta suka kada suka yi ja,ko ba a fada ma ka ba ka san ba karamin kuka ta sha ba,ai da ganin Alh Kabiru zaune kusa da ita,bata san time ɗin da ta fada jikin shi ba tare da fashe wa da sabon kuka"Alh Ayman in mu,har yanzu be farfaɗo ba,ina tsoron abinda zai same shi wlhh, kullum yana fada ina dauka wasa ne,daman ya ce duk Randa Jaazmeen ta bar duniya to wanann ranar shima ba zai kara numfashi ba",da sauri ya rufe mata baki"ya isa haka Asiya ki ma daina fadin irin wanann munanan zancan,babu abinda zai samu Ayman ɗin mu kowa yayi shiru,a daina kukan nan haka,kar kan ku ya yi ciwo,Doc Hussain is trying all his best,and kin riga da kin san best Doc ne da ya kware sosai da aikin shi,so stay calm babu abinda zai same shi okay"ya kare yana shafa bayan ta, alamun lallashi,dan shiru ne ya biyo  baya ka fin can ya nisa,tare da amayar da abinda ke cikin sa.


"Asiya ni kam wai me suka ce muku yayi causing mutuwar yarinyar nan ne,da duk ya sanya my boy ficewa daga hayyacin sa?,nisawa tayi sannan tace"a bisa binciken doctors dai sun ce jinin ta ne kaf ya kare,ita da jaririn da ke cikin ta,wanda is very strange ace yarinya lafiyar ta kalau mu ka kawo ta, banda dan ciwon Nakuda da ke damun ta,amman wai jinin su ne ya kare duka"ta  kare tana me jajanta lamarin.


"Yau na ke ganin abun mamaki,Asiya babu wani ciwo ko wani zuban jini kawai ace jini ya kare"


"Wlh Alh mu ma nan tun jin labarin a cikin mamaki muke,ni kaina na kasa yarda da maganan Doc in nan,domin sai kace wace tayi gamo da mayyu,suka shanye mata jini,ita da abun cikin ta,sai dazu ne ma hankali na ya ɗan kwanta jin cikakken labarin me ya faru",zama ya gyara sanan yace yi sauri ba  ni labarin abinda ya faru"


"To dazu dai,duk muna zaune ana jajanta lamarin,sai na yi over hearing in wani cleaner nayi Wa dan uwan sa  gulma,in sa kunne sai na ji kamar labarin da ya ke yi ya shafi Jaazmeen,shine na kira shi I asked him me ya sani,nan ya ke bani labarin wai ashe ya zo shara ta kusa da ita,to sai ya ga tana waya,jim kadan ta hau wani irin tari kamar wanda ake shirin zare wa rai,wai ashe akwai wani mutum kusa da ita da goron faro a hannun shi,don har bottle in ma ya nuna mun,to shine mutumin  ya bata ruwan ta karba a take ta sha ya kai rabi,to gama shan ta ko mintuna ba ta kai ba,wai shine ta fadi kasa tana ta juye juye kan doctors su zo har ta cika,nan bayan binciken su,aka gano wai jinin jikin ta ne ya kare tas tare da na Babyn cikin ta,abinda yayi causing mutuwar na ta ke nan,sakamakon haka ya jefa Ayman in mu a wani hali"ta kare tana wani irin sabon kuka.


Da sauri Alh Kabiru ya mike,zufa na karyo mi shi ta ko ta ina,idanun shi a warwaje kamar wanda aka shake ko ya ci yaji,bugun zuciyar shi na karuwa,har wani fizfizga yake yi,sai a lokacin brain in Shi yayi clicking,sai lokacin ya tuno wayar da Sen ke ta yi mishi har ya kashe wayar don avoiding calls in Shi,lokacin da ya tuna sanda ya ke ce wa Rilwanu ya je Rimi ba zai rasa me cikin da zai bayar ba ai sai ya dafe baki tare da saurin cire babban rigan shi,a fili ya furta"Na shiga uku ni Kabiru,me na aikata haka"ya kare cike da tsoron abinda yake tunani kar ya zama gaskiya.


"Alh me ya faru da kira wa kan ka shiga uku haka?,in kan jikin Ayman ne ka kwantar da hankalin ka please,sanin kan ka dai Sarai kana da Bp"Amaryan shi Kubra ta fadi tana taɓe baki,ba tare da ya kalle ta ba balle ta sanya ran samun amsa daga gare shi, domin zuciyar shi ba ta gurin,fargaba cike da tsoro ke tattare da shi,nan gurin ya yarda Babban rigar shi tare da ɗaukan makullin motar shi,dan ko wayar ta shi ma be dauka ba,gani ya ke kamar bata lokaci ne,bayi da burin da ya wuce ya gan shi cikin gidan Audu Waziri.


"Alh ina zuwa kuma,na ga yanzu ka dawo daga tafiya,ai ka tsaya ka huta dai ko,ko kuma gida za ka koma ka ɗan watsa ruwa,ka ci wani abun sai ka dawo kila zuwa nan Ayman in ya farfaɗo,ga dare yayi  balle a samu a kai yarinyar nan kabarin ta"Asiya ta kare tana kallon shi,shi wlhy tsaf ya mance ma da maganar kai Jaazmeen kabari,ashe sai an yi mata wanka da Sallah,ga shi dare ya riga da yayi  ,duk tsiya ya san in dare yayi ba a kai mamaci makwancin shi,saidai a jira gobe"Ku jira ni akwai important abinda ya taso mun,yanzu zan je na gama,zan dawo sai ayi abinda ya dace in"be kuma cewa komai ba ya sanya kai tare da ficewa daga cikin asibitin yana jin yar shi na kiran "Daddy ka mance da babban rigar ka",be juyo ba balle ya tsaya sanya ta don ba ita bace a gaban shi.


A 360 ya fige motar don cewa driver ma yayi ya bar shi zai yi driving da kan shi,coz gani ya ke in ya bari driver ya yi driving in ba zai yi saurin da ya ke so ba,tafiyar yan mintoci ne ya kawo shi GRA daga Rimi clinic,horn ya ringa danna wa kamar zai tashi gidan,da sauri securities suka zo don ganin waye haka,da yamman nan ke neman daga musu hankali.


Lekawan da su Sunday za su yi kuwa,su ka ga motar Alh Kabiru wanda ya ke ji kamar ya haura ta saman katangar gidan,ba karamin mamaki suka sha ba,don daga ganin yanayin shi mutum zai tabbatar da ba ya cikin nutsuwar shi,don tun sanin su da shi be taba zuwa gidan cikin tashin hankali haka ba.


"Will U open that gate in samu in shiga ko sai na ci uban ka"ya kare a zafafe,jin haka ya sanya Sunday saurin wangale gate ɗin,tare da saurin matsawa don saura kiris Kabirun ya bi ta kan shi da mota,ba tare da ya tsaya gama parking ba motar na kan diri ya bude tare da fito wa"Rilwanu na ciki?,shine abunda ya tambayi Sa"eed da fitowar shi ke nan daga dakin sa na gidan,"yana ciki sir,tun dazu  da yamma da ya dawo be fita ko ina ba i think",be amsa shi ba illa nufar cikin gidan da yayi,da kallon mamaki Sa"eed ke bin shi thinking me ke samun Alh Kabiru haka da ya fito ko hula babu a kai haka.


"RILWANU AUDU WAZIRI!!,sunan da Kabiru ke shouting at the top of his lungs ke nan bayan ya shigo cikin parlo in Sen,shiru babu almaun Sen balle amsan shi,hakan ya kara frustrating in Shi,ya shiga kwala mishi kira kamar throat in Shi zai fashe,Sen da ke cikin toilet,jin yanda ake ta shouting sunan shi and in ba kunnan shi ke yaudaran shi ba kamar muryan Aminin shi ya ke jiyowa daga kasa,hakan ya sanya shi sauri wanke hannun shi,tare da janyo towel ya goge hannayen shi tare da fuskan shi,sannan yayi saurin fitowa,zuciyar shi kal don tun dazu yake neman layin Kabirun don sheda mi shi yanda aka yi,amman be dauki wayar ta shi ba,da sauri ya fito daga toilet in tare da sanya classic slippers in Shi ya fese jikin shi da designers turaruka, sannan ya fito, cikin takun isa wanda hutu da kudi suka zauna mishi,fuska dauke da murmushin samun nasara da cikar burin shi,domin zoben shi ko 30 mints be yi da bada yarinyar nan ba,ta matse shi tam tare da yin haske alamun Sacrifice in Shi ta karbu ke nan,jin shi ya ke sakayau yau babu wani tsoro ko fargaba a tattare da shi,dariya ya sake don ganin sun kusa clashing da juna da Alh Kabiru don yana sauko wa daga staircase shi kuma Kabirun yana haurowa.


"Ahhh mutumi na!dan halak ya ki ambato,ina ka shige ne ina ta kira,baka picking karshe kuma wai wayar a kashe"ya kare yana me jan hannun sa suka shiga sauko wa,jin shiru be amsa shi bane ila idanun da ya zuba mishi baya son ya gaskata zargin zucin da ya ke mi shi.


"Wai tsaya kar ka ce mun dawowa kayi, saboda Ni?kar saboda na ce na kasa samun matar da zan bai wa Odogwu ya sa ka dawo don ka taimaken?,ba tafiya ka ce za ka yi ba?,be damu da rashin amsa shi da Kabiru ke yi ba,ya cigaba"gaskiya Amini na you are one in a million,just imagine wani aboki ne will stick with you throughout your difficulties in life,gaskiya am blessed by your presence in my life"ya kare yana rungumo Kabirun jikin shi 


Hankaɗe shi Kabiru yayi don jin wani irin tukukin bakin ciki da ya tokare zuciyar shi,idanun shi da suka kaɗa suka yi jawur,ya zuba su akan Sen yana bin shi da wani irin kallo,mamaki kwance a fuskan Rilwanu shima ya zuba mi shi na shi idanun,deep down asking himself what the hell is wrong with Kabirun.


"Rilwanu na dawo ban ma dade da isowa Bauchi ba,ka kira wayar tana jaka da na hau jirgi kuma na sanya ta flight mood na kuma mance ban cire ba"..."au na mance kai fa haka kake in kayi tafiya ka yi ta ɓace ɓacen rai,yanzu dai na ga kamar a gajiye ka ke,ko za mu shiga daki kayi wanka,a kawo ma ka abinci ka ci,sai ka zo muyi celebration"wani irin tsinke wa zuciyar Kabiru yayi,a hankali ya furta"Na shiga uku kar dai fa zargi na ya zamo gaskiya"


"Celebration in me kake so muyi Rilwanu wani abun ne ya faru",asking with the hope of Allah ya sa ba abinda yake zargin ji bane zai fito daga bakin Aminin na shi


"Well da na so sai ka nutsu in sanar ma ka,don tun dazu na ke ta kira don in sheda maka, unfortunately Baka dauki waya ta ba,wlhy shawarar ka a kullum shine best,da mutum ya dauka damuwar shi ta ke yaye wa,my friend you get brain aswear to God,dan nisawa yayi sannan ya cigaba,ka san at first brain ina ya toshe ban ma San ta ina zan fara ba,Saida muka yi waya ka kawo suggestion in why not in je asibiti,wlhh kuwa kamar ka sani ina zuwa ban fi 20 mints ba na samu abinda ake nema,har na bada ita"


Baki na rawa Kabiru ya ce"Wani asibiti ne,Rilwanu wani asibiti ka je??"mu zauna mana in kawo maka lemu ka sha"..."Rilwanun ba ta lemu na ke ba,can you answer the damn question na ce WANI HOSPITAL KA JE",ya kare ran shi na tafarfasa.


Mamaki ne ya kama Rilwanu "why are you sounding harsh,wai what is wrong with you ne?.."Rilwanu can you pls tell me wani Asibiti ne ka je pls,i have been asking you since"ya kare a kufule yana ji kamar ya rufe Rilwanun da duka.


"Just imagine,wai wani irin tambayoyi ne haka kamar wani dan jarida,ba kai ka bani shawarar zuwa Rimi ko As_salam ba"da sauri ya katse shi da "i hope As_salam in Ka je ko?


Dan tsaki Rilwanu ya ja "wani irin As _salam Ni da ba wani sanin kan asibitin nayi ba,in dau kafa all the way from GRA har Gida dubu,bayan ga yanda muka fi kusa,Ni kam Rimi na je,and lucky me na samu me cikin da i think ma tana gaɓa da Nakuda a take na bata ruwa a gora tana tari ta sha,ba ka gan ta ba kuwa fara sol me I think ma ba yar nan kasar ba ce don ta fi kama da Laraba wa,ta sha jan lallan ta kuwa,dan kai ya girgiza sannan yace baiwar Allah da mijin ta kuwa take waya kawai tari ya kama ta,am looking for an opportunity daman,a take na bata ruwa ta sha without any hesitation,Ni ko nayi saurin barin asibitin, poor lady ya kare yana me sheke wa da dariya ".


Yanda kuka San saukan guduma haka Alh Kabiru ya ji saukan kalaman Sen,rai a matukar ɓace,har idanun shi na dishi dishi ya yo kan Rilwanu ba tare da bata lokaci ba ya damko kwallan rigan shi rai a matukar ɓace,zuciyar shi na tafarfasa,bakin shi har kumfa yake gurin kiran sunan shi


"RILWANU AUDU WAZIRI!!ka ko san wa ka bada wa Odogwu,babban Bura uba yau ake yin ta,DARA TA CI GIDA wlhy Sirika ta ka bada,Matar 'da na Ayman ka bada,yaron cikin kuma jika na ne da ke shirin zuwa duniya,kana hauka ne Rilwanu ni za ka ci wa amana bayan duk abinda nayi maka a gidan duniyar nan ka rasa da me za ka saka mun sai haka",ya kare yana girgiza Sen kamar me shirin cire masa rai.


Kwata kwata Rilwanu be fahimci yanda zancen nashi ya dosa ba,kamar ya ya ci Amanar shi,a ta wani hanya ma ya ci mishi amana?,ganin yanda yake rike da kwallan rigan shi,har yanzu yana bin shi da wani irin kallon da be ma san matsayin da zai aje kallon ba ya sanya shi jin ran shi ya soma ɓaci ,be ga dalilin da zai kawo Kabiru har cikin gidan shi ya nemi ci masa mutunci ba,yo ina ma dalili,yana dan takarar gwamna a ce wani ya shigo ya ga yanda Kabiru ke rike da wuyar rigar shi ai ya zubar mishi da mutunci,cikin ɓacin rai,shima ya fusge hannun Kabirun daga rikon da yayi masa,ido cikin ido yace"Kai dallah dakata mun wani irin giya ka sha ne haka da za ka shigo cikin gida na,kana fada mun duk maganar da ya zo bakin ka,Are You mad or something?Na yi maka kama da dan iska ne,da za ka kalli tsaban ido na ka ci kwalan riga na,sannan ka budi baki kana kira na da maci yi Amana?a gidan uban wa na ci maka amanar,ko a yaushe ka bani Amanar har na ci maka ma oho,You better watch your tongue while speaking to me,in Ka mance in tuna maka cikin gidan Sen Rilwanu Audu Waziri kake cikin parlor in Shi,and in Ka kuma mantawa in tuna ma ka Ni dan takaran gwamna ne me jiran gado,so Kabiru I respect you a lot as a friend Kar mu yi abinda za muyi danasani daga karshe"ya kare yana zama a kan kujera tare da daura daya kan daya.


Tafi Kabiru ya shiga yi hannu biyu biyu"Wow!wow!!just Wow,daman me zan yi expecting bayan haka,lalle Rilwanu yau ka cika mugun butulu kuma dan iska,Ni za ka kalli tsaban ido na ka ce za ka fada mun magana son ran ka",a harzuke Rilwanu ya mike"Kai Kabiru daka ta mun,kar ka ga nayi maka shiru ya baka daman fada mun duk abinda ya zo bakin ka,in ana maganar iskanci har kana da bakin kiran mutum dan iska?yau nake ganin ikon Allah wai har kura zai kira kare mayye,mutumin da baya iya bacci ba tare da ya ji shi jikin mace ba,mutumin da tsaban iskanci da zalamar shi ya kan hada mata hudu ya kwanta da su lokaci daya ne wai har yake da bakin kiran wani dan iska",ya kare yana shekewa da dariyar iskanci .


"Yayi kyau Rilwanu, Amman ina so in sanar maka wani abu in tone tone aka ce za a yi to kai ma ai ba tsira za  ka yi  ba".."daman wa ke tsoron tone tone kashi ne ko wannan mu yana manne da shi a duwawun shi,ba zai yu don ina kaunar ka ka maida Ni dan iska ba,ce maka aka yi ban san ciwon kai na ba,ko ka ɗauke ni yaron gidan ka ne,ka shigo har cikin gida na kana fada mun magannun da duk suka zo bakin ka,tun zuwan ka na lura da magana a ranka,amman na kwantar da kai nake ta bin ka a sannu,dauka na kayi Jaki ne ni ko me?,


A harzuke Kabiru yace"miye maraban na ka da Jakin,domin Dabba ne kawai zai iya aikata abinda ka aika ta,shine duk yanda me kiwon shi ya kai ga kaunar shi wataran sai ya butulce masa,why on earth would you stab me from behind,me nayi maka Rilwanu da za ka mun haka,Yarinyar da kake kirarin ka ba da ita,ba kowa bace sai Matan Ayman yaro na,sirika ta ce,and saboda abinda ka aika ta yaro na na kwance in a critical condition fighting for his life"ya kare yana hararan Rilwanu,idanu Sen ya zaro sai yanzu wlhy ya fahimci yanda maganar Kabirun ya dosa,goshi ya dafe a garin yaya ya bada Surukar Aminin shi be sani ba,ya Salam yau ake yin ta,dole kam yayi fushi,cikin muryan lallashi da kyar ya iya fadin"Come and seat down pls let's talk,yanzu na fahimce ka wlhy,your anger is well justified amman I want you to hear from me, kafin ka kai ga yanke hukunci".


"Seat down!Ni za ka fada wa kalman seat down ma,ai duk maganar da za muyi gwara mu yi shi a tsaye,don ka san am fucking serious,taya ma zan zauna Ayman na kwance rai a hannun Allah"..."excuse me Kabiru ya kamata ka zauna ka saurare ni,do you think yanda kake son Ayman Ni Bana son sa ne??Ko dauka kake da gangan zan bada Sirikar ka, believe me between me and my God ban San yarinyar nan matar Ayman in Ka bane,kar ka mance time in da aka yi auran su ban samu zuwa ba,tunda ba a kasar nan aka yi auran ba,and tunda mu ke for once Ka taba nuna mun ko da  hoton ta?Balle ka ce with intention in ci maka amana na bada ita,Kabiru you are  more than a friend to me,in abun cutar wa ya zo Ni zan iya dauke maka ka rayu,balle a ce ni zan zamo silan jefa ku a damuwa,haba kar ka haɗa brain in Ka da tuwo ka cinye mana",


"Bloody lies,Kai Rilwanu ka dube Ni da kyau ba yaro bane ni,da za ka raina mun wayo😏ba,ka ba da jinin Sirika ta tare da jika na,sanna ka zo kana mun wani kokarin cover up,Na rantse muddum wani abu ya samu yaro na wlhy tallahi,i swear to you with my living God sai na ga bayan ka,Ni nan zan kashe ka da hannu na"


Tassssss kuke jin saukan mari a fuskan Alh Kabiru,da matukar mamaki,tsoro da firgici ya dago hannu dafe da kumatun shi, can't believe wai Mari ya ji ya sauka a fuskan shi,rabon da hannu ya kai jikin shi a sunan duka ai ba zai iya tuna wa ba,bakin shi na bari "Rilwanu ni ka mara?


"An mare ka din,maybe this slap will bring you right back to your senses,how dare you,za ka kalli tsaban ido na ka ce wai sai ka kashe ni akan wawan 'dan ka me kama da yan daudu ya mutu"..."Rilwanun!!!na rantse da Allah zan ci maka mutunci,in ban ga bayan ka akan Ayman ba in zama ɗan wuta",wani irin wawan dariya Sen ya sanya


  "Au wai daman kana tunanin kai din ba dan wuta bane,🤣🤣funny you,Ka ci naman mutum ka sha jini, uban ka ke raba Aljannar da zai baka ka shiga ehyeeeee,dan tafa hannu yayi sannan yace au wai yanzu ne aka taba yaron gold ko da kake tunanin daukan rai na saboda shi, don't forget yarinyar da ka bada shawarar a haukatar da ita,a kashe ta that's my only Daughter,I am her father,ya kare cike da ihu wato Ni ban san ciwon kai na ba ko,yaron ka ne yaro wanda aka haifa da jini a jikin shi,Ni nawa yarinyar ai tsintar ta nayi ya sanya duk shawarar da ka bani na ke dauka,kai Kabiru lemme remain you something da kake yawan fada mun kullum,'Everything is fair in Love and War',so in ni ne Kai Wlhy ban ga abun tashin hankali ko abun magana ba,a kullum me kake ce mun kar in duba me zai faru,ranar biyan bukata rai ba a bakin komai yake ba,don na dau advice in Ka shine me,na ga asibitin nan kai ka sanya ni zuwa,sannan i even swear to you that wlhh ban san in law in Ka bace da ba zan bada ita ba, Amman ka ki yarda,to shike nan Kabiru Ishaq na bayar da so called daughter in law in na ka intentionally kayi duk durun uwar da za ka yi ,tunda kai Shege ne mara mutunci to wlhy daidai nake da zamanin ka,am done with you za Ka iya barin mun gida na tunda ba da kudin uban ka na gina ba,sannan is of no use talking to you,tunda kai ba ka san mutunci ba",ya kare yana haurawa upstairs zuciyar shi kamar zai fado saboda bakin ciki,he just can't believe wai Kabirun da suka sha gwagwarmaya tare ne,ya shigo har cikin gidan shi tare da yi mishi irin wannan diban albarkan akan laifin da it wasn't intentional 


"Yayi kyau ,nace da kyau Rilwanu walk away from me,but wlhy put it in the back of your mind and Kar Ka kuskura ka mance i will get back to you,I will hunt you down in dai wani abu ya samu yaro na,mark my words you just started a war between us,and yakin ya fara kenan kai dai plead with God,za Ka iya sanya uwar ka ma taya ka rokon shi wani abu kar ya samu Ayman don wlhh in dai yaro na ya mutu sai ka mutu kai ma,my eyes are on you,if I am going to hell I will make sure to take you with me"ya kare cikin ihu.


Wata wawiyar dariyar Sen ya sanya"ai duk me yi baya fada Kabiru, it's been long tun da na roki Allah wani abu,but i promise you yau din nan kwana zan yi ina rokon shi akan wanann dan iskan ɗan naka da aka yi asarar haihuwar sa me zubin dan Daudu ya mutu sai in ga uwar da za kayi,su 'dan na ka ne ai 'Da?Yau watanni nawa nawa yar ban san duniyar da take ciki ba,na taba blaming in Ka? Amman saboda kai Shege ne Wawa mara tunani har za ka zo kana fada mun haka,kar ka yi  tunanin don ka mun silan arziki ya zamo sai yanda ka yi da ni sanin kan ka ne Sarai ni Rilwanu ba sakarai bane,ina kyalle ka ne kawai saboda na san mutunci,in an taba Ka kace kayi mun hallaci nayi maka butulce,na ga silan kudin kawai kayi mun,ko ka taba bada wani abu don nayi benefiting from you,this should be the first and last time in da za ka ma kara tunanin yi mun gori,as you said war ya fara,to don Allah kar ka fasa,Nima baran fasa ba,mu zuba mu gani Allah tsine wa uban da ya ji tsoro,i am ready for you kuma kamar yanda ka ce Ni ma zan fada maka You better watch your back,don ba kyalle ka Nima zan yi ba,maza ka fice mun daga gida tun ban kira police sun zo sun kame mun kai ba,ka kare rayuwar ka a gidan yari"...."fine yayi kyau Rilwanu let's see Shege Ka fasa mu zuba Ni da kai din".."ai in Ka fasa ka raina uwar da ta kawo ka duniya,dan iska wanda ke neman mutum da sharri,kai yaran mutane nawa ka cinye da za ka zo kana fada mun magana son ran ka,to ba sai ayi War in ba uwar ka nake tsoro ko uban ka",Sen Rilwanu ya fada kamar zuciyar shi zai fado yana haurawa sama don baya butakar komai a daidai wannan lokacin da ya wuce giya...iya bakin ciki Kabiru ya shige ta,da kallo ya raka Rilwanu da yayi shigewar shi dakin shi,ji yake kamar ya bishi ya soka mishi wuka ko ya harbe shi da bindiga,be taba sanin Rilwanun dan Akuya bane sai yau,wai har shine yau Rilwanu ke kora daga gidan shi,a wani gidan ma,shi da shine silan arzikin shi,wato gaskian hausawa ne da suka ce 'in ka ga wani mutum a rana bar shi a nan yanda ka gan shi,domin ba ko wani dan Adam bane yayi deserving inuwa daga gare ka,sai kayi mishi rana shi kuma yayi maka dare',kwafa yayi tare da jan ƙafafuwan shi da suka yi mishi nauyi da sanyi ya fito daga cikin gidan,ji ya ke kaman ya kunna wa gidan wuta Rilwanu ya kone tare da mutuwa kowa ma ya huta, addu'a kawai yake a ran shi Ayman ya warke domin in Ayman ya bar duniyar nan to babu abinda zai hana shi daukan ran Rilwanun,motar shi kai tsaye ya fada tare da kunna ta a 360 ya bar gidan,duk ma'aikatan gidan sun san ba lafiya ba,ganin yanda ya fito kamar wanda ake shirin tashin kiyama,ga hayaniyar da suka ringa jiyowa daga parlorn Rilwanun,mamaki suka yi sosai ba kamar Sa"eed ma,don duk wanda ya ke zaune gidan ko kake tare da Rilwanu to dole ka san da zaman Kabiru domin abu ne mafi wahala ka ga daya ba tare da ka ga dayan ba,to rashin sanin abinda ya haɗa sun ya sanya kowa jan bakin shi tare da komawa bakin aikin shi,Kabiru be iya komawa Asibitin ba,guest house in Shi  kai tsaye Kabiru ya wuce domin a halin da ya ke ciki baya jin zai iya shiga cikin mutane,he just need some mad sex and alcohol ko zai dan ji sassauci daga kunan zuciyar da ya ke ciki,ba tare da bata lokaci ba kuwa ya kira karuwan shi har biyu,tare da ce da su,su same shi a guest house in Shi,wannan daran mutane ukun nan ba su samu kwanciyar hankali har su samu bacci cikin nutsuwa ba,Nameer fargaban abinda CT scan in Nadeeya zai nuna yake, gefe guda kuma he is scared of losing her,har Saida Mama ta gaza hakuri ta tambayi me ke damun shi don ya sanar mata gobe sassafe za su asibiti shi da Nadeeya,ciwon kai ya ce yana yi inda ta bashi magani tare da mishi addu'ar samun sauki,shi kuma Rilwanu takaicin abinda Kabirun ya masa ne ya hana shi ba bacci,haka yayi mankas a daki yayi ta fashe fashe,while Kabiru raba dare yayi yana zina da yaran mutane wai duk don ya samu haushin cin amanar da Rilwanu yayi mishi ya bar ran shi(Ni ko na ce ko a taya ya ci Amanar ma ka sai Allah 🤔😏).


***************KADUNA STATE


kamar yanda suka yi da Doc Akim Mustapha kan sassafe za su kawo Nadeeyar kuwa sun cika alkawari,da wuri Mama ta shirya ta, Mujaheed ya zo ya dauke su suka taho,Mama ce mishi tayi duk yanda ake ciki za su yi waya,in kuma ba su dawo da wuri ba ta gama abun da take yi za tayi wa Angel wanka sai su taho tare,da wayo da dabara aka samu aka sanya ta cikin Machine in da ake Scan in a hakan ma saida aka kai ruwa rana,da duka kuka da komai aka samu Allah yayi aka yi scan in aka kammala,a hannun wata Doc me kirki aka bar ta,sannan suka wuce office in Doc Akim Mustapha don jin me zai ce game da scan result in.


Saida ya kalli result in for some mints Yana dan nazari sannan ya nisa tare da dagowa ya kalle su,"Doc I hope ba wani damuwa bane ko"Mujaheed ya tambaya idon shi na kan result in kamar me shirin gane abinda ya kunsa.


Ajiyar zuciya ya sauke sannan yace "Doctors Baran boye mu ku ba,akwai matsala",bugawa zuciyar Nameer yayi tun kan ya ji miye matsalan har ya ji jikin shi yayi sanyi,"Doc Akim hope ba wani babban matsala bane right,ina ce za ta warke ko",Nameer ya fada kamar zai yi kuka.


"Well abunda Scan result in ta ya nuna gaskia matsala ce,amman ba wanda ba ra a iya warke wa from it ba,kamar yanda ka fada mun Chlorphenamine aka ringa dura mata,which ka riga da ka sani high dose of that drugs or injections ɗin shi usually blocks the effect of Acetylcholine,Dan nisawa yayi sannan ya cigaba shi Acetylcholine in nan as you already know is a chemical in the brain that helps send message between cells,so by blocking Acetylcholine can causes temporary drowsiness, confusion, mental illness and can cause memory loss also".


Nisawa Nameer yayi domin tas bayanan Doc Akim Mustapha babu karya haka ne,ko randa ya fara ganin aluran ba karamin tashi hankalin shi yayi ba,domin ya na jin labarin effect in magani da alluran ke causing,if care not taking ma har kashe mutum ya na yi,ajiyar zuciya ya sauke sannan ya ce"to Doc duk mun ji and mun gane but what is the way out pls,akwai wani abun da za a iya yi na ganin ta dawo hayyacin ta?


Dan nisawa Doc Akim Mustapha yayi sannan yace"Well akwai several ways ma,but in her on case the best solution here is to undergo a Psychosurgery on her,don in muka ce za mu bi ta drugs ba wai na ce ba zai yi working ba but it's will take time gaskia,domin an riga da an yi mata injections in da yawa"


"Nameer ka san dai Sarai Ni ba gane wannan abubuwan na ku nake ba,wai me yake nufi",nisawa Nameer in yayi sannan ya ce"bayanin CT scan in nata ya ke mun,wai it's shows that due to aluran da Doc Bashir yayi ta daura mata yayi blocking Acetylcholine in ta,wanda shi ne yayi causing in haukace war ta,kuma in ana son samun lafiyar ta da wuri dole sai an yi mata tiyatar ƙwaƙwalwa, Mujaheed am very scared wallahi what if wani abu ya faru da ita",shi karan kanshi saida ya ji tsoro jin Nameer in ya ambaci tiyatar ƙwaƙwalwa,amman saboda ya karfafa shi sai ya danne nashi damuwa"common Gee miye abun jin tsoro,duk ba aikin ku bane mutane nawa ake wa tiyata kuma su tashi lafiya lau"


"Hmm Mujaheed ke nan Neurologist daban da kuma Neurosurgeon,mu na mu field in gano cuta ne na brain da ba da magungunan su,while su kuma duk abinda ya shafi tiyata to su ake samu, so ban san ko Doc Akim Mustapha duka biyu ya karanta ba",dan dariyar Doc yayi sannan ya ce"daya tal na karanta Doc Nameer dole in za a iya aikin daman ba ni zan yi ba,i have to call a friend from India,kwararre ne sosai ya san aikin shi,sai ya zo yayi mata,sunan shi Doc Nawazzudden,in kuma kana ga zai fi muku sauki ku fitar da ita sai in hada ku da shi to",da sauri Nameer yace"a'a Doc ai ina ga zai fi sauki in shi din ya zo,am ready to pay ko nawa ne in ya yarda ya zo,kuma Pookie za ta samu lafiya",dan jim Doc Akim yayi sannan yace "okay as you wish but it's kind of expensive gaskiya"


"Big Broz kar ka damu da tsadan shi,in dai kana da assurance in ya zo za ta samu lafiyar,we are ready to pay ko nawa ne,just tell us the price"Mujaheed ya fada


"Don lafiya kam sauki na Allah ne duk gurin shi muke nema,saidai i can assure you duk wani tiyatar da Doc Nawazzudden zai yi to successful yake zama,yayi wa masu brain tumor ma an samu waraka balle na Nadeeya bare za mo da damuwa ba,in sha Allahu za ta warke within 3 weeks don masu cases irin nata basu wuce haka suke warke wa after 13 hours surgery in da za a musu",idanu duk suka zaro jin ya ambaci 13 hours,dan dariya yayi Sannan yace"kar kuyi wani mamaki kun san in abun da ya shafi brain ne da heart tiyatar su akwai wahala, mistake kadan mutum zai yi shike nan an rasa wannan ran na har abada ba",kai Nameer ya dage alamun haka ne,don brain shine organ in da ke sending message zuwa ga duk sauran sassan jikin dan Adam,in ya samu matsala duk jiki ma ya samu,


Nan dai suka yi ta tattauna wa game da yanda aikin zai kasance,inda Doc Akim yayi ta kwantar musu da hankali Musamman ma Nameer kan kar su damu in sha Allah za a samu nasara,basu bar asibitin ba Saida suka karbi Form da za su cika suyi payment don ya ce in sun gama da wuri ma zuwa jibi Doc Nawazzudden zai iya zuwa,a cikin kudin da za su biya daman harda na transportion da accomodation in Shi,Saida suka biya suka karbi Form in sannan suka fito daga asibitin Nadeeya na biye da su, Mujaheed ke driving while Nameer na going through form in


  "Mujaheed Allah ya kawo mana sauƙin matsin rayuwar nan da muke ciki,kasan wai kudin aikin nan 30 thousand dollars,in kayi converting in Shi to Naira zai baka 25 mil za a biya",burki Mujaheed ya taka sannan ya shiga salati"ikon Allah Nameer ashe talaka be Isa jinyar brain ba a kasar nan,25 mil sai kace hauka,gaskiya yayi yawa",kai Nameer ya girgiza"waya fada maka ai shi jinyar ƙwaƙwalwa daman cin kudi gare shi,balle kasan ba wai Doc in mu na nan bane zai yi aikin dole sai an cire mishi kudin jirgi da abinci da gurin zama,ga kuma kudin aikin shi,maybe ma akwai wasu abubuwan da za a yi using wanda ba mu da su a nan dole sai ya zo da su,ga kudin gadon asibiti da za mu biya Doc Akim ina ji shine yayi mana total in komai ya tashi 25 mil","duk da haka Nameer yayi tsada wlhy,to yau da talaka mara juya kobo ne jinyar nan ta same shi da ya zai yi ke nan,gaskiya zan yi wa Yaya Hydar magana ya masa magana ya rage mana yayi yawa,sai kace hauka",ya kare yana daukan wayan shi.


"A'a my Gee kar ka kira yaya,an very sure Doc Akim bare cuce mu ba,don be yi kama da macuci ba,in dai har za a samu biyan buƙata ai ko mil 50 ne wlhh a shirye nake da na biya",da kallon mamaki Mujaheed me kallon shi,lalle ya yarda da wanan so da kaunar da Nameer ke wa Nadeeya ikon Allah,a yanda duniyar mu ta zamo yanzu lulura ta same ka, yan uwan ka ma na jiki sun guje ka balle ace bare ke shirin kashe wannan makudan kudaden akan yarinyar da be san komai game da ita ba, without thinking of anything in return, gaskia ya kuma godia ga Allah da ya bashi amini kamar Nameer me zuciyar tausayi da taimako,mata nawa da maza jen su ke gudun su a duk time in da wani jarabawa ta ciwo ta same su,amman Shi he has been there for her since day one supporting her and caring for her,a fili yace "ubangiji ya wa rayuwar ka albarka Nameerun Mama Allah ya Azurta Ni da samun kyakkyawan zuciya irin taka", murmushi Nameer in yayi tare da girgiza kai don wani zolayar Mujaheed in sai shi.....


*************Bauchi 


Ba Alh Kabiru ya samu kan shi daga tashi daga wahalalliyar baccin gajiyar da ta kwashe shi ba sai around karfe 10 na safe,hakan ma kiran wayan shi da ake ta yi ne ya daga shi daga baccin,ya shiga neman wayan don be ma san yanda ya jefa shi ba,yana dai jin ringing ɗin shi,ganin yana bata musu lokaci ne ya sanya suka ce ya sallame su sauri suke yi,be yi musu ba don bayi ma da karfin jan zance da shi ya bude jaka tare da zaro kudi ya mika musu,yana me fada musu kar su manta su rufe mishi kofa in sun fita, toilet ya fada kai tsaye ba tare da ya cigaba da neman wayan ba ya samu ya tsaftace jikin shi,yayi brush sannan ya fito,jin har yanzu kiran ake ya sanya shi jan tsaki waye haka ke damun shi da kira sassafe,shi tsaf ya mance da batun Ayman na kwance a gadon asibiti,lucky him ya samo wayar can kasa kusa da kujera saura Kiris ma ta fada kasan kujera,ba tare da ya tsaya kallon me kiran ba don har yanzu ba wai giyar da ya sha ta gama sake shi bane,ga uban baccin da ke idanun shi,cikin sanyin murya yace"Hello"


  "Alh wai ina ka shiga ne tun jiya muna ta neman ka,kayi sauri ka zo Ayman fa ya rasu"ya tsinkayi muryan Asiya tana kuka kamar ranta zai fita ............  



Washhhh Allah na yasin na gaji 🥺



  Assalamu alaikum


  Ayi mun afuwa na ji na shiru kwana biyun nan, What's app ina ne ya samu matsala bayan na gyara kuma sai mu ka shiga fama da rashin wuta,saboda daminan nan da muke ciki,wayar babu charge sai yau Allah yayi a ka gyara mana,da fatan na biya ku bashin ku da kuke bi na,masu kira da cikiya ta don jin lafiya ta, Alhamdulilah ina cikin koshin lafiya ina godiya da kauna da kulawar ku a gare ni,


   More comments more updates 😸


Ina yi wa kowa fatan Alkhairi


  Sai zuwa Monday in me kowa me komai ya kaimu, 


 Have a  lovely weekend 😘


   


Ina masu sha'awar shiga Adashen online,inda za a rike miki Amanar kudi,ba tare da runto ko Ojoro ba,inda za ki zuba ki kuma kwashi kudaden ki, cikin kwanciyar hankali da yardar Allah,ba tare da wata matsala ko tashin hankali ba,


Akwai Matan da sam kudi be cika zama musu a hannu ba,da kin samu sharp an kashe su,someone like me🥺lol,to yar uwa ta shiga Adashe a nan ne,zaki tara kudin ki hankali kwance,


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L7ai2fYGh4UAIK9MhC9awJ


Kindly ki shiga cikin group in nan,2500 weekly,I can assume you Bara ki samu any disappointment ko Damfara ko wani rikici ba, 


For more information,chat her up via:


       08149541182

Sai mun ji ku🙌😍

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


     This page is yours my dearest kawata  Ameenatu Abubakar (Mufeedatu na),


Ina godia da kaunar ki  gare ni,🫶🏻❤️

             

..........


My What's app group link


https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0


In kin San ba karanta book ina da sharhi bane zai kawo ki,don Allah ki yi zaman ki ba sai kin yi joining ba☺️


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


******************


Tallah! Tallah!! Tallah!!


   

   Ina uwar  da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


  Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


   Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


    To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌

    

https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


         08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌           


...........

          Page forty seven


************


Wata irin wawiyar jiri ce ta dauke shi,da gama sauraran Asiya,ji yake kafuwan shi sun masa nauyi tare da gaza daukan shi,kunnuwan shi wani dummm suka yi,yana jin zafi da nauyi a cikin kirjin shi,ji da ganin shi sun tafi naucin gadi a daidai wannan lokacin,he just can't believe his ears,a taya Ayman ɗin shi zai mutu,garin yaya ma,shike nan Rilwanu ya ci galaba a kan shi,ya raba shi da yaron shi da ya fi kauna sama da komai a duniya,taimakon Allah ne ya samu ya ja sanƙararrun ƙafafuwan shi tare da zubewa akan makeken gadon da ke dakin,trying so hard ya yi numfashi,da ke sam ba Allah ba ne a zuciyar shi bakin shi be iya ambatan sunan Allah ko wani addu'ar neman taimako ko na yaye damuwa kunci ko musiba a yayin da ya samu bawa,balle ya ji sassauci.


Banda zazzare idanu, da faman hada uban gumi kamar wanda kunama ta harbe shi,a yayin da ƙaruwar bugawa da maimaita kalman na shiga uku da zuciyar shi ta ke ta faman yi,gaba daya ya rude ya susuce hawaye wannan ta kasa fitowa daga cikin kwayan idanuwan shi,shi da kan shi,neman hawayen yake su zubo ko zai samu ya ji sanyi daga tafarfasan da zuciyar shi ke yi mishi,wato dai Rilwanu Saida ya kashe Ayman hankalin shi ya kwanta(Ni ko na ce wlhh daga dan iska sai kai Alh Kabiru,wannan dai fadan rashin gaskiya kake yi,Rilwanu a ina ya isa kashe rai wannan ai hurimin Allah SWT ,shi kadai yake iya zartar da abun da ya so a lokacin da ya so,yo daman a ina za ka sani tunda ilimin addini ba shi gare ka ba, saisa jahilci be yi ba wallahi,da zama da jahilli gwamma zama da ɓarawo,domin sai ka aje zai dauka,ya Allah duk tsanani duk wuya kar ka raba mu da imani da kuma mutuncin mu).


Ya kai fiye da minti 10 a cikin wannan yanayin,don a yanda ya ke jin shi,dauka yake shima kwanan shi ya zo karshe (Yan uwa na maza da mata,wallah sai mun sassauta wa kan mu akan mugun kaunar yaran mu da muke yi,duk yawan yaran ki akwai wanda kike ji kin fi kauna har cikin zuciyar ki,kila saboda ya fi kyautata miki,da jin maganar ki ne,ko kuma haka kawai ubangiji ya jarrabe ki da kaunar yarinya ɗaya tal ko yaro daya tal daga cikin yaran ki,don ya ga ko za ki iya yi wa sauran adalci,don kin fi son yaro daya cikin zuciyar ki ba shi ya ke nuna ki fito da kaunar fili har ki sanya yan uwan sa su gane,a take shedan ya raya musu shi shiga yi mishi bakin ciki da hassada,ko in ba su yi mishi hakan ba,ki sanya tsana me tsanani a tsakanin su,Saisa ya zo a Hadith in Annabin Rahma mun,kan "ya ku iyaye ku ji tsoron Allah,ku kuma tabbatar da kun yi adalci a tsakanin yaran ku",wannan zafafa kaunar karshe shi ke jawo wa uwa da yaron ta ko uba da 'dan shi su tsaya blaming juna suna zagin juna a gaban Azza wa Jallah,domin kaunar da kike masa,ba zai bar ki nutsuwa ki yi tarbiyyan shi tare da tsawatar mi shi a lokacin da yayi ba daidai ba,muyi iya iya wan mu,ganin mun koya wa yaran mu hakuri juriya da kuma tawakkali,uwa uba kuma tsoron Allah,don wanan shine jigon jin dadin zaman duniya,Allah ya ba mu ikon tarbiyantar da yaran mu ta hanya me kyau,domin ba shakka sai Allah ya tsaida mu ya tambaye mu game da Amanar da ya danka mana,don yaran mu tamkar ababan kiwo ne,Allah ka tsare mana yaran mu a duk yanda suke).


Har yanzu ba wai numfashin shi ya daidai tun bane,kiran wayar shi da Asiya ke ta faman yi baya dauka ne,ya zaburar da shi,cikin sauri kuwa ya mike tsaye yana me dafe kan shi da ke mugun sara masa,sai a yanzu ya kuma gaskata maganar Asiyar kan Ayman fa ya tafi,wani irin ihu ya fasa wanda ba iya dakin ba saidai gidan gaba daya Saida ya dauki sautin ihun na shi,"Ina wallahi ba zai yu ba!!Ayman ɗina ba zai mutu banza ba,inaaaaa ai ba ma zai yu ba,wallah tallahi in dai ina doron kasa ina numfashi,sai na tabbatar da na dauki fansa akan abinda Rilwanu yayi mun,yanda ya sanya zuciya ta zugi sai na sanya tashi tafarfasa,shi ya zo duniya wasa,har wanda ya daura ka a layi kake son gwada wa kai dan iska ne, ka fini kwarewa a bariki ko,dan dariya yayi wanda daga gani ka san na bakin ciki ne sannan yace ba ka san da wa kake wasa ba,amman ka tabo tsuliyar dodo babu abinda zai hana Ni ganin bayan ka,tunda kai dan iska ne Shege butulu wanda be gaji abun arziki ba"ya kare a harzuke tare da ɗaukan wayan shi da ke ta ringing,ganin har yanzu Asiya ke kan kira,ya sanya shi picking cikin tsantsan bacin rai yace "wai ke dan uban ki miye kike ta damu na da waya ne?


Ba karamin sosuwa ran ta yayi ba,Amman sai ta danne ta bashi uzurin dimaucewar mutuwa ke damun shi"Alh daman game da gawan yaran nan ne,ana bukatar a sanya hannu kafin a bamu su,a samu ayi musu wanka",ta kare tare da saurin danne kukan da ke cin ta,domin ba iya mutuwar Ayman ya sosa Mata zuciya ba,harda wannan bakin hali na mijin ta Kabiru,saboda Allah ace dan ku ke kwance rai hannun Allah Amman ace tun jiya guraran Magrib da ya sanya kafa ya bar asibitin ba su kuma ganin shi ba,ko banza dai ya san presence in Shi is something,don a halin da take ciki she need a shoulder to cry on,amman babu shi babu alamun shi,ta dau zai dawo ko da cikin dare ne,ko zai kira ya ji halin da suke ciki amman babu ɗaya kanwar biyu,gashi har Allah ya karbi abun sa,tun safe take ta faman kiran shi baya dauka,da kyar ta samu ya dauka,tana kuka ta sanar da shi mutuwar baban 'Dan su,inda mutumin arziki ne kuma ya san mutunci ya ci ace ai ya bar duk abinda yake yi,ya zo tunda Sarai ya san ai sai an yi cike cike kan a basu gawan,ba ma wanann ba sanin kan shi ne dai duk a dimauce suke ya ci a ce yana kusa ko lallashin su ne yayi ai ko.


"Ke lafiyar ki ina ta magana kin yi mun shiru",saurin dawowa hankalin ta tayi daga tunanin da ta fada sannan tace"ban ji ka bane network ke breaking",nace ba Fu'ad na nan tare da ku ba,ya je yayi clearing all bills sanann ya cika hannun,ai shima yaro na ne,in da bana nan ba fa?Maza ya je yayi abinda ya dace sannan a ba ku gawan,a je ayi musu wankan akwai abu me mahimmanci a gaba na in na gama zan sa me ku a gida"ya kare cike da bacin rai, domin daga nan baya jin zai iya zuwa ko ina in ba gidan Sen Rilwanu Audu Waziri ba.


"Amman Alh kana ganin ya dace ace sai mu mata da su Fu'ad ne za muyi komai har a kai su?ko za ka dawo kafin nan", katse ta yayi da fadin"wai baki ji na ce da ke akwai abinda zan yi me mahimmanci ba?Yaro dai ya riga da ya mutu ko?Don haka aikin gama ai ya riga da ya gama,da zuwa na da kin zuwa, ba shi zai dawo da ran shi jikin shi ba,and da kike ce mun ku za ku yi komai daman ba ke ce uwar shi ba,in da bana nan fa??Jiki na bari kin iya kira ki sanar mun,ya ci ace ai kin kira sauran yan uwa na nesa da kusa ki sanar musu a zo a kai su,tunda ke na ga gwana ce gurin yaɗa news mara dadi"ya kare yana me jan tsaki tare da kashe wayar shi,da kallon mamaki Asiya ta bi wayan hannun ta da shi,idanun ta sun kaɗa sun yi jawur,bata taɓa regretting bin son zuciya ta auri Kabiru ba sai yau,wato ta yarda da karin maganar nan duk wanda ya hau motar kwadayi a tashar wulakanci take sauke shi,wato yau Kabiru ita zai yi wa haka,after a lot of sacrifices ɗin da tayi mishi a rayuwa,ta sakar masa rai rayuwa da kuma ragamar jikin ta,tun auran su duk abin da ya bida bata hana shi ba kuma ta tunani take yarda,domin har Anal sex yarda take yana yi da ita,ba tare da ta san dalili ba, although deep down zuciyar ta na raya mata duk abinda zai janyo yayi Anal sex da ita to ba abin kirki bane,amman saboda kwadayi da mugun son abun duniya bata damun kan ta ko kadan,a haka suka yi ta rayuwa,shi kuma yana kulawa da ita tare da bata ta da kudi masu nauyi,domin ya samu abinda yake so,abun da ko matan bariki in ka nemi saduwa da su ta baya ba yarda suke ba,amman cikin sauki ya samu kan Asiya ta na bashi duk sanda ya bukata,a yayin da kudaden  shi ke  karuwa fiye da tunanin me tunani.


Amman bata taɓa dana sanin auran shi ba sai yau,bayan abun da yayi mata yayi losing all respect da take mi shi yau,as in in ba dan iska ba,ta kira ta ce da shi yaron su ya mutu,yo in da kara ai ko da yaron ta ne ta zo dashi gidan shi,irin hallacin da tayi mishi ya ci ace ya zo a lokacin da take neman shi,hawayen idanun ta ta share tana jin zuciyar ta na kuna ta kira wo Fu'ad ta sanar da shi sakon baban na  shi,mamaki kawai take ganin har sun gama cike komai an basu gawan amman babu alamun Kabiru balle me  kama da shi,kukan zuciya da na fili kawai  take  yi,tana jin tsana da haushin Kabirun fiye da mutuwar Ayman 'Dan ta,(Ni ko nace ai in da kwadayi daman dole ya zamo da wulakanci,wlhh mata da iyaye in ba mu ji tsoron Allah mun cire kwadayi da Dogon buri a zukatan mu ba,to Bara ku daina kashe kawukan mu da kan mu ba,ƙarara kina zaune da miji shi kan shi ta san don abun hannun shi kike tare da shi,and kiyi expecting respect daga gare shi🤣🤣🤣funny you!!gashi dai Dan su ne ya mutu,me ya fi wulakanci ace uba na raye da lafiyar shi yana gari Amman Yace wai aje ayi duk abinda ya dace 🥺,kai Allah ka raba mu da kwadayi da buri a rayuwar nan).


Cikin sauri ya dauki wayoyin shi da ke watse a kan gado, tare da zuba su cikin aljihun rigar jikin shi,car key in Shi ya dauka,tare da saurin fitowa daga dakin,be tsaya rufe gidan ba ma,banda me gadi da yayi wa jan kunne,akan kar ya bar kowa ya shiga masa gida,a 360 ya cilla motar shi kan titi,tare da ɗaukan hanyar gidan Rilwanu Audu Waziri, banda tsaki babu abinda ya ke yi,tare da sharara gudu kamar wanda zai bar gari, addu'a kawai ya ke yi a cikin ran shi Allah sa Rilwanun na gida be tafi yawon campaign ɗin shi na Asara ba.


Be wani bata lokaci ba kuwa ya iso kofar gate ɗin mansion in Sen, bugawar zuciyar shi na karuwa,sai haki yake ta faman yi kamar wanda ya tako da kafa,bacin duk tsaban zallar  ɓacin rai ne,tuno abinda yayi musu last zuwan shi,ya sanya Sunday saurin wangale mi shi gare tare da saurin ja baya,in da a take ya danna hancin motar shi sai cikin gidan,a nan harabar gidan yayi parking in rashin arziki,sannan ya fito yana me jefa key ɗin a aljihun shi ba tare da ya rufe murfin motan ba,sai Sunday ne ya taso da rawar jiki tare da rufe mishi kofar,yana me tambayar kan shi,me ke damun Kabirun don daga jiya zuwa yau,ya fuskanci changes tattare da shi, babu annuri ko farin ciki a tare da shi balle har ya sanya ran samun dan kyautar kudin da ya saba bashi tare da sauran workers in gidan, don Alh Kabiru akwai iya bada kudi,in zai dauki sati yana zuwa gidan Sen to in sha Allahu kullum in zai tafi sai yayi wa workers in Sen rabon kudi,kai ya girgiza tare da komawa bakin aikin shi,yana tabbatar wa kan shi duk abinda ke damun Kabirun to baban abu ne.


Ba tare da sallama ba ya kutsa kan shi cikin parlor ɗin gidan,baban burin shi kawai a yanzu shine su yi ido hudu da Sen ya ga yanda ake karshen Iskanci,aiko abun ku da rabo yana shigowa wa kuwa ya hango Sen zaune bisa daya daga cikin lafiyayun kujeran Dinning table in Shi,da ke gefen Parlor ɗin da kadan, abinci ne na alfarma shake a gaban shi,ga kuma cup wanda ke dauke da kakkauran tea,ga kuma Drinks nan kaloli daban daban akan table in,harda su fruit da sauran tarkacen abinda masu kuɗi ko yaran su suke ci during break fast🥺🤣,a take ya ji ran shi tayi masifan sosuwa wato Rilwanu ya kashe mishi first born in Shi,saboda yana da liver har yana iya zama a kawo masa tulin kayan dadi na more rayuwar duniya,ya baza baki da ciki yana ta faman cin abincin shi hankali kwance,domin ko digon damuwa babu a fuskan Rilwanu banda cinyar kaza da ya dauko ya shiga yaga a hankali cikin nutsuwa yake yin breakfast ɗin shi,a harzuke Kabiru ya iso Dinning in ran shi haɗe,"Kaiiii!!wlhy ba ka isa ba wato bayan ka sanya ni cikin bakin ciki,tare da daga mun hankali kai kana nan a nan hankalin ka kwance har dadi ma kake ci ko??ya kare a zafafe,jin saukan muryan shi da furucin da yayi ne ya sanya Sen yi wa duk wani worker da ke gurin alamu da hannu akan su fice daga bangaran shi,nan ko Sa"eed ya kada kan su tas suka bar gurin,ran su be so ba domin ganin yanda Alh Kabiru ya zo da kuma maganar da yayi,ko ba a fada maka ba, kasan da wata a kasa(as you already know Yan aiki akwai son tsegumi,basu da burin da ya wuce su san duk wani moment in da kake ciki, ubangiji ka haɗa mu da Yan aiki na gari).


Sen be dago ba balle Kabiru ya samu arzikin kallo har ta kai ga ya furta mishi wata kalma ma,banda glass cup da ya dauke cike da Mango juice da ice cube a saman shi,ya shiga kurba yana lumshe idanu alamun dadin lemun ya ratsa har zuciyar shi,ganin yanda ya baiwa banza ajiyar shi ne ya sanya Alh Kabiru dada hasala,a zafafe yayo kan Sen tare da cukumo wuyan gaban rigar shi,daga nan zaunan da yake,shi kuma yana tsaye bisa kan shi"Dan uban ka har kayi girman da zan shigo cikin gidan ka,ina maka magana kana baiwa banza ajiya ta???tissue Sen ta dauka cike da nutsuwa ba tare da damun  kan shi daga rikon wuyan rigar shi da Kabirun yayi ba,bakin shi ya goge sannan ya dago idanun shi tare da zube su kan Alh Kabiru kai ya girgiza,sannan ya saki murmushi,cikin muryan ko in kula yace"Dadi na da kai Wlhy kan ka be fiye lafiya ba,amman nayi maka uzuri kila garin mugun son kudin ka,har gefen brain in Ka,da ke sanya wa ka banbance baki da fari,ka hade duk ka baiwa Odogwu,in banda haka a taya kana cikin gida na kuma kana tambayan wai nayi girman da za ka shigo gida na kana magana ina share ka, dan dariya yayi sannan yace ka ja kujera ka zauna kayi break domin daga yana yin ka na gano akwai muguwar yunwa da ke dawainiya da cikin ka",jijiga kwalan rigan Sen ya shiga yi,"Rilwanu wlhy kayi kadan ka maida Ni Mahaukaci, har kayi kudin da za ka ce na zo cin arziki gurin ka??Ina kudin suke abinda Ni ne nan nayi sanadiyar samun su,ya kare yana nuna kan shi,har kana da bakin ce mun wai yunwa na dawainiya da Ni,to in Ka mance in tuno maka yanda na tarar da kai,kafin na kai ka,a sanya ka cikin daulan nan da kake ciki,Rilwanu Audu Waziri kar ka mance irin bakar talaucin da kake ciki,na rufa maka asiri na maka silan arzikin ka,na yi maka riga,nayi maka wando,duk wani matsayi da kake takama ka samu,da duk wani Niimar da ka samu a rayuwar ka Ni ne nan sila!!ya nuna kan shi da hannun shi,amman saboda kai butulu ne har Ni za ka ci wa amana,Shege mara mutunci wlhy ba zan kyalle ka ba yau",a harzuke Sen ya tashi tare da dakan table in gaban shi, sanadiyyar haka,glass cup in da ke kai ya fadi kasa tare da tarwatsewa  nan take,"Enough!!ya ishe ka haka Kabiru,ba wai don nayi shiru ina sauraran duk wani banzar maganar da ta zo bakin ka ba,ka dauka ban da hankali,Kabiru ban taba sanin kai Wawa bane sai yau,ashe kai makiyi na ne ban sani ba🤨can you stop bitting around the bush and go straight to the point,kace kana yi mun bakin cikin daular da nake ciki,dan tashi yayi tare da tafa hannu, wow Kabiru wlhy ban dauka kai din Mahassadi bane kuma dan bakin ciki sai yau,wato arzikin da nayi da fame in da na samu fiye da kai shine abinda ke daga maka hankali right?ka rasa yanda za ka ga down fall ɗi na shine ka biyo ta wannan hanyar?No wonder mana ka ga zabe na karantowa ya sanya ka tsiro mun da Iskanci da rainin wayo da karyan banza don ka ga ban yi nasarar zama Governor ba ko??To ai da ba ka wahala kan ka ba,ka fito ka fada mun tun tuni kan kai fa kana bakin ciki da Ni,wlhy Kabiru ka bani mamaki ban dauka Upon all people Kai zaka yi mun haka ba"..."in ana maganar waya yi wa wani haka kai har za ka yi magana,Rilwanu after all I have done for  you in this life kayi stabbing ɗina from behind, are you for real!!Rilwanu in ana maganar mugu mara son ci gaban dan uwan shi har kana da bakin magana,ka cinye mun suruka sannan ka ba da jinin Yaro na,first born ɗin my pride and the absolutly love of my life, Rilwanu kasan irin kaunar da nake wa Ayman kuwa?ka san irin son da nake mishi?a duk cikin yaran na bana hada son Ayman da na kowa a cikin zuciya ta, domin ko Asiya bana mata so da kaunar da nake wa Ayman,amman duk ka tsallake wanann after all the warnings in da na  na maka,Saida ka kashe shi ka ji dadi,to wlhy yanda ka kashe mun yaro Nima ba barin ka zan yi ba,dole yanda ya tafi kaima sai ka tafi"ya kare yana takowa inda Sen ke tsaye.


"One more step and I promise to take your life!!Rilwanu ya fada rike da kwalba a hannun shi,idanun shi jawur,Na rantse harda girman Allah Kabiru in Ka daura dirty hands in Ka jiki na sai na tabbatar da ka kwanta baccin da baza ka kara bude idanun ka ba,and wlhy Ka San hali na bana cewa zan yi ban yi ba,Are you that stupid ashe??Kai Wawa ne ban sani ba,miye hadi na da Ayman da zan kashe shi,ohhhh ashe babu dadi,kai ka ma gode wa Allah kana da wasu yaran za ka gan su ka ji dadi,what about me??My one and only child Saida ka San yanda kayi ka raba ni da ita,na taba blaming in Ka ko da na rana daya?and you talking about Kai kayi mun silan arziki,duk wani love and respect da ake baiwa mutum a duniyar nan na baka har fiye da haka,i do respect you a lot don ko banza Ni ba Mahaukaci me hade hankalin shi da tuwo ya cinye bane irin ka,wato Ni ne nan dan iska da na biye ka muka haukatar da yarinya ta,saboda ban san ciwon ta ba ko?dan shiru yayi tare da nufan katon mirror in da ke manne a parlor in,idanu ya zuba wa kan shi sannan ya cigaba,Kabiru wlhy ban taba sanin Ni Wawa bane mara wayo sai yau,wato Ni ga me Aboki,duk wani abinda ka fada mun ko ka ban shawara ba tare da dogon tunanin ba nake dauka,a tunani na baza ka taba iya cutar da Ni ba,little did I know Ashe Kai baban mayaudari kuma masharran ci ne,na kasa yarda wai yau Amini na na hannun dama na,wanda ya san duk sirri na ke accusing ɗina na kashe yaron shi da sirikar shi, goshi ya dafe sannan ya juyo ya kalli Alh Kabiru da ke tsaye yana ta faman huci kamar wani Zaki.


"Kabiru I thought by now ka riga da ka gama sanin hali na,ko yawo tsirara nake don hauka ba zan iya bada wani daga cikin family member ɗin ka ba,tunda Aminta na gaskiya ce a tsakanin mu,amman ka bani mamaki wlhh da kake zargi na da kashe Ayman me yayi mun da zan kashe shi,ko matar shi ma da na san surikar ka ce da bazan bada ita ba"dalla rufe mun baki har wani gaskiya da girmama wallahin   me shan jini da zai maka ka yarda da shi??..."excuse me kar ka ga ina bin ka ina lalaba ka ka dauka ban san ciwon kai na bane,Kai Kabiru tunda duk bayanin da nayi maka ka gaza fahimta na na kashe Ayman ɗin do you worst!!ai da jin haka Alh Kabiru ya dauki broken bottle in da Sen ya fasa,ya nufo shi gadan gadan"na rantse Rilwanu yau sai na kashe ka,wlhy kayi kadan baka kai ba ka ce za ka kashe mun yaro sannan  ka zo kana fada mun duk maganar da ka ga dama",da sauri Sen ya ja drawer in gefen shi tare da ciro ƙaramar bindigar da ya ke aje shi a gurin dan bacin rana"Aswear to you with my living God in Ka iso yanda nake babu abinda zai hana ni harbe kan ka in fasa brain in Ka without any second doubt,in kana jin kai Shege ne matso in ban kashe ka ba,ai ban dauka wlhy haukar naka ya kai haka ba sai yau,dan Bura uban ka har Ni ne za ka shigo cikin gida na ka nuna Ni da kwala!in ban kashe ka na shanye jinin ka ba ka canza mun suna,wato yaron ka ne aka haifa daga ciki ko, yaran da duk muke bada wa ai tsinko su ake daga jikin bishiya,Kabiru kai ban taba ganin mugu me shegen son kan shi ba irin ka,wato dan Ni ne dan iska ban san ciwon kai na ba,na bada Matata ka sanya aka haukatar mun da yarinya"dalla rufe mun baki Shege me bakin yan wuta,da kake daura mun blaming ni na sanya aka haukatar da yarinyar ka dole nayi maka??Shawara ce na baka,da ke kai dakiki ne ka dauka,duk abinda nace kayi shi kake yi Wawa mara ra'ayin kan sa,dauka kake wai kaunar ka can nake yi,dan dariya yayi sannan ya cigaba,babu kauna tsakani na da kai,don in dauka kake kauna ce ta haɗa mu kayi kuskure,amintar mu bisa son zuciya da son ran mu muke yi,and i promise my self daman whenever am going to hell to ba zan yarda in tafi Ni kadai ba,Saisa nayi introducing in Ka to Brotherhood,and saboda Iskanci da kwarewa a makirci ka fada siyasa ina zaune kayi Reps kayi Senator har sau biyu yanzu kana kokarin neman Governor ace war ka babu zuciya a kirji  na ne??ko ka dauka ba zai mun ciwo bane Ni da na kawo ka ace ka fini shahara da suna a duniya?Sannan duk da haka ina ta hakuri ina jure zama da kai,and yanzu ka zo ka bada Ayman ɗi na,to wlhy an zo in da ba zan iya dauka ba,akan Ayman wlhy ban ki daga Ni har kai mu mutu ba",


Hakika nin gaskiya ba karamin girgiza Alh Rilwanu yayi da gama jin kalaman da ya fito daga bakin mutumin da ya dauka a matsayin amini ba,wato in ya canka daidai Kabiru be taba kauanr shi ba,ya zauna da shi zuciya Daya Amman shi ba haka bane a nashi bangaran ikon Allah Saisa aka ce ka ga dan Adam ka bar shi a yanda ka gan shi,domin sanin zuciyar mutum sai Allahn da yayi shi,shi dauka yake Kabiru Aboki kuma Aminin rufin asirin shi ne,duk abinda zai faru he can count on him,amman Ashe using in Shi yayi for his on selfish reason,wato tun asali Kabiru bakin ciki yake da shi,ya sanya be taba bashi shawaran da ya dace ba,be taba sanin shi Wawa bane sai yau,domin duk wasu abubuwan da suka faru a rayuwar shi shawaran Kabiru ne,a kullum kalman Every thing is fair in love and war Shi yake maimaita mishi,sannan ya daura da ranar biyan bukata rai ba a bakin komai yake ba,ashe Wawa dan iska ya maida shi,No wonder mana ko bayan barin su gurin Odogwu sanda Nadeeya ta kai stage in Aure ya nemi why not suyi haɗin gida,tunda duk kanwar ja ne,a hada ta da Ayman dan wajen shi,ido ya sanya wa toka ya ci wa Rilwanu mutunci tare da nuna tsantsan bacin ran shi,a wannan ranar yayi making in Shi clear to Rilwanu kan duk abinda zai faru kar ya sake yayi involving in wani daga cikin family member in Shi, gumi ya goge domin ba karya ne felt betrayed,zuciyar shi ban da tafasa babu abinda yake yi,ji yake kamar ya rufe Kabirun da duka har sai ya daina numfashi.


Takowa yayi har ya iso gaban Alh Ido cikin ido ya daga hannu tare da kada masa mark"Kabiru ka ci uwar ka da uban ka da yaudara ta da kayi,Shege tsinannan ne wanda ba zai taba gamawa da duniya lafiya ba,wlhy tallahi bayan abinda ka sanar mun yau da Ayman be mutu ba Ni nan da hannu na zan murde wa Shege me sufan yan Daudu wuya in kashe shi har lahira ka ji zafin yanda ake ji,kuma wlhy ka sanya a ranka ka yi da Rilwanu kai ka yi introducing ɗina to Brotherhood fact in nan ba zai canzu ba Amman zan gwada maka tabbas Ni ba a yi da Ni ban rama ba,ba dai kace ba za ka bar Ni ba,to Ni da kai Shege ka fasa duk wanda ya fasa ya raina uwar da uban da suka haife shi,a buga wasan kamar yanda ka kira Ni da dan shan jini,kaima ai jinin kake sha don Allah kar ka fasa kuma kar ka janye ka ga ko zan fasa cin uwar ka ne"...hannu ya daga tare da kokarin bugawa Sen kwalban a kan shi,yana shouting "Rilwanu!!how dare you in ban kashe ka ba yau ka kira Ni da arne"a zafafe Rilwanun ya rike hannun shi tare da gyara zaman gun inshi yana saitawa a kan shi"har kana da bakin ce wa a kira ka Arne,mutumin da zai sha giya,ba zai yi Sallah ba,yayi Caca,ya nemi matar shi ta Baya,ya kwanta da matan kwalta,sannan yayi raping yarinyar shi yar 9 years,tare da tsohuwar sirikar shi har yana da bakin kiran kan shi musulmi daman"..."ka fada mun cikin laifukan nan wane ne baka yi ba??? Mutumin da ya kwanta da Matar uban shi,ya bada uban shi da Mahaifin Matar shi,Kai Rilwanu ko ka mance abinda yayi silan sumewar yarinyar ka har ya kai ta ga accusing ɗin ka tare da auna maka zaguna a gaban media ne?In ka mance in tuna maka....tunda har ka mance kana da bakin zagi na bayan tulin kashin da ke makale a duwawun ka bari na tuna maka......in ce nan Nadiyar da kake kuka da wakan kana so fiye da komai,ta kama ka a daki da"......,da sauri Rilwanu ya cukumo rigar shi tare da kwada mishi mari,ba tare da wata wata ba Shima Kabirun ya dauke shi da mari,ai a fusace suka damki gaban rigar juna kowa na ja yana huci,"in dai tone tone kake son ayi wlhy Kabiru in nace zan budi baki na sai an yi maka tofin Allah tsine","yanda kake gadara kasan sirri na,Nima Sarai ka san na san na ka, don Allah kar a fasa tone tonan nan,mu ga Ni da kai wa za a yi wa tofin Allah tsine ɗin"suna shirin bawa hammata iska ke nan,Alh Salisu da shigowar shi ke nan ya saki wani irin sallati tare da nufo su,har yana kokarin harɗewa.


"Subhanallahi!!Kai jama'a me zan gani haka,ashe maganar yaron nan Sa"eed gaskiya ne da ya kira yace mun gidan ka babu lafiya,ku kuwa me yayi zafi har haka da zai sanya ku fada da juna,fadan ma na dambe kamar wasu kananun yara,haba Alh Kabiru ko ba mutuwa aka yi maka ba,yanzu na gani na ta yawo a yanar gizo,shirin da nayi ma gidan ka zan wuce don maka gaisuwa da jin dalilin da baka sanar mun ba har aka kai shi,na dau Rilwanu na can already har raina na sosuwa akan kun ware Ni,Saida Sa"eed ya kira yace na zo fa babu lafiya a rude na taho ashe kuna nan kuna fada kamar wasu karnuka,haba me yayi zafi har haka da ba zai iya hakura ba a gama zaman makokin yaron ka,kan ku tattauna wlhy duniya ta ji ma sai su yi muku Daria,ai ko dan rikon ka ne,mutuwa ta wuci wasa da za ka zo nan kuna hayaniya for crying out loud mutuwa fa aka yi mana fa,wlhy kun bani kunya"Alh Salisu ya kare kamar ya rufe su da duka don takaici da bakin ciki


A zafafe Sen yace"Gashi nan ai Salis,ya fada maka,uban da ya kawo shi gida na ya na fada mun magannun banza,ka ga karya wa nake hankali kwance Ni Wlhy ko sanin mutuwar yaron ma ban yi ba,yanzu kai Kabiru ace anyi maka mutuwa akan karamin abu ka zo muna ja Ni in ja ka da kai,this is so bad ai",harara Alh Kabiru ya watsa wa Sen sanann ya kalli Alh Salisu"yi hakuri Salisu wlhy ban cikin senses ina ne ya sanya ban kira na sanar maka ba"


"Ni ba wannan bane damuwa ta,Kabiru me ya hada ku da Rilwanu da zafi da za ka zo har kuna shirin daukan ran junan ku,shi na same shi da gun a hannu,kai kuma broken glass,for God sake da ban zo ba da yanzu kuna wani hali ke nan??dan tsaki duk suka yi a tare sannan Sen yace "gashi nan Salisu waka bakin me ita ya fi dadi,domin Ni ban ma San me nayi masa ba,amman kila in ya fada maka yanzu sai in sani"goshi Alh Kabiru ya dafe domin ganin rainin wayon da Rilwanu ke shirin yi masa.


"Look guys no need in San ma abinda ya hada ku,koma dai miye kuyi hakuri and ku kai zuciyar ku nesa,yanzu in workers suka ji fadan nan naku me kuke son nuna musu ke nan??Haba ai be dace ba,koma dai miye don Allah let's it be! let's all bygones be bygones,Bana son kara jin dayan ku ya ce wani abu,maza ku je kuyi getting ready mu tafi gurin karban makokin nan kar ayi abun kunya,ace an yi mana mutuwa iyayen yara basa gurin don na riga da na san har ma an kai su,sai mu je ayi zaman makoki da mu,sannan mu cigaba da nema musu yafiyar ubangijin mu",ba tare da ran su ya so ba dai suka haura samar kamar su cinna wa juna wuta su huta haka suke ji,dariya Sen yayi sannan yace"aikin banza wai hoda a duwawu,a banza an girmi sarki,yo banda daukewar basira ina Shege ke wa dan uwan sa Shege gorin uba,ashe mutum karamin Shege ne,sai cika bakin karya, yasin na dauka ai mutum na da liver ɗin sanar wa the world dirty secrets in mu,tonuwar asiri na tonuwar asirin ka ne da kungiya baki daya, Odogwu kuwa uban ka zai ci muddum ka tona masa asiri,You better hold your mouth to yourself and Mourn your son's death in peace",a harzuke Kabiru ya yo kan shi suke ji muryan Alh Salisu na cewa"guys ya muka gama yi da ku?ba tare da sun ce da shi kalla ba suka haura,a bisa dole suka kara wanka sannan Kabiru ya sanya sabbin tufafin Sen a bisa maganar Alh Salisu,har suka gama shiri suka fito babu wanda ke kula dan uwan shi,duk yanda Alh Salisu ya so da ganin sun watsar sun sake like before amman ina abu ya gagara, ganin hakan ya sanya shi kame kan shi shima,deep down Yana tunanin miye haka ya hado su da zafi har haka,duk su ukun a motocin su suka tafi,in da suka iso gidan Alh Kabiru da ya cika da yan uwa da abokan arziki,nan da nan  Sen aka shiga karban gaisuwar in da a take ya shiga bajintar riyar da ya saba(yo Riya mana abinda duk aka yi shi ba don Allah ba,saidai don mutane su gani su raba ai lada kam babu shi,ladar mutum na gurin fadi da yabon da mutane suka yi mishi,ya Ubangiji ka tsare mu da aikata aikin Alkhairi ba dan kai ba sai don wani bawa na ka ya gani ya yaba)in da Kabiru kam ya cika tam kamar kace cassss ya fashe,ji yake kawai kamar ya ga bayan Rilwanu (Ni ko nace Allah tsare mu da abota da irin su Kabiru,don daman can ba kaunar Allah ya ke wa Rilwanun ba,don da kaunar tsakani da Allah ne ma bare yi introducing in Shi to Brotherhood ba,in kana son abu kana so wa abun arziki ne,daman can hassada yake da Rilwanu domin in ba haka ba little misunderstanding in nan da suka samu be zai jawo ace yayi mishi irin wanann mugun tsanar ba,🥺🥺yan uwa na pray harder and believe in Allah wlh this world is full of wicked people,Kai ka wanke zuciyar ka kana zaune da mutum zuciya daya amman babu abinda yake so da ya wuce faduwar ka😭,ba komai ke haddasa hakan ba kuwa ya wuce Hassada!!ya Ubangiji ka raba mu da son zuciya da Hassada,Allah ka raba mu da cutar da bayin ka masu nufin cutar da mu ka maida musu mugun nufin su kan su,duk wanda yake tare da mu don son ganin bayan mu ko wani mugun nufi da ya boye a ran shi,Allah ka nisan ta mu da su).


******************** Kaduna state


"Ikon Allah sai kallo,yanzu Habeebu kashe ayyukan gaban ka kai ma ka yi tare da biyo Babana all the way from Bauchi to Kaduna,to aikin kuma kuka barwa wa?Mama tayi tambayar tana me kafe shi da idanu,domin cike take da mamaki kamar daga sama suka ga shigowar shi,suna zaune Nameer na yi mata bayanin da Doc Akim Mustapha yayi musu,sun sha mamaki sosai inda ya sanar da su kwantancan da Nameer ya taba yi mi shi ya sanya shi taho wa,and Alhamdulilah Allah ya sa ya iso har gidan with the help of Map in wayar Shi da yayi using,ko Nameee be san da zuwan na shi ba,domin suprise daman yake da niyar ba shi.


"Mama wlhy gani na yi shirun ta yi yawa shine nace bari na leko na ji ko lafiya,domin kwana biyu ko na kira a waya bana samun su".."hmmm Habeebu ke nan,ai halin Babana sai Allah na san da gangan ya kashe wayar don kar a neme shi a gurin aiki,banda abun shi ma wanda ya ke yi don ita ko be nan Sarai ya san zan kula da ita har fiye da shi ma,ta warke nayi mata Auran gata da Mujaheedu,amman sam rashin yarda tayi masa yawa"


"Mama ki fa daina maganar aura wa Mujaheed Pookie in ba so ake ayi yaki a gidan nan ba, Pookie dai nayi mata miji kuma ba Mujaheed bane domin ba zan bari ayi wa yar uwa ta kishiya ba,kuma ba zan kai Pookie ta gidan me mata ba,domin so nake yanda ta sha wahalar nan a baya a ce ta samu cikkaken Hutu da kulawar da ya dace da ita"


Idanu Mama ta zaro"to Ubana akan kaine wa a gurin ta da za ka mata zaben miji?Cikin sauri kuwa yace"ai Mama like this now kamar uba nake a gare ta,domin amanar ta a hannu na ya ke,so Ni nake da right in zabar mata mijin da ya dace da ita","in kai uba kake mata,Ni kuma uwar ka ce ba"ta kare tana hararan shi, duk dariya suka sanya sannan ta kwala wa Zaliha kira kan ta kawo musu abinci su samu su ci,domin daga gani suna jin yunwa barin ma Habeeb da isowar shi ke nan daga tafiya,Saida suka ci suka yi dam suka yo sallah sannan suka dawo parlorn suka kara maida zama,suna jiyo ihu da hayaniyar Nadeeya da Angel da alamun wai wasa suke,nan Nameeer ke Saida wa Mama kan maganar aikin da za a yi wa Nadeeya da kuma amount in da aikin zai ci,dan shiru ne ya ratsa parlor in kafin can ya nisa yace"Mama ga shi cash in da ke hannu na da wanda suke Bank ba za su kai 25 mil ba,nayi deciding siyar da fili na in ya so sai in hada da kudin hannun nawa,mu samu mu kai Bank ayi payment in don a samu a kira Doc Nawwazuddin da wuri"dan nisawa Mama tayi domin siyar da Filin sam be yi ba,don babban fili ne,and in ya fitar yanzu ya ce zai Saida za a iya masa tayi ko siyan wulakanci domin an ga yana matse,"Gee baza a yi haka ba,fili kam ba zaka Saida shi ba,ko ba shi bane land in da kake burin kina asibiti a kai?da kai ya amsa mishi,ba tare da damuwa ba Mujaheed in ya cigaba"nawa ne yanzu a hannun naka??"Gee wlhy bana jin kudin guri na za su haura 10 mil","to Alhamdulilah ka ga guri na akwai 5 mil sai na baka a hada da na gurin ka saura nawa ke nan?"Nima Mujaheed za a samu 5 mil a guri na,fado account no in yi muku transfer,don bazan bar ku,ku kadai ku samu wannan uban ladan babu Ni ba"Habeeb ya ce yana ciro wayar shi daga aljihu.


Hawayen farin ciki ne suka ciko a idanun Mama da Nameeer,yana dada gode wa Allah da irin Abokan rufin asiri da ya bashi,tsaban murna ma ya rasa bakin magana"Ah lalle yan samarin nawa kudi suke ji,ashe an kusa kai Ni yawo kasashen waje"Mama ta fadi tana dariya,su ma duk.dariyar su ka sanya sannan tace"Ni dai ba zan bada kyauta ba aro zan bada cikoton 5 mil ɗin,in Allah ya sa aka yi aiki lafiya ta warke in an zo hidimar aure da my son sai a dawo mun da kudade na,"duk dariya suka sanya domin a yanda ta yi maganar duk.wanda ya ji ya san a sikar wasa tayi maganar,ba karamin addu'a Mama tayi mu su duk su ukun ba tare da sanya mu su albarka,domin a zamanin nan samun Abokai na gari irin na su yana wahala,Saida suka gama barkonci a tsakanin su,sannan suka fita duk su ukun kan za su kai kudin Bank sannan su dan daga da Habeeb ya ga gari,fatan dawowa lafiya Mama tayi musu sannan suka fito daga cikin gidan,rungume su Nameeer yayi tare da fara zubo musu godia, karfadar shi Mujaheed ya ɗan daka"yo ban da Iskanci wai godiyar na mecece kake mun?don na kashe wa Amarya ta yan kalilan kudadan nan miye a ciki"tsaki Nameer ya ja,tare da fincikar hannun Habeeb"dalla wuce mu tafi ka kyalle wanann dan iskan"banda dariya babu abinda suke masa a haka suka shige motar Mujaheed,Nameer ke driving su ka nufi Bank da shi.


*******************Specialist hospital

                                           (Bauchi state)


"Sister Kareematu,kin ga irin kyau da fresh in da kika kara kuwa?,kin cika kin yi bul bul da ke gwanin ban sha'awa Masha Allah"Nurse Naja'atu ta fadi tana bin Kareematun da kallo don ba karya tayi kyan gani,dan dariya Kareematun tayi "kai Naja am,dadi na da ke wlhy zolaya,banda abun ki ina kyan ya ke?ke dai mun kwana biyu ba mu hadu ba ya sanya kika ce haka,abinda ma ban dan ji dadi ba,ai na ma rame a hakan",cike da mamakin furucin ta Najan ke kallon ta" kin rame fa kika ce?Ashe to da mun hadu ba zan gane ki ba,gaskiya ki zo ki fada mun wanann sirrin kyau da kika yi,by the way sannu ya jikin naki? Ubangiji ya kara mana lafiya baki daya"..."Àmeen fa,ke ba kin tsaya ruwan ido ba,ki fidda miji muyi Auran ki, ko ke ma Oga zai na baki special kula ko kya samu ki dan ciko da wannan muguwar kashin wuyar taki kamar marikin lema"(irin ta Girlfriend 🤣🤣),dariya duk su ka sanya sannan Najar tace"wlhy sister ba ki da dama,Allah ya kawo mana na gari ke dai kawai,mazan ne yanzu abun tsoro wlhy".."hmm bari Naja ai yanzu abun haushin na garin wuyan samuwa suke yi,tunda ba wai a rubuce yake a goshin su ba,wanin za ki ga kamar abun arziki in yana neman ki,sai bayan Aure ya nuna miki tantirin dan tasha ne shi,ga Zaituna Masha Allah tayi Auran ta na ji ma kamar yanzu akwai ciki a jikin ta,ke kin tsaya wasa"..."hmm ke dai bari,Nima zuciyar nan zan yi in samu in yi Auran nan,mu samu mu ji uwar da kuke ji a cikin auran nan",dariya Kareematu ta sheke da shi"ke Mama ta Aure Yasin akwai dadi, musamman in kika yi dace da na gari,haba ji za kiyi nan gidan duniya kamar kin wuci tunanin uban kowa"ta kare tana suna sakin dariya tare da tafawa,daga ganin su za ka dau babu wani damuwa tattare da su,miƙewa Kareematun tayi"ke Naja Yasin na biye ki yau haka a lalace za mu zauna zaman hira har a tashi ki jawo mun magana yau duty na"ta kare tana daukan baby hijab in ta,tare da baɗe shi da turaruka,ba tare da damuwar haramcin yin hakan ba,"lah kin ga na so mantawa ashe tun dazu Doc Bashir ya aiko ni gurin ki,mun tsaya hira na so mancewa ya ce ki je,yana office in Shi,ya ce ki same shi a can", a ta ke fuskan Kareematu ya canza daga fara'a ta daure fuska tamau kamar bata taɓa dariya ba,domin har yanzu rike take gam da abinda Bashir yayi mata tun kwanaki,ya sanya ta fice harkan shi baki daya tun bayan dawowar ta aiki,guri in ma ta san yana zuwa a cikin asibitin ta daina zuwa,domin ba karamin zafin abinda yayi mata ta ji ba,haka zalika tun last maganar ta da Abdul jikin ta ya ɗan yi sanyi,a cikin kaso 100 ta watsar da 70 daga cikin yawon biye biyen maza da take yi,domin ta kan yi sati guda bata fita ko ina ba tana nan gida tare da yaran ta,inda ba karamin dadin zaman na ta suke ji ba,daga su har Abdul in,domin ko ba za ta yi musu komai ba sanin tana zaune tare da su a gida ya kan kwantar musu da hankali .


Cikin tsare gida tace"kamar yaya na same shi a office in Shi?Bashi ya bani ko tara,Ni fa ba na son Iskanci da hakuran banza fa"..."Ni dai maida wukar domin ba Ni na kar zomon ba,haduwa muka yi da shi ina wuce wa ya tambaye ki,nace kina Nurses station shine yace na ce yana kiran ki",tsaki me tsaho Kareematun ta ja sannan ta sanya hijab ɗin nata"aikin banza aikin wofi,wlhy na tsani takura a rayuwa ta,duk kiran da ya ke ta mun ina kin dauka,da duk avoiding ɗin shi da nake yi,amman wai duk be gane ba,shine har sai ya aiko a kira ni"mitar da take ke nan har ta iso kofar office in Doc Bashir ɗin.


Ba tare da ta tsaye knocking ba,ta kutsa kan ta cikin office ɗin,a zaune ta tarar da shi ya wani mimmike kafafu yana cin tsire,ga ƙatuwar robar Coke me sanyi a gefe yana dan sipping a hankali,yayi playing din old school music yana sauraro a nutse tare da bin wakan yana dan gyada kan shi alamun dai duniyar nayi mishi dadi,wata uwar harara ta maka mi shi,sannan cike da tsiwa ta rike waist tana karkada jiki,wanda ke nuna tsantsan masifa na cin ta"Ka sanya a kira ni na zo na ga kuma kamar You are busy,so ina da abubuwan yi,zan tafi if you are ready to talk Ka neme ni",har ta juya kuma ta tsaya tare da kallon shi,"ko da yake babu bukatar neman ta wa,domin we got nothing talk between the 2 of us",ta kare tana nufon kofar fita,bata san time in da ya ta so ba,sai jin hannun shi tayi ya riko waist in ta tare da manno ta jikin shi,cike da Iskanci ta shiga sinsinar ta kamar wani Bunsuru,saurin hankaɗe shi tayi daga jikin nata,tare da saurin matsawa"kar ka soma Wlhh Bashir bar ido na,bana cike da Iskanci da rainin wayo,na sanin kan ka ne Sarai Iskanci na ya girmi taka,so mind your own business and let me be"kara takowa yayi har ya iso yanda take dab dab,cike da kashe murya kamar mace yace"tsakanin ki da Allah Kareeme ta baki missing ɗina?? don't you missed my touch?Baki missing in hannu na around your body?Tsaki ta ja me tsaho kamar tongue in ta zai fita kafin tace"dalla ja ka bani guri,ko wane jarababbe irin ka,akan uwar me zai sa nayi missing in Ka,look Bashir after what happened between us the other time wlhy ko kallon ka bana son yi, saboda ban taba haduwa da dan iska me tsananin son kan shi,da mugunta irin ka ba,Bashir wai har Ni ne za ka yi implicating a matsala?ta nuna kan ta,ai Wlhy ka bani mamaki,kuma ka fice mun a rai"da sauri ya rufe mata baki da hannun shi"common my love ke ma dai kin san duk duniyar nan babu wanda ke son ki da arziki da ya wuce Ni,Kareematu ke ma kin san ke ta daban ce cikin zuciyar ta"Mari ta kwada mishi a baki"yi mun shiru munafuki,ina soyayyar ta ke??."haba Kareeme ta ke ma da kin sani sarai duk duniyar nan babu macen da nake kashe wa kudi da nuna kulawa irin ki,babu macen da nake jin dadin kwanciya da ita sama da ke,Kareematu na kin hadu Wlhh laushin jikin ki,da tattausan tongue in ki,tare da dadin ki abu ne da zai sanya ba zan taba iya rabuwa da ke ba,ke Kareematu Wlhh ban ki a yau ki kashe Auran ki na aure ki,don nuna Miki tsantsan son da nake miki,amman na san ba abu bane me yuwa,na san na bata miki rai ya sanya na tura miki dubu dari uku ki je ki sha ice cream ko zuciyar ki za ta ɗan yi sanyi"hararan shi take yi amman da jin kudaden da ya ambata ya sanya ta washe baki tare da fadawa jikin shi,"Shege Bashari na,wato ala dole Bara ka bar ni nayi fushi da kai in peace ba ko"ta kare tana wani narke mishi a jiki,dariya ya sanya tare da make mazaunan ta"i missed you my Kareeme Wlhh nayi kewan jikin ki sosai"...bakin ta,ta kai kan nashi sannan tace "missed you more"a nan office in suka shiga watsewar su kowanne na kokarin nuna wa dan uwan shi yanda yayi kewar shi,ba tare da kunya ko tsoron Allah ko na wani ya shigo ya kama su ba,(illar zina ke nan,wlhy Zina da Giya ba karamin addiction ya ke zamo wa duk wanda ya fara shi ba,in ba anyi da gaske ba da kyar ya ke iya bari, balle in ya hade wa mutum da son duniya, Ubangiji ya shirya mu,ya kuma tsare mu da aikata zina mu da zuri'ar mu baki daya,masu yi ubangiji ya shirya su in masu shiryuwa ne).


***************Kaduna state


Duk wani cike cike da tsare tsare duk sun gama yin shi,don tun randa suka biya kudin aikin Doc Akim ya kira Abokin shi ɗan India Doc Nawwazuddin inda ya tabbatar musu da yana nan tahowa,ana gobe zai taho Doc Akim ya kira su Nameer a waya tare da sheda musu su taho da Nadeeyar ta kwana a asibitin ya karasa yan dube duben da zai yi akan ta,kafin gobe a gudanar da aikin 


Mama da kan ta ta haɗa musu kayan su,inda ta kai Angel gidan yar sister in ta,da ke aure nan garin Kaduna,domin ba da ita za suyi zaman asibitin ba,babu yanda ba ta yi da Nameer kan ya koma bakin aikin shi ba,tunda an riga an gama komai,za ta iya zama da ita har ta farfaɗo within 3 weeks in da suka ce za ta warke in ya so sai ya dawo,amman sam yace shi kam be san zancan ba babu in da zai je ba tare da ya san halin da Nadeeyar ke ciki ba,cikin dare kuwa Mama tayi mata wanka tare da shirya ta tsaf cikin dogon riga,sannan ita ma ta shiga wanka.


Fitowan Nameer ke nan daga daki ya ji ta fado jikin shi tana kyalkyale dariyar da be san abinda ya haddasa dariyar ba,haka kawai ya ji wani irin sanyi da dadin jin ta kwance a gadon bayan shi,juyo da ita yayi tare da hugging ɗin ta so tight ta gaba,yana jin wata irin zazzafan kaunar ta na ratsa mishi zuciya,sun kai kusan mintuna 3 a haka,idanun shi a lumshe don zai iya cewa tun bayan rasuwar mahaifiyar Angel be taba rungumar wata mace har haka ba sai yau, actually be ma san abinda ya shige kan shi ba,kawai abinda ya sani shine yana cike da farin ciki da nishadi mara adadi jin ta a jikin shi,and Baya fatan abinda zai zamo ya raba shi da ita,Saida ya ji ta fara kananun kuka alamun ta gaji da matsa da yayi mata sannan a hankali ya zare ta daga cikin kirjin na shi,da idanu ya bita ganin hawaye na gangarowa daga cikin idanun ta,da sauri ya sanya hannu tare da goge mata"Don't cry Pookie am sorry okay"murmushi tayi kamar ta fahimci me yake fada,hannun ta ya riko tare da jan ta har dakin shi,a kan gado ya zaunar da ita,sannan shi ya zauna nan kasa tare da kamo both hands in ta ya damke


"Pookie tomorrow is gonna be the big day of your life,and kuma abun tsoro gare Ni,za a miki tiyata gobe and am very sure by Allah you will stay strong and the operation will be successful,Dan shiru ya ɗan yi sannan ya cigaba"Pookie i don't want to picture my life without you in it, without me knowing you have become a part of me,Nadeeyaaaaa ya Dan ja sunan nata,am so scared of losing you wallahi"ita dai da idanu kawai take bin shi irin wanann kuma me yake fada ne🤣🤣🤣


"Yeah na sani ba ki Sanni ba,but Wlhh bana jin zan iya rayuwa babu ke,i try so hard in Ka na mantar da kai na daga tunanin ki,but abu ya gagara,Nadeeya i don't know where how or when na zamo so attached and addicted to you,and am so  scared ki warke ki mance da Ni,ko kuma kina da wanda kike so,pls don't listen to Mama wai tana cewa za ta baiwa Mujaheed ke,dan dariya yayi sannan yace Pookie You Are MINE!!I can never let you go,promise me dat you will be with me till enternity,ya mika mata hannun shi alamun ta daura nata,banda dariya babu abinda take yi mishi,a hankali ya daura hand in ta a saitin heart in Shi,kafin cikin kasa da murya yace ko da kin mance Ni,kar ki mance da kina cikin nan gurin🥺, kwala masa kiran da Mama tayi ne ya sanya shi saurin miƙewa tare da fitowa,da idanu ta bishi sannan tace "Ina yarinya ta??,dan kai ya sosa sannan yace "Mama tana ciki dan magana muke yi"harara  ta watsa mishi sannan ta shige dakin tare da fito da ita, jiki duk a mace haka ya shiga ya sako wanka tare da shirya wa suka nufi asibitin bayan an hada komai da za su bukata a cikin mota.



Kamar yanda aka tsara randa Doc Nawwazuddin ya ce zai zo Nigeria be saɓa alkwari ba,duk suna cikin asibitin hankali a tashe ba kamar Nameer domin Saida Mujaheed ya riko shi,don in an bar shi be ki a shiga dakin tiyatan da shi ba,haka akan idanun su aka zo aka wuce da ita dakin tiyatar inda Doc Akim yace da su,duk su kwantar da hankalin su in sha Allah za a yi a kare cikin Sa'a,ko da Nameer ya nemi ya shiga,Saida ya baiwa duk gurin dariya,nan ya ba shi hakuri tare da sanar mishi ba abun daga hankali bane za ta tashi lafiya lau in sha Allahu,nan suka Mujaheed da Habeeb suka ja shi akan su je masallaci don an dade da kiran sallar Isha,su samu suyi sai su roka mata Allah haka suka fice bayan Nameer ya sheda wa Akim ya bar mishi amanar Nadeeya a hannun shi ya kula da ita.


Cikin yardar Allah kuwa suka fara gudanar da aikin su cike da kwarewa in da Nadeeya kam bata ma san duniyar da take ciki ba,banda addu'a babu abinda suke yi,ba yanda su Mujaheed ba su yi da Mama ta koma gida ba tunda har sai zuwa safiya kafin a san halin da ta ke ciki,amman tace ina babu yanda za ta tafi,su Mujaheed dai ya koma gida kar ya bar Jamila ita kadai,inda shima yayi insisting a nan zai zauna,duk su suka taru suka cigaba da kwantar wa Nameer da hankali wanda idanun shi suka yi jawur kamar kace cassss ya fashe maka da kuka,damuwa goma da ashirin ce ta hade mishi,babu wanda ke tashi in ba sallah na nafila za su yi ba,haka wannan daran Nameer raba shi yayi gurin Sallah yana kai kukan shi ga Ubangiji kan ya baiwa Nadeeyar sa lafiya.


Around karfe 8 na safiya aka fito da Nadeeya daga NCCU ,kan ta nade da Bandage,aka wuce da ita Neurosurgery nurses unit domin a nan gurin za ta cigaba da recovering,da sauri su Nameer suka rufa musu baya,idanun shi akan Nadeeya da har yanzu bata riga ta bude ido ba,kallo daya za ka mata ka san a wahale take, kanta lullube da Bandage,babu abun da ya fi daga mi shi hankali ganin aske gashin ta da aka yi ta side in da aka yi operation ɗin,a bakin kofa Doc Nawwazuddin ya dakatar da su,sannan aka shige da ita,ganin haka ne ya sanya Nameer saurin nufan office in Doc Akim Mustapha,a take kuwa Mujaheed ya rufa mi shi baya.


"Doc how is she??I hope the Surgery was successful right,na ga har yanzu ba ta bude idanun ta ba,hope dai babu abinda ya same ta,and am hoping ta rabu da haukar nan ko?tambayoyin da Nameer ke jero wa Doc Akim ke nan ko hadiyar yawu baya yi.


Murmushi ya dan yi sannan ya zauna a kan kujeran shi"well Doc we can all thank Allah coz the Surgery was successful!!gaba daya ajiyar zuciya suka sauke,suna me fadan kalman Alhamdulilah!


"As you already know most people wake up a few hours after their brain surgery,but for her own case I decided to keep her asleep for some few days,to help her recover fast,with the help of Sedatives it's will keep her asleep,and Kar ku daga hankalin ku while she is asleep,she will be breathing through Ventilator machine,so no need Ku daga hankalin ku,she is out of danger and within no time ,I can say your Babe is a fighter!so babu wani abun daga hankali,You can all go home and have some rest,we will take care of her,har ta farfaɗo"ya kare yana murmushi Nameer na son yin magana,amman Mujaheed ya hana shi,jan hannun shi yayi,suka baro office in bayan godiyar da suka yi wa Doc Akim zuciyar su fall Nadeeya ta samu lafiya..........



To!! Jama'a ga dai  Pookie  an samu lafiya 💃💃💃💃month in tonuwar asirin Sen ya kama🥺🥺



Bare with the typing Errors 🥺 pls ban riga nayi editing ba


    In na ga ruwan comments kuma za ku ga ruwan updates da wuri wuri ma😸


   Have a  lovely weekend 😘


   Ina yi wa kowa fatan Alkhairi,Allah ya karba mana ibadun da addu'oin mu na wanann ranar ta Jumma'at .


Ina masu sha'awar shiga Adashen online,inda za a rike miki Amanar kudi,ba tare da runto ko Ojoro ba,inda za ki zuba ki kuma kwashi kudaden ki, cikin kwanciyar hankali da yardar Allah,ba tare da wata matsala ko tashin hankali ba,


Akwai Matan da sam kudi be cika zama musu a hannu ba,da kin samu sharp an kashe su,someone like me🥺lol,to yar uwa ta shiga Adashe a nan ne,zaki tara kudin ki hankali kwance,


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L7ai2fYGh4UAIK9MhC9awJ


Kindly ki shiga cikin group in nan,2500 weekly,I can assume you Bara ki samu any disappointment ko Damfara ko wani rikici ba, 


For more information,chat her up via:


       08149541182

Sai mun ji ku🙌😍

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


Wannan page ɗin sadaukar wa ne a gare ku:


Princess

Mariam(me suna)

Anty Kaiyyatu

Magama

Maman Sultan 

Wasila Ibrahim

Mrs Abdul

Khadijat

Ummu Husnat and Nihal


Ina matukar godia da kaunar ku gare

ni,🫶🏻❤️


..........


My What's app group link


https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0


In kin San ba karanta book ina da sharhi bane zai kawo ki,don Allah ki yi zaman ki ba sai kin yi joining ba☺️


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


08100046388


******************


Tallah! Tallah!! Tallah!!



Ina uwar da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌 


...........

Page forty eight 


************


..................... Three(3) weeks later 


Tun asuba Sen ya tashi daga bacci kamar wanda ibadar ce gaban shi,inda babu sallah balle sallati,don rabon shi da ya kai goshin shi kasa da sunan gaida ubangijin shi ya manta, 

sammako yayi domin ya samu ya shirya da wuri don yau ta ke ending of the month kamar yanda kuka sani akwai zuwa meeting kauyen OFFA,zulumi yayi ta yi a daki shi kadai,domin baccin ma fita tayi daga cikin idanun shi,gaba daya rayuwar bata yi mishi dadi,ga shi dai ya mallaki duk wani abinda ya ke burin samu a rayuwar shi,amman deep down sai yana jin kamar he is empty,a rayuwar shi,domin babu mutanan da ya fi ba wa mahimmanci irin Alh Kabiru,Nadeeya da Afzaal,sai ga shi lokaci gudu komai ya tarwatse mi shi,Kabiru a halin da suke ciki ko ga snake ba sa da shi,don ba karamin artabu suka sha da Kabirun ba a cikin sati Ukun nan da suka gaba ta,domin idanun Kabiru ya rufe babu abinda ya ke neman gani sai down fall in Sen babu abinda ya ke son gani da ya wuce bayan shi,inda ya sako shi gaba,duk sanda Sen zai yi Campaign to in sha Allahu ba lafiya ake kare taron ba,domin shi kan shi Rilwanun sai an yi da kyar ake fito da shi a tsiratar da rayuwar shi, unnecessary attacks dai ga su nan haka Kabiru yayi ta kai wa Sen Allah na tsiratar da shi,ganin abun na shi yayi yawa ne ya kuma yi crossing all lines and limits ɗin shi,ya sanya Sen sanya wa a sato ma sa shi,farm house ɗin shi aka kai Kabiru in da ya sanya aka yi masa dukan da Saida ya kwana biyar yana jinya a hospital,domin Sen nuna mishi yayi shi din karamin dan iska ne,nuna mishi yayi iskancin shi ya girmi na sa,bayan sun yi masa lilis ya zuba musu Petrol gaba daya tare da kokarin kunna wuta,a cewar shi babu amfanin rayuwar su a ban kasa,ba karamin kaduwa da firgicewa Alh Kabiru yayi ba domin ya san Sen Sarai ba hankali ya fiya ba,yanzu sai ya kashe su,a nan ya shiga bashi hakuri da kyar Sen ya hakura domin rantsuwa yayi kan sai ya kashe su duka,a cewar shi ko ya mutu be da wani regret banda guda daya shine na rashin zama Governor ɗin da ya kwallafa rai a kai,he make ya shata wa Kabiru layi,and yayi rantsuwa har da buga kasa kan ko ciwon kai ya kwanta sai ya ga bayan Kabiru,be tabbatar Kabiru karamin Shege bane sai wannan ranar domin ba karamin fita masa a giya yayi ba,Saida ya tabbatar ya nuna wa Kabirun shi karamin Shege ne,sannan ya nuna mi shi sam shi ba sa'an yin shi bane,ruwa ruwa aka fita da Alh Kabiru daga farm house in harda aikin yin fitsari a jiki domin ba karya ya ji jiki,tun daga wanann ranar ya sama wa kan shi lafiya,domin dif Alh Kabiru be kuma yi mi shi wani abu ba,saidai wai an ce na ciki dai na ciki,don tun daga rana basu kara hada inuwa ba,Alh Salisu yayi fadan,yayi nasiha,yayi lallami,amman duk a banza,and abunda zai baku dariya da su,duk wanda ya so sanin miye hada fadan na su,ko wa sai ya ce a tambayi dan uwan sa,(Ni ko nace daman ina ku ke da bakin fadan me ya hada ku fada,ai daman sai dai kuyi ta kame kame,shi rashin gaskiya daman haka yake).


Babu abinda ya fi tsaya masa a rai kamar lamarin Nadeeya domin bayi da burin da ya wuce ya san yanda ta ke,he want to talk things out with her,Yana so yayi mata bayani tare da wayo tunda diyar sa ce,No matter how bad he is dole ta zauna da shi,and ya san fadin kalman tsanan nan da take masa a iya fatan baki ya tsaya,domin deep down ya san dole akwai raguwar soyayyar shi a ran ta, ko banza ai shakuwa ba karya ba ce,a yanda ya so ta ya kula da ita tare da tattalin ta,be taba dauka lokaci daya za ta iya juya masa baya ba,ya rasa gane har yau a garin yaya ta kama su🤦,he did everything in his power to make sure this little dirty secrets ɗin sa Are safe,but lokaci daya ba tare da yayi tunanin ranar na zuwa ba asiri ya bangada,and abun da ya fi masa ciwo yarinyar sa da ya haifo daga cikin sa ya ke so fiye da komai ita ce ta gano abinda ko a lahira baya fatan ta sani, actually ya san ya cutar da rayuwar Nadeeya cuta mafi girma amman kuma in ya duba ta wani fuskan sai ya ga sam be cutar da ita ba,domin duk wani abinda ya yi,domin ita yayi shi don ya ga ta samu rayuwa mafi inganci ta taso cikin kula da gatan da be samu ba time ɗin da yake yaro,he make sure ya bata duk wani dadin duniya da bata ma taba tunanin akwai shi ba,kudi kam tun tana ciki ta san su domin in dai akan Nadeeya ne baya tsoron kashe mata ko nawa ne don dama can don ita ya ke neman su,yeah ya sani cuta daya ne har yau yake regretting ɗin shi da yayi mata shine Mahaifar (Womb) ɗin ta da ya baiwa Odogwu wanda tun tana 9 years a duniya ya sanya aka cire mata,shi ne kawai zai iya ce wa be kyauta mata ba,Amman kuma shi din ma don ya zo ma shi a babu yanda zai yi ne,Soul,Brain ko Womb in ta Odogwu ya ce dole ya zabi daya ya bada,a na shi tunanin Saida yayi dogon nazari for her on good ne ya bada Womb in nata,a halin da ya ke ciki yanzu ba karamin missing ɗin ta yayi ba,domin a kwanakin nan da suka wuce duk ya kwanta bacci sai yayi mummunan mafarki da ita,wanda ba karamin firgita shi yake yi ba,domin a mafarkin kullum cikin wuta ya ke ganin shi cikin wani katon rami,yana ihu saboda Azabar wutan da ke ratsa shi tare da kuka hawaye biyu biyu,yana me mika mata hannu, a yayin da ita kuma tana daga zaune bakin ramin tana kuka kamar ranta zai fita tare da mika nata hannun sai yayi dab zai kama nata sai wani haske ya zo ya gilma ta gaban shi,sannan sai ya ga wanann hasken ya tafi da ita,ire iren mafarkan da ta ke yi ke nan,a duk sanda yayi kuwa wuni ya ke a firgice,wanda mafarkin ke hana shi samun bacci me nutsuwa yanzu,domin ba wannan bane ya fi daga mi shi hankali,banda irin furucin da Nadeeyar ke fadi cikin mafarkin ba,ya rasa gane me yasa ya ke jin kamar wani babban abu na shirin faruwa da shi,wanda kuma a zahiri be san miye ba!gashi abokin cin mushen nashi sun samu saɓani balle ya je gurin shi su tattauna,and kun riga kun sani at times Ka sanar da damuwar ka inda za a saurare ka,a lallaba ka,tare da baka shawara ma it's something,duk garin Bauchi be da Aminin da ya wuce Kabiru kai zai iya cewa duk duniya ma,domin Alh Salisu basu wani ja shi jiki ba,ana dai abota amman sirrukan su a tsakanin su suke tattauna wa,don gujewa tonuwar asiri,don ba kowa bane daga haduwa da shi ake bude masa ciki ayi ta bayyana mishi sirri ba.


Saida ya ga gari ya soma dan haske sannan ya samu ya baiwa kan shi hakuri daga tunanin da ya matsa wa kan shi da shi,wanda har sakamakon hakan ya ji wata irin ciwon kai ta kama shi lokaci guda,da kyar ya samu ya fada toilet tare da hada ruwan zafi ya shiga ciki tare da lumshe idanu yana tunanin abubuwa da yawa da suka faru a rayuwar shi,ganin tunanin babu inda za ta kai shi ne ya sanya shi watsar wa,domin abinda ya faru ya riga da ya faru babu me canza wa,babu abinda ya fi masa ciwo kamar ɓacewar Afzaal lokaci guda ya juya masa baya,after they have been through this together,don tun randa ya masa duka be kuma taka kafar shi cikin gidan ba,yana dai ganin ana yawan zaran kudade masu kauri daga account ɗin shi,and duk duniya babu wanda ke da Access to his bank account Kai tsaye da ya wuce Nadeeya da Afzaal,tunda ya riga da ya san babu Nadeeyar babu wanda zai zara masa kudade sai Afzaal,hakan be dame shi ba,ila shariyan da Afzaal ɗin yayi masa ne ya fi ci masa rai.


A gaggauce ya tsane jikin shi tare da saurin shiryawa cikin manyan kaya,da kyar ya daure ya ci breakfast ɗin da Falmata ta haɗa masa,domin kwata kwata tunda ya tashi daga mugun mafarkin yau da yayi ya ke jin jikin shi kamar ba na shi ba,cikin sauri ya kammala duk abinda ya ke son yi domin baya son su yi yamma a tafiyar su,ya sanya shi ma kin komawa bacci,ba tare da bata lokaci ba kuwa ya fito tare da fadawa motar,yana me jaddada musu kan su lura da gidan har ya je ya dawo,as usually Sa"eed ne ya tuka shi har suka isa,this is the first time da suka je meeting ba tare da waya da juna ba, although ba a mota daya suke tafiya ba,kowa motar shi ya ke shiga amamn sun yi ta waya ke nan har sai sun isa,don tun ana saura sati suke shiga tattauan wa game da bukatun da za su gabatar a gaban me girma Odogwu.


****************BLAZED 🔥 HOUSE



Kamar kullum yau ma babban hall in da Odogwu ya saba gudanar da taron ending of the month ɗin shi na shedanancin,cike ya ke fal da mutane ana sha red and black,a ciki kuwa harda Sen da Alh Kabiru wanda tunda aka shigo meeting ɗin,idanun Odogwu ke zube a kan su,kallon su yake babu kyafta idanu yana jiran a kammala meeting ɗin ya gana da su,ai ko nan aka shiga gudanar da abubuwan da aka saba yi duk meeting,masu kawo Sacrifices na yi,wanda suke kawo new members aka karbe su,tare da karanto musu rules and regulations in kungiya,sanann Odogwu yayi exusing ɗin kan shi,yana me nuna wa Kabiru da Rilwanu alamu da hannu kan su biyo bayan shi, bayan ya gama sauraron koken kowa da ke gurin,tare da jadada musu kan ce wa kar shi ji tsoron sanar da shi matsalolin su,sannan su sanya yarda da imanin su gare shi,da sannu zai biya tare da cika wa ko wanann su muradan son ran su.


Jiki babu karfi suka mike tare da bin bayan Odogwu nan private room in Shi suka same shi,hakince akan kujerar tsafin shi,idanun shi a kulle yana shafan kai da jikin macijiyar shi hankali a kwance,duk da ya ji shigowar na su ba shi ya sanya shi mike wa ba,balle su sanya ran zai kula su,ila ma kara relaxing da yayi tare da mimike kafufuwa kamar wanda ke kwance gadon bacin shi,har wani ajiyar zuciya ya shiga saukewa na time to time,tsaban Iskanci da nuna isa wai nan wanda be san shi ba dauka zai yi bacci ne ya dauke shi me masifan nauyi.


Ganin mintinan su kusan 10 durkushe a gurin daki baki wuluk har iyanzu haske be bayyana ba,balle su sanya ran jin dalilin kiran na su daga bakin shi,ya sanya hankalin su mugun kaɗuwa domin ko ba a sanar musu ba,yau kam sun san sun shiga ukun su,domin ga dukkan alamun Odogwu na tsananin fushi da su,a kuma iya tunanin su,sun gaza gano miye abinda suka yi mishi har ta kai shi ga yin irin wannan fushin,domin duk tunanin su ba su ga yanda suka kuskure ba balle a su sanya ran game da hakan ne ya ke fushi da su.


Wasu 5 mints ne suka kuma wuce wa,har zuwa lokacin Odogwu be motsa ba,balle ya bude ido ya ma kalle su,balle su sa ran jin muryan shi hakan ne ya kuma kidima su,domin yanzu kam ya tabbata fushi Odogwu ke yi da su,nan take suka rarrafa tare da nufan inda Odogwu ke zaune suka fadi a gaban shi tare da rushewa da kuka,ido wannan ya dago be yi ba balle ya ce da su miye dalilin kukan na su,nan suka shiga rokan shi suna kuka suna masa kirari da turanci da kuma Yarbanci,kusan mintuna Biyar suna abu daya ka fin can ya wani zabura tare da mike wa zaune,fuskan nan ta mau tsaban bacin rai half face ɗin shi ya koma na snake while other half in na mutane.


Hannu yayi clapping cikin fushi nan take kuwa sai ga wasu katti majiya karfi,sun shigo cikin dakin hannun ko wanann su dauke da doguwar bulala,suka zube gaban Odogwu suna me yi mishi kirari,kawukan su ya shafa, sannan ya nuna musu Rilwanu da Kabiru da ke durkushe gefe guda,"Beat the hell out of this 2 idiots"ya kare bakin shi har na kumfa,idanu duk suka zaro da jin abinda ya fadi,to me suka mi shi da zai sanya a musu mugun duka haka,ba su kai ga bude ba ki ba,suka ji an wulla su sama tare da caɓe su nan take kuwa aka mike su,ba tare da sun farga ba Kattin Odogwu suka shiga tsala musu bulale ta ko ta ina,babu abinda suke banda ihu da kukan neman agaji,domin ba karamin shigar su bulalan suke ba,tun hawaye na fita a cikin idanun su,har ya kafe ya daina zubowa muryan su ya soma shigewa saboda tsantsan ihun azaban da suke ta faman yi, Odogwu na nan zaune ya lumshe idanu ba tare da damuwa da ihun kiran sunan shi da ya taimake su da suke ta faman yi ba.


Saida ya ga suna shirin barin duniya don azaba,ya tabbatar da sun yi laushi iya laushi sannan ya tafa hannu alamun su daka ta,a take suka dakata,tare da barin dakin suna me bin ta kan hannayen su da kafafun su.


Tashi wa Odogwu yayi tare da daga hannun shi sama sai ga wata kwarya da ke cike da jini,watsa musu yayi a take kuwa suka sauke wata irin wawiyar ajiyar zuciya,tare da fashe wa da sabon kuka,wannan Azabar har ina,a ce ayi musu irin wanann dukan har Saida suka suma ba tare da sanin laifin da suka aikata ba.


Cikin ihu ya soma magana cikin yaran turanci"Ashe daman baku da hankali ba ku da mutunci ban sani ba?How dare you 2,kuna tunanin bana ganin duk abinda kuke yi ne?,me na fada muku a cikin rules in brotherhood?Ban ce da ku dole ku koyi rike sirri ba,tonuwar asirin daya tonuwar asirin kungiya ce baki daya,and da ku tonawa kungiya asiri gwamma na kashe ku da hannu na"ya kare yana me matse mu su wuya,nan take idanun su suka firfito "saboda ba ku san me kuke yi ba a cikin bainar mutane kuke neman tonawa kawukan ku asiri,wlhy kun ci Sa'ar wanann ranar ina good mood ne da sai dai ku ga baku numfashi yan iska bunch of illiterates and hopeless people kawai",ya kare yana wanke fuskan su da dirty slap,nan suka shiga ba shi hakuri zuciyar Rilwanu na tafasa domin har ga Allah ya soma gajiya da wanann mulkin kama karyan da ya ke musu,sai da ya gama ci musu mutunci tare da kare musu zagi tsaf sannan suka samu da kyar ya yafe musu,fuskan cike da murmushi Alh Kabiru ya shiga kwararo godiya kamar wani Ubangijin shi yayi wa laifi ya ce ya yafe mishi,da hannu yayi musu alamun su tashi su ɓace masa daga gani,bayan sun masa alkwarin no matter what next time ba za su kara yin abu makamancin hakan ba,ba karamin sosuwa ran Rilwanun yayi ba domin gani yayi Odogwu ya raina masa wayo,tunda Sarai ya san abinda ya faru a tsakanin shi da Kabiru ya kuma san sarai da gangan ya bada in law in sa ba,why be wanke shi daga zargin da Kabiru ke yi mi shi ba,har sun kai bakin kofa suka ji muryan Odogwu yace "Rilwanu you stay back I want to have some words with you!,da jin haka kuwa Kabiru ya yi saurin ficewa daga dakin,zuciyar shi na azazzalar shi gurin Sanin abinda Rilwnaun za su tattauna da Odogwu,bin shawarar zuciyar shi yayi tare da makale wa nan jikin kofar yana me baza kunnawa domin sauraran miye dalilin kiran da Odogwu yayi wa Rilwanu.


Saida Odogwu ya gama yi wa Rilwanu kallon wulakanci sannan yace da shi"sit down i want to have a serious talk with you"ba musu kuwa Rilwanun ya nemi guri ya zauna idanun shi a kasa....."Rilwanu tun joining ɗin ka ƙungiyar nan nake kaunar ka saboda kwazan ka,You make sure kayi duk abunda aka sanya ka yi,You have shown your loyalty towards Brotherhood and I do appreciate you for that,ya sanya in abu akan ka ne bana samun kwanciyar hankali sai na ga na saisaita maka,dan nisawa yayi sannan ya cigaba as you know election is around the corner,and babu biggest dream in da kake da shi a yanzu da ya wuce ka lashe wanann kujerar zaben,da sauri ya daga kai alamun haka ne.


Miƙewa tsaye Odogwu yayi a take fuskan shi ya sauya zuwa na fushi,"Saida na ga masifa na tunkaro ka Rilwanu!!akwai babban abinda zai same ka,if care is not taken",da sauri Rilwanun shima ya mike tare da cewa "Odogwu and what is that?yanda na zo so far ɗin nan i don't want any distractions,duk abinda zai zamo silan rasa takara ta i hate that thing with passion"..."I can't say ga actually abinda zai same ka,but all I know is masifa na tunkaro ka,kuma musifa ce ne girman gaske don tsaf zai iya zama silan rashin zaman ka Governor!

domin a halin da ake ciki your daughter has regain her senses,domin Aljanun da na aika suna monitoring ɗin ta,an raba ta da su,a bisa sakamakon haka suka dawo mun in a bad way,just take a look at my face and see",da sauri Rilwanu ya dago tare da zuba wa Odogwu idanu ,wani irin tsoro da firgici ne ya kama shi,domin ganin irin yanda rabin fuskan Odogwu ya babbake ya kwale tare da sidewa,wani irin wawan Amai ne ya ji ya taso masa,domin tun shigowar shi be lura da fuskan Odogwu ba kai babu wanda ya lura saboda kyelen da ya sanya ya rufe,tashin hankalin ne ya hade masa biyu da jin kalman Nadeeya ta warke wai,(tun ranar da Mal Hukmullah yayi wa Nadeeya Rukiyar karshe miyagun Aljanun nan da suka bar jikin ta, direct gurin sender ɗin su Odogwu suka nufa,inda a samakon kona su da aka yi suka huce haushi a kan shi,basu yi sanya ba suka babbaka mishi barin fuska tare da cinyar shi guda,ba karamin wahala da jinya ya sha ba domin ba karya ya konu in kuka gan shi kamar wanda aka yi barin gaushi a fuskan na shi,a hakan ma wai fuskan yayi kyau da ya dage da neman magunguna domin abun kunya ne a zo meeting a tarar da shi haka,hakan ya sanya ganin har iyanzu fuskan be cike ba ya sa yake using kyalle tare da kare konar na shi,don gudun kar jama'ar da ya tara mara sa tsoron Allah su gani,Ni ko na ce madallah ai da ran ka suka raba ka da shi kowa ma ya huta),abinda ya kuma frustrating ɗin shi ke nan ya sanya aka zane musu jiki,don suyi sharing pain ɗin,duk abinda ya ke don su wai har za su tsaya Flighting each other like Cat and Dog.


A firgice Sen ya shiga tambayar Odogwu way out ya zai yi domin wlhy baya son rasa kujearar shi,da wani ido zai kalli duniya,in haka ta same shi,duk ya bi ya rude kamar har an yi zaben sakamako ya ke jiran ji,dan dariya Odogwu ya sanya sannan ya ce "sanin kan ka ne Odogwu na da solution to each and every problems ɗin ku, wannan ma yana da solution in har Ka yarda za ka yi abinda zan fada maka, failure to do it kuma sai ka fara counting ranar shiga tashin hankali da damuwar ka"da sauri Alh Rilwanu ya ce am so ready Odogwu in dai akan Mulki na ne,na bada Ubana da Kishiyar uwa ta,Mata da yaran Dan uwa na,ban ga abinda da ba zan iya ba,fata na dai wanann Bala'in da ke tunkaro Ni ya yi nisa da Ni, domin Ni kai na i have been having bad dreams kwana biyun nan "ya kare zufa na karyo mishi.


Dan dariya Odogwu yayi tare da komawa ya zauna,sannan yace"ina sane da irin miyakun mafarkan da kake yi game da yarinyar ka,and I swear to you with my living self Odogwu of all Bokaye da yan tsafi dukka duniya,in har baka aikata abinda zan fada maka ba,abinda zai same ka sai ya fi abinda kake gani a mafarki muni da ciwo "......"Odogwu just say it am ready,nayi sacrificing su Ummi ma Wlhy"....a zafafe Odogwu ya daka mi shi tsawa"how many times na ke warning ɗin ka game da kira mana sunan wasu ababen bauta,ka san su ka zo gurin mu?"Ya kare a zafafe.


Hakuri Rilwanu ya bashi tare da neman yafiyar shi kan ba zai sake hada shi da ko wani irin abun bauta ba(Inalilahi wa ina ilahi raju'un 🥺🥺a rayuwar nan babu babban arziki da Dan Adam zai samu da ya wuce Allah ya bar shi da imanin shi,tare da bashi ilimin banbance daidai da ba daidai ba,Allah kar ka mana jarabawa da abinda zai fidda daga Muslunci,Allah kar ka raba mu da imanin mu,ka kare mu daga yi maka shirka,sannan duk tsanani duk wuya ka ba mu ikon kadaita ka kai kadai a gurin bauta da neman taimako,wlhy mu ji tsoron Allah mu daina ɗaukan hakkin Allah muna baiwa wanin shi,Allah ka shirya mana Zuri'ar mu ba don mugayen halayen mu ba).


Dan shiru dakin yayi for some mints kafin Odogwu ya ɗan nisa"tun farko Rilwnau taurin kan ka ne ya jefa ka a cikin halin da kake ciki,and yanzu abu da ya riga da ya kusa zama late kake neman mafita".."na sani Odogwu amman kai me tausayi ne kai taimake Ni kar duniya su yi mun dariya"....mike wa tsaye yayi sannan yace "well am very sure Bara Ka taba manta abinda mu ka tattauna da kai 2 years back ba",idanu Rilwanu ya rintse domin baya kaunar abinda zai tuno masa da abinda ya faru 5 years back ba,domin wannan tashin hankalin ya faro neme lokacin da Nadeeya ta cika 18 years a duniya ta ta kuma zama babbar budurwa son kowa kin wanda ya rasa ba,a lokacin da manema suka fara zuwa mata,har yanzu yana jin maganar Odogwu a cikin kunnuwan shi amman gani ya ke babu abin kunya da zai aikata a duniya da ya wuce ya nemi yar cikin sa da karan kan shi,a yanda ya ke tsananin so da kaunar Nadeeya,ko hannun wani Shege ya gani rike da jakar ta ko kasan takalmin ta sai ya tabbatar ya raba wannan mutumin da rayuwar shi,domin Nadeeya daban take a cikin zuciyar shi,ya kwari yarinyar kwaruwa me girma a duniyar nan a taya wai shi da kan shi zai nemi yarinyar da ya haifa a cikin sa,ai kazantar tayi muni da yawa,Saida aka kai ruwa ranar sannan ya samu Odogwu ya canza masa,wanda ya ji sam shima ba abu bane me yuwa domin Odogwu ce masa yayi ya zamo dole ya je ya sadu da Uwar sa mahaifiya wace tayi silan zuwan shi duniya a hakan ma ta baya,ba karamin kaduwa da tashi hankalin shi yayi ba,a nan ya zube yana kuka ya ce wlhy ya hakura da kungiyar in har sai ya nemi Mahaifiyar shi ta baya ne,ba karamin artabu suka sha da Odogwu ba kafin ya samu ya kuma canza ma sa,tare da sanar da shi wannan shine last time ɗin da zai bashi task ya nemi a canza masa domin ai ba shi ka dai bane a kungiyar,ko wanda aka ba shi ba karamin kada mi shi da hanjin ciki yayi ba,ya ji kamar ba zai iya ba amman kallon da Odogwu ya watsa mi shi ya sanya shi karba tare da yarda domin a ganin shi gwara wannan sau dubu akan ya nemi diyar da ya haifa,ko uwar da ta haife shi.


"Am very sure shirun nan da kayi ka yi ka tuno komai ne dai ko?"shiru yayi ba tare da ya ce komai ba yana jin bugawar zuciyar shi na karuwa,baki na bari yace"Odogwu i beg of you plssss"hannu ya daga mi shi alamun yayi mi shi shiru kar ma ya karasa"Rilwanu!this time around ba ka da wani option da ya wuce maka aiwatar da abinda na sanya ka 5 years back,domin shine kadai abinda zai ce ce ka,ya zamo maka dole a cikin biyun nan ka zabi guda,is either Ka nemi Uwar ka ta baya,ko ka jira Nadeeya tana nan zuwa gurin ka cikin kwanakin nan ita ka neme ta ta bayan, because you are one of my Fav ya sanya na baka choice biyu,don haka zabi ya rage naka,ya kuma zame maka dole within 3 days ka aikata hakan ko ka ga abinda ran ka baya so "ya kare yana me mikewa,a haukace Rilwanu ya nufe shi tare da takatar da shi daga barin dakin"Odogwu kar ka mun haka,sins ɗin da na yi a baya ma sun yi yawa sun munanan da yawa,and bana fata har Hajiya ta mutu ta san su,ka bar Ni in ji da abin kunyan da na aika ta wa Nadeeya wanda na san ta sani kuma har yau nadamar sanin ta nake yi,don na san ya fito duniya har ta mutu mutane ba ra su daina tsangwaman ta ba,ka canza mun wani Odogwu ba zan iya yin wannan ba"nan Odogwu ya rufe ido yace sam be son zance ba ya zama dole sai ya zaba a cikin abu biyun nan ko kuma ya kuka da kan shi,ba karamin rudewa Rilwanu yayi ba,kuka ya ke da hawaye biyu biyu,a taya ma zai fara neman Hajiya tashin hankali,da girman san nan ko rungumar ta,ba yarda za tayi yayi ba balle har ta kai su da ya sadu da ita, don wulakanci ma wai ta baya,yau ko ta gaba baya jin ko zai mutu za ta ba shi balle ta baya,ai asirin shi kawai Odogwu ke san tonawa,Nadeeya kuma cutan da yayi mata ya isa haka,a ma taya zai tube yarinyar cikin shi ya hau neman ta ta baya ai abu ya lalace,a yanda Nadeeya ta mugun tsanar shin nan ai babu abinda zai hana ya kashe shi,ganin fa duk irin rokon da ya ke wa Odogwu ya ki bashi listing ears balle har ya kai shi ga ya janye maganar shi ya sanya shi miƙewa a mugun fusace,domin baya jin ko sama da kasa za su haɗe be ga abinda zai kai shi neman Uwa ko diyar shi ta gaba ma balle ta baya,ko Nonon su ya ce ya shafa wlhy baya jin zai aikata balle har ta kai ga Anal sex.


A harzuke yace"Kai Odogwu dan uwar uban ka nace ba zan iya ba ana dole ne!!,wlhy tallahi saidai duk abinda zai faru ya faru amman ba zan taba neman su ta gaba ba ma balle ta baya,haba kai wani irin dan iskan Halitta ne?duk irin abubuwan da na aikata domin kai baka gani ba,sai ka kaini ga aikata abinda zan rasa raina,wlhy Hajiya kashe Ni za ta yi tsaf ta kama Ni ina kokarin neman ta ta baya",a harzuke Odogwu ya juyi"Kai Rilwanu Ni kake wa shouting??"Ayi maka din kai ka hallice ki ko uban ka?wlhy na gaji ba zan iya ba,ban taba haduwa da tantirin dan iska irin ka ba,babu abinda ka sanya gaba sai batar da bayin Allah,kai a kullum baka bada task sai wanda in mutum ya ji sai ya girgiza,to wlhy I can't take this anymore,in da Kai din na gaske ne,ai da tuni ka kawar da matsalan da ka hango tattare da Ni,me ya hana ka sanar wa Kabiru kan cewa bani na kashe Jaazmeen ba??ko ka janye maganar kan nan ko kuma wlhy in fice daga kungiyar nan domin na gaji Ni ba dan iska bane,ko baka fada ba am very sure in na sadu da su mutuwa za su yi,to ina ranar kudin nawa domin su na tara amman duk wanda ya dace su mori arziki na kansa ya na bada su,na baka Gwoggo matar da na fi kauna sama da Hajiya ta,na baka Mahaifi na, mutumin da baya hada soyayya ta da na kowa,yanzu don baka da kunya ka ce wai in kwanta da Nadeeya bayan duk irin Azabar da na sanya ta a ciki,To Allah ka ji dai na rantse ba zan yi ba"


Ai a harzuke Odogwu ya shako shi tare tare daga shi sama"You bastard ungrateful fellow,bayan duk abinda nayi maka a rayuwa Ni kake fada wa haka,saboda kai butulu ne ko?to wlhy kayi kadan in baka umarni ka ce ba za ka yi ba,laifi na ne da na nuna maka kauna tun farko,duk wani abinda na ke sanya ka ba for your own good nake yi ba,amman da ke ku Hausawa yan iska ne shegu wanda ba su son hallaci ba,shine without any fear za ka tsaya kan idona kana fada mun magana son ran ka ",at that moment zuciyar Rilwanu ya riga da ya bushe ya dade yana tara Odogwun daman,hakan ya sanya shi sanya kafa ya tokare shi a ciki,tare da kai hannun shi barin da ya kone a fuska ya damka gurin,wani wawan ihu Odogwu ya sake tare da saurin sake shi ya fadi kasa,da sauri Macijiyar Odogwu ta yo kan Rilwanu ba tare da tsoro ba ya sanya kafa ya take mata ciki,a take ta sandare,wani wawan Ihu Odogwu ya sake "Rilwanuuuuuu!! How dare you",a fusace yace "in ce wannan ne karfin tsafin naka to na kashe shi,kayi uban da za ka yi,and from now on Ka Bude kunann ka ka ji Ni da kyau Na bar Brotherhood domin na raina karfin tsafin ka,ace tun yaushe yarinya ta ta ɓace ka gaza gano yanda ta ke,kai a hakan kana kiran kan ka Odogwu to from now on Dan uban ka nine nan Odogwun kaina and in ga dan Bura uban da ya isa hana Ni cin zabe na,with or without you Zan cigaba,gwara in je in Nemo wanda ya fi ka karfi,ko Ni da kaina na zamo master ɗin kai na,kila na huta daga wannan rashin kwanciyar hankalin da nake ciki"


"Kayi kadan Rilwanu,ba ka isa barin Brotherhood ba,ka riga da ka siyar mana da soul ɗin ka da na yarinyar ka,na rasa nata ta karfin tsiya shine kaima kake son kwace naka, after all duk abunda mu ka yi maka a kungiyar nan?..."har akwai abinda kuka yi mun for free,nan na ga ko 5 kobo ban taba samu daga gare ka ba tare da na bada wani abu in return ba,na shiga kungiyar nan ne bisa ra'ayin kai na kuma don yan uwa na su mori arziki suyi rayuwa cikin rufin asiri tare da matata da yara na,Saida ka tabbatar ka raba Ni da duk wani farinciki na,na baka mata na,yara na kusan 5 ina baka su ba tare da ma sanin mata bane ko maza,ka sanya ne aikata mumman abun kunyar da ba zan iya kallon yarinya ta ido cikin ido ba,I AM FED UP ODOGWU!!kamar yanda nace maka na shiga ne don ra'ayin kai na haka zalika ban ga uban da ya isa hana Ni fita ba,daga yau Na bar Brotherhood in kuma ka isa kamar yanda ka ce ka hana Ni zama Governor in garin Bauchi"ya kare zuciya a zafafe tare da ciro zoben tsafin da ke sanya a yatsan shi ya hurga,ya juya tare da kokarin barin dakin.


"This will be the biggest mistake of your life Rilwanu you better get back to your senses, your soul is mine and in har Ka ce za ka butulce mun i will make sure in nuna ma zalunci na"..."wai har akwai zaluncin da ya fi wannan, Odogwu na fita do your worst"dariya Odogwu ya sake"alright bayan duk chances ɗin da na baka be sanya kayi hankali ba, let's Aswear to you with my throne and power sai na tozar ta ka, in har baka aikata abinda mu ke so ba,sai ka wulakanta ka,and I will make sure gurin ganin ka rasa duk wani abinda ka mallaka"tsaki Rilwanu ya ja domin a daidai wannan time ɗin baya ji baya gani, zuciyar shi ya riga da ya bushe,kofa ya bude a fusace,tare da fadawa wani dakin da suke aje kayan su,ba tare da lura da Kabiru da ke makale bakin kofa ba,cikin sauri ya shiga sanya kayan shi,yana jan tsaki akai a kai,don Iskanci wai sai mutum ya dube zindir gaban Wani kato,shi dai yau zai huta domin be ga abinda zai sanya shi cigaba da zaman kungiyar nan mara adalci ba,be dauki time ba ya gama shiryawa tare da fitowa,burin shi be wuce ya gan shi cikin motar shi ba,da sauri ya ji an capko hannun shi"Rilwanu You have to think about this,Kar kayi abinda za ka yi danasani a karshe, Odogwu ya wuce duk yanda kake tsammani,ka koma ka bashi hakuri kafin ya zama to late",fincike hannun shi yayi"Stay away from me and hold your advice to your fucking self Kabiru bana bukata,har ma yaushe ka damu da lafiya ko akasin sa a gare Ni, munafuki to ka rike fake concern ɗin ka,don ba zai yi aiki a kaina ba,domin an yi Walkiya na riga da na san waye kai,from now on babu Ni babu kai"ya kare yana me watsa mishi harara tare da tafiyar shi,be damu da dimbin mutanan da ke zaune a gurin jiran dawowar Odogwu ba ya ja musu tsaki tare da ficewa daga hall ɗin,kan shi tsaye ya fada motar shi tare da ba shi wuta yana me barin gidan, yana sanyawa a ran shi babu abinda zai dawo da shi kuma, Odogwu na tsaye idanun shi lumshe har yanzu ya kasa yarda wai Rilwanu ne ya masa irin wanann cin mutuncin ,thank god ma ya kira su private room ɗin shi da a bainar mutane zai ci zarafin shi,ai ko Rilwanu ya kira War domin tunda ya nuna masa kasawar shi,shi kuma yayi alƙawarin sai ya muzan ta Rilwanu sai ya maida shi abin da za a dade ana maganar shi a garin Bauchi,kujeran mulkin kuma sai ya hau ya gani,daman can da taimakon shi ya ke taka rawa tunda ya iya butulce masa daga yau zai zare hannun shi a kan shi,wannan ranar be koma cikin hall ɗin ba don bakin ciki,domin gefen face ɗin shi da Rilwanu ya damka har yanzu sai fidda jini ya ke yi,a haka aka watse daga meeting ɗin ran kowa babu dadi,domin da yawan su ba su riga sun fadi bukatar su ba.


************Kaduna state


Cikin yarda da hukunci na Allah aka yi Surgery ɗin Nadeeya aka kare cike da samun nasara,ba karamin kyan jiki gare ta ba domin kwana uku da yi mata tiyatar ta farfaɗo tana iya cin fruit irin su Banana,da apple tare da ruwan dumi,Mama tsaye ta ke a kan ta,duk da har yanzu ba wai bari ake su gan ta ba,domin kwana biyar da yi mata aikin Doc Akim Mustapha yayi suggesting a wuce da ita Rehabilitation Centre,domin ta nan ne za tayi saurin samu tayi regaining certain functions and activities of her daily living(Rehabilitation may include working with physical therapists (PT), Occupational therapists(OT),Speech therapists and other specialists depending on each patient unique needs) .


Satin ta biyu a gurin and ba karamin dadi su Mama su ka ji da wanan shawara ba domin tana da bukatar hakan,at time aka yi wa mutum brain surgery tafiya wanann sai an komo an koya maka,domin brain yana daga cikin important organ a jikin dan Adam da ke watsa sako zuwa ga sauran part of the body,da kyar Mama ta shawo kan Nameer ta samu ya bi Habeeb suka koma bakin aikin su,akan ya bari sai zuwa 3 weeks ɗin da doctor yace by then za a iya maida ta gida in ya so sai ya dawo,don babu amfanin zaman na shi since ba shiga gurin ta ya ke ba and gurin aikin sun fara complain,a haka ta samu ya tafi Amman kuma kullum yana cikin kira minti minti domin jin ya lafiyar ta ya ke, Mujaheed da matar shi Jamila su suke taya mama da wasu sunturin,har Allah yayi yau ta cika sati Uku cif cif,kuma yau suke tsammanin sallama daga asibitin,tun sassafe ya ke cikin asibitin,a zuwa yanzu Mama ta daina mamakin halayen Nameer sai ma dariya da ya koma bata,don ta dade bata ga soyayya me karfin wanann ba,ko lokacin da ya so marigayiya Raa"isaah be yi irin wanann haukacewar ba,domin in ba idanun ta ke mata gizo ba har fadawa ta ga yayi sai uban dogon hanci a fuska,to ba dole ya rame ba,ina ka fito Nadeeya ina za ka Nadeeya,and ka taba shi ya ce wai tausayi ne,ita bata taba sanin Nameer ɗin sakarai bane sai yau,wato yana so ya ce be san son ta ya ke yi ba,akan ta ya fara soyayya da zai ce be gane ba,ko kuma dai ya gane yana dai jin tsoron rejection ne daga gurin ta,ya sanya ya ke ta danne son da ya ke yi mata din,maganar shi ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta fada,in da ya sanar da ita kan su je office ɗin doc Akim yana son ganin su.


Nan suka shiga cikin office ɗin,bayan sun gaisa ne,Doc Akim Mustapha ya miko musu takardar sallamar ta"ga shi nan Doc yau za ku ɗauke mana Pookie daga hospital ɗin nan(karfi da ya ji duk Saida suka kama sunan Pookie tsaban yanda Nameer ke yawan ambata, actually I can say she is indeed a fighter domin ban taba ganin a irin case ɗin ta mutum yayi saurin warkewa ba irin ta,make sure to continue taking care of her,in za ta yi wanka a na rufe kan,sannan har yanzu bata kai na daukan abu me nauyi ba ko kuma cin abinci me nauyi ba,ayi avoiding mata too much stress,sannan kar ayi wasa gurin ganin ta ta sha magungunan ta akan time,Allah ya kara mata lafiya za ku iya tafiya da ita gida yanzu,zan yi wa nurses magana su kai muku ita mota,in kuma akwai wani matsalan da ta taso game da health in nata make sure to give a call"ya kare yana mika wa Nameer hannu,wanda ya ke ji tsaban murna kamar ya dauki Doc ɗin ya goya yayi ta yawo da shi a bayan sa,godia sosai suka yi mishi sannan suka mike tare da fitowa daga office ɗin Nameer har harɗewa ya ke yi garin sauri don ya je ya ga Nadeeya don ba karamin missing ɗin ta yayi ba,"slow down Baba na Nadeeyar nan dai gidan mu za mu tafi da ita fa ko ka mance ne" ...."Wa ai kyalle Shi kawai Mama ai yau kuma babu wani sarki sai Allah Hajiya Pookie an samu lafiya "Mujaheed ya fadi yana dariya,kala Nameer be ce da su ba,ila ma kara saurin da yayi banda dariya babu abinda su Mama ke yi mishi.


Da kyar aka samu ya iya tuka motar wanda ya seta face in Nadeeya da ke bacci hankali kwance through front mirror,a haka dai suka samu suka iso gida lafiya,shi ya shigo da ita har dakin Mama tana dauke a hannun shi,ya zuba wa kyakkyawan fuskan ta ido,ta rama sosai fiye da farkon ran da ya fara ganin ta,duk da can daman ba wani kibar a zo a gani bane gare ta,making up mind ɗin shi yayi ya zama dole ya nemo mata abubuwan gina jiki ta hau ci,domin be ji dadin ganin ta a rame ba,Saida Mama tayi magana sannan ya samu ya aje ta akan gado tare da fitowa daga dakin ran shi be so ba, a nan palor duk suka zauna sannan Mama ta sanya aka kawo musu abinci,Saida duk suka ci cikin kowa ya dauka sannan Mama tace Jamila ta taso su shiga tayi wanka tare da rama sallan Magrib da ba su samu sun yi ba,ba musu kuwa ta bi bayan ta zuwa dakin,a cikin kayan da ya siyo wa Nadeeya Mama ta dauki Abaya sabuwa ta baiwa Jamila ta saka bayan ta fito daga wankan,inda Mujaheed kuma dakin Nameer suka wuce suka yi wanka sannan suka wuce masallaci domin lokacin Isha ya kusa shigowa.


********************Kareematu 


Tun ranar da suka dinke da Doc Bashir a office ɗin shi ya makale mata,a cewar shi wai ta kara dadi sannan ta tara bashihikan sa a kanta don haka bata isa ba sai ta biya shi,baya missing ɗin opportunity ɗin neman ta,inda abinda ta kwana biyu bata yi ba wato fita night duty ta dawo da shi kusan kullum, sosai ta saki jiki da Doc Bashir kamar wani mijin ta suna moran juna yanda suke so,a yayin da ya ke mata barin kudi son ranta,ba karamin sosuwa ran Abdul yayi ba,domin in akwai abinda ya tsana a rayuwar shi wannan night shift ɗin da Kareematu ke yi ne,and wlhy Allah ne shedar shi ba wai yana zargin ta bane na cin amanar shi,ko daya don ko sau daya be taba barin shedan ya raya mi shi Kareematu na cin amanar shi ba,duk da yana ganin pacakar da take yi da kudade a yan tsakanin satikan nan,inda ta sanar da shi adashe ta shiga kuma dauka ta biyo ta kan ta,so kudin ta ke more wa,a take ya yarda don a ciki har tayi cefanan gida don ta rage ci masa mutunci yanzu,tayi wa su Khairat ɗinkin uniform,tare da biya musu kudin makaranta,shima Abdoul din har kaya kala biyu ta dinka masa,inda yayi ta mata godiya tare da sanya mata Albarka.


Tun safe yau bata zauna ba tana gurin aiki sai yamma liss ta dawo a gajiye,inda ta samu Khairat da yan uwan ta sun gyara gidan tsaf tare da dafa abinci,bata bi ta kan su ba ta fada dakin ta,tare da shiga bincikan gurin ajiyar kayan ta,domin tana son yau tayi kwalliya irin wanda bata taɓa yi wa Bashir ba, magungunan mata ta karbo,masu kyau da aji da rikitar da mutum ta aje gefe,domin tana son yau ta kurewa Bashir tunanin shi,don yayi alƙawarin siya mata sabuwar mota muddun ta jiyar da shi dadin da zai sanya shi mantar da kan shi,inda ita kuma tace da shi ya tsimaye ta tare da tanadan key ɗin motar,don za gani,a haka suka rabu tare da sanar da ita kan cewa zai mata texting ɗin address ɗin da za ta same shi, ta samu ta fito kafin 8.


Suna zaune da Abdoul a parlor ba ma wuta yana musu fitata da hand fan ɗin hannun shi ta muskuta sannan tace "yauwa Ababan Khairi na mance ban fada maka ba,wlhy Doc Haneefa ta gyaiyace mu dinner in taya murnan karin matsayin da aka mata a gurin aiki",rana na farko duk shekarun auran su da ta fada mi shi magana ya ji sam be gamsu da maganar nata ba, sanan kwata kwata be yarda da ita ba,domin a kan idon shi ya ga tana ta shaye shayen magungunan matan ta,wanda shi rabon da suyi kwanciyar aure har ya mance,da yayi magana za ta ce "Kai babban Khairi wlhy ka fiye fitina,baka ganin su Khairin sun fara zama budurwa ne,dubi har nono ne a kirjin ta,me kake son mu koyar mu su ke nan"da irin wanann excuses ɗin ta ke hana shi hakkin shi a duk sanda ya tambaya.


"Kayi shiru ina maka magana baka ce komai ba"...kallon ta yake ido cikin ido sannan yace "Kareematu tsakanin ki da Allah Dinner in Haneefa za ki je ko kuma wani gurin na ki daban"


A harzuke ta mike"ban gane wani irin magana bane haka,Abdoul abun na mu har ya kai haka,zargi na kake ko kuma gulman mutane ka fara yarda da shi,da har za ka fada mun haka,to wlhy duk wani munafikin da ke kawo maka gulma na ya guji randa zan kama shi,domin wlhy sai na kan uwar mutum duk girman shi kuwa, maganar kuma ina zani na fita hakkin ka na sanar maka,Ni dai dinner ɗin Haneefa zan je,in ka ga dama ka yarda da magana ta ko kuma ka yadda da gulman mutanan da suke kawo maka"ta kare a zafafe kamar tana magana da yaron ta,(Mata wlh tallahi mu ji tsoron Allah mu guji kuntata wa da raina mazajen mu,domin ya fito daga bakin da baya karya,da za a yarje ayi wa wani sujjada bayan Allah madaukakin sarki,to kuwa da an sanya Mace tayi wa mijinta sujjada,domin a nuna muku mahimmancin da miji ya ke da shi a musulinci,manta da cewa wai ai yana cuta na yana ha'inta na bari na rama Nima gurin hana shi kwanciyar hankali, foolish you!!Na rantse da girman Allah mance da duk wani sallah da azumin ki duk macen da ta mutu tana gallaza wa mijin ta har ya kai ga ya budi baki bayan mutuwar ta yace ai wace hmmm,kwata kwata ban ji dadin zama da ita ba,wlhy babu makawa ke da Aljana sai dai ki ga ana shiga,domin aure darajar shi ya wuci wasa,ko da ace yana muzguna Miki,yi hakuri ki bar shi da Allah in kun je can ya biya ki,in kuma kin ga baki iya dauka to ya fi cikin sauki ku hakura da auran,domin babu macen da ta isa hukunta mijin ta ba,don neman Aljannar ki kike je,kuma Aljannar ki na tafin kafar shi,Allah ya ba mu ikon gyarawa ya kuma tsare mu da yi wa mazajen mu rashin mutunci da rashin kunya,wanda ke fuskantan cin mutuncin da na miji a gidan Auran su,Allah na sane da ku,yi ta kai kukan ki ga Ubangijin da baya bacci,da sannu zai yi mi ki mafita na Alkhairi,Allah ka tsare mu daga sharrin shedan sannan ka kara mana lafiya da zaman lafiya me daure wa).


Bude baki yayi da niyar yin magana,wayan ta ya fara kara alamun kira na shigowa,da sauri ta dauke wayan daga kusa da shi,ganin me kiran nata ne ya sanya ta saurin fadawa daki,da kallon mamaki ya bi bayan ta,haka kawai zuciyar shi ta gaza nutsuwa Saida ya tashi ya bi bayan ta,tare da tsayawa a jikin kofa,abinda be taba mata ba a rayuwar sa sai yau,ji yayi tana fadin "yi hakuri abu ne ya ɗan sha kai na, Abdoul ke neman batan rai,ta dan ja tsaki sannan ta cigaba aikin banza mutun ba sisi ba sai iyayin tsiya,send the address right away yanzu zan watsa ruwa na taho", da haka ta kashe wayar tare da fadawa toilet tana me kananun wakokin ta,cikin sanda Abdoul ya shigo cikin dakin tare da ɗaukan wayan nata da ke kan gado,lucky him be riga ya shiga key ba sau hakan ya bashi daman shiga in box din ta da ke babu security,a take kuwa ga message ya shiga daga number da aka yi saving da "My love"da uban emojis a gaba,wani irin jirin zaune ne ya kama shi,ba tare da ya bude message ɗin ba yayi appearing a saman Address ne na Yamir hotel da ke nan garin Bauchi tare da room number a kasa,sai ya daura da kiyi sauri Baby na yau a mugun matse nake,da sauri ya rintse idanun shi tare da kife wayar akan gado,jin motsin ta ya sanya shi saurin miƙewa tare da barin dakin,yana jin kirjin shi nayi masa nauyi ya kasa yarda da abinda idanuwan shi suka gane masa,cikin sauri ita kuwa ya shirya tare da tsantsara uban ado sannan ta dauko wayar ta da jakar ta tare da fitowa,a parlor ta tarar da shi zaune ya hade kai da cinya ya rasa me ke masa dadi,ba tare da damuwa da halin da ya ke ciki ba,tace "to Ababan Khairi mu kam mun wuce,na san da kyar in dawo da wuri ka san sha'anin taro,ku kwanta kawai abun ku zan dauki spear key in na dawo zan bude ba sai na tada ka ba"be iya ce da ita komai ba,ta sanya kai tare da ficewa daga parlorn tana tsotan sweet a bakin ta,don yayi kamshi kafin ta isa,banda uban kanshi babu abinda ta ke zuba wa,babu wanda zai kalle ta ya zata mata wani ce,duba da irin dammamnum suturan da ke jikin ta,dauka ma za ka yi,irin zaurawan nan ne masu zaman kan su,wanda su ka ba wa lahira baya.


Tallah!!Tallah!!Tallah!!!!


Ina Mata? Ina yangayu? Ina amare harma damasu jego? To duk Ku biyoni kusha lbr🎤kamshi empire sunxo muku d ingantattaun turarukan wuta, na kalolin itatuwa😊 akwai turaren gida, akwai na wanka, akwai na wanki, akwai na mopping dana wardrobe🥰 muna da turaren kabbasa Wanda KO kin wanke kayanki sunanan👌akwai sirrintaccen turaren tsugunno Wanda KO toilet Kika shiga Wanda y shiga abayanki sai yaji. Akamshi empire zaku sami hadaddun humrori masu launi d kamshi kala kala, akwai kalolin kulacca d ingantattun mayukan gashi💃 bafa iya nan muka tsaya ba muna hada sourvinire na fita kunyar bakinku👌babban abin farin cikin muna d online classes damuke koyar d turaruka akan farashi me sauki. Kedai kulla kawance d kamshi empire ta wannan lambar 07053717605 KO adireshinmu no 13 biuroad Badarawa Kaduna sai kunzo🤝


Nan kasan parlor ɗin ya zube tare da rike kirjin shi setin zuciyar shi da ya ke ji kamar zai fado,ya shiga sakin wata wawiyar kuka me hade da ihu,kuka ya ke bil hakki kamar ran shi na shirin fita,bakin shi na maimata kalman Inalilahi wa ina ilahi raju'un,ya rasa yarda da abinda ya gani,yau da wani ne ya sanar mi shi yana ji sai yayi karan mutumin court, Kareematu matar da ya ke Bala'in so da kauna,uwar yaran shi,duniyar shi kuma matar rufin asirin sa,matar da ya ke rokan Allah ya bar su tare har a Aljanna wai ita ce yau ta ke kokarin aikata zina da auran sa har tana wa wani saving da My love,nan ta ke ya kuma fasa wani irin ihun kuka,wanda sai da ya taso da Khairi daga baccin da suke yi ita da yan uwan ta,da sauri ta fito kai ko dan kwali babu ta fada jikin Abban nata tare da fashe wa da wani irin kuka itama,domin duk abinda zai sanya Abban ta kuka irin wanann to babban abu ne,don ko mutuwar Baban shi be yi kuka ba,ya dai yi kwalla.


Jin ta a jikin sa,tana kuka ya kara karyar masa da zuciya,a take ya kankame ta suka cigaba da rera kukan tare babu me lallashin wani,da kyar tayi na maza tace"Abba lafiya meye kake kuka haka,waye ya mutu?Ina Umma kuma?,jin abinda ta fada ne ya sanya zuciyar shi kara karye wa,wani baki zai bude yace da ita Umman ta ta tafi Hotel kwarton ta na can na jiran ta,ta je su yi Iskanci,"Abba don Allah kayi shiru ka fada mun waye ya mutu"ta kare tana rungume shi kam.


Tsagaita kukan na shi yayi tare da zato ta daga jikin sa,ya shiga goge mata hawayen fuskan ta,murmushi dauke a kan fuskan sa,yace"don't cry Khairi na,babu wanda ya mutu Umman ku ce suka samu dan hatsari amman babu abinda ma ya same ta,so ki kwantar da hankalin ki"ya fadi yana shafa bayan ta don ganin yanda take kokarin firgita da jin ya ce Umman su tayi hatsari.


"Maza ta shi ki koma gurin Kannan ki,ki kula da su,yanzu zan je in dauko ta,zan kule ku ta baya sai na tafi da key ɗin make sure ki koma bacci,kin ji ko"kai ta gyada masa tare da goge masa hawaye tace"Abba ka daina kukan nan in sha Allah babu abinda zai samu Umman mu",kan ta ya shafa sannan ya dauki key ɗin Machine ɗin shi da ya karbo daga gurin gyara jiya,don be ma yi niyan gyarawa ba ashe da rabon zai masa amfani,Saida ya tabbatar ta shiga daki ta kwanta,sannan ya fito daga gidan tare da rufe gidan ya hau kan titi,idanun shi har biyu biyu ya ke gani,banda sunan Allah babu abinda ya ke kira,domin a daidai wannan lokacin Ubangijin kawai ya fi buƙata, addu'a ya ke Allah ya sa mafarki ya ke ba gaskiya ba,ko Allah ya sa sharri ake son hada mata,domin har yanzu ya gaza yarda da wai cewa Matar shi ne ta tafi Hotel haduwa da wani daban can,


Da taimakon Allah,ya samu ya iso Yamir hotel da ke nan cikin garin Bauchi a unguwar GRA bayan makarantar Dolphin Maria College,ko da ya shigo harabar hotel ɗin motoci ne cike kala kala,na alfarma domin babban sabon hotel ne mostly masu kuɗi ke yawan kama sa,cike da jan ƙafafuwan shi da suka yi masa mugun sanyi ya samu ya shiga cikin hotel ɗin, hawayen da ke kokarin zubo masa ya ke ta kokarin ganin ya maida su,a Reception ya tsaya,inda Receptionist ɗin hotel ɗin da ke sanye cikin uniform ɗin suka zuba mi shi idanu,don gani kamar ba a cikin hayyacin shi ya ke ba.


"Abdoul!kamar kai na ke gani a Hotel ɗin ga,lafiya me ka zo nema cikin daran nan?,jin ambatan sunan shi da aka yi ne ya sanya shi dagowa,Abokin shi Sani ya gani sanye da kayan ma'aikata,Aminin shi ne sosai,and ya san yana aiki a Hotel amman be taba dauka a nan Hotel ɗin ya ke aiki ba,ganin shi ne ya ɗan sanya shi jin dama dama,sauri ya ja shi gefe tare da shiga rokan shi kan ya ba shi spear key ɗin dakin da ya gani a cikin text,Saida aka kai ruwa rana sosai sannan ya samu ya yarda ya bashi key in ba tare da kowa ya sani ba domin yin hakan ya saɓa wa dokon aikin su,amman ganin Aminin shi ke nema kuma ya ce da shi it's urgent ya sanya ya bashi,yana me bin shi da addu'ar Allah ya sa lafiya.


A bakin kofar ya tsaya,jikin shi na karkarwa domin har ga Allah har taron bude dakin ma ya ke ji, addu'a ya shiga yi,duk wanda ta zo bakin shi,yana kaɗaita ubangijin shi tare da rokon shi ya kawo mi shi komai cikin sauki, Addu'a ya ke Allah ya ba shi ikon Mallakan zuciyar shi,domin baya son aikata abinda zai zo ya zama ana danasani daga karshe,a karshe dai Shahada yayi tare da sanya key ya bude dakin idanun shi da zuciyar shi na yi masa nauyi,cikin kiran sunan Allah ya kutsa cikin dakin da sauri ya kuma rintse idanun shi,zuciyar shi yana kokarin tarwatse wa sakamakon ihu da furucin da ya ji Kareematu na fada da suka sauka a cikin kunnan sa,fadi take "wayyooooo Allah na My love dadin ka daban ne,duk duniya wlhy ban ga wanda ya kware a sarrafa mace a gado irin ka ba,ka haɗu,ka fi wancan Wawan mijin nawa,kai Wlhy ka fi duk sauran mazan da nake harka da suuuuuuuu"


Wawan jiri ne ya dibe shi da sauri yayi baya zai fadi, Allah yayi taimako ya fada jikin kofa wanda ya sanya shi buga bayan sa,duk da karan da yayi making gurin faduwar hakan be sanya sun lura da shigowar shi ba,harkan gaban su ka kai,ganin hakan ya sanya shi fusata amman bakin shi be bar ambaton sunan Allah ba,domin duk wace ya kama matar shi ta aure tana zina a kan idon shi,in be kashe ta ba shi zai iya kashe kanshi.


Toilet ɗin dakin ya fada tare da ciki ruwa a bucket,ba tare da wata wata ba ya fito,tass ruwan nan ya watsa musu,a zabure ya sauka a kan ta tare da kokarin kare jikin su,domin yanda suka ji saukan ruwan nan ko ba a fada ba wani ne ya shigo ya kama su.


Cikin kuka Kareematu ta ji muryan Abdoul na fadin"Kareema matata ta sunnn"sai ya fashe da kuka.


A zabure ta mike tana me maimata kalman "Inalilahi wa ina ilahi raju'un,baban Khairat me ka zo yi nan,waya ce maka ina nan,don Allah tsaya ka ji nayi maka bayani",ta kare tana sauko wa daga kan gadon hankali ta a matukar tashe,hannu ya nuna mata alaman ta daka ta,sannan ya goge hawayen idanun Shi


"Allah kai ne sheda,Ni ba mazina ci bane,Allah kar ka hukunta yara na da laifin Mahaifiyar su, Kareematu wlhy da ko daga sama za a fada mun za ki yi wanann mummunan abun ,ai rantse harda Qur'ani ba za ki iya ba,ashe Ni kika maida Wawa,Kareematu me na yi Miki,don Allah ne na rage ki da shi,ko don jarabawa ta fada mun???da kin san kin gaji da zama da Ni ai da kin fada mun na sauwake Miki cikin sauki,da duk ba ta kai mu ga haka ba,kin san illan abinda kika yi a musulunci kuwa?hawaye ya share wanann ya ce yanzu da da su Khairat muka zo ki a da bakin yin musu bayani,nan ya juya ya kalli Bashir da ya boye kan shi cikin bargo,"yanzu Kareematu don girman Allah da me wannan ya fi ni?ko ban fada ba na san kana da iyalai kuma kana da yara,ka ji tsoron ranar haduwar ka da me sama,kuma ka sanya a ranka Zina bashi ce tunda kayi da matata ta sunna sai an yi da na ka matar"kalla Bashir be ce ba banda bari da ya ke ta faman yi,da sauri Kareematu ta nufo shi"kar ki kuskura ki taba Ni da Najasar wani tattare da ke,ki shiga banɗaki kiyi wankan tsarki , sannan ki zo ki sanya kayan ki mu koma gida yaran ki na jiran ki"da farko gaza yarda tayi da abinda ya ce domin a yanda ya kaman tan nan duka take jira daga gare shi ko kuma Saki Amman sai ta ji kamar ya ce ta shirya su tafi gida to wani gidan ko gidan iyayen ta ya ke nufi,Saida ya maimaita mata sannan tafi saurin fadawa toilet a gaggauce tayi wanka ,tun cikin bandakin ta sanya kayan ta tare da fito wa kan ta a kasa,"Allah Ubangiji ya shirya ka sannan ban yafe maka Amanar aure da ka ci ba,in kuma Amana gaskiya ce za ta ci ka,wuce mu tafi muna kara yin dare",simi simi ta bi bayan shi ba tare da tsayawa daukar jakar ta ba.......





Bare with the typing Errors 🥺 pls ban riga nayi editing ba,and wlhy cikin rashin lafiya na yi typing ɗin nan,ku sanya Ni a addu'a don Allah mura me hade da zazzaɓi ke damu na🥺🥺🥺 ga kuma kurji ya fito mun a ido screen ɗin ma ba da kyau na ke gani ba,Allah ya bani lafiya tare da sauran al'ummar musulmai baki daya😭


    In na ga ruwan comments kuma za ku ga ruwan updates da wuri wuri ma😸


   Da yardar Allah in na ji dama dama za ku ji Ni zuwa Friday.


   Ina yi wa kowa fatan Alkhairi .


Ina masu sha'awar shiga Adashen online,inda za a rike miki Amanar kudi,ba tare da runto ko Ojoro ba,inda za ki zuba ki kuma kwashi kudaden ki, cikin kwanciyar hankali da yardar Allah,ba tare da wata matsala ko tashin hankali ba,


Akwai Matan da sam kudi be cika zama musu a hannu ba,da kin samu sharp an kashe su,someone like me🥺lol,to yar uwa ta shiga Adashe a nan ne,zaki tara kudin ki hankali kwance,


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L7ai2fYGh4UAIK9MhC9awJ


Kindly ki shiga cikin group in nan,2500 weekly,I can assume you Bara ki samu any disappointment ko Damfara ko wani rikici ba, 


For more information,chat her up via:


       08149541182

Sai mun ji ku🙌😍

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


Wannan page ɗin sadaukar wa ne a gare ku


Hajara Ibrahim shu'aib(Kawata)

Mummyn Nasmah

Ayshourt (my dear)

Anty Binta(Kwalliya Roman jaɓa)

Babyn baby

Maman Ramadan 

A'isha Muhammad

Oum Ramlah


Ina godia da kaunar ku a gare ni🫶🏻❤️


..........


My What's app group link


https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


08100046388


******************


Tallah! Tallah!! Tallah!!


Ina uwar da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌 


...........

Page forty nine 


************


***********Nadeeya


Around karfe 12 na dare ta farka da tsananin ciwon kai,a hankali ta samu ta bude idanun ta tare da bin dakin da ta ke kwance da kallo,ko kadan hankalin ta be bata ma ta san da mutum kwance a gefen ta ba,dakin ta ke ta bi da kallo trying so hard ta tuno duk abinda ya faru da ita amman ta kasa,duk iya nisan tunani tayi Amman daga inda Sen ya ce a dauke ta daga gidan sa,a nan tunanin na ta ya tsaya,ta dai san ta tuna sanda aka kai ta asibiti ta farka ta gan ta da chain,amman tun ranar da Azzalumin Doc Bashir ɗin nan ya sama mata wani alurai me zafi shike nan kuma ba ta kuma sanin waye ita ba sai bayan farfaɗowar ta ta gan ta a kwance akan gadon asibiti,duk yanda ta so jin wani abu daga bakin staffs ɗin asibitin ba ta samu jin komai daga bakin su ba,dan juyin da Mama tayi ne wanda ya yi sanadiyar hannun Mama ya shafi cinyar ta,a garin bacci ya sanya ta sakin wani gigitattciyar ihun tsoro,a firgice Mama ta farka daga baccin da ya dauke ta,tare da mikewa zaune zuciyar ta na tsinke wa,domin a iya tunanin ta lafiya lau ta kwanta kusa da Nadeeyar da ta tabbatar tayi nisan bacci,don Saida ta shafe ta da Azkars din bacci tukun na ma ta kwanta.


Cikin rudewa ta samu ta kunna switch ɗin hasken dakin,a take kuwa haske ya baiyana a dakin,domin har yanzu Nadeeya ihu take tana kuka kamar wanda ake shirin zare wa rai,bayyanar hasken dakin yayi daidai da shigowar Nameer hankali a matukar tashe domin ko takalmi babu a kafafun shi,ihun kukan ta ne da ya soma ji kamar a mafarki,jin karfin shi ya ganar da shi ba mafarki ya ke ba da gaske ne Pookie ke wanann kuken da ihun cikin dare haka,shigowar shi cikin dakin yayi daidai da lokacin da Mama ta riko Nadeeyar tana me kokarin sanya ta cikin jikin ta,domin ta lallashe ta tare da mata tofin addu'oin,a yayin da Nadeeya ta sanya iya kan force ɗin ta tare da tunkuɗe Mama,wanda har yayi sanadiyar kusan bugewar ta,da katakon gado,da sauri Nameer ya je ya taro ta tare da sauke ajiyar zuciya ganin babu abinda ya same ta.


Kamo hannun Nadeeya yayi a hankali tare da kallon ta yanda take ta kuka tana ihu kamar wanda haukar nata ya dawo mata"Listen to me Pookie,you are gonna be fine,just try to hold your self together okay!!na san You have been through enough,but by Allah komai zai zamo tarihi,am here now and forever will be there for you okay"ya kare kamar zai yi kuka.


Fincike hannun ta tayi,cike da mugun masifa da tsiwa tace"Back offffff!!you little dog 🐶 stay away from me or I will make sure to ruin your dirty life forever,na san Daddy ne ya aiko ka ka kashe Ni ko???why can't you guys just let me be ne pls?why can't I live my life cikin farin ciki kamar kowa ne, ain't you ashamed of taking orders from that mugun mutumin,hmmm kune ba ku san waye shi ba,amman wlhy am ready to fight back now,ba zan taba barin ku cutar da Ni ba"tana kare wa ta mike tare da ficewa daga dakin da mugun gudu,daga Mama har Nameer mutuwar zaune da tsaye suka yi,duk duniya babu muryan da ya ke kaunar ji da sauraro kamar na Nadeeya Amman yau da ta budi bakin ta sai ya ji kamar wuta ta watsa masa a jiki da kunann sa,ba karamin kaduwa da tashi hankalin shi yayi ba,ya kuma mugun shiga firgici da tsoron jin furucin ta,a Bayyane ya furta"Inalilahi wa ina ilahi raju'un kar dai da gaske Pookie ta manta Ni,bata san ni ba,Na shiga uku!!shine kalman da ya furta yana jin kamar duniya tana kokarin zuwa karshe.


"Ka tsaya surutai Babana ai yanzu ba lokacin haka bane,yi maza ka taro yarinyar nan kar ta fita ta hau titi cikin daran nan wani mugun abu ya same ta,don Allah bi bayan ta,bari na sanya hijabi na biyo ku",kamar wanda ya suma Saida ya ji maganar Mama a kunnan shi ne,yayi saurin zaburar da shi tare da saurin bin ta yana me kunna wutan parlorn, addu'a ya ke a ran shi Allah ya sa ba tunanin barin gidan nan bane ya zo ran ta, Inalilahi wa ina ilahi raju'un in ta fita wani abu ya same ta,ya ce wa yan uwan ta me?to taya ma zai iya rayuwa babu ita?duk da ma Allah ya taimaka shi da kan sa ke rufe gidan kafin ya kwanta ya san ba za ta iya fita ba domin keys na gurin shi,ya sani this will be so new to her but be dauka za ta manta shi ba,this is the actual first time da suka hadu face to face with to hope of za ta gane shi ta san shi waye,sannan ya zauna ya bata labarin Sirrin da ya dade yana kunshe da shi a ran shi,amman daga kalaman ta ya fahimci kamar bata ma san su ba,"Ya Allah ka sa Pookie firgici ne ya sanya ta fadin haka ba wai mantawa da Ni tayi ba"ya kare kamar zai yi kuka.


Jin motsin ana taba gate ne tare da yunkurin son a bude shi,ya sanya shi nufan waje da sauri,tsaye ya ganta cikin short night wears ɗin da ke jikin ta,da ya ɗan wuce mata cinya kadan,kan ta ko dan kwali babu,lallausan suman kanta da ya sauka har shoulder line ɗin ta a bayyane,kafafu ko takalmi babu,ya sanya shi saurin sauke ajiyar zuciyar,da sauri ya nufe ta,tare da taba ta"don't you dare touch me again with this your dirty hands!Nawa ya biya ka??Na wa ya baka ka kashe masa Ni?i promise to double the amount don Allah just open the damn gate and let me go,na yi alkawarin barin kasar nan am even ready to change my identity just to let you out of trouble,I promise you babu wanda zai san Nadeeya Audu Waziri na raye,but you Are not gaining anything by killing me"ta kare tana kuka,hannu ya sanya tare da saurin rufe mata baki da tafin hannun sa,"Shhhhh"ya fada calmly,yayi daidai da fitowar Mama"Baba na ka sa me ta ina?hope bata yi trying harming kan ta ba dai ko?"a tare duk suka juyo tare da zuba wa Mama idanu har ta karaso inda suke tsaye,gaba daya tarar da su tayi idanun su yayi jawur,hakan ya sanya ta ce wa"sakar mata baki,mu koma cikin gida, it's late already kar mu tashi hankalin Makota mu hana musu bacci",da sauri Nadeeya ta noke kafada"Am not going back inside this house,wai don Allah su waye ku ne ma tukun na?and a ina nake ina ne nan?me kuma za ku mun?don Allah kar ku kashe ni,wlhh ko nawa wancan mugun ya ba ku Ni me iya kara muku ne me i just want to be far away from him"ta kare tana durkusa wa nan gurin tare da sakin kuka me tsuma zuciya,ta kasa yarda wai Uban ta mahaifi mutumin da ta dauki duk wani so da kaunar duniya ta daura mi shi,mutumin da ta ke wa kallon duk duniya babu ya shi,shine duniyar ta ta kasa yarda har yau wai shi ke farautar rayuwar ta,ya ke neman ganin bayan ta,domin ya sanya ta yin shiru don gudun tonuwar asirin shi a duniya.


Tsungunawa nan kasa Mama tayi tare da rungumo ta,ta shiga shafa mata baya"yi shiru Nadeeya and ki kwantar da hankalin ki babu me niyar cutar da ke a cikin mu,ki tashi mu shiga ciki don Allah ba wani isasshen lafiya gare ki ba,i promise to explain everything in details to you,kin ji ko",dagowa tayi da runannun idanun ta tare da kallon Mama"and how do you think I will believe you,bayan Malam bahaushe na cewa wai Kama bayi da mugu ne ko miye,me i can't recall the saying kuma", murmushi Mama tayi sannan tace"cewa ake wai Mugu bayi da kama,but i want you to look straight into my eyes and tell me nayi kama da wanda zan cutar da ke?am a mother my self,A mother of 3 children ma self with 5 grandchildren,wannan da kike gani tsaye he is my second born,so me zan yi gaining in na cutar da ke,am just like a mother to you,domin ina da yarinya Bara ta wuce ki ba,and duk zaman ki da mu ba mu cutar da ke ba why sai yanzu da kika dawo senses ɗin ki ne za mu cutar da ke?Tashi kin ji,mu shiga ciki and talk this out kamar yanda Uwa da yar ta suke magana", haka nan Nadeeya ta ji wani sanyin dadi a zuciyar ta har ta kai ta da sauke nannauyan ajiyar zuciya,domin ba karya maganganun Mama sun kwanta mata a cikin ran ta,hakan kuma ya sa ba tare da musu ba ta tashi tare da riko hannun Maman"let's go in Baba na it's late already"Mama tace suna nufan cikin gidan.


Nan fa suka yada zango a parlor da kan ta Mama ta dago ruwa tare da bai wa Nadeeya ta sha,ba musu kuwa ta karbi ruwan tare da sha,sannan Mama ta zauna tana me riko hannun ta"My dear I want you to look at us and tell me ba ki tuna komai game da mu ba,kin san mu?kin gane wannan" ta nuna Nameer da ke tsaye jikin bango kan shi na kasa.


Kai Nadeeya ta shiga girgiza wa sanan sannan tace"ban gane ku ba,all abinda na san zan iya tunawa shine Ubana Mahaifi na da yayi silan zuwa na duniya,yana kokarin salwantar da rayuwa ta,tare da lakaba mun cutar haukan dole,har ta kai ga an kai Ni asibitin Mahukunta,from the time da wani wicked Doc ya fara mun injection ban kuma tuna komai ba"


Murmushi Mama tayi,sanann tace "Allah sarki,kin ga wancan da ke tsaye,shine wanda ya kawo ki gidan nan a lokacin da ya kawo ki kuma hauka kike tuburan....nan Mama ta kwashe labarin komai ta sanar wa Nadeeya daga farko har karshe.


Kuka sosai Nadeeya ke yi,a rayuwa ba ta taba sanin akwai mutane irin su Mama da Nameer ba,a yanda duniyar nan ta zamo yanzu,naka ma sai ya zama dole kake taimakon shi balle ace ka dauko bare daga wani guri da baka ma san waye shi ba,ka tsaya a kan shi tare da maida matsalan shi na ka,har ka yi sanadiyar nema mishi lafiya,don ganin ya cigaba da rayuwar shi kamar kowa,tabbas samun irin su sai an tona,a take wata irin kunya ta lulube ta tuno irin bakaken maganganun da ta fada musu,a take kuwa ta shiga neman yafiyar su,da sauri Mama ta tsare ta tana me fada mata ko kadan ba su ji haushi ba,hasali ma duk wanda ya ke matsayin ta zai iya yin abinda ya fi haka,ta ci kuka sosai na bakin ciki da farin ciki,domin ace wanda kake wa kallon mahaifi shi ya zamo silan shigan ka cikin wani hali,sai wanda ba ku hada komai ba sai musulunci wai shi ya zamo silan dawowar hasken rayuwar ka,haka Allah ke yin abin shi wato sai ya haɗa ka da mutumin da ba ka sani ba,yayi silan taimakon ka a rayuwa,a halin yanzu babu abinda ta ke bukata da ya wuce ta gan ta a jikin Hajiya she want to cry her heart out to her,tana son sanar da ita abubuwa da yawa da bata sani ba game da Sen,saidai kafin nan akwai abu guda da take son isar wa wanda ya zamo mata dole ta je garin Bauchi.


Nan ta shiga gode musu bisa dawainiyar da suka yi da ita,tare da yi musu addu'a na Alkhairi, yanda take jin Hajiya na yi wa Sen a duk sanda ya kyautata mata,sannan ta shiga rokon su with pleading hands kan tana son zuwa Bauchi cikin daran nan,da kyar Mama ta kwantar mata da hankali tare da lallashin ta domin kuka ta saka musu,ta ke sanar da ita zuwa Bauchi bare yu cikin daran nan ba,ta bari zuwa a kwana biyu kan nan ta kuma warware wa domin Doc yayi warning ɗin su kan suyi avoiding mata stress,sam ta ce bata san zance ba,da kyar da maganganu masu dadi Mama ta shawo kan ta,kan ta bari to zuwa gobe sai su kai ta Bauchin,in ta matsa yau sai su ga kamar ta gaji da zama da su ne,haka dai aka samu ta yadda,Mama ta bata magungunan ta nan cikin lallaba wa kamar wata baby Mama ta samu bacci ya dauke ta, sannan ta rufe mata kofa ta dawo parlor ta zauna.


"Baba na,don Allah make sure gobe early in the morning kayi mana booking ɗin train to Abuja,daga nan sai kayi mana booking flight daga Abuja zuwa Bauchi,don mu samu yarinyar nan ta ga family ɗin ta,ita ma ko hankalin ta zai kwanta"a hankali Nameer ya sauko tare da zuwa ya zauna kusa da Mama kan shi ya kwanta a cinyar ta,tare da sanya hannun shi ya rungumo duka cinyoyin ta da karfi,tana kokarin magana ne,ta ji damshi na bin jikin ta,a rude ta ce"Baba na lafiyar ka kuwa?ko dai baka da lafiya ne kamar hawaye na ke jin zubar su a jiki na",ai be san time ɗin da ya fashe da kuka ba,a rude ta dago da face ɗin shi, hawaye ta gani daya na bin daya"Inalilahi Babana wani abun aka ma ka???


Cikin muryan kuka ya ce "Mama!Mama!!why why haka za ta faru da ni,shike nan Mama zan rasa ta,Mama shike nan tafiya za ta yi ta bar ni?a rude Mama ta ke kallon shi don ba fahimtar inda zantukan na shi ya dosa ta ke ba.


"This pain started the first time I set my eyes on her,and I tried so hard to hold it back and lived with it for so long!!I usually know almost exactly how I feel,but the problem is that I just can't tell anyone about it,Mama believe me when I say this,since the very first day I laid my eyes on her, my feelings grew stronger by each day,and I try my best to erase her out of my mind wallah,but I just don't know if this is love,or just an infatuation!Mama I don't know maybe my emotions are getting the best of me ,but I tried all my best to hide this from myself and the entire world including the people living with me,I tried so hard to be strong and try to move forward with my life,but each time I look at her i used to find her so innocent,cute,sweet har ta kai ga i couldn't take my eyes and mind off her!!the more I try to let her out of my mind,the more I find myself devoured in her thoughts,Mama it makes my heart beat faster and slower at the same time by just hearing her name being called by someone!Wallahi am tried of all this pretending and I cannot hold my feelings to myself any longer ,Mama I am Completely and Madly In Love With NADEEYA RILWANU AUDU WAZIRI!!!And har yanzu wlhy Mama ban san how when or where na fara son ta ba,but abinda na sani is i just can't live without her,don Allah Mama don't let her go away from me I cannot stand losing her,I love her so much 🥺 kin ji Mama ki ce mata kar ta tafi don Allah"ya kare har yanzu kukan ya ke yana jijiga legs ɗin Mama pleading with her Kar ta bar Pookie ta tafi kan his life will be boring as hell in har babu ita a ciki.


Idanu Mama ta zuba mi shi tana mamakin irin Wannan al'amari na Nameer,ikon Allah rabon da ta ga Nameer yayi kuka irin haka ai ta mance,bata jin ko mutuwar Raa'isaa ya zubda irin wanann hawayen,dan murmushi tayi tare da girgiza kan ta,wato ya gama duk wani dan waken zagayen sa ya furta sirrin ruhin sa,kan shi ta shiga shafa wa a hankali sannan tace"Amman Baba na sai na ji kuma na ga kamar tausayin yarinyar nan kake ji,to miye abun zama kana kukan banza kuma,sauki ya zo mata dole ta tafi abun ta Bara ta yi ta zama da mu har abada ba,Ni da nake shirin nema wa Mujaheed Auran ta"


"Mama wai waye ya ce tausayin ta nake ji ne?i swear to you with Allahu subhanahu wata'ala son Nadeeya na ke yi,wlhy Mama da kin kuskura nema wa Mujaheed Auran ta da kuwa mutuwa zan yi,dago wa yayi sannan ya cigaba,wai Mama ba ki jin an ce abinda babba ya hango yaro be iya hangowa,i thought wlhh kin fahimci since na kamu da soyayyar Nadeeya,Ni dai Mama pls help me out,don Allah kar in rasa rai na ko dan little Angel ita"me Mama za ta yi ban da dariya,wato yaron ta ya fada tarkon kauna,wayyo kuruci dangin hauka,"Baba na ke nan ban da abin ka ai tun ranar da ka kawo mun Nadeeya gidan nan da suna ka taimake ta,na ke mata kallon Matar da za ka aura kuma suruka a gare ni,ba karamin dadi na ji ba domin it's been long da na ga kana rawar kai akan mace haka,tun daga wannan ranar na dauki son duniya na daura mata,domin ganin kana kaunar ta kai ma,kallon ka kawai na ke yi da kake ta wakar tausayi tausayi,daman wanann ranar na ke jira da za ka fada son da kake mata da bakin ka"


"Ni dai Mama tunda kin gano Ni don Allah kar ki bari ta tafi ta bar Ni,wlhy Mama jin ta nake kamar bugun zuciya ta"zame kan sa tayi daga cinyar ta "ka ci gidan ku Baba na,wai yau ina kunyar jinin Fulanin ka ya ke ne,da bakin ka kake zaiyano wanna zance",be san sanda murmushi ya suɓuce masa ba,wato ko za a kashe shi,shi kan shi be san ya aka yi ya shiga zaiyano irin wannan zantukan wa Mama ba,shi dai abinda na sani kawai yana son Nadeeya and Baya son rabuwa da ita,da kyar Mama ta samu ta shawo kan shi,kan yayi hakuri in sha Allah Nadeeya rabon shi ce,so ya kwantar da hankalin shi su kai ta gida,don hankalin yan uwan ta su kwanta,don ace ana neman shekara an rasa yarinya kila har ma sun cire tsammani ga me da ita,haka dai suka shiga hira inda ya yi ta zaiyano wa Mama irin tulin kauna da soyayyar da ya ke wa Nadeeya,tun Mama na mamakin sa har abin ya koma bata dariya,wai soyayya me maida mutum mahaukacin dole,wani abu sai kuruciya,kuruci dangin hauka,wannan ranar ba su suka kwanta bacci ba sai around 1:30 a hakan ma ita ta kora shi ya kwanta, Saida tayi nafilolin ta,ta kuma dade tana roka mishi Alkhairi a gurin Allah sannan ta kwanta bacci.


Sassafe kuwa ta sanya Zaliha hada musu kaya,kafin suka hada breakfast,da kyar suka samu ta sha ruwan sha yi,domin ita fa tunda ta ji labarin Kaduna take hankalin ta ya karkata zuwa Bauchi kuma, around 11:30 suka gama komai,don Nameer ma ba kwanciyar hankali ne tattare da shi ba balle ya samu ya ci abincin sosai,har train station Mujaheed ya kai su yana musu Allah ya kiyaye hanya,Saida ya ga tashin su sannan ya samu ya dawo gida,cikin yardar Allah ba tare da bata lokaci ba kuwa suka shigo garin Abuja,sallah suka yi tare da neman abinda za su ci,sannan suka shiga jiran tashin jirgin su,Nadeeya ji take kamar tayi tsuntsunwa ta gan ta a Azare a dakin Hajiya.


Cikin hukunci na Allah sai around Magrib jirgin su yayi landing a Abubakar tafawa balle wa Airport da ke nan cikin garin Bauchi,nan ko suka shiga fitowa wa jiki duk a gajiye ba kamar Mama da kafafu suka ishe ta da ciwo,a take Habeeb da ya yi kusan 15 mints Yana jiran isowar su,ya nufo su fuska dauke da fara'a,Saida suka gaisa sannan ya taya Nameer kwasan kayan su zuwa matar shi,shi ya ke tuko su, inda suna tafe suna hira banda Nadeeya da ta zuba wa window ido tana me kallon waje,idanun Nameer na kan ta,ta front mirror ya ke kallon duk motsin da ta ke yi,a kai a kai ya kan ga ta ja tsaki ciki ciki tare da goge kwalan da ke zubowa daga cikin idanun ta,wanda zai iya ce wa kasa controlling tears ɗin tayi,don duk yanda ta so rike su kar su zubo sai zuba suke kan yi,ko ba a fada ba ya san memories ke fada mata da ke sosa Mata zuciya har ta kai ta ga zubda hawaye,shi ko jin hawayen nata ya ke har cikin ran sa,idanu kawai ya lumshe tare da kwantawa a seat ɗin motar domin baya jin zai iya juran cigaba da kallon hawaye na zuba a idanun ta.


Nan gidan da ya kama na Fadaman Mada suka ya da zango,inda Habeeb ya sa a share a kuma wanke ko ina babu abinda gidan ke yi sai kamshi turarukan wuta,masu dadin kamshi,ba za ka dubi gidan ka dauka ma gidan maza bane don yanda ko ina ya ke tsaf tsaf ka dau akwai mace a ciki,a parlor suka bar su,inda aka shirya Dinning table da kayan abinci kala kala,ko ba a fada masa ba ya san wannan aikin Muhibba ce matar Habeeb,kai ya girgiza tare da yi masa godiya,nan ya nuna wa Mama daki su shiga su watsa ruwa su ci abinci,bari su je su dawo.


Ko da suka fita Saje suka biya,Nameer ya yo take away ɗin sandwich da ice cream sai box of pizza 🍕,sannan suka biya ta Bauchi club suka siyo gassasun kaji,suna tafe suna hira da Habeeb har suka iso gida,tarar da su Mama ya yi a parlor,nan ya mika mata kaza da Drinks da ruwan da ya siyo,while Nadeeya ya bata box ɗin pizza da ice cream tare da sandwich din da ya siyo domin ta,ba karamin mamaki ta sha ba,domin abubuwan da ta ke Bala'in so ya kawo mata, godia tayi sannan ta wuce da su daki,for once tun farfaɗo wan ta sai yau ta tsinci kan ta da yin murmushi,a nutse ta zauna ta shiga cin kayan dadin ta tana kuma yaba kirki irin na bayin Allahn nan.


Around 8 bayan ya dawo daga masallaci sun yi sallama da Habeeb ya koma gida,ya tarar da Nadeeya tsaye a jikin bangon parlon, idanu ya zuba mata,wanda har Saida ya sanya ta jin kunya ta shiga kokarin barin gurin


"Wait pls!yace da ita a hankali,do you need something??ya tambaye ta da turanci domin ganin ba wani fahimtar Hausan sosai ta ke ba,dan sosa kai tayi sannan tace"actually amm if you won't I want to borrow your car for some mints ina da important abinda nake son yi,and unfortunately I don't have my car keys with me so if you don't mind can you give me your keys?ta tambaya tana narai narai da idanu,"wannan yarinya ba dai shagwaba ba"shine abinda ya fada a cikin zuciyar shi,"why are you going cikin daran nan,hope all is well dai ko??? murmushi ta mi shi me tafiyar da zuciya sanna tace"all is well the car key pls"numfashi ya sauke sannan yace"kin ga dai dare yayi yanzu ko,if you cannot wait har zuwa gobe kafin ki fitan to i cannot let you leave this house all alone,go get your hijab ki zo mu tafi",


Baki ta cuno sannan tace "Ni fa bani da wani hijabs"dariya ta so ba shi,ya dai danne tare da cewa"ki je ki ce wa Mama wai na ce ta baki Hijab ki sanya za mu unguwa"ba tare da kula shi ba ta shige daki gurin Maman,jim kadan sai ga ta kuwa ta fito sanye da Maroon hijab har kasa,irin wanda ake daure igiyar shi ta baya,da ke fara ce sai hijab ɗin ya haska ta,"all set can we go??tace da shi tana checking ɗin kan ta out,da hannu yayi mata alama da ta zo,ba musu kuwa ta zo,matsowa yayi daf da ita tare da ce mata ta juya, juyawan tayi inda ya sanya hannu tare da kamo igiyar hijab ɗin ya daure mata shi"yauwa ko ke fa yanzu kika zama ready,go and seat in the car ga Ni nan fitowa okay"kai ga gyada mi shi tare da barin Parlor ɗin,inda shi kuma ya wuce dakin Mama tare da sanar da ita,zai kai Pookie wani guri,tambayar shi ina zai kai ta tayi,inda ya ce shima be riga ya sani ba tukun na, addu'ar tsare hanya tayi musu,sannan ta ce da shi su dawo da wuri su kuma kula saboda kiyaye shiga matsala,da haka ya fice daga cikin dakin yana me tabbatar mata ba ra su yi dare ba.


Ko da ya shiga Mota tana nan zaune tayi shiru tare da zuba uban tagumi,i can say she is lost in her on thought,clapping hands ɗin shi yayi sannan yace"What is my Pookie thinking about?ya yi maganar yana tsare ta da idanu,a hankali ta maimaita kalman"my Pookie"irin abun ya bata mamaki,sai ya maze be kuma ce wa komai ba ya kunna motar,"off to where??ya tambaya a daidai lokacin da suka hau kan titi,"GRA" tace da shi cikin sanyin murya,be kuma ce mata komai ba ita ma bata ce da shi komai ba,ila da hannu da ta ke nuna mi shi hanya,har suka iso gidan Alh Salisu,tun a bakin gate aka sanar da su kan Alh Salisu is out of town amman zuwa jibi zai dawo,ba haka ta so ba amman babu yanda ta iya haka suka juyo,"Gida za mu koma ko kuma ina? Ya tambaye ta yana kallon titi,"No pls Dan yi gaba pls ka kaini gidan Big Daddy tunda ban samu small Dad ba,na san she kan for sure yana gida"nan dai ta kwatan ta masa gidan Alh Kabiru,da kwatancen ta har suka samu isowa,aka bude musu gate,bayan sun tambaya securities ɗin gidan ko yana ciki,suka tabbatar masa da yana gida,Saida yayi parking sannan yace mata"make sure to take care of yourself inside okay,I will be here waiting for you"smile kawai tayi mishi tare da bude murfin motan ta fito,tare da nufan cikin gidan zuciyar ta na bugawa.


A main parlor suka ci karo da daya daga cikin yan aikin gidan,gaisawa suka yi sannan ta tambayi ina mutanan gidan,nan yarinyar ta sanar da ita Alh na study room ɗin while Hajiya da yaran su fita biki, godiya ta mata,sannan ta nufi Study room ɗin shi,da ke ba bakuwa ba ce a gidan,so ba inda ba ta sani ba,Saida tayi knocking ya ce ta shigo sannan ta bude kofar cikin siririyar murya ta ce"Excuse me", ai kamar a mafarki Alh Kabiru ya ji saukan muryan ta a kunnan sa ta sanya shi saurin mike wa,in dai har ba yaudaran shi kunnuwan shi ke yi ba tabbas muryan Nadeeya ya ji yanzun nan, ai da sauri ya juyo tsaye kuwa ya gan ta jikin kofa, bakin shi har bari ya ke yayi pointing ɗin ta da finger ɗin shi"Princess ke ce,ko kuma gizau idanu na suke mun",da sauri ta karasa shiga cikin study room ɗin tare da fadawa jikin shi,sai ta saki kuka"Big Daddy am the one,Ni ce am still alive"a matukar mamake ya ke kallon ta da kyar ya samu ya ciro ta daga jikin shi,shi duk tsoro ne ma ya kama shi,a garin yaya,yaushe ta warke?and yaushe ta dawo gari?daman can wai tana raye,amman da ke ya kware a munafurci sai ya daki table ɗin gurin"i knew it!daman na san babu abinda zai same ki princess na san dole za ki dawo safe and sound,Kai Allah thank you for protecting my princess,Nadeeya how have you been,and for all this while ina kike,ba karamin daga mana hankali kika yi ba"


"Dad it's a long story actually I have been through a lot,but I managed to fix it,and I am here standing in front of you cikin koshin lafiya ta"..."seat down my love let's talk"ba musu kuwa ta ja ta zauna,shima zama yayi sannan yace"My daughter you are looking good,tell me ya aka yi kika bar hospital ɗin su Doc Bashir and wa ya sace ki,me kuma suka miki,wlhh in har wani ya cutar da ke ki fada mun sai na ga bayan ko ma waye shi",dadi ta ji sosai ko banza ta san Alh Kabiru zai tsaya mata a ko wani hali.


"Big Daddy it's a long story but to cut it short,wani ne ya taimake ni tare da kai Ni can gidan su a nan suka yi ta kula da Ni har Allah yayi na samu lafiya", numfashi ya sauke sannan yace"gaskiya sun yi abinda ya kamata a yaba musu,kin je gida gurin Daddy ɗin ki ne??ya san da dawowan ki"da sauri murmushin face in ta ya gushe a take ta sauya fuska"Big Daddy I hate that man with passion I regret having him as a Daddy,and wlhy I swear to you sai nayi komai with my power ganin na ruguza shi"wani irin farin ciki ne ya lullube zuciyar Alh Kabiru, perfect opportunity in da ya ke jira Allah ya kawo masa har gida,lokaci yayi da zai rama cin mutuncin da Alh Rilwanu yayi mi shi.


Zama ya gyara sannan yace"actually at first Nima nayi misunderstanding ɗin ki saboda misleading ɗin mu da Sen ya ringa yi,yana koke koken karya da wofi, trying ya wanke kan sa,babu yanda ban yi da shi kan a bi komai a hankali,domin dagewa yayi kan cewa sai ya kashe ki,ganin yanda idanun shi suka rufe ne ya sanya na ba shi shawarar kawai a ce hauka kika yi,akan in an Kai ki asibiti after 3 days na faki ido na zo na fito da ke,amamn da ke mutumin nan mugu ne,da ya gano plan din na ya sanya aka sace ni,tun daga lokacin na fahimci tabbas ba sharri kike mi shi ba,and cikin hayyacin ki kike,domin tabbas akwai abinda ya aikata a gare ki me muni da ya sanya ki yi mi shi haka,tabbas Nadeeya uban ki ya kasance mugun uban da ko a labari na dade ban ji irin shi ba,and your husband contribute a lot a ruining life ɗin ki, domin ba karamin bincike nayi ba,bayan babu ke na gano ashe abinda ya aikata a gare ki ke nan,ai sai ya fashe da kuka,ohhh Allah duniya wato kullum bakin shi na ambaton Allah ashe mugu ne ban sani ba,Nadeeya Ni kai na da kike gani na Uban ki yayi mun abinda ba zai mantu mun ba,and wlhy da na san haka ya ke kuma haka zai cutar da ke da na hada shi da hukuma since day one"shiru yayi domin ita kan ta Nadeeyar kuka ta ke,Saida suka sha kukan su me isar su sannan ya cigaba"Ni yanzu tsoro na ma a taya irin wannan mugun mutumin ya zamo shi zai mulke mu,wani irin shugaba za a yi ke nan?cikin kuka tace"Big Daddy,wlhy har yanzu na kasa yarda wai Daddy na shi ya kashe Mom ita saboda samun cikar burin shi,ace saboda neman duniya Daddy ya ba da Mom ita,hade da Womb ina wanan wani irin son duniya ne", "hmmm ai my daughter babu amfanin tone tone,babu yanda kika iya uban ki ne,amman wlhy da na san Sen kungiyar asiri ya ke ciki da da kaina zan sanar wa Hajiya tun wuri a nema mi shi mafita,amman wannan ai mu ya zubar wa da mutunci ya bar miki abun fada"


"Daddy wlhy ba zan taba barin Sen ya ji dadin rayuwar shi ba,yanda ya tarwatsa nawa rayuwar dole na ruguza ta shi,and wlhy abinda ya ke gudu sai ya faru sai duk duniya sun san abinda ya aika ta mun"wani irin murmushin samun nasara Alh Kabiru yayi sannan yace"Princess maganar gaskiya Alh Rilwanu be kyauta ba,ya bani mamaki da kunya wlhy,and ni dai ina bayan ki,domin cutar da aka miki a baya ma rashin sani ne,yanda kika dauke Ni uba haka kike yarinya a gare ni,so ki bar komai a hannu na na san yanda zan bullo wa lamarin nan,in sha Allah cikin daran nan zan kira lawyer na a samu a shigar da karan shi court kin ga ta nan ne,duniya za su san waye shi tare da yi masa tofin Allah tsine,domin sorry to say Uban ki is a monster not a human being,and irin su ba su yi deserving rayuwa a duniya ba,so kar ki damu in sha Allah kukan ki ya zo karshe,mu je a zuba miki abinci ki ci,sannan ki shiga Kiyi wanka ki huta ko"...."A'a Dad na gode sauri na ke zan koma,bana son ya san ina nan,gudun kar ya kuma attempting kashe Ni,don na ga alamun idanun shi sun rufe by fire by force so ya ke sai ya yi nasara,and nayi naam da advice in Ka,maka shi a court of law sune za su yi masa hukunci daidai da abinda ya aikata sannan mutane za su san waye shi,Ni dai pls ko magana ta koma mi shi an gan Ni a nan,ka ce da shi karya ne ban zo ba"...."haba daman ta ya ma zan ce kin zo,tunda ba za ki zauna a nan ba You should take care okay,ga card ina nan we will stay in touch okay!God bless you my dear and ki kwantar da hankalin ki domin karshen zaluncin Rilwanu ya zo,just stay In a low key to avoid cutar da ke da zai yi"nan suka yi sallama yana jaddada mata kan kar ta kuskura tayi maganar nan da kowa,sannan ta kula da kan ta,har down stairs suka fito,a take ya bata cash in 5 mil wai ko za ta yi wani abun da shi,tunda komai na ta baya tare da ita amman tace ya bar shi kawai bata bukata,haka dai ya matsa mata Saida ta karba,suka rabu ta fito,tare da barin Kabiru zuciyar shi cike da farin ciki,domin ji ya ke kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha don murna,haka zalika a hanyar su ta komawa gida ma babu wanda ya kula wani a cikin su,deep down Nameer ya ji dadi don at first ya dau wayo ta yi mi shi ya kawo ta Bara ta fito ba ganin irin time in da ta bata,Saida suka zo bacci ne ta ke cewa Mama tana son in ba damuwa gobe ta je Azare gurin Granny inta domin ta san hankalin ta ba karamin ta shi yayi da batan ta ba,Mama a take ta amince mata,nan ta sanar wa Nameer kan ya shirya gobe su kai Nadeeya Azare kamar yanda ta bukata,at first hankalin shi ya tashi nan Mama ta shiga kwantar masa da hankali tare da nuna mi shi ai daman Bara su cigaba da zama da ita na har abada ba,dole ta koma wa family inta,in ya so a can sa je su nemi Auran ta,gaba dayan su Are eager su ji labarin ta,Amman ganin ba ta ce da su komai ba ya sanya Mama cewa kar su matsa mata in ta ji tana son fada musu za ta sanar musu.


Kamar yanda Mama tace kuwa washegari tun safe Nameer ya je yayi full tank wa motar shi,a gurguje suka karya sannan suka yi wanka suka dauki hanya,wanan shine karon farkon su na zuwa garin Azare da ke ba wani kwana kwana bane hanya ce mikakkiya ya sanya Nameer be sha wahalar tuki ba,idanu Nadeeya ke bin garin da shi,tana me jin farin ciki yana ratsa ta,ta ko ta ina,sai yanzu ta ke jin kwanciyar hankali ya zo mata,domin ta san ta tsere wa Sen da mugun kaidin shi.


Da kwatancen da ta musu,suka samu isowa tangamimiyar gidan Hajiya Rakeeba,wanda duk a fadin Azare ba ma unguwar Matsango ba ka fin ka samu gida me kyan nata sai ka bude idanu ka duba,domin ba karamin kudade Sen ya narka gurin ganin an kera wa Mahaifiyar sa gida na bugawa a jarida ba.


Horn ya matsa a take gate man ya taso tare da wangale musu gate ɗin gidan,hancin motar shi Nameer ya shigar tare da yin parking a in da ya aka an tana da gurin aje motoci,ba tare da ta jira ya gama parking ba ta balle murfin motar tare da kwasa a 360 sai cikin gidan.


Ummi da fitowa ta ke nan daga kitchen hannun ta dauke da warmer shake da haddadiyar stew da ya ji kaji baja baja za ta kai kan Dinning table,suka ci karo da Nadeeya,a take kuwa warmer in ta fadi miyar ta zube nan kasa,"ya Salam wai waye haka sam ba nutsuwa kin shigo wa mutane gida ko....maganar ce ta makale mata a lokacin da tayi arba da Diyar dan uwan ta da suka fidda rai da samun ta ma,a tsaye a gaban ta"Hajiya!!Hajiya!!Hajiya!!na shiga uku fito Hajiya don Allah"Ummi ta ce tana zazzare idanu.


Idar wan ta daga Sallah ke nan,tana lazumi ,ta ji irin kiran da Ummu ke ta faman kwada mata,ai a tsorace ta fito hannun ta dauke da casbaha,"Kee ummi lafiyar ki kuwa,ko dai gamo da Aljanu kika yi ne" da hannu ta nuna mata Nadeeya da ke tsaye kusa da ita"Hajiya kin ga kamar Nadeeya na ke gani ko idona ke neman yaudara ta"


Tallah! Tallah!! Tallah!!!


Ina Mata? Ina yangayu? Ina amare harma damasu jego? To duk Ku biyoni kusha lbr🎤kamshi empire sunxo muku d ingantattaun turarukan wuta, na kalolin itatuwa😊 akwai turaren gida, akwai na wanka, akwai na wanki, akwai na mopping dana wardrobe🥰 muna da turaren kabbasa Wanda KO kin wanke kayanki sunanan👌akwai sirrintaccen turaren tsugunno Wanda KO toilet Kika shiga Wanda y shiga abayanki sai yaji. A kamshi empire zaku sami hadaddun humrori masu launi d kamshi kala kala, akwai kalolin kulacca d ingantattun mayukan gashi💃 bafa iya nan muka tsaya ba muna hada sourvinire na fita kunyar bakin ku👌babban abin farin cikin muna d online classes damuke koyar d turaruka akan farashi me sauki. Kedai kulla kawance d kamshi empire ta wannan lambar 07053717605 KO adireshinmu no 13 biuroad Badarawa Kaduna sai kunzo🤝


Kafin Hajiya ta kai ga bude bakin ta,sai ji tayi Nadeeya ta fado jikin ta,tare da rungume ta kam kam,bata san time in da ta fashe da kuka ba"Hajiyaaaaaaa ta",bakin Hajiya har yana bari"Nadeeya,ke ce ko mafarki na ke yi?...cikin kuka itama tace"Am the one Hajiya,ni ce nan Nadeeyar ki"ai da jin haka Hajiya ta kankame ta a jikin ta,kamar me shirin maida ta ciki"Nadeeya ashe ina da rabon kara ganin ki,ashe kina raye, tabbas an ce daman in da rai to akwai rabo,and ko sau daya kar bawa ya taba cire rai daga rahamar Allah,and na yarda babu bawan da zai daga hannu ya roki Ubangijin shi yana me kuka da kaskantar da kai, sannan ace Allah be amsa masa ba,na sani daman wlhy ko ba jima Allah zai amsa mun,tun can daman ban sanya a raina ba ki raye ba,na san duk daran dade wa za ki dawo gare mu,ko a mace ko a raye, Alhamdulilah ya rabil alamin da ka dawo mun da jikata gare Ni lafiyan ta kalau,Nadeeya duk dadewar nan,a ina kike?sannan kuma me kike yi,bani labarin me ya same ki"


Ta bude baki da niyar magana ke nan suka ji sallamar Mama,Ummu ce ta amsa mata,tare da kife ta da idanu wa domin ba su taba ganin fuskan ba.


"Baiwar Allah lafiya daga ina?da sauri Nadeeya ta nufo su sannan tace Small Mom tare muka zo da ita,mutuniyar kirki ce,and su suka taimake ni"jin abinda ta fada ne,ya sanya Hajiya matsowa kusa da su,"Sannu da zuwa shigo daga ciki,ga gurin zama,Ummi kawo mata abinci da abun sha"fuska dauke da murmushi Mama ta zauna 


"Hajiya na san da maganganu dauke a bakin ku,tare da tarin tambayoyi,amman in ba za ku damu ba ina son gabatar da sallah first domin ya same mu,muna kan abun hawa"...."haba haba babu komai mu shiga daga ciki Kiyi sallan, Ummu make sure kin shirya mata abincin da Nadeeya kan su fito"Hajiya Rakeeba tace tana me nuna wa Mama hanyar dakin ta,duk da bata san ta ba,ganin ta tare da jikar ta,hakan ya tabbatar mata da cewa mata ce me mutunci,and duk da ance mugu be da gama,daga yanayin ta da shigar ta be nuna alamun tana da nufin cutar da su ba,"Hajiya akwai yaro na tare muka zo yana waje ko za a kai mishi ruwan alola?.."Nadeeya saidai a bar ta wato tare kike da baki,shine kika yi shigowar ki tare da barin su waje,maza ibi ruwan alola ki kai mishi, akwai masallaci kofar gida ya shiga yayi Sallah sai ya shigo ya ci abinci,ai ba a bar shi waje shi kadai ba"ba tare da Nadeeya ta ce komai ba ta dau ruwa tare da yin waje don kai wa Nameer,da ta fara jin haushin nattacen kallon da ya ke bin ta da shi.


Saida Mama suka ida Sallah,Hajiya ta sanya Ummi kawo musu abinci da abun sha,Saida suka dan taba abincin sannan aka shiga gaigaisawa da kyau,ba tare da boye komai ba Mama ta baiwa Hajiya labarin tun farkon da Nameer ya kawo ta gidan ta,sanann da irin zaman da suka yi da Nadeeya a karshe ta rufe da ba wa Hajiya hakuri bisa daga musu hankali da suka yi,da rashin neman dagin ta da ba su yi ba,a nan Mama ta karbi laifin ta,saidai ta ce tayi hakan ne domin kare yarinyar daga fadawa halaka don Nameer ya sanar da ita tsohon Mijin ta ne ya biya Doc kan yana son ya mata aluran mutuwa,inda aka yi dace Nameer ya ji ya kuma taimake ta tare da tsiratar da ita, Allah yayi kwanan ta na gaba,in da ta daura da "to Hajiya abin ki da yaro sai ya rasa wa zai yarda da kuma,tunda miji kam ai duniya bayan iyayen ka in kai dace babu wanda zai so ka kamar shi,sannan shine zai zamo kariya tare da bangon tsayuwar ka,to ganin yanda shi da kan shi ke son ganin bayan ta bayan ya mata Saki har uku ya sanya ya ji ina babu kuma sauran wanda zai yarda da shi,bayan duba da irin Abinda ke faruwa tsakanin ta da Mahaifin ta ya sanya shi dauke ta zuwa Kaduna,amman muna neman afuwan daga muku hankali da muka yi,wlhy Hajiya Baba na ba da nufin cutar da yarinyar ku ya dauke ta ba,sannan be yi da nufin daga muku hankali ko sanya ku cikin wani hali ba,and wlhh tun ranar da na fara ganin Nadeeya na rike ta matsayin diya na so ta tare da kaunar ta,na kuma tsaya kai da fata har Saida na ga ta samu lafiya,Amman Hajiya kuyi hakuri da halin kuncin da kuka shiga sanadiyar ɓacewar ta"


"Haba Hajiya,sannu ku da kokari,bani ma da bakin godiya,wlhy in har ba mu gode muku ba to ba mu da bakin aibata ku,tabbas kun yi abinda ke wahalar samuwa a wanann duniyar ta mu,ba ku san ta ba,baku san asalin ta ba,amman kuka dauke ta,kuka maida ta na ku,bayan Mijin ta ke farautar rayuwar ta,ba karamin Mamaki na ji ba jin wai Afzaal ke biyan kudi a kashe Nadeeya,ikon Allah to daman can Ummi Ni kam ba Auran so da kauna suka yi da yaron nan ba?ko daman can Auran hadi ne?and shi Abul baiti ɗin yana uwar miye har ake farautar rayuwar diyar shi haka?


"Hajiya wlhy soyayya sosai suka ci kafin Aure,a iya sani na babu wani dole a lamarin Auran su,iya abinda na sani shine rashin kyan gani da lalacewar da na ga Nadeeya tayi bayan Auran ta wanda ya tsaya mun a rai"..."tabbas na ga haka Nima sam kwanciyar hankali da kiban da ake na bayan Aure yarinyar nan babu shi tattare da ita,abun ya bani mamaki sosai don Ni farko ma dauka nayi rabo aka samu,kin san Ni tun farko daman yaron ba wai ya kwanta mun bane,to ganin tace tana so,kuma uban ta ya fi ta nuna zumudi ya sanya na bi su da addu'a kawai,domin bincike wannan hana wa yayi akan cewa ya gama komai,Amman duk wanda ya gan ta kam zai fahimci babu kwanciyar hankalin da ta samu a rayuwar Auran ta"


"Hajiya ina kike expecting zan samu kwanciyar hankali daman,bayan wanda nake wa kallon rayuwa ta abun alfahari na sannan silan zuwa na duniya shi ya zamo silan bakin ciki na,mutumin da nake so fiye da komai a rayuwa shi ya zamo sanadin tarwatsewar rayuwa ta,Hajiya a yaya daman zan yi rayuwar farin ciki a gidan Aure na bayan Ubana Mahaifi shi ya zamo mun Kishiya a gurin Mijin da nake so da kauna"gaba daya idanu suka zuba mata domin sam ba su fahimci yanda zantukan nan nata ya dosa ba,a taya Uban ta zai zamo mata kishiya har ya zamo silan rugujewar farin cikin ta,anya ta san me take fadi kuwa?


"Ke Nadeeya bana son sakarcin banza,wannan wasu irin kalamai ne kike jifan Mahaifin ki da su,ko har yanzu cutar haukan ke damun ki,kin taba ganin yanda Uba ya zamo kishiyar yarinyar sa,a yanda uban ki ke kaunar ki bana tunanin zai iya barin wani abun cutar wa ya ma zo kusa da ke"..."Hajiya Ni kai na da ba da idona na gani ba ba zan taba yarda ba,tabbas labari na cike ya ke da abubuwan mamaki and babu shakka a nawa labarin Ubana ne ya zamo kishiya ta,and a yanzu ba sai anjima ba zan baki labarin abun da ya faru tun farko,bazan boye miki komai ba,saidai ina jin tsoron halin da za ku shiga bayan gama sauraron labarin da zan baku,saidai Hajiya ina so ki sani,babu karya ko sharri cikin labarin da zan baku"ta kare tana share hawaye zuciyar ta nayi mata nauyin fitowan wannan labari daga bakin ta,zama Hajiya ta gyara sanann tace "muna sauraran ki",domin ba karamin matsuwa tayi akan son jin abinda ke boye tsakanin Sen da Nadeeya (kamar yanda na san Readers kuma duk kun matsu ku san wanann mummunan sirrin da ke lullube a boye🥺🥺).


"Baba na ta shi mu ba su guri,domin suna bukatar privacy don da alama wannan serious discussion za suyi,wanda ya shafi family members kadai,ka ga dole muyi respecting privacy in su"yana kokarin mikewa Hajiya tayi saurin tsayar da shi"Sam Hajiya in kika mun haka ba ki mun adalci ba,ashe ma in har zan ce ku fita to na cika yar Adam butulu,ai an riga da an zama daya,babu wani abun boye wa a tsakanin mu,kun dauke ta ba tare da sanin waye ita ba,don haka ina neman alfarman ku zauna ta ba mu labarin ta tare da ku,domin yanzu mu da ku daya ne wlhy,and na san ko kun fita ba kwanciyar hankali za ku samu ba,karshe shedan ya shiga ya bata mana zumunta"Mama dai ba ta so ba domin daga gani wannan labari na Nadeeya babban sirri ne,"muna sauraran ki"dan kallon Hajiya tayi da ido alaman ta fadi komai gaban su Mama babu damuwa?Idanu ta lumshe mata alamun eh ta fada babu komai,zama ta gyara sannan ta shiga ba da labarin rayuwar ta tun bayan komawar ta gidan Sen......


"Suna na kamar yanda na fada muku,kuma kuka riga kuka sani Nadeeya Rilwanu Audu Waziri,Hajiya zan dauko labari na daga tushe saboda su ina so su fahimce Ni sosai,sannan sai ku fada mun shin ina da laifin zagin mahaifina da nake yi ko bani da laifi,Na kasance yarinya daya tilo a gurin Sen Rilwanu Audu Waziri,asalin mu yan Garin Azare ne,wannan da kuke gani ita ce Grandma ita wato Mahaifiyar Daddy na,sunan ta Hajiya Rakeeba Ali Abbas,kamar yanda na taso na ji a labari Mijin ta ya rasu Mal Audu Waziri tare da Amaryan sa wace suke kira da Gwoggo,Baba na shine babba a gidan su,wannan kuma sunan ta Anty Ummi Salma ita ce Auta a dakin su Daddy na ina kiran ta da Small Mom kasancewar ita ta zamo mun tamkar uwa,tunda Ni na taso ban san dadin nawa mahaifiyar ba,a yanda Daddy ya fada mun randa aka haife ki Mommy ta late:Hajiya Bahiyya ta ce ga garin ku nan,domin an ce ko face ina bata gani ba balle ta san ya nake ta rasu,hawaye ta dan goge sannan ta cigaba,saidai ina fitowa duniya aka ce sak kamannin ta na dauko,in ka cire wasu abubuwan da na dauko na Dad ina,tun randa aka haife ni from Hospital direct gidan ta Hajiya ta wuce da Ni,Saida suka kai ruwa rana sosai da Daddy na kafin ya yarda Hajiya za ta rike ni a gurin ta.


Na taso cikin soyayya tausayi da gata na both dangin uba da kuma ubana,domin ba karamin so da kauna ta suke yi ba,Hajiya in kana son ganin bacin ran ta to ta ji kuka na,domin ko barna nayi ta hana a duke ni,hakan kuma be hana ta fara bani tarbiyyar da ya dace ba,ina shekaru uku a duniya lokacin har an fara shirin sanya ni a boko Daddy ya sanya borin be yarda na yi karatu nan Azare ba,zai dauke Ni mu koma Bauchi,babu yanda Hajiya bata yi ba don ganin ya bar mata ni amman sam Daddy yace be san zance ba!!a haka aka tattara mun komai na muka tafi akan zai na kawo ni gurin Hajiya duk in aka yi huta,saboda Nima kuka na saka mi shi kan bana son in tafi daga gidan ta.


Zan iya ce muku ban taba ganin yarinyar da ta samu gata irin tawa ba ,domin Hajiya kullum complain in ta da Daddy shine gatan da ya ke nuna mun yayi yawa,tana jin tsoron kar wataran a wayi gari babu shi,ko kuma babu rayuwar jin dadin da ya ke nuna kuma ya ke jiyar da ni,domin a rayuwa Ni na tashi da duk abinda na gani to kafin  na ce ina so ma Daddy zai sanya a kawo mun wannan abun,sam ban taso na san babu a rayuwa ta ba,a duk sanda Hajiya tayi irin wanann maganar ya kan yi dariya yace"Hajiya banda abun ki nawa Nadeeya ke?and a rayuwa in ban muku ba wa zan wa? Nadeeya ce rayuwa ta and akan ta nake neman kudi babu dare babu rana,domin tabbatar da rayuwar ta tayi kyau,sannan bana fatan a wayi gari Nadeeya ta ga abu ace na kasa yi mata shi Saisa a kullum nake kara nema don ganin farin cikin ta,yanda Mahifiyar ta bata mori kudin nan ba,ina son in jiyar da Nadeeya dadin da sai yara da yawa sun yi sha'awar kasancewa ita a duniyar nan"sam Hajiya bata jin dadin hakan amman babu yanda ta iya ne ya sanya ta zuba musu idanu, don gani take soyayyar da Rilwanu ke wa Nadeeya ya so yayi yawa,don a shirye yake ya bata da kowa akan ta.


Tabbas na zamo abun kwatance sannan topic in zantawa a garin Bauchin nan,kasancewa da irin so da kaunar da ke tsakani na da Daddy na,PRINCESS shine sunan da ya sanya ya ke kira na da shi, it's hardly ka ga ya kira ni da real name ina,wato bond ɗin da ke tsakani na da Dad ina bond ne me mugun karfi,we became so close to each other har wasu ke cewa saboda Ni ya ki kara Aure tun bayan mutuwar Mommy na,duk wani tattali da kula babu wanda ban samu a gurin daddy abinda uwa ke yi wa diyar ta Ni Daddy ke yi mun,kama daga wanka wankin kaya na,wanke gashi,kitso har lalle,abinci kuwa tare muke ci and Shi yake feeding ina har sai na koshi,sannan ya goya Ni a bayan shi yayi ta yawa har sai na yi bacci,sannan ya ke kwantar da ni akan gadon shi muke kwana sharing same pillows and blankets da shi,My Dad was just the super best Daddy in the whole world domin yar aiki wanann da kyar ya dauko Baba Falmata wanda ta zamo a gun ta na dan san wasu abubuwa.


A Sunshine International school nayi nursery and primary with secondary sch ina, Sunshine yana daya daga cikin best and most expensive school da ke nan cikin garin Bauchi,na taso cikin kudi domin Daddy baya mun shamaki da komai na shi, Motocin kai Ni school da dauko ni kawai sun fi 100 haka zalika School items ina,kullum cikin canza su nake and haka na taso bana using in Abu in ba designers ba.


Ba zan taba mantawa ba tun lokacin da na fara wayo nake yawan complain in ciwon ciki me tsanani wanda in ya tashi mun kwana muke ba muyi bacci ba,haka Daddy zai yi ta kuka yana lalaba Ni kamar karamin yaro,don shi haka yake ko ciwo na ji to shi sai ya fi Ni jin zafin sa,don akan haka ma na daina zuwa Islamiyya tun wani rana da aka yi general duka a class in mu,hannu na ya tashi Daddy ya ce kar na kuma zuwa ya cire ni za a nemi wani makarantan marasa mugun ta,tun ina tuna mi shi yana cewa ya sa a duba har ya watsar Nima na watsar.


I was around 9 aka yi admitting in mu a hospital Hajiya in ba za ki manta ba har Daddy ya ce da ke Appendix ke damu na za a yi mun operation a cire,not knowing Womb ina aka cire a wanann time in,da ke ina yarinya jiki na kuma na da kyau ban dau time ba na warke na cigaba da normal activities ɗina,Daddy was my best friend,don Baya bari na ina fita waje,ko anyi Hutu be cika bari na in zo Azare ko in je Kaduna ko Adamawa gurin sisters in sa ba,kullum a cewar shi the world was full of evil people so Yana tsoron wani abu ya same ni he cannot stand losing me domin a cewar shi ina tuno mishi da late mom ina wanda kuma haka ne,domin kama daga farin fata,yanayin hallitan fuskan mu,tsarin halittar jiki na duk nata ne,gashin kai ne kawai ta fini,so na taso rayuwa ta daga Daddy sai Falmata sai kuma Big and Small Daddies ina wanda suka kasance tight friend wa Daddy na wato Alh Kabiru da kuma Alh Salisu to da su ne ma Daddy ya kan bari in je gidan su,don ko na so making new friends a sch abun baya yuwa coz securities ne zagaye da ni ta ko ta ina,ko wani moves ina suna gani,bana mantawa akwai first yaron da ya fara cewa yana so na lokacin muna SS2 ba karamin duka securities in nan suka yi masa ba,Saida na tausaya masa,Allah yayi kwanan shi na gaba be mutu ba,tun daga nan na kara bakin jini kowa ya ja distance ɗin shi daga gare ni i become all alone,in har dad baya nan to ina daki ni kadai na,ko kuma Ni da waya na ina jin waka.


Babu wakar da in aka sake ban iya sa ba,inda za ku yi mamaki in na ce muku cikakkiyar Fatiha a matsayina na wace na ke amsa sunan muslma ban iya ba,yanda na ke son waka ya sanya duk wani music performance da za a yi wala  a nan gida Nigeria za a yi ko na yan outside countries to in sha Allahu babu fashi Daddy sai ya biya mana mun je wataran har da shi,at times kuma mu tafi da yaran Alh Kabiru domin Alh Salisu ba kasafai ya fiye barin diyar shi Zahra tana yawon kasashe ba.


Lokacin da na kai 15 years lokacin na gama Secondary school ba karamin grand party Daddy ya hada mun ba,inda na san class mates ina har gobe suna labarin partyn domin duk Bauchi ba a taba ganin party irin shi ba,duk wasu favourite musicians ina Saida ya dauko mun su a wanann party ɗin,am living a life that ko wace yarinya za ta so samu,domin Princess in da daddy ke kira na da shi ba iya a baki bane ya nuna wa duniya tabbas am a Princess domin sai abinda nake so ake yi mun.


Dan shiru tayi sanann ta saka kuka"Hajiya shakaru na 16 a duniya cikakken alola ban iya ba,haka ma Sallah,babu abinda na sani game da addini na,hakan kuma be taba damun Daddy ba,duk Randa na ji ina ra'ayin yin Sallah domin a gurin Baba Falmata da class mates ina sai kuma in na zo nan a nan nake koyi alola da salla wanda ya zamo kawai dungure nake yi don wlhh Fatiha wanann ba iya ta nayi ba,amman babu latest wakar da ban haddace a kai na ba, don at times Daddy ke taya ni haddar wakar ma, problem in farko da na fara fuskan ta,shine a matsayi na na mace sam bana Period don ko kadan ban san shi ba ma,Saida watarana na a sch aka yi mana topic in Puberty a nan ne hankali na ya tashi don an ce wasu matan at 10 11 ages ma suna fara wa Amman Ni I was around 13 that time kuma ko sau daya ban taba gani ba,bani da kawa balle nace za muyi sharing damuwa ta da ita,thank God that time Dad was so open to me so shi na je na fada wa hankali na a tashe,na ce mu je asibiti a duba ni,nan ya shiga kwantar mun da hankali akan ce wa kar in damu normal thing ne kila in na kuma girma zai zo,watakila kuma ina daya daga cikin special kind in Mata masu baiwa wanda ba sa period a rayuwar su,ya ce da ni in ko ina cikin su na ji dadi na,domin irin mu Are lucky a rayuwa babu mu babu wahala sannan irin mu rushing ake ana son Auran mu kuma sadakin mu daban ne,ya kare yana dariya,Nima abunku da kuriciya sai ban bawa rashin yin wani damuwa ba sai ma na shiga murna da farin ciki don ya ce mun babu komai cikin period in ma banda azaba.


Bayan gama Secondary sch ina ne ya nemo mun Admission a most expensive University da ke kasar Uk aka yi mun shiri kamar yar gidan shugaban kasa na tafi,bayan ya ja mun kunne nayi karatu banda soyayya domin Daddy na lura in dai akan neman boko ne  ko nawa zai kashe don Saida ya tambayan sch in ya yi mun na ce eh kafin aka kai ni,a kullum bayi da maganar da ya wuce,yana so na zama very successful a rayuwa nayi ilimi nayi kudi har ma na fishi domin yara na su ji dadi fiye da yanda ni na ji dadi, duk abu in dai ta shafi fannin sch to baya wasa da shi har mamaki ya ke bani,domin tunda nake Daddy be taba tambaya na kin yi sallah?Azumi kan ma Saida na kai 15 years kafin ya fara bari na ina yin full azumi don cewa ya ke ban kai matakin yin full ba,Salati Hajiya Rakeeba ta sanya tare da tafa hannu wa tana mamaki duk wannan abubuwan wai Rilwanu ke aiktasu,hawaye Nadeeya ta goge sannan ta cigaba"sai in na je gidan su Zahra Small Daddy ke saka mu a gaba musu salla to gurin na dan tsinta wasu abubuwan daga gurin ta na ibada sai kuma in na zo nan,amman babu wani Addu'a da na iya shi banda wanda ya zamo common ka kan ji shi a bakin mutane,haka Daddy ya sanya aka siya mun katon gida da motoci biyar a kasar Uk wai wanda zan fara zirga zirga da su,sannan ya cika mun account da kudi, kafin muka tafi da kan shi  ya kai Ni,inda yayi miki karya kan a hostel tare da yaran abokan sa za mu zauna duka,Hajiya at times ni da Kai na na kan yi mamakin,wai wani irin mahaukatan kudade ne Daddy ke da su haka?tun da nake da shi a rayuwa tun ina yarinya ban taba jin ko a wasa nace ina son abu ya ce bari to in na samu,ko yace yanzu kasuwa ta ɗan yi kasa kiyi hakuri zuwa next week, a'a shi Daddy highest nace ina son abu in ban samu within an hour ba to baya wuce 24 hours kuma wlhy kudaden shi kullum karuwa suke,inda mu kuma cin su muke kamar hauka.


Haka na fara University cikin gata domin ba a yin 3 weeks Daddy be zo duba Ni ba,Saida kowa ya san ni a Makarantar mu don yanda Daddy ke zuwa guri na wasu dauka ma suke Miji na ne ko Saurayi na domin sam baya boye soyayyar da ya ke mun,haka zalika nima ina kaunar shi with every blood in my body,duk wanda ya san mu ya san kamar hanta da jini muke ni da shi masu wuyan rabuwa,sai a lokacin ne na dan fara keeping friends inda nayi rashin dace na samu wanda su ma duniyar ne kawai a gaban su,nan muka cigaba da moran duniyar mu,Shedan na kaɗa mana ganga muka shiga zuwa club, Allah ya tsare nu ya kuma kare ni bana bin maza duk da irin offers in da nake samu kuwa kwata kwata na dau hakan as kauyanci,to ina ce mostly don kudi ake bin mazan ni kuma nawa Uban kama daga 1 mil har zuwa 100 in nace a take zai bani,haka ma drugs at first friends ina sun so jan ra'ayi na in Fara drugs Allah ya taimake ni ban yi ba,saidai dan dunguran sallan da na kan yi da yanzu kam duk na watsar,don da Ibadan tana burge Ni barin in na zo Azare in na ji Hajiya na karatu ko tana sallah na kan ji sha'awa amman lokaci guda na ji na tsana ma baki daya,haka rayuwa ta cigaba da tafiya cikin sauri ina cigaba da karatu na gashi Allah ya mun Sharp brain,ina daya daga cikin masu jan point a department ɗin mu, Rayuwa na cigaba da tafiya,ina dada girma kyau na na kara fitowa tare da dirin da Allah ya yi mun,ina kara rikidewa sak Mama na,maza na kara rushing a kai na amman duk bana ba su fuska saboda maganar Daddy.


Ko a nan ma am one of the talk about,cause ina daya daga cikin mutanan da ake gani da sabon abu in ya fito, iPhone tun daga kan na farko har zuwa na inda aka tsaya kafin na fara rashin lafiya babu wanda ban mallaka ba,haka zalika I watch daga series in farko har na karshe,Daddy yayi make sure ban yi lacking komai ba kamar yanda ya dau alkawari,tafiya ta cigaba da tafiya,inda na kasa keeping promise ɗin da nayi wa Daddy na akan ba zan yi soyayya ba sai right time ya zo,don i try so hard na ga ban kula mazan da ke rububina a kullum domin ko ba a fada ba na san ina daya daga cikin mata masu amsa sunan Kyau,don ina da kyau,ga wanka,ilimi da kuma aji,Addini na ne dai shiru babu abinda na sani a ciki.


Dan mumfasawa tayi sannan ta cigaba ba zan taba manta first love ina ba,Ahmad Sulaiman sunan shi and lecture ne a school in mu,shima dan Najeriya ne,saidai aiki ya kai shi Uk har ya koma zama a can,shine saurayi na farko da na fara and akan shi na san menene So,mun yi soyayya sosai da shi,domin mutum ne me hakuri tare da dubin kulawa,shi ya zamo mutum na biyu a rayuwa ta da na zama very free with,ko da aka yi hutu na ce zan koma gida, insisting yayi kan sai dai mu tafi tare,yana son ganin Daddy sannan ya sanar da shi so na ya ke in ya yarda nan da 3 months ya ke son Auran mu in ya so sai mu koma Uk tare na cigaba da karatu na,a take na yarda domin nima ina kaunar shi sosai.


Babban tashin hankalin da na fara fuskanta shine randa ya zo gida ganin Daddy na,lafiya lau muka gaisa yana ta tsokana ta,tare da fada mun ya kusa dauke ni daga gurin Daddy na daga yanzu zan koma his Princess not Daddy's Princess,ina ta dariya ya shige ciki domin Ahmad mutum ne me son tsokana da wasa,saidai tun fitowar shi daga parlorn Daddy direct gate ya nufa ba tare da ya ko kira Ni ba,Saida na fito na tambaya ake ce mun ya tafi,abun ya bani mamaki sosai don tun daga wannan ranar Ahmad be kara kira na ba,be sake ko da mun text message ba,I was so worried in na kira na baya dauka,karshe Saida na canza line na kira ya dauka,wanann ranar ba karamin kuka na sha ba saboda ganin ashe Number na ne baya son daga wa,shine na masa tas nace ya ba Ni mamaki ashe duk soyayyar da ya ke mun na karya ne,me nayi masa zai guje ni,Nan ya ce mun shi ban yi masa komai ba Uba na ne dai mutumin banza wanda baya tsoron mutuwa,shi ya gode wa Allah ma da be dade da sani na ba domin ko wani ya ji zai hada zuri'a da mu sai ya hana shi,don tarayya da Mahaifina ya haramta,domin tantirin dan iska ne,a take na ji raina ya ɓaci,na ji gaba daya soyayyar da nake masa ta fice tas a raina,domin a rayuwar nan duk wanda ya ce zai taba Daddy na a shirya nake na rabu da ko ma waye, domin kowa ya san Daddy na mutumin kirki ne,ba karamin zagin sa nayi ba sanann na ce da shi ta fi nono fari ya je can shine ɗan iska,daga wanann ranar na rabu da Ahmad Sulaiman,Daddy da kan shi ya zo ya same ni da maganar wai ganowa Alh Kabiru yayi Ahmad dan shaye shaye ne ashe shine ya ce ba zai bashi aure na ba shine ya zabi ya ci wa ubana mutunci,bakin ciki sosai na ji da ban wanke fuskan shi da mari ba,a haka Daddy ya ma canza mun Sch na koma United State of America nan ma wata makaranta me tsadar ya kuma sanya ni,duk don yin mance da Ahmad,nan na cigaba da karatu na,Samaruka suna nan kamar su kashe ni na ki ba su dama,a haka dai na samu wani Khaleed daga friendship muka koma soyayya, kyakkyawa ne sosai,kuma ya haɗa duk abin da ake nema a mijin aure,amman kallo daya Daddy ya ce wai shi sam be yi masa ba,abun ya bani mamaki,a haka dai muka cigaba da soyayya har ya kai yana son ganin Daddy don turowa,tarihi ne ya maimaita kan shi,don wanann karan kam ma,Khaleed akan ido na ya zage Mahifina tas tare da yi masa tofin Allah ya tsine,sanann yace na mance na taba sanin me kama da shi ma,nayi kuka kamar raina zai fita,don ba kukan rabuwa da shi ma nake ba kukan abubuwan da ya fadi kan Mahaifina ne,inda na ce ban yarda ba sai na shigar da kara court daddy ne ya hana ni,tun daga nan na watsar na cigaba da karatu na har na gama na dawo Nigeria bayan ya hada mun Graduation party na gani na fada.


Ko bayan dawowa na a daya daga cikin companies in Shi ya damka mun nake handling,haka na cigaba da rayuwa ta ina aiki na cikin kwanciyar hankali,nayi Samaruka kusan biyar bayan Khaleed wanda suka nuna suna son aure na amaman sam baya kare mana ta dadi,don da zagi da cin mutunci muke rabuwa,inda a karshe sai a bakin Daddy nake jin bada side in su,don daga ya ce daman can dan shaye shaye ne sai ya ce dan iska ne,karshe dai na watsar da hidimar mazan dai,don lokacin aka around 23 years har lokacin Daddy be sanya Lahadin aure ba.


Ba zan taba manta wa ba,na tashi a office ina hanyar dawowa gida mota na ta samu matsala,domin ni kadai na fito at times securities ɗin Daddy takura ni suke yi,fitowa nayi don ganin me ya samu motar,ga hadiri ya hadu sosai waya ta kuma ta mutu due to rashin charge,da na kira daddy yayi mun sending driver an zo an dauke Ni, kamar daga sama na ga wuce war motar shi,be fi mintuna da wuce wa ba kuma sai ga shi ya dawo,parking yayi a gaba na tare da sauke glass in motar,Masha Allah na furta domin arba da nayi da shi kyakkyawa ne na ajin farko,yana sanye da kananun kaya ga wata Black shade a idanun shi shigar da yayi ya kara fito da ainihin kyawun su,duk da kasancewar shi yana da duhun fata,babu abinda ya ke ban da kamshin turaruka masu dadi,daga ganin shi kun san irin yan gayun nan nan.


"Hey Damsel do you need some help"ya tambaya yana mun murmushi,Nima murmushin nayi nace"a'a my car just broke down but I can manage thank you"a nan dai yayi ta insisting tare da kananade Ni da dadin baki domin kallon farko da nayi masa na san tabbas zai yi dadin baki,domin irin matasan nan ne da ba su taking no as an answer,a haka ya yi ta ja na da baki tare da roko har sai da na yarda na hau motar shi ya dawo da ni gida,be tafi ba Saida ya matsa tare da karban number na ya ce da ni sunan sa Afzaal!!


Farko da mutunci muka fara kafin mu ka zama very fun of each other, Afzaal has been so calm and caring towards to me,da ya sanya ni fadawa soyayyar sa,ba tare bata lokaci ba muka shiga soyayya inda kullum nuna makale da juna,ina tsananin so da kaunar Afzaal domin zan iya ce wa duk cikin samarukan da nayi babu kamar shi,don daban ya ke ya haɗa tare da iya soyayya, kuma sam be da duhun kai a waye ya ke,randa Daddy ya fara ganin mu tare ba karamin kaduwa hankali na yayi ba,don ina mugun tsoron ya ce be yi masa ba,don wanda suka fi shi komai ma sun zo daddy ya ce baya son su balle Afzaal wanda ya kasance Maraya gaba da bayan sa bayi da kowa sai yan uwan nesa don yace mun shi kadai ne a gurin iyayen sa kafin su mutu,nayi mamaki kwarai inda kallo daya Daddy yayi masa ya ce ya kwanta masa a rai,muka cigaba da soyayyar mu don kusan kullum sai ya zo gida hira guri na,wataran Daddy da kan shi ya ke cewa mu shigo parlor har abun ci da sha ya ke sanya wa a kawo masa,mamaki be gama kashe Ni ba Saida ya je gaban Daddy kan yana son turowa don neman aure na actually a toilet na wuni ina zawayi saboda tsoro don in har aka maimata abinda ya faru a baya na hakura ba sai na yi aure ba kuma,domin bana jin zan kuma samun wanda nake so,wanda kuma ke so na kamar Afzaal ba,sai ko na ga ikon Allah domin shine mutum na farko da ya taba nema na ya zo gurin Daddy suka yi maganar Aure na,ya fito ya ce da ni Daddy ya ce ya turo an bashi ni,mamaki kusan kashe Ni yayi Hajiya domin ba karamin yabon Daddy na yayi ba,haka nayi ta murna na je har dakin Daddy na masa godiya,inda ya ce da ni tunda ina son shi ai shima babu abinda zai hana shi son shi.


Zan iya cewa akwai wata shakuwa da kyakkyawar alaka a tsakanin Ubana da kuma Miji na,don lokaci guda suka yi wani dinkewar ban mamaki,Daddy ya canza masa mota in da ya siya masa ƙatuwa kuma babbar mota me uban tsada,ya kuma ce da shi ya yafe masa komai shi ya dauki nauyin sa a bakin mu,don nan da 2 months aka saka Auran,ba karamin nutsuwa na samu na ganin irin kusancin da Daddy ya ke da shi da miji da zai aura,a haka har muka yi aure aka yi mun bikin gata,don babu abinda ba a yi ba a biki na,gida kato me dankaran kyau Daddy ya sanya aka gina mun,ina kuka ina komai aka tafi da ni gidan miji na da na matsu in Fara new life ina da shi,bayan su Small Mom sun watse an yi mun nasiha tare da sanar da ni duk abinda ya dace suka yi tafiyar su tare da bari na,daga Ni sai ni tun ina jiran shigowar shi har na fara jin bacci,ba shi ya shigo gida ba sai 11:30 har bacci ya fara dauka na,a take ya shiga creating excuses yana bani hakuri akan abune me mahimmanci ya taso,ban nuna fushi na ba saboda ban ga wani alaman abun zargi tattare da shi ba,wanann daran duk da kasancewar ni ba wasu friends garan ba sannan ban cika karance katancen books ba Amman a girman da na yin nan na san me ake kira da First night,ina jiran ya ce muyi salla kamar yanda na ji a labari sai gani nayi ya shiga cire kaya tare da fadawa toilet be dade ba ya fito tare da goge jikin sa,ya sanya kayan bacci tare da haurawa gado,"Na gaji sosai,ki samu ki yi wanka ki sanya something light ki zo ki kwanta Kiyi bacci ko ke ma za ki huta gajiya,good night"shine abinda ya fada mun,nayi mamaki sosai amman sai na mike nayi wankan tare da kwanciya a wanann ranar ko finger na be taba ba,Nima ban taba shi ba.


Hajiya in yanke miki story in nan short har na gama kwanakin Amarci na na koma aiki Afzaal ko kissing ina baya yi,kusa da ni in be zamo dole ba baya son zuwa,tun ina maida abun ba komai ba har abun ya zo ya fara damu na,kwanaki suka fara tafiya cikin sauri,wanann kula da tattalin da Afzaal ke nuna wa a kai na yanzu duk babu shi,kullum yana makale da waya yana chatting tare da phone call and na lura mostly da Daddyna suke yawan waya,don har cikin dare waya suke,sai ya ce mun business call suke da ke Daddy ya bashi share a business in Shi,abun tun ina jin dadi yanda ya dau Baba na da mahimmanci sai na zo kuma abun ya fara bani haushi,domin wani irin shakuwa ce a tsakanin su da tayi yawa,sam ba sa kwatan ta al'adan malam bahaushe,don Afzaal har a cinyar Daddy zama ya ke don yawan cin kullum yana gidan Daddy,zai hau cinyar shi ya zauna,ko ya kwantar da kai a kan cinyar shi baya kunyar rungumar Daddy a ko da yaushe,abun haushi ma at times har a baki daddy ke ba shi abinci,kwata kwata hakan baya mun dadi don ko ni zan iya cewa attention in da Afzaal ke samu gurin daddy ni bana samun shi,don ko cikin dare ya kira zai ce bari ya zo ya same shi,ko time in da na nuna bana jin dadin hakan sai Daddy ya hau ni da fada kan cewa in be so Afzaaal ba ya zai yi,ai dole ya taya Ni son shi tunda Ni ce kadai yarinyar shi,and yana jan shi jiki ne saboda kar ya wulakanta ni,haka na ja baki nayi shiru.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


Wannan page ɗin sadaukar wa ne a gare ku


Jamilatu Hamza(Girlfriend)

Abruk

Khoobsurat

Ayshoutu

Naman Annur

Khadijah Murtala

Hafsah Amarya


Ina godia da kaunar ku a gare ni🫶🏻❤️


..........


My What's app group link


https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


08100046388


******************


Tallah! Tallah!! Tallah!!


Ina uwar da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌 


...........

          Page Fifty 


************


   Numfashi Nadeeya ta sauke sannan ta cigaba"Watannin Auran mu na ta tafiya,inda gaba daya na soma lallacewa domin ni dai dadin aure da ake fada har yau ban san shi ba,duk wanda ya ganni zai dauka kishiya ke gallaza mun in da sam babu kishiya a labari na,sai dai Ubana ne ya ke neman zamo kishiya ta,don ni na kan ga kamar da gayya at times in na je gida sai ya na ce mun ai my son ya zo ya taho mun da kaza dazu Allah dai yayi mishi Albarka inda ni ko sweet baya riko mun in ya fita,da abun ya ishe ni ne na samu wata Aaafiya gurin aikin mu daya,shine ta bani shawaran ina wankan kananun kaya tare da koya mun yan wasu dabaru na mata,ai ko na gwada inda ko a jikin shi,don inda na lura Afzaaal fa aure na yayi amman bana gaban shi,domin na mance rabon da mu zauna guri daya da shi ma,kullum yana cikin yawon kasashe,abun da ya ishe Ni ne wata hudu da Auran mu,na sanya kuka,nace na gaji ya sake ni kawai,da kyar ya shawo kai na,tare da bani hakuri wai ayyuka ne suka masa yawa,raina ya ɓaci sosai don ba haka muka tsara rayuwar auran mu da shi ba,na ce da shi har wani aiki ne,zai sanya shi juya mun baya irin haka,wanann ko Auran dole muka yi sai haka,na gaji gaskiya,yayi ta  lallashi na tare da bani baki,sai a wanann daran ne na samu muka kwana gado daya da shi,har na samu yayi romancing ina shima yi yake kamar ana watsa mishi wuta a jikin shi,muna tsaka da haka wayar shi tayi ringing ko ba a fada ba na san Daddy ne,inda a take ya zame ya bar Ni nan kwance,wanann daran nayi kuka sosai kamar raina zai fita,na rasa gane dalilin wanann shegen kusancin da ke a tsakanin Uba na da Miji na,har tambayar kai na nake,wai shin suna manta su Hausa Fulani ne?,ko ba su san kalman kunya da ke tsakanin surukai ba?Mata ma ba su cika son juna suna Surukan juna ba,sai su Maza,domin mun riga mun sani in dai Surkanta ka ta,hada ka da mutum to tabbas akwai wanann kara da kunya a tsakanin ku,ban da ma yanzu da abu ya zo da zamani an dan samu cigaba,tun daga nan na watsar da lamuran shi na cire shi a rai na cigaba da rayuwa ta kawai,sai ranar da don kan shi in ya ji ra'ayi ya ja Ni da romance,ban mancewa akwai randa na sanya darun na gaji da romance in sai yayi abinda ya kada mun hankali duk da kasancewar ba wani ilimin addini gare Ni ba amman na san tabbas babu kyau Anal sex,a yayin da Afzaaal ya nufi baya na a haukace ta ko wani hali yana bukatar hanyar shiga,hankali na ya tashi inda muka yi dambe sosai kafin Allah ya bani sa'ar fasa masa kai,na gudu,ina mamakin wanann abu,domin nuna mun yayi tunda sex nake bukata in har ba ta baya ba bazai yi ba,kwana guda muna wasan buya da shi,Daddy baya nan yayi tafiya,dawowar shi ko zama be yi ba ya yo gida na,i was happy Babana ya zo for the first time and tunda shi kadai gare ni ina da niyar fada masa abinda Afzaal yayi mun,amman sai na gan su tare da Afzaal in ran shi a matukar ɓace,abinda tun tasowa na be taba faruwa ba sai wanann ranar domin Daddy Saida ya kwada mun maruka har guda uku,wai akan me zan fidda jini a jikin Afzaal koma me ya mun be dace na daga hannu na a kan shi ba,wanann shine wai a dake ka a kuma hana ka kuka,nayi kuka sosai ya kuma sanya ni tsungunawa har kasa na bashi hakuri.


Tun daga nan Afzaaal ya kara  fita a raina domin na tsani munafuki,domin munafurcin yayi mun,haka na dauki lamuran su na watsar,don ban san wanda zan kai wa kuka na ba,Uban da ya kamata ya zamo bango na me share mun hawaye shi ne ya zamo silan zuban su,nan na cigaba da aiki na don ba addini na sani can ba balle na ce wai zan tashi tsaye tare da mika wa Allah lamura na,tabbas in nace bana jin zafin yanda Afzaal ke rawan kafa akan Daddy nayi karya,to amman babu yanda na iya,domin da akwai yanda zan yi na wargaza wannan shakuwa da soyayyar da suke cewa don Ni suke wa juna da na wargaza shi,domin har ga Allah har ma da na ji dama mace ya auro ya kawo cikin gidan nan in san eh da gaske Kishiyar gare ni,domin a halin da nake ciki na kasa banbance wa shin Daddy UBANA NE KO KISHIYA TA ne shi,don a iya sani na babu me bakin cikin cigaban mutum na rayuwar aure irin kishiya,ita ce duk yanda ta san za ta yi don ganin ba ki yi achieving komai a auran ki ba shi ta ke yi,to a nawa labarin Daddy ne mutum na farko da ya taimaka gurin rugujewar aure na.


Haka na cigaba da rayuwa cikin kunci,ni dai a duniya na ke matar aure,amman a gida kam ni da budurwa ba mu da maraba,domin da aure na,amman ya koma tsakani na da miji na sai gani sai hange daga nesa, domin fita nayi harkan shi na cigaba da rayuwa ta,inda zan iya cewa shi hakan ma dadi yayi masa,domin a ganin shi zai fi samun sakewa daga takura ta,nan shima ya dauki kashi na ya watsar,sai nayi kwana uku ban sanya shi a ido na ba,nan na shiga danasanin yin auran ma baki daya,domin ba haka nake ganin online couples ke gudanar da rayuwar auran su ba,ina yawan ganin yanda couples ke tattali tare da haba haban faranta wa junan su rai,amman ni nawa abinci ma,zan iya irga sau nawa muka taba ci tare,hakan ma ya faru ne tun farko farkon auran mu,ji nayi gaba daya duniya na tsani kai na,i just hated my whole self,and the damn situation din da nake ciki,but babu yanda zan iya haka nayi ta hakuri,domin abun kunya ne ace mace kamar ni da nake amsa sunan mace ta ko wani siga wai miji na bana gaban shi, haka zalika bana burge shi,sai na ji ban ma cika mace ba,ban kai na amsa wannan sunan ba,gaba daya ina cikin tsaka me wuya domin duk kan su biyu mutane ne masu mahimmanci a rayuwata, Hajiya duk da zuciya ta,ta yi ta kawo mun munanan tunani game da UBANA da ya koma KISHIYA TA,da kuma Afzaallllll miji na, wanda na aura da yarda ta,saboda tsananin son da nake mi shi,amman sam bani son in yadda da zargin da nake a kan su,a ma taya,ai ba zai taba yu wa ba,Daddy na mutumin kirki ne,shine abinda na yi ta raya wa a cikin zuciya ta,duk sanda wani thought mara kyau ya shigo kai na.


Ashe ba tare da na kula ba,my life is about to turn up side down,domin ba zan taba mantawa da wannan incident din ba,har zuwa ranar da zan mutu,har yau gani nake kamar yanzu ya ke faruwa a cikin ido na",kasan hijab in ta,ta ja tare da goge running nose din ta,tissue Anty Ummi ta mika mata"use this and clean up my love"ta kare hawaye na zubowa daga cikin idanun ta,duk da ƙwaƙwalwan ta ya riga da ya hasko mata abinda Nadeeya ke shirin fada,amman sam ta zuciyar ta,ta kasa yarda da abinda kunnuwan ta ke shirin ji,Hajiya na zaune kamar mutum mutumi,ita ko hawayen ma ta gaza yi,while Mama ta jika hijab in ta sharkaf da hawaye,domin gani take kamar almara labarin da Nadeeya ke ba su,daman akwai irin mugayen uba irin su Sen masu yin komai domin samun cikin burin su a duniyar nan,dauka ta ke kawai a Films ne,ko Novels ake samun cases irin haka ba a real life ba,while Nameer na zaune shiru kan shi na kasa,ya dunkule hannayen shi kamar me shirin kai duka,kallo daya za ka wa kyakkyawan fuskan shi,ka hango tsantsan ɓacin rai da bakin ciki.


Ajiyar zuciya Nadeeya ta sauke bayan ta face hancin nata,sannan ta samu ta cigaba"watan mu biyar da aure,yace da ni zai yi tafiya,he said China za shi,akwai wani muhimmin abu da ya taso,nan muka yi sallama ya sa kafa ya tafi abun shi, telling me to take care of myself,don zai dan kwana biyu a can,dan dariyar takaici tayi, sai kace can daman ya damu da ni ne,nan yayi tafiyar shi ya bar ni, without any phone calls,tunda ya tafi i have been trying his lines bana samun shi,i was kind of worried at first,sai daga baya na zauna na tambayi kaina,wai damuwar na  miye na ke yi akan mutumin da ba damuwa da ni yayi ba,ai ko da tuno haka da nayi,tuni na dauki kashin shi tare da watsar wa,na cigaba da day and day activities ɗina,tunda ance da wanda ya damu da kai,da shi ya ka mata ka damu,rayuwa ta cigaba da tafiya,sati daya,sati biyu babu Afzaal babu labarin shi,izuwa yanzu na cire rai daga tsammanin zan ji dadin rayuwar aure nima,na sanya wa kaina ni ke Auran kai na,i quite social media domin gudun ɓacin rai,coz in na hau na ga yanda Couples ke rayuwar su abun na ci mun rai sosai,haka zan kwana ina kuka,na rasa gane miye laifi na,Asin me yan matan Tik tok da Instagram suka fini da shi,wanda su majajen su na zaune da su lafiya,suna son su tare da tattalin su,why nawa ya zo daban,gaba daya Auran nan fice mun yayi a kai,domin sam ban ga amfanin shi ba,haka dai na cigaba da hakuri,in abun ya ishe ni in zauna in yi ta kuka,na yarda ba a komai bane kudi ke amfani,inda kudi na Siyan farin ciki da kwanciyar hankali then am very sure da ina daya daga cikin wanda za a yi kwatance sun fi kowa jin dadi kwanciyar hankali,tare da farin ciki me daure wa.


Ranar da ba zan taba manta wa har in koma ga Allah,ranar da duniya ta ta kife mun up side down,ranar da har yau ina danasanin ganin ta,ranar da ta kasa goge mun a cikin idanu na,ranar da na fahimci dalilin da ya sanya Miji na abun kauna ta ya tsane ni,ya kasa bani attention in da nake bukata,and a wannan ranar Uba na da ya kawo ni duniya ya tabbata kishiya a gare ni,hawaye ta goge sannan ta cigaba,it was on Sunday evening ba zan taba mantawa ba,ranar da muka cika 6 months cif da aure da Afzaal,and har zuwa wanann lokacin be dawo ba, sannan ba nema na ya ke yi ba, tun randa Daddy ya zo har gida ya mare ni na dauki fushi me tsanani da shi,don na saba duk bayan 2 2 days nake zuwa duba shi a gida,amman tun da ya mare ni ban kuma kiran shi ba,balle har na je gidan, don ba karya rai na ya ɓaci sosai sosai,amman hakan be hana shi sanya wa a tura mun kudi duk weeks kamar yanda ya saba ba, domin every week na duniyar nan,sai na ga credit alert a waya na,haka nan ya sabar mun tun tasowa ta,i missed him a lot,ya sanya yau nayi making up in mind ina zan je in duba shi,and I was planning on giving him a suprise visit don na san yana gida,ya sanya na ce ba zan kira shi ba,nayi niyan in na je in kwana masa biyu domin na gaji da zama ni kadai a cikin gidan nan kamar mayya,ga dai kayan duniya na more rayuwa babu abinda babu a gida na,farin ciki kawai nayi lacking,so da wuri na gama abinda zan ji a office na taso,kwalliya na ci nayi kyau abun na,domin ina son daukan Daddy mu je Saje muyi having dinner a can,don na ji an ce ta gurin nata ya hadu,so I don't want to miss out,saida na tsaya a gurin Secretariat a ta gurin gefen gurin suna siyar da fresh fruit,na lodo wa Daddy don na san shi da son fruit,sannan na biya na karba,na dauko hanyar gida,ina tafe ina jin waka,tare da bin wakan hankali na kwance,har na iso gida,ko da aka bude mun gate,don tabbatar wa sanda na tambayi Sunday bayan mun gaisa kan Daddy yana ciki?Ya ce mun eh yana nan, throughout yau kam ko kofar gate be fito ba,and babu wanda ya zo duba shi,domin kwana biyun nan ma babu inda ya ke zuwa,ya kuma hana kowa zuwa ganin shi,don ya ce a ce wa duk wanda ya zo ganin shi baya nan,yayi tafiya,mamaki ne ya kama ni,domin jin bayanan Sunday why on earth Daddy zai rufe kan shi a gida ya ki fita,sannan ya hana kowa zuwa ganin shi,kar dai wani abun ke damun shi,na tambayi zuciya ta,ji nayi Sunday yace"and little Madam,your oga self they inside oooo,na about 1 month he dey this house I don't know why ooo",da sauri na zaro idanu jin abinda Sunday ya fada,how comes,Kai na girgiza in disbelief domin sam wanann maganar ba abinda hankali zai dauka bane,me zai kawo Afzaal nan bayan ya ce da ni ya tafi China,and in ma yana nan to uban me ya ke a gidan Daddy har tsahon wata guda,muna gari daya be zo gida ba,hauka ya ke yi,tuno da shirme irin na Sunday ya sanya ni jan karamin tsaki,nace ya bani guri in shige da mota ta,ina fada wa kaina Sunday dai ban ga ranar da zai yi hankali,yana sanin abinda zai fada ba,sam haka yake maganar tsiya gare shi.


Ba karamin kaduwa hankali na yayi ba a lokacin da nayi parking mota ta,na fito,domin har wani dan karamin jiri ne ya kama ni,nayi saurin dafe jikin mota ta,ba kuma komai ya hadda sa mun shiga wanna lamarin ba,face motar Miji na Afzaal da ya ce da ni ya tafi China yau kusan wata guda,me motar shi ya ke yi parke a gidan Daddy na?,da sauri na hade kai na guri guda,tare da saurin kawar da ko wani irin mugun tunani a raina,na dauki handbag ina tare da ledan fruits din na shigo cikin gidan,ina raya wa zuciya ta kan cewa kila mistake aka samu gurin dawo da motar shi, instead of a kawo gidan mu sai aka kawo gidan daddy,kwarar da zancen ma nayi,tare da shiga, gurin su Baba Falmata na fara zuwa,coz na kwana biyu ban gan ta ba,da sauri kuwa ta nufo ni tare da rungumo ni,one thing that am always and forever be proud of myself about is Bani da kyashi ko tsana ko kaymar talakawa,and I don't know why,ya ci ace yanda na taso cikin kudi haka,uba na wani ne,be kamata ace bani da girman kai ba,amman i make sure to respect each and every one da yake aiki a gidan mu, especially Baba Falmata don matar daban take a guri na, coz tayi contributing a lot a tasowa ta,nan muka gaisa cikin sakun fuska,take tambaya ta why bana leko su kwana biyu,hankalin ta ya ki kwanciya tana ta tunanin ko lafiya,ita a tunanin ta ma ko ciki nayi ya ke bani wahala,dan dariya nayi sannan na bata hakurin daga mata hankalin da nayi,sannan na kawo mata excuse in aiki ne yayi mun yawa,za ta kuma magana nayi saurin katse ta,domin a yanzu babu wanda nake son gani irin Daddy,tambayar ta nayi daddy na ciki?nan ta ce mun eh ai ya kwana biyu ma baya fita,tun zuwan Alh Afzaal kullum suna tare,don da farko ma ta dau tare muke,ko da ta tambaye shi sai yace wai ban dan ji dadi bane,wannan karan tsoro ne ya kama ni da jin abinda Falmata ta ce,baki na har na bari gurin tambayar ta,how long yayi a gidan nan,nan ta dan sosa kai, sannan ta ce ya kwana biyu gaskiya,ai da gama jin haka na na nufi bangaran Daddy,da ledan a hannu na,garin sauri nan gurin su Baba Falmata na bar jaka da veil ina.


Haki nayi ta yi lokacin da na iso tsakiyar parlor in Daddy saboda gudun da na sheko,saidai wayam babu kowa a parlorn sai karan T.V,hakan ya sanya ni haurawa sama, ban san me yasa zuwa lokacin bugawar zuciya ta ta mugun tsanan ta ba,domin jin zuciya ta nake kamar za ta fado kasa,wanda kuma ba komai ya haddasa hakan ba sai firgici tare da wasiwasin da shedan ke ta kawo mun, cikin matsanan cin kuka tace"Hajiya ko da na isa kofar dakin Daddy,na kama handle in zan shiga ke nan,na jiyo muryan miji na a cikin dakin baccin Baba na suna magana,jiri ne ya ibe ni da sauri nayi kokarin rike kaina,domin wallahi ko da Falmata ta fada mun Afzaal na cikin gidan nan kasa yarda nayi,domin tunanin duniya nayi amman na kasa gane dalilin da zai kawo shi har cikin dakin Daddy,jiyo muryan shi nayi yana cewa"Ni dai a gaskiya Daddy ba zan koma ba!me take mun a gidan?Duk wani dadi da nutsuwa kulawa tare da kwanciyar hankali babu wanda bana samu a gurin ka,so why on earth zan so tafiya in bar ka???"mamaki da tsoro ne suka mugun kama ni, saidai na bar shi a kunnuwa na ne basu ji mun daidai ba,jin daddy ya fara magana cikin muryan lalashi ne ya hana ni shiga cikin dakin,fadi yake"look at me my love ni kai na kasan in ba ya zama dole ba,babu abinda zai sanya ni son yin nisa da kai, domin a duniyar nan bayan Nadeeya bani da abun so da kaunar da ya wuce ka"....kamar wani me shirin yin kuka Afzaal yace"common Daddy am very sure duk irin son da kake mun be kai nawa ba,tun da kai ashe bayan Nadeeya ne,Ni ko ko uwar da ta kawo ni duniya bani mata son da nake maka,Daddy i just can't do without you wallah I don't know where how or why but am just so addicted to you,that I don't think I can survive this life time without you,Daddy don Allah let's delete Nadeeya from our life and enjoy it to the fullest,wallahi na gaji da wanann boye boyen da muke mata,kana Sona ina son ka,why can't us be together?kawai zan saki Nadeeya in San bata rayuwa ta,domin wlhy ko nawa za a bani ba zan iya rayuwa da wata mace ba,in har ba kai ba bani son kowa",da sauri Daddy yace"kai Afzaal baka da hankali ne?Talk softly pls"...."yes na ji bani da hankali,ni fa Daddy ido na sun rufe kai kadai nake so,and in har da gaske kake kana so da kauna ta kamar yanda ka ce then am tired of all this,I have to set Nadeeya free ko za mu ji dadin cin duniyar mu da tsinke"...."hey My boy ka san dai sarai ina son ka kuma ina ji da kai,fiye da komai a rayuwar nan,domin kai wani sashi ne na jiki na,wanda ta kai ta kawo har yarinyar da na haifa a ciki na kishi na ke da ita akan ka,but i want you to understand me,Afzaaal setting Nadeeya free and baiyanar da relationship din mu a duniya is not the solution, because ka riga ka sani a Nigeria ba su riga sun yi Legalizing Auran jinsi ba,da ma kamar a kasar waje muke America or Indian da sauki,amman ka san muddun aka san me and you are into each other a kasar nan kashin mu ya bushe in ma ba a kashe mu ba,and mutunci na ne zai zube a idanun duniya, don't forget ni Dan siyasa ne so i have a reputation and name to maintain,so ko dan haka we have to keep it in a low key,but believe me in nace da kai i love You so much,the problem is that Princess!! yarinyar nan ina mugun jin tausayin ta sosai,don in baka sani ba ka sani yau Nadeeya bata da Womb,wanda ni na sanya aka cire mata tun tana 9 years old"da sauri Afzaaal yace"Whaattttt!!!kamar yaya bata da Womb,ka sa aka cire mata,but why"...."Sam wanann ba abinda ya shafe ka bane,am just telling you ne,but sanin why ba naka bane,and ka ga tun randa aka daura auran ku ko sau daya ban bar ta ta samu kwanciyar hankali da soyayyar ka ba,i make sure to snatched all her rights and duties da ya ke kan ka,out of jelousy da kaunar da nake maka,a matsayi na na Uban ta na koma kamar Kishiyar ta,sanann ka ce kana doubting soyayya ta gare ka,duk duniya bana hada soyayyar Princess da kowa,but akan ka na daga hannu na wanka mata maruka har uku,saboda ta bata maka rai,wanda akan haka for almost a month now ba ma magana da ita,so pls bana son abinda zai jawo mana matsala,duk da bana so Amman ya zama dole ka koma gida gurin ta,kar ta ga shirun yayi yawa"


"Daddy wai why can't you understand me ne,ni fa ko na zauna da ita,ko hannun ta bani iya taba wa,don kwata kwata ko tsirara za ta na yawa kullum gaba na,ba zan ji sha'awar ta ba,saboda already ka sabar mun da jikin ka,so why not in sake ta,ka ga babu wani more tashin hankali,sai mu yi Rayuwar mu cikin farin ciki da kwanciyar hankali,ko kuma mu kashe ta,in ya so sai mu gudu USA ko Indian a daura mana aure a can ko ba haka ba"...."Afzaaal kar na kuma jin kayi irin wanann tunanin ma,balle har na ji ka furta shi,ba zan taba iya kashe Nadeeya kamar yanda na kashe Mahaifiyar ta ba!!Nadeeya is my flesh and blood ko ka mance ne?And I do love her! cutar da ita da nayi haka ma ya isa,all I know is that ina son ta bana son abu ya same ta, domin duk abun nan da ka ga  ina yi saboda ita nake yi,and you at the other hand bana jin akwai abinda zai sanya na rabu da kai,saboda so da kaunar da nake maka,so take it easy okay,na san kana jin tsoron rasa ni ne,amman banda abun ka kana young and handsome da kai,ai ni ya kamata in na jin tsoron kar a kwace mun kai, nothing will happen between us da har zai sa mu rabu okay,so forget about Nadeeya a duniya ta ke matar ka,amman a zahiri ni ne nan kadai na ka, so kar ka damu kan ka da ita okay,maza ta so muyi ko da one round na Doggy style  kafin mu je mu ci abinci,kasan i can never get enough of you,dadin ka yawa gare shi"na ji muryan daddy na ya gama fadin maganganun banza da iskancin nan wa Miji na,yana yar dariya.


"Hajiya at that point my world just crashed into smaller  pieces,ban san time ɗin da na zube a nan kofar dakin ba,a take ledar hannu na ya zube fruits din ciki suka zube,ji nake kamar zan mutu,ko kuma zan amayo zuciya ta,domin yanda ya ke mun zafi tare da buga mun,ina ma in mutu a yau din nan,domin abubuwan sun yi wa brain ɗina yawa,i just want to cry my eyes out but wlhy ko digon hawaye babu a idanu na,sai a lokacin komai ya dawo mun fess a cikin kai na,haba no wonder mana,no wonder wannan shakuwa ta su daman akwai ayan tambaya,no wonder duk abinda nayi bana gaban Afzaaal ashe ashe neman juna suke da Daddy"da karewa kuwa ta fasa kuka me cin rai sannan ta cigaba"ji nayi gaba daya duniyar na juya mun a hankali na mike kafafu na suna rawa hannu na dafe da ciki na,wanda har yau na kasa yarda wai ni Nadeeya bani da Mahaifa,sai na ji ni very empty!!ba karamin tsanar Daddy bane na ji tana huda mun zuciya ina jin kamar in kashe su duk biyu In huta,na kasa yarda Daddy wai shi ne ya kashe mahaifiya ta,my Late Mommy to me ta yi masa,ban san daga ina na samu karfin gwiwa ba,sai gani na nayi na nufi kofar domin duk da abubuwan da na ji ina son idanu na su zama mun sheda,akwai kuma abubuwan da ya dace in fada masu,thank God ko mancewa suka yi ina murda handle din kofar ya bude,a take na kutsa kai na cikin dakin ina rokan Allah ya sa karya ne duk abubuwan da kunnuwa na suka jiyo mun,saidai kas tawa ƙaddarar ta riga fata,domin da nishin su kamar wanda ake zare wa rai na fara cin karo,kafin in tarar da Uba na da ya yi silan kawo ni duniya tumbur haihuwar uwar shi,a kan Mijina wanda ya kasance abun kauna ta, shima tumbur haihuwar ta shi uwar suna suna".......sai ta fasa kuka.....Saida ta goge fuskan ta sannan ta cigaba"wata irin gigitattciyar ihun da na sanya ne ya yi saurin zaburar da su tare da saurin barin jikin juna,sai a lokacin na samu hawaye suka soma zubo mun,baki na yana rawa haka ma jiki na nace,Daddy! Afzaal!!what!sai na fashe da wani irin kuka,da sauri Daddy ya shige cikin blanket while ni kuma ido na da hankali na sun gushe domin cikin ɓacin rai da daga murya na shiga surfo musu duk wata ashar din da ta zo baki na,don har zagin da ban iya ba yau duk nayi musu,inda Daddy ya shiga ce mun in tsaya in ji he can explain,at that time bani da burin da ya wuce in ga na tara mishi jama'a na kuma tona wa yan iska asiri,domin sai lokacin na shiga danasanin rashin dauko jaka ta da ban yi ba,domin waya ta na cikin jakar,don da na zo da shi babu abinda zai hana ni daukan su video na kuma yada su a duniya.


Tallah! Tallah!! Tallah!!!


Ina Mata? Ina yangayu? Ina amare harma damasu jego? To duk Ku biyoni kusha lbr🎤kamshi empire sunxo muku d ingantattaun turarukan wuta, na kalolin itatuwa😊 akwai turaren gida, akwai na wanka, akwai na wanki, akwai na mopping dana wardrobe🥰 muna da turaren kabbasa Wanda KO kin wanke kayanki sunanan👌akwai sirrintaccen turaren tsugunno Wanda KO toilet Kika shiga Wanda y shiga abayanki sai yaji. Akamshi empire zaku sami hadaddun humrori masu launi d kamshi kala kala, akwai kalolin kulacca d ingantattun mayukan gashi💃 bafa iya nan muka tsaya ba muna hada sourvinire na fita kunyar bakinku👌babban abin farin cikin muna d online classes damuke koyar d turaruka akan farashi me sauki. Kedai kulla kawance d kamshi empire ta wannan lambar 07053717605 KO adireshinmu no 13 biuroad Badarawa Kaduna sai kunzo🤝


Babu yanda Daddy be yi ba kan nayi shiru na saurare shi,he can explain himself but sam na ki yarda balle na bashi listing ears,hanyan kofa nayi don fita domin babu abinda ke raina da ya wuce in tona musu asiri, duniya ta sheda ta san abinda suke yi,don at that time Yan sanda nake da niyar dauko musu,kuma ban boye musu ba na fada musu kan wallahi ko zan rasa raina a yau ba sai gobe ba sai na tona musu asiri,a zafafe na nufi kofar fita,inda na ji muryan Daddy na fadin "Afzaaal get her back kar ka kuskura ka bar ta,ta fita daga dakin nan,in ta fita ta bude bakin ta na shiga uku"ya kare hankali a mugun tashe,nan a zafafe nace "wlhy babu abinda kuka isa yi mun in kuma kun isa bismillah,asiri kuwa wlhy tallahi sai na tona shi,Alh Rilwanu Audu Waziri sai duniya ta san waye kai,wlhy na tsane ka! tsana mafi tsananin,in sha Allah sai ka ga abinda zai same ka,ka ji kunya wlhy ace wai kana Ubana ka na soyayya tare da neman banza da Miji na,na aure what a shameful thing,you are indeed a disgrace to fatherhood, no wonder mana na kasa gane kan miji na,ashe Ubana ne ya zamo kishiya ta"...."Nadeeya wani irin maganar banza kike fada wa Daddy haka"Afzaal ya kare yana kokarin riko ni,a zafafe na daga hannu na kuwa ba tare da wata wata ba na kwashe shi da mari,wanda ko ba a fada ba na san ya shige da,don Saida ta kai shi kasa"yi mun shiru karamin dan iska,Wawa jaki,Animal wanda be san inda ke masa ciwo ba,wlhy in ka kuskura ka taba ni da wannan dattin hannun naka sai na kashe ka,sai ka jira in sa da kai tukun na,jaki wanda ya Saida jikin sa da imanin shi wa wanann tsohon dan iskan,no wonder mana Afzaal no wonder tunda muka yi aure na kasa gane kan ka,no wonder sai yanzu komai ya dawo mun Wlhy Daddy kayi abun kunya,ashe abinda kake sanar wa Samaruka na ke nan in sun zo neman aure na, suke kin amincewa karshe sai ka bi su da sharri,Wow wow just wow!!Sen kayi matukar bani mamaki,and Afzaal wlhy ka ji kunya,kuma na gode wa Allah da be sanya mun hada jiki da kai ba ,domin da na samu cikin ka har in mutu ba zan taba yafe wa kai na ba,kuma zan kare rayuwa ta cikin danasani na haifi yaro da ƙaruwar na miji,kamar yanda na san har in mutu ba zan daina danasani kasancewa ta diyar wanann monster din ba"tana kai wa nan ta nufi kofa gadan gadan,don at that time zuciya ta ya riga da ya bushe,babu abinda nake nema irin ganin tonuwar asirin su,"Afzaal get her!! don't let her leave this room ko kuma rayuwar mu za ta tarwatse"jin haka ya sanya ni bude kofar da sauri tare da tattaran rigar jiki na don in kwasa da gudu, unexpected na ji buguwar abu a bayan kai na,wanda ya sanya ni sakin kara a take kuwa na zube a gurin,don bakin da na fara gani,ina jin Daddy na fadin"me ka aikata haka Afzaaal kar dai kashe ta kayi,nace maka nayi kar ka bar ta ta fice ba wai ka kashe mun yarinya ba,kasan waye Nadeeya a guri na kuwa, tabbas rayuwar ta na da matuƙar amfani,in har wani abu ya same ta,to tabbas kaima sai na kashe ka"daga haka idanu na suka rufe kirib ,ban kuma sanin yanda kai na ya ke ba sai da na kwana biyu a ina kwance ashe,farkawa ta ke nan,na ga Baba Falmata a kai na,inda har ta canza mun kaya,zuwa ash material mara nauyi,nan ta hau gode wa Allah domin a fadar ta kwana na biyu ina kwance ban san inda hankali na ya ke ba,a nan ne nake tambayar ta ina Daddy,nan ta hau jero mun sannu tare da ce mun Daddy ya ce su kula da ni yana da meeting a  Conference hall ɗin shi na gidan,ta tafi ai da jin haka na ji sanyi a cikin zuciya ta a take na ce da Falmata ta nemo mun abinci ina jin yunwa,da fitan ta daga dakin kuwa nima na fito kafa na ko takalma babu,balle in damu da tsayawa daukan dankwali ba,buri na be wuce yanda Daddy ya tarwatsa mun rayuwa nima in tarwatsa na shi ba,da gudu kuwa na nufi meeting hall in nashi,inda na samu yana tsaka da jawabi da yan media,nan ko na rufe idanu tare da yi masa zagin tsamen nama,ba tare da damuwa da ana dauka na ba,raina ba karamin ɓaci yayi ba ganin ban ga Afzaaal ba,domin niya ta in hada su duk biyu nayi wa zagin fitan arziki,daga nan ne kuma ganin ina shirin tona mishi asiri shine ya matsa wa Abokin shi big Daddy kan sai ya kashe ni,don gudun tonuwar asirin shi,inda shi kuma Big daddy yace ina ba zai iya kashe ni ba,a karshe dai ganin yanda ya matsa masa ne,ya sanya a karshe ya bada shawarar a haukatar da ni,inda da hankali na da komai saboda gudun tonuwar asirin sa ya kai ni asibitin azzalumin nan Doc Bashir Saida ya san yanda yayi har ya ga na haukace,a hakan ma be yi musu ba,a yanda wanann ta nuna Nameer da idanun shi suka gama yin ja don bakin ciki,yace mun Afzaaal ya biya Bashir in kudi don ya kashe ni,inda a lokacin ne Allah yayi ya samu ya taimake ni shine ya gudu da ni can Kaduna gurin Maman shi,a nan suka yi ta kula da ni har Allah ya bani lafiya,to shine tunda na farfaɗo na matsa musu sai sun kawo ni gida,jiya dai Bauchi muka kwana inda na je gidan Big Daddy na sanar da shi duk abinda ke faruwa,don shi ya fada mun ma ashe daddy so yayi a kashe ni da farko,kuma ya sanar mun kungiyar asiri daddyna ke ciki,shi ma Allah ne ya so shi don son kashe shi yayi,amman ya bani hakuri tare da tabbatar mun zuwa gobe zai sanya a shigar da karan daddy zuwa Court domin can ne za su fi samun daman hukunta shi,daidai da laifin da ya aikata,and da yin haka ne duniya za su san waye shi,su kuma yi tofin Allah tsine da shi sannan kuma ya fadi zaben da bayi da burin da ya wuce ya ga ya lashe shi,cikin kuka ta kare da fadin Wannan shine labarin Nadeeya wanda Uban ta ya zamo Kishiya a gare ta saboda son zuciyar shi,saboda son abun duniya ya sanya ya kasa barin tilon yar sa moran rayuwar auran ta,ya sanya na kasa banbance wai shin UBANA NE SHI KO KUMA KISHIYA TA,and saboda zalunci da son rai ya sanya aka haukatar da ni don gudun tonuwar asirin shi, Mijina abun kauna ta kuma ya biya kudi don a kashe ni amman Allah ya tsiratar da ni silan bayin Allahn nan da suka zamo mun Goofy Angels dina"ta kare tana kuka kamar ran ta zai fita.


Kamar wanda aka yi ruwa aka dauke haka parlon yayi tsit,baka jin komai sai sheshekan Mama,Ummu da kuma Nadeeyar ita kan ta,kusan mintuna shiru babu wanda ya iya cewa komai a cikin su,inda Hajiya na zaune gurin kamar babu numfashi tattare da ita saboda yanda ta kame guri guda idanun ta sun kakkafe,ko yatsan ta bata motsa wa,Nameer ne ya fara lura da halin da ta ke ciki,domin ya ji sanda ta sauke wata nannauyan ajiyar zuciya daga nan kuma sai dif,da sauri ya tashi tare da nufan ta inda sanya hannun da zai yi a jikin ta kuwa ta tafi luuuuuuuu da sauri ya taro ta,domin sam babu alamun numfashi a tattare da ita,ba sai kuka ya koma biyu ba,nan fa Ummi da Nadeeya suka rude suka shiga kwala wa Hajiya kira suna kuka kamar ran su zai fita,Usmanu da ke kwance a daki yana sauraran duk abinda ke faruwa shima kukan ya sake,daman ya dade yana zargin ya'yan na shi ,yana jin tsoron ranar irin wanann domin tabbas in Hajiya bata mutu ba to kuwa zuciyar ta zai kusa bugawa,domin ace a cikin ka ne ka haifi irin wanann mutumin ai dole mutum ya  kusa hadiyar zuciyar sa,be taba danasanin rashin kafar shi ba sai wanann ranar,ya san Hajiya na bukatar support in shi tana buƙatar yanda za ta sa kan ta tayi kuka sosai,daman Abul bait haka yake Inalilahi wa ina ilahi raju'un kawai ya ke ta maimatawa tare da karanto duk addu'ar da ta zo bakin sa,baya fatan ya rasa Hajiya domin ita kadai ta rage masa rayuwar nan wanda ya ke gani ya ke jin dadi,bayi da mata balle yara,daman Hajiya da yan uwan sa kadai suka rage masa,haka yayi ta yunkurin miƙewa ya samu ya fito ya ga abinda ke faruwa amma sam babu hali,banda kuka da addu'a babu abinda ya ke yi,tare kuma da mamakin Rilwanu a cikin zuciyar shi.


"Small mom akwai asibiti kusa ne?Mu samu mu kai ta don ceto rayuwar ta,domin tana raye so ku kwantar da hankalin ku Please"Nameer ya ce cikin sanyin murya,cikin kuka kuwa Ummi ta mike tare da cewa"eh akwai bari na dauko mayafi na sai mu tafi"ba tare da bata lokaci ba kuwa ta shiga ta dauko abinda ya kamata,sannan ta leka gurin Usman ta sanar da shi kan za su kai Hajiya asibiti,yana kuka ya musu fatan dawowa lafiya tare da roka wa Hajiyar sauki a gurin ubangiji.


Ba tare da bata lokaci ba kuwa,Nameer ya dauke ta a motar shi duk suka nufa asibitin inda Mama ta zauna a gaba,while Nadeeya ummi da Hajiya suna baya,inda Nadeeya ta daura kan Hajiya a cinyar ta,while Ummi ta daura kafafun ta,a haka har suka isa asibitin,idanun Nameer na kan Nadeeya da ke kuka kamar idanun ta za su fita,ji ya ke kamar ya rungumo ta ya lallashe ta,domin yarinyar nan ita ta ga wahalar rayuwa,wani irin so kauna hade da tausayin ta ne ya ji yana huda masa zuciya,a haka har suka samu suka iso asibitin a take kuwa aka karbe ta,inda Nameer yayi cike ciken da ake bukata aka wuce da ita Emergency domin samu a ceto rayuwar ta,nan Nameer da Mama suka yi ta kwantar musu da hankali tare da tabbatar musu da babu abinda zai same ta in sha Allah,so suyi ta mata addu'a shock ne kawai and in sha Allah za ta farfado.



***************Bauchin Yakubu


Tun bayan barin gidan Alh Kabiru da Nadeeya tayi ya ke cike da dumbin farin ciki da annashuwa,domin ji yayi kamar an sanya shi cikin Aljanna,ya ji dadi sosai da dakikan ci irin na Nadeeya ya sanya ta zuwa gurin shi bata nufi gida kai tsaye ba,and ya ji dadi sosai yanda yayi controlling temper in Shi be kashe ta ba,domin a yanda ya ke jin kan shi so yayi su yi 'An Eye for an Eye' yanda ya kashe mishi Ayman ɗin shi,shima ya kashe Nadeeya shike nan sun yi balancing komai,amman a hakan ma ya ji dadi sosai,domin ya san watan tonuwar asirin Rilwanu ya kama,don tabbas babu abinda zai hana shi tsaya wa kai da fata gurin ganin ya kai Rilwanu kasa,sam ba zai taba yuwa daukakan nan da ya samu shi ya tashi a babu ba,shi yayi masa silan daula sannan ace ya fishi samun komai a harkan nan,ai hakan ma ba me yuwa bane,ya dade da tsanar Rilwanun amman yana ta hakurin boye wa,amman yanzu kam ya kai shi bango tunda ya kashe mishi Ayman,tabbas sai ya wulakanta shi kuma ya tozarta shi.


Be yi sanya ba kuwa Nadeeya ka barin gidan shi ya Barrister A.K.Y Zakariyya domin yana daya daga cikin best Lawyers in da ake ji da su a garin Bauchi da ma kewayen ta,ya kware sosai gurin aikin sa, inda kowa ya riga ya san in har ya shiga court to baya faduwa,a take kuwa ya jika shi da kudi tare da sanar da shi kara suke san shigar wa,kan Yarinya ke tuhumar uban ta da neman mijin ta,sannan ya kashe mata mahaifiya tare da bada Womb inta duk don samun cikan burin sa,da farko Barrister ya so kin yarda ya karbi karar ta sa,domin da ya ji wai Sen Rilwanu Audu Waziri ake son shigar wa kara,yayi mamaki sosai jin irin cases In da ake tuhumar sa, domin duk wanda ke garin Bauchi ya san Sen Rilwanu Audu Waziri mutumin kirki ne,me cike da dadtaku, amman saida Alh Kabiru ya san yanda zai yi ya murde Barr tare da yi masa yayyafin manyan kudade har ya yarda ya karbi case ɗin,


A take kuwa ya kira Rilwanu bayan barin Barr daga gidan shi,cikin Sa'a kuwa ya samu Rilwanu ya dauki wayan "Ikon Allah wai na kwance ya fadi,su Kabiru ko batan kai aka yi ne,na ga kana ta kira na babu kakkautawa","hmm Rilwanu ke nan,in ko ka ga kira ai samu ne,i just call to check on you in san kana cikin koshin lafiya ko yaya"dariya Sen ya fashe da shi,"ikon Allah sai kallo Kabiru can you drop the act and go straight to the point,ni da kai in zan tuna we are not in a good term inda har za ka ce ka kira don duba lafiya ta,kai dai wani munafurcin kake son isar wa maza isar bani da lokacin ka,ina da abubuwan yi".


"Sannu agogo Sarkin aiki,ko wa za ka wa karyan iskanci oho, kai Rilwanu ka san ni da kai kar ta san kar ce so in kana rike iyayin banzan kan nan ka rike ta,domin na ci gaban uban ka na yaga leda,wlhy na fi karfin ka da kuma yardar Odogwun da ka wulakanta ka nuna be Isa ba sai na ga bayan ka,masifa na tun karo ka me masifan karfi,a matsayin mun yi zaman tare a baya duk da ka zo ka zamo dan iska ka butulce mun to ni ba haka nake ba,so na kira in sanar maka da babban murya that you should watch your back,domin in baka yi ba za ka sha mugun mamaki,i have already taken a vow sai na ga bayan ka and wlhh ba zan taba samun kwanciyar hankali ba muddum ban gani ba,na riga da na dasa maka bomb tashin ta kawai ya rage mun,and I promise you sai ya tarwatsa ka tare da abinda kake takama da shi"ya kare cikin fushi"Kabiru! Kabiru!! Kabiru!!! Wlhy ni damuwa ta da kai har yanzu hankali ne baka fiya ba,sai kace wanda ya sha nono kanwar shi,sha ba zan yi blaming in Ka ba,shi wancan dan iskan da kuka sayar wa soul and body in ku maybe harda brain in Ka ka haɗa mishi saboda tsinannan son kudin ka,to wlhy kul in kana karyan iskancin ka ka kiyaye ni domin ni na girme maka a bariki wlhy,tunda na kwanta da mijin diya ta,na kuma haukatar da ita saboda neman duniya ya kamata ka san eh tabbas da gaske nake,and for your own information wannan barazanar karyan na ka ba kama ni zai yi ba,don haka kar ka fasa and I promise you I won't watch my back I want to see har wani irin extend za ka kai don son ganin down fall ina,mugu butulu me zuciya biyu,wlhy in akwai wanda ya kamata ya ji kunya kai ne, saboda ka ci Amanar zumunta wawa sakarai me hassadan masifa,to wlhy kar ka fasa tada bomb in naka ni kuma in ga dan Bura uban da ya isa hana ni samun cikan buri na"..."haka kace ko Rilwanu to shike nan,za kuma ka gani wlhy wannan karon da gaske nake,sai na nuna maka Nonon kanwar ta wa na sha dan uban ka".."in ka fasa ka raina Allah da Odogwun da kake bautawa,Jaki mara hankali wlhy da na san saboda haka ka kira ni babu abinda zai sanya ni daukan kiran ka,and duk sanda ka sake kira na sai na sanya an kama mun kai"ya kare yana jan tsaki,"Rilwanu kayi kadan ka fada mun magana son ranka,zan ko gwada maka Ni din babban Jaki ne,and Odogwu ya tsaya mun,I will show you Shege without any Mercy"..."Da Kai da Mercy in duk kan ku kun ci Bura uban ku, shashasha bani da lokacin mahaukaci dan giya irin ka,Fuck offffff!!!and go to hell"da gama fadin haka kuwa ya kashe wayar shi,dariya Kabiru yayi irin na mugayen nan sannan yace"mu zuba mu gani Rilwanu karshen ka ya riga da ya zo sai na tabbatar na wulakanta ka, wulakanci mafi tsanani sai na muzanta ka a garin Bauchin nan".......







  In na ga ruwan comments kuma za ku ga ruwan updates da wuri wuri ma😸


   Assalamu alaikum mutanan kirki 


    Am so sorry na ji na shiru da kuka ji kwana biyu,i have been dealing with some stuffs ne wallahi,but am safe and sound Alhamdulilah thanks for you concern.


And wlhy waya ta na ta bani ciwon kai so probably gobe zan kai gurin gyara,in Allah ya sa an gyara da wuri za ku ji ni zuwa jibi in sha Allah,in kuma be gayru ba to sai kun ji Ni🤗


   Ina yi wa kowa fatan Alkhairi .


Ina masu sha'awar shiga Adashen online,inda za a rike miki Amanar kudi,ba tare da runto ko Ojoro ba,inda za ki zuba ki kuma kwashi kudaden ki, cikin kwanciyar hankali da yardar Allah,ba tare da wata matsala ko tashin hankali ba,


Akwai Matan da sam kudi be cika zama musu a hannu ba,da kin samu sharp an kashe su,someone like me🥺lol,to yar uwa ta shiga Adashe a nan ne,zaki tara kudin ki hankali kwance,


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L7ai2fYGh4UAIK9MhC9awJ


Kindly ki shiga cikin group in nan,2500 weekly,I can assume you Bara ki samu any disappointment ko Damfara ko wani rikici ba, 


For more information,chat her up via:


       08149541182

Sai mun ji ku🙌😍

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


     Wannan page din na ku ne Yan group din UBANA NE KO KISHIYA TA,ku yi yanda kuke so da shi.


Ina godia da kaunar ku gare ni🫶🏻❤️

             

..........


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:

    

            08100046388


******************


    Tallah! Tallah!! Tallah!!


   

   Ina uwar  da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


  Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


   Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


    To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌

    

https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


         08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌


...........

          Page fifty one


**************


              ************ 3 days later 



     Alhamdulillah jikin Hajiya Rakeeba yayi kyau sosai,don Nameer tsaye yake akan kafafun shi game da jinyar nata,inda jikin kuwa Masha Allah yayi kyau sosai coz a halin da take ma yanzu kam she is out of any sort of danger,babu wanda y’a dauka da ta kai labari,daga su Nadeeya har doctors din,balle wai ace har tayi saurin farfado wa,domin in suka tuno halin da suka kawo ta.


  Ta sha wahala sosai,don ba karamin hawa jinin ta yayi ba,Alhamdulillah a zauna ma take irin haka ne,Allah y’a kiyaye in mutum na tsaye y’a yanki jiki y’a fada,shikenan in y’a zo da tsautsayi sai shanyewar barin jiki🥺Allah ka raba mu,ga zuciyar ta da Likita y’a ce y’a soma tabuwa,amman da ke kwararun likitoci ne a kan ta,Wanda suka kware kuma suka san ta kan aikin su,a gefe guda kuma ga Nameer y’a bude musu bakin aljihun shi,sai gashi Masha Allah jiki yayi fesss yayi kyau,domin yau suke sanya ran sallama ta,saidai doctor din ya ce da su na kawo ta a kai akai for regular check up,domin Ummi ce ma ta matsa kan sai anyi musu sallama ganin to jikin nata yayi kyau,and ta fi kowa sanin yanda Hajiya ta ki zaman asibiti,sam bata so.


       Haka dangi kuwa suka yi ta yin tururuwa zuwa duba Hajiya da jiki,saidai ko da wasa Ummi bata sanar wa Yan Uwan ta su Yan biyu kan ce wa Hajiya bata da lafiya ba,domin tabbbas in har suka ji sai sun zo,in kuma suka zo sai sun nemi Jin ba asin zance,sai sun so sanin abinda ya faru har ya haddasa wa Hajiya shiga Wannan halin da ta ke ciki yanzu,wanda ko kadan Ummi bata fatan labarin da Nadeeya ta basu ya fita waje,don sam wanann ba labari me dadi bane,haka zalika wannan abun boye wa ne,sam ba labarin da ya kama ta ana yada wa bane,domin har iyau ita karan kanta ta kasa yarda wai babban y’a yan su da suke wa kallon Uba shine ya zamo monster haka dare guda,Innalillahi wa Inna ilaihi raju’un tayi kuka har bata sam adadin sa ba,tabbas Yaya Abulbait y’a bata mamaki sannan kuma y’a ci amana,ba shakka kuma y’a zalunci diyar shi zalunci mafi tsananin gaske,wlhy har yau sai tana ganin abun kamar irin mafarki ne ko kuma irin tatsuniyar nan,haka Mama tayi ta dannan ta,tare da bata baki tana me lallashin ta hade da kwantar mata da hankali,ba karamin karfafa ta Mama ke yi ba,domin a yanzu in ta sare ita kuma Nadeeya y’a zai kasance da ita ke nan??So she has to be strong ko dan family din ta,da haka Mama ta samu ta shawo kan Ummin har ta kwantar da hankalin ta,saidai ta cigaba da kukan zuci,tare da taya su Mama kwantar wa da Nadeeya hankali.



A wannan ranar kuwa doc ya rubuta musu sallama,amman saida ya rubuta magungunan da ya dace a siye su dan shan ta,tare da sanar da su irin abinciccikan da ya d’ace ta na ci,and ya kamata ta yawaita shan kayan fruits,and also yanzu cin Kayan gishiri da yawa da Ajino motor ba nata bane,Pharmacy da ke kusa Nameer ya nufa a take kuwa ya siyo duk magungunan da ake bukata,ba tare da damuwa da tsadar magungunan ba,sanann ya dawo yayi clearing sauran  bills din da ke kan su na zaman asibitin,sannan aka ba shi takardar sallamar tasu,cike da farin ciki kuwa ya shiga dakin,tare da sanar da su kan su fito anyi sallamar,cikin dadin rai kuwa Ummi ta gama hado komai na su,sannan suka riko Hajiya tare da sanya ta cikin mota,Wanda har lokacin kuwa Hajiya da idanu kawai ta ke bin mutane,bata iya ce wa komai,Nadeeya kuwa duk Sanda Hajiya ta sanya idanun ta akan ta,saidai a ga ta fashe da kuka,inda a take hankulan su ke tashi su shiga aikin lallashi karshe ma su bige da taya ta kukan,inda abun ba karamin ciwo ya ke wa Nameer ba duk time din da ya ga suna kukan nan,a rayuwa zai iya cewa in ka cire kukan Mahaifiyar sa,Wanda ya dade be ga zuban hawaye a fuskan ta ba,da kukan Marainiyar Angel din shi,to babu abinda y’a tsana kuma yake saurin tasar masa da hankali irin y’a ga hawaye na zuba daga cikin kyawawan idanun Nadeeya,ba karamin hargitsa masa lissafi hakan y’a ke yi ba,sai ya ji zuciyarsa na zafi har kamar ya janyo ta su zauna su ci kukan tare ya ke ji(ni ko na ce su Nameerun Mama manyan gari🤣,sam Yaron Mama be kurbi zumar kaunar ta shi da sauki ba).



Babu wanda y’a kula wani a cikin motan shiru ko wannan su da zancen zucin da y’a ke yi a ransa,saida Nameer y’a biya ta kasuwa ,da kan shi y’a shiga y’a hado wa Hajiya kayan abincin da wanda y’a tashi ko yake jinya zai ji dadin cin su,sannan y’a biya gurin masu fruits y’a lodo mata su,sai kuma gurin masu saida bottle water,y’a siyo pack pack tare da hado wa da Malt da kuma packs din madaran ruwa,sai kayan shayi tarkace dai ga su nan,y’a kashe kudi sosai kam,don ko da aka zo lodawa a bayan motan Ummi saida ta rike baki don mamaki,ikon Allah wai Ashe da gaske haka na iya faruwa ace mutum stranger baku hada komai da shi ba,karshe y’a zamo shine me taimakon ka,yanzu Nameer ba su hada komai ba amman dubi yanda y’a ke dawainiya da su,wanda she is very sure ko mijin ta ne kila ba zai yi rabin abinda Nameer din ma yayi ba,babu abinda ta ke yi sai roka masa karin budi tare da taya shi rokon Allah kan duk abinda y’a sanya gaba y’a samu (d’aman haka ne,a rayuwa ba lalle sai na ka ke cire ka a kunci ba,wani abun ma in kana neman tashin hankali to duk

Naka sun iya sanya wa,Saboda no matter how and what sun san y’a zamo dole ka zauna da su ne,y’a sanya ake cewa wai Naka sai naka dadin zama sau bare,Allah ka hada mu da mutanann kirki a duk inda muke,and yana da kyau duk kankantar alkhairi da mutum zai yi maka,ba sai y’a zamo lalle sai kai ma ka ji sai kayi returning favor din ba,in ka ji hakan ma abun ne me kyau,amman at that time in Baka da abun bayar wan,roka masa khairan a gurin Allah,riba biyu ne domin kana roka ne kaima Mala’ikun rahma suna roka maka,Ubangiji y’a datar da mu y’a kuma ba mu ikon ganin mutunci da Alkhairin bayin sa,kar y’a sanya mu kasance cikin munafikai ko butulai).



Saida aka gama shirya komai tsaf sannan y’a shigo tare da jan mortar suka dauki hanyar gida,Ummi na son yi masa Godia saidai bakin ta nayi mata nauyi,domin bata ma san ta ina za ta fara masa godiyar ba,domin dawainiyar tayi yawa,tana zancen zuci tare da yaba kyan hali irin na Nameer ta ga an yanko kwanar unguwar su,tun daga farkon layin suka ga mutane cike Wanda abun y’a so ba su mamaki,ba su m’aida hankali ba balle har su tsaye tambaya,Ummi ce ma tace da su kila wani dan siyasan ne ya zo taro saisa aka cika haka,nan Nameer ya cigaba da kutsawa cikin unguwar,Mutane ne cike ana ta kaiwa da kowawa,ganin haka ya sanya hankalin Nameer ya gaza kwanciya har saida ya tsare wani matashi “sannu Malam don Allah ko cikar me ake yi a unguwar nan haka?”saida matashin ya kalli Nameer sannan ya ce”ehhh tabbas yanzu shigo war ka ga duk kan alamu,yooo ai Gobara ce ta tashi a cikin  wata babbar gida a unguwar nan,ni ko ya sunan masu gidan na mance,saidai tun dazu ake ta kokarin kashe wutar saidai abu ya gagara,and abun mamaki irin yanda wutan ke mugun ci,ya ci ace by now duk gidajen makota ya kama,amman zallar gidan ke ci kamar Jahannama”ya kare yana yin gaba abun shi.



  “Ohh ni Indo banda abin yaron yanzu shi ina ya taba ganin Jahannama har ya santa ya kuma san wuta me kamannin ta”..”uhmmm ai Hajiya yaran unguwar nan sai Allah,saidai ki bar su,babu yanda ba muyi da Hajiya à canza mata wanann unguwar amman sam ta ki yarda”murmushi Mama tayi kawai domin sam Ummi ba za ta gane ba,yanzu ko ita ce aka ce za a Gina mata gida a London ko China ta bar gidan da Mijin ta ya gina da gumin shi ai an nemi daru da ita,to haka ne in ka riga ka saba da guri,barin gurin nayi maka wahala,”Allah sarki ko gidan waye yayi Gobara sai Allah,ni wlhy an Kwana biyu ma ban ji ko a labari ance anyi Gobara ba,mostly a sanyi ake samun irin cases din nan,d’aman har a zafi ana Gobaran ne?”Ummi tayi tambayar tana kallon Mama,” hmm wlhy ke dai jarabawa kila ko tsautsayi,gaskia mostly kamar yanda kika fadan ne an fi samun issues din Gobara da sanyi,Ubangiji dai y’a kyauta y’a kuma sa rai be tabu ba,abinda aka rasa kuma y’a dawo musu da shi ninkin banin kin”duk da Ameen suka amsa.



  Wai tashin hankali ba a sanya miki rana,babu ruwan Allah yin abinda y’a so

Y’a ke yi a kuma lokacin da y’a so,hannu na ba zai iya rubuta irin tashin hankalin da duka Yan cikin motar suka shiga ba a yayin da suka nufo gidan Hajiya,domin mutane ne cike,daga gurin da suke suna iya hango hayaki na tashi,wani irin tsinkewa zuciyar Hajiya da Ummi yayi,da sauri Nameer y’a samu gurin parking tare da fita daga cikin motar,ai ko da y’a kutsa cikin mutanan saida gaban shi y’a yanke y’a fadi ganin yanda wuta ke ci a gidan Hajiya,”Y’a salam Ashe a gidan Hajiya Gobarar nan ta tashi,Innalillahi”shine abinda Nameer ke fadi,” wlhy duka duka ko mintuna 40 ba a yi ba fa da fara cin wutar nan amman babu irin ruwan da ba mu zuba ba amman sam y’a ki mutuwa,dadin abun ma ance an ga fitan su Hajiya tun Kwana hudu da suka wuce,an dai yi asarar kayan duniya domin duk Azare in za a yi kwatancen gidan masu kudi sai an sako nan,duk da kasancewar sa a unguwar talakawa amman gida ne me amsa sunan sa na House sai gashi yau sai konewa y’a ke,mun gode wa Allah ma da babu rai a ciki,don Kayan duniya ana iya kara samun Wanda y’a fishi ma,tunda yaron nata me shegen kudi ne”..Nameer dai da ido y’a ke bin mutumin da yayi maganar,wato wasu mutane bakin Rexa gare su,da kyar y’a iya furta “to Allah y’a kyauta,y’a kuma maida Alkhairi “..ai à take mutumin y’a cabe da fadin “kyautawar dai,domin abu kamar Wanda aka yi musu ture,maganar Alkhairi kam zai ma maida ko

In ce da kai y’a ma mayar tunda wuyan ta yaron ta y’a ji abinda y’a faru ne,za ka ga cikin sati biyu zai sanya a gina mata gidan da ta ci uban wanann ma,kai wlhy kudi

Sun yi ne”kai Nameer y’a girgiza tare da saurin barin gurin,mutane ke ban burin kowa y’a mallaki kudi,y’a samu abun duniyar da za a yi karyan rayuwa da shi,ko wani me kudi yawanci burge talaka y’a ke yi,tare da sanya masa DOGON BURI(Littafin Mom Sayyid😌❤️)a Taya shima watarana zai mallaki irin nasa ko ma fiye da na sa,ba tare da tunanin ta wani hanya mutum y’a bi kafin y’a samu kudaden ba,wlhy duk wani me kudi to yana da story behind yanda yayi kudin shi,ko ta hanyar zafin nema,ko kuma gadan su yayi ko kuma ta hanyar kazantattciyar harka,Ubangiji y’a raba mu da kazamar kudi ,sannan y’a rage mana Kwadayi da buri da muke fama da shi ba don halayan mu ba.



   “Small Mom am sorry to say wlhy gidan ku ne wutan nan je tashi,and mutane sun ce kwata kwata ne fi 40 mints da fara cin wutan ba,kuma from nowhere wutan ya fara ci an yi anyi a kashe kuma ya ki ka suwa,so saidai ayi hakuri da rashin da aka yi tunda Alhamdulillah babu na rai ma a ciki” Nameer ya kare fuska cike da alhini.



    “Usmaannnn!Usmanaannn!!Ummi Usmaaan!!!Usmaan na cikin gidan nan Innalillahi wa ina ilaihi raju’un,shikenan shima rasa shi zanyi kamar yanda na rasa Aliyu na,wayyo Allah na wannan wace irin masifa ce “Hajiya ta kare cikin gunjin kuka,wai tashin hankali ba a sanya miki rana,suka ba shaf sun mance Usman na cikin gidan ba, Haba nan take kuka y’a barke bil hakki,domin Hajiya ta gama rudewa tare da fara fita a hayyacin ta,domin sam bata son rasa Usmaan din,ganin duk yanda hankulan su y’a tashi ne,y’a sanya Nameer ce wa Mama ta kwantar musu da hankali pls bari y’a je y’a ga ko akwai hanyar da zai bi,in shaa Allah kuma babu abinda zai samu Usmanun,zuciyar Mama na tsinkewa amman da ke Mata ce ita wanda ke cike da dadtaku tare da dunbun kawaici sai tayi murmushi tare da gyada masa kai irin babu komai za ta kula kar y’a ji komai,har y’a juya ta riko hannun shi kasa kasa tayi murmuring “you should take care of yourself don Allah wuta ba abun wasa bane,Allah y’a tsare ka sanann y’a kare mun kai”ta kare kamar za ta yi kuka,murmushi yayi sanann y’a amsa da “ameen y’a Allah”daga haka kuwa y’a wuce,kai tsaye Nameer inda dandazon mutanan ke tsaye ya nufa,ganin ya nufi gidan gadan gadan yana shirin shiga ne ya sanya suka yi saurin riko shi baya,”Haba bawan Allah ka nustu mana,ga shi a ido kallo daya za a maka a gano lafiyar ka lau,balle ayi tunanin Mahaukaci ne kai,ba ka san abinda ke faruwa ba,in Banda haka baka ganin yanda wutan nan ke ci ne?A kan tsiratar da dukiya abun duniya da za a iya tara wanin su,shine kake shirin salwantar da rayuwar ka?”faucewa daga rikon da suka mishi Nameer yayi tare da kallo Wanda y’a gama maganar yanzu sannan a zafafe yace “wai ku baku da maganar da ta wuce ta Dukiya!!ana ta rai wa ke ta maganar wata dukiya,da wannan yawan magangagun da kuke yi da zuwa kuka yi kuka taimaka mun ko ma Samu mu ceto rayuwar uncle dina da ke cikin gidan nan” da sauri wani yace” Subhanallahi! Wai d’aman akwai mutum me rai a cikin gidan nan?Domin farkon tashin wutan nan muna zaune a nan da kuma sauri mu ka ga fitowan yan aikin gidan, a nan suke ce mana kan su Hajiya yau kusan kwana hudu basa gidan,to ba mu ma kawo akwai wani a ciki ba” da sauri Nameer ya ce “wlhy akwai domin Uncle Usman na ciki” “ ya salam Usman Ashe fa yana ciki,Wayyo bawan Allah daman a taya zai iya samun daman guduwa balle har ya ceta ran shi,amman gaskia yan aikin nan mutanan banza ne kuma sam basu kyauta ba,wato ba su damu ba tunda su sun samu sun taira da nasu rayuwar wato shi ko oho ko”shi dai Nameer mamakin furucin nasu ya ji,domin me ya hana Uncle Usman din kokarin tsira da rayuwar shi har yan aikin suka gudu suka bar shi,ko dai kofofi sun datse ne ,tunda normally doors sukan rufe kirib yayi Gobara,amman sai ya danne mamakin na sa tare da cewa”don Allah ku taimaka mun,mu samu mu ceto rayuwar shi” a take kuwa ya samu goyan bayan mutanan domin duk unguwar kowa ya San kirki da mutunci irin na Hajiya Rakeeba,don mata ce ke cike da dumbin alkhairi ga kyauta,sam abun hannun y’a be rufe mata Ido ba(dadin zama lafiya da mutane ke nan,a rayuwa duk tsanani duk wuya in ka kasance mutumin kirki tare da kyautata muaamalan ka da jama’a to wlhy za ka rayu cikin farin ciki da Jin dadi,domin duk Sanda ka yi kokarin m’aida matsalan wani naka to ba shakka duk Sanda wata matsala ta same ka za ka ga sai yanda karfin su ya kare,duk Wanda za ka zauna da tabbatar zuciyar ka daya sannan ka kyautata masa muaamala in ya cutar da kai shi da Allah,amman duk daran dade wa sai ya fadi Alkhairin ka,Allah ka kara tsarkake zukatan mu,sannan ka ba mu ikon zama lafiya da kowa,kar ka bamu ikon cutar da wani kuma kar ka Bari a cutar da mu🤲🏼).


 A take kuwa ba tare da bata lokaci ba suka San yan dabarbarun da za su lulluba kan su tare da shiga wa gidan bayan Nameer y’a sanya an kira yan fire service,ba karamin ci da wuta gidan ke yi ba banda tari babu abinda suke yi Sabida hayaki duk da ma sun toshe hancinansu,cikin iko da yardar Allah kuwa suka nufi cikin gidan gadan gadan,Akan ce normally in ana Gobara doors din gida na rufewa amman lucky them kofar bata riga ta kulle ba,saidai ta yi baki kirin tare da daukan zafi dan ma ba ta karfe bace,haka dai suka Samu suka shige cikin parlon Hajiya da wuta y’a riga y’a cinye komai banda Alquranan da ke gurin,sai kuma abun sallah da Qur’ani da ke aje gefe guda,Wanda xan iya cewa spot din da Hajiya ke yawaita zaman yamman ci ke nan tana karatu tare da yin adduo’in ta,da sauri Nameer kuwa y’a je tare da daukan Que’anan yana me rungume su à kirjin shi,sannan suka shiga kukkutsawa suna me kwala wa Usman din kira.


  Sun wahala sosai kafin Allah ya taimaka su suka tsinto shi kwance akan gado,inda dakin tayi baki wuluk saidai wani iko na Allah ko alamun wuta babu a kusa da shi,balle har ayi tsammanin zai kone,don duk Wanda ya ga irin cin da wutar ke yi to tabbas ba zai dauka Wanda ke ciki zai yi rai ba,tabbas duk Wanda ya rike Allah to kuwa shakka babu Allah ya isar masa,domin ko kadan bakin Usman be gushe ba daga ambaton Allah ko da na second daya,su kan su sunyi mamakin yanda suka same shi kalan shi babu alamun rauni tattare da shi,saidai sakamakon hayakin da ya sha tare da tarin da yayi y’a yi ya haifar mishi da suma,ai ko ba tare da bata lokaci ba suka made hannun Riga tare da kinkimar shi,cikin iko da yardar Allah kuwa duk suka fito lafiya,ba tare da ko wannan su ya rasa rai ba saidai dan raunikan da ba za a rasa ba,a ciki kuwa harda Roméo domin ya kona hannun shi,inda shi sam ko lura da hannun ma be yi ba,zuciyar shi fal farin ciki ganin an ceto rayuwar uncle Usman din,sanann duk wani Qur’ani da ke gidan Wanda wutan be kama shi ba duk saida y’a fito da su,bayan su kam unfortunately komai y’a kone,suna fitowa kuwa kamar Wanda aka hurga bomb,ana jiran su fito y’a tashi,wutan da ke ci ta ninka ta baya!,wata irin nannauyar ajiyar zuciya Mama ta sauke tare da mika godiyar ta ga Allah,a lokacin da ta hango Nameer din ta da mutane a bayan shi d’auke da Usman a hannun su,da sauri Hajiya ta mike suna ma kokarin riko ta,amman ina sam ta ki yadda,”Usmanu na shike nan shima na rasa shi ko?Kamar yanda na rasa me sunan Malam dina,ohhh ni Rakeeba wanann wani irin jarabawa Allah ke yi min nida zuri’ata,Allah na tuba”ta kare tana me fashe wa da kuka,cikin lallashi Nameer yace” Hajiya ga Qur’anan ki nan,ki kwantar da hankalin ki,kamar yanda babu abinda y’a same su saboda kariyar Ubangijin mu,to haka zalika Uncle Usman ma yana nan da ranshi suma yayi sakamakon hayakin da ya shaka amman babu abinda ya same shi”wata wawiyar ajiyar zuciya ta sauke tare da shiga zubo godiya da kirari wa Ubangijin sammai da kassai,ba tare da bata lokaci ba kuwa suka sanya shi cikin mota,ba karamin godiya su small Mom suka yi wa mutanan ba,inda babu yanda Nameer be yi da su kan su karbi kyautan kudi ba,amman sun ce sam ba su san zance ba!da ya matsa ma sai suka nuna mishi bacin ran su,domin ba su ga dalilin da akan dan sun taimaki Hajiya Rakeeba wai sai an biya su wani abu ba,su à matsayin hakkin makota suka sauke,domin Hajiya ta wuci hakan a gurin su,godiya tare da dumbin Albarka su Mama da Hajiya suka sanya musu,sannan suka wuce asibiti da Usman don ba shi taimakon gaggawa ba tare da bata lokaci ba,without waste of any time kuwa aka yi admitting din sa tare da shiga bashi taimakon gaggawa,duk suna zazzaune a asibitin kallo daya za ka musu ka san hankulan su ba kwance y’a ke ba,banda hawaye babu abinda Hajiya ke yi,ta san by now kam yanzu gidan ta ya riga da ya zamo TOKA!she just can’t believe it wai yau gidan ta ne ya kone kurmus haka,tare da zamo wa Toka duk a abunda be wuce hour guda ba,duk wani tunanin duniya tayi shi akan me y’a haddasa Gobaran amman ta kasa samu ko gano musabbabin wutan,kai kawai ta hade da gwiwa tana me jin zuciyar ta nayi mata nauyi,tabbas babu shakka wannan babban jarabawa ce daga gurin Ubangijin ta,in banda haka ace haba abun yayi yawa,masifa daga wannan sai wanann,Alhamdulillah ma doctors sun sanar da su kan su kwantar da hankulan su ba wani abu bane ya samu Usman din,babu abinda take maimatawa sai Istighifari,sallatin Annabi,tare da wasu adduo’in,wai ko za ta dan ji sanyi a cikin zuciyar ta,domin Allah ta tuba wannan jarabawa za ta iya cewa yayi mata tsauri da nauyi,tana dai kan rokan yafiya maybe tayi masa wani laifi ne,tare da rokon shi akan y’a sassauta mata,sanann y’a bata ikon cinyewa.



    A hankali Nadeeya da ke zaune kusa da Ummi ta mike tare da nufan inda Nameer ke tsaye inda har ta iso inda y’a ke be ma san ta zo ba,coz he is so lost on his thoughts,yayi nisa sosai gurin tunanin yanda su Hajiya za su zauna yanzu da gidan su ya riga ya kone,sam shi be san kowa a Azare ba domin wanann shine ma karon shi na farko da ya zo garin,so neman gida a yau din nan zai zamo abu me matukar wahala,saidai ya kama musu hotel su kwana kafin zuwa gobe sai a san yanda za a yi,ba karamin tausayi Hajiya ta ba shi ba,daga kwanaki hudun da suka wucen nan matar nan na ganin rayuwa shock din abinda Mahaifi da Mijin Nadeeya suka aikata be bar ta ba,sai ga wannan kuma,cikin tuananin na shi y’a ji saukan sassanya kuma zazzakar muyan Nadeeya wace ta ke yar siririya a dodon kunan shi “Hey Super hero!”tace tana dan murmushi,idanu y’a zuba mata domin daga zuwan su Azare zuwa yau fuskan ta yayi mugun kumbura sakamakon kukan da ta ci ko in ce ta ke kan ci,haka zalika idanun ta sun yi lufu lufu,sun yi Yan kananu da su,wato a rayuwa zai iya ce wa be taba in ma ya taba to zai iya cewa ya jima ne ga hallita me kyau da tsari tare da daukan hankali irin Nadeeya ba,komai mata me kyau ne,as in she is so perfect,everything about her yayi mi shi,daga kan kyan ta,tsari da zubin halittan ta,murya,tafiya,magana,he just love everything single damn thing about her wallahi,she is just so sweet innocent and beautiful 🤩,barin ma in tayi smilling OMG her smile alone kan iya sanya wa mutum y’a mance duk wata damuwar da ke da shi a doron duniyar nan,ya Riga da ya sani yana Son Nadeeya,Soyayya me tsanani ma kuwa,yana mugun so kauna da kuma jin tausayin ta,bayi da burin da ya wuce a yanzu ya ga ya fallasa mata sirrin zucin sa,and yana fatan ta karbe shi,domin be shirya rasa ta ba,sam be hango zai iya rayuwa babu ita ba,his life will be so boring and dull without her in it,ganin ya zuba mata idanu without talking ya sanya ta dan yi waving hannun ta”Hellooooo”tace da shi,firgit ya dawo hankalin sa,lallausan murmushi ya sake mata sannan yace”Pookieeeee!!!”da sauri ta kalli gefen ta,ganin babu kowa tsaye ne ya ta nuna kan ta as in bata gane ba,irin is this guy referring to me,har yanzu idanun shi na kan ta,ko blinking eyes baya yi,fuskan shi sauke da murmushi ya gyada mata kai alamun yes da ita fa ya ke yi,ganin haka ya sanya ta tabe baki sanann tace “am sorry my bad,ban fada maka suna na ba ko?”da sauri ya ce “na sani already you are my Pookieee,my innocent sweet poookie”da sauri ta zaro idanu tare da nuna kan ta,”you must be mistaken ni dai suna na Nadeeya na wata Pookie ba domin ni ban ma san ta ba,and am here to say thank you for risking your life just to save my uncle’s life,am so so grateful! Kai ya girgiza mata sannan yace”ko raina na bada domin ki sam ban fadi ba wallahi”sam ita kam ba fahimtar inda zancen na shi ya dosa tayi ba,hakan ya sanya ta sakin murmushi kawai tace” actually you are a great man with a pure heart of gold,you are just so nice and kindhearted,ban ma san wani words suka dace nayi using gurin maka godiya ba”saukan idanun ta a hannun sa ne ya sanya ta zaro idanu tare da kasa karasa zancen da ta fara,”oh my God!Can’t you see and feel it” da sauri y’a ce “What?”yana kan kallon ta har yanzu,”your hand,can’t you see ka Kona hannun ka ne,you need to see a doctors right away”ta kare kamar za tayi kuka,ai da ganin haka shima sai y’a tabe fuska tare da shirin yin kuka”Mama naaaaa”y’a fada kamar wani karamin yaro,saidai a hankali ya kira sunan

Maman inda daga shi sai ita ne za su ji,ganin yanda yayi ne ya sanya ta jin tausayin shi,cikin lallami tace “Hey it’s gonna ne alright okay,pls don’t cry big boys ba sa kuka, na san zai yi zafi amman you have to be strong you are a man,Oya let’s go and see a doctor”da sauri ya kanne kafadan sa kamar wata Angel,cikin matso tears din gulma yace”noooo am not going to see any doctor coz all doctors are wicked ,mugunta kawai za su yi mun,ba tare da sun ji tausayi na ba,kawai a bar shi”da sauri tace”who told you that?waya ce ma ana wasa da kuna,Oya let’s go see a doctor ya duba hannun ka,and believe me as a man ba wani zafi za yi maka ba”da sauri ya katse da fadin”If you are the one that is going to attend to my wound then am right yanzu ma let’s get going”harara ta banga mishi sannan tace”are you normal?as in how ni ce zan maka dressing wound din ka,for your own information am not a doctor nor am I a nurse”shima cikin daure fuska yace “okay fine and good tunda ba za ki yi ba,Nima na hakura zai yi healing da kan shi by time passes”goshi ta dafe a rayuwa Anya ta taba haduwa da mutum me irin taurin kai haka,”let’s go”shine abinda ta ce da shi,na me watsa masa harara kasa kasa,in da shi kuwa sarai ya ganta amman sai yayi kamar be gan ta ba,a haka suka nufi Nursing station,a haka kuwa don fitina irin na Nameer dagewa yayi kan lalle saidai in Nadeeya ce za ta yi masa in ko ba haka ba y’a hakura,ala dole dai Nadeeya ta Samu ta gyara masa ciwon na shi,da taimakon wata nurse me mutunci,inda Nameer don iskanci har kukan shagwaba saida yayi mata,inda Nurse ko tayi ta musu dariya domin ba karamin burge ta suka yi ba,har ma saida ta kasa hakuri ta ce da Nameer” amman gaskiya Mr Husband kana da raaki da almau Madam ta fika juriya,ga dukkan alamu,na so yasin Maza ma na haihuwa,da sai nace ta bar maka ka yi guda daya,ko ma Samu mu sha drama lokacin haihuwar,ka ga da ni da kaina kuwa zan karbi haihuwar ta kare tana dariya,inda shima Nameer din dariya y’a sanya sannan y’a ce”ai kina ganin tan nan mugun tausayi na ta ke ji bara ta so na wahala ba ko?”ya kare yana kallon ta,tare da daga mata gira daya,tashi tayi tare da ficewa daga office din abin ta, domin in ta biya ta na shi,sai ya cika mata ciki domin ta ga alamun ya fiye son wasa,shima saurin biyo ta yayi,zuciyar shi fess ko banza dai shima ya Samu yayi spending dan Time da ita.



    After Magrib prayer ne Nameer ya dawo da ledojin Kaza da drinks tare da take away din abinci,don ya san dole za su ji yunwa,carpet din da ya siyo a hanyar shi ta dawo wa asibiti y’a siya,shimfida musu yayi gefe guda inda babu mutane sosai,samnan suka zazzauna ya bai wa kowa abincin sa,cikin nutsuwa kowa suka shiga cin abincin su banda Hajiya da tayi zugum alamun tunani ma ta ke yi,a hankali Nameer ya zauna kusa da ita sannan yace” Hajiya”dagowa tayi tare da sauke idanun ta a kan shi,a take sai ta ji idanun ta sun tara ruwa,ina ma Abul bait din ta haka ya ke,ina ma yanda zuciyar yaron nan ta ke fari tas haka na Abul bait din ta,domin ba karamin zuciya da halaiya me kyau yaron nan ya ke

da shi ba,Haba ace yaro ne san su,amman dubi irin dawainiyar da ya ke ta faman yi da su,da kyar ta iya budan baki tace”wlhy bani da ma bakin fara gode maka,saidai na ce Ubangiji yayi wa zuri’ar ka da kai albarka,Allah kuma y’a raya ka bisa sunnah da tafarkin Manzon taira,tabbas Mahaifiyar ka ta iya kuma tayi sa’an haihuwa,domin irin ka ake Kira da ‘Da daya tamkar da dubu,yanda ka tsaya kan zuri’a ta kai da fata Ubangiji y’a tsaya maka akan naka kaima,y’a kuma duba bayan ka ko da bayan baka nan”ta kare tana hawaye,da sauri yace”Hajiya don Allah ki daina kukan nan ki Samu ki ci wani abu ki sha magungunan ki,kin ga fa yau kika tashi daga gadon asibiti ba ishasshan lafiya gare ki ba,ga shi kuma kin wuni da yunwa,ga damuwa don Allah ki kwantar da hankalin ki,in sha Allah komai zai tafi daidai”,murmushi tayi masa sannan ta share hawayen ta “Allah yayi maka albarka” “ameen thuma ameen “ya amsa yana me jin dadi har cikin ransa.



 Haka dai da lallami tare da kalamai masu kwantar da hankali tare da sanya wa mutum nutsuwa Nameer ya samu Hajiya ta dan ci abincin,saida ya ga kowa ya ci ya koshi Hajiya kuma da Nadeeya sun sha magungunan su sannan ya tafi masallaci,bayan idarwan shi ne ya dawo suna nan yanda ya bar su,don dadin zaman gurin su ke ji,yanda dan iska ke huro su,guri ya samu gefen Mama ya zauna,sannan ya kalli Small Mom yace” ni kam Small Mom za’a samu Hotel kusa kuwa?Don na ga dare na kara yi,ina son yin payment da wuri in ya so zuwa gobe sai ki taya ni nemo gida ko,kuyi hakuri wlhy ba mu san kowa a Azare ba da mun je kun Kwana can” ai Hajiya bata san sanda murmushi ya subuce mata ba,da jin furucin Nameer din,ita kan ta Ummin saida ta dan dara sannan tace” yoo banda abun ka miye wani har sai ka nema mana gurin kwana,Yan Azare ne mu fa gaba da bayan mu ma kuwa,duk dangin Hajiya da Malam a nan suke fa”ta kare tana dan dariya,shima sai yanzu yake dariyan kan shi, “Ummi ke dai bar Babana wlhy at times in yayi miki wani abun kamar wani yaro dan goye,gashi kuma ba dan fari ba”Mama ta ce tana dariya ita ma, “babu wani yaron goye tausayi ne gare shi,tare da m’aida matsololin wasu na shi “Hajiya ta ce tana murmushi.


  Sai around 9:30 suka kammala hada koman su,sannan suka fito daga asibitin,saida ya biya ya kara siyo musu Kaji da Yan abun da ba a rasa ba na ciye ciye,sannan da taimakon kwatancen Small Mom suka iso har kofar gidan Margayi Mal Ali Abbas(Mahifin Hajiya Rakeeba),rapper Yan dubu daddaya ya ciro guda daya making dubu dari daya,ya  mika wa Ummin sannan yace” Small Mom ga wannan ko wannan acicin za ta nemi abu cikin dare”y’a kare yana kallon Nadeeya alamun da ita y’a ke yi,harara Nadeeya ta galla masa tare da ficewa daga motar domin ta fara gajiya da wannan shishigin da Nameer ke yi mata,da kyar ya samu Unmin ta karba kudin domin ce wa tayi dawainiyar tayi yawa,inda shi kuma y’a bada ne wai ko za su bukaci wanni abun kafin zuwa safiya,godiya da Albarka ta sanya masa sannan tayi mishi saida safe tare da shigewa cikin gidan,don already d’aman ya ce da su ba a gidan zai Kwana ba,babu yanda ba su yi da shi ba amman kunya ne zan ce ko miye ya hana shi Kwana gidan,


Daga shi sai Mama ya rage a motar,inda sai sanya mishi albarka Mama ke ta yi,domin ita kan ta ta sani samun yaro irin Nameer a wannan zamanin yana wahala matuka,saisa a kullum ta ke gode wa Allah,tare da jinjina wa kan ta da irin tarbiyar da ta baiwa Yaron nata,sun dan taba hira da Mama saida ta ga ya fara hamma sannan tace da shi ya je ya kwanta,sannan ya kuma kula,ya samu ya huta gajiyar jikin sa,saida ya tabbatar bata da bukatar komai,sannan su ka yi sallama,ta sauka daga motar,har ya kunna motar ita kuma ta juya ya kwalo mata kira “Maaamaaa”juyowa tayi “kai Babana da hankalin ka kuwa?Cikin dare kana shouting name dina haka”dariya ya fashe da shi,sannan yace “Make sure to take care of My Pookie pls,and don Allah Mama no matter what kar ki kuma barin ta tayi kuka,kuka y’a isa haka “da gama fadin haka ya ja motar na shi tare da saurin barin gurin,baki bude Mama ke bin bayan motar da kallo,Ah lalle Nameer wato soyayya na neman fitsara mata da yaro,domin tana ankare da irin mayatattcen kallon da y’a ke ta bin Nadeeyar da shi,oh zamani ita kan ta ta rasa wani irin so ne haka dan nata y’a ke yi wa wannan pookieen,kai ta girgiza sannan tace “dan nema ai da ka tsaya,wai Babana ni zaka kalla kace wai na kular maka da Pookiee in ka,ko ina kunyar ta ka ya tafi oho”wata zuciyar ce tace da ita,ina fa zai ji kunya yi masa uzuri kawai giyar soyayya ke dawainiya da shi,after so many years dole yayi farin ciki,”Ubangiji ya sa Pookiee din nan rabon ka ce Babana,Allah ya sanya mata son ka da tausayin a ran ta kamar yanda kake kaunar ta,Ubangiji yayi muku albarka ku duka,ya sa kuma Alkhairi za mu hada”ta kare da shigewa cikin gidan,Ummi ce ta kai mata ruwan wanka tare da kara gyara mata dakin da za ta kwana,tare da sanya mata maganin sauro domin yanda ‘dan ta ke nan nan tare da kula wa da su,suma ya ci su nuna mata karamci,haka Yan uwan Hajiya suka yi ta shigo wa ana jajanta abinda ya faru,tare da kawo musu abinci da abun sha,saidai duk babu Wanda ya ci abincin domin a koshe duk suke,nan aka zauna ana ta zance tare da yin murna da barkan dawowan Nadeeya,haka suka dinga nan nan da Mama tare da yi mata addu’oi masu dadi,da kuma dumbin godiya bisa kula da rike Nadeeya da amana da tayi,sai around 11:30 kowa ya shige dakin baccin sa,tare da barin su Hajiya su huta gajiya.


Idarwar Hajiya daga salla ke nan ta gama lazumomin ta,ta juyo tare da kallon Nadeeya da ta lafe a jikin Ummu idanun ta rufe sai sauke ajiyar zuciya ta ke ta faman yi,a hankali Hajiya tace “Nadee zo nan”mikewa Nadeeya tayi tare da Isa inda Hajiyar ke zaune akan abun sallahn ta,durkusawa tayi cikin siririyar murya tace “here i am Hajiya”bude arms din ta Hajiya tayi tare da ce wa “come over here”ta nuna mata hannun nata da ta bude,da sauri kuwa ba musu Nadeeyar ta fada jikin Hajiyar inda ta kankame ta kam kamar me shirin m’aida ta ciki,sai kuma suka fashe da kuka a tare,kuka suke me ratsa zuciyar me sauraro daga gani da kuma jin kukan za ka tabbatar daga cikin kasan zuciyar su suke yin ta,a cikin su babu me kokarin lallashin wani,kam kam Nadeeya ta rike Hajiya tana kuka,inda ita ma Hajiyar haka ne,Ummi na daga gefe tana kallon su bata yi kokarin ba su baki ba,balle ta hana su kuka domin ta hanyar kukan ne kadai za su dan ji sanyi cikin zuciyar su,ita kan ta hawayen ta ke sharewa domin she is just trying and pretending to be strong ne amman abubuwan da Nadeeya ta fadi game da Rilwanu ke ta dawo mata a kai.



Cikin kuka Hajiya tace “am so sorry Nadee dee,ki yafe ni don Allah,I have failed you”domin babu abinda zuciyar ta ke yi banda zafi,a abunda ya faru ta kasa daina ba wa kan ta laifi,tabbas da ta tsaya tayi wa Rilwanu jan Ido ta rike Nadeeya a gurin ta kila da bata shiga halin da ta ke ciki yanzu ba,ko ace da ta m’aida hankali da tunani akan ta,tare da lura da yanda take gudanar da lamuran ta kila da duk haka be faru ba,yo kamar Wanda Rilwanun ya shanye tunda ya tafi da Nadeeyar daga gidan ta,bata kuma bi ta kan ta ba,balle ta san ya halin da ta ke ciki,balle maganar ilimi da karatun ta,duk sanda sukai waya dai ta kan ji tana cikin koshin lafiya shike nan sai ta nade kafa ta zauna Akan hakan,tabbas tana da laifi domin za ta iya cewa ita ma ta bada nata gudumawar a lalacewar Nadeeyar,don banda haka ina za ta bar wa Rilwanu shi kadai ba mata ba tarbiyar yarinya mace,babu abinda in ta tuna yake Kara sanya ta kuka kamar wai ace kamar Nadeeya da za ta iya kai wa 25 years bata da ko Izu daya daga cikin Al-qur’ani me girma,balle ace Haddisan Manzon Allah ko kuma sauran littatafai,yau dan Mahaifiyar ta ta mutu shike nan suka banzantar da tarbiyar ta,yau da ta mutu duk sai tai shariah da su à gaban Allah,kuka ta kuma fashe wa da shi tare da kara kankame Nadeeyar da ta ke jin kaunar ta da tausayin ta na ninkuwa a cikin ran ta……….




    Ayi manage da wannan in sha Allah mun kusa gama wa dai,duk mu huta🥰



    A Taya ni sharing sauran groups pls🥺,sai kuma in an Kwana biyu in Allah y’a sa mun kai,and ayi hakuri da typing errors.



Ina yi wa kowa fatan alkhairi.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


     

Kofa a bude ta ke ga me son yin joining Saidai pls Banda maza and bana son talla 🥰



    https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0


My what'sapp group link,you are all welcome to join amman Banda maza pls .


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


            08100046388


******************


    Tallah! Tallah!! Tallah!!


   

   Ina uwar  da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


  Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


   Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


    To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


         08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌


...........

          Page fifty two


***************



       "Nadeeya am so sorry don Allah ki yafe mun",da sauri Nadeeya ta rufe wa Hajiya baki sanann ta shiga girgiza kan ta idanun ta har yanzu na zubda hawaye tace "Hajiya can you stop apologizing pls,ni fa ba ki mun komai ba,Daddy and Afzal ne suka

cutar da ni,and I don't think I can ever i forgive them for that", "tabbas Nadeeya abunda suka miki ba su cancanci yafiya ba saidai fa in da na su nima nan da laifi na,a matsayi na na kakar ki wace ta san ya kamata tare da ilimin addini wlhy na kasa sanin a garin yaya na bar ki a gurin Abul bait har ya lalata miki rayuwa har haka,Nadeeya baki iya alola ba,baki iya salla ba,ba ki iya tsarki ba balle wanka bayan gama al'ada aje na janaba a gefe,cikin kuka ta cigaba da fadin cikakken saurori biyar ba za ki iya karanto su ba daga cikin qur'ani,babu haddisi fiqhu balle tauhidi a tattare da ke,rayuwa kike kara zube kamar wata dabba,a baki dai kike amsa sunan musulma amman am very sure ko 5 pillars of Islam ba sanin su kike yi ba,balle a zo ga maganar girki,to uban ki be koyar da ke hanyar da za ki bi duniya da lahiran ki su yi kyau ba wa ke ta batun girki,na yi danasanin mika masa ke da nayi kina yarinya,da ace na jajjirce na rike ki guna da duk haka be faru ba, da ace kina guri na na san no matter what da yanzu kin yi sauka 5 ko fiye da haka,amman ace a shekaru irin naki ko tsaida salla baki iya ba"sai ta kara fashe wa da kuka,ita ma

Nadeeyar kuka take kamar ran ta zai fito,sai yanzu ta kuma yarda tabbas Sen ya cuce ta,ya so ya sanya ta zo duniya a banza ta koma a wofi,me ake da uba irin nata,duk wani dadin duniya babu Wanda bata ji shi ba,kasashe har mance wa ta ke da ta je wasu,duk wani gogewa da waye wa da ake nema har ma ta wuce nan,amman fanin addinin ta zero,domin babu abinda ta sani game da wannan,wani irin kunya da nauyin Ubangijin ta take ji,yau in da ta mutu me za ta ce da shi,muryan Hajiya ne ya katse mata zancen zucin ta "har yanzu Nadeeya kunnuwa na sun kasa gasgata mun maganar da kika yi akan Mahaifin ki,tabbas biri yayi kama da mutum,hakika nin gaskiya ko ni irin kudin da Abul bait ya same su a dan kankanin  lokacin nan,ni ki na abun ya kan bani mamaki matuka,saidai a duk sanda nayi tunani ko yunkurin yi masa magana sai na ji baki na ya mun nauyi,duk laifi na ne,da ban m'aida Ido sosai Akan shi tare da sanin wani hali ya ke ciki ba,duk a sunan wai karar dan fari,sannan na zo na banzantar da lumuran ki,hakkin mu ne nema miki miji na gari Wanda zai zamo uba na gari wa yaran da za ki haifa,amman a bisa sakaci na kika kare da wannan mugun jahilin dan Luwadin"kuka duk suka kara fashe wa da shi sanann Hajiya ta cigaba "na kasa yarda wallahi wai 'dan da y'a fito daga cikin ciki na ne y'a aikata wanann danyar aikin,Neman jinsi??Ace neman ma ka rasa Wanda za kayi da shi sai Sirikin ka mijin yarinya ka,wannan wani irin masifa ne,sannan babu abinda in na tuna ke Kara ci mun rai kamar in na tuno wai Abul bait shine y'a kashe Bahiyya lahaula wala kuwata ila billah,yanzu ace jini na yaron da na dauka na raina a ciki na shine y'a san daukan rai da hannun shi"sai ta kuma fashe wa da kuka,kankame ta tsam Nadeeya tayi sanann ta shiga goge mata hawayen ta, "Hajiya don Allah kiyi shiru ki daina kukan nan kin ga zuciyar ki bata da Lafiya kar wani abu ya same ki"cikin shasheshekan kukan Hajiya tace "Bari ni Nadeeya barni nayi wlhy ta hanyar kukan ne kadai zan samu sassauci daga zafi da radadin da zuciya ta ke yi mini,ai kuka ya  za me mun dole,ace wai daga ciki na na haifo wanann masifa,inalilahi Allah na tuba Allah ka sassauta mun wannan jarabawar ta yi min tsauri wlhy,da me zan ji eheyy Nadeeya ai dole nayi kuka,babban yaro na ne fa,da nake masa kallo da uban sauran yara na,Wanda na san ko bayan bani zai tsaya ya kula min da yara na,yanzu Akan neman duniya ne Abul bait ya mance da Allah tare da lahira,sanann ya mance inda ya fito,ina addini da sanin Allahn sa suka tafi?Kullum yana nan yana mana lubo lubo Allah a baki Fir'auna a zuci,ya mance daga wani zuri'a ya fito,da fadin Azare da Bauchi babu Wanda be san waye Mahaifi na ba,ta fanin addini amman ace wai yau jikata cikakken sallah ma baki iya ba,babu shakka ya cutar da mu,sannan ya zalunce ki"ta kare tana kuma fashe wa da  kuka,domin ji take kamar zuciyar ta zai fado,wai Rilwanun ta ne ya koma haka,to ko dai da gasken kungiyar asirin ya shiga,idanun shi sun rufe Akan neman duniya ya saida imani da mutuncin shi,idan har yayi hakuri ma duk wani abun da ya mallaka daman can Allah ya rubuta rabon shi ne,ba zai taba mutuwa ba sai ya same su,kuma ya gama cinye su,tunda tun ran da aka halici bawa  Allah zai sa a rubuta adadin arzikin ka,sannnan sai ka cinye tas kafin ka koma gare shi,Wanda ka ga baka ci ba ka mutu,d'aman can Allah yayi ba rabon ka bane,y'a shiga Kayan magada,domin yanda ajalin ka ke neman ka,haka ma robon ka ke neman ka,zan iya cewa ma rabon y'a fi,me yasa Rilwanu ya kasa hakuri ya jira lokacin da Allah ya kaddara zai samu wannan tulin dukiyar ta hanya me kyau,ya zabi da ya kwauce wa hanya don kawai yayi gaggawar mallakar abun da ya ke rabon shi ne already.


Cikin kuka Nadeeya ke lallashin Hajiya tana bata baki "Hajiya  Sen sam be kyauta ba,domin daga yau ba zan saké hada suna na da nashi ba,ko kuma in Kira sunan shi,ko in danganta shi da ni ba,domin duk duniya babu abinda na tsana sama da shi,ya cutar da ni cutar wa mafi girma,ya kasance mugu kuma azzalumi,kuma ba zan taba yafe musu ba musamman shi na kashe mun Mahaifiya da yayi,ya sanya ni tasowa babu uwa,ya maida ni marainiya tun Ina yarinya ta,saidai in na tuno wani abu y'a kan sanya na ji sanyi da sauki a cikin rai na,domin big Daddy tsaye y'a ke a kan kafafun shi gurin ganin sai y'a kwato mun hakki na,na san koma yaya ne ana nan ana shirye shiryen shigar da karan su court inda judge zai yanke musu hukunci daidai da abunda suka aikata" , cikin sauri Hajiya ta ciro ta daga kirjin nata, cikin sanyi murya tace "why me yasa Nadeeya kika kai karan Mahaifinki court?Ko ba ki san by doing that asirin mu baki daya kika watsa a duniya'' "Hajiya i get no option ne,and Big Daddy ne ya ce da ni wannan shine daidai abun da za ayi wa Sen,kuma by doing that zan samu in zama free from this so-called Auran da ke tsakanin mu da Afzaal,am very sure in aka shiga court dole ya sake ni”ta kare tana hawaye, “na san basu kyauta miki ba my dear amman kai su kara court ba solution bane,and in duniya da gaskiya kuma ai Kabiru be dace yayi wa Abul bait haka ba,domin in har aminin gaske ne duk iya yin shi sai yayi don ganin asirin mahaifin ki ya rufu ba wai ya zama shine me bada gudumawa tare da taimakawa gurin ganin ya tona masa asiri ba,ni daman can wallahi ba kaunar yaron nake ba,kawai babu yanda na iya ne ya sanya na zuba wa amintar nasu ido,domin budewar idon yaron yayi yawa,and babu yanda ma zai ce be san abunda ke faruwa ba,domin yanda suke very tight da Abul dole zai sanar da shi,tunda shi sam ba hankali da sanin yakamata ya fiya ba,ba yi da wuyan yarda da mutum tare da daukan duk yarda ya  ba shi,nayi matukar mamaki da jin wai Kabiru ne yayi haka,sam shi ya sanya bana son yaron sam be kwanta mun a rai ba,amman fitina da naci irin na Mahaifin ki ya sanya ya ki rabuwa da shi,gashi ai shi ya tsaya kai da fata gurin ganin sai ya tozarta shi,tare da bangada asirin shi a duniya,a irin amintakan da ke tsakanin su na tun yarinta,ya ci ace in wani ne yace zai tona wa Sen asiri ya zama sai inda karfin shi ya kare,shine abota na gaskiya,and tabbas ina zargin shi,domin in ba rami me ma zai kawo batun rami,a taya kuma a ina ya san Sen yana cikin kungiyar yan shan jini?Jiki na bari harda sanar miki,in da gaske ma yana kungiyar a mu ya kama ta ya zo ya fada wa ba ya kai kara court ba,amman babu komai Allah shi ya san daidai da kuma komai”ta kare  tana me dada janyo Nadeeyar cikin jikin ta,inda ta ke dada jin kaunar ta da tausayin jikar nata na dada karuwa cikin ran ta,daga  yau Allah gatan su ita kuma za ta zamo gatan Nadeeya,za ta tsaya akan kafafun ta gurin ganin ta bata rayuwa mafi inganci,bayan ta ta shiga shafawa a hankali,tun tana jin sheshekan kukan ta har ta koma sauke ajiyar zuciya,tare da sauke numfashi,hakan ne ya tabbatar wa Hajiya tayi bacci ke nan,ta dade tana karewa Nadeeyar kallo tunanuka da yawa na kai kawo a cikin ran ta,kafin can ta tofe ta da Azkars din bacci,domin ta san ba iya su tayi ba balle har tayi wa kan ta,a haka dai tana yan adduoin ta har bacci ya dauke ta,tana jingine da jikin gado yayin da Nadeeya ke rungume a kirjin ta,domin ko kusa bata fatan abinda zai kuma cutar da ita,domin a  yanda ta ke jin ta yanzu indai akan Nadeeya ne sai yanda karfin ta ya kare.


 

         ********************************


     Cikin sauri ya fito daga cikin toilet din da ke dakin,towel daure a waist din shi,karamin towel ya dauka ya hau goge ruwan jikin shi,mai ya shafa da hanzari sannnan ya dauko doguwar wando ash color tare da jira ash long jalabiya akai,agogon dakin ya kalla da ke manne jikin bango,ganin lokaci na tafiya ne ya san ya shi kara sauri domin ko kusa baya son rasa flight din sa,don a yanda ya ke ji babu abinda zai hana shi barin kasar Nigeria sai mutuwa,domin guje wa tonuwar asiri,ko kusa be hango kan shi cikin court gaban Alkali ana mishi titsiye akan case din neman jinsi (Luwadi,ya Subhanallah),to ma ya fara kallon mutane da wani ido,ba zai taba yuwa ba,ya gwammaci yin nisa da kasar tare da komawa ko da can New York ne ya koma sabuwar rayuwar,domin ta fi nan ddi da Yanci,but for now ya ci ya kara sauri domin in ba mistaken yake yi ba yau ne za a fara hearing case din su,ba tare da bata lokaci ba,ya gama hada kan komai na shi,domin be ga abunda zai dawo dashi Nigeria nan kusa ba,farar Hirami ya dauko tare da daurawa a kai,sai ya sanya Black new face mask a fuskan shi,idanun shi kawai ake hangowa,tare da black cover shoe  a kafafun shi, Ai ko sai ya fito kamar wani Terrorist!cikin sauri ya dauki suitcase din shi tare da fitowa,don gujewa samun matsala ya sanya shi shiga sabuwar motar shi wanda babu wanda ya san ka da shi,kai tsaye ta boyayan hanya da ba wanda ya san da hanyar sai shi,direct airport ya wuce,babu abinda y ke yi Banda murmushi da sauke ajiyar zuciya ganin ya iso airport din,domin gani yake a daidai wannan lokacin duk wata rikici ko damuwa tare da matsalolin shi sun zo karshe,ba tare da bata lokaci ba ya fito tare da bar wa security key,akan ya rike mishi yanzu friend din shi da ya kira a waya yana kan hanyar shi,zai zo ya dauki motar,ran shi ba karamin dadi yayi ba ganin ba a basu bata lokaci gurin Boarding ba,nan aka gama komai,sannan suka shige jikin jirgin da zai kai su Abuja daga nan sai su wuce can kasar.



Wawiyar ajiyar zuciya ya sauke a yayin da ya gan shi zaune kan seat inda yake kusa da window,sai a wannan lokacin ya samu nutsuwa,nan ya dauko wayar shi  misses calls ne rututu saidai majority calls din Sen Rilwanu Audu waziri, tsaki ya ja tare da dafe goshi sannn ya shiga message din sa.


Number din Sen Rilwanu Audi Waziri ya danna sannan ya fara rubuta mishi message kamar haka ‘ Hi Sen Rilwanu Audu Waziri I don’t have so much to spend asking how are you doing,coz ba shi ne a gaba na ba actually I will just want to go straight to the point,by the way it was so so nice meeting you but sincerely speaking am tired of staying with you and unfortunately yau ne ranar rabuwar,domin ban ga dalili ba akan old hag irin I can’t risk my life to be in prison forever,am to young and for that,as you already know my skin is so fresh da ba zai iya juran wahalar gidan yari ba,by the way ka manyanta already so ba wani dade wa za ka yi ba a can za ka mutu shike nan ka huta ,but what about me??na san I might sound selfish but ba yanda na iya ne idanu na sun yi budewar da son jin dadi kawai nake hangowa and thanks to you,kai ne silan komai,so I want you to forgive and forget me if possible without holding any grudges duk da na san abu ne me matukar wahala ka manta ni domin ko banza an gurji juna,amman maybe if you are lucky enough ka samu wani a can prison din y daura daga inda muka tsaya,domin na gaji da cin kyamusheshen tsoho irin ka me budurwan zuciya (Ya salam🥹)don haka zan je in nemo irin taste dina matashi me kananun shekaru,ko na ce dan sugar boy dina wanda bayi da katon tumbi irin naka,so by the way na mance ban sanar da kai ba,a matsayi na na na karuwar namiji wanda kake fucking babu dare babu rana, na ibi makudan kudade da za su ishe ni in yi sabuwar rayuwa ta babu kai,daga cikin account din ka,ko ban fada ba ka san ladan karuwancin da muka yi ko in ce na more ni da kayi ne,so pls ina so ka mance da ka taba sanin wani me suna Afzaal from now on a rayuwar ka,domin nayi gaba and bana fatan kara hadu wa da kai har gaban abada,thank you for making me rich 🤑,my regard to that stupid Ex wife of mine(Nadeeya) ,sincerely yours “Afzaal”.


   Wata yar dariya ya sake a lokacin da ya ga message din ya tafi,Yana me jin zuciyar shi wasai ko banza Sen zai ji abunda ya ji a ran shi time din da ya ke dukan shi kamar jaki,yanzu ya nemi abun duka ai,domin babu abinda zai kuma hada shi da Sen ya yarda kwallon Mango ya huta da Flies,a take ya sanya wayar ta shi a flight mood,sannan ya fara goge gogen duk wani videos,pictures,tare da love messages da suke exchanging wa juna,domin sam baya son barin wani memories din su,balle in ya fara new relationship ya zamo suna samun matsala wai maganin bari aka ce kar ma a soma,shiru yayi tare da zubawa wasu bakaken mutanen da ke gefen shi ido,da wata bakar jaka a hannun daya daga cikin su,haka kawai ya ke jin son sanin abun da ke a cikin jakar,wanda kallo daya za ka wa mutanen su baka tsoro,domin sun yi kama da Terrorist,ganin kallon da ya ke musu ne,ya sanya kamar hadin baki suka sake mishi wata wawan kallo,ya sanya shi saurin kau da kan shi gefe,tare da dina kallon na su,domin a yanzu bayi da burin da ya wuce ya ga jirgin su ya tashi,don haka kawai zuciyar shi ke ta faman bugawa.


 

   A daidai lokacin da jirgin na su ke shirin tashi ne,aka yi sanarwa kan kowa ya kashe wayo yin sa,saannan a saka belt domin jirgi na neman tashi,aka yi saurin dakatar da matukin jirgin,a take kuwa aka baiwa passengers hakuri akan yan sanda ke son shigowa su yi bincike,domin ana zargin Yan ta’adda na cikin jirgin,da jin haka kuwa mutane suka rude,aka shiga kallon kallo,kafin ka ce me,motocin yan sanda da yawa sun yi parking,ko wannan su sanye da uniform tare da bindigogin su,nan aka ce kowa ya zauna a position din sa kar kowa ya motsa,domin zasu shigo bincike ne,ana zargin Terrorist na cikin jirgin wanda suka gudo daga prison and suna dauke da miyagun makamai harda bombs tare da harmful drugs a tare da su,ba tare da bata time ba kuwa polices din bataliya guda suka shiga shigowa cikin jirgin,inda aka nemi kowa da ya zauna a kan kujeran shi,nan suka fara bin seat by seat suna bincike tare da duban criminals din,mutanan da ke zaune gefen Afzaal hankulan su ba karamin tashi yayi ba,domin tabbas sune Criminals din da ake nema,and tabbas in aka kama su sun shiga uku,sam basu fatan abunda zai jawo a maids su bayan duk bakar wahalar da suka sha gurin trying guduwa,ganin an yo kan su gadan gadan ne ya sanya su saka black face mask din su,ogan su ne ya rada wa wanda ke rike da jakar magana a kunne,ai kuwa da sauri ya mike yana kokarin guduwa hakan ne ya yi nasarar janyo attention din yan sandan da sauri kuwa suka nufo shi,ganin haka ne ya sanya shi saurin gefa bag din gurin seat din Afzaal kafin kace me ya shige kasan kujerar,sabida hayaniya ya sanya babu wanda ya lura da hakan inda har shi Afzaal din ma be lura ba.


Rikici ne sosai ta balle tsakanin Polices din da su yan ta’addan domin bude wuta suka yi ta ko wani hanya neman tsira kawai suke yi,a sakamakon haka unfortunately su ka harbe police har hudu,ba karamin daga wa mutane hankali suka yi ba,tare da sanya musu tsoro da firgici,kafin Allah ya basu nasaran capke su,tare da yin waje da su,a gefen su kuwa ko a jikin su duk da an kama su,sun samu sun yi wayon aje jakar su a kasan seat din Afzaal domin duk wani important abubuwa na ciki,in ya so sai su san yanda za su yi su sami waya don kiran Ogan su,don ya san yanda zai yi ya dauki jakar tare da nema musu hanyar fita don sam ba za su kuma yarda su yi zaman gidan yari ba,yan sanda na kokarin shiga motocin su ne,Ogan su ya tsayar da su,nan ya ce da su,ya ci su koma a karasa checking din jirgin tare da sauran mutanen da ba a yi searching din su ba,saboda gudun samun matsala,domin ba karamin shedanu bane su kuma yanda suka yi saurin yin relaxing haka dole kila akwai sauran mutanen su ka badda kama a cikin jirgin,ai ko a tashe hankulan su yayi mugun tashi da jin furucin Ogan yan sandan,amman kuma babu yanda suka isa yi saidai zare idanu suna fata kar a samu jakar,har sai Bomb din da suka yi activating ya tashi,nan ko ba tare da wasting time ba duk suka koma cikin jirgin inda aka kuma baiwa passengers hakuri,sannan suka cigaba da searching din su,wai aka ce me rabon Shan duka,ko in ce tsautsayi in yana bin ka saidai kawai ka gode wa Allah,har sun juya  fa za su tafi,daya daga cikin su yace wa Ogan “Sir ni fa haka kawai nake zargin wancan yana daya daga cikin su domin yanda ya kame guri guda shi kadai,and kusan irin shigan su ne a jikin shi,sam hankali na be kwanta da shi ba”ya kare yana me pointing din Afzaal da yayi saurin zaro idanu jin abunda police din yace,,a take kuwa suka dira gaban Afzaal don saida yayi magana ne duk suka ga fa yayi kalan zargi kam,gashi kuma yana sanye da face mask,nan ko umurce shi da ya mike,bakin shi har na rawa gurin furta “Oga sir me me nayi,can i know my offense pls??Na rantse da girman am not a criminal and am not one of them ban san su,ba su son ni ba don Allah let me be,am an innocent and also a responsible person”ya kare zuciyar shi na bugawa kamar me shirin yin kuka.


Harara daya ya maka mishi sannan yace “wannan sai after an gama searching din ka ne za mu sani kuma mu yarda you are indeed innocent ko kuma criminal kamar yanda ka fada,now zip up that mouth of yours kafin in fasa ma kwakwalwa”ya kare yana zaro mishi red eyes din shi,jikin Afzaal banda bari babu abinda ya ke yi,daga haka suka hau searching din jikin shi,ganin ba su samu komai bane ya sanya shi sauke wata wawaiyar ajiyar zuciya tare da yin hamdala,da sauri yace “ I told you daman,haba I told you daman am innocent ni bana daya daga cikin su,gashi yanzu after searching me baku samu komai…..maganar ce ta makale masa a makogoro jin wani yace “Sir have found this under his seat”ya kare yana nuna jakar tare da mika wa Ogan,”Mr am so innocent what can you say about this?”Ogan ya kare yana bin Afzaal

da ya firfito da idanu kamar an shake shi da kallon tabbas yau za ka ci uwar ka har ma da uban ka a hannu na,da sauri ya ce da mutane su yi shiru,saboda hayaniyar da suke yi,sannan ya umarce

su da suyi baya,domin yana jiyo yar kara daga cikin jakar,ko da ya bude kuwa mutane sai kuka da Ihu suka saka suna masu tsine wa Afzaal sakamakon arba da Activated Bomb 💣 da suka yi arba da shi,tare da miyagun kwayoyin shaye shaye da kuma hodar ibilis,already daman daman da yan Anti bomb team suka zo,don kamar sun san za a yi haka,inda da sauri aka shigo da su,da ke sun kware ba tare da bata lokaci ba suka yi deactivating din Bomb din da ya rage saura 3 mints ya tashi,nan aka hau godiya wa Allah guri ya rikice domin iya tsoro da firgita mutane sun shiga abu kamar a film,masu kuka nayi,ma su salati,ganin haka ne ya sanya Ogan daka musu tsawa sannan suka nutsu,nan ya ce da su “you are good to go now,and ina son kowa ya nutsu ya kuma kwantar da hankalin shi,things are under our control now,so babu abinda zai same ku,and ina me baku hakurin daga muku hankula da muka yi yanayin aiki ne ya zamo dole sai da haka,at the end ina wishing naku peaceful and successful journey Allah ya kai ku lafiya”daga gama fadin haka kuwa guri ya dau tafi,domin yan sanda da sojoji abun a yaba musu ne,yanda suke risking rayuwar su don aAl’ummah,ubangiji ka dada tsaya musu tare da taimakon su sannan ka dada shirya su tare da tsare musu imani,mutunci,dukiya,da kuma iyalan su.



  Nan suka tiso keyar Afzaal da shock ya gama kama shi,banda faman rantse rantse akan sh babu abinda ya sani kan jakar fa ba ta shi bane,hasali ma shi me kama da ita ma be taba gani ba,ganin ya dame su ne ya sanya aka daka mishi tsawa,tare da cewa yayi musu shiru sannnan zai fi masa kyau ya adani kalaman shi,domin za su yi masa amfani a court,don duk abunda zai fada yanzu can be use against him in the court of  Law!haka yana ji yana gani aka sanyo shi a mota sai police command,wai aka ce in ka ga baka iya kuka ba uwar ka ce bata mutu ba,sannan hawaye ma ashe rahama ce,domin ko kadan hawayen ma kasa zubo masa suka yi,yau wace irin muguwar lukutin bala’i ne haka,wani irin taka sawun barawo ne yayi haka,ko kadan sun gaza yarda da shi,domin har yan ta’addan an tambaya kan sun san shi,nan duk da ke babu Allah a ran su suka ce sarai sun san shi,yana daga cikin manyan leaders din su ma,baki bude kawai Afzaal ke bin su da kallo,da iyanzu ya koma kamar mutum mutumi,haka yana ji yana gani aka jefa shi cikin cell,(Ni ko nace Madallah kadan ma ka gani dan iska,wai har kana tambayan me kayi?Daman an ce maka taba Allah wasa ne,kayi mafi muni da girman laifi wanda Ararshin Allah kanta girgxa take duk sanda aka aikata Luwadi sannan kayi tunanin karewa lafiya,dadina da Allah wani hisabin tun a duniya yake fara yi wa bayin sa,kafin a je can,Allah ka dada shirya mu,ka sa kuma mu fi karfin zukatan mu,sannan ka ba mu ikon gamawa da duniya lafiya).




             ****************************AZARE


     Early in the morning ya shigo gidan da kaya niki niki,domin hado musu kayan breakfast tare da kayan sawa,don sanin da yayi kayan su kaf ya kone,fada sosai Hajiya ta hau shi da shi domin ganin dawainiyar Nameer din da ya ke yi da su ta yi yawa,inda shi kuma ya nuna mata babu komai ai,albarka sosai ta sanya masa,tana jin kaunar yaron har cikin ran ta,domin nutsuwa tausayi tare da taimakon da sanin ya kamatan yaron suna matukar burge ta,tabbas Nameer ya cika ‘Da wanda ko wace Uwa za ta yi burin samun irin shi.



   Bayan duk sun yi wanka sun kimtsa ne,aka fito ana karyawa,Inno Sa’adatu Matar ya yar Hajieeya Rakeeba ce ta shigo,guri ta nema ta zauna sannan suka shiga gaisawa,ganin bata fita bane ta mike kafafu ya sanya Hajiya ta gane magana ce dauke a bakin ta, ai kuwa as expected ta ji ta fara “ohhh sannu Rakeeba ashe abubuwan da suka yi ta faruwa ke nan,Wayyo kun ga masifa ganin idanun ku ku kam”kallon ta Hajiya tayi domin wai ana cewa sanin Hali tafi kama,don fa Inno haka take tun tuntunin ta bakar munafuka ce me kuma masifan son jin gulma da kuma ya’da zance.



“Ba dai masifa ba jarabta ce daga gurin ubangiji and tunda har yanzu muna a raye ai Alhamdulilah dukiya a duniya muka same ta,in Allah y kuma so za mu sake samun wanda ya fi na da ma” da sauri ta yanke ta “ aa Rakeeba ni fa ba ta wannan nake ba,a labarai nake jin wai ashe Abul bait an shigar da shi kara court,akan wai ya kashe mahaifiyar Nadeeya sannan yana nema da mijin ta,abun ya matukar girgiza ni,domin sai da na zauna da na ji labarin nayi ta nazari anya Abul din mu zai yi haka,to shine kuma yau da safe na ji an kuma sanar wa wai court ta yi watsi tare da koron karar domin an gano tuggu ake son hada mishi don bata siyasar shi,bincike kuma ya nuna Aminin shi ne ya aikata mishi hakan oh duniya kana tare da mutum na zuciyar shi daban na baki da daban,kin ga kuwa,ai dole nayi miki jajje da kuma barka,sunan yaron mu be baci ba,domin a yanda na ji ma wai an ci Kabiru ya ke ko wa taron kudi masu yawa,ladan bata suna da yayi mishi” ta kare tana washe baki,wata doguwar ajiyar zuciya Hajiya ta ja,tare da gode wa Allah a ran ta domin abun da ta ke gudu ke nan daman tonuwar asirin su sai gashi Allah ya kawo mata komai cikin sauki,he wish dama da gaske ne duk sharri ake wa yaron nata,saidai deep down ta san gaskiya ne,sai da ta kurbi ruwan shayin ta sannnan tace “eh wlhy abu kam babu dadin ji,amman mun gode wa Allah Amintakar yanzu kam majority na karya ne,amman Alhamdulilah tunda an yi watsi da karar kuma gaskiya tayi halin ta,mu ma nan in muka gama kimtsawa da wuri Bauchin za mu shiga,in be yu ba kuma zuwa gobe”, “eh ya kamata mu je din,saboda ko ba komai yana bukatar mu,bari na je na shirya kaya na,kin ga ma muna isa zan yi masa zancen aure duk rashin mata ne ya jawo masa wannan abun”baki bude Hajiya ke kallon ta,wannan mata saidai a bar ta,kai ta girgiza tare da murmushi ko wa ya ce da ita tare za su oho,ganin ta nufi kofar fita ne,ya sanya Hajiya saurin cewa “Inno ai da kin zauna domin tafiya dukan babu amfani,ko dan kula da Usmanu da kin zauna a nan din in ya so sai in mun dawo sai ki je,ko na ce da shi kina neman shi” ba don ran ta ya so ba ta yarda ba za ta je din ba,domin har ran ta ta so zuwa ko dan ta samu ta karasa jiyo kan gurmin kuma ta yako rabon ta,amman babu yanda ta iya domin wani shakkar Hajiyar ta ke ji Allah yayi mata wata irin kwarjini sam ba za ta iya ce mata aa ba,da kallo Hajiya ta bi bayan ta,sannan ta saki tsakin da ba ta ma san ya fito ba domin sam ba dabi’ar ta bane yin tsaki,kallon Nadeeya tayi sannnan ta ce “ in kin gama karyawa ki yo mun kiran Yayan naki (Su Malam Nameerun Mama yayan Pookien sa😂😂😂💃🏻).



    

        *********************BAUCHI 


        9:30 na safiya 



    Zaune Sen ya ke akan dinning table din sa wanda ke cike da kayan abinci kala kala,amman sam ko kallo ba su ishe shi ba,damuwowi ne cike a birnin zuciyar shi,tun safe zai iya cewa da tashin hankali tare da bala’i ya farka,domin tashin shi ma aka yi da kiraye kirayen waya,inda ake sanar da shi Gidajen man shi,tare da Plazas din sa,gidaje sun fi 30 haka kawai aka ga suna kama wa da wuta,an yi an yi a kashe abu ya gagara,ba karamin kaduwa hankalin shi yayi ba da jin haka,don ma Allah ya taimaka shi Lawyer din da Kabiru ya biya ya zago ya sanar masa da komai,inda yayi masa kyautar kudade masu nauyi,yayi mamaki matuka jin wai Kabiru ne ya shigar da karar shi da sunan Nadeeya domin sam bayi da masaniyar Nadeeya ta dawo gari,abun ku da me hannu da shuni kuma masu influence a take ya sanya ka kori karar tare da maida wa Kabiru da ke expecting ganin downfall din shi laifi,don da ba haka ba yau ne za a fara sauraran karar ta su,yana tsaka da haka ya ga shigowar message din Afzaal wanda ya kusa wargaza duniyar sa,domin ba karamin ciwon text din ya ji ba,be taba expecting haka daga gare shi ba,sai gashi abun da ya jima be yi ba wato kuka yau yayi da ganin message din Afzaal din,abun ya zaffafe shi matuka domin ba karamin so da kauna ya ke wa Afzaal din ba,ya gama daukan duk wani so amana yarda da kaunar shi ya damka mashi amman wai shi zai ci amana har dace wa ya gaji da cin old hag irin shi,wato ma shine old hag me katon tumbi,abun ya masa ciwo Wlhy,kuka yayi sosai,har saida idanun shi suka zamo red don masifa goma da 20 ne suka hade masa,bayan duk abun da yayi wa Afzaal a rayuwa sakayyar da zai masa ke nan,ya yarda ya sadaukar da komai har diyar shi duk saboda shi amman ya ci amanar shi a karshe,be damu da ubangiji ko abun da duniya za su ce ba duk ya yarda ya maida Afzaal

Love of his life amman da irin sakayyar da zai masa ke nan,after what they have been through together,sam Afzaal be kyauta mishi ba sannan be kuma masa adalci ba,a yanda ya ke tsananin kaunar shi ko da zai rasa ran shi ne ba zai taba bari a kama shi ba,ko da kuwa shi din za a kama shi,in da ya ma kwantar da hankalin shi ba za su kai ga zuwa court ba ya san abunda ya ke jin tsoro ke nan,amman miye amfanin wannan tulin dukiya da ya tara da uban connections da ya ke da su,sam ba kudaden da ya ibar masa bane ya ke bashi haushi,rasa shi da juya masa baya da Afzaal yayi at the time da ya fi bukatar shi the most ne abun ya sanya shi kuka🥹😂(ni ko na ce madallah shegu yan iska mara sa tsoron Allah ai kadan ma gani tunda kai abun kunya ka sa gaba,ba damuwar ka yanda za ka koma ga Allah ba ka samu kayi murnan rabuwar ku kila silan shiriyar ka ne amman ka zauna kan wa mutane kukan banza kyamusheshen tsoho da kai ke katon tumbi 🫣🤭in ji Afzaal ne ba Meemarh ba,Allah ka raba mu da abun kunya duniya da lahira).



Damuwar da ya hade mishi ke nan har ya haddasa kasa cin abun cin sa,domin salam yake jin bakin na shi ba taste a halin da ya ke ciki yanzu babu abinda zai iya wuce wa ta throat din shi balle har ya shige cikin stomach din sa,yayi zurfi sosai a tunani ya fara jiyo karar wayar shi,ne sau dauk ba da farko saidai ganin yanda aka dame shi da kira,sunan Alh Kabiru ya gani yan yawo akan screen din wayar,tabbas a yanda ya ke jin zuciyar shi babu abinda zai hana kartawa Kabiru bura uba muddum yace zai masa hauka,domin cike ya ke tam da shi kiris yake nema ya samu ya ci uwar sa,domin yayi Allah wadarai da Amini irin Kabiru me neman ganin bayan Aminin shi,ashe ba laifin wasu bane in sun ce ba su bukatar aboki ko kawa a cikin rayuwar su,faruwar irin haka suke gujewa,daukan wayar yayi idanun shi har na fitowa don masifa.



  “Rilwanu Audu Waziri na dade ban ji tsanan abu irin yanda nake jin tsanar ka a cikin rai na ba,tabbas ka cika babban shege kuma dan iska,yau ce ya kama ta ya zamo ranar farin ciki da dumbin murna a gare ni,domin yau ne nayi niyan karya alqadarin ka na har abada ya zamo na bar maka abun fadi,amman ban san wani irin luck ne gare ka me karfi ba har ka samu kayi turning table din da nayi setting da kai na against me,Wlhy Rilwanu kayi kadan ka maida mun farin ciki na ciki,tabbas ba zan hakura ba”,da sauri Sen ya katse shi da “Ai muddum hakura ma ka Raina shegen Odogwun da kake bautawa kuma ba zan yafe maka ba in ka hakura baka ci ubana ba,kai Kabiru ya ishe ka fa Wlhy zan ci me cin uwar ka na zauna kuma

Lafiya wai kai in baka nemi mutum da fitina ba,baka ganewa ko,to Wlhy na gaji I am so FADE UP with you Bastard!haba da anyi zance ka ce wai kai ne silan komai,to dan Uwar Uban ka da ka kaini aka mun kudin uwar ka na bada ko uban ka kafin na samu kudin” “Rilwanu sunan Uwa da ubana su yi saurin barin bakin ka,domin Wlhy har yanzu da bazata kake rawa,Odogwun da kake rainawa daba dun ni da shi ba da ka kare rayuwar ka a cikin mugun talauci,dan banza masu iban taki”dariyar takaici Sen ya fashe da shi wanda ya kuma kullar da Alh Kabiru kafin yace “I don’t have your fucking time Jahili mahaukaci,ka je can surutu kai ta kama domin kana da zaman court ina kuma jiran miliyoyi na domin kwandala ba zan yafe maka ba dan uban ka,ya sanya aka ce in za ka gina ramin mugunta gina shi kadan kila kai za ka fada ciki,and ita shari’a mata ne me ciki ba a san abunda za ta Haifa ba,ka kai kara na don ka tozarta ni sai gashi kai na musguna shege wawa dan shan jini kawai maza a je a Jiki da kudaden da za a fitar a baiwa dan gidan masu iban taki,ko ya samu ya siyo takin da yawa”ya kare yana dariyar shakiyan ci,ihu Kabiru ya sanya domin ba karamin haushi Rilwanun ya bashi ba,har ji yake zuciyar shi na tsananta bugawa kamar zai fado “ na rantse da girman Allah tare da taimakon Odogwu Rilwanu sai na kashe ka yau ba sai gobe ba in baka tsinci kan ka cikin kabari ba zina aka yi aka haife ni,jinin ‘da na da matar shi ba za ka ci a banza ba,Wlhy tallahi sai na kashe ka,sai na hallaka ka sai nayi maka kisan da ko an gan ka ba za a gane ka ba,sai…..” “ina nan cikin gida na ina jiran ka in ka fasa kashe ni shege ne kai,wawa jaki butulu wanda be san hallaci ba tir da Amini irin kai wallahi”Sen ya kare yana buga table ran shi a matukar bace be jira kara sauraran abinda Kabirun zai fada ba ya kashe wayar tare da yin wurgi da shi,da Kabirun ya san abunda ya ke facing da sam be ma yi tuannin kiran shi ba,amman babu komai he is ready for the war in har Kabiru ya shigo gidan shi yau to Wlhy tallahi babu abinda zai yana shi kashe shi saidai duk abinda zai biyo baya ya biyo,haba ya gaji da wannan iskanci na Kabirun.


   

 Wata irin wawiyar ihu Kabiru ya kwala tare da dakan sitiyarin motar,ji yake zuciyar shi na tafasa tare da azazzazalar shi muddum ba daukan rayuwar Sen yayi yau ba to ba zai iya bacci ba,tabbas ya tsane shi ya kuma dade da tsanar na shi domin babu abinda ya ji game da shi sai haushi da bakin cikin cigaban da ya samu,ganin irin daukaka da bunkasar da Sen ke yi a kullum shi ya haddasa tsana me tsanani a cikin zuciyar shi sai kuma aka zo aka yi rashin dace abun Jaazmeen din nan ya bullo a tsakanin su,a bayyane ya furta “Rilwanuuuuu Audu Waziri yau nayi maka alkwari shine ranar ka na karshe a doron duniyar nan,yau am gonna settle the score da ke tsakanin mu,idan ka mutu hankalin kowa ma sai ya huta,I hate you with so much passion  duk wani abunda nake burin samu kai ne ka same su,ni na kai ka amman ka zo ka fini yau komai zai zo karshe don wallahi yau din nan zan kashe ka”da gama fadin haka ya dauko gun din shi da ke shake da bullet ya danna mota tare da daukan hanyar gidan Sen,yana aiyana irin kisan gillan da zai yi wa Sen in sun hadu,ya zo daidai ta Roundabout da zai dauke shi hanyar gidan Rilwanun from nowhere wata katuwar babban Trailer ta yo kan shi,kamar kiftawar ido ya hango babban motar a take ya zaro idanu kafin ya kai ga kokarin kwace masa tayi awun gaba da shi,Inalilahi wa inna ilahi raju’un,da ta buge saida motar tayi sama sannan ta dawo kasa,a take kuwa ta bi ta kan motar da tayi rugurugu,a 360 kuwa ta figa a guje tare da barin gurin,mutane ne suka taru duk da gurin ba wani mutanan kirki bane,saidai duk wani me imani in ya zo wuce wa dole ya tsaya kasancewar yanda naman Alh Kabiru yayi daga daga yayi fata fata akan titi kamar an manmanna🥹🥹🥹🥹ya salam Duniya zancen banza kana shiri naka Allah na nashi kuma wai na Allah shine daidai,da Alh Kabiru ya san ajalin shi na kusa kila ko fitowa ma ba zai yi ba,kila da ya tuba ya nemi gafara saidai wai aka ce rashin sani😭😭😭abun takaici aikin da yayi niyar yi na karshe daukan rai ne ohhh ni duniya,yau ina duk duniyar da ya tara lokaci daya attajiri irin shi yayi mutu war wulakanci da kasaskanci wanda ko wanda ya fi kowa talauci ba zai yi ba,cikakken gawan shi ma an rasa shi🥹😭😭wayyo Allah duniya zancen banza upon all abubuwan da ya aika ya mutu shike nan sai kuma ya tanadi amsoshi gurin ubangijin shi na shirkan da ya aika ta masa,ko kusa be taba kawo wa kan shi mutuwa yanzu ba domin yanzu ne ma ya ke tsaka da jin dadin rayuwar shi,amman wai kwana ya kare,Jama’a mu dada tsoron Allah mu kuma gyara halayen mu domin ita mutuwa ba sallama ko message take ba kafin ta dauki mutu😭😭😭🥹Allah ka yafe mu ba don halin mu ba ka bamu ikon yin kyakkyawan karshe,kar ka karbi ran mu sai kana farin ciki damu🥹🥹😭………




    Jiki na ya mutu Wlhy🥹😭😭unfortunately a nan zan tsaya a page din yau,ku dai kara mun hakuri mun zo karshe in sha Allah🤧🤧🤧🤧sauran mu kiris in sha Allah kun san ance aski in ya zo gaban goshi ya fi zafi🤧🥹but mun zo karshe da yardar Allah,kar kuyi fushi da Anty Meemarhn ku.



   😭😭😭😭😭a hada mana zaman makoki a gidan Fanash ko Ummu iman domin I no get space da mun yi a gidana lol,su Kabiru an tafi duniya ke nan,Afzaal kuma na hannun hukuma Allah ka sa muyi kyakkyawan karshe🥹



   Sai zuwa Monday in Allah ya sa mun kai da rai da lafiya🙄🙄amman fa sai na ga ruwan comment💃🏻💃🏻



    Ina wa kowa fatan Alkhairi🥰.

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)


This page is yours 


Nana(Newlife)

Oum Mursheed

FarukuAisha

Aisha Muhammad Bashir

Maman Anwar 


Kuyi yanda kuke so da page din nan,na gode sosai da kauna da kulawar ku a gare ni🥹❤️



Kofa a bude ta ke ga me son yin joining Saidai pls Banda maza and bana son talla 🥰



    https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0


My what'sapp group link,you are all welcome to join amman Banda maza pls .


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


            08100046388


******************


    Tallah! Tallah!! Tallah!!


   

   Ina uwar  da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


  Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


   Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


    To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


         08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌


...........

          Page fifty three 


******************


         Cike da takun nutsuwa kamar wace ke tsoron kasa ta iso inda Nameer ke zaune akan saman motar shi,tun fitowar na ta ya zuba mata idanu,ji yake kamar ya hadiye ta ta koma cikin shi da zama tsantsan so,face inta babu komai fayau da shi,sai ma tashin  da idanun ta suka yi alamun ta kwana ta wuni tana kuka,haka zalika face din ta da lips din ta sun dan kumbura,tana sanye da dark green hijabi har kasa,wanda ko ba karamin amsar ta yayi ba, ita kan ta yanzu har Allah Allah ta ke ta sanya hijab din don ba karamin sha'awa yake ba ta ba,kafafun ta sanye da black flat shoe din da ya siyo domin ta sai ya ga kuwa sun mugun karban kafafun nata,shi dai a rayuwa ya rasa gane wani irin so ya ke wa Nadeeya domin ko a wani irin shiga ya gan ta ji ya ke kamar ya sace ta ,tabbas ya yarda wani son gamon jini ne ko in ce kaddara ce daga gurin ubangiji daman can ya rubuta zai faru,amman duk wanda ya ji labarin su dole zai yi  mamakin a taya ya fara son ta,wanda shi karan kan shi har yanzu be da wannan amsan,ko za a kashe shi da tambayar akan wani dalili yake son Nadeeya shi kan shi be sani ba,all he knows is that daga tausayi ne ya koma so,wanda ya ke jin ta kamar jinin jikin shi ,wallahi lokaci daya ji ya ke kamar Nadeeya ita ce mahadin rayuwar sa sannan kuma bugun zuciyar sa,don zai iya cewa abunda ya ke ji akan ta be ji kwatan kwacin shi akan late wifey din sa ba,ya san wasu za su ce abu ne me matukar wahala samun wanda zai so ka yayi accepting din ka  haka bayan sanin komai game da kai,(My sister one thing in this life is that in har mutum don Allah ya so ki to babu abinda zai same ki da zai juya miki baya,domin he is not after wani abu daga gare ki,ke din dai ya ke so kuma ya ke kauna,shi wannan son gaskiyan no matter what baya saurin fading,Ya Allah ka hada mu da masoyan mu na gaskiya a duk inda muke,ka nisan ta mu da wanda sai amfanan su ya tashi suke neman mu).


 Cikin turo baki gaba ta dan daga murya tace "I have been talking to you since fa"ganin tayi magana ya kai sau biyu be ce da ita komai ba, banda aikin kallon ta da ya ke ta faman yi "Green looks good on you Pookie i love it,besides kalan Aljanna ce,you are like my world and also my paradise can you keep on wearing it pls"idanu ta watso mishi da sauri yace " I mean the Hijab yayi miki kyau sosai Miss Nadeeya,so how are you?"kai ta dan giriza domin ba shakka ya fara kai ta bango, "Hajiya wants to see you if you are free ke nan fa"ta bashi amsa ba tare da ta amsa tambayar da yayi mata ba,dirkowa yayi daga kan motar sannan ya ce " at your service Mi Lady,ba abunda nake yi let's go"bata ce da shi komai ba ta juya,shima be kara ce mata komai ba ya bi bayan ta,yana ta aikin sakin murmushi shi kadai,har suka iso dakin Hajiyar,a waje ya tsaya saida ta ce ya shigo mana sannan ya shigo,duk tarar da su yayi a zaune,so guri kusa da Mama ya nema ya zauna tare da riko hannun ta a hankali,cikin muryan rada yace "Hajiya Mama na hope kina lafiya ko?"hannun ta ta

janye,sannan tace "ubangiji ya shirya mun kai Baba na,ina lafiya Alhamdulilah"murmushi Hajiya da Umma suka yi domin ba karamin burge su wannan bond din na su ke yi  ba,be damu da mutanen gurin ba all he really cares about is his Mother!ya ji ya lafiya ta,saida Hajiya ta dan yi gyaran murya sannan ya dago ya kalle ta,da hannu tayi masa alama ya zo kusa da ita,ba tare da musu ba ya taso ya zo kusa da itan ya zauna, "Hajiya ya karfin jiki?"murmushi tayi sannan tace "bana so sai yanzu wato ka lura da ni", murmushi yayi tare da girgiza kai,sannan ya daura da " Small mom hope ba ku bukatar komai and Hajiya ta sha magungunan ta ko?".


   "Na sha duka ba da dadewa ba kuwa,and Alhamdulilah babu wani abun da muke bukata,ka wadata mu da komai Nameeru ba zan gaji ba gurin yaba maka,tare da godiya da kuma sanya maka albarka ba,domin ka yi mana abinda dan ciki na ma bana tunanin zai yi mana kwatan kwacin abunda kayi mana,hakika duk inda ake neman mutumin kirki me nagarta to ka ma wuce nan,a yanda taimako tayi karanci  sosai a duniyar mu ta yanzun nan,naka ma ba son taimakon shi ake ba balle bare", da sauri yace "Hajiya don Allah stop calling kan ku strangers wlhy ni family na dauke ku,and ban ga abinda zan muku na fadi ba,so pls ki daina gode mun", "ya zama

dole na gode maka Nameer,and baki na ba zai taba gajiya gurin roka maka Allah ba domin abun da ka yi mana ni da family na Allah ne kawai zai iya biyan ka,tabbas kai haske ne,haske me haskaka rayuwar Nadeeya ta da ni kai na,daba dun kai ba kila da yanzu Nadeeya ta babu ita,in har ma lokacin tafiyar ta be yi ba da yanzu ba mu san yanda ta ke ba,amman kai ka tsaya a kan legs din ka risking your whole life don ganin ka inganta nata rayuwar,na gode sosai Allah ya maka Albarka sannan ya kula da lamuran ka,ya kuma kare ka duk inda kake" ta kare tana murmushi cike da jin dadi ya amsa da "Ameen ta rabil alamin",dan zama ta gyara sannan tace "Nameer kar ka gaji da mu don Allah,taimako muke nema",da sauri yace "haba Hajiya wani irin gajiya kuma just say koma miye kan ki tsaye,don kun wuce neman taimako a guri na",har ran ta ta ji dadin furucin nasa, "Bauchi nake son ka kai mu domin Allah don akwai abubuwan da nake son yi,duk da an ce an kori karar da Nadeeya ta shigar ina son ganin wannan sakaran mijin nata,don karba mata takardar sakin ta let her be free from this meaningless relationship,ko ta samu ta huta",zama ya gyara sannan yace "Gaskiya shigar da karar ma be yi ba,don da na san kara za ta shigar da ba zan bar ta ba,domin duk lalace war shi he is still her father,and am so glad and happy da aka kori karar domin tonuwar asirin za ta yi yawa,maganar kuma wancan mutumin Hajiya Indai kan shi ne ba sai kin bata kafafun ki ba",hannu ya sanya a aljihu tare da zaro farin paper da ke nade, "Hajiya this is Nadeey's divorce paper tun randa yayi planning kashe ta ya rubuta mata saki uku,ya aje kusa da ita da na je daukan ta na dauko tare da takarddar sakin,na aje shi very safe with me,and Allah ma ya taimaka saki uku yayi mata babu wani batun yin idda"ya kare yana mika wa Hajiya takaddan,karba tayi tare da budewa sannan ta shiga karanta  wa don wulakanci ma da turanci yayi mata sakin,and kamar yanda Nameer ya fada tabbas haka ne saki uku yayi mata,sassanyar ajiyar zuciya Nadeeya da Hajiya suka

sauke a tare,sannan Hajiya tace "Alhamdulilah Allah na gode maka,Nadeeya kin ga yin Allah ko tun dazu nake ta nazarin hanya da za mu bi na karbo miki sakin ki,sai gashi ta hanya mafi sauki Allah yayi mana,ubangiji ya sanya hakan ne mafi Alkhairi ya kuma baki wanda ya fishi"duk da Ameen suka amsa banda Nadeeya da ta ke jin can kasar zuciyar ta inaaa babu wannan batun kuma domin yanda ta ke jin ta tabbas ta gama aure babu abinda zai sanya ta kara sauraran wani na miji balle har ta sanya shi a rai,babu abinda ke gaban ta yanzu da ya wuce ta ga tayi improving addinin ta,shine kawai ne a gaban ta,domin tana da burin ganin ita ma ko izu goma ko sha biyar ne Allah ya bata damar haddace wa sannan ta iya sallah alola tsarki yanda Annabin rahma koyar,maganar Hajiya ne ya katse mata  tunanin ta inda ta ke cewa "to Alhamdulilah tunda ma ya sake ta already amman kar ka gaji da mu ina son zuwa bauchin dai akwai maganganun da nake son yi ni da Abul bait" , "ba komai Hajiya ku shirya zuwa duk

Sanda kuka ce sai mu tafi" cikin dadin rai tace "Allah yayi maka albarka,ka je ka huta ko zuwa rana haka sai mu wuce tunda ba wani nisa bane daga nan zuwa bauchin", mike wa yayi sannan yace "to shike nan Hajiya nima bari na leka asibiti na ga ya jikin Uncle Usman din kila ya farfado", "to shike nan Allah ya tsare,tashi Nadeeya ki raka shi kar dawainiyar tayi masa yawa shi kadai"har ran shi ya ji dadin haka domin ji yayi kamar ya goya Hajiya don murna ko banza zai samu ya kalle ta to his heart content,ita ko ba don ranta ya so ba ta tashi tare da shigewa daki,ba tare da ta dau time ba ta fito sanye da green hijab din dai,ta so canjawa but haka kawai wani sashi na heart din ta ke azazzalan ta akan ta bar shi,a haka ta bi bayan shi sai asibitin,haka yayi ta cika ta da surutai inda sai shan Kamshi take bata kula shi ba,be damu da shariyar da take yi masa ba all he really know and cares is that yana son ta soyayya me tsanani and deep down yana ji a jikin sa watarana za ta zamo mallakin sa,a haka suka isa asibiti inda har yanzu Uncle Usman din be farfado ba saidai he is not in any sort of danger now,ba su dade a hospital din ba suka fito,saida ya biya da ita gurin shan ice cream,suka siya sannan suka juyo gida,tun a mota ta bude ta fara sha domin ta yi missing ice cream,duk wanda ya san ta ya san she is an ice cream lover, ganin yanda take sha tana ta faman lumshe idanu ne yayi matukar burge Nameer domin as he can see wani farin ciki na daban take samu,yanda take behaving kamar wata karamar yarinya da ta samu abunda ta dade tana craving,wayar shi ya dauko a boye ya shiga daukan ta pictures da video coz she looks so cute and adorable,a haka har suka iso gida,inda ta dauki siyayyan da yayi mata,har ta bude kofar fita sai kuma ta juyo cikin sanyin murya ta ce da shi "thank you,I had fun today"daga haka bata kuma cewa komai ba ta bar motar,da kallo ya raka bayan ta,saida ya ga shigan sannan ya ta da motar,zuciyar shi cike da kewan Nadeeya ya bar kofar gidan.




  **********************BAUCHIN YAKUBU


     

    Cikin sauri Alh Salis yayi parking din motar shi a harabar gidan Sen,fitowa yayi ba tare da daukan wayoyin shi ba domin kallo daya za ka masa ka fahimci yana cikin tsantsan tashin hankali da damuwa, "sannu da zuwa ranka ya dade", "Yauwa Sa'eed sannu,Sen yana ciki ne??"Alh Salis ya tambaya yana nufan kofar shiga gidan, "yana nan babu inda ya je tun shigar satin nan"be jira karasa jin ta bakin Sa'eed din ba ya fada cikin  gidan,Sen yana nan zaune a kan dinning har yanzu domin sam bayi da kuzarin iya tashi ma,haka kawai ya ke jin jikin sa nayi masa nauyi tare da yi masa wani iri,babu abinda ya ke jira sai isowar Alh Kabiru domin daga yanda ya ji muryan sa ya san tabbas yau daya daga cikin su sai ya rasa ran sa,and ya shirya ma ko ma miye ne tunda har Kabirun ya nuna shi dan iska ne,to yau kam za su yi ta su kare domin ya gaji,a yanda ya ke jin ran shi na tafarfasa ko da Kabirun be nemi rayuwar shi ba shi kam a shiye ya ke ya dau nashi ran ko zai huta.


  "Distinguish  ashe kana nan,na dauka ma a bakin ka zan fara jin abunda ya faru,ashe kai kam ma break fast kake having"Alh Salis ya kare yana me jan kujeran kusa da Sen tare da zama,dagowa Sen yayi tare da zuba wa Salisun idanun "Salis Wlhy ba ma iya cin abincin nake ba,baki na kwata kwata babu dadi,yau na tashi da tashin hankali don zan iya kiran wannan rana bakin rana a gare ni,tun safe shaguna na da gidajen mayuka ma companies tare da gidadaje da motoci na ke ta cin wuta from nowhere,asara ta ko ta ina samu na take na ma rasa ta ina zan fara tun safe nake zaune a nan Wlhy ko ruwa ya kasa wuce wa ta throat dina,am just here na ma rasa me ke mun dadi", "subhanallahi wlhy na gani kuwa yana ta yawo saidai ba cikeken bayanin na gani ba so ban ma kawo a rai kan naka bane,wayyo jarabawa ce wlhy,babu ruwan Allah dole hankalin ka ya tashi kam asara ko ta biyar ce bata da dadi,balle na makudan dukiya,and Wlhy dole hankalin ka ya tashi ana wannan kuma ga wannan ga asara ga rasa rai da wanne daya za ka ji" da sauri ya kalle shi "Salisu sai na ji kamar ka ambaci rashin rai ko waye kuma ya mutu", "haba Senator kar ka ce da ni baka da labari,kai da ya kamata a ji zancen a bakin ka,amman kuma kamar ma ba ka da ma masaniya akai", "kamar ya ni fa sam ban gane inda zancen naka ya dosa ba", "kar ka ce da ni baka hau social media ba domin ko wani kafafin sadarwa zancen ke ta trending", "ni fa Wlhy Salisu rabo na da hawa social media na ma mance ina jin,kawai sanar mun in ce dai ba wani abun da ya shafi siyasar mu bace?"ya kare yana me kafe shi da idanu.


Zama Salis ya kuma gyara wa sannan ya ce "ko daya ba abunda ya shafi takarar mu bace,saidai na san zai yi matukar girgiza ka amman babu yanda ka iya sai hakuri",ajiyar zuciya Sen ya sauke sannan yace "to Ai da sauki tunda ba siyasar mu bace ta samu matsala,koma mecece za ta zo mun da sauki,domin a halin da nake ciki yanzun nan Salisu ban ga abunda zai kuma girgiza ni ba,in ba cewa aka yi na fadi takarar zabe", "dadi na da ki ke nan Sen Wlhy sam ba ka kaunar abunda zai taba maka takarar ka,by the way sai dai mu dauki hakuri domin Allah yayi wa Aminin mu Alh Kabiru rasuwa,na san za ka ji babu dadi kam domin ka fini sanin shi kusa da kuma shakuwa da shi but believe me ni kai na wlhy mutuwar nan ta taba ni,barin in na turo irin mutuwar da yayi ,amman babu yanda muka iya ba mu isa questioning din Ubangiji gurin tambayar shi why ya dauke mana Kabiru ba,saidai mu bi shi da fatan samun rahmar ubangiji da kuma nema mishi yafiya da tuba a gurin Allahn mu,tare da fatan in na namu ya zo ya sa mu cika da imani"kamar saukan aradu da ka haka Sen Rilwanu ya ji saukan kalaman Salisu,wani irin fat fat zuciyar sa ke yi,tabbas ya ji kalman mutuwa kuma in har ba yaudarar sa kunnuwan sa ke yi masa ba to tabbas ya Salisu ya ce kamar Kabiru ne ya mutu,saidai sam brain din shi ta ki tsayuwa guri guda balle har ya kai ga yarda eh tabbas Kabiru aminin shi ne da suka gama waya dazu suna neman ran juna a fujajan ne ya mutu,da kyar ya iya budan baki yace "Salisu don Allah wani Kabirun ne ya mutu?",kai Alh Salis ya girgiza domin ya san za a yi haka daman,tun da ya ji shiru ya san tabbas Rilwanu be san da mutuwar aminin na shi ba,and ya san abu ne da zai zamo mafi wahala Rilwanu ya yarda da mutuwar kabirun domin duba da irin shakuwar da suka yi,zai iya cewa ma mutuwar nan wa Rilwanu aka yi wa domin ko Aisha ba ya jin za ta kai Rilwanu jin zafin mutuwar nan da aka yi musu,duba da irin fadi tashin da suka sha tare da jimawan da suka yi suna abota abu ne na tun samartaka har girman su dole kam ya girgiza,ya ma ga karfin halin shi da be suma ba.



 Ajiyar zuciya ya sauke tare da mike wa,kusa da Rilwanun ya zo tare da dafa hannayen shi,kafin cikin sanyin murya ya fara magana "Tabbas mutuwar nan wa kai aka yi wa Sen ni kai na ina gani wlhy na san an maka mutuwa,domin babu wanda ya sanka be san alakar ka da margayi Alh Kabiru ba,na san dole ka ji wani iri amman ya muka yi wanda ya fi mu son shi ya karbi bin sa,saidai muyi ta taya shi adduar da cewa a gurin Ubangijin mu",hannun shi ya zare da sauri tare da mike wa tsaye "Salisu wai wani irin mutuwa kake son fada mun Kabiru yayi,mutumin da ko dazu saida ya kira ni a waya ya na me sanar mun kan me hana shi daukan rai na saidai in ya mutu,sannan yanzu ka ce da ni babu shi,zaman nan da ka ga ina yi zaman jiran shi na ke ya zo muyi ta ni da shi ko ni ko shi,domin na gaji da Bura uban da yake mun,wani irin Kabiru ya mutu,ko ran Friday din nan da ya wuce nan ya biya lawyer makudan kudade don a shigar da kara na court don bata mun

suna,Allah yayi Lawyern da ke me son abun duniya ne ya yo gida na direct bayan barin gidan shi tare da zayyano mun abin da ya faru,a take na siye shi tare da sanya wa ayi watsi da karar,inda court ta sanya dan iskan Bunyan matukadan kudade,na Deformation of character da ya mun,ko dai ba baya son biyan kudaden ne ya sanya ya biyo ta haka,domin na fi kowa sanin halin wannan dan iskan da shegen son abun duniya koma miye zai iya aikata wa don kudi,domin a yanda na san Kabiru da taurin kai da rai ba mutuwar yanzu ba",da sauri Alh Salis ya rufe masa baki "haba Rilwanu watch your tongue mana babu kyau zagin wanda suka riga suka mutu fa", "thank God wanda suka mutu ka ce domin am very sure Kabiru na a raye Salisu babu abinda ya samu Kabiru balle ace ya mutu"ya kare yana janyo wayan shi don kiran layin Kabirun,domin be ga abunda zai sanya ya yarda Kabiru ya mutu ba,to akan ma me zai mutu yanzu,shi Odogwu din yana  ina har ya bar Kabiru ya mutu,bayan yayi musu alkwarin in suna so sai sun kai fiye da 100 years ma suna nan a raye da lafiyar su,duk da shi ya fita har yanzu babu abinda ya same shi,to akan me Kabiru zai mutu bayan har yanzu shi yana cikin brotherhood.


    "Alh Rilwanu pls try and hold your self together,na san akwai ciwo rashin na kusa da kai but babu yanda muka iya,duk zaman jiran lokacin mu yayi mu tafi muke yi,so pls in rai ya baci kar a bari hankali ya gushe!we are all Muslims and am very sure kasan yadda da kaddara me kyau ko akasin shi yana daya daga shika shiken imani,so pls kayi hakuri ka kuma dau dangana,go get yourself ready ka zo mu je a karbi gaisuwar da mu tunda ba a samu piece na shi ko guda da za a yi wa wanka da sallah balle a kai kabari ba" da sauri ya juyo "Salis wai don Allah da gaske kake Kabiru ya mutu,na shiga uku wai yanzun nan fa ya kira ni a waya,to me ma ya kashe shi daman can be da lafiya ne?" .


   "Lafiyar lau Distinguish mummunan hatsari ya samu ta hanyar round about,yanda dai na ji mutane sun ce wai Trailer ce babba ta bi ta kan shi,ta nika shi tare da markade bones da tsokar shi,domin unfortunately Kabiru ya hadu da mutuwa me muni coz ko gudan bone din shi babu wanda ya gani,aka ce haka naman shi ya daddage ya manmannu a jikin titi,abun tausayi abun kyama,to kuwa ka ga taya za mu fara neman abun da za a binne ai kawai saidai a hada zaman makoki,Allah dai ya sa ya tafi a saa",hawayen da suke kokarin zubo mishi ne yayi saurin maida su,be ma san wani yanayi zai misalta halin da ya ke ciki ba,murna ya kama ta yayi obstacle din shi guda daya da ya hana shi rawan gaban hantsi ya mutu,mutuwar ma ta wulakanci,ko kuma bakin ciki ya dace yayi na rasa Amini kuma abokin cin mushen shi na tun yarinta,wato in ya canka daidai a kan hanyar Kabiru ta zuwa gidan shi don kashe shi ne ya hadu da wannan hatsarin,ba komai bane ila alhaki na,ya ayyana hakan a ran shi,in ya ji Salisu na wa Kabiru adduar samun rahmaar ubangiji abun har dariya ya ke kusan bashi,yo Allah na tuba in ba Uban shi bane babu ta inda za a yi Allah ya yafe mishi har a kai ga yayi mishi rahma bayan tulin abubuwan da ya aikata a rayuwar nan,sam be ji dadi ba domin ba haka ya so ba,ya so Kabirun yayi wulakanta tare da azabtuwa a hannun shi inda shi da kan shi zai na wa kan shi fatan mutuwa,amman ko hakan ma yayi tunda ya san da kyar ayi saurin mancewa da irin mutuwar da yayi,daman duk wanda ya ce be son tukunyar wani ya tafasa to kuwa ya jira na shi ko dumi ba zai yi ba,ya so Kabiru ya tsaya da ran shi da kuma lafiyar shi,da shi da so called Odogwun na shi su ga victory din shi,a lokacin ne zuciyoyin su za ta buga don bakin ciki in sun ga ya hau kujerar mulki.


   " Sen don Allah ka samu ka je ka shirya ka zo mu wuce kar mutane su yi yawa a lura babu mu don ba karamin abun kunya da zagi zai zamo mana ba", "zagi!abun kunya na ji fa ka ce ?Salisu har abun zagi ya wuce abunda Kabiru yayi mun,to in baka sani ba ya mutu ne a kan hanyar shi ta zuwa gidan nan domin daukan nawa rayuwar reshe ta juya da mujiya sai ga shi ya mutu,to tunda ya tafi Allah ya bada ikon kwanciya lafiya ni bacci zan je nayi",duk da Alh Salis ya rude da jin furucin Alh Rilwanun amman sai ya danne tare da riko hannayen shi "look at me Sen just look at me,na san koma miye Kabiru yayi maka ne kyauta ba but kar ka mance ko wani zama ba ma abota ba ana samun sabani dole daman zo mu zauna zo mu saba ne,so kar ka bar don silly misunderstanding din da kuka samu ya sanya ka kasa paying last respect din ka,me kake son duniya su ce in har baka je an karbi makokin sa da kai ba??what are you promoting me kake son masu friendship na tun yarinta irin na ku su ce,don Allah let's all bygones be bygones and face the reality ka zamo me yafiya don Allah".


    "Yafiya fa na ji ka ce?Salisu ka san me Kabiru yayi mun kuwa da ke dan iska ne mutumin banza wai zargi na yake ni na kashe yaron shi me zubin yan daudun nan Ayman ya ke ko wane,nayi iya kokari na nuna mishi kan cewa bani da laifi amman wai dake Wawa ne dan jaka wai har farautan rai na ya ke yi,duk hauka na Ai family came first babu ta yanda za a yi na bayar da yaron Kabiru domin Amininta Ai ba karya bane"ya kare a zafafe,tabbas da Alh Salis a nutse yake sannan ba kallon wanda damuwa ta dame shi ya ke wa Alh Rilwanu ba to da babu abinda zai hana shi gano wani abu amman dake shi din ma ba a nutse ya ke ba sai cewa yayi "duk na ji kuma na fahimce ka amman ka sani wanda ake maganar shi baya duniya yanzu kayi hakuri mu je don Allah,ka mance da duk abinda ya faru mu je yanzu dai ayi komai da mu am begging on his behalf 🥹pls forget and forgive duk abinda ya faru na san ba intentionally yayi maka ba,we are all human beings so we are bound to make mistakes amman wanda ya fi kowa cikin mu shine me yafiya tare da saurin mantuwa,and kar ka mance inda Kabiru ya tafi duk mu ma wataran za mu je,Wlhy irin mutuwar da yayi ko makiyin ka bara ka so yayi irin mutuwar ba,don Allah ka shirya ka zo mu je lokaci kar ya tafi"ya kare with pleading hands 🙌.


  Haka dai ya samu ya lallaba  shi da bashi hakuri har ya samu dai ya shiga toilet don yin wanka,ba don ran shi ya so ba yayi wankan tare da fitowa ya shirya cikin manyan kaya farare wanda suka ji aikin hannu,hula ya sanya da agogo tare da fesa turaruka da takalmi sannan Alh Salis ya riko shi suka fito,sai wani bata batan rai Sen ke yi shi aka dole ba son zuwa ya ke ba,don kar ma ya ki ya sanya a motar Alh Salis suka tafi Sa'eed ne ya tuka su,ba a son ran Sen ba suka tsaya tare da yin shopping na tashin hankali domin tsaya wa Alh Salis yayi akan sai anyi don gudun zargi don sam baya son su bada wata kofar da zai nuna suna da matsala da Mamacin,tun daga kofar tanfatsetsen gate din Alh Kabiru jikin Senator da Alh Salis yayi sanyi,ganin yan uwa da abokan arzikin da suka zo,domin Alh Kabiru ba laifi yana da jama'a,abokan karatun su,yan Brotherhood yan uwa tare da abokan shi na gefe du sun zo,yarn shi kuwa idanun su ya kada yayi ja,haka fuskokin su ko baka fada ba kasan sun sha kuka ne har sun gode wa Allah,babu abinda ya fi ci musu rai kamar rasa gawar mahaifinsu da suka yi,da dadi yau ace ka mutu ga gawar ka nan an wanke yara da iyaye abokai tare da yan uwan arziki su raka ka zuwa makwancin ka akwai dadi,amman ace yau Uban su ya mutu ko kwayar idanun shi babu balle gangan jikin shi,wannan abun kadai in suka tuna ya kan sanya su kuka,duk kudin mahaifin su wai akan titi ya mutu namar shi ta daddage Wayyo Allah,fitowar Sen da gudu karamin yaron Alh Kabiru ne suna Al-Ameen ya nufi Sen tare da fadawa jikin shi ya kankame shi kam,cikin kuka da kuruciya kamar ne shirin hadiyar ran shi yace "Big Daddy!Big daddy wai da gaske ne Daddy is no more"ya kare yana fashe wa da kuka,ba karamin sanyi gwiwan Sen yayi ba,be san time din da ya rungumo yaron jikin shi ba.


   "It's okay little Champ am here  now okay,your Big daddy is here for you so cry no more pls,daina kukan nan haka"ya shiga lallahin yaron kamar shima zai yi kuka,ganin haka ya sanya sauran yaran duk suka nufo shi suna kuka, domin akwai  shakuwa me karfi a tsakanin su,Ayya tuni ya mance da gabar da ke tsakanin sa da mahaifin su rungumo su yayi tare da shiga lallashin su yana yi musu nasiha tare da tabbatar musu ba zai taba bari suyi maraici ba,da kyar ya samu ya shawo kawukan su har ya samu suka daina kukan banda dan shasheka da zubar da hawaye,nan suka shiga aka shiga sauko da ruwa da drinks don da Sen ya zo da shi,a take duk wanda ya san shi da Kabiru suka shiga yi mishi gaisuwa tare da jajanta mishi,ba karamin karaya  yayi ba jikin shi haka yayi sanyi kalau kamar an watsa mishi ruwan sanyi,domin maganar ma kasa yin ta yayi,Jan shi Alh Salis  yayi tare da neman guri suka zauna,inda yace da yaran su je suyi musu sallama da Uwayen su don su samu su yi musu ta'aziyya,a take kuwa Al -Ameen da yan uwan sa guda uku suka shige cikin gidan don taya masu aiki fito da abinci,shigan su da kamar 5 mints sai ga Asiya ta fito kafauwan ta ko takalmi babu,kai ko dankwali babu fuskan ta ya sintuma sosai daga ganin ta ko ba ka tambaya ba za ka san ta sha kuka har ta gode wa Allah domin damuwa ce fal cikin ranta,na rashin mijin ta da kuma rashin lafiyan da take fama da shi,daman jira take ya je ya dawo ta sanar da shi halin da take ciki ya samu a fidda ta waje domin wani irin azaba da tashin hankali take ciki,babu halin zama don da ta zauna take jiga guri,in har ba idanu ta ke yaudarar ta ba jiya da ta shiga bayi yin bahaya fararan tsutotsi ne ta ga suna fitowa daga duwawun nata 🥹🥹🥹inalilahi ya Allah ka raba mu da mumannan kaddara,ba karamin tashi hankalin ta yayi ba,domin kan ta gaba daya kullewa yayi ta ma rasa da ta ina za ta fara,da kyar ta samu ta tsakaita da kuka har bacci barawo ya dauke ta kan gobe sassafe za ta sanar wa Kabiru halin da ake cika,don zuciyar ta cike ya ke da tsoro,sai kuma aka yi rashin saa sassafe yace da ita zai fita,ta so suyi magana kafin ya fita don ya san halin da take ciki amman ya nuna mata fitan nashi na da mahimmanci hakan ya sanya ta danne nata damuwar har kan sai ya dawo sai ta sanar mishi su nemi mafta tun da wuri,domin shine silan komai saida ta ga tsotsotsin ne ma komai ya dawo mata fresh a kan ta,ta sha jin labari akan masu bari ana saduwa da su ta baya(Anal sex)ko kuma yan Luwadi suna fuskantar irin wannan matsalan ko fiye da hakan ma,kuka kam ta sha shi sosai domin sam ta rasa sanin wani irin son abun duniya ne ya rinjaye ta har ya sanya ta baiwa Alh Kabiru daman yin sex da ita ta baya,a nan Parlor ta tsaya tun fitar shi don a halin da take ciki zama na neman gagara ta jira kawa take ya dawo a samu a san nayi,domin sam ba za ta yarda ta zauna tsutsotsin nan su gama cinye mata jiki har ta  mutu mushe ba,tunda Allah yayi yana da kumban susa (arziki)dole kuwa duk inda za a kai ta ta samu lafiya ya kai ta ta samu,don sam ba za ta yarda tayi mutuwar wahala da azaba ba,tana nan tsaye jiran dawo war shi ne aka zo musu da sakon da ya firgita ta tare da kusan tarwatsa mata duniyar ta,wato sakon mutuwar Kabiru,wai tashin hankali ba a sanya miki rana domin rasa ma ta ina za ta fara tayi,duk irin kiyayyar da ke tsakanin ta da Abida Amaryan Alh Kabiru sai ya koma ma ita ke bata baki,domin ganin irin ficicikewar da ta yi lokaci guda,sam ba iya mutuwar Kabiru bane ya daga mata hankali,makomar nata rayuwar take duba wa,ina za ta shiga da uban yaran da suke da shi tare da kuma

lalurar da ke tartare da ita,da kyar aka samu aka shawo kan ta,tunanin tulin dukiyar da Kabiru ya mutu ya bari da tayi ne ya sanya mata nutsuwa da dan kwanciyar hankali,domin wannan tulin kudin ba ita da yaran ta ba ko tattaba kunnan ta ba za su jiyo kamshin talauci ba,domin yana da safe room da ya hana shiga inda ya ce da ita mahimman abubuwan sa ne a ciki,gab da zai mutun nan ta leka inda ta ga abun mamaki da firgici ganin idanun ta,domin ruwan kudi ke zuba a dakin kudade babu na kasar da babu,yo ko iya wannan ya ishe su rayuwar duniya ita da yaran ta da yaran su,balle in an hada da kadarori da ya mallaka ai su kam ba su ba talauci,yo tuno hakan da tayi ne ya sanya ta dan ji sassauci domin ko jira ayi sadakar arba'in ba za ta yi ba za ta ibi kudade ta tantsama duniya da yawon kashe shen waje don nemo wa kan ta lafiya.


  

  Wai tashin hankali ba a sa miki rana tana daki gurin yan uwa ana ta kuka tare da jajan ta mata mutuwar Kabirun da irin mutuwar da yayi(kun Riga da kun san gulma ajali ko a ina aka samu dan chance sai anyi,hakan ya sanya ba kowa ke yarda ayi wanann taron gaisuwar ko me ake kira am sorry na manta sunan abun bayan mutuwar shi ba,don garin nema mishi yafiya gurin Allah sai a kara masa zunubi don mostly yanzu cin abinci da munafurci ke kai mutane gidan mutuwa,Allah ka raba mu da karya gulma da munafurci ba don halin mu ba🥹).



Me aikin ta ne ta shigo dakin da mugun gudu ko sallama babu,kafin ta kai ga magana yarinya ta tari numfashin ta "Hajiya ki zo wuta ya tashi a kitchen kuma su Al-Ameen na ciki ya kasa mutuwa" hankali a matukar tashe ta mike "wani irin wuta kuma Zubaida"ta fada tana yin hanyar kitchen din saidai da sauri ta ja ta tsaya ganin wani irin bakin wuta da ke tasowa a kitchen din,a take matan da ke gidan kowa ta fara tattaran skirt tana nema wa kan ta mafita,domin ganin yanda wutan ke masifan ci,daga inda ta ke tsaye tana jiyo kukan Al-Ameen da sauran yaran suna kwalla mata kira,masu aiki tare da Abida Amaryan Kabiru duk suna ciki,ganin wutan fa ci yake bil Hakki ya sanya ta kwasowa a guje ta fito ko hijabi babu(ni ko nace rudewa ya sanya Asiya ta mance da batun takaba🥹🥹Wayyo Allah ka raba mu da sharrin wuta na duniya da na lahira),ai ko kamar jira wutan ya ke ta fita daga gidan,sai ko wata irin kara kamar an tashi bomb a take wutan ya fara cin main house din,ganin haka ya matukar firgita mutane da sauri Sen da Alh Salis suka nufo ta, "Alh Yara na Wayyo Allah na yara na,ku taimake su don Allah kar su ma in rasa su kamar yanda na rasa Daddyn su"shine kalman da ta fadi na karshe tare da yankan jiki ta fadi luuuuuu,da sauri Sen ya tare ta tare da taimakon Alh Salisu suka sanya ta a mota sai asibiti da sauran yaran da suka rage ba su mutu a wutan ba su 3,babu wanda ya ce da mutane su tafi don kan su don kuma tsiratar da rayuwar su kowa ya kwashi kafafuwa tare da sanin yanda dare yayi masa,domin babu alamun wutan nan yana da mutane tsayawa banda dada ci da yake kan yi kamar ana zuba mishi petrol,kun dai san ko ban fada ba kowa ya tafi da tunanu ka tare da abubuwan fada da yawa game da mutuwar Alh Kabiru,mutane na cike da mamaki tare da tunanin wannan me ya aikata haka,tun daga irin mutuwar da yayi tare da konewar komai nashi lokaci guda ya sanya zukatan mutane a cikin shakku,saidai rashin in da za su sami kwakkwaran amsa ya sanya su fadin duk abinda ya zo zuciyoyin su(oh ni duniya ina za ki damu🥹🥹🥹shi tsiyan kudin jini ke nan duk yanda ka kai ga tara su daga sanda ka yi kokarin fita ko kuma ka mutu,ko talalar Allah ya kare ya tashi nuna maka kasawar ka Wlhy sai ka fi kowa muzana🥹🤧yau ina ranar arzikin da Kabiru ke takama da shi,me ya fi wanann ciwo Jamaa ka mutu one single piece da za a samu na ka a kai a birne babu🥹,gidan da za a zauna a karbi ta'aziyyar ka ma babu,sannan uwa uba dukiyar da Uba ke barin wa family members din shi da za su rike kan su bayan shi(gado)wai shima duk babu🥹😭ya ilahil alamina Allah ka dada shirya mana zuria,ka raba mu sannan ka kare mu daga son zuciya da son abun duniya ba don halayen mu ba).



Direct Rimi clinic su Sen suka kai Asiya,inda a take aka shigar da ita emergency domin a samu a bata taimakon gaggawa,ba karamin tashi hankalin Alh Salis yayi ba domin tunda ya ke be taba ganin masifa irin wannan ba,don a labarin da ya zo musu duk

wata single kadara da Kabiru ya mallaka sun kone,inda abun kamar asiri don wuta ne ke ci ba a ma san daga ina ba,babu wanda ke bashi tausayi kamar Asiya domin be san ya za ta ji ba in ta farfado ta ji sun rasa komai,a ciki kuwa har da yaran ta 3 kishiya da kuma kuma yaran kishiyar ta guda 3 sai yan aiki 4 duk Allah ya karbi rayuwar su sanadin wutan da ya tashi wanda sun gaza gane dalilin tashi,Sen dai shiru yayi kawai yana me zazzare idanu domin tsaf ya fahimci komai,Odogwu ne ya kwashe duk wani abunda Kabiru ya tara a dalilin shi,daman haka ne rules din kungiya duk wani abinda ka samu dalilin shi,to da ka bari ko ka mutu sai sun kwashe komai,sai yanzu ya fahimci komewar da kadarorin shi suka yi ta yi,wato Odogwu ke son kwashe duk wani tattalin arzikin shi,kai ya girgiza da sauri tare da fadin " ina wallahi karya ne,ba ku isa ba!!"ya fada da dan karfi,wanda har ya so firgita Alh Salisu,dafo

Shi yayi, "Sen lafiyan ka kuwa??"


   "Salisu hmm lafiya ba lafiya ba,amman babu komai ",dafa shi Alh Salis yayi sannan ya ce "Senator are you sure you are alright kuwa?"da sauri yace "of course am alright kawai dai am just over thinking ne akan family din Kabiru da ya mutu ya bari,musamman Asiya Wlhy duk ta karyan zuciya,ban ma san ta ina zan fara ba"



  "Hakika we are going through a tough time,but stay strong okay komai zai wuce in sha Allah,and game da Asiya dole hakuri da dangana za ta sanya wa ranta duk da na san an mata rashi me zafi da ciwo wanda zai yi mata matukar wuya kafin ta manta shi"


 "Eh wlhy Salis mutuwar Kabiru da yaran ta ba karamin wargaza mata lissafi zai yi ba", "to shi kam ina ruwan Allah haka ya ke yin abinda ya so lokacin da ya so and ba mu isa tambayar shi me ya sa ba,fatan mu Allah ya sa mu cika da imani kawai,sannan ya kara mata hakuri da dangana,in sha Allah ba za mu bar yaran shi suyi maraici ba za mu kula da bayan shi,duk da na ji ance komai da ya mallaka ya kare🥹ni na rasa irin wannan masifa da ke bibiyar ku,sha koma miye akwai gida na da ke old GRA layin first bank,in ya so in ta warke sai su koma can da yaran nata su zauna,tunda na ga for now baka da inda za ka sanya su ko akwai?" Da sauri Sen yace "Wlhy abu kamar wasa ko in ce mafarki Salisu gidajen da na mallaka harda wanda ake hayar su kusan guda 100 wai duk sun kone,babu shakka wanann jifar mu aka yi,amman babu komai Ai Allah na kallo,shawarar da ka yanke tayi daidai,ka kai su can din Allah ya kara budi an gode".


   "Haba Sen yanzu har in nayi wa Kabiru abu sai an gode mun?Ashe kuwa ban amfani zaman tare ba,kar ka mance fa Kabiru was a very good friend of mine kafin rasuwar shi so don na taya ka kula da bayan shi ai ban ga wani abun tashin hankali ba,fata na dai Allah ya kara mana hakurin rashi sanann ya bata lafiya",da Ameen Sen ya amsa sanann yace da shi su je office din Doc don sanin wani hali take ciki,coz yana son koma wa gida,is like jinin shi yayi low due to tension din da ke dawainiya da shi,ba tare da daukan time ba kuwa suka je suka gama da gurin doctor tare da aje masa kudade sanann suka fito,kai tsaye gidan Sen suka koma hankalin su duk a tashe a yayin da jikin su sanyi kalau.



A parlor duk suka yada zango,saida suka sha ruwa sanann Sen ya dauki waya don kiran Falmata don ta shirya musu abinci “Aa Distinguish I don’t think zan tsaya in ci abinci,I have to go home don in sanar wa su Hafsa halin da ake ciki,ta samu ta aika yan aiki da za su kula da Asiyan”


   “Haba dai Alh bara ka tsaya mu ci abinci ba bayan long day din da muka yi having na san you must be hungry by now,in ya so sai ka wuce bayan mun gama

cin abincin”, “aa Distinguish in na ce zan tsaya sai sai na ci abincin nan am very sure ina gama ci jiki na nauyi zai mun na ji kasala tare da bacci,ai kawai zan wuce na ga ma na fara kiraye kirayen sallar la’asar”ya kare yana mike wa tare da gyara zaman hulan shi, “to ka gani ko za ka bari mu shiga muyi salla in mun fito ka wuce ne?”


“Aa Sen gida zan wuce don tun safe Hafcy ta sanar mun Zahra na hanya za ta zo gari,ina son in je in gan ta,so in na isa nayi sallan a can,zuwa anjima zan dawo duba ka in sha Allah,make sure to eat and also take some drugs in ka ga yayi worse call me or call a doctor pls”ya kare yana mikewa tare da gyara zaman hulan shi, murmushi Sen yayi sannan yace  “ba komai a gaida mun da daughter pls”,yana bakin kofa yace “Haba dai za ma ta zo har gida gaida ka zuwa gobe in sha Allah”da haka suka rabu ya shige motar shi tare da ficewa daga gidan yayi daidai lokacin motar Nameer ya danno kai cikin gidan,tunda suka shigo harabar gidan Nadeeya ke bin gidan da kallo,hawaye na zubowa daga cikin idanun ta,duk wani childhood memories din ta na dawo mata fresh a cikin kan ta,ba ta taba sanin za tayi missing gida ba irin haka,hannun ta Ummu ta kamo tare da murzawa a hankali “stay calm my dear don’t let your emotions get over you”hawayen ta ta share a hankali a daidai lokacin da Nameer yayi parking motar nashi,bude kofar tayi tare da sanya kafafuwan ta a hankali ta fito idanu ta lumshe sakamakon iskan da ta shaka,a hankali ta fito daga cikin motar inda da sauri Sunday ya nufo yanda ta ke,bakin shi har rawa yake gurin fadin “Jesus Christ karama Hajiya is this you”murmushin dole ta saki masa ganin inda ya wani zaro idanu kamar ya ga ghost ko wani abun tsoron, “ iko Allah Madam so you dey still alive?”ya tambaya yana washe baki,harara ta watsa mishi ganin Sunday ba zai taba canza halin shi daga tsinanniyar surutun nan nashi na fama ba, “ Sen na ciki??”shine tambayar da ta yi mishi,cike da washe baki yace “he dey inside na now now he came back self from Alh Kabiru’s burial”,idanu ta zaro cike da mamaki don bata da labarin mutuwar Alh Kabirun sai yanzu ma ta tuna ashe tahowar su a cikin motar Nameer da ya kunna radio ta jiyo sanarwa wani attajiri ya gamu da hatsarin mota inda tayi sanadiyar rayuwar shi,and duk wani dukiyar da ya mallaka duk sun kone within a blink of an eyes,don yanda ta ji ma hatta gidan shi ma ya kone inda yayi sanadin mutuwar rayu ka da dama,don ko inda za a karbi gaisuwar mutuwar shi babu,haka mutane suka watse,ba karamin jajantawa suka yi duk yan cikin motar ba,kowa da irin nashi tuannin da abinda kuma yake fadi game da mutuwar na shi,jiki a sanyaye ta fara tafiya zuciyar ta na bugawa,inda da sauri Sunday ya hau kwalo wa workers don gidan kira yana ihun “Small Hajiya don come back ooooo!!!”Sama sama Sen da ke kwance kan 3seater na parlor din shi ke jiwo hayaniyar workers din nashi,haka akwai tun ficewar Salisu daga gidan ya ke jin wani iri,shi da kan shi ko za a  kashe shi akan ya fadi yanda ya ke ji ba zai iya ba,wani irin sanyi jikin shi yayi haka zalika ya rasa why zuciyar shi take bugawa da sauri da kuma karfi,sai ya alakan ta hakan da maybe don BP din shi is low ne(ga wanda ke experiencing saukar jini wato Low BP sun san da hakan, at time mutum kan samu bugawar zuciya tare da matsanan ciyar ciwon kai,da kuma jiri,ubangiji ya yaye mana tare da ba mu ingantattaciyar lafiya baki daya🥹🥹)



Idanun shi a lumshe saidai sam ba bacci ya ke ba,kamar daga sama ya jiyo suna ihun kiran sunan Nadeeya,hakan ne ya sanya shi firgit din bude idanu tare da saurin mikewa tsaye,da sauri ya tunkaro kofar fita domin jin hayaniyar tayi yawa don da farko dauka yake shirme ne,wanda yayi daidai da sanyo kan Nadeeya cikin parlorn inda ya rage saura kiris su bugi juna,da sauri ya ja baya tare da kare mata kallo daga nesa nesa,tabbas in ba yaudaran sa idanuwan sa suke yi ba kamar Nadeeya diyar shi da ta bace kimanin watannni nawa ya ke gani tsaye kan kafafuwan ta sanye da hijabi purple har kasa a gaban shi,wani irin jiri ne ya ji ya zo masa lokaci guda da sauri yayi kokarin rike kan shi daga faduwa,bugawar zuciyar shi na karuwa tunanika da yawa na kai kawo cikin zuciyar shi,tabbas Nadeeya ce diyar shi daya tilo tsaye a gaban shi tana yi masa kallon kurilla idanun ta taf da hawaye,how when a tayaya Nadeeya ta samu lafiya,for how long now da samun lafiyar na

ta,and da wa da wa ta hadu tun bayan warkewar ta,wai yaushe ne ma ta zo gari?Sai yanzu ya gaskata maganar Barrister din da Kabiru ya dauka da yace da shi Kabiru ya ce mishi wai Nadeeya ce ta zo har gida crying and begging for his help,da farko ya dau karya da munafurci irin na Kabiru ne,amman ganin ta tsaye gaban shi  wanda bayi bukatar tambayar kowa ya san tana cikin koshin lafiya domin kallo daya za ka mata ka fahimci hakan.


A hankali ya shiga takowa inda take tsaye idanun ta akan shi tsaf ko kyaftawa ba gagara yi,she can’t believe it wai Mahaifin ta abun kaunar ta wanda ta so da duka rayuwar ta,and ya tasarwatsa mata duniyar ta tare da kokarin ganin bayan ta ne wai tsaye a gaban ta,a hankali ta ji hannun Sen a fuskan ta tare da shafawa a hankali don tabbatar wa kan shi eh da gasken Nadeeyar ne,jin eh ita din ce tsaye a gaban shi,ya sanya bakin shi har bari ya ke gurin furta “Princess!!is this really you?”ya kare yana manna ta da jikin shi tare da rungume ta kam a kirjin shi yana jin wani irin kewar diyar ta shi,for a moment ya ma mance da tulin crimes din da ya ke da shi a gurin ta,idanun shi sun rufe kauna da kewar yar shi kawai ke dawainiya da shi,a tare suke zubar da hawaye na ban tausayi,domin ita kan ta Nadeeyar neman kaso 10 tayi na tsanar da tayi wa Sen ta rasa,is not easy shi ta sani tun tasowar ta,akwai kyakkyawar alaka da kauna me karfi a tsakanin su,har ta ware hannayen ta domin hugging din shi back,a take kuma komai ya dawo mata sabo fil a cikin rai da kan ta da mugun sauri ta sanya duk hannun ta biyu cikin karfin da Allah ya bata ta hankade shi.


  “Let’s goooo of me you cruel man”😡😡ta kare kamar za ta buge shi,jiki a sanyaye ya dago ya kalla ta,sai yanzu ya ma kare mata kallo tare da lura da irin kallon tsanar da take jifan shi da shi, bakin shi har na rawa gurin furta “Nadeeya did I just heard you calling me cruel?”,ido cikin ido tace “yes of course you heard me right,Sen Rilwanu Audu Waziri the greatest of all,the man behind so many faces,the wicked soul I have ever met in my entire life,yanzu don Allah ba ka ji kunyar kallo na ba,after all abubuwan da ka shirya akai na,am still standing in front of you,shame to you Sen am so ashamed of calling you my Dad,I want you to watch my lips as I say this I hate you so fucking much much”ta kare breaking down to tears.



  “Wow just wow 😯 did I just heard you right,Nadeeya”da sauri tace “don’t you ever fucking call my name again not even ko filin kiyama bana fatan na kara haduwa da me kama da kai,I just hate you with everything in me”


   Dariya Sen ya dan fashe da shi sanann yace “watch your tongue little Dummy no matter what am still your father,and my blood still runs through your veins,lalle Nadeeya kin girma so you have the guts ki tsaya looking at me right through my eyes kina fada mun duk maganganun da kika ga dama,after all I have sacrificed for you,after duk abubuwan da nayi going through don ganin na baki best life din da mata dubu dari ke mafarkin samun rabin sa,why are you being so ungrateful ne bayan kin san I worked hard just to make sure kin samu future me shegen kyau,but har ni kike fada wa magana don ran ki,Nadeeya ko kin san irin wahalar da na sha kuwa for you nayi fighting da mutane da yawa don tabbatar da na bar ki a raye kusa da ni,babu abinda na ke tsananin so da kauna irin ki,you are my little doll and I love you so so much,duk abinda kika ga nayi Wlhy is for your own good ne,now come over to daddy and give him a super big hug,I really missed you so much my princess”ya kare da iya kar gaskiyar shi yana me bude mata arms din sa,kallo ta watsa mishi ne cike da mugun tsana, “what are you thinking of come here my baby girl”ya kare yana mata alamu da hannu,takowa tayi a nutse har ta zo gaban shi idanun ta har yanzu na kan shi,cikin sanyin murya tace “Daddy why do you do this to me,I used to love and adore you since I was a little baby,you have been my refuge,my star and also my role model,kasan miye Daddy tun ina yarinya bani da burin da ya wuce in na girma na auri miji irin ka,because you are so beyond perfect,you are just the lovable gentle man I have never met in my life,you are my best friend my dad and also my mom,you are my first love and also my first boyfriend,hanci ta ja hawaye na cigaba da zubowa daga idanun ta,I used to love you so much because baka taba sanya ni jin maraicin Mom ita ba,you make sure to make all of my wishes granted,you tired so hard as you said ganin ka bani best education and jin dadin duniya,but what about my Akira me kayi akan wannan??ta fashe da wani irin kuka take a good look at me Sen just look at me am fucking 23 years old turning 24 soon amman ko sallah ban iya ba,ban iya alola tsarki balle ace karatun Al-Qurani ba,and you are here talking about sacrifice din da kayi a kai na,for my own information duk wanda ke tare da kai na nesa ko na kusa ka kai shi Mecca but what about me?Babu kasar da ban je ba a duniyar nan in ka cire Saudi Arabia?you tired so hard ka ga na mori duk wani jin dadin duniya amman kwanciyar hankalin da jin dadin lahira ka hana ni,why Dad just tell me why??”ta kare tana wani irin kuka domin ba karamin ciwon abun ta ke ji ba,ace katuwar matar daki da ita amman bata ma san ta ya za ta bauta wa wanda yayi silan zuwan ta duniya ba.



   “Hey baby girl try to relax and listen to me okay,why duk abinda nayi is out of love and saida na duba in your best of interest”,da sauri ta katse shi gurin fadin “best of my interest fa na ji ka ce bada Womb dina da ka yi ne ko kuma kashe mun Mahaifiya da kayi ne ya zamo best of my interest ohhhh na mance maybe neman miji na son in law din ka da Luwadi ne ya zamo kayi best of my own interest”…… “Nadeeeyyyyyaaaaa!!!”


  “Don’t you ever shout at me again you Murderer,I cant believe it wai Daddy na me nuna wa duniya kullum shi ma Allah ne Mr I to know and also most holy man da na sani ne ya kashe mahaifiya ta,Daddy me tayi maka??wani laifi ta maka da ta yi deserving kisa daga gurin ka,ta kara fashe wa da kuka me tsuma rai,kaico na ni Nadeeya ban yi dacen uba ba,Dad I can’t still believe wai my very own Father is a Murderer and also a Gay inalilahi”ta kare tana fashe wa da kuka a zafafe Sen yayo kan ta tare da dago ta yana me shake mata neck ran sa a matukar bace “har kin yi girman da zaki fada mun magana son ran ki dan uban ki,ya wanke fuskan ta da Mari ji kuke tasssss,after all abinda nayi domin ki baki gani ba shine har za ki zo don kunya ya miki karanci kina fada mun maganganu,yeah na ji na kuma yarda ni na kashe mahaifiyar ki so what?Ki ba abun ki kama kafa na kina gode mun bane,do you think is an easy decision in rabu da matar da na fi so fiye da komai saboda in ga kin zo duniya??i gave her up for you to be here with me,coz ni da ke shares a strong bond tun kina cikin ciki na ke kaunar ki fiye da komai nawa,I decided to sacrifice your womb saboda ke din a bar mun ke ki rayu tare da ni,amman yanzu nayi danasanin fighting da nayi a kan ki,da na sani da ke na bada tun kina ciki da yanzu Baheeya na raye tare da ni,do you think baya mun ciwo ne how i lost my beloved wife?Tun daga wannan ranar har yanzu rayuwa ta ba ta dawo daidai ba,duk saboda wa??I did it all because of youuuuu!!yes youuu but I don’t blame you and daman ban yi expecting za kiyi saurin Understanding ba after all you are still a kid,but am very sure za ki fahimta sosai in kin kara girma coz why not you are my flesh and blood,my blood runs through your veins so you are and you will be just like me”


   Cikin kuka da tari ta yi shouting “Allah tsare ni I will never be like you I despise you a lot,coz you are nothing but a shame to my name and my life,ka bar mun tabon da har na mutu ba zan mance ba and I will forever curse you for that,wlhy da ana canza uba da na canza ka coz you don’t deserve a daughter like me much less a good mother like her”ta kare tana nuna direction din kofar waje da su Hajiya ke tsaye tana kuka kamar ran zai fita,da jin furucin ta a zafafe ya kara wanke fuskan ta da Mari wanda ya sanya bakin ta fashe wa tare da wulli da ita ta fadi kasa timmm,kara ta saki sakamakon buguwar da tayi, “how dare you talk back to me,laifi na ne da na baki so much love and freedom da har kike tuannin ni da ke daya ne,don’t you ever in this miserable 😩 life of yours talk back to me,I will beat the hell out of you,Wlhy da na san haka zaki zama da tun kina yarinya na baiwa Odogwu brain blood and entire body din ki ya cinye ya bani kudi masu yawa da shi da yanzu na huta da takaicin nan”ya kare yana kokarin taka ta,da sauri Hajiya tace “Abul bait!!”


A take ya sankare da jin muryan Hajiyar a dodon kunnan shi,a zafafe ta kara so inda ke tsaye bata yi wata wata ba ta wanke fuskan shi da Mari ne karan gaske abunda ya jima bata yi wato zagi shi tayo mishi cikin dacin rai tace “dan uban ka ni za ka fara kashe wa ba ita ba,nace ka zo ka kashe ni ko zan samu in huta da bakin cikin da ka kunsa mun”ta kare tana fashe wa da kuka me mugun karfi,da sauri Ummu ta nufo ta Itama tana kukan tare da rungume ta tana bata baki.


   “Sakar ni Ummi bar ni don Allah,Wlhy gwamma ya kashe ni ko nima zan huta,yanzu Rilwanu abinda ka zamo ke nan?yau ce rana ta farko da ta kama sunan shi na aini ta fada,Rilwanu ashe haka ka dawo ban sani ba,wani irin tsananin son abun duniya ne ya rufe maka ido har ya kai ka ga shiga kungiyar asiri har da bada matar ka da mahaifan diyar ka hakan be yi maka ba har da nema da mijin ta yanzu tarbiyan da nayi maka ke nan?ina tunani da ilimin addinin ka suka tafi ne?no wonder mana duk sanda ka rabe ni nake jin wani irin yaaamm a jiki na ashe baka kulla gaskiya ba,akan neman duniya ka zabi ka yi wa ubangiji kishiya?inalilahi wa ina ilahi raju’un Allah kana kallo ni dai wlhy wanann ba tarbiyya ta bace iya kokari nayi gurin ganin na wadata ku da tarbiyar da ta dace duk da Allah be wadata mu da arziki ba amman nayi kokarin ganin na sanya muku k’awa da zuci tare da tsatsan tauhidi a zuciyar ku,me nayi da na cancanci irin wannan sakayyar a gurin ka,shin ko ka mance bayan duniya akwai lahira ka tanadi hujjojin da za ka fada wa Allah game da hakkin da ka dauka,tabbas gajen hakuri gare ka domin da kayi hakuri arzikin ka zai zo maka ta yanda baka yi zato ba ta hanyar halal ba ta hanyar haram ba,har yanzu na kasa yarda wai da Haram kudin jini ka gina kan ka,ka gina  Ni mahaifiyar ka,Yarka,yan uwan ka sannan da sauran al’ umman gari,ta fashe da kuka Ummi da Mama na taya ta,Allah kai ne sheda ta ban taba hada ka da kowa a gurin bauta ba,iyaye na Malamai ne and nayi iya kokari na gurin ganin na sauke nauyin da ka daura mun na tarbiyan tar da yara na,amman ina jin nawa jarabawar ke nan”ta kare tana kuka kamar ranta zai fito.



 A zafafe Sen yayi kan Nadeeya ganin haka ya sanya Nameer saurin shan gaban shi,ai kuwa a take ta kankame shi tsam domin lokaci daya ta ga Uban nata ya koma mata kamar dodo, cikin zafin rai ya fara magana “ka matsa mun na samu na ci uwar yarinyar nan shegiya watsattsiya nayi nadamar barin ki a raye Wlhy da na san haka zaki mun da ni da kai na zan kashe ki tun kina yarinya,wani irin soyayya ce ban miki ba,akan ki mutane nawa na kashe don dai ki rayu,Wlhy yanda nayi making so far din nan I won’t allow you all to defeat me,I worked so hard day and night sacrifice a lot of people just to earn a living and make sure na muku providing luxurious life da kuke living a ciki yanzu,kun san wahalar da na sha kuwa?uncountable sleepless nights din da na samu,nayi abubuwa da dama don ganin na mallaki kudi don jiyar da ku jin dadi,I wasn’t born with sliver spoon in my mouth but I make sure na haskaka rayuwar ku fiye da nawa,tun ina yaro in ke da burin ruyuwar hutu da na masu kudi,i fought a lot kafin na kawo wannan gurin da nake yanzu,with the help of my friend Kabiru yayi introducing dina to Brotherhood inda na samu arzikin da duk kuke takama da shi,kamar zarare ya juya tare da kallon ko wanann su,sannan ya cigaba I want you all to take a good look at your own selves haka kuke before??Maybe ba don ni ba da yanzu yunwa da talauci ya kashe ku,but I make sure as the first son of the family nayi taking care all responsibilities din ku,although ya zo da big heavy price to pay na samun key to this luxurious life da kuke having yanzu,kun san irin struggle din da nayi going through kuwa,I have to Mercilessly Rape my very own Stepmother har ta mutu,kuna tunanin abun be mun ciwo ba???duk duniya babu wanda na so kuma nake so kamar Gwoggo amman unfortunately I have to sacrificed her,she was my first sacrifice din da nayi making,then My very own brother Usman!!!am the one da na kashe Matar shi da yaran shi biyu sannan na sanya aka saukar masa da jinya for all this years don na ga ya fara poking nose din shi a harkan da be shafe shi ba,Na zo na kashe Mal Audu Waziri although shi babu yanda na iya ne dole sai na kashe shi don in samu in inganta is wannan rayuwar da muke ciki,dan shiru yayi sannan ya cigaba my next victim was Nusaiba yarinyar Umma Aliya😂😂dan dariya yayi sannnan yace ni na cinye ta,after her na cinye mata biyun da na kuma aura,then I met with Bahiyya ina tsanannin son ta sosai tare da kaunar ta but I have no choice na bada ita don in tsiratar da rayuwar ki,yayi pointing Nadeeya da ke boye bayan Nameer tayi sumar tsaye,na zo still na bada Baban Bahiyya unfortunately nayi haka ne don in yi winning  takarar Senator da na fito,after that I still have to sacrifice your womb Nadeeya to keeps you alive and also dukiya ta domin ke ce source din kudi na,I tried so hard ganin na tsirar da ke tare da kokarin kare ki don kar wani cutar wa ya same ki,but still ban tsira ba I have to make a tough decision akan ko na neme ki ta baya,ko na Nemi Hajiya ko kuma na nemi mijin da za ki aura,saboda soyayyar da nake miki nayi choosing na zabi mijin ki,coz Hajiya already na san daman no go that area ne coz ta Riga da ta fi karfin mu,duk da ma na samu an rufe mata baki da idanu akan wasu abubuwa da nake yi ya sanya sam bata iya mun magana,daga lokacin ne duk wanda ya zo neman Auran ki in an fito masa da kudiri na akan shi sai su ki yarda,a haka kusan 4 maza suka zo suka tafi ko?Lucky enough na sami Afzaal daga lokacin na dauki so da kauna na bashi,tare da yarda da amana ta,,idanu ya lumshe sannan yace nayi abubuwa da yawa masu muni a ciki kuwa harda sacrificing din innocent Babyn Zahra yar gidan Aboki na Salisu unfortunately yaron has to pay a price akan laifin da be ma san ya aikata ba🥹🥹,da jin haka Alh Salis da ke bakin kofa yayo cikin gidan da mugun gudu don tun dazu da Sen ya fara magana yana nan tsaye,idanun shi cike taf da kwalla ya yo kan Sen da sauri Nameer ya riko shi don ganin yanda yake a zuciyen nan zai iya kisa.



  “Na sha giya na ci naman mutum da jinin mutane,na nemi maza tare da mata ta baya,ban san sau nawa ba,amman duk da haka na san Alh Kabiru ya fi ni neman mata domin wannan dan iska ne sosai,duk ma ba muyi rabuwar dadi ba dan uban shi mistakenly na bada Daughter in law din shi,shike nan ya dauke ni da gaba and wanted to hunt my life down,ni ko naceee Naaa ba zai taba yuwa ba,akan dan Daudun dan shi ya mutu,I have worked so hard just to make a name of my self and to earn a living don na ga duniyar yanzu sai kana da shi ne ake yi da kai,amman har kuna da bakin yi mun magana in har baku yabe ni ba Ai ba za ku tsine mun ba,recent and last sacrifice din da nayi was Ammatullah yar gidan Ummi Salma” da wani irin ihu Ummu tace “Whaaatttt daman kai ne ka kashe mun diya??”


Cike da isa yace “Yessss Ummu ni na kashe ta amman Ai na biya ki fiye ma da kudin ranta,shiru yayi tare da saurin rintse idanun shi domin jiyo muryan Odogwu da ya ke yi cikin kunnuwan shi yana fada mishi “if you want that mukamin gwamman then go have Anal sex with your Mom over there,or Nadeeya your daughter,and I promise to make your dream come through”,ihu ya sanya sannan yace “go to hell and burn to ashes Odogwu I will never do that,I want you to mark my word and also read my lips sai na zamo Gwamman jahar Bauchi ko da uban ka baya so,I worked so hard and mutane ma kauna ta,so I don’t need your help anymore banda ma wanann banzar yarinya ta tona mun asiri Ai da ba wannan zancen ake ba,watch me and see Gwamna kamar na zama ne dan uban ka”dariya Odogwu ya fashe da shi wanda har saida ya sanya gidan girgiza,don kararar kowa na jiyo karar dariyar nashi da yanda gidan ke rawa alamun zai iya rashewa any moment from now.


  Cikin tsawa Odogwu yace “you son of ungrateful bitch I will make sure to make your life a living hell,sai na kwace duk wani abinda na mallaka maka,and kai da yin governor har gaban abada”ya kare yana Jan tsaki a take kuwa gidan ya fara girgiza da sauri suka fara kokarin fita daga parlorn,a hannu Nameer ya fito da Hajiya tare da sanya ta cikin mota don ko ba a tambaya ba ya san ciwon ta ya tashi,zo ka ga yanda ake ta guje guje gurin ganin kowa ya tsiratar da rayuwar shi,domin gidan har ya fara rushewa har Nameer ya zo shiga mota Nadeeya ta riko shi idanun ta taf da kwalla tace “Ya Nameer My Daddy!!Daddy na yana ciki”sai ta fashe da kuka,window ya leko tare da kallon Small mom da ta kifa kai da cinya sai risgar kuka take yi,Mama ya kalla da idanu ta itama ya kada yayi jawur yace “Mama look over her pls lemme go and get him out”be jira jin amsar Mamar ba ma ya nufi hanyar gidan ,da sauri Alh Salis yace “let him die he deserves it,mutum shedani Mugu irin shi wannan mutuwar ma tayi mishi sauki”murmushi yayi sanann ya nuna mishi Nadeeya da hannu “Uncle I have to bring him out for her sake”be jira kara jin amsar shi ba ya fada cikin gidan,inda ya tarar da Sen zaune kan kujera sai surutai yake wanda shi kan shi be sanin me ya ke fada,a ciki dai na gano yana cigaba da confessing tulin laifufukan da ya aikata,tare da tsine wa Odogwu da Kabiru sannan da kara jaddada musu babu abinda ya isa hana shi yin mulki,kallo daya za ka mishi ka gano kan ba lafiya ya tabu,da kyar da taimakon Allah Nameer ya samu ya fito da shi tare da sanya shi cikin mota a 360 suka bar harabar gidan inda kamar jiran fitan nasu ake suna fice wa gida kam ya shiga rushe wa gadan gadan………






    Afuwan don Allah Wlhy dan uziri ne ya rike ni amman tun yamma na so yi muku update.



In na ga ruwan comments ku ga update jibi in ban gani ba kuma sai randa Allah ya so🤧


Bare with the typing errors ban Riga nayi editing ba.



  Ina yi wa kowa fatan Alkhairi .

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)



Kofa a bude ta ke ga me son yin joining Saidai pls Banda maza and bana son talla 🥰



    https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0


 

...........

          Page fifty four


******************



        *********A MONTH LATER



     tabbas in nace muku a lots has happened within this month ku yarda da ni,ban ma san ta ina zan faro muku ba but well yanda na ga duk kun matsu tare da tambaya kullum ya labarin Sister Kareematu ne,nayi deciding bari na fara leko muku gidan ta don ganin wainar da aka toya babu mu tsakanin ta da Abdul mijin ta da ya kama ta da Doc Bashir a hotel room suna zina (Wa'iyazubillah🥹)


        WAIWAYEN BAYA

KADAN.......

    

               *************Kareematu 



      Tabbas a rayuwa babu mugun abu da ya wuce zuciya ya sanya Manzon Allah da kan shi ya ce akwai wata tsoka guda a jikin dan Adam da muddum in tayi kyau  to tabbas gaba  daya gangan jikin dan Adam zai zamo a gyare,in kuma ta baci to duk jiki ma ya lalace wanda ba komai bace face "Al-qalb" (Zuciya),hakika babu abinda ya fi biya wa son zuciya tare da barin shedan ya kada maka gangan shedananci a cikin kunnuwar ka,tabbas akwai wanda suka kasance azzalumai wanda ya kai ta kawo ma zaluncin wa Karan kan su suke yi wa,babu abinda ya kai rayuwa tsananin matukar baka gode wa Allah tare da kau da kan ka daga wanda suka fi ka kuma suka wuce ka ba,duniyar nan ka fi dubu ne dubu sun fika,saida wawa ne har yanzu be gane hakan ba,in kana son rayuwar ka tayi saurin daidaice wa kuwa karshe ka kasance cikin nadamar da ba za ta taba maka amfani ba to ka biye wa son zuciya tare da daura wa kan ka masifan son duniya da kuma DOGON BURI(Littafin MOM SAYYID),to kuwa lokacin da duniya ta tashi juya maka baya sai an tausaya maka,idan kuma kana neman tabewa rashin nutsuwa to saki Ubangijin ka sannnan ka dauki hanyar saba mishi kullum to ina da tabbacin kai da farin ciki kuwa kun yi hannun riga,tabbas babu abinda ya kai rayuwar aure dadi falala da kuma samun cikakken nutsuwa,domin shi din wata nau'i ce ta salon bautar ubangiji madaukakin sarki,wanda ya kasance kuma tsa'ni na shiga Aljannah cikin sauki,ya sanya duk tsanani ki rike martabar Auran ki tare da yin hakuri da juriya domin samun Aljannar ki,duniyar nan cike take da miyagun kuma macutan mutane,ya sanya a duk lokacin da kika yi dacen masoyi na gaskiya to kiyi iya yin ki gurin ganin kin rike shi hannu bibbiyu don a wannan lokaci da muke ciki yanzu babu abinda ya yi karanci kamar soyayya ta gaskiya tare da kuma rikon amana,saida kaico wasu daga sanda suka samu dan dama sai su mance da Allah da komai idanun su ya rufe ya zama babu abinda ke gaban su sai samun cikar burin su wanda karshe ke sanya su cikin danasani mara amfani,karshe a alakanta hakan da kaddara,wanda in da kaddara akwai sakaci da kuma son zuciya,Allah ka shirya mu baki daya ka sa mu gane kuma mu daina yawon saba maka,in mun tashi koma wa gare ka ka bamu ikon yin tuba ta gaskiya 🥹.



       " Ban taba jin kunya da tsanar kai na kamar randa Abdul miji  na,uba ga yara na,ya kama ni a hotel ni da Bashir muna tsaka da aikata sabon Allah ba,ko a mafarki ban taba mafarkin ganin wannan bakar ranar ba wanda har iyanzu fresh abun yake a cikin ido na,hakikanin Gaskiya na cuci kai na sannan lokaci daya na ji na tsani kai na tare da wai irin mugun kunya da nauyin Abdul da na ji ya kama ni,tsoro fal rai na banda rawa da karkarwa babu abinda jiki na ke yi a lokacin da Abdul ya ce da ni in wuce mu tafi gida,sam na gaza yarda duk da sanin da nayi Abdul mutum ne me hakuri,kawaici da maida abu ba abu ba abu ba,but sam na gaza yarda da na ga ya yi parking a kofar gidan auran mu,ba haka nayi tsammani ba Wlhy dauka nayi tun a hotel din zai mun dukan tsiya ya mun zagin fitan arziki,ya sake ni bayan ya gama tona mun asiri a duniya,in kuma be yi haka ba wlhy na dauka gidan iyaye na zai maido ni ya tsaya ya sheda musu halin da muke ciki domin nayi deserving fiye da hakan ma,don ko kaffara ba zan yi ba in har da ni ce na kama Abdul da wata daki daya ma ko ba Zina suke ba wlhy na gama auran shi ke nan har gaban abada,hakan kuma sai na tabbatar da nayi mishi zagin kare dangi tare da tabbatar wa na ci mishi mutunci,sannan in rabu da shi,in da gaba zai ji tsoron kara cin amanar matar shi da wata can daban,amman sam na rasa dalilin da Abdul be yi hakan ba.


Parking din mashin din shi yayi a kofar gida tare da sauka,murya can ciki yace da ni "sauko"ba tare da ko ya kalle ni ba ya nufi kofar gidan tare da bude wa,inda kuka san an zare mun lakar jiki na haka na ji a daidai wannan lokacin,domin kasa sauka ma daga mashin din nayi,don tunanuka ne da yawa ke kai kawo a cikin kai na,ganin ban taho bane ya sanya shi juyowa ya kalli,irin kallon ke fa nake jira,ganin haka ne ya sanya ni aro jarumta tare da sauko wa,zuciya ta na bani kila yau ce rana ta ta karshe a duniya,don haka kawai zuciya ta ke bani kila Abdul ya zabi mu dawo gida ne yanda zai kashe ni bayan ya gama cin ubana cikin sauki,tabbas na san duk inda ake neman me hakuri tare da gudun damuwa to miji na ya kai,don irin Abdul saidai kai ka cutar da su amman sam ba za su iya cutar da mutane ba,shiru shiru gare shi so da dama ya sanya ake jin tausayin shi na auran ta da yayi,coz an san Kareematu uban shi za ta ci sabida tsiwa da rashin mutuncin ta,kamar wanda kwai ya fashe wa a jiki haka na shiga takowa a hankali ina bin bayan shi,da taimakon hasken kwan fitilar da ke zauran mu na samu na shigar da kai na cikin gidan,ko sallama ban samu damar yi ba,kamar wanda aka jefo ta sai ga Khairat ta fado jiki na tana kuka "Mama Alhamdulilah lafiyar ki kalau babu abinda ya same ki"shine abinda ta fada tana me kara kankame ni,for the first time in my life na ji tausayi da kaunar Khairat ya darsu a rai na,tare da wata irin muguwar kunyar ta,haka nake tun haihuwar ta ni ban cika sanya yara a rai balle har na ja su jiki na ba,sam babu wata alamar shakuwa tsakani na da diya ta da sauran yaran nawa,coz ni ban ma san komai game da su ba, lafiyar su cin su,shan su,damuwar su duk Abdul ne ya san wannan,domin I was so carried away da neman abin duniya,one thing da na sani is that I tried my best to provide them da kudi tare da kayan sawa,bayan nan babu wata kulawa ko soyayya wanda ya dace uwa ta baiwa yaran ta a tattare da ni,tun suna yara kullum ina ganin kauna ta cikin idanun su,tare da hawayen neman I'm so su,saidai sam ban shirya ba coz in banda ma abun rabo da babu abinda zai sanya na haife su,a hankali Abdoul ya sanya hannu tare da zare Khairat din daga jikin ta,ganin duk sun zuba mishi ido ne ya sanya shi cewa "Khairi Maman ku a gajiye,bari tayi wanka ta sha pain reliever sai ki gan ta da kyau tunda kin ga ai babu abinda ya same ta"cike da murmushi yarinyar tayi toilet tare da dauko bucket ta zo ta juye ruwan flask tare da iban na drum ta sirka ta kai mata bandaki sanann ta dawo ta dau kwandon wakan ta tare da kujerar zama,jiki a sanyaye Kareematu ta wuce dakin ta domin sarai ta gano Abdul najasar jikin ta ne da bata wanke ba baya so ta taba Khairi da shi,jiki ba kwari ta cire kayan jikin ta tare da dauro zanin wanka ta nufi hanyar bandakin,a tsaye ta samu Khairi a gurin, da sauri yarinyar tace "Mama bari na jira ki a nan ko in za ki bukaci wani abun"idanun ta taf da kwalla tace "je ki kwanta Khairiya babu abinda zan bukata Allah ubangiji ya miki albarka ke da sauran yan uwan ki"da Ameen yarinya ta amsa sannan ta nufi daki tare da fito mata da kayan da za ta sanya in ta fito,haka Kareematu ta shiga wankan zuciyar ta duk a tunkushe ta rasa gane me ya kai ta biye wa son zuciya har ta bar wannan zuria nata me kaunar ta tare da tattalin farin cikin ta,ta je tana neman maza da auran ta,ta ci amanar aure ta kuma ci amanar su Khairiya a matsayin ta na uwar su da ya dace ta zamo role model me kyau gare su,hawaye ne suka shiga wanke fuskanta wani irin tsanar kanta da kunyar duniya da lahira ne suka kama ta,yanzu da kamar yanda Abdoul ya fada su Khairiya ne suka kama ta da idanun su ana zina da ita ya zata,da sauri ta rufe bakin ta jin wani kuka me karfi ya zo mata,ta dade tana kuka kafin ta samu ta baiwa kan ta hakuri tare da yin wankan janaba sannan ta yi normal wanka ta daura zani ta fito.



Ko da ta fito tarar wa tayi Khairi ta yi bacci don ta dan dau time cikin toilet din,kwanciya ta gyara mata sanann ta shirya cikin kayan baccin da yarinyar ta zabo mata,saidai abinda ya bata mamaki bata ga Abdoul ba ta duba ko ina amman shiru babu shi babu alamun shi,ganin lokaci na kurewa ne ya sanya ta tashi khairin a hankali "Khairiya ina Abban ku ko ya shige dakin shi",saida yarinya ta da mustiske idanun ta da bacci ya fara kama ta sanann tace "Umma Abba ya shi yace ma in kwanta yanzu zai je ya dawo"daga haka ta koma baccin ta,mamaki ne sosai ya kama Kareematu to ina Abdoul zai je cikin daran nan domin it's already past 12,wata zuciyar ce ta ce mata ko dai guduwa yayi ?A take ta ji zuciyar ta ya buga,sai  kuma tayi saurin cewa kan ta "kai ina Abdoul ba zai taba mun haka ba,ba zai taba guduwa ya bar mu ba"idanu ta runtse a hankali hawayen nadama na ta zubo mata akan fuskan ta,don kwata kwata bata da idea din ina Abdoul ya tafi,motsi kadan sai ta kalli kofa with hoping wai ko za ta ga Abdoul ne amman shiru babu shi babu labarin shi,tun tana hawaye har kuka me karfi ya kwace mata,kuka take sosai tana jin gaba daya duniyar ma ta fice mata a kai,duk sai ta ji ya ma tsani rayuwar ta,why ta kasa fighting da son zuciyar ta ta zauna da mijin ta me kaunar ta me son farin cikin ta,ta zauna da shi ta kyautata masa kamar yanda ya ke daukin kyautata mata,why ya zabi duniya tare da mantawa da lahiran ta?Abdoul has try all of his possible best don ganin ya zamo miji na gari a gurin ta babu abinda be yi ba don ganin ya sanya ta farin ciki,ya mata wanki,guga,girki,wanke wanke,shara tare da kula da yaran su,he sacrificed a lot just to make her happy,akan ta ya rasa aikin shi tare da sai da gidan shi,duk don ganin ta cika mata burukan ta,domin Allah yayi ta mace me dogon buri da son abin duniya,a lokacin da ya dace ta nuna mishi hallaci da kauna bisa sadaukar wan da ya mata,sai ga shi lokacin ne ta ji a zuciyar ta ba za ta iya zama da talaucin shi ba,tabbas in tace bata son Abdoul tayi karya dalilin da ya sanya ta kasa fita daga gidan shi ma ke nan,da taimakon Doc Bashir ya sanya ta zabi cin amanar shi tare da cin amanar Auran ta da yaran ta,a tunanin ta babu randa zai sani domin cikin nutsuwa take gudanar da harkan bin mazan nata,babu ruwan Allah in ya so tona maka asiri domin an ce wai rana dubu ta barawo one single day for the owner!sai gashi ba tare da zato ba abinda bata fatan har mutuwar ta a sani yau mijin ta ya kama ta da wani a hotel suna iskanci.


 

 Sai gashi abinda ta manta rabon tayi shi ko in ce ma bata cika yin shi ba,wato sallahn dare,sai gashi yau tana yi  taci kuka sosai tana rokon Allah ya sa Abdoul ya dawo gida ya kuma tsinewa Doc Bashir domin duk shine silan fadawan ta wannan halin da take ciki(Ni ko nace in da kwadayi daman da wulakanci😒yo kya daura wa Bashir laifi daman can da mugun halin ki🙄🙄wai ja ni ce ta tarar da muje,Allah ka raba mu da yin aikin danasani)a nan kan sallayar bacci barawo ya dauke ta,saida gari ya soma haske ta samu ta mike tare da yin asuba,a hakan ma Khairat ce ta tado ta,idanun ta sun yi ja tare da kumbura,ko da ta tayi sallan Khairi sanya ta tayi ta koma bacci don ce wa yarinyar tayi zazzabi da ciwon kai ke damun ta,ba musu kuwa ta koma gado tana me yaba sanin yakamatan yarinyar,ita tayi aikacen gidan tsaf ta gyara ko ina,tare da daura musu girki,sannan ta kama kannan ta ta wanke tas tare da yi musu shirin makatanta,sai da suka ci abinci sannan tayi wanka ta shirya ita ma,kafin ta zo tayi wa Kareematu sallama,cike da shauki da kaunar yaran ta bi bayan su da kallo,bayan ta baiwa Khairi 2k kan suyi kudin abin hawa da kuma kudin break,ran su kal suka bar gidan suna mata sai sun dawo,Itama fuskan ta dauke da murmushi ta yi musu a dawo lafiya.


    Tun tana zuba idanun ganin dawowan Abdoul har dare shiru babu shi babu labarin shi,tayi kuka har ta gode wa Allah sam Abdoul be kyauta mata ba,da be yanke shawarar guduwa ya bar su ba,in har ita ce baya son gani wlhy a shirye take ta bar gidan ko zai zauna lafiya da yaran shi,amman baya cutarwan da tayi mishi sam ba za ta so ta zamo sanadiyar rabuwan shi da yaran shi  kuma ba,inda su Khairi suka yi ta nan nan da ita,inda ta sanar musu Abban su tafiya yayi,bata taba sanin yara rahma bane kuma suna da dadi sai tsakanin jiya da yau,ashe shi yasa ake cewa wai haihuwa me dadi,dan lokaci da attention din ta da suka samu sai ya zamo ba sa son abinda zai sanya su yi nisa da ita,haka wannan ranar ma suka kwana babu labarin Abdoul domin ta kira duk layukan shi a kashe haka dai tayi ta kuka har ta gode wa Allah.


Kwana uku cur babu labarin Abdoul,zuwa yanzu kam abun tsoro ya koma bata,ganin shirun yayi yawa  ya sanya ta yanke shawara tafiya gidan su Abdoul din dan sheda musu halin da ake ciki,saida ta bari rana tayi sanyi sanann ta shirya tare da barin wa Khairi gidan domin sam hankalin ta ya gaza kwanciya,bude kofar da za ta yi suka ci karo da shi yana kokarin shigowa,ai bata san time din da ta fada jikin shi tare da kankame shi kam ba tsaban murna "Abban Khairat in ka tafi ne?Kwana biyu mun neme ka mun rasa"ta fada hawaye na zubo mata,a hankali ya janye ta daga jikin na shi,sannn yace "wani abu ne ya taso na gaggawa amman ba ga ni ba"daga haka yayi wucewar shi cikin gidan ,jiki babu kwari ta biyo bayan shi,a parlor ta tarar da shi zaune yayi tagumi,kallo daya za ka mishi ka san yana cikin matsananciyar damuwa,ga idanun shi ma duk sun kumburo alamun ya ci kuka har ya gode wa Allah,sanann kallo daya za ka musu ka san be samu isasshen bacci ba,a take ta kuma jin ta tsani kan ta,tabbas ba tayi wa kan ta,yaran ta da Abdoul adalci ba,sam be yi deserving mace irin ta🥹jiki babu kwari ta nufi daki don aikata abinda zuciyar ta ya umurce ta da shi,cikin sauri ta sauko da katuwar akwatin ta,sannan ta shiga hada kayan da za ta bukata a ciki,saida ta gama zuba komai,sannan ta sako katuwar bakin hijabi,kafin ta fito tare da akwatin ta a hankali don ya mata nauyi ma,da sauri yaran suka nufo ta .


    "Mama!Mama tafiya za ki yi ne?",saida ta saci kallon Abdoul idanun ta taf da kwala tace "gida za ni amman ba jimawa zan yi ba zan dawo"daga haka ta nufi hanyar kofar fita, "Maman Khairat ni kam ba na ce ban yarda da tafiya gidan nan naki da kika ce za ki yi ba"ta jiyo muryan Abdoul ya fadi hakan tare da zuwa inda ta ke tsaye,karban akwatin yayi,tare da kai wa daki,sannan ya kalli Khairat ya ce "maza kama hannun kannan ki ku tafi gidan su Rahma ki ce in gaida Baban su,domin baya kaunar ko  a mafarki su Khairi su san abinda Mahifiyar su ta aikata(haka ya dace Ma'aurata su zama duk tsananin laifin da daya zai ma daya try kuyi sulhu tsakanin ku never involve your kids a cikin fadan ku,domin kuna cutar da su ne wallah,in kuma zaman ne ba zai yu ba to ayi rabuwar mutunci,za ka ga uwa ta tara yara tana basu labarin abinda Uban su yayi mata na batanci ko baki san tsanan shi kike tusa wa yaran ki ba?ko ku ga Uba gaban yara yana zagi da dukar Mahaifiyar su,to me kuke son su koya in sun girma?daman babu zaman da ba a samun sabani but don Allah ku daina barin yaran ku sunan sanin halin da kuke ciki,try your very best to act well a gaban yaran ku,in ya so in ma Zane juna za kuyi ku yi shi a daki😂😂,Allah ya sa mu dace ya kuma kara mana hakuri juriya lafiya da zaman lafiya ).


   Saidai ya ga fitan yaran sanann ya ce da ita "zo ki zauna"ya nuna kusa da inda ya ke zaune,ba musu ta nemi kasa kusa da kafafun shi ta zauna,kan ta a kasa domin wani irin nauyi da kunyar hada idanu da shi take,kallon ta yayi for some mints sannan a hankali yace "Da ina kike tunanin zuwa Maman Khairat?"ya jefo mata tambayar.


A take idanun ta suka fara tsiyayar da hawaye, "Abban Khairat gidan mu zan tafi in samu in sanar da su halin da muke ciki,I want to confess to my crimes duniya su san wace irin mace ce ni,in ya so ko kashe ni ne ayi,duniya ta yi mun tofin Allah tsine ko zan samu na ji sanyi a rai na,na sani I have been nothing but a terrible wife and a bad mother to my own children ban yi deserving cigaba da rayuwa ba,gwamma na mutu maybe in babu ni ka samu peace da kwanciyar hankalin da baka samu ba tunda ka aure ni"ta kare tana wani irin kuka zuciyar ta na zafi.


  "Kin yi tunanin makomar yaran ki in kika aikata abinda kike shirin yi?ko ni kin yi tunanin halin da zan fada?"da sauri ta dago ta kalle shi "yeah haka dai na ce Kareematu so kike duk inda su Khairi suka wuce ace ga yaran da aka kama Maman su a hotel tana iskanci ko so kike duk inda na wuce a ce ga mijin da ya kama matar shi da wani suna iskanci?ko kina daukan mutuwa shine mafi sauki a gare ki,shi kuma abinda za ki tarar a can fa kin shirya amsa wa Ubangiji ki tambayoyin da zai miki?ko kin manta duk abinda kike yi yana kallon ki ne,and sai ya tsaida ke a kai,me za ki ce da shi in kin mutu,tunda sarai kin san abinda kika aikata babban laifi ne,Kareematu why kika biye wa son zuciyar ki,why abinda baki yi kina yarinya ba saida girman ki da yaran ki zaki aikata su"ya kare shima yana hawayen.


Cikin kuka tace "Abdoul hakikanin Gaskiya babu babbar azaluma wace bata son kan ta iri na,babu abinda ka gaza mun amman kullum buri na in kuntata maka,na kasa hakuri nayi tawakkali da abinda Allah ya hore mana kullum buri na shine in ga na shiga sahun manyan mata masu juya duniya a hannun su,hakan ya sanya idanu na suka rufe na mance da irin gidan da na fito,nayi watsi da tarbiyar da aka mun,na mance ni Matar aure ce wanda mijin ta ke kaunar ta a shirye yake ya sadaukar da rayuwar shi don farin cikin ta,na manta da amanar yaran da na haifa wanda suke tsananin kauna da jin tausayi na,nayi watsi da addini na ba tare da tuannin ranar da zan kwanta a kabari a tashe ni tare da nuna mun ayyukan da na aikata ba,nayi iya kokari na ganin na boye maka da duk duniya halin da nake ciki,amman na mance wanda ya yi ni,ko cikin kasa na shige yana kallo na,tabbas nan kyauta ba ban kuma kyauta wa rayuwa ta,Abdoul na kasance mace me son zuciya da tsananin son kan ta da kuma abin duniya,na sani nayi maka abubuwa da yawa marasa dadi amman don Allah kafin ka sake ni ka yafe mun abubuwan da na maka sanann ka yafe mun cin amanar Auran ka da nayi in za ka iya,ko zan samu in mutu cikin sauki,wallahi tallahi nayi nadama nayi danasanin biye wa son zuciya sannann ina tsananin tsoron haduwa ta da ubangiji na domin zina yana daya daga cikin manyan laifuka"ta kare tana fashewa da kuka,shi din ma kukan ya ke yi domin ba karamin ciwo abin yayi masa ba,wlhy ko wahayi aka yi masa kan Kareematu za ta bi maza zai ce karya ne ko yace kuskusre ne ba Matar shi ba,yana son Kareematu soyayyar ta zai iya ce wa halitta ce ko jarabawa a gare shi,ba karamin girgiza yayi da ganin ta a jikin wani Kato ba,yana mugun kishin ta ya sanya ma ya bar musu gidan na kwana uku don ya samu zuciyar shi tayi sanyi sanann ya san matakin dauka,yayi kuka sosai har ya gode wa Allah and he think it sosai sosai don har Allah ya baiwa zabi sannan ya samu nutsuwa da kwanciyar hankalin dawo wa gida.


   "Kareematu!sai kuma ya dan yi shiru tare da goge hawayen shi,idanu ta har yanzu na zube a kan shi, "tabbas abinda kika yi ba ki kyauta ba,and wlhy ba wani ba wa kan ki ne baki kyauta ba,amman tunda har Allah yayi kin gane laifin ki kuma kin yi nadama Allahu gafurur Rahim ne in ya so sai ya gafarta miki,tun randa abun ya faru nayi iya kokari na tare da rokon Allah ya bani ikon mallakar zuciya ta kar na yanke hukunci cikin fushi,Kareematu na san za kiyi mamaki sosai ganin ban dau matakin da kike tsamanin zan dauka a kan ki ba,maybe kin dau zan sake ki immediately,ko in tozarta ki ko?da sauri ta daga kan ta domin tayi deserving hakan,murmushi ya dan yi sannan ya cigaba Kareematu ke mata ta ce ta sunnna wanda na aura out of so da kaunar da nake miki,muna da yara har 4 tare da ke miye riba na in na tozarta ki?uwar yara na riba me zan samu,ni ne ya dace na tsaya kai da fata ganin na kare mutunci da martaban ki,hakikanin gaskiya in da laifin ki nima da nawa,ko da na rasa aiki na na saida gida na don biyan bashin da na ci don ganin Kim gama karatun ki,ba shi ya bani daman mike kafa in gaza neman wani aikin ba,na san ki sarai Kareematu kina da son kyale kyalen duniya wanda a jinin ya wancin mata ya ke,wallahi da ace na azurta ki da komai da ba za ki bi mazan waje ba,domin na tabbatar kina kauna ta kuma ba wai na gaza gurin biya miki bukatar and auratayya bane,so ina so kiyi hakuri ki yafe ni,don nima ban sauke dukkan nauyin da ke kai na".


 Da sauri tace "Aa Abdoul Wlhy babu ruwan ka,ba kai bane son zuciya ta ne ta jawo,da ace na sanya wa kai na godiya da abinda na samu da duk haka ne faru ba,Allah ya sani nima sheda ce kana iya bakin kokarin ka a kan mu,ni dai don son ka da manzon Allah SAW ka yafe mun ,wallahi ba zan kara ba,in ga so sai nayi tafiya ta inda ba za a kara jin labari na ba,in yi ta rokon Allah yafiya har mutuwa ta riske ni"ta kare tana durkusawa gaban shi,tare da hade hannaye guri guda alamun roko,tana kan kuka har yanzu.


"Bar kukan nan haka don Allah,Kareematu in dai ni ne wlhy na yafe miki duniya da lahira,tun randa na aure ki aka kawo ki gida na nace wa kai na duk abinda za ki mun duk girman laifi na dauki alkawari kan na yafe miki duniya da lahira,laifi da wanda na sani da wanda ban sani ba in dai ke kika yin mun na riga da na yafe ki,don haka tsakani na da ke Wlhy n yafe,saidai ki roki Allah ya yafe ki na saba mishi da kika yi nima in sha Allah zan taya ki rokon shi,batun tafiya kuma babu inda za ki je aure na da ke ina fatan har Aljanna ki kasance mata na,kuma ina me miki farin ciki tare da kara roka miki Allah kan ya cigaba da shirya ki,domin babu ribar rabuwar mu bayan shekarun da muka dauka tare,ina son ki Kareematu ina kaunar ki soyayyar ki halitta ce a jini na yake,kuma ina ji a jiki na da shi zan koma wa Mahalicci na"da sauri ta mike tsaye tana me girgiza kan ta cikin tsananin kuka "Aa Abdoul don Allah kar ka yaudari kan ka akan tausayi na da kake ji,in kuma mafarki nake to ka farkar da ni don Allah,amman sam ba mu dace mu cigaba da zama ba,Abdoul

Ka san maza nawa na bi kuwa??amanar Auran ka na ci fa,wani irin mutum ne kai don Allah??anya akwai zuciya cikin kirjin kuwa?"ta kare tana kuka.


Murmushi yayi tare da kamo fuskan ta ya shiga goge mata hawayen ta "ban aure ki don in kin mun wani abu na rabu da ke ba wataran,duk wuya duk rintsi na yarda zan zauna da ke,domin soyayya ba karya bane,duk wanda zai guje ka bayan laifi ko wani abu in ya same ka ba masoyin gaske bane,and Allah ne ya nufe ki da Alkhairi da be taba tona miki asiri ba,sannan yanzu ya nufe ki da rahma da ya sanyo miki shirya,don haka na yafe miki zama na da ke kuma har karshen numfashin mu in sha Allah,Allah ya kare gaba ya tsare mana Imanin mu,masu hali irin haka Allah ya shirya su,saidai ina neman abu biyu daga gare ki"da sauri tace "fada mun koma miye ne zan yi maka Wlhy"saida ya murmusa sanann yace "ki mun alkwarin ba za ki sake bin maza ba"da sauri tace "har abada Abdoul wlhy ba zan sake ba na tuba na daina,gobe ma zan je in kai musu takardar barin aiki na"murmushi  yayi sannan yace "Allah ya miki Albarka ya kara shirya mu baki daya,ban yarda ko a labari wasu su ji wannan sirrin na mu ba,ki binne shi a ranki kamar yanda nima zan birne a nawa ran mu mutu da shi,duk tsanani duk wuya kar ki kuskura ki fada wa kowa tunda Allah ya rufa miki asiri babu wanda ya isa ya tona miki,duk randa kika sake kika fada wa wani to ba zan taba yafe miki ba"kankame shi sosai tayi tana wani irin kuka tare da masa godiya,tana yaba kyan hali da mutunci irin na Abdoul,anya a duniya za a samu miji irin shi kuwa,baya kama ta da yayi da idanun shi wai har ya yafe mata sanann ya ki sakin ta,tabbas Abdoul irin su ne ake kira d mazan rufin asiri masu kaunar ka da tsaya maka a ko wani hali kake ciki,hakan da yayi kuwa ba karamin kima mutunci da martaba ya kara a idanun ta ba,tana jin kaunar shi da tausayin shi har cikin ran ta,ta cutar da kan ta da tayi ta masa cin mutunci da wulakanci a baya,(🥹🥹hakika nin Gaskiya ko ni abun da Abdoul yayi ya mugun burge ni🤧🤧haka mijin kwarai ya dace a same da halin dattaku irin nashi,Allah ya ba mu ikon mallakar zukatan mu yayin da muka yi fushi😩).



 Washe garin ranar kuwa ta kai takardar barin aikin ta,da kudaden hannun ta tas ta kwashe ta baiwa Abdoul ya ja jari tare da yi musu chefane da biya wa yaran kudin makatanta,inda Allah yayi kuwa ya fara a saa ko in ce kafar dama domin cikin kankanin lokaci sai ga budi ta ko ta ina,wani irin tattali da kula daga shi har yaran suke baiwa Kareematu inda ita kuma sam ta kasa sakin jiki kullum tana cikin kuka da tuba tare da danasanin abin da ta aikata,Abdoul yayi fadan har ya gaji,domin tun randa suka yi maganar ya nuna mata komai ya wuce ko a fuska be kara nuna mata wani alamun wani abu ba,amman an ce wai guilty conscience ba zai taba barin ta ta sake ba kuma,inda yanzu ita kanta ta fi jin dadin kan ta,babu inda take zuwa kullum tana gida kusa da mijin ta da yaran ta,haka take bata dare babu bacci kullum tana cikin salla tare da kuka gurin rokon Allah kan ya yafe mata,don yanzu kullum tana cikin sallah da zama da hijabi kamar me takaba,tayi sanyi sosai kamar ba Sister Kareematu ba wayar ma gaba daya ta daina amfani da shi,ibadar ta ne kawai a gaban ta,cikin kan kanin lokaci duk ta fice a hayyacin ta tayi baki sosai.


Sati biyu da faruwar haka ta kwana tare da tashi da wata irin matsananciyar zazzabi me zafin gaske har sumbatu yake sanya ta,cikin azama Abdoul ya sanya ta a motar da be fi kwana uku da siyar sa ba suka wuce asibiti yana ta yi mata sannu,ko da suka isa ba a sha wuya ba aka dauki jinin ta don yi mata test a san me ke damun ta,a tunanin likita malaria ne saida gwajin ya nuna ba shi bane,da aka zurfufa bincike ne aka gano ta na dauke da cuta me karya garkuwar jiki wato (HIV).


  Ba karamin girgiza da tashi hankulan su yayi ba,inda tayi kuka kamar za ta mutu domin gani take rayuwar ta ya zo karshe,har ga Allah ta so tana da sauran lokaci da za ta nuna wa yaran ta da mijin ta so saidai babu yanda ta iya da abinda Allah ya so faruwar shi,sosai likita ya shiga kwantar musu da hankali inda ya ke sanar musu ana rayuwa in har aka bi kaidojin shan magani da cin abin gina jiki,basu bar asibitin ba saida Abdoul ya sa a dauki nashi jinin a gwada inda aka yi dace shi bayi da shi,domin rabon da  su yi kwanciyar aure da Kareematu har ya manta,kullum ya zo mata sai ta gaji ko baya ganin su Khairat sun girma ne,saida yayi da gaske sannan ya samu hankalin Kareematu ya kwanta,inda ya nuna mata kar ta butulce wa Allahn ta daman ko wani tuba da kalubalan da ya ke zuwa ta sani ko silan cutar nan ya zamo silan kankaran zunuban ta ranar lahira ta tashi fess sai Aljanna,da irin wannan kalaman da nasihan ya samu ya kwantar mata da hankali tare da karfafa ta ta shiga cigaba da ibadar ta babu dare babu rana.


Abdoul duk inda ake neman mutumin kirki mijin arziki to ya ma wuce gurin domin ya tsaya kai da kafa gurin ganin ya dauke wa Kareematu damuwar ta,tare da karfafa ta kullum,shi ke bata abinci ya tabbatar kuma ta sha magani a kan lokaci,ko da wasa ne bari wani ya san da abinda ke damun ta ko da yan gidan su suka samu labarin jinyar ta,ce musu yayi Malaria da typhoid ne suka yi mata mugun kamu,haka ta cigaba da rayuwa cikin godiya wa ubangijin ta kullum da ya bata daman tuba da wuri,a yayin da ta tsine wa Alh Jidda domin tabbas shine baren da ta sadu da ita na karshe kafin kuma Bashir tabbas shi ya sanya mata cutar nan don be yi using protection ba lokacin in za ta tuna,murmushin bakin ciki tayi ashe shine dalilin bata milayan guda da yayi,ya san ya cuce ta ya kassara mata rayuwa,wani gefen tana tausayin Bashir domin ta san tabbas shima a yanzu ya samu,amman madallan shi neman matan shi ya jawo masa,Alhamdulilah ita Allah ma na kaunar ta da ya sanya ta gano laifin ta ta tuba da wuri sannan ya hada ta da miji me kaunar ta,tabbas karshen Bashir ba zai yi kyau ba.


Kwata kwata ta gaza kwantar da hankalin ta duk da irin kulan da Abdoul ke bata,abubuwan ne duk sun hadu sun yi mata yawa,inda ya tsaya da cin abincin ta ne ya sanya ko kusa ba ta rame ta lalace ba,saidai ta dan fada kam,kullum to mutum yana cikin kuka,haka kawai take jin kamar mutuwar ta na kusa,a duk sanda ta fada wa Abdoul sai yace mata wa ya fada mata cuta mutuwa ce mutane nawa ke rayuwa da HIV a duniyar nan ita ma babu inda za ta za su rayu tare har su aurar da Khairiyar su,ta kan yi murmushi tace "Abdoul da ko wace mace za ta yi dace da samun miji irin ka da na tabbatar yanzu babu zaurawa a duniya,na gode sosai Allah ya saka maka da mafificin Alkhairai Allah ya kara wa rayuwar ka albarka,na gode sosai sosai"wannan shine maganar su ta karshe inda ya nuna mata baya jin dadi in tana kasa godiyar nan hakkin sa ne yayi mata,wanann daran ta ji dadin jikin ta sosai sosai don tare duk suka ci kaji da ice cream da yaran da ya siyo musu,aka ta hira ana wasa ana raha har around 11:30 sannan ta ce da su kowa ya je ya kwanta domin ta gaji sosai,a rungume a kirjin Abdoul bacci ya dauke ta yana tsaka da mata hira,ganin tayi bacci ne ya sanya ya gyara musu kwanciya.


 Kamar yanda ta saba 3 dot ta farka a hankali ta zame jiki ta shige bandaki don tsarki da dauro alola,haka kawai take jin jikin ta a mace duk sai tana jin ta wani iri,a daddafe tayi alola ta zo ta tada sallah,in ta samu tayi raka'ar farko da kyar,ta kai Sujjada a Raka'a ta biyu Allah yayi  ba za ta mike ba domin ya karbi abun shi,inalilahi wa inalilhi raju'un Allah na ka bamu mutuwa me sauki 🥹ka ba mu ikon tafiya in lokacin mu ya zo ka sa mu cika da imani,tabbas Kareematu ta yi laifufuka da yawa a rayuwar ta amman da ke tana da rabo sai Allah ya bata ikon tuba sannan ya bata ikon tafiya tafiya mafi kyawu tana cikin sallan dare🥹🥹Allah ka jikan iyayen mu da suka riga mu gidan Gaskiya mu ma ka ba mu ikon tuba me kyau kafin mutuwar mu ta riske mu.


  Asuban fari suka tashi da mutuwar Kareematu,ba karamin girgiza su mutuwar yayi ba,sun yi kuka sosai har suka gode wa Allah,a haka aka wanke ta aka kai ta gidan ta na gaskiya,Abdoul bakin shi dauke da yi mata adduar samun rahmar ubangiji tare da sanya mata albarka yana fadin yayi rashin mata ta kwarai shi kam yanzu ba zai kuma aure ba domin Kareematu ce kadai matar da ya so kuma zai cigaba da so har ran da zai mutu,nan ya rungumo yaran shi tare da koya musu sanya Mahaifiyar su a addua duk sanda suka yi sallah,haka yan uwa da abokan arziki suka yi ta zuwa masa gaisuwa suna taya shi kuka don kowa ya san irin son da ya ke yi mata,amman babu yanda ya iya dole ya sanya wa kan shi hakuri tare da daukan  alkwarin ba zai taba daina yi wa Kareematu addua ba,sannan ba zai taba iya kara aure ba,business din shi ya cigaba da yi yana cigaba da kula da yaran shi,tare da nema wa matar shi yafiya da rahmar ubangiji.



        ***************Family din Audu Waziri 


    Tun ranar da Nameer ya fito da Sen aka wuce da shi asibitin mahaukata domin duba lafiyar shi,inda kafin a isa hauka kam ya dauki uwar daki,gwajin duniya lokitoci sun yi amman ance lafiyar brain din shi lau babu abinda ke damun shi,na rasa gano haukar daga ina ne,nan aka daddaure shi da manyan chains sanann a ka kulle shi a daki shi kadai domin haukar na shi ta yi yawa,inda daga gurin direct asibiti ya wuce aka yi admitting Hajiya Rakeeba da ita Karan kanta Nadeeyar likita ya ce sai ya duba ta,don in baku manta ba daga tiyata ta taso.


Sati guda sannan aka samu Hajiya Rakeeba ta dawo hayyacin ta domin ba karamin wahala aka sha ba gurin ganin an ceto rayuwar ta,zuciyar ta by now ya kumbura sosai any small shock zai iya karasa ta,don already heart din yayi so weak,kuka kam sun yi idanun su har saida yayi jawur,Nameer da Nadeeya tare da Small mom har gida suka je gurin Alh Salisu domin bashi hakuri da nema wa Sen yafiya,fushi yayi sosai domin Sen ya cuce shi for all this will ashe Ritualist ne shi ne be sani ba,suka kulla aminta haka,sosai Nadeeya tayi ta bashi baki har aka samu ya hakura domin sam ba laifin Nadeeya bane,nan ya nuna musu babu komai wallahi laifin da Sen ya masa kuma ya yafe mishi ya ci darajar Nadeeya,sannan ta kwantar da hankalin ta in sha Allah daga yau sai inda karfin shi ya kare a kan ta,domin daga yau ta zamo responsibility din shi,zai zamo mata uban da tayi rashi,daga yau zai zamo gatan ta,Allah kuma ya mata albarka da ita da Nameer,sai a lokacin hankalin ta ya dan kwanta,ina ma tana da dama kuma ta san duk mutanen da Sen ya cuta da ta bi su ko da za su buge ta ne ta nema musu yafiya,domin Nameer ya sanar mata wani hakkin tsakanin bayi Allah baya yafewa wani kuma ya kan yafe domin shi me yawan yafiya ne ga wanda ya so,to in ta ce haka za ta yi ta ina ma za ta fara bayan wasun sun riga da ma sun bar duniyar,abinda in ta tuna yake kuma sanya ta kuka ke nan.


   Hajiya Rakeeba ba  karamin kuka ta rizga ba da ta farfado,tayi kuka har ta gode wa Allah,babu abinda in ta tuna ke mata ciwo kamar wai dan ta ne yayi sanadiyar mutuwar abokiyar zaman ta,matar da ta raine sa tun yana dan yaro,ta so shi fiye da yaran cikin ta,sannan kuma wai shine ya cinye uban shi da ya nuna mishi kauna fiye da sauran yaran shi,ya kuma yi sanadiyar kwantar Usman a jinya na tsahon shekaru,ya kuma kashe yara da kuma matar Usman,ya cinye Maman Nadeeya da sauran matan shi,inalilahi wa ina ilaihi raju'un in ta tuna wai daga cikin ta wannan monster din ya fito shine abinda ya ke kara sanya ta kuka,ace wai ita ta Haifa irin wanann annoban wa duniya,ace Abul bait kadai yayi sanadin mutuwar rai da dama,Wlhy da ta san abinda za ta Haifa ke nan da bata yi Auran ba ma wlhy,in ko da ta sani da ta cire mahaifar ta da zuwan wanann duniya gwamma ta mutu ba haihuwa,Wlhy da ta sani da tun randa ta haife shi ta zaune shi ya koma wa mahaliccin shi da yanzu ta huta,saida aka dage mata sosai aka samu aka shawo kanta har aka sallame su,wata tashin hankalin wai ba a sanya miki rana tuni labari ya bazu ta ko ta ina,domin su Sa'eed sun saki Video din fadafaden Sen da haukan shi,inda gari ya dauka kowa sai tofin Allah tsine da tsine masa suke,wato ya dade tana yaudarar mutane da sanya riga da fuskan musulinci,tare da Allah wadarai da halin irin na Sen da Kabiru.



  Ko da suka koma gida Hajiya ta hana kowa zuwa asibiti duba halin da Rilwanu ke ciki,domin ta ce babu ita babu shi kuma bata yafe mishi nonon ta da ya sha ba duniya da lahira sai sun tsaya gaban Allah,domin Allah ya gani iya yin ta yi gurin ganin ta bashi tarbiyya na gari amman ya cuci kan shi tare da fadawa harkan shan jini don tsaban son abin duniya,she has to be so strong ko dan yaran ta da jikokin ta,Allah ma ya taimaka yayun ta tsaye suke akan kafafun su so ba su ba wa matan su daman yin gutsiri tsomi ba,don rantsuwa suka yi duk yar iskar da ta tsoki Hajiya Rakeeba kan abinda Rilwanu yayi a bakin Auran ta,don labari har gidan radio,ko da Alh salis ya ji a gidan Radio ran shi be so ba,amman aikin gama ya gama already kuma wai ance tsuntsun da ya ja ruwa.



Ummi ce ma ta so samun matsala a gidan Auran ta domin mijin ta irin murdadun mazan nan ne,don har sai da ta dawo gida satin ta guda,kafin Nameer ya shiga maganar aka samu ta koma dakin ta,don baka da right din hukunta wani da laifin wani,ciki daya suka fito amman halin kowa daban,Alhamdulilah Usman ya tashi shima ya ci kuka kamar zai mutu,Yan biyu ma sun samu labari sun sami zuwa inda suka yi kuka kamar su mutu suma,Hajiya ba karamin nauyi da kunyar su take ji ba,haka ta duka har kasa tare da hade hannaye guri guda tana me rokon su yafiya,inda suka nuna mata basu ji dadin yanda ta ke rokon su ba,uwar su ce ita kuma Abul yayan su ne suna mishi fatan shiriya ,saidai da sanda yake tafiya,Hajiya da kanta ta ce da su Nameer su koma ganin dawainiyar tayi yawa ba a son ran shi ba suka tafi shi da Mama don su ma suna da abubuwan yi,saida ya tabbatar ya yi settling din su da kudi me nauyi sanann ya tafi kan in sha Allah zuwa karshen wata zai dawo,haka suka rabu suna kewan juna inda suka tafi tare da Ummu suka sauke ta a Zaria.



 Saidai tunda suka koma Kaduna Nameer ya kasa samun nutsuwa domin zuciyar shi na Azare gurin Nadeeya,ya so sanar da ita sirrin ran shi kafin su tafi,amman ganin halin da take ciki ne ya sanya ya ce is not the right ya fada mata,domin ba karamin sanyi ta yi ba,daga ita har Hajiya sun koma wani irin shiru shiru,sam basa yawan shiga mutune,barin  Nadeeya yanzu duk rabi da kwatan time din ta tana spending din su ne gurin daukan karatu a gurin Hajiya,Alhamdulilah yanzu ta iya alola,ta iya sallah yanda Annabi ya koyar ta iya tsarki,kuma za ta iya kawo maka daga Na'si zuwa Sabbi wato izu daya da kai,don Masha Allah yarinyar tana da saurin daukan karatu,ita kan ta wani dadi da nishadi take ji tare da nutsuwa domin nutsuwa sosai ke tattare da ibadan Allah,ubangiji ya dauwamar da digadigan mu akan addinin shi.



      *************************Doc Bashir



    Tabbas akwai certain mutanen da sam basu son Allah nayi musu talala ba,akwai mutanen da shagala son zuciya da neman duniya suka rufe musu idanu,duk wani sign da ya kama ta mutum ya gane Allah na fushi da shi baya gane wa,wasun kuma su kan gane amman ba su sa ranar bari ba,wasu kuma suna son bari amman Allah be yi lokacin shiryan su tayi ba,tabbas kowa da irin yanda Allah ya hallice shi and babu me son shiga wuta sai wanda Allah ya so,in Allah ya wanke maka zuciyar ka tare da kare ka ya gama maka babban rabo domin za ka na taka tsantsan gurin sabon shi,hakika rahma ne ma ka yi sabo har ka samu daman tuba don ka san abinda kayi ba daidai bane,akwai mutanan da laifi suke amman sam ba su ma sa a rai ba daidai suke balle har su sanya lahadin tuba ba,wani ko Aya guda ya gani kan idon shi sabida kankashewar zuciyar shi ba zai tuba ya koma wa Allah ba,some one like Doc Bashir,da yawan mutane su kan faro rayuwar su da aikata aikin Alkhairi sai sun zo gab da mutuwa sai littafin su ya juya su koma aikata aiki irin na yan wuta karshe su mutu su shiga wutan Allah ya mana tsari,wasu kuma kan faro rayuwar su da aikata aikin banza,sai gab mutuwar shi sai ya littafin sa ya juya ya koma aikata aikin yan Aljannah karshe Allah ya masa rahma ya mutu ya shige ta (some one like Kareematu),babu abinda Allah baya yi,shi ke yin abinda ya so lokacin da ya so kuma ba mu isa tambayar shi me ya sa ba,duniyar nan karamin guri ne try your very best ganin mun aikata Alkhairi da har mu koma gare shi ana yaban mu da shi,Allah ka raba mu da munannan karshe ka bamu ikon rayuwa me kyau me dadi sannan ka ba mu saar tafiya in lokacin mu ya zo.



   Tun randa mijin Kareematu ya kama shi da ita a hotel suna zina na dauka Bashir zai saduda ya koma ga Allah,amman sam be ma sanya lahadin tuba ba balle ya ji a ran shi zai bari,ammn ina ko kadan jikin shi be yi sanyi ba balle ya ji zai tuba,ya yi iya yin shi ganin ya samo Kareematu sun cigaba amman ina duk wasu layukan ta na rufe,yayi bakin ciki sosai da ya ji labarin ta bar aiki,domin baya ma asibitin ta kawo takaddar,yayi iya yin shi ganin ya nemo ta amman abu ya ci tura,domin ba karamin sabo yayi da jikin ta ba yana jin dadin ta fiye da tunanin me tunani,kun Riga da kun san yanda Zina ke da mugun kama rai,saisa Allah da kan shi yace "ka da ku kusanci Zina" ba ma kar kuyi ba don ilolin ta yawa gare ta,(Allah ka tsare mu da zuriar mu baki daya).



Ganin ya rasa Kareematu be sanya ya saduda ba sai ya cigaba da neman matan shi up and down,ya cigaba da forcing kan shi kan kananun nurses in sun ki yarda kuma ya sanya a kore su,ance daman duk abinda kake dubun ka wataran sai ya cika,Doc Haneefa ce ta gaji da irin halin iskanci na shi da halin karnikan ci ya sanya suka hada kai da Nurses din da yayi assaulting suka hade kai suka kai kara sama,a take kuwa aka karbi korafin nasu domin Haneefar mijin ta ana  damawa da shi a gwamnati,ganin korafin nashi tai yawa ne ga cuta ga bin mata,ga kora ba a kan ka'ida ba ya sanya aka yi gaggawar dakatarwa da shi tare da kwace License din shi,saida yayi da gaske ma aka hakura ba tare da an kai shi  gidan gyaran hali ba,lokaci daya duniya ta nemi juya mishi baya,irin wannan kora babu kudin Pension and gratitude 😂,gashi sam shi ba mutum bane me wani tattali baya jin akwai wasu kudi masu nauyi cikin account din sa,to duk ya kwashe ya baiwa matan kan hanya,daman da aikin ya dogara don ko business ba yi yake ba,inda aka baiwa Doc Haneefatu matsayin Doc Bashir,Habeeb kuma aka ba shi matemakin ta,Nameer da Muhibba ba karamin murna suka yi ba,don Nameer ya riga ya rubuta letter of request son dakatar da aikin shi da asibitin don yana son zuwa Abroad karo karatun shi.



   Around bayan la'asar Doc Bashir yayi dawowar bazata gidan shi,domin sam Murja bata da masaniyar zai dawo da yamman don kwana biyun nan sai cikin dare ya ke dawo wa gida,tsit ya ji tsakar gidan kamar ba kowa a ciki ,mamaki ne ya kama shi ganin be ji ko mostin Murja ba,karamar diyar shi da ke zaune ta ci kuka har ta gaji ya kalla inda tayi dama dama da jikin ta da kashi,flies sai bin ta suke.


  "Keee ina Mamar taki take kina nan zaune ke kadai??",cikin gwarance tace "Baba yaya makota" "na ji su yayan ki na makota Mamar ki fa ko ita ma tana makotar??",kai ta girgiza tana shan majina tace "Mama daki",be jira kuma jin ta bakin ta ba ya wuce dakin Murjan saidai wayam babu ita,dogon tsaki ya ja tare da kudurtawa a ran shi bata nan ne kuma Wlhy in har ta dawo sai ya ci Uban ta,domin ya gaji da mugun halin da Murja ke masa tun bayan rasa aikin sa,hanyar dakin shi ya nufa ran shi matukar bace,wani irin wawan burki ya ja tare da jin zuciyar shi ta buga da sauri,sakamakon wasu irin kananun kuka da ihun mace da na miji da ya ke ji daga cikin dakin shi,the more yana nufan dakin the more yana jiwo wasu irin Nishina masu karfi da fitar da mutum daga hayyacin shi,tabbas wannan ihun na Murja ne and a iya sanin shi sai lokacin da ake saduwa da ita take irin kananun kukan nan,to in shi yana nan ihun wa yake jiyowa daga cikin dakin baccin shi,kar dai da sauri ta ka'war da wannan tunanin "inaaa Murja ba za ta ci amanar aure na ba,da me na rage ta da za ta bi maza,mazan ma har cikin gidan auran ta,da kyar ya iya hade kan shi guri guda tare da kama handle din kofar ya bude kamar ran shi zai fito tsaban tsoro da firgici,wata wawan ihu ya sake a daidai lokacin da idanun sa suka yi arba da Murja Matar Auran shi tumbur ba kaya jiki ta tayi darai darai a kan Tajo yaron gidan shi shima a tube tana tsaka da tsalle a kan shi inda shi kuma ya riko gashin kan ta,ya mimmike sai wasu uban nishi ya ke kamar me shirin haihuwa,ganin sam ba su ka san da zuwan nashi bane ya kuma harzuka shi,a gaggauce ya nufe su be yi wata wata ba ya finciko Murja tare da watso ta kasa,Tajo da idanun sa a rufe jin ta daina jiyar da shi dadi ya sanya shi cewa "Wayyyo My Kankanaty why kuka bari bayan kin san ban Riga na koshi ba".


  "Babban Bura Uba kai Tajo dan me cin Uwa ta ka matar tawa kake kira kankanaty??Ke Murja ashe yar iska ce ke Mazinaciya ban sani ba,dan Bura uban ki kwarto har cikin daki na,a hakan ma ki rasa wanda za ki kawo sai yaron da na Raina,Tajo upon all the people na duniyar nan"cikin kidima da tsoron Tajo ya ce don Allah Dacta kayi hakuri Wlhy ba yin kaina bane ita ke matsa mun kullum"


 "Kayi mun shiru dan uban ka matsa maka ko,daga yau ko Nonon mace be kuma kara baka sha'awa bayan na tabbatar da na ci uban ka balle ka yi tunanin kara neman wata mata,don baka da hankali Tajo ni da na maka rana ni za ka yi wa Bura Uba ni za ka nemi mata ta,babu abinda zai hana ni cin uwar ku Wlhy sai na yada ku a duniya tunda baku da mutunci baku san hallaci ba,ke Murja miye ban miki ba a duniyar nan amman ki rasa wa zaki nema sai Tajo kam bala'i Wlhy yanda kuke a tube ko arzikin zani ban bari ku daura haka za mu tafi gurin yan sanda su cika mana FIR mu shige court yasin sai an kashe ki tunda shegiya ce ke,kai kuma sai kayi gidan yari don ba zan bari a maka bulalai kadai ba,shegu  yayan yan isku sai na ga bayan ku wlhy"ba karamin kyarma jikin su ke yi ba tabbas a hauka irin na Bashir zai aikata fiye da hakan ma,ganin yana kokarin fita don tara musu mutane ne ya sanya Murja daukan babban flower vase da ke gefen ta bata yi wata wata ba ta muka mishi a kai,a take kuwa ya zube a kasa sumamme jini sai malala ya ke bayan ihun da ya kwalla,juyowa tayi a harzuke ta watsa wa Tajo mugun kallo da ke  ta kuka jikin shi na ta kyarma don ya mugun tsorota, "kai dallah tashi sakarai wawa kawai,kana na miji amman ka tsaya kukan banza ko ni mace na fika kokari,shege duk dadin da ka kwasa a jiki na amman wai dole na maka zan ci uban ka ni da kaine wlhy"


Cikin sauri kuwa mike "Murjiss ya zamu yi da Bashir kar fa ya mutu", " kai dallah manta  da dan iska,ni zai wa karyar bariki,da ke shege ne ba mijin rufin asiri ba wai ni ya ke son yi wa tireran bankada a duniya,dan uban shi duk matan shi sun guje shi ni kadai na zauna da shi,amman ba zai iya kau da kai duk abinda nayi masa ba,tashi dallah mu wuce"ba tare da musu ba kuwa ya mike kuwa ya sanya kayan sa,saida suka tabbatar sun kwashe duk wani kudi da abin kudi da ke gidan sanann suka kada wa keyar su iska suka san yanda dare ta musu,(😂😂😂dadi na da Ubangiji wata sakkayar tun a duniay ake yin ta,wato Bashir kai ne me zuciya a kirji ko😂😂ka san kishi time din da kake kwana da matan wasu su mazajen su basu da kishi ne???ai daman Zina bashi ce,in kayi da uwar wani ayi da uwar ka,kayi da yar wani ayi da yar ka,kayi da matar wani a yi da matar ka,ah toh kai kana tunanin ka ci bulus ko,to ba a yi wa Allah wayo ai,Allah ya shirya masu son kai zuciya da son iskanci irin na Doc Bashir ya shirya mu ya shirya mana zuriar mu ba don halin mu ba🥹).



Kwanan Bashir guda yana sume kafin ya farfado,tashin hankali ba a sa mata rana tun daga ranar da su Murja suka gudu mishi da dukiya ya bi ya lalace ya kasa tawakalli domin ko ficika ba su bar mishi a cikin account din shi ba,saida yayi yar karamar hauka,ya neme su har ya gaji,yayi kuka kamar idanun shi za su fita,inda a karshe ya kwanta jinya domin wasu manyan kuraje ne suka fito masa kafin ka ce me sun fara fashe wa sannu a hankali ya fara wari,Zahrau da Hadiza da suke rayuwa cikin kwanciyar hankali da sabin mazajen da suka aura suka zo tare da kwashe yaran su,domin ance wani hanin ga Allah baiwa ce Allah ya musu sauyi da mazaje masu son su kauna da kula da su in kun ga yanda suka yi jawur suka murje kamar ba su ba😂Masha Allah arziki ya zauna,sun matukar tausaya wa halin da Bashir ya ke ciki,domin gaba daya abokai mutanan unguwa da yaran cikin shi ma sun guje shi,(yo daman baka ji kan yara ka tausaya musu ba tsoron ka suke ji da zasu ji kan ka su tausaya maka,Allah ka bamu ikon yi wa yaran mu adalci tare da sauke dukkan nauyin su da ke kan mu🥹),a nan ne fa suka ba shi kudi tare da kayan abinci don ya samu ya je asibiti a duba me ke damun shi,da kallo ya rings bin su ganin yanda rayuwar su ya canza lokaci guda sun yi kyau Masha Allah kamar ba matan da ya ke cin uban su ba,Allah sarki da ke akwai zuciya me kyau a kirjin su sai suka raba yaran Murja a tsakanin su akan za su kula da su tunda ta gudu ta bar su ba wanda ya san inda take,haka suka tafi Bashir yana kuka don ko magana be cika son yi ba,don har cikin baki ya ke jin kurajen nashi duk wanda yayi wa rana sun ki su taimake sa yayi kuka har ya gode wa Allah,ya a samu ya kuma gode wa su Hadiza sun bashi kudi da suka zo, haka ya samu ya lallaba ya kai kan shi asibti inda gwajin farko aka gano yana dauke da HIV,da jin gwajin sakamakon kuwa zuciyar shi ta buga a take ya fadi a gurin ya mutu,ba tare da kyakkyawar tuba wa ubangijin shi ba,inalilahi wa inna ilahi raju'un 🥹🥹Allah ka sa mu cika da imani,nan Doc ya sanya aka fitar da shi tare da kai shi mortuary,kafin Allah ya so su zahra suka samu labari aka aiko yaran shi aka gama cike cike sannan aka wuce da shi gidan shi na gaskiya,🥹ya mutu ba tare da neman yafiyar mutanan da ya cuta da zalunta ba sai mu ce Allah dai ya sa mu cika da imani.



      ************************


        "Mujaheeed ka dubi girman Allah ka taimake ni ka kara gudun motar nan,ko za mu samu mu isa da wuri wlhy zuciya ta kamar za ta fito haka nake ji,I missed her so very much ina son na kuma sanya ta a idanu na",baki bude Mujaheed ke bin shi da kallo kafin yayi kwafa ba tare da ya ce komai ba ya cigaba da tukin sa,ganin yayi banza da shi ne ya sanya yace "Ayya Buddy kana jina fa ka ke share ni"ya kare kamar kamarin yaro,burki Mujaheed ya ja tare da yin parking, "Sharukkhan uban yan soyayya ko dai na baka tukin motar ne watakila ka tasar da mu sama tunda ni sam a hankali nake tafiya"ya kare yana galla masa harara.


 "Ayya Mujaheed bara ka san yanda nake ji bane Wlhy", "yo ina ni da iya jin yanda kake ji Ai wannan sai ku manyan mu,ka san girman Allah Nameer in baka yi controlling kan ka ba ina gab da fara cin Uban ka,wai duk sai ka gama zubar mana da mutunci me gurin yarinyar nan ta san kana mata son mutuwa salon ta raina ka".


  "Wlhy Mujaheed in da raini daga Pookie ne ni kam na yarda na bata meat and knife,na amince ni mijin tace ne"wata irin wawan dariya Mujaheed ya fashe da shi "shege Nameerun Mama ka ce ka ga ba guri ka fallasa sirrin ran ka,nace nan na gani da ce mun kayi tausayin yarinyar nan kake ji?Amman sabida mugunta da bakin hali irin na ka daga jin na ce zan je neman ta shike nan ka shafa wa idon ka toka ka kwace mun mata", "Wlhy Mujaheed in Pookie bata bar idon ka ba sai na cire ma idanu matar ka a gidan uban wa",da sauri yace "gidan uban ka mana,na ga Mama da kan ta tace za ta bani ita kyauta nayi ta biyu da ita"da sauri ya daki kafadar sa "da kuwa kun kashe ni Wlhy ita ce bugun numfashi na",murmushi Mujaheed yayi sannan yace "am so happy for you my friend finally Our Little Angel za ta yi new Mommah,Allah ya sa Anty Pookie tayi saurin karban mu,kar ta wahalar da mu"da Ameen duk suka amsa sannan suka cigaba da hirarrakin su,babu yanda Mujaheed be yi ba kan su je su dauko Habeeb a zo da shi amman Nameer fir yace be san zance ba su wuce gidan su Pookie kawai.



 Sai around bayan Azahar suka shigo Azare,saidai suka tsaya suka yi sallah sannan suka nufi gidan su Hajiya Rakeeba,ba karamin dadin ganin su Hajiya ta ji ba duk da zuwan bazata suka yi mata,a take ta shiga aika wa a kawo musu abinci da abun sha,saida suka ci suka yi nak sannan Nameer ya sanya aka shigo da tulin siyayyar da yayi musu,tare da sanar da su Mama na gaida su,albarka sosai Hajiya da Uncle Usman da zuwa yanzu jikin shi na ta kyau don Nameer ya karbo mishi magani daga gurin Malam Hukmullah kuma Alhamdulilah maganin tayi masa aiki don yanzu ya kan dan yi tafiya babu sanda,ganin shiru ba su ga Nadeeya bane ya sanya Mujaheed ce wa "Hajiya mutuniyar bata nan hala"dan murmushin manta tayi domin tun ran zuwan su ta so ta fahimci Nameer kaunar jikar nata yake,in ko haka ne sai ta fi kowa jin dadi wlhy.


 "Sallah ta ke,Usman dubo mun Nadeeya ko ta idar ta fito su gaisa da yayun nata,be dade da shiga ba kuwa suka fito tare da Nadeeya tana sanye da baby pink hijab ne igiyar daurewa har kasa,a hankali Nameer ya saci kallon ya yana jin kamar ya cire zuciyar shi ya bata don kauna,da sauri ya mike sakamakon wayar shi da ya fara kara,yana fadin "Hajiya ina zuwa bari na amsa waya"murmushi tayi kawai domin tsaf ta gano komai,ba kowa ya kira wayar ba face Mujaheed don ya samu excuse din fita ganin haka ne ya sanya ta playing along ita ma bayan sun gama gaisawa da Mujaheed din tace "Nadee maza leka waje ki dubo yayan naki na ji shiru har yanzu be shigo ba",baki ta cunno gaba a hankali sannan ta nufi wujen,tana yan kananun mita,ganin baya tsakar gida ya sanya ta fita har can waje inda ta hango shi zaune cikin mota,harara ta galla wa motar sannan ta nufi inda ya ke,dan knocking tayi ba tare da ya zuge zip din ba ya bude mata motar alamun ta shiga,ba don ran ta ya so ba dai ta bude murfin motar ta shiga.


 Tunda ta shigo motar ya kafe ta da idanu ba tare da ko ya kyafta su ba,inda it kuma duk ta tsargu d kallon da yake ta bin ta da shi,baki ta turo sannan tace "Hajiya tace wai na dubo ina ka tsaya",murmushi ya dan yi tare da saukar da seat din motar ya dan kwanta,sannan a hankali ya ce “shike nan ke kullum baki zuwa gurin mutum sai in Aiken ki Hajiya tayi be jira amsar ta ba ya taso tare da zuba mata idanu,wai don Allah Pookie ni kam ni Ojuju ne da kike tsoron zuwa guri na??”ya tambaye ta yana me tsare da ta idanu.


 Baki ta turo domin duk sanda ya zuba mata ido irin haka duk sai ta ji ta a rude, “ni ka ga ina wanann kallon naka ne bana so,and why on earth will you be calling me Pookie for crying out loud my name is Nadeeya fa”ta kare kamar za ta sanya mishi kuka,shika narai narai din yayi da fuska ganin shagwaba take jin yi masa “aswear to almighty Allah you are so damn cute and adorable ne that’s why nake kiran ki da Pookie (some thing cute),and ina jin dadi duk sanda na kira ki da hakan,dan shiru duk suka yi sannan kamar wanda ya tuno wani abu,yace Yauwa what do you said about my eyes ma?Pookie don’t tell me kina jin wani iri duk sanda muke tare kuma nake kallon ki”,da sauri ta juyo “wani iri kuma ni I felt nothing kawai dai kallon naka ne na yawa”, da sauri yace “Allah Pookie ban yarda ba dole kina jin wani irin in ba haka ba why baki iya kallon cikin ido na?”shiru tayi ba tare da bashi amsa ba shi din ma shirun yayi ganin kusan 2 mints ba wanda ya ce komai ne ya sanya ta yanke shawarar komawa gida,inda shi kuma yake ta having second doubt anya ya fada mata kuwa?What if bata son shi ya zai yi?Wani gefe ne na heart din shi ke ta azazzalar shi kan kawai ya fada mata a wuce gurin,ganin ta kama murfin motar ne ya sanya shi saurin cewa “can you wait for some mints pls I want to tell you something da na dade ina binne wa a rai na”,ba ta so zaman ba amman babu yanda ta iya ya sanya ta fasa fitar “am all ears”shine abinda ta ce da shi,dan numfashi ya dan ja domin sam be ma san ta ina zai ma fara ba,zuciyar shi na tsanan ta bugawa,ganin yana bata mata time ne kuma kamar she is kind of busy ya sanya shi aro courage sannan a hankali ya kira sunan ta 


 “Nadeeyaaaa!!!bata amsa ba shima be damu sai ta amsan ba ya cigaba da fadin na san have been through a lot lately and maybe this is not the right time for me to say all this,but na kasa rike kai na I just have to let you know”jin abinda ya fada ne ya sanya ta dagowa a hankali ta kalle shi,ganin Itama shi yake kalla ne ya sanya ta saurin sauke idanun ta,cikin sanyin muryan sa me dadin sauraro yace da ita 


  “ 

      You know what??  I like you!! Out of nowhere ta ji kalman a kunnan ta,da sauri ta daga ta kalle shi,kai ya daga mata cikin dakewa yace “Yeah na san daman you will be shocked to hear this ,But I want to let you know that I like you in a way I like no one else! And am so serious, I admit  today that you set my heart on fire. You have ignited a spark in me. I have a dream to spend my life with you.

I have decided not to be shy about saying what I have been feeling for so long. I love you, and I have been hiding it since we met.

My feelings for you are not worth keeping inside. They need to be showcased in front of you. Let me do it,so I decided to do it now, coz an ce a bari ya huce shi ke kawo rabon wani,it’s good to dream and we all dream, and the universe makes it happen. I have been dreaming of being with you forever for so long!

I hope it doesn’t sound creepy that I have some special feelings for you. I love you, and it was love at first sight.🥹🥹I always thank God daily for your presence in my life,coz you have changed my whole world completely,Can you pls make this presence permanent? Coz I want you to be forever in my life,coz am madly in love with you don girman Allah Nadeeya don turn me down🥹Wlhy I can’t stand losing you”ya kare kamar zai yi kuka.


  Wata irin numfashi Nadeeya ke saukar wa domin sam bata yi tsammanin jin haka daga bakin shi ba,as in har ta kai matsayin da kamar Nameer zai budi baki ya ce yana son kai ina dole mafarki take yi,jin tayi shiru bata ce komai bane ya sanya a raunane yace “shike nan na shiga uku,baki So na ko Pookie??,ban miki ba?”da sauri ta ce “aa ko daya ba haka bane Ya Nameer I was just shocked ne da jin abinda ka fada,wait are you for real pls???”ta fada tana me satar kallon shi.


  “Just take a look deep down into my eyes your answers are there,Nadeeya kin san months nawa nayi ina boye kaunar ki a cikin zuciya ta,don Allah take me in ko za mu samu mu zamo family,ki zamo Mama wa little Haanaan din mu”ya kare ya cire wayar shi tare da shiga gurin hotuna,pictures din ta da Haanaan ya shiga nuna mata lokacin tana hauka,kallon hotunan take amman sam ba za ta iya tuna time din da aka dauke su,a hankali yace “she has lost her Mom tun randa ta zo duniya,I have been with her a kullum ni da Mama ba tare da bata chance din jin kewar late mom din ta ba,tunda nake ban taba ganin wanda Angel ta so kuma ta sake lokaci daya da ita ba irin ki,Nadeeya tun randa na gan ki na san dole akwai something special tattare da ke domin tun kan na gan ki face to face sunan ki ya kasa barin rai na,don Allah ki yarda and be my wife,ki taya ni rainon baby na pls,I can’t do without you wallahi”ya kare yana hade hannaye guri guda alamar roko,kan Nadeeya gaba daya ya kulle ta ma rasa ne za ta ce da shi,daman can ya iya magana har haka?take tambayar kan ta,jin har yanzu tayi shiru ne ya sanya shi kara fadin “ko you want me in baki some time to think about this,na san abu ne da ya zo miki bazata and baki yi tsammani ba beside ina da Daughter and mata ba ku cika son auran me mata da yara ba”


 Da sauri ta katse shi da fadi “ can you stop saying that pls,you baby is the most cutest little girl da na taba gani a rayuwa ta,and tunda nake ban taba ganin mutum me hankali,hakuri,tausayi,sanin ya kamata,taimako irin ka ba,Ya Nameer you have done a lot wa ni da family na da bani ma da bakin gode maka,akan ka ne na yarda da har yanzu Humanity still exists,coz kayi abinda ko family members dina bana jin za su iya mun,ka kashe kudi,time,energy da komai na ka don ganin ka inganta nawa rayuwar,ya Nameer am very sure da kyar a samu irin ka a rayuwar nan,and babu macen da ba za ta yi farin ciki ba in ta same ka a matsayin miji,but not Nadeeya,da sauri ya dago ya kalle ta,yeah banda Nadeeya domin ko kadan ba ku dace da ita,babu abinda baka sani ba game da ni,ka fito daga good background anyi maka tarbiyya ne kyau wanda duk inda ka shiga ana son ka tare da son kasancewa da kai,but what about me?Ko ban tuna maka ba ka san waye Dad dina ka san labari na,ka san waye tsohon miji na,as my age wai sai yanzu nake sanin farillan alola da abubuwan da ya shafi musulunci,tabbas baka dace da auran mata irina ba,domin ana ganin laifin Daddy ne kawai na yayi running life dina amman nima da kaina ni na taya shi running din,coz da ace na sanya son neman ilimin addini da yanzu ba wannan labarin ake ba,amman na watsa nima tunda be sanya ni ba nima

ban nemi in sanya kai ba,hawaye ta share a hankali sannan ta cigaba,muyi wa kan mu adalci Wlhy Ya Nameer ko kusa ba ka dace da Mace irin Nadeeya wanda uban ta ya zamo dan shan jini ba,wani tarbiyya kake son bai wa Daughter din ka after all nima sai yanzu ake mun tarbiyyan,besides ni na gama aure a rayuwa ta,bana son kara yin aure like this now I just want to work on my Deen gurin ganin na gyara tsakani na da ubangiji na shine kawai a gaba na,so pls Ya Nameer ka yi kokarin cire Nadeeya a ran ka,ka nemi mace saliha ta gari wace ta dace da kai,and har abada ba zan taba daina maka addua fatan Alkhairi da daukan ka a matsayin brother na ba,na gode sosai Allah ya saka maka da Aljannah sanann ya baka mata ta gari wace za ku yi daidai da ita”ta kare tana hawaye.


 Ya kai 3 mints yana kallon ta kafin yayi dan murmushi “so Pookie do you think am gonna judge you base on your past and story?I mean who does that,halin Dad daban naki daban,a sau nawa yan sanda suke haifan barayi?just take a good example Hajiya mace ce kamila me addini diyar malamai,inda ta auri miji shima me ilimin amman ba ga shi abinda Dad ya zo yayi ba?Tunda kike kin taba jin kina sha’awar aikata kwankwacin laifin da Sen ya aikata?kai ta girgiza alamun aa,so you see kowa da yanda Allah ya hallice shi and don parent din ka ba mutanen kirki bane be zamo lalle kaima ka zamo irin su ba,Christians nawa suka haifi Muslims,bbu abinda Allah baya yi,and abinda ya so shi ke faru,so pls ki daina irin wannan thinking din wai don past din ki ba zan yi accepting din ki ba,Nadeeya ko ya kike ina son ki a haka wlhy!and  kin manta ne each one of us had his or her share of mistakes,yan Adam ba za mu ce we are 💯 perfect ba but I want you to know that am gonna love and accept you the way you are,and from now on till the end of time all your flaws and scares will be MINE!!coz I have never seen anything as beautiful as you!No one else could ever make me feel complete and put a smile on my face every single day as you do,so pls Nadeeya ki bar duk wani tunani and come let’s build a home together,I want to take you a place that babu walls no doors or windows zai zamo daga ni sai ke ne balle wasu su kalle mun ke,and I promise to protect and take care of you har randa zan koma wa ubangiji na,all I need from you is just a simple Yes na amince”ya kare kamar zai mata kuka hoping that za ta yarda da shi,hawayen ta ta share sannan cikin dakiya race “am so sorry Ya Nameer but ni da kai ba mu dace ba Wlhy,I pray Allah zai kawo maka mata ta kwarai”daga gama fadin haka ta bude kofar ta fita da gudu sai cikin gida,baki bude Nameer ke kallon ta yana jin zuciyar shi na yi masa zafi be san ma hawaye ya ke ba sai da Mujaheed yace “Nameer lafiya kuwa na ga Anty Pookie ta shigo da gudu tana kuka,kaima ga ka nan na same ka kana kukan”Ai da sauri ya rugume Mujaheed tare da fashe wa da kuka “Mujaheed cewa tayi wai bata so na,wai I deserve better than her,wai am too good for her could you imagine ni a yanda take a haka nake son ta wlhy,Mujaheed Allah da gaske ina son Nadeeya so me tsanani ma”ganin duk yanda ya rude sai kuka yake kamar yaron goye ya so baiwa Mujaheed dariya amman ya danne ya shiga lallashin shi,kan ya daina kuka in sha Allah Nadeeya sai ta zamo ta shi,da lallami da komai ya samu yayi shiru,inda ya ce wa Mujaheed su koma Kaduna baya jin zai iya kwana a garin,ba a son ran Mujaheed ba suka yi wa su Hajiya sallama tare da yi mata karya Haanaan ce bata jin dadi,ba don ran ta ya so ba tayi musu adduoi suka

dau hanya don a yanda suka ce mata da sai sun

Kwana biyu ,ba yanda bata yi ba ma su bari sai gobe da safe amman ina Nameer yace sai gida.



  Wasa wasa Nameer sai da ya kwanta jinya,lokaci daya ya fara ramewa tare da yin duhu,ganin na kokarin kashe kan shi ne ya sanya Mujaheed zama ya baiwa Mama labarin komai,don ganin kamar Nameer din soyayya na neman maida shi Mahaukaci😂😂,jin haka ne ya sanya Mama aje kara da kunya ganin tana neman rasa ‘Dan nata ya sanya ta shirya wa cikin satin tace da Mujaheed su tafi Azare ba ma tare da sanin Nameer din ba,ko da suka isa Hajiya ta ji dadin ganin ta,inda bayan an yi gaisuwar yaushe gamo ne Mama ta kora wa Hajiya labarin abinda ke faruwa,bata boye mata komai ba don ganin matar take kamar mahaifiyar ta,mamaki da salati Hajiya ta ringa yi, barin da ta samu labarin wai Nameer na kwance ba ma lafiya,fada ta hau yi sosai domin ran ta ba karya ya baci,akan me ya sa tun ranar Nameer be sanar da ita ba,har akan Nadeeya zai kwanta jinya,inda yaron nan ya maida su nashi bata tunanin ko ran ta ya nema za ta hana shi,haka ta kira wo Nadeeya ta rufe da fada kamar za ta doke ta,Mama ce ma tayi ta bata baki kan a bi komai an hankali in kuma son shi ne bata yi ya hakura don ba za ta so a taauye mata Hakki ba,a take hajiya tace “ta ma isa dan uban ta in bata so shi ta aure shi ba akwai uban da ya fishi da zai zo neman Auran ta ne bayan tulin abinda uban ta yayi,kawai shashanci ne fa wai tana ganin basu dace ba”,dariya Mama tayi sanann tace “Nadeeya ke nan tun randa Babana ya kawo ki gida na ji ina kaunar ki tunda shima yana son ki,Wlhy ke kamar yarinyar ciki na kike and ko a ya kike muna son ki,don haka ki kwantar da hankalin ki pls”, “har wani lallaba ta za kiyi ai kar ma ta kwantar in kun koma ku fada wa Matsoracin Ango an sanya ranar auran su nan da wata me zuwa in sha Allah” daga Mama har Mujaheed sun ki dadi sosai inda suka yi ta wa Hajiya godiya,haka suka koma Kaduna zuciyoyin su kal,ko da Nameer ya samu labari sai ga shi ya mike tsam kamar ba shi ke jinya ba,inda Maama da Mujaheed suka yi ta tsokanan shi,wasa gaske sai ga shi an dauki shiri both family domin at least after duk abinda ya faru yanzu suna da reason to celebrate,duk da ma Nadeeya ta ce bata son yin event ko daya a bikin,a shafa kawai a kai ta don yanzu Nadeeya ta zamo karamar Uztaza😂😂😂,ana sauran sati daya biki ne su Mama suka gama hada laife inda aka yi wa Nadeeya akwatina rantsatsu guda goma sha biyu,a lokacin ne kuma

Anty Bilki ta dawo daga kasar waje (Maman Amrah),inda ta rufe ido sam tace Nameer ba zai auri yar gidan dan shan jini ba,akan wani dalili ma ga nan Amrah kowa ya san tana kaunar shi kuma yar uwar shi amman ya tsallake ta ya na neman ibo musu masifa,in an yi Auran nan saida bayan ran ta,inda Mama ita ma ta shafa wa nata idon kwalli don bata ga dalili kanwar miji ta yanke hukunci kan yaranta ba,inda tayi rantsuwa kan in Nameer be auri Nadeeya ba sai in mutuwa tayi,domin yarinya babu ruwan ta mutuniyar kirki ce,wasa wasa karamar magana ta zamo babba,inda su Khadija na bayan Anty bilki kan basa son Auran,magana be mutu ba saida Mama ta kai kara gurin Maman su Bilkin (kaka gurin su  Nameer),haba nan tayi wa su Bilki tas tare da cewa in ta isa ta dakatar da auran,tana ma hauka ne yaro ba son yarinya yake ba a matsa mishi sai ya aure ta,tana son Amrah tayi irin Auran da tayi ke nan karshe a sako ta kamar yanda aka sako ki ko nan tace ko bayan ran ta haba nan tayi wa su Bilki tas tare da cewa in ta isa ta dakatar da auran,tana ma hauka ne yaro ba son yarinya yake ba a matsa mishi sai ya aure ta,tana son Amrah tayi irin Auran da tayi ke nan karshe a sako ta kamar yanda aka sako ki ko nan tace ko bayan ran ta bata yarda a matsa wa jikokin ta kan Auran abunda ba su so ba,da haka aka samu aka kashe zance aka cigaba da shirye shirye,



      Dangin Nadeeya ba karamin dadi da murna aka yi ba randa laife ya iso,domin kaya ne masu tsada kyau da alfarma Nameer ya hado wa Nadeeya kamar wata budurwa kowa saida yayi mamaki don wasu yan matan ma ba samun kamar hakan suke ba,nan su Anty Ummi da su yan biyu aka cigaba da bada himma gurin gyaran Amarya,ba karamin kyau da haske Nadeeya ta kara ba domin wani irin kula da tarairaya take samu na musamman daga gurin uwayen nata,inda kuma Nameer kullum na makale da ita a waya ya na kashe ta da kalaman love.


Alh Salis shi ya  dauki nauyin duk wani abinda Uba ke yi wa diyar shi in zai aurar da ita,Kayan daki,parlor kitchen gara na kece raini yayi mata,domin siya mata mutunci a gurin dangin miji duk da Nameer ya ce da kar ta je da komai,duk

Wani abin al’ada da Uba ke yar shi Alhamdulilah Alh Salisu yayi wa Nadeeya,ba yanda su Jamila da Muhibba da mazajen suka kulla zumunta a tsakanin

Su ba kan Nadeeya ta yarda ko Dinner ayi amman tace inaa bata san zance ba highest in sun matsa saidai ayi walima.



  Wai in da rai duk wani abinda aka sanya wa rana sai ya zo in da rai da lafiya yau saura kwana daya cal a daura Auran Nadeeya,tun safe suka fita da Uncle Usman ba tare da sanin hajiya ba suka nufi Bauchi sai asibitin da Sen ke kwance,zuwa lokacin duk wanda ya ga Sen sai ya koka masa domin duk ya bi kare ya yankwane ta rame sai jini ke ta fita daga cikin idanu hanci kunne,ga kuma tustostin da suka fara fita ta bayan shi,lokaci guda halittar shi ta canza,kuka sosai Nadeeya tayi jin yanda yake ta wari,tare da yi mishi danasanin halin da ya jefa kan shi a ciki,shi kan shi Usman din ma da kuka suka baro asibitin,yanzu da ya bi ta hanyar Allah da ba da shi ake ta hidimar nan ba,haka wannan ranar Nadeeya ta kwana zuciyar ta babu dadi,su Jamila sun yi tambayar har sun hakura.


  

   Sassafe aka hau buda tare da dafe dafen abinci,angwaye an ci wanka tun asuba don dauki da rawar kai,inda misalin karfe 11 Daidai za a daura aure,Alh Salis ne yayi kiran Nameer da Hajiya tare da Nadeeya inda ya sanar da su sakon da ya girgiza su wato sakon Mutuwar Sen da aka wayi gari yau da shi,babu ruwan Allah ana Murna ga kuma abin bakin ciki ya faru,Allah dai ka bamu ikon tafiya yanzu ina rana da irin rayuwar Sen??🥹ai a take Nadeeya ta yanki jiki sai suma,cikin sauri su Ummu suka yo kan ta suna kukan bakin cikin rashin tuban dan uwan su,ganin halin da aka tashi da shi ne Alh salis yace ko za a daga daurin Auran zuwa wata sati kafin nan komai ya lafa,inda Hajiya Rakeeba tace sam bata san zance ba wanda ya mutu kam ya mutu bayi dawowa ya je can ya girbi abinda ya shkuka and sam bata yarda ba ta kuma yi rantsuwa kan kar wanda ya  yarda ya kawo mata gawar Sen gida ba,don babu abinda zata kuma yi dashi,a take tace da Nameer “akwai sadaki hannun ka”,da sauri ya ciro dubu dari biyu da hamshi ya mika mata,nan cikin Parlon a take ta ce  a daura,ba musu kuwa aka daura  AURAN NAMEER ABDULLAHI TARE DA AMARYAR SHI NADEEYA RILWANU AUDU WAZIRI,bisa sadaki 250k cash,inda Alh salis shine waliyin amarya while Uncle Usman yayi waliyin Ango,wannan shine wai ga biki ya zo amman babu zanin daurawa😂😂Su Pookie dai ana sume ka daura aure,sai zuwa a farfado kuma a samu Malam Nameer ya Angwance ko ya maida kashin wuya yayi bulbul 😂😂…….



    Ayi hakuri da jina shiru kwana biyu wlh ciwon kai ne me tsanani ya sako ni gaba🥹🥹



  Bare with the typing errors ban Riga nayi editing ba.



  In har kun ji dadin update din yau make sure kuyi commenting🥹


Ina wa kowa fatan Alkhairi 🥰

😭😔UBANA NE KO KISHIYA TA 💔💔


WRITTEN AND STORY

                  BY

NERNAH MARYAM

(MARTEYBEE)






Kofa a bude ta ke ga me son yin joining Saidai pls Banda maza and bana son talla 🥰



    https://chat.whatsapp.com/EUrVVaKJnIBDTlQsxurZv0


My what'sapp group link,you are all welcome to join amman Banda maza pls .


Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via:


            08100046388


******************


    Tallah! Tallah!! Tallah!!


   

   Ina uwar  da ke shirin Aurar da diyar ta kwanan nan??To matso ki baza kunne ki ji,


  Kin dai san halin mazan mu na yanzu,dole sai kin bude jaka kin yi abun bajin ta idan kina son siya wa diyar ki mutunci a idanun Miji,dangin , Miji,da kuma Kawaye,domin sune farkon zuwa gidan Amarya dauko rahoto bayan Aure....


   Kayan daki,Gara,da su Tsaraba bashi ne kawai ba,dole ki baje ki samu ki gwangwaje diyar ki gurin siya mata kayan kitchen na gani na fada,ko dan gudun mata raini,


    To nesa ta matso kusa,kina daga zaune cikin dakin ki,zaki hada wa diyar ki kayan kitchen na alfarma,inda in an ga kitchen in 'Yar ki dauka za a yi a kasar waje ake,saboda ingantattun kaya💃💃💃,


Yanda kuke nuna mun kauna,kun san dai duk inda na ga abun karuwa dole na sanar da ku💃💃to a garzaya gurin Hajiya KHALEESAT me kayan kitchen na yan gayun😍😍,kayan kitchen in ta du babu na yar wa,kaya ne masu kyau!,Aji! Da kuma quality!!,to me ya fi wanga??,and uwa uba kayan ta akwai sauki,


Duk wani Nau'in kayan kitchen da zaki bukata,na zamani,wanda yar ki za ta dade tana santin kitchen in ta,ita da mijin ta😍😍,my sister just chat her up,you will never regret doing business with her ☺️🙌


https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA


Wannan What's app group link in ta ne,for direct message or call, contact her via:


         08149541182


An ce wai a barin tayi akan bar arha!!Siyan na gari me da kudi gida,sai mun ji ku💃🙌


...........

          Page fifty five🔚🔚🔚🔚


******************


    Kamar wanda aka tsoma ran shi da duka gangan jikin a Aljanna tsaban farin ciki,tabbas da a yanzu Allah zai dauki rayuwar shi to da ya tafi yana me matukar farin ciki,domin Allah ya cika mishi burin shi,har yanzu zuciyar shi ta gaza yarda wai muradin ran shi matar da ya dade yana kauna Allah ya mallaka masa a matsayin matar shi ta sunnah,wai shine yau aka daura wa Aure Auran ma da Masoyiyar ran shi,Wayyo wani farin cikin baki ya kan gaza misilta shi,babu abinda ya ke banda kirari da kwararo godiya ga Allah madaukakin sarki me yin yanda ya so a lokacin da ya so,tabbas Allah maji rokon bayin sa ne ya roka kuma ya amsa mishi ya bashi Nadeeyar,and a yanda ya ke jin ta a ran shi baya fatan ko mutuwa ta dauke ta ta bar shi,he promise ya tsaya tare da ita through thick and thin,he will love and support her zai yi making sure ya jiyar da ita duk wani farin ciki da jin dadin da ke cikin duniyar nan,zai nuna mata so da kaunar da zai mantar da ita duk damuwar da ta ke ciki,fatan shi kawai Allah ya basu zaman lafiya ya kuma kara mishi so kaunar ta da tausayin ta domin baya fatan ya bata mata ko ya zalunce ta a rayuwa,yana son ya nuna mata zallar kauna da riritawar da ta yi missing a rayuwar ta ta baya,yana son goge duk wani bakin ciki da kuncin da ke past din ta,yana kuma fatan Allah ya ba su zaman lafiya ya sanya mata kaunar shi kamar yanda ya ke mugun san ta.



  Sam bakin shi ya gaza rufuwa,gaba daya hankalin shi ya tafi kan Nadeeyar da su Small Mom suka shige da ita daki,bayi da burin da ya wuce ya san halin da take ciki,yana son ya rungume ta suyi kukan tare domin tabbas ya san yanda zuciyar ta ke tafasa tare da yi mata zafi,rashi ko na Dabbar da kuka shaku da ita ne akwai ciwo balle na Mahaifi,ya sani dole abun ba zai zo mata da sauki ba,domin duk lalacewar Sen he his still her Father jinin shi na running a jikin ta,and daga yanda ta bada labari akwai kauna da shakuwa me karfi a tsakanin su,tabbas shima be so mutuwar Sen ba ko don farin cikin Nadeeyar ya so Allah ya shirye shi ya nutsu ya dawo cikin su suyi rayuwa cikin farin ciki da kaunar juna,saidai Allah baya taba barin wani don wani ya ji dadi,sannan shi ke yin abinda ya so lokacin da ya so,ko da ace Sen ya shiru ya dawo cikin mutane kyamatar da jama’a za suyi ta masa ma kadai sai ya ji kamar ya kashe kan shi,Allah kawai ya jikan shi sannan ya bashi ikon rike Nadeeya da amana.


  Hajiya na hankalce da shi,banda murmushi babu abinda take domin ji take  zuciyar ta sakat babu wani nauyi da damuwa kuma,don damuwar nata daman Nadeeya ne to kuma Allah ya ji tausayin su ya hada ta da miji wanda ke son  ta fiye da nashi kan,miji da zai zamo me nuna mata hanya tare da kamo hannun ta zuwa ga Aljanna,mijin da ta san ko yau ta mutu shi da dangin ta ba za su taba barin Nadeeya tayi maraici ba domin sun zame mata garguwa,tabbas Nameer ya cika dan halak bata kuma jin Nadeeya za ta taba samun matsala da shi,fatan ta dai Allah ya basu zaman lafiya ya kuma yi albarka wa rayuwar Auran su,nan tayi ta tsokanna Nameer wai yau kukan banza ya kare dai ko tunda Allah yayi ya mallaki Nadeeya,kunya ne sosai ya kama shi har ya kai shi ga mike wa ya bar parlor din,da dariya su Alh Salis suka raka bayan shi,suna me jin kaunar shi har cikin ran su domin yaron sam bayi da damuwa.



A waje ya hadu da su Mujaheed da Habeeb da sauran abokai da yan uwan arziki,wanda da suna zaman jiran lokaci yayi a je a daura aure sai ga labari ya zo musu aure kam an daura shi,murna suka yi ta taya shi tare da yi masa fatan Alkhairi,inda su Mujaheed suka yi ta daukan shi hotuna da videos suna ta tsokanan shi wai finally yau wani zai angwance,don ba karamin kyau Nameer din yayi yau ba,shi dai banda murmushi babu abinda ya ke yi,ina irin tsantsan Happiness din da har magana ma ya kan sanya ka,ka ma rasa me za ka ce domin he is so over the moon,ji yake rayuwar shi da shi kan shi is finally complete now da ya samu ya aure Nadeeyatu(Eheey😂Su Nameerun Mama yau kam

Ai ba wani sarki sai Allah an zamo Ango,after a long time),nan  duk suka shiga don gudanar da dan reception din da su Mujaheed suka hada musu,saidai komai suke suna kallon time don yau suke son tafiya da Amarya tunda ba Event za a yi holding a nan Azaren ba,don Walimar ma a can Kaduna za a yi sa.


Nadeeya tunda ta farfado take kuka me ban tausayi,sosai mutuwar Sen ya taba mata zuciya,mancewa tayi da duk wasu laifufukan da ya aikata tayi domin a rayuwa babu abinda ta ke so kamar Mahaifin ta,ta ji ciwon mutuwar sosai musamman in ta tuna ya mutu yana hada Allah da wani a gurin bauta sai ta ji duk zuciyar ta ya kuma

karaya,tabbas ta so Daddyn ta ya shiryu kafin ya koma ga Allahn sa amman sam hakan be yu ba,kuma bata isa canza abinda Allah ya rubuta ba,tashin hankalin sai ya hade mata biyu da ta ji wai an daura Auran ta da Nameer,sam Nameer be yi tunani da kyau ba in banda abin shi ina ruwan Monkey da gada,ita da shi sam ba su dace ba,ko Mahaifa ba bata  da shi amman sai da ya nace ya aure ta a haka,wannan wani irin so ya ke yi mata ne haka,wani irin tausayin sa ne ya kama mata rai domin samun me son ka irin haka abune me matukar wahala,domin ko rantsuwa tayi ba za ta yi kaffara ba Nameer tsakani da Allah ya ke son ta ba wai don wani abu nata ba,to ma ina abun ya ke iya kan abinda za ta ce yayi saura mata shine Kyan ta,sai kuma kyan halayan da take kokarin ganin ta koye su yanzu,ganin duk baki da lalashin da su Small Mom ke bata taki yin shiru ne ya sanya Hajiya ta kira ta,saida ta wanke ta tas da soso da sabulu na masifan akan wancan wawan uban nata take neman sanya wa kan ta ciwo?ko kuma kan an daura mata Aure da Nameer ne take neman isan mutane da kukan banza,saida ta mata tass sannan kuma rungumo ta tare da fara bata baki cikin hikima da nasiha da lallashi ta samu ta shawo kan ta har tayi shiru,nan ta shiga nuna mata tare da bata shawarwarin yanda za ta zauna da mijin ta ta kuma dada kame zuciyar sa,ta kuma nuna mata babu wanda ya kai ta dacen miji domin ko shakka babu za ta samu happiness da bata yi tsammani ba a gidan Nameer ita dai ta rike shi da yarinyar shi amana ko don saka hidimar da yayi da su,hakuri biyayya,tsafta,tattali,iya magana,girki(duk da ba wani kwarewa tayi a nan ba),kula da shimfidar shi da duk bukatun shi,uwa uba riritawa da nuna soyayya,in ta rike wanann abubuwan to za ta zauna lafiya da shi,sannan ko da wasa banda Raina dangin shi,sosai nasihan Hajiyar suka ratsa ta,inda ta rungume ta tana kuka,addua sosai Hajiya tayi musu tare da sanya mata albarka sanann aka samu ta shiga wanka,ba tare da bata lokaci ba ta fito inda Small mom da su Yan biyu ne suka shirya ta cikin ramtsatsiyar farar lace fara sol me tsada,wanda aka yi masa dinkin Riga da skirt ba wani kwalliya aka wa kayan ba very simple but yayi kyau sosai tare da daukan idanu,inda ta sanya kuwa ya zauna mata daram a jiki,gyaran gashi da simple make up aka yi mata tare da kashe mata dauri,domin uwayen nata yan gayu ne sai kuwa ya fito Masha Allah da ita,dan kunne da sarka masu tsada da takallimi duk kalon fari aka sanya mata,sannan aka shiga yi mata wankan turaruka masu dadin kamshi,babban farin veil Ummu ta yafa mata aka rufe har fuska,Wayyo sai ta fito Amaryan ta sak ga Jan lallen nan ya fito

Yayi das a hannun ta duk wanda ya kalle ta dole ya so kara kallon ta don ba karamin kyau tayi ba,a take kuwa aka saki guda ana yaba irin haduwar da tayi,masu daukan ta hotuna da videos don samun yin status na yi ta yi,kar su Jameela su samu labari,Small Mom ce ta sanya aka kira mata Nameer don tana son yi musu Couple pictures,ba musu kuwa ya taho da su Habeeb,an yi dariya sosai gurin daukan hotunan don tsokanan su duk su biyun aka yi ta yi,kafin aka gama,Su Anty Bilki suka ce a basu Amaryan su za su dauki hanya don tafiyar ba na kusa bane.



  Sosai Hajiya ta hade su guri guda tare da yi musu nasiha masu ratsa jiki game da hakki da kuma

rayuwar aure,kan su ji tsoron Allah su san Aure ba abin wasa bane ibada ce,don haka suyi kokarin gurin sauke hakkunan da ke kan junan su,banda yada sirrikan juna gurin kawaye ko abokai,sannan suyi hakuri gurin zama da juna karahe ta rufe da yi musu fatan Alkhairi tare da yi musu adduar Allah ya basu zaman lafiya,sanann ta daura hannun Nadeeyar da ke kuka kamar ran ta zai fita,a hannun Nameer “ga ta nan na baka Amanar ta,yanzu ta dawo karkashin kulawan ka,na san ba za a taba samun matsala daga gurin ka ba,amman ance zo mu zauna zo mu saba no matter what,ka ka mance matar ka ce kuma mace ce me rauni so duk abinda za ta maka think before taking action,Allah ya kiyaye hanya ya tsare ya baku hakurin zama,ka ce ina gaida Mamar ta ku,da Kishiya ta da taki zuwa biki,yau dai Ai kukan banza ya kare ko?”ta kare tana dariyar karfin hali domin deep down damuwa ce fal ranta,she was just trying and acting to be strong amman ba karamin girgiza ta mutuwar Rilwanu yayi ba,no matter how bad he is yaron ta ne daga cikin cikin ta ya fito and shine first fruit din da ta samu daga gurin Allah,Although bata nuna wa sabida karar’dan farko da ake amman tana kaunar shi sosai a cikin ran ta,jira take a watse ta samu tayi kuka ko ranta zai dan yi sanyi.



  Nan aka fara shiga motoci, bayan an gama jera komai domin kai Amarya,hannun Nameer na rike da na Nadeeya har yanzu yana murzawa a hankalin don baya son abinda zai nisan ta  shi da ita ko na minti daya,su Mujaheed dai baya suka yi suna ganin ikon Allah don yau suke ga yanda za a kai Amarya daga gari zuwa gari ga yan uwa cike,amman Ango na neman saka Amarya a motar shi su tafi tare,Anty Bilki ne ganin rawar kan da Nameer din ke yi kamar be taba ganin mace ba ya sanya ranta baci,tare da maka masa uwar harara tace “ka sake ta dai mu tafi ko bawan Allah lokaci na tafiya kar dare yayi mana a hanya”,har ga Allah ya so yace da ita a motar shi za ta tafi,sai kuma Alh Salis ya fito,inda ya ce hakkin Uba ne kai yarinya gidan Miji,don haka shi da kan shi zai kai Nadeeyar a motar shi,ba tare da musu ba kuwa  aka sanya ta a motar na shi tare da su Jameela da Muhibba sai Small Mom a gaba,a haka suka dau hanya,inda suka yi ta bata baki har tayi shiru ta koma sai sauke ajiyar zuciya.



  Ba su suka iso Kaduna ba sai guraran La’asar inda gidan Mama direct aka wuce da su don ana ake holding din Walimar,da isowar su kuwa aka hau buda ana yi musu sannu da zuwa,tarba me shegen kyau suka samu a gidan Mama,bayan masu cin abinci sun gama ne aka shiga yin wanka don yin shirin Walima,ba tare da bata lokaci ba kuwa Nadeeya tayi wanka,Mama da kan ta ta kawo wa Nadeeya wata rantsamtsiyar Black lace me touch din Golden,kallo daya zaka wa kayan ka san me tsada ce,an yi masa dinkin Riga da skirt yar yayi,sai sarka da awarwaro da zuben gold,takalmi golden tare da Alkaybba me shegen kyau,hatta inner wears saida Mama tayi providing din Nadeeya da shi,godiya sosai su Small Mom suka yi mata,domin matar sam bata da damuwa mata ce da ta san mutunci me kuma cike da mutunta yan Adam,inda ta nuna musu sam su daina gode mata duty din ta ne kula da Nadeeya coz diyar ta ce,and ta Riga da ta dauka wa Hajiya da Nameer kan za ta kula da Nadeeya kamar uwar da ta haife ta har karshen rayuwar ta,ba za ta bari a cutar ko ta cutar da ita ba.



Ba tare da bata lokaci ba kuwa suka taya ta shirya wa inda ta fito kamar a sace ta don ba karamin haskata da kyau kayan yayi ba,duk da ba wani style din tashin hankali ko wani heavy kwalliya tayi ba but Masha Allah Nadeeya is naturally beautiful 😻,nan aka gama shirya wa sai kamshi take ta faman yi aka fara gudanar da Walimar,inda aka ci aka sha sannan aka dauko malamai mata suka yi wa’azi game da rayuwar aure,ba karamin kokari Mama tayi ba don Walimar ta kayatar inda ta tara mutane da yawa,irin su Girl friend da Sunainah can na gano su suna ta dambe akan shinkafa🤣🤧dariya nayi nace “ku dai duk inda kuka je sai kun nuna halin ku”,juyawan da zan yi na gano Fanash an ci kwalliya nayi mamakin ganin ta,coz ban yi expecting zuwan ta ba don tana da exams,harara ta tayi tace “Au wai Meemarh dauka kike ba zan zo Aurar Nadeeyar tawa ba,you must be joking 🙃”baki na ja don ganin kan ta ya dau zafi,in yi gaba kadan na ga Ummu Iman sai goge Camera take ita a dole so take sai ta fi kowa daukan Nadeeya hotuna don ta samu na status😂, “Ummu Iman da barin daukan hotunan nan kika yi kika zo muka gama cin abincin nan kar ya huce”na tsinkayo muryan Nanan Oga tana fadi rike da yar jinjirar ta a hannu sai afa shinkafa take,dariya nayi sosai don ban yi mamakin ganin nata ba,don bikin Aminin Oga ake dole ta hallata,Maman Affan na gani zaune kusa da su Hajiya Na’ima,Anty Binta da Oum Mursheed ana ta hira yanda biki ya kayyatar,ni kam nayi mamaki sosai don ban dauka duk za su samu zuwa haka ba,can na kara ganin su HajaraIbrahim ma an ci kwalliya sai kwadayin nama ake,nace daman ta can kika fi kauri ai,Ummu Sadiq,Khadijat,Maman Sultan na gano sai kokarin style ake kusa da Amarya ana son a dauki hoto,🥵, “Momcey ki ce da su Babyn baby da Yar Mommyn ta su matsa bana ganin Amarya da kyau”na jiyo muryan Daughter na fadi sai turo baki take kamar me shirin kuka,daman ai yau da shagwabar aka tashi😂,ina shirin tambayar ko ina su Mrs Abdoul da Kubsoorat da Momcey na,da Aishatu Muhammad Bashir,Maman Ummi,Maman Anwar,da kuma Maman Shuraih suka  makale?sai na gano su bakin Kofa wai jira suke a gama walima a tafi kai Amarya da su,don suna son cin kazar amarci(🥹ni ko nace duk kajin da kuka ci ana be ishe ku ba,wallah babu me bin su Nameer gidan su eheee),kai Masha Allah biki yayi biki na gano yan UBANA NE KO KISHIYA TA da yawa sun samu zuwa wasu har boye wasu ma suke,sun yi kwalliya tsaf da su Masha Allah,har mamaki nayi ta yi daman haka group din ya tara kyawawan Mata haka,😻😻inda sai around Magrib taro ya watse kowa ya tafi ran shi kal da jakar kayan dadin shi a hannu,tare da yi wa Ango da Amarya fatan zama lafiya.



 Duk inda Nameer ya so dauke Amaryan shi su tafi gidan su amman sam Mama ta ce bata san zance ba,yana ma hauka ne ta bashi ita bayan uwar gaji yar nan da ta yi,ga yan uwan ta ma za ta so kwana cikin su ai,sai ga Nameer na marairaice wa Mama kan wai ta yarda da shi babu abinda zai mata fa😂😂harara Mama ta maka masa sannan tayi wucewar ta,ganin haka ya sanya ya ce to akwai abinda ya ke son fada mata don Allah,ko na minti 20 ne Mama ta bashi ita,Sam Mama tace bata san zance ba,haka ya karaci nacin shi ya tafi zuciyar shi ba dadi,don ya zo kwana da ita a gidan su yau,haba nan su Mujaheed suka har dariya tare da tasokanan shi,sai guraran 12 ya samu kan shi,sannan ya kira ta a waya,basu dade da gama hira da su Jameela ba inda suka gama tsorata ta tare da tsurar mata da ciki gane da first night sai ga kiran nashi,da kyar ta dauki wayar domin har ga Allah ta tsorata,sosai yayi ta jan da hira,inda ba shi ya bar ta ba sai da ya fara jiyo saukan numfashin ta alamun tayi bacci,sannan ya kashe wayar tare da rungumar pillow cike da kewan ta bacci ya dauke shi.


 

  Washe gari yan kai Amarya sassafe aka dau hanyar tafiya,inda aka rabu cike da kewan juna don sun ji dadin tarban da Mama ta yi musu,daga Small Mom sai yan biyu sai su Jameela suka rage kan sai sun kai Nadeeya gidan miji sanann su wuce,da Ummi ma ta so su yan biyu su koma gidajen su don ita Zaria take

daman ba wata nisa bace tsakanin su,amman suka

ce ba su san zance ba sai sun kai diyar su dakin miji

kan su koma na su gidan,haka ko Mama tayi ta nan nan da su,abinci kam an ci har an bari,Nadeeya ba karamin nutsuwa ta samu ba  don ganin yanda dangin Nameer ke ta nan nan da ita,in kun cire Anty Bilki Khadeejat da Amrah da ke ta yi mata kallon gani gani,sam ta rasa me tayi musu domin ko gaisuwar arziki bata samu daga gurin Khadijat ba,tun jiya da suka iso Angel ke manne da ita,ita kam ma har mamaki yarinya ta ke bata yanda ta manne mata,kuma bata mance taba duk da ita Nadeeya ba tuna ta tayi ba,saidai bugun farko ta ji yarinyar ta kwanta mata a rai,sai bayan Magriba Nadeeya ta kuma wanka tare da shirya wa cikin wata haddiyar kuma tsadaddiyar Super  exclusive orange da ratsin fari dinkin Riga da skirt ya sha pattern and stone work sai kyalli ya ke,ai ko ba karamin zama mata a jiki kayan yayi ba,Mama da kan ta ta nada mata wata tsadaddiyar milk lifaya me masifan kyau ya ji ado ta kasan shi,inda ta bata wani abu a cup tace maza ta shanye kafin motocin daukan Amarya su iso,ba musu kuwa ta shanye abunda ba ta ma

san miye ba,sanann Mama ta rufe mata fuska da Lifayan tare da feshe ta da turaruka masu sanyin kamshi,nan ta hau jan ta da hira cikin hikima irin ta su ta manya take kara nuna mata yanda za ta zauna ta ji dadin rayuwar Auran ta,tare da nuna kar tayi kasa a gwiwa duk sanda Nameer yayi mata ba daidai ba ta zo ta fada mata domin ita Amanar ta ce.sai guraran bayan Magrib motocin suka iso inda da kuka aka sanya Nadeeya a motar domin in ta ita ce bata ki a bar ta gidan Mama tayi ta zaman ta ba,ta dan samu kwanciyar hankali ganin ba tare da su Khadeejat da Anty Bilki za a kai ta ba,an dan yi tafiya sanann aka iso Malali inda gidan ta yake,tun daga time din da gate man ya bude Gate su Jameela da Small Mom ke fadin Masha Allah don ba karamin kyau da haduwa gidan yayi ba,basu tashi santin gidan ba ma saida suka shiga ciki,wato Alh Salis ba su da abinda za ce da shi sai dai fatan ya gama

Lafiya domin ba karamin kudi ya kashe gurin siyan kayan nan ba,parlor biyu ne daya Royals aka zube while dayan kuma aka yi English parlor me masifan kyau da daukan ido,haka ma dakunan baccin duk saida ya sheke su da kaya,hasken wuta ne da kamshin turare ta ko ta ina,kuma dai kun san kyan gidan Amarya in mutum ya je ba son dawo wa ya ke ba😂😂.


  Dakin ta direct suka wuce da ita tare da ajiyar ta tsakiyar kan gado sanann aka shiga dan taba hira,ita dai shiru tayi musu don at that time ta bar kukan saidai tsoro ne fal ran ta don su Jameela sai kara kada mata hanjin ciki suke,sai around 9 suka fara jiyo hayyaniyar angwaye hakan ne ya tabbatar musu da sun iso,da sauri Small ta kara fashe Nadeeya da turaruka sanann ta kunna na wuta a dakin,tare da cewa kowa yayi shiri yanzu za su wuce,ko da su Nameer suka shigo bakin shin nan har kunne idanun shi zube kan Nadeeya da ke lullube a tsakiyar gado,a gurguje su Mujaheed suka dan yi musu nasiha tare da adduoi,sanann su Jameela suka ce a basu kudin kawancen su,dariya sosai suka baiwa su Small Mom domin dauka take wanann al’adar dole sai yammata,Nameer da kan shi ya basu kudin kawancen don so yake su samu su tafi su bashi guri ya ga Pookiee da kyau,tare suka raba kudin da su Small Mom a cewar su wai karamar uwa ma kawa ce😂😂haka dai bayan sun gama tsokanar su suka ce Nameer ya raka su ya rufe kofar za su tafi,sosai Nadeeya ta rungume Ummu tana kuka,da kyar ta banbanre ta daga jikin ta sanann suka tafi abun su tana jin kewa da tausayin Nadeeyar a ran ta,amman ya ta iya,wai aka ce Aure yakin Mata,da haka za ta saba.


  

  Saida ya rufe ko ina sanann ya taho,takun ma na daban yake yi irin takun yau n cika buri na😂😂daddaya har ya iso dakin da Nadeeyar take,tsaye yayi bakin kofa ya zuba mata idanu yana me jin so da kaunar ta a cikin zuciyar shi,ya dan du lokaci yana kallon ta sanann kuma ya fita,kitchen ya nufa tare da dauko tray da plate da cups,kazar da su Habeeb suka siya sai turiri yake ya juye akan plate din,sanann ya sako drinks da fresh milk me sanyi,kafin ya dawo dakin tana nan zaune yanda ya bar ta,da sallama ya shiga,saida ya aje tray din a gefe sannan ya hau kan gadon,yana me jin zuciyar shi kal da farin ciki,nan fa ya shiga aikin lallashi da lallama ta yana rike da hannun ta har ya samu ta daina kukan,alola ya raka

ta toilet tayi yayi shima sanann ya shimfida musu abin sallah,sallah raka’a biyu ya ja su,inda ya dafe goshin ya dau lokaci yani masu addua,sannan cike dabara ya shiga koya mata yanda ake wankan janaba da sauran abubuwan da ba za a rasa ba,sanann ya ce da ita from now on shine Malamin ta duk bayan sallahn magrib za ta na kawo masa karatu shi kuma zai na mata dauri,sanann yace da ita duk abinda yayi mata bata ji dadi ba ta sanar masa don ance zo mu xauna zo mu saba,kafin ya samu da kyar ta dan ci kazar da madarar,kallo da ya za ka mata ka san a matukar gajiye take,hakan ne ya sanya ya ke jin a ran shi ba abinda zai mata yau,zai daga mata kafa zuwa gobe kan nan ta dan warware kuma ta kuma sakin jiki da shi,coz he don’t want to rush her,tashi yayi tare da shiga toilet ya hada mata ruwan wanka,sanann ya ce da ita ta je ta yi wanka tare da bata towel,ba musu kuwa ta nufi toilet din don ita ma tana bukatar wankan,closet ya bude ya dade yana kallon jerin kayan baccin da ke shake a ciki,idon sa ne ya sauka kan wata white sexy kayan bacci wanda guntu ne me spaghetti hand,haka kawai ya ji yana son ganin ta cikin kayan so fito da shi yayi tare da aje mata kan gado,paper ya dauka da pen tare da rubuta “wear this tonight pls”ya nade tare da aje paper akan kayan,sanann ya wuce dakin shi don yin wankan shima,saida ya daura towel zai shiga wanka wayar shi ta hau ringing ganin Mujaheed ne ya sanya shi sakin dariya tare da dauka “shege mutumi na na dau by now Ai kana cloud 11”tsaki Nameer ya ja sanann yace “kowa ne dan iska irin ka,Wlhy Mujaheed ban son iskanci,kawai cikin dare kana kiran mutum da matar shi,are you mad or something?”


 Dariya Mujaheed ya fashe da shi “au wai sai yau ka sani ashe ,kai da kake kira na kullum me na ce maka,to a dai ji tsoron Allah a bi yar mutane a hankali,Wlhy ka ji mata ciwo Mama dafa ka za ta yi mu cinye,don yarinya dai karama ce ba zai yu mutum ya juye mata abun da ya dade yana tarawa shekara da shekaru ba”, “Allah ya shirya ka Mujaheed ko ma miye gobe sai ka taho da wuri ku cinye ni din”dariya Mujaheed ya sheke da shi “Wlhy ni dai babu ruwa na ka bi yar mutane a sannu”da haka suka yi sallama yana ta tsokanan shi while Nameer na auna masa zagi.


 Cikin sauri yayi wanka da brush tare da fitowa,cikin kayan bacci ya shirya kan shi ya fesa turaruka sanann ya nufi dakin nata,hango ta tayi dunkule a cikin blanket ta kudindine kanta alamun har ta fara bacci,don tunda ta yi wanka ta fito da kyar ta iya sanya kayan da ta gani kan gadon,tuno Hajiya tace tayi masa biyayya ban da musu ya sanya ta sanya wa kawai ta bi gado,sanyin Ac ne ya sanya ta shigewa blanket jin shiru shiru be leko ba ya sanya ta saki jikin ta har bacci ya fara kokarin daukan ta.


   Cikin takun nutsuwa ya nufo gadon,tare da hawa yan me bude blanket din don shiga ciki, hankali ya kwanta  gefen ta tare da Jan blanket d'in ya rufe su  da shi ,ganin ta fara bacci ne ya sanya shi dan ma tsawa  gefen ta ya kwanta ,domin ba ya son abinda  zai had'e jikin su wuri guda domin gujewa tashin ta daga bacci,and yana avoiding matsala don ganin ta fara jin dadin baccin nata baya son katse mata,don da kyar ya samu ma ta kwanta coz tsoro ne fal ranta,cikin bacci ta dan mirgino tare da yin birgima daga jin alaman mutum kusa da ita ta k'ara mirgi nowa cikin sanyi ta d'aura hannun ta kan k'irjin shi,tare da shige wa cikin jikin shi,jin laushi ya sanya ta kara gyara kwanciyar ta jikin shi,da jin nata a jikin na shi kuwa yayi saurin kai idanun shi kan ta,domin ko hannun ta dazu ba bari ya take yana tabawa ta dadi ba,murmushi ya sake don ganin tabbas cikin  bacci take yin komai.



Idanu ya zuba mata tare da yin shiru yana me kare mata kallo,yanda ta ke sauke ajiyar zuciya alamun kukan da ta sha kafin tayi baccin,inda chest din ta ke up and down yake bi da kallo,a hankali yana lumshe idanun shi ,trying hard to resist abunda ya ke ji,a yayin da ita ta kam ko a jikin ta,a hankali take numfashin ta me dumi ke sauka a kan wuyan shi,wanda a take ya saukar masa da wata wawiyar kasala tare da fara rabashi da nutsuwar shi,a take kuwa ya shiga sauke ajiyar zuciya akai akai kamar wanda yayi tsere.



Cikin lumshe ido,da fara fita a hayyacin sa ya sanya hannun shi a kasalance ya rungumo ta kam,a hankali ya sauke hannun shi a cinyar ta tare da shafawa a hankali,taushi da laushin cinyar ne ya rude shi har ya fara raba shi da hankalin shi ya kamo kasan yar rigar baccin nata tare da fara yin sama da shi cikin tsananin saukin so da kauna,hankali ya maida sosai gurin ganin ya dage rigar nata,har ya samu nasarar daga rigar hakan yayi exposing chest din ta that are so full and perky,ai ko arba da yayi da ƙirjin nata ne ya sanya shi sumar kwance tare da fara dimaucewa,domin duk da babu haske me yawa a dakin hakan be hana shi yi musu kallon kurrila ba,jin iskan Ac ya ratsa bare skin din ta ne ya sanya ta saurin k'ara k'amk'ameshi,ai ko dan bawan Allah da jin soft naked jikin ta jikin shi ya kara birkicewa,da sauri ya kamo lips din shi na kasa ya shiga tsotsa a hankali,tare da kara kankame ta,da hannu daya kuma ya janyo soft blanket din don kara rufe su da kyau,sannan a hankali ya shiga   sauya salon kwanciyar  tasu da darrusan sa masu wuyan fada.


Cikin bacci  taji wani bakon  sabonsalo da yanayin da bata saba da shi ba,da kyar ta samu ta bude idanun ta a hankali ta diresu akan kyakyawan fuskar Nameer  da ya gama yin mutuwar kwance sakamakon arba da yayi da surar ta da kyau,jikin shi har bari yake gurin son ya taba ta,domin he can't actually recall when last ya taba mace,jin haka ya sanya a hankali ta fara janye jikin  ta daga nashi domin jin yanda zuciyar ta ke bugawa lokaci daya ta fara jin wani irin bari sakamakon tsoron da ya kama ta,ganin hakan ne ya sanya shi saurin riko ta domin ko kadan baya fatan abunda zai raba shi daga soft skin din tan nan,jin rikon da ya mata ne ya sanya cikin rawar muryan tsoro,wanda ta ke can k'asa kasa tace  "Paapiii"jin yanayin  da ta kira sunan nashi ne tare da ja ya sanya shi kara matso ta,tare da manno ta jikin shi,cikin murya me kama da rada wanda shi kan shi be san ma yana da ita ba yace "Pookieee Where are you planning on going?"


Idanu tayi saurin rintse wa jin yana yi mata tafiyar tsutsa a naked bayan ta,jin yana hauro da hannun nashi ne ya sanya ta saurin cewa " Ya Nameer I want to go to the living room ni baccin ma duk ya ishe ni,I want to go watch some movie"ta kare sounding childish,dan murmushi Nameer ya sake domin tas ya gane a mugun tsorace ta ke 


"Ni baccin ya ishei zan koma palo, duk a tsorace take maganar, "Yaya bazato ba tsammani yahade lips din su  waje daya, yayinda hannunsa yake kan qirjinta yana  Squeezing boobs din ta so gently,taushin  lips din nata ya sanya ya shiga kissing din ta sosai domin ba karamin dadin hakan ya ke ji ba,ga sanyin Ac yana ratsa su,har hakan yasa hankalinsu yafara barin jikinsa  gaba daya ya manta da komai, shi Kansa ya manta waye shi, ya manta wacce duniya yake,shan bakinta kawai yake fatan sa kawai Allah ya yanke  masa wahala, yana wannan tunanin ya zare bakin shi a hankali daga nata,tare da sauko wa a hankali zuwa kan kirjin ta yana me mannawa each part din da ya ci karo da shi kiss,sannan a hankali ya maida bakin shi kan kirjin ta ya shiga wasa da tongue din shi cikin so da kwarewa, dan zabura tayi domin sam bata yi expecting hakan ba,dadi ne from

nowhere take jin yana shigan ta,hakan ya sanya ta yin mika tare da saurin riko kan shi kam,tana me susa gashin kan shi a hankali,idanun ta a lumshe suke  tana jin  wani irin fitinan nan dadi yana shiga jikin ta wanda bata taba sanin akwai shi ba,inda Nameer kuwa hakan da tayi  masa  ba karamin kara masa dadi  sosai yayi ba,sai  yake jin sa  kamar wani dan baby wanda maman sa ta riqe kan sa take bashi nono yake sha,sosai yake shan guda daya,yayin da dayan kuma yake wasa da shi a hankali da hannun shi.


Cikin matsanciyar shauki da zazzafar sha’awa ya birito ta tare da shiga kissing each and every part of her body,yana me sauke wata irin numfashi,kallo daya za ka mishi ka fahimci yana enjoying din moment din nasu,da hannu daya ya yage yar rigar baccin jikin nata,wanda ita tayi mishi shamaki daga kallon full body din ta,sannan shima ya cire nashi kayan,sannan ya dada  rungumo ta jikin sa,haka kawai ya ke samun wata irin nutsuwa a yayin da ya ji ta a kirjin shi,he still can’t believe it wai Nadeeya Audu Waziri,Pookiee din shi da ya ke tsananin so da kauna,tare da mafarkin samu ne wai yau kwance a kan kirjin shi,be san sanda hawaye ya shiga saukowa daga idanun shi ba,wanda zan fi kiran hakan da hawayen farin ciki da samun cikan buri,cikin tsantsan so da kulawa tare da tsananin shaukin bukatuwa ya shiga sarrafata ta yadda yake so,a yayin da ita kuwa wahalar da take  ciki bai hana ta  gane ne yake  shirin yi mata ba,a take ta kuma tsorata coz this is her very own first time,and already su Jameela da Muhibba sun gama tsorata ta game da first night experience.



Cikin muryan kuka da tsoro,a take kuwa jikin ta ya hau  rawa ta ce “Ya Nameer don Allah  kayi hakuri,ka bar ni haka,aswear to almighty Allah tsoro nake ji,i don’t think I can do this”ta kare tana hawaye.


Ganin yanda jikin nata ke bari ne ya tabbatar masa da cewa eh tabbas a tsorace take an muddum ya ce zai matsa mata,zai iya ji mata ciwo,a yanayi da ya ke ciki baya jin akwai abinda zai hana shi samun ta a daran yau domin tabbas in yace zai daga mata kafa to shi zai kashe kan shi,har mamakin kan shi yake yanda ya ke rawar jiki,tare da kasa controlling kan shi akan Nadeeyar,he just believes akwai something so special game da jikin ta da ya ke ji be ki ya kre rayuwar shi  a manne a jikin ta ba(Ni ko na ce ba dole ba su Nameerun Mama yaushe rabo Ai dole kayi rawar kafa😂,almost 3 years fa),kara manna ta yayi da jikin shi,wanda hakan ya kara sanya mata firgici da tsoro,cikin murya maikama da wanda zaiyi kuka yace “relax and try to be calm Pookiee,stay calm okay I can’t and I won’t harm you okay,am your loving husband fa,wanda ke tsanannin so da kaunar ki,kin ga wannan abun da zan miki yanzu shine aure my love is high time da ya ci a ce yanzu kam kin girma ke ma kin zama cikkakiyar mace,and duk wace  matar da kika ganta gidan mijinta to kullum sai anyi mata abinda zan miki yanzu,so stay calm okay bana son na ji miki ciwo,and i promise you I will be so gentle kamar wanda ke handling din egg,all I want from you is you should stay calm and pls don’t cry okay kukan daga mun hankali yake Pookiee”ya kare yana sakin mata kiss a kumatu,tare da fara kokarin nema wa kan shi hanya.


 Da sauri ta riko shi tana kuka “ Aa Paapiii ni dai Allah bana so,I don’t want to grow up ,kawai kayi hakuri I can’t do it,and Muhibba da Jamila sun ce mun is extremely painful akwai zafi sosai indai first time din mutum ne,ji ake kamar wai za a bar duniya,and this is my first time  fa”ta kare a matukar rude,jin haka ne ya sanya shi shiga hura mata iskan bakin shi da sai kamshin mint yake a fuska tare da kunnan ta a hankali,yana mata whispering din love words da ni kai na ban jin me yake fadi a cikin kunnan,saida ya ga ta fara mika alamun sakon shi ya fara shigar ta sannan ya shiga mata magana cikin tattausan muryan “Pookiee Allah I really need you so badly don Allah kar ki ce aa,Allah ba wani zafi can bane fa karyan su jamila ne kawai don su tsorata ki amman zafin kadan ne,besides wanda mijin su baya son su ne suke jin zafi sosai,amman ke kam ai ina son ki you are my sweetest addiction I cannot hurt you in any way,so ki kyalle su kin ji, a hankali zan miki Ai na san this is your first time so I will be so so gentle with you kamar yar baby na”yana shafa kanta , “Ni dai a a ba yau ba,kawai mu bari sai gobe,I want to sleep”ta kare tana zazzare idanu,dariya ma ta so bashi this time around,babu abinda zai hana shi ci wa su Jamila mutunci gobe duk su ne suka tsorata mishi mata gashi yanzu wankin hula

na neman kai shi dare,a hankali ya sanya tongue yana dan lasan kunnan ta,tare da hura mata iska “it’s okay my love seeing is believing daman ko?Oya let’s give it a try na yarda in har kin ji zafi the moment da muka fara ki fada mun and I will let you be,amman maganar bacci kam babu ita kin taba ganin amarya tai bacci dan first night din su?” Baki ta turo sannan tace “ni dai aa”, shima bakin ya turo sannan yace “Allah Piookie in baki yarda ba zan miki kuka,ba na ce miki in dai kin ji zafi let me know zan ma hakura na bar ki,sai har randa kika shirya”, dan kallon face din shi tayi duk da cikin duhu  ne don tana son ganin yanayin face din nashi kafin ta yarda da shi,ido daya ya kanne mata alamun just say yes pls,kamar me tsoron yin magana tace “Promise?”,saida ya manna mata kiss a goshi sannan yace “Pinky promise Mi Lady”be jira kara jin ta bakin ta ba ya shiga hargitsa ta da salon soyayyar shi me tsayawa a rai,har hakan ya so sanya wa Nadeeya ta yarda kan su Jamila karya suke mata,domin a hankali yake tafiyar da ita,hankalin ta be tashi ba saida ta ji yayi mata adduar saduwa da iyali a kunne tare da fara kokarin nema wa kan shi hanya,a lokaci daya dadin nan ya kau wata iriyar zafi radadi da azaba ce ta ratsa ta lokaci guda,wanda ya sanya ta mancewa da kukan da Nameer yace da ita kar ta yi,ihu ta kwala iya kam

muryan ta ba tare da damuwa da wani zai iya jiyo

su ba kasancewar dare ne,da sauri ta hau fadin “Ya Nameer ya isa haka as you promised kace in na ji zafi you are letting me go,Wlhy akwai zafi”ta kare tana hawaye tare da kokarin ture shi daga jikin ta. inaaa sam Oga Nameer kam be ma ji ta ba balle ta sa ran zai Kyalle ta,domin yayi nisa jin shi ya fara shiga wata sabuwar duniya wace baya fatan barin sa,cikin so da kaunan ta ya cigaba  da abinda ya ke yi,domin wata nutsuwa ce ta zo mishi ta daban da ya samu ya sama wa kan shi hanya,wata irin kukan zafi da azabar da ta ke ji ta sake lokaci daya gwanin ban tausayi,tana ta kokarin ture shi fadi take “Ya Nameer you have broke our promise  wayyo Allah Mama zai kashe  ni ki zo ki taimake ni,Ya Nameer am gonna die pls let me be”.



Ina Nameer  kam yayi nisa baya jin kira shi kanshi baisan halin da yake ciki ba bare yasan halin daNadeeyar  ke ciki  baya iya fidda numfashin sa da kyau tsaban kukan azabar da  Pookie ta sha gaba  daya  har muryar ta ta dashe ida nunta sunyi jazir sun kumbura sintim tana kukan har yanzu amman babu mai jin sautin kukan,a yayin da karfin ta gaba daya ya kare gurin kokarin pushing din shi away from her ,tayi laushi sosai domin hannayen ta banda rawa da kafafuwan ta babu abinda suke,a yayin da jijiyoyin kanta suka firfito,cinyoyin ta kuwa kamar ba a jikin ta suke ba,tuni ta yi  wani irin galabaita,

tana jin azaba na ratsata amman bazata iya taimaka wa kanta  da kanta ba.


Nameer kam ya manta waye shi Karan kan shi,balle kuma Nadeeya da ya ke tare da ita, ya manta matsayin shekarun ta tare da mancewa this is her first time ba,domin ko kadan he wasn’t gentle as he promised ,domin gaba daya mancewa da komai yayi he feels like kamar baya duniyar nan so ba laifin shi bane kasa controlling kan shi yayi,domin iya gyara kam Nadeeya ta sha shi gurin su Mama da Ummu,ta tsumu iya tsumuwa,kwata kwata k'asa gano duniyar da yake  ciki yayi balle ya tuno da alkwarin da yayi mata,haka yayi ta had'a mata wahala da gajiya inda ya dauki  lokaci yana abu daya, sai yanzu ya samu wani irin nannauyan numfashin sa ya fizgota tare da fashe wa da kuka kamar wani karamin yaro, kuka ya rinqayi yana sabbatu cewa ya ke “ Babe Allah ya miki albarka ,thank you so much for making me the happiest man on earth kin gama mun komai,that Bastard ya gama mun komai da ya bar mun budurcin ki,I love you so fucking much Pookiee maizan miki ke ma  ki ji dadi kar yadda kika jiyar da ni dadi? You are indeed my life Pookiee you are finally mine now and forever in sha Allah,I promise to be with you only you no matter the reason or season,I want you to stay with me throughout Madness🥹I don’t want anyone else but you,Allah ya kyauta even if we ever break up we’ll stay best friends until we get back together,you are my home Pookiee and  I want to be be with you till Jannah be our final home,I love you 🥹❤️I will continue to love you till I took my last breath,you are my peace the absolutely love of my life I love you so much Nadeeyaaaaaa ta,thank you so much for giving me the best gift ever,Allahuma barik fiki”ya kare yana me kankame ta a jikin sa kamar wanda ake shirin kwace masa ita,yana jin wata irin kaunar ta da soyayyar ta na dada karuwa a cikin zuciyar shi(Tabbas duk budurwan da tayi hakuri ta rike kan ta har ta kai budurcin ta gidan mijin ta,to Wlhy kima da soyayyar ta da kyar ya ke barin idanun shi,in  ba kuma kin hadu da dan iska mara mutunci ba,amman duk wanda ya san me yake yi,he will respect and love you for that,Budurcin ki shine kima na siyan mutunci a idanu mijin ki my dear,kar ki biye wa rudin duniya ko kuma tunanin ai ba zai gane ba,Wlhy in har ya san me yake yi tsab zai fahimci virgin and wanda ba Virgin ba,so ki rike abun ki ki kai inda za a ga mutuncin ki ba samarin kan titi yan iska yan yaudara ba😒).



Jin babu alamun numfashi tattare da ita ne yayi mugun firgita shi “Oh my God Nameer me ka aikata haka?”shine abinda ya fada wa kan shi tare da saurin kunna switch din dakin ,a take kuwa haske ya bayyana,idanu ya zaro in disbelief a lokacin da ya ga aika aikan da ya yi wa Nadeeya, “Ya salam what’s get into me da na aikata haka,me ya sa ban bita a hankali ba after knowing this is her first time,oh my Allah ,Pookiee pls wake up am sorry okay Wlhy an zan kara ba” shine abunda ya fada a matukar rude yana dan taba kumatun ta,ganin babu almaun tana jin shi ne ya kuma firgita shi a take ta janye ta daga jikin shi tare da saurin saukowa daga gadon,nan ne ya ga yanda jini gaba daya ya bata kan white bedsheet din da ke shimfide akan gadon,da sauri ya fada toilet saida ya wanke jikin shi,sannan ya dauro towel ya fito da ruwa a hannun shi cikin cup ,lokacin guraran 3 ake nema, da sauri ya rungumota kirjin shi ya shiga kiran sunan ta “ Pookiee !Pookiee ta don Allah wake up kin ji am so sorry 😞 ,Allah I promise ba zan sake ba now pls wake up I can’t stand seeing you like this”ya kare kamar zai yi kuka,sai dai ko gizau bata yi ba,hakan ne ya sanya shi shafa mata ruwan da ya ibo a face da kirjin ta domin ya gano suma tayi,saidai a banza don ko motsi bata yi ba,hakan ya so dada tsorata shi amman yayi ta maza ya kara shafa mata ruwan,a karo na uku ne ya ga a hankali ta  sauke wata wahalalliyar ajiyar zuciya,a take wasu hawaye masu zafi suka shiga zubo mata,cike da tsantsan farin ciki ya rungume ta kam tare da sakin mata kiss a goshi, “thank God Baby kin farfado I was damn scared and worried,am so sorry okay ba zan sake ba forgive me pls🥹”ya kare kamar zai yi kuka,bata ce da shi komai ba ya cigaba “Pookiee ta da yardar Allah ke yar Aljanna ce inda Aljannar ki na kasar kafa ta Wlhy na dage miki kawai ki shige ta,daga yau har randa zan koma wa ubangiji na duk wani laifin da za ki mun wanda na sani da wanda ban sani ba na yafe miki shi duniya da lahira,now let’s get you clean ki samu ki huta ko na san kin gaji sosai sai ki samu ki kalli movie din da kike son kallo dazu”ya kare yana me mikewa tsaye dauke da ita a hannun shi kamar wata baby,duk da kasancewar tana jin haushin shi saboda saba alkwarin da ya mata,amman hakan be hana ta jin wata irin sanyin dadi da nutsuwa da kalaman mijin nata,wata irin soyayyar shi ce ta ke ji from nowhere yana ratsa jinin jikin ta,tabbas samun miji irin Nameer a yanzu kam sai an tona domin duk wani nagartar da ya dace yana da ita har ma fiye da haka,hawayen farin ciki ne ke zubo mata domin ta rasa me ta yi wa Allah ya ji dadi har ya azurta ta da samun abokin rayuwa irin Nameer,a take ta ji haushin na shi ma da ta ke ji ya goge inda ta dauki anaiyar zama da shi tare da yi masa biyayya har karshen rayuwar ta, bata fatan abinda zai raba ta da shi.


Tana dauke a hannun shi ya hada ruwan zafi,tare da sanya ta a ciki,yana me riko both hannayen ta ya rungume a chest din shi,sannan ya shiga shafa mata kai, daidai lokacin da ruwan zafin kuwa ya ratsa ta a take ta zabura tare da kwala kara “Wayyo Allah paapiii zafi”ta fadi hawaye na zubo mata,gashin kan ta da ya hargitse ya shiga shafawa a hankali sannan ya shiga hura mata kunne “ na san da zafi Baby doll amman ki daure kin ji you are my fighter my little Champion don’t forget that,in kin dan zauna za ki daina jin zafin kin ji”ya kare kamar zai yi kuka duk sai ya ji wani iri ganin tana hawaye “can you stop crying pls Pookiee I said am sorry ba zan kara ba don Allah ki daina jin haushi na kin ji”baki ta dan turo tare da kokarin tsaida hawayen nata “ni ba haushin ka nake ji ba”ta fada tana dada turo baki gaba, “this one da kike turo mun lips Pookie yanzu kuma in nace zan yi musu kiss ace Nameer is wicked ko?”ya kare tana narai narai da idanu,da sauri ta maida lips din nata tana yan kananun mita kasa kasa,shi dariya ma ta so bashi ita a dole wai masifa take,a haka dai da lalalbi da ban hakuri tare da kallaman soyayya ya samu ya gasata da kyau,sanann ya wanke su tas tare da yi musu wankan tsarki,sannan ya nado ta a towel suka fito,bayan ya daura musu alola,sannan suka fito.


Kan sofa ya aje ta sannan ya yaye zanin gadon tare da hurga shi toilet,sabo ya dauko ya shimfida sannan ya dawo inda take kwance,Mai ya shafa mata tare da sanya mata long sleeping gown me kauri don ji da yayi jikin ta ya fara daukan zafi,kwantar da ita yayi kan gadon sannan a ce mata “a mint princess”da sauri ya fada kitchen ruwan zafi ya dafa cup daya tare da hada mata tea me kauri,sai da ya saisaita daidai sha sannan ya dauro kan tray tare da bottle water da pain reliever and PCM a kan tray sannan ya dawo dakin samu yayi har ta shiga blanket ta rufe idanun ta alamun bacci yana son daukan ta,cikin lallami ya tada ta tare da bata tea din saida ya ga ta sha kusan rabin cup sannan ya bata maganin,rungume ta yayi a kirjin shi don yana son ya dan wuce mata kafin ta koma ta kwanta,kusan 2 mints tayi lamo a jikin shi inda take ji kamar kar ya kwantar da ita,pillow ya gyara mata sannan ya shimfida ta a hankali “Go to bed Pookie ki samu ki dan rintsa kafin asuba na tada ki kiyi sallah,I love you so much okay”ya kare yana manna mata kiss a lips din ta,idanu ta lumshe a hankali ya ji ta ce “ I love you too Paapiii”da sauri ya kalle ta inda tayi saurin boye idanun ta,dariya ya sake tare da shafa kan shi,sannan ya wuce toilet yana jin zuciyar shi sakayau haka ma gangan jikin shi,zanin gadon ya wanke tare da shanyawa sanann ya dauro alola ya fito,sallaya ya hau tare da gabatar da nafila wanda zai iya kiran shi na godiya wa Allah,ya dade yana kirari tare da tsantsan nuna farin ciki da godiyar shi ga ubangijin shi domin ya gama mishi komai,duk wani jin dadin duniya yau ya same shi,a zaune a kan sallaya ya zuba mata idanu yana ta musu adduar samun zaman lafiya da rayuwa ne dadi na har abada aka kira asuba,inda ya tashe ta a nutse tare da taimakon shi tayi alola suka yi sallah inda sai uban shagwaba take zuba mishi,a yayin da shi kuwa ya biye mata domin ko juyi tayi a take zai ce mata me ke mata ciwo,a haka dai suka samu suka maida baccin gajiya suna rungume da juna,bayan ya gama kashe ta da kalaman soyayaya……sai mu ce Asuba ta gari  NADMEER….💃🏻💃🏻💃🏻POOKIEN NAMEERUN MAMA AN ZAMA MACE🥹🤧😂.



    Sassafe washe gari Mama ta sanya aka kawo musu breakfast,don gulma Jameela ce da Muhibba ma suka kawo,inda suka zo da Hanaan wuni suka mata,suna ta tsokanan ta Nameer ko sai nan nan yake yi da ita,sai yamma liss mazajen su suka zo suka tafi da su,inda Nadeeya ta so a bar mata Haanaan,amman Mama tace ba yanzu ba sai ta gama cin amarci,tsokana kam ya sha su gurin su Mujaheed wai yau har wani shunning ya ke😂😂ni ko nace ba dole ba su Nameer an iba gara🤣.


  Sati ta guda yau inda Nameer kullum na cikin tattali da kashe da da madarar soyayya,inda dawowar shi daga gidan Mama ke nan sun gama tattaunawa kan za su dauko Hajiya Rakeeba da Uncle Usman su dawo nan Kaduna don su biyu ne cal a Azare,za su fi jin dadi don suna kusa da Nadeeya da kuma Ummu,Mama ce ma ta fi karfafa zancen don ba wanda zai kaita jin dadi Hajiya in ta dawo kusa da ita matar akwai dadin zama,nan suka tsayar kan a satin nan za ta je da kan ta ta taho da su,in ya so sai a nema wa Uncle usman aiki Hajiya kuma kusa da Mama za ta zauna.


  Saida suka gama cin abinci da Nadeeya sanann ya ke fada mata yanda suka yi da Mama,dadi sosai ta ji nan ta shiga yi musu addua,cike da jin dadi ya rungumo ta tare da amsa wa da Ameen ya Allah,sannan ya ce da ita ta rufe idanun ta,ba musu kuwa ta rufe,kafin ya ce ta bude,Visa ce ya nuna mata nata da nashi na tafiya Umara tare da Dubai wanda Alh Salis ne ya biya musu,haba ihu ta saki tare da yin tsalle ta fada jikin shi sai tukwikuye shi take yi,inda shima sai dariya ya ke yana fadin kar fa ta karya shi,daga hka ya ja ta daki tare da canza salon wasar ta su.


   Nan ko suka hau shiri domin nan da kwana hudu jirgin masu zai tashi,murna kam Nadeeya tayi shi har ta gode wa Allah,burin ta ya ciki ashe daman tana da rabon xuwa dakin Allah,har gida suka je suka wa Alh Salis godiya ana jibi za su tashi,inda ya baiwa Nadeeya 2mil wai tayi guziri tare da cewa ta sanya shi a addua don zabe ya zo,kuma yanzu shi aka tsayar matsayin gwamna bayan mutuwar Sen don,alkwari tayi za ta sanya shi sanann tace in sha Allah ma Nasara ta shi ce,sai kawai suka biya ta Azare dan dauko su Hajiya,tunda Mama bata samu halin zuwa ba,saida aka kai ruwa rana sosai sanann Hajiya ta yarda suka biyo su,domin daman gujewa daura musu nauyi da zancen mutane take amman ita kanta zaman Azaren ya ishe su,don matan gidan kullum cikin habaice habaice suke mata,Mama ba karamin dadi ta ji ba da ganin su Hajiya inda aka kai Usman part din Nameer na da while Hajiya kuma

Na kusa da Mama don cewa tayi bata yarda tayi nesa da ita ba don Mahaifiya ta dauke ta.



  Har Airport su Mujaheed da Mama suka raka su Nameer tare da yi musu Allah ya kiyaye hanya,sosai Nadeeya ta zage gurin rokar yafiya a gurin Allah da isowar su Saudiyya,tayi kuka tayi murna sanann ta nutsu tayi aikin Ummaran ta cikin kwanciyar hankali,wato wata nutsuwa ta musamman ta samu zuwan ta Makka da Madina,haka suka gama satin su guda aka sanya mata hakorin zinarin ta Nameer sai tsokanan ta yake wai yau ta zamo Hajiya Nadeeya Rilwanu Audu Waziri,ita tun randa suka yi aure ta so canza sunan baban ta ta koma using sunan shi,amman yace sam be yarda ba ta bar sunan ta domin duk wanda ya yi using sunan wani bayan ya san ba shi ya haife shi ba kuma yake amfani da sunan a matsayin mahaifi to Aljanna ta haramta a gare shi,daga nan kuma Dubai suka lula inda suka yi wani shakuwar ban mamaki,soyayya suke nuna wa juna su kowa na tattalin junan su,inda duk su biyun sun murje sun kara kiba tare da sheki da kyau na tashin hankali,siyayya kam Nadeeya tayi har ta gaji,domin bayan kudin da Alh Salis ya bata Nameer ma ya jika ta da kudade,kullum suna makale da juna su je nan su je can,wata biyu cur suka dauka suna yawan kasa she sannnan suka hakura suka dawo gida Nigeria,tarba me kyau suka samu inda Mama kamar ta hadiye su don murna,sun yi kyau sosai barin ma Nadeeya banda ta san bata da Mahaifa da sai tace ciki gare ta,amman babu wani ciki tsantsan huta wa ce.


    Dawo war su da sati daya aka yi zabe inda Alh Salis ya lashe kujerar takarar gwamman jahar Bauchi saida duk suka tafi Bauchi don attending liyafar da ya hada,suna hanyar dawo wa ne a labarai suka ji wai wani matashi da aka kama da laifin ta’addan ci me suna Afzaal Allah ya mishi cika wa,sakamakon mutuwar kuwa addabar sauran prisoner’s yayi da mugun wari don ya soma rubewa,shine su kuwa suka kashe dan iska😂🥹ko a jikin Nadeeya,Nameer ne ma mutuwar ta so ba shi tausayi😂😂ni ko nace au ta so ne ma,suna dawowa aka shiga hidimar Auran Uncle Usman inda ya samo wata kyakkyawar Bazawar irin sakin wawan nan makociyar su Ummu ne Allah ya hada jinin su aka daura Aure,suka tare a gidan da Nameer ya siya masa ga shago guda yana da shi na saida shadduna takallma da kayan maza dai haka,kuma Alhamdulilah kasuwar akwai albarka don yana samun budi sosai sosai,bikin shi da sati daya labari ya baza gari har a news a nuna mutuwar da ya girgiza yan kungiyar Brotherhood,domin lokaci guda wuta ya hau ci a Blazed house inda daga Odogwu har kayan tsafin shi suka yi munannan kone wa,da kyar aka fito da shi halittar shi ta canza kala sai cizgan namar jikin shi yake yake cinye wa,tare da wani irin wari,a haka aka kai shi asibti cikin dare ya balle ya gudu mota ta bi ta kan shi ya mutu kurmus,Ba karamin dadi da nutsuwa Nadeeya ta samu ba da ta ji wannan labari domin ko banza wanda ya cuce su yayi sanadiyar barin Daddyn ta a musulunci shima

yayi mutuwar wulakanci, mutuwar Odogwu yayi sanadiyar shiryuwan mutane da dama da ke Brotherhood inda suka koma ga Allah tare da neman yafiyar sa,domin aya ce babba suka gani ganin idanun su,daman Allah ya kan dade yana maka talala sai lokaci daya kuma in ya tashi kama ka sai ka ji a jikin ka,inda wasu kuma da zuciyar su ya Riga ya bushe marasa rabo basu tuba ba,suka shiga neman wani Odogwu domin akwai ire iren shi da yawa da wanda suka ma fishi iskanci saidai fatan me ce Allah ka kare mana imani da mutuncin mu……




          ********************* 12 YEARS LATER 



Abubuwa da dama sun faru masu dadi da marasa dadi a dumbin shekarun nan da suka wuce,a ciki kuwa harda mutuwar Hajiya Rakeeba da tayi a shekarun da suka gabata inda gaba daya mun jijjiga da mutuwar nata,anyi kuka sosai karshe dole muka fawalla wa Allah tare da roka mata rahmar ubangiji domim kam mun yi rashi,Uncle Usman a nashi bangaran zan iya cewa daman me kashin arziki ne,domin a yanzu yana daya daga cikin masu kudin yan kasuwar da ake damawa da su a garin Kaduna,suna zaune lafiya da Matar shi inda Allah ya azurta su da samun haihuwa har yara 4,zumunta ne me karfi tsakanin Ya Umar da Anty Ummu Salma domin a yanzu yana Auran diyar ta ce,wani irin kima da mutunci na yake gani,don tun bayan guduwar da matar shi tayi da dukiyar shi,Mama ce wa tayi ba ruwan ta sai yanzu ya san ya dawo gida,ince nan da mace ya bi duk arzikin shi be amfana musu komai ba sar matar shi saida ta gudu ne yanzu ya san da gida,ni na tsaya tare da baiwa Mama baki domin Allah ya sanya mata kauna ta tana mugun jin magana ta,kafin ya samu Mamar ta yafe mishi inda na sanya Nameer ya bashi jari ke girma ta fara business shima,Hamdiya diyar Anty Ummu ta zo mun hutu ya ganta ya ce yana so haka na shige mishi gaba har aka bashi Auran ta,domin ya mugun yin nadama tare da danasanin bin mace ya aje family din shi gashi rana guda ta gudu ta bar shi,mutanan da ya gudan nan dai su suka zame mishi garkuwa,inda na karbi Aleem yaron shi nace zan rike guna,ita kuma Hamdiya ta rike sauran biyun suna zaune lafiya cikin farin ciki da kaunar juna,inda ita ka ta kuma haifan yara har 3.


  Bangare na da Khadeejat da Anty Bilki tare da diyar ta Amrah kuwa,na so shan wahala a gurin su,don ma Allah ya bani miji me kauna ta tare da gudun bacin Raina ya taka musu burki sosai,saida aka kai ruwa rana sosai kafin na samu Anty Bilki tayi accepting dina domin sila na dai diyar nata tayi aure inda na hada ta da Yayan Zahra Yusuf yaron gidan Alh Salis da ya zame mun Uba na gari ya aure ta,tun Alh Salis na kan mulki shike nan Anty Bilki hankali ya kwanta diyar ta na Auran dan gidan gwamma,dadi na daya yanda na ga suna kaunar junan su,kafin nan hankali na ya kwanta na san dan Nameeru na is safe😂😂Nadeeya kishi,yanzu haka su ma Allah ya azurta su da yara uku,zumunci sosai muke da ita.



   Khadeejat kuwa ya yar mijin ta ce wata me masifan bala’i Allah yayi Auran ta ya mutu,shike nan ta kwashe kayan ta ta dawo gidan Khadeejan da zama inda mijin kuwa irin me shegen son yan uwan sa ne,haba man ta shiga cin uwar Khadeejat tare da matsa mata,ita da gidan ta amman sam bata da halin shan iska ko sakewa,in tayi wa mijin magana yace sam ba haka ba,lokaci daya tayi baki ta lalace ga tsohon ciki,inda karshe ma saida Auran nata ya mutu,gida na na dawo da ita inda nayi ta kwantar mata da hankali a nan ne jikin ta yayi sanyi ta shiga neman yafiya ta,ta ji ma duk ta tsani kan ta akan tsana ta da tayi tun ranar farko,kafin kace me mun dinki da ita ta dawo kamar kawa ta,inda da ta tashi haihuwa aka samu diya mace a take kuwa tace suna na za a sanya wa yarinya,nan ko ranar suna yarinya ta ci sunan Nadeeya ana kiran ta da Little Deeya,sosai na ji dadi tare da yin abun bajinta ranar suna ni da su Jameela da muka yi mugun shakuwa tare da zamo wa Aminan juna,tana yin arbanin kuwa ta koma dakin mijin ta,domin ni da Nameer da Mujaheed muka je har gida muka samu kuka kashe wanann issue din,tun daga rannan Khadeejat ke ganin mutunci na domin wani sakayyar daman tun a duniya ake yin ta,ke daga ya yan ki ya auro mata ki hau tsannan ta ke ga isasshiya ko?ba tare da tunanin ke ma mace ne za ki yi aure wataran kuma a rubuce take duk abinda kayi wa wani sai anyi maka kai ma,Allah dai ya kyauta.



   Bangare na kuwa bani da abinda zan ce sai Alhamdulilah domin Allah ya bani duk abinda na bukata har ma da kari,yanzu haka nayi saukan Al-qur’ani sau uku,inda Nameer ya biya mun na tafi can Sudan na karanci Islamic and Sharia law,sai gashi Nadeeyar da ta taso bata san komai ba cikin kankanin lokaci na wadatu da ilimin addini na ban mamaki,ko da na gama na dawo babbar Makaranta Nameer ya bude mun inda ya zuba mun malamai don koyarwa dadi sosai na ji,domin sai yanzu na san ina rayuwa amman da kamar dabba nake ashe,ilimi haske ne kuma me shi ya fita daban ko daga yanayin maganar shi,Nameer ma ya kammala course din da ya je yayi inda ya dawo Babbar likitan kwakwala kuma zai iya yin tiyata,soyayya da tattali kuwa sai abinda ya faru,domin ni duk wannan fadan da ake tsakanin ma’aurata zan iya ce wa  na wa da sauki,don na Riga da na fahimce shi shima ya fahimce ni,so muna da good understanding a tsakanin mu sanann we learn to Communicate ko wani abu da ya faru,be taba ba nima ban taba kwana da shi a Raina in ya bata mun rai ba,duk da yana iya kan kokarin shi gurin ganin ya bani duk abinda nake bukata amman kun san ance tsakanin halce da hakori ma ana samun tsabani,saidai nawa kam na gode wa Allah don miji na daya ne tamkar da dubu,baya neman mata ni daya tal ni ce a gaban shi.



    

               **************

      Cikin sauri na gama shirya kai na cikin hadaddiyar jar lace me ratsin fari,an yi mun dinkin dogon riga,gaban mirror nake tsaya ina kokarin murza dan kwali na,don na san any moment Paapiii zai iya fitowa da yara ya ce mun sun gama shirya wa,ina kokarin gama daurin ke nan sai ga shi kuwa ya shigo kamshin turaran shi ne ya tabbatar mun da shi din ne,cikin takun nutsuwa ya matso yanda nake tare da kamo waist dina ya manna a jikin shi, “Pookie taaaa” ya ja sunan tawa,dan dariya nayi tare da juyowa kiss na manna mishi a lips din shi don ba karamin kyau yayi mun ba,yana sanye cikin dakkkiyar Maroon shadda wanda ba karamin karban shi tayi ba,a kullum Nameer kara mata kyau da koma young yake kallo daya za ka masa ya burge ka domin irin kyan da ya kara alamun kudi sun zauna,don har dan tumbi ya aje babu wanda zai kalle shi ya dau ya kai 43 years don yanda yake sam girma

bata nuna masa,murmushi yake ta zuba wa Nadeeya wanda ta yi masifan kyau,ta kara cika ta girma tare da kara wani kyau fatan ta ya murje alamun tana

Samun kula daga gurin shi,hips din ta ya kuma fitowa sam bata yarda ta yi kiba ba,don bata isa ba kafin Nameer yace ta masa girma babu wanda zai kalle ta ya dauka ta kai 36 years ita da don ta san yanda take kula da kan ta,murmushi ta zuba mishi sannan tace “Mijin Nadeeya har an gama shiri?”shima murmushin yayi yana rike da ita yace “ke kadai muke jira Pookie,amman kwalliyar nan tayi yawa”ya kare yana kokarin lashe mata jam bakin da ta sanya domin yana bakin cikin tayi kwalliya in za su fita,da sauri tayi baya tare da narai narai da idanu “kai Paapiii I have to look my absolute best a Graduation din Little angel din mu”dariya ya sanya sanann yace “Angel is no more a little baby kar ki manta 15 years take fa,gashi har ta gama secondary school”


   “Gaskiya time flies da wuri wai har Haanaan ta kai 15 kamar ba ita bace yar karamar yarinyar da ke bins duk inda ka je tana wakar “Popoo a auke ni(ko dauke ni)”duk dariya suka sanya sanann yace “yanzu kam

Ke da ita ban san me daukan wani ba”Harara ta galla masa sanann tace “ko aure Pookie tayi ba za ta taba girma a idanu na ba she will forever be my little Angel”ya bude baki zai yi magana ke nan muka ji shigowar Areef da mugun gudu Areefa na biye a bayan shi,sun ci kwalliya cikin kaya masu mugun kyau,da gudu ya fado jiki na “Pookiee !Pookie kin ga Areefa ko wai don na tsinka ribbon din ta by mistake shine take son dukana”da sauri na boye shi a baya na tare da kallon Areefa da idanu ta ya ciko da kwalla,duka duka yaran ba za su wuce 9 years a duniya ba yanzu suke Primary 5 sai wayon tsiya,yaran da suka yi Adopting a shekarun su na uku da aure,inda jinjiraye ne danye aka ba su su,kyawawan yan biyu kallo daya Nadeeya ta ji tana kaunar su haka Nameer,taron suna sosai suka yi musu,inda macen ta ci sunan Hajiya Rakeeba ana kiran ta Areefa don ita ce babba,while na mijin kuma aka sanya masa Abdullahi sunan late father din Nameer ana kiran shi  Areef,tun daga nan Nadeeya ta rungumo su tare da yin Allah ya isa duk sanda wani a family ya fada musu kan ba su bane real parent din su bata yafe ba,inda Mama ma tace ita ma

tayi Allah ya isa,tabbas ba sai ka Haifa da daga cikin cikin ka za ka so shi ba,domin tun daga wanann ranar Nadeeya ke kauna tare da tattalin yaran ta guda uku,hade da Aleem dan gidan Umar.


  “Anty Areefa kukan na miye kuma to”ta fada tana shafa fuskan yarinyar “Pookie ba shi bane”ta kare tana hawaye,daukan ta Nameer yayi don ya tsani kukan yaran,”yi shiru Reefa ta bari mu gama da school din su Adda za mu je shan ice cream banda su Pookiee da Reef”nan ake kuwa ta hau murna,Harara Nadeeya ta watsa mishi domin dalilin shi karfi da yaji sun maida mata suna Pookie har a family kowa Pookie yake kiran ta yanzu,tayi fadan har ta gaji ta bar su.


  Cikin sauri ta yafa mayafin ta,tare da daure wa yarinya gashin da ya barbazu da ribbon sanann ta dauko jaka,duk turaruka ta fesa musu sannan ta kamo hannun su suka fito,a mota suka samu Yaya Aleem zaune yana jiran su,so shiga suka yi suma Nameer ya ja su sai Grays International College,inda suna cikin yan high table sun sami su Jameela a can da su Umar da Khadeejat don sun Riga su isa ma,nan aka fara gudanar da Graduation din cikin tsari da kyan gani,su Haanaan kamar a sace ta yanda tayi mugun kyau yarinya ta zamo budurwa Masha Allah kamanin ta sak da Nameer,saidai ita fara ce ya sanya in Nadeeya tace diyar tace babu me musawa don sai ace hasken ta ta dauko while kama kuma na Paapiin ta.



  An yi shagali sosai inda Haanan ta karbi kyautuka da dama domin yarinya ba dai brain ba,ko da aka tashi bada Overall student ita aka bai wa,tare da wasu lamban yabon,saida Nadeeya tayi hawayen farin ciki domin yanda aka yi ta yabon yarinya tare da fadan kyawawan abubuwa akan ta,tare da yaba wa Mahaifiyar ta kan ta samu tarbiyya me kyau,she just made her feel proud of herself,hotuna sun sha sosai inda Hanaan ke makale da Nadeeya tare da sanya mata Graduation cap din aka dauke ke su a hoto,friends din ta sai zuwa gaishe ta suke don in har ka san Haanan to dole ka san Pookien ta kullum tana cikin labarin Nadeeya,sai around Azahar aka watse inda direct gida suka wuce su duka,don Nadeeya ta dan hada mata karamin party tare da yi mata baking cake me hoton ta,don yanzu kam Nadeeya ba dai iya abinci ba,celebration sosai suka yi aka ci aka sha,sannan suka sha rawa ta karbi gift sosai sanann zuwa la’asar Nameer ya ce su je su shirya za su fita,Jan matan Nadeeya tayi tare da shirya wa cikin wata rantsatsun baby pink din Abaya iri daya duk su ukun,rolling iri daya Nadeeya tayi musu sanann Haanan tayi musu simple Make up,hotuna ta shiga daukan su don ba kara min kyau suka yi ba,saida suka yi la’asar sanann suka fito,Nameer ma ya chakare cikin kaya iri daya Areef da Aleem.



  Sun dan yi tafiya sannan suka iso inda za su,ido ya rufe wa Nadeeya har suka iso bakin wani katon haddadiyar building sanann ya bude mata idon,su Jameela da yaran ta da Muhibba su khadeejat kowa dai ya zo ta gani,cike da farin ciki ta hau sake musu murmushi,almakashi Nameer ya mika mata tare da cewa tayi  cutting rope din,kallon saman building din tayi inda ta ga an rubuta da manyan baki

 

      “NADMEER SPECIAL CLINIC”,da mamaki take kallon shi don sam bata yi tsammanin har ya kammala asibitin na shi ba, “Paapii wat a surprise!”ta fada tana murmushi tare da yanka rope din nan aka hau daukan su hotuna ana tafi,mamaki be gama kashe ta ba saida suka shiga asibitin,domin ba karamin kudi ya zuba ba,yayi kyau sosai sanann ya wadata asibitin da kaya,abun da ya sanya ta kuka da ya mika mata takarddun asibitin akan cewa nata ne ya mallaka mata shi duniya da lahira tayi yanda take so da shi,a take ta kankame shi tana kuka domin bata ma san da wani baki za ta fara gode mishi ba,bayan business da yawa da ta ke juyawa ya dauki sukutum asibti  kuma ya bata,Nameer haske ne a rayuwar ta,nan aka shiga taya ta murna ana ta hotuna da videos sai around 5:30 aka tafi a matukar gajiye suka dawo gida,suna zaune ne akan dinning sun gama cin abinci,ta sanya su Afree kara yi masa godiya tare da masa adduoi,yana jin dadi sosai yanda Nadeeya ta koya wa yaran yi musu addua duk kankantar abinda ya basu,sanann shima yana jin dadin yanda take masa godiya a duk sanda tayi mata kyauta,duk da yana jin ko me zai mata be biya ta kauna da soyayyar da take masa ba,Khadeejat ne tayi sallama da yaran ta har uku,da sauri Deeya ta fado jikin Nadeeya tana “Pookie oyoyo”rungume yarinya tayi domin tana tsananin son ta,tace “my Deeya kun zo ke nan”daga haka suka hau tafi da su Haanan da Areefa, “Ah Khadeejat kune da Magriban nan”zama tayi tare da aje jakar ta 


  “Wlhy Anty Pookie mune fa,kin ga tafiya za muyi da Daddyn su Deeya gobe shine nace bari na kawo miki yaran ki su taya ku zama”harara Nameer ya watsa mata, “wai ni kam Day care ko Orphanage kuka maida gidan nan duk sanda kuka gaji da yaran ku sai ku kawo wa mata na gata uwar son yara ko?to maza tattara kayan ki in ba za ki da su ba ki gaisu gidan Uncle usman,ko gida Ya Umar mana sai gida na” baki ta turo tace “Kai ya Nameer kowa dai ya san Anty Pookie akwai ta da son yara(kun san wanda be taba haihuwa ba haka yake da son yara🥹),sanann duk inda zan kai su babu inda za su sake su ji dadi kamar gidan nan”


  

“Ba shakka to maza ni dai ki dauke wanann Rabbits din naki ku tafi tare ko kuma ki kai su wani gurin don mu ma nan gobe tafiya za muyi”


  “Paapii tunda ta kawo su ba duk sai mu tafi da su ba”idanu ya zaro yace “Kee Nadeeya!!kina da hankali kuwa?Amarci za mu kara ci fa sabida ga ki kin fi kowa son yara sai mu tafi da su ko”duk dariya suka snaya inda Khadeejat kam tace ta kawo su ba za kuma ta koma da su ba,babu yanda Nameer be yi ta kwashe yaran ta ba amman tace sam bata san zance ba,domin shi fa yana son ya samu some time da matar shi ne su su dan more ya sanya ma ya musu Visa zuwa Paris,amman ya ga alaman Nadeeya bata gane lisaafin,sallama ta musu sanann ta gudu abun ta,cika tam Nameer yayi tare da wuce wa dakin shi,ganin haka ne ya sanya Nadeeya bin shi,saida ta yi da gaske ta shawo kan shi don Nameer din rikici gare shi kamar wani karamin yaro,inda ya ke ce da ita tafiya fa za su yi ta karbi yara,nan ta ce da shi to why not su kwahe su kab su kai gidan Mama ajiya sai sun dawo,daman sun kwana biyu ba su je mata ba,rungumo ta tayi tare da yi mata kiss a wuya “That’s why I love you my Pookiee”murmushi tayi tare da kwanta wa a kirjin shi sanann tace “Ya Nameer daman gobe ne muke da haduwa da Directors din da na baka labari suna sun suyi film din UBANA NE KO KISHIYA TA so zan je na basu labari su san yanda za su tsara film din don zai ja hankulan mutane da dama”da sauri ya dago fuskan ta tare da ce wa “Ban yarda ba,Pookiee ba na ce a bar maganar labarin UBANA NE KO KISHIYA TA BA,domin duk sanda aka tashi bada labarin nan sai kin yi kuka,ni kuma na dauka wa Hajiya alkwarin ba zan taba barin kiyi kuka ba,besides wanann labari no matter bad he is he is still my father In law don haka don Allah a bar mun Senator Rilwanu Audu waziri ya kwanta lafiya”ya kare yana Jan hancin ta cike da soyayya ita ma hancin na da ta ja,wato Nameer ya hadu ta ko wani fanni,duk da abinda Daddy ya aikata har yau yana girmamma shi don ko da suka dauk

wato Nameer ya hadu ta ko wani fanni,duk da abinda Daddy ya aikata har yau yana girmamma shi don ko da suka dauko su Areef ya so a sanya masa sunan Rilwanu ita ce ta ki yarda don ance mutum ya kan dauki halin wanda aka yi wa takwara da shi,da kan shi ya shirya ta Itama ta taya shi shirya wa sanann suka fito tare da kiran yaran don tafiya gidan Mama,a babban mota duk suka tafi Nadeeya na nan da yaran(Nadeeya uwar yara),hakika nin Gaskiya Nameer haske ne a rayuwar ta,da kuwa ta rasa shi da tayi babban asara,ya zamo mata Uwa Uba Miji Aboki,Dan uwa da kuma Masoyi na har abada,lokaci ya tafi sosai amman har yau in ta kalle shi sai ta ji kamar yanzu ne ta fada soyayyan shi,tabbas haka Allah ke abun shi in ya so sai ya hada ka da mutum daya tamkar ta dubu,in ta duba rayuwar ta na baya cike yake da dumbin ta shin hankali,tare da ban tausayi,amman lokaci daya Nameer ya shigo ya canza komai,tana mishi don da ita kan ta bata yi wa kan ta,domin ya sadaukar da komai na shi don Sanya ta farin ciki,gashi silan sa ta samu babban family inda kowa sai nan nan ya ke yi da ita,babu abinda za ta iya ce wa ga Allah sai Alhamdulilah da irin wannan sauyin rayuwa da ya bata,yau ita ce Nadeeya Audu Waziri ta cika shekaru 12 da aure tare da mallakan yara har hudu me ya fi wanann?tayi alkwarin tsaya wa gurin basu kula da tarbiyan da ita ta rasa tun tana yarinya,a hankali ya murza hannun ta don ganin tayi nisa a tunani “What’s up with you Baby girl”ya fada yana smiling,itama murmushi tayi sannan tace “ina kawai tuno rayuwar mu na baya ne,ko a next life dina Ya Nameer I want you to become my Husband,thank you so much for making me matar da nake yanzu,I love you so very much🥹❤️”ta kare tana wa hannun shi kiss,murmushi ya sake mata yana me jin kaunar ta na kara samun guri a zuciyar shi sanann ya yi kissing back hannun ta tare da fadin “I love you more Nadeeeyatun Nameerun ta,Maman yara na,Pookie ta kuma matar Aljanna ta in sha Allah”,da sauri yaran suka shiga tafi domin yanda iyayen nasu ke so tare da tattalin junan su na matukar burke su “Awnnnn we love you both Pookiee and Paapiii”suka fada out of excitement,dariya duk suka sake don shaf sun mance da yaran na cikin motan….nan nima na juyo tare da fadin I LOVE YOU SO MUCH MY FANS………. 



    Alhamdulilah !!Alhamdulilah !!Alhamdulilah!! Duka duka anan na kawo karshen wanann labarin me suna UBANA NE KO KISHYA TA!!



    Duk kan yabo da godiya sun tabbata ga ubangijin sammai da kasaai da ya bani ikon fara labarin nan lafiya na kuma kare shi a yau lafiya ina me rai da lafiya🥹abinda na rubuta daidai Allah ka bani lada,wanda nayi kuskure Allah ka yafe mun,ka sa kuma mutane sun amfana da Alkhairi da daidan da ke ciki labarin nan,kuskuren ciki da rashin daidai Allah ka bamu ikon gyara wa baki daya…


    Godiya ta musamman ga Sweet lovely sister na coz she always stood by me and make sure that I believe in my self,I love you so much Yar baka baka ta🥹❤️for supporting and pushing me to give my best.


   Masoyiya (Mum Sayyid)I started this journey without you,but mun zo mun hadu along the line,thank you so much always encouraging me tare da nuna mun I can do this,don at times ita ke pushing dina nayi typing ko ban so ba❤️


Girlfriend (Jameelatu hamza),My Sunaina(Ameenatu Abubakar),Best best (Khadeeja Zakriyya)🥹❤️you guys have been there with me tun ina rubuta muku Shirmen story na a exercise book muna shan Agwaluma da chocolates ina karanta muku😂😂❤️haka za ku ta rokon in rubuta ka a tashi daga sch I love you much guy’s without you 3 da yanzu na bar rubutu.


  

   Ummu Sadiq (CEO),thank you so much for correcting each and every one of my mistakes Allah ya saka da Alkhairi ya bar zumunci❤️


   Zahra Auta

Anty Sadiya(Mrs BBK)

Mom twins

Ummu Samir

    

      Alkhairin Allah ya isar muku tare da cigaba da tsaya mana a rubutun mu🥹❤️


  

  Ummu Mansur’s Novel fan’s na gode sosai da support din da kuka bani tun farkon book din nan har karshe, Anty Admin ita without you ni da book din nan ba kowa ba ne ya na sadaukar miki da whole book din,Allah ubangiji ya yi wa su Mansur Albarka sannan ya tsaya miki a duk inda kike🥹❤️


  

  My group members 

Aishatu ummulkhair(my Sweetheart)

Yar mommyn ta

My Fanash 

Ummu iman 

Nanan oga

Maman Humaira

Maman ummiey 

Babyn baby

Maman Mursheed 

Maman Affan

Daughter 

Momcey ta 


  Kai da ma sauran ku..Alkhairin Allah ya isar muku a duk inda kuke,yanda kuka yi hakuri kuka kasance tare da ni tun farkon labarin nan har zuwa karshe Allah ya so ku ya kasance tare da duk har karshen rayuwar ku,Meemarh na godiya da kaunar ku kare ta nima ina muku so da kauna sabida Allah🥹❤️


    Fanash,Ummu Iman,Babyn baby,Nanar Oga yau Anty Meemarh za ta yi bacci me kyau ba tare da kun dame ni da kwala kiran dare don Allah ayi mana Update ba😂🤧



  Masoya na wanda na sani da wanda ban sani ba na gode sosai da kaunar da kuka nuna wa littafi na,komai yayi farko akwai karshe am sorry for the delay kun san kana naka ne Allah na nashi,ina yi wa kowa fatan Alkhairi,sai mun hadu a sabon book dina  me suna WASA DA SO!! wanda zai zo muku nan da ba da dade wa ba🥰🥰…………….


No comments